Sashe 5
Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya juya yana kiran Larai don tazo
ta kwashe barin da aka yi yana kumna
gayawa Hajiya.
Durkusawa nayi saboda murdawan
da yake yi mun da irin azabar da na
ke sha.
Ahmad yana shigowa tare da
Hajiya daidai lokacin dá naji kamar
fitsari yana zubo mun.
Hajiya ce ta fara salati tana karawa,
wannan wane irin mummunan
faduwa ki ka yi 'yannan. Ai jini nake
gani."
*Jini Hajiya?" Ahmad ya fadi
daidai ya kara matsowa inda nake
cikin sauri ya dauke ni zuwa mota
muka tafi asibiti.
Jinin da ya zuban ya yi yawa, don
haka cikin ya lalace wankin ciki aka
yi mun aka sallamo ni da magunguna
58
muka dawo gida wajen karfe sha
biyun dare saboda cewar da Ahmad
yayi a sallamo ni mu dawo gida.
Cikin dan kankanin lokacin da abin
ya faru nayi wani irin ramewa saboda
bakar azabar da na sha.
A daren Hajiya tazo duba ni ta
kuma hado mun da abincin da ta girka
mun, tuwo miyar kuka ta ce na ci na
sha maganina.
Ba karamin jjjaga Ahmad ya yi da
barin da nayi ba, don kuwa shi mutum
ne mai son haihuwa.
A yanzu kuma Zinatu ita ce
karamar 'yarshi, wacce a bana ya ce
mun shekarunta takwas.
Hakanne yasa ni daurewa nayi
niyyar wartsakewa duk kuwa da abin
da ke damuna a zuciyata.
59
Da safe ma Hajiya ta shigo ta
gaishe ni, haka Larai da Bala direba
de matarshi sai Zubairu.
Wajen karfe tara ne Ahmad ya sake
shigowa ya kalle ni, ganin ina zaune a
kan gadon "Har kina iya tashi?
Na dan yi murmushi na ce, "Ai naji
sauki. Ya zuba mun ido tare da
kamo hannayena duka biyu ya rike a
nashi hannuwan yana dan matsawa.
Yace, Kin dai daure Hauwa'u ba
kin ji sauki ba, ki taya ni addu'a
Ubangiji ya ba mu. wasu masu
albarka." Na ce, "To amin."
Yayi shiru zuwa wani lokaci ya ce
"Ina son zama da ke Hauwa'u. Ina
rokonki ki kara hakuri da duk wata
matsala da ki ke fuskanta a tare da ni
ko wai nawa."
60
Ban fahimci inda maganar tashi ta
dosa ba, amma sai na dan yi
murmushi kawai.
Duk kokarina bai wuce na ganin na
nunawa Ahmad cewa naji sauki ba.
Na dan daure na yi kwalliya na sanya
doguwar riga na fito ina lallabawa
zan shiga dakin, shi ne naji maganar
Zubair.
Kamewa nayi na kasa shiga.
"Na rantse Baba naga lokacin da
Ziradat ta saka ai ba zan yi maka
karya ba, amma ina gaya maka ne
don kada wata rana suyi abinda yafi
haka."
Ahmad ya ce "To kai Zubairu me
yasa da ka ganta ba ka ce komai ba?"
Ya ce, "Ai ni ban san da wata
manufa tayi ba. Na juyo. na dawo
dakina saboda na fahimci wani
61
muhimmin abu ne duk da dai ban san
ko menene ba.
Wajen La'asar na rinka jiwo ihun
yaran, sai dai n1 kam ban je ba, don
ban san abinda yake faruwa ba kumna
babu ruwana ko ma menene.
A dakina yau ma na kwana sai dai
tare da Ahmad.
Washegari matar Bala direba ta
dawo gaishe ni tana zaune a kan
kujera muna yar hira saboda
mutuntani da matar take yi da kuma
kokarin shiga sabgata yasa nake dan
hira da ita.
Don ba za ta wuce sa'ata ba.
"Oh ni 'yasu, wadannan yara kuma
ashe sune."
Na ce, Su ne kamar ya ya?
Wadanne yara? " Nayi mata
tambayoyin a tare kuma lokaci daya.
62
"Au, jiya ba ki jiyo ihunsu ba? Ai
Baban ne ya yi musu duka ba na wasa
ba, don wansu yaje ya gaya mishi
cewa ita wannan shu'umar ita ce ta
saka miki abu ki ka fadi."
Nayi shiru ina kallonta saboda jin
abin da take fada, abin dai ya yi
matukar bani mamaki, sai dai duk da
haka ban tanka ba don tsoron halin
mutane.
Shiru nayi a kwance ina tunani me
nayi wa wadannan mutane haka?
Ahmad ya shigo ya nemi wuri kusa da
ni ya zauna.
"Ya ya Amarya me ke faruwa ne?"
Ban ce mishi komai ba sai zuba
mishi ido da nayi. Ya jawo ni jikinshi
yana cewa.
63
"Kin san fa tunda wannan ya fita to
aiki ya koma baya, sabon zubi kumna
zamu yi yanzu."
Daurewa nayi na ce mishi "To,
amma dai ai ba yanzu ba ko?" Ya ce,
"Eh to, ko gobe tunda Likita ya ce
bari ba a wuce kwana uku, ko ba haka
ba?"
Wartsakewa nayi saboda
farantawa maigidan rai na nuna mishi
naji sauki don hankalinshi ya kwanta.
Haka nan kuma abubuwa sun
matukar yi mun sauki ba kadan ba,
tunda dai yanzu zan iya ganin Ziradat
a hanya ba tare da ta ja mun tsaki ba.
Abin har mamaki nake yi, wai 'yar
karamar yarinya mai shekaru goma
sha uku ce ta ke irin wannan abin.
64
Lokacin komawan Zubair
Makaranta ya yi, don dama hutun
nasu ba mai yawa ba ne.
Tambayar shi nayi abinda yake so
nayi mishi na tafiya. Ya yi shiru yana
'yan tunane-tunane.
Ya ce, Ai ba na so ne Baba ya ji
zai ce na cika fitina, tun da ana siya
mun komai."
Na ce, "To fada mun ba zan bari ya
ji ba." Ya ce, "To ina son kek irin
wanda ki ka yi da sallah."
Na ce, "Sai me?" Ya ce, "Ko shi
kadai aka yi mun Aunty na gode. Na
ce, "To shi kenan.
Cefane sosai nasa aka yi na kira
Larai muka yi aikin tare. Cincin nayi
mishi mai yawa, nayi mishi kek na
sassaka su a leda daidai saboda kada
su bushe tunda Makaranta ce.
65
Sai dambun naman da nayi mishi
cikin babbar roba fara.
Ana gobe zai tafi na ba shi tsalle ya
rinka yi kamarzai yi ya ya don murna.
Sallamaa muka yi mai dadi ya kumaa
roke ni idan Babanshi zai je mishi
visiting na raka shi muje tare, na ce
to.
Da yamma ne Ahmad ya shigoo
bayan ya kai shi Makaranta ya dawo
na kawo mishi ruwa mai sanyi yasha
sannan ya yi hamdala ya ce "Zubairu
ya ce na sake yi miki godiya."
Ban saurare shi ba kicin na koma
na hado mishi fruit salad na kawvo
mishi, ya karba yana sha ya ce "To ni
ina nawa dambun naman?"
Na kalle shi na gane da gaske yake
yi na ce "Ban ajiye maka ba saboda
ya ce ba ya so ka sani."
66
Ya dan yi murmushi ya ce, "Haka
ya gaya mun, to amma kuma sai ya
kasa yin shirun ya fada mun da
kanshi.
Kin san alheri komai kankantarshi
yawa ne da shi, to ballantana irin
wannan."
Na ce, "Kai dai don Allah bari zuga
ni, ai ba da kudina nayi ba a cikin
cefanen gida na saka."
Ya ce, "Ko ma dai ya ya ne ai
cefanen gida idan wata ce ba za ta yi
ba, ina so kuma na gaya miki cewa ba
Zubairu ki ka yi ma ba ni ki ka yi ma,
zan kuma tabbatar. ban mance
alherinki ba."
Komawar Zubairu Makaranta sai
abubuwwa suka sake rincabewa. Ashe
dama sun bari ne don sun gane yana
kai kararsu wurin Babansu.
67
To yanzu ba ya nan sun ci gaba
daga inda suka tsaya. Sai dai Ziradat
ta riga ta tsorata saboda dukan da
Baban ya yi mata a kaina.
Zainab ce take nuna mun salo iri-iri
na rashin kunya da kuma nuna 1sa,
amma na danne zuciyata ko kallon
iya-shegenta bana yi.
A daidai nan ne kuma wani sabon
laulayin ya kama ni, watanni uku
bayan barin da nayi.
Amma a hakan na tsaya tsayin daka
wajen ganin na gamsar da mijina duk
wata lalura tashi.
Kullum nayi mishi maganar zuwa
gida sai ya yi mirsisi ya hana ni, ya ce
ba na yi mishi adalci da yana gari
amma sai na tsallake hidimominshi na
tafi gidanmu.
68
Na ce, To ai kai da rana kana
kasuwa, da daddare ne ka ke dawowa
gida ka bar ni mana naje da rana na
dawo kafin lokacin dawowarka gida?
Sai ya ce, Wai a'a yafi son idan ya
tuna ni a lokacin da yake kasuwa ya
rinka tuna ni a cikin gidan shi ina
harkokina.
Kallon Ahmad kawai nayi nayi
murmushin takaici, amma a raina
tunda ba ni da abin yi a kai, ba na
musu dashi koda kuwa hukuncin da
ya yanke bai yi mun dadi ba.
Hakanne yasa da yazo tafiya Kano
gaida kanin Babanshi da ya yi rashin
lafiya, tafiyar kwana daya sai na tuna
mishi da zuwana gida.
Ya ce, Ba ki fa da lafiya Hauwa'u.
Na dakatar da hada mishi kayan da
69
nake y1, na ce "Haba yallabai, ba
haka muka yi da kai ba fa."
Ya ce, "Eh na sani, amma ai
wannan karon tafiyar tawa ba mai
jimawa ba ce, kwana daya zan yi."
Na ce, To ni ai tawa tafiyar wuni
ce. Shiru yayi sai da ya fita wurin
Hajiya ya dawo sannan ya ce naje
gidan yau Bala zai kai ni."
Nayi tsalle don murna ya ce, "To
kin gani ba. Nayi-nayi da ke ki rinka
kula da irin wadannan abubuwan kin
ki kanmar kin mance da abinda ya
same ki wancan karon."
Ahmad yana tafiya nayi shirina tsaf
na rufe sashena na fito na shiga wurin
Hajiya don nayi mata sallama.
Sannan na fito harabar gidan na
samu Bala har ya yi warming din
mota ni yake jira.
ta kwashe barin da aka yi yana kumna
gayawa Hajiya.
Durkusawa nayi saboda murdawan
da yake yi mun da irin azabar da na
ke sha.
Ahmad yana shigowa tare da
Hajiya daidai lokacin dá naji kamar
fitsari yana zubo mun.
Hajiya ce ta fara salati tana karawa,
wannan wane irin mummunan
faduwa ki ka yi 'yannan. Ai jini nake
gani."
*Jini Hajiya?" Ahmad ya fadi
daidai ya kara matsowa inda nake
cikin sauri ya dauke ni zuwa mota
muka tafi asibiti.
Jinin da ya zuban ya yi yawa, don
haka cikin ya lalace wankin ciki aka
yi mun aka sallamo ni da magunguna
58
muka dawo gida wajen karfe sha
biyun dare saboda cewar da Ahmad
yayi a sallamo ni mu dawo gida.
Cikin dan kankanin lokacin da abin
ya faru nayi wani irin ramewa saboda
bakar azabar da na sha.
A daren Hajiya tazo duba ni ta
kuma hado mun da abincin da ta girka
mun, tuwo miyar kuka ta ce na ci na
sha maganina.
Ba karamin jjjaga Ahmad ya yi da
barin da nayi ba, don kuwa shi mutum
ne mai son haihuwa.
A yanzu kuma Zinatu ita ce
karamar 'yarshi, wacce a bana ya ce
mun shekarunta takwas.
Hakanne yasa ni daurewa nayi
niyyar wartsakewa duk kuwa da abin
da ke damuna a zuciyata.
59
Da safe ma Hajiya ta shigo ta
gaishe ni, haka Larai da Bala direba
de matarshi sai Zubairu.
Wajen karfe tara ne Ahmad ya sake
shigowa ya kalle ni, ganin ina zaune a
kan gadon "Har kina iya tashi?
Na dan yi murmushi na ce, "Ai naji
sauki. Ya zuba mun ido tare da
kamo hannayena duka biyu ya rike a
nashi hannuwan yana dan matsawa.
Yace, Kin dai daure Hauwa'u ba
kin ji sauki ba, ki taya ni addu'a
Ubangiji ya ba mu. wasu masu
albarka." Na ce, "To amin."
Yayi shiru zuwa wani lokaci ya ce
"Ina son zama da ke Hauwa'u. Ina
rokonki ki kara hakuri da duk wata
matsala da ki ke fuskanta a tare da ni
ko wai nawa."
60
Ban fahimci inda maganar tashi ta
dosa ba, amma sai na dan yi
murmushi kawai.
Duk kokarina bai wuce na ganin na
nunawa Ahmad cewa naji sauki ba.
Na dan daure na yi kwalliya na sanya
doguwar riga na fito ina lallabawa
zan shiga dakin, shi ne naji maganar
Zubair.
Kamewa nayi na kasa shiga.
"Na rantse Baba naga lokacin da
Ziradat ta saka ai ba zan yi maka
karya ba, amma ina gaya maka ne
don kada wata rana suyi abinda yafi
haka."
Ahmad ya ce "To kai Zubairu me
yasa da ka ganta ba ka ce komai ba?"
Ya ce, "Ai ni ban san da wata
manufa tayi ba. Na juyo. na dawo
dakina saboda na fahimci wani
61
muhimmin abu ne duk da dai ban san
ko menene ba.
Wajen La'asar na rinka jiwo ihun
yaran, sai dai n1 kam ban je ba, don
ban san abinda yake faruwa ba kumna
babu ruwana ko ma menene.
A dakina yau ma na kwana sai dai
tare da Ahmad.
Washegari matar Bala direba ta
dawo gaishe ni tana zaune a kan
kujera muna yar hira saboda
mutuntani da matar take yi da kuma
kokarin shiga sabgata yasa nake dan
hira da ita.
Don ba za ta wuce sa'ata ba.
"Oh ni 'yasu, wadannan yara kuma
ashe sune."
Na ce, Su ne kamar ya ya?
Wadanne yara? " Nayi mata
tambayoyin a tare kuma lokaci daya.
62
"Au, jiya ba ki jiyo ihunsu ba? Ai
Baban ne ya yi musu duka ba na wasa
ba, don wansu yaje ya gaya mishi
cewa ita wannan shu'umar ita ce ta
saka miki abu ki ka fadi."
Nayi shiru ina kallonta saboda jin
abin da take fada, abin dai ya yi
matukar bani mamaki, sai dai duk da
haka ban tanka ba don tsoron halin
mutane.
Shiru nayi a kwance ina tunani me
nayi wa wadannan mutane haka?
Ahmad ya shigo ya nemi wuri kusa da
ni ya zauna.
"Ya ya Amarya me ke faruwa ne?"
Ban ce mishi komai ba sai zuba
mishi ido da nayi. Ya jawo ni jikinshi
yana cewa.
63
"Kin san fa tunda wannan ya fita to
aiki ya koma baya, sabon zubi kumna
zamu yi yanzu."
Daurewa nayi na ce mishi "To,
amma dai ai ba yanzu ba ko?" Ya ce,
"Eh to, ko gobe tunda Likita ya ce
bari ba a wuce kwana uku, ko ba haka
ba?"
Wartsakewa nayi saboda
farantawa maigidan rai na nuna mishi
naji sauki don hankalinshi ya kwanta.
Haka nan kuma abubuwa sun
matukar yi mun sauki ba kadan ba,
tunda dai yanzu zan iya ganin Ziradat
a hanya ba tare da ta ja mun tsaki ba.
Abin har mamaki nake yi, wai 'yar
karamar yarinya mai shekaru goma
sha uku ce ta ke irin wannan abin.
64
Lokacin komawan Zubair
Makaranta ya yi, don dama hutun
nasu ba mai yawa ba ne.
Tambayar shi nayi abinda yake so
nayi mishi na tafiya. Ya yi shiru yana
'yan tunane-tunane.
Ya ce, Ai ba na so ne Baba ya ji
zai ce na cika fitina, tun da ana siya
mun komai."
Na ce, "To fada mun ba zan bari ya
ji ba." Ya ce, "To ina son kek irin
wanda ki ka yi da sallah."
Na ce, "Sai me?" Ya ce, "Ko shi
kadai aka yi mun Aunty na gode. Na
ce, "To shi kenan.
Cefane sosai nasa aka yi na kira
Larai muka yi aikin tare. Cincin nayi
mishi mai yawa, nayi mishi kek na
sassaka su a leda daidai saboda kada
su bushe tunda Makaranta ce.
65
Sai dambun naman da nayi mishi
cikin babbar roba fara.
Ana gobe zai tafi na ba shi tsalle ya
rinka yi kamarzai yi ya ya don murna.
Sallamaa muka yi mai dadi ya kumaa
roke ni idan Babanshi zai je mishi
visiting na raka shi muje tare, na ce
to.
Da yamma ne Ahmad ya shigoo
bayan ya kai shi Makaranta ya dawo
na kawo mishi ruwa mai sanyi yasha
sannan ya yi hamdala ya ce "Zubairu
ya ce na sake yi miki godiya."
Ban saurare shi ba kicin na koma
na hado mishi fruit salad na kawvo
mishi, ya karba yana sha ya ce "To ni
ina nawa dambun naman?"
Na kalle shi na gane da gaske yake
yi na ce "Ban ajiye maka ba saboda
ya ce ba ya so ka sani."
66
Ya dan yi murmushi ya ce, "Haka
ya gaya mun, to amma kuma sai ya
kasa yin shirun ya fada mun da
kanshi.
Kin san alheri komai kankantarshi
yawa ne da shi, to ballantana irin
wannan."
Na ce, "Kai dai don Allah bari zuga
ni, ai ba da kudina nayi ba a cikin
cefanen gida na saka."
Ya ce, "Ko ma dai ya ya ne ai
cefanen gida idan wata ce ba za ta yi
ba, ina so kuma na gaya miki cewa ba
Zubairu ki ka yi ma ba ni ki ka yi ma,
zan kuma tabbatar. ban mance
alherinki ba."
Komawar Zubairu Makaranta sai
abubuwwa suka sake rincabewa. Ashe
dama sun bari ne don sun gane yana
kai kararsu wurin Babansu.
67
To yanzu ba ya nan sun ci gaba
daga inda suka tsaya. Sai dai Ziradat
ta riga ta tsorata saboda dukan da
Baban ya yi mata a kaina.
Zainab ce take nuna mun salo iri-iri
na rashin kunya da kuma nuna 1sa,
amma na danne zuciyata ko kallon
iya-shegenta bana yi.
A daidai nan ne kuma wani sabon
laulayin ya kama ni, watanni uku
bayan barin da nayi.
Amma a hakan na tsaya tsayin daka
wajen ganin na gamsar da mijina duk
wata lalura tashi.
Kullum nayi mishi maganar zuwa
gida sai ya yi mirsisi ya hana ni, ya ce
ba na yi mishi adalci da yana gari
amma sai na tsallake hidimominshi na
tafi gidanmu.
68
Na ce, To ai kai da rana kana
kasuwa, da daddare ne ka ke dawowa
gida ka bar ni mana naje da rana na
dawo kafin lokacin dawowarka gida?
Sai ya ce, Wai a'a yafi son idan ya
tuna ni a lokacin da yake kasuwa ya
rinka tuna ni a cikin gidan shi ina
harkokina.
Kallon Ahmad kawai nayi nayi
murmushin takaici, amma a raina
tunda ba ni da abin yi a kai, ba na
musu dashi koda kuwa hukuncin da
ya yanke bai yi mun dadi ba.
Hakanne yasa da yazo tafiya Kano
gaida kanin Babanshi da ya yi rashin
lafiya, tafiyar kwana daya sai na tuna
mishi da zuwana gida.
Ya ce, Ba ki fa da lafiya Hauwa'u.
Na dakatar da hada mishi kayan da
69
nake y1, na ce "Haba yallabai, ba
haka muka yi da kai ba fa."
Ya ce, "Eh na sani, amma ai
wannan karon tafiyar tawa ba mai
jimawa ba ce, kwana daya zan yi."
Na ce, To ni ai tawa tafiyar wuni
ce. Shiru yayi sai da ya fita wurin
Hajiya ya dawo sannan ya ce naje
gidan yau Bala zai kai ni."
Nayi tsalle don murna ya ce, "To
kin gani ba. Nayi-nayi da ke ki rinka
kula da irin wadannan abubuwan kin
ki kanmar kin mance da abinda ya
same ki wancan karon."
Ahmad yana tafiya nayi shirina tsaf
na rufe sashena na fito na shiga wurin
Hajiya don nayi mata sallama.
Sannan na fito harabar gidan na
samu Bala har ya yi warming din
mota ni yake jira.