← Book details Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 10

Sashe 6

Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

70
Sai kawai ga Zainab da Ziradat sun
fito su ma za su je unguwa. Kai tsaye
suka nufi motar za su shiga.
Bala ya ce, "A'a Zainab kada ki
shiga motar nan, Hajiya zan kai
unguwa a ciki."
Tayi mishi wani wawan kallo.
Akwai wata HHajiya nc a gidan nan
baya ga wacce dama can na sani? Ina
tsaye a gefe ina kallonsu ban tanka
ba.
Ita dai Ziradat ta dan nutsu duk da
dai nasan ba wani hankali ta kara ba.
Zainab ce da Bala dircba suke ta
jayayya ya shiga mota ya tuka ya ki,
ita kuma ta fita a motar ta ki.
Ziradat fita kije ki kira mun
Hajiya. Ba a wani jima ba sai ga
Hajiya ta iso wurin cikin hijabinta.

71
"Lafiya?" Ta kalli Bala dircba. Nan
da nan ya fara yi mata bayanin abinda
ke faruwa.
Hajiya ta kalli Zainab ta ce, "To ke
Zainaba ku shiga mana idan aka
sauke ta a gidansu sai a kai ku taku
unguwar ba shi kenan ba."
Nan take ta fashe da kuka ita
gaskiya ba za ta shiga mota da ni ba,
bayan ba sonsu nake yi ba.
Na kalli Bala na ce, "Bala idan ka
kai su ka dawo kayi mun magana.
Ya ce,"To Hajiya. Na dawo na shiga
dakina na zauna.
Ban san yadda zan yi da yarannan
ba, abinda na sani shi ne bana kin su.
Na zauna kato-kato ina jiran Bala ya
dawo da su Zainab mu tafi bai dawo
gidan ba sai wajen karfe hudu da rabi.
72

Har sashena ya iso yayi sallama, na
ce "Kun dawo Bala? Ya ce, "Eh
Hajiya kiyi hakuri zai fara yi mun
bayani na ce a'a Bala babu komai je
ka kawai."
Ya tsaya zai ci gaba da ba ni
hakuri, na ce ba fushi nayi ba Bala,
amma kaga gidanmu zan je yanzu
kuma yamma ta riga tayı, ya ce to
Hajiya na gode.
Washegari ba ni da halin fita tunda
Ahmad zai dawo gida a ranar, don
haka tashi nayi don nayi mishi shiri.
Da aikin wurinshi na fara. Na
wanke bayan-gida, nayi shara ko ina
fes sannan na canza labilayen dakin
gaba daya na zuba wasu na kira mai
wanki na ba shi.
Na sake shimfida ko ina ya yi kal,
sai kamshi kawai. Na dawo sashena

73

na shirya mishi abinci na yi mishi
fruit salad sannan na shiga bandaki
nayi wanka nayi kintsi na sosai.
Nayi kwalliya mai kyau ta riga da
siket, ina gamawa ko sai ga isowar
motarshi cikin gidan.
Sai da ya shiga wurin Hajiya kamar
yadda ka'idar shi yake, sannan ya
shigo wurina da gudu na isa inda yake
na rungume shi ina mishi oyoyo.
Yana dariya ya ce, Anya Hauwa'u
ce kuwa ba canje aka yi mun ba da ba
na nan?
Na ce, Canje kuma 'Yallabai? Ya
ce, Eh mana naga ne sai wani
danyacewa ki ke yi kina dawowa 'yar
karamar yarinya.
Sashen shi muka shiga don ya yi
wanka, yana ganin irin gyaran da na
yi wa wurin ya ce, "Wow! Ke da

74

waye ku ka yi wannan aikin
Hauwa'u?
Na ce, "Da waye ka ke tsammanin
zan yi?" Ya dan yi shiru zuwa can ya
dan kada kai ya ce, "Ke kadai ko?"
Na ce, Yauwa ashe ka gane kenan?
Ya ce, To Allah yayi miki albarka. Na
wuce shi na shiga bandakin shi ina
hada mishi ruwa da turarukan wanka.
Ya shiga ni kuma na fito na ciro
mishi jallabiya ruwan kasa saboda
sanin da nayi zai fita zuwa Masallaci
idan anyi magriba.
Yana cin abinci ina zuba mishi
yana ba ni labarin garinsu da mutanen
garin.
Ya ce, "Sai kin haihu zamu je su
ganki suga abin da muka samu. Ya ce
kin ga ma na manta jiya da muka yi
waya ban tambaye ki su Umma ba.

75

Na ce, Ai ma ban je ba. Ya kalle ni
ya ce, Ba ki je ba kuma? Na ce, Eh. to
saboda me? Nayi shiru ban ce mishi
komai ba.
Ya ce, Ke dinnan fitanarki yawa ne
da ita, da ban bar ki ba da har yanzu
kina yi mun mitar na hana ki zuwa
gida.
Ya fita sallar Magriba ya wuce
wurin Hajiya, bai dawo ba sai da aka
yi sallar Isha'i sannan ya shigo.
Tashi ki shirya muje gidan tare.
Sannan ya wuce sashenshi. Ya dawo
sanye da jamfa da wando na yadin
material din maza yana rike da
mukulln mota a hannunshi.
Ni ma yadin material na saka mai
hadari ya kuma yi mun kyau sosai.
Muka fito tare muka shiga wurin
Hajiya don yi mata sallama.

76

Ta ce, lna zuwa haka a daren nan?
Ya ce, "Yar wata unguwa zata raka
ni. Ta ce, To a dawo lafiya. Muka
fito.
A wani babban shago ya tsaya ya yii
siyayya mai yawa, sannan muka wuce
gida.
Hira muke yi sosai da Umma shi
kuwa yana wurin Babana ba mu dawo
ba sai wajen karfe goma na dare.
Tashi nayi naga jini kadan-kadan
yana fitar mun, sai dai ban kula na
gani ba sai bayan da Ahmad ya tafi
kasuwa.
Bana son daga mishi hankali, don
haka nayi nufin bari sai ya dawo naayi
mishi bayani.
Nayi ta aikace-aikacena ba tare da
wani abu a raina ba, tunanina dai bai
wuce laulayi irin na ciki ba.

77
Sai da na gama ayyukana na shiga
bayan gida da nufin yin wanka, sai
kawai na ganni kace-kace cikin jini.
Sauri nayi na fito na dauki waya na
sanarwa Ahmad cewa ina son Zuwa
asibiti, ya ce lafiya? Na ce ch, ba na
dai jin dadi ne kawai, ya ce to Allah
ya sauwake.
Bala ya kai ni asibiti sai dai tun
kafin nan a takure nake cikin sauri
aka kai ni dakin Likita sai dai gwajin
farko ya tabbatar mana cikin ya
lalace, ya fita daga mahaifa dole a
cire.
Duk da halin da nake ciki a haka na
daure na kira Ahmad.
Cikin kankanin lokaci ya iso
asibitin, sai dai duk da saurin da ya yi
har an shigar da ni don wanke mun
mahaifa.

78

Duk da kokarin da nayi tayi na
hana kaina kuka kasa daurewa nayi da
Ahmad ya iso kaina.
Wannan karon ma bari nayi na ciki
wata hudu har da sati biyu, kamar dai
wancan kenan.
Kwana nayi a asibitin kowa kuma
yazo duba ni har daga gidanmu.
Likita ya shigo saboda sallama ta da
za a yi Ahmad yana yi mishi wasu
yan tambayoyi.
Ya ce, To dai a fayil dinta na ga ta
samu matsala makamanciyar wannan
shima a watanni hudu, don haka
tunda ga abinda ka fada zamu sake yi
mata scarming don mu gani ko da
matsala.
Likitan ya jawo wata 'yar takarda
yayi rubutu ya bamu. Ahmad ne da
kanshi ya kai ni wurin scarning din

79

muka dawo Likita ya duba ya ce, "To
a gaskiya ta samu matsala ne a
mahaifa saboda jijigar farat-daya da
mahaifarta tayi a wancan karon.
Saboda irin faduwar da tayi, hakan
ne yasa mahaifarta ba za ta iya rikke
wani ciki da zai yi fiye da watanni
hudu a mahaifarta ba.
Saboda bakin mahaifarta da ya riga
ya bude. Kuma shawarar da zan ba ku
a yanzu shi ne, kafin a san matakin da
za a dauka a kan matsalar, ta dan yi
hutu.
Don kuwa idan tayi wani cikin ma
a yanzu abinda zai faru kenan.
Dawowa gida muka yi jikinmu a
sanyaye, ni kam Ciwo ne ya rufe ni
jinya sosai Ahmad kwata-kwata ranar
bai fita kasuwa ba.
80

Bai kuma fadawa kowa abinda
Likita ya ce ba. Kwana biyu ko
abincin da zan ci daga wurin Hajiya
ake kawo mun.
Kullum kuma Ahmad zai ba ni
hakuri saboda lurar da yayi na dan
saka damuwa a raina.
Duk kokarin da nayi kada ya
fahimci wani abu kasawa nayi. Yau
ma yana zama zai fara mun magana
kuka na kama yi.
Sai da nayi ya ishe ni sannan na
share hawayena, babu abinda ke tsaya
mun a rai naji zuciyata ta baci irin na
tuna 'ya' yan Ahmad ne suka yi mun
wannan sanadin.
To tambayar ita ce, shin idan da ni
ce nayi wa wani a cikin su haka anya
zan zauna lafiya kuwa?
81

Amma gashi nan ni sun yi mun sun
zauna lafiya, sun ma mancc in ban da
shi Ahmad da yake ba ni hakuri.
Duk da warkewan da nayi a duk
lokacin da na tuna ina jin wani iri na
kuma kasa sakewa nayi harkokina
kamar da.
Ko shi Ahmad din ya lura ya gane
hakan, don yau ma muna zaune a
falonshi muna kallon labarai ya Juyo
yana kallona.
Hauwa'u magana nake so nayi
miki. Na lura duk tsawon lokacin nan
har yanzu ba ki saki jikinki ba.
Na kuma tambaycki shekaran iya
ko wani abu na damunki ne kin ce
a'a, lafiyarki kalau.
Ina so ki san wannan abun ba ke
kadai ya samu ba har da ni, amma

82
kuma kin takura ni na rasa walwalar
da a da nake farin cikin samu.
Idan ni ne nayi miki wani abu ki
gaya mun na gyara, idan kuma a kan
matsalar nan ne ina so kiyi hakuri.
Ina kokarin a wannan watan da zai
kama idan zan yi tafiya mu tafi tare
saboda wannan matsalar, sai ki ga
Likita a Dubai."
Ban ce mishi komai ba, amma nayi
kokari wajen ganin na rage takura ko
don saboda Ahmad.
Sai dai har karshen wata yazo ya
wuce Ahmad bai yi tafiyar ba, bai
kuma ce mun komai ba.
Muna kwance a dakinshi da
daddare a daren da ya dawo daga
Legos dauko wasu kayan shi da suka
shigo.
Chapter 6 · 0% Book details