Sashe 2
Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na gama na tsiyaya mishi coconut
juice din da nayi mishi na fara mika
mishi.
Ya karba ya dan yi murmushi ya
ce, "Bismillah zan fara cin abincin
amarya. Nayi murmushin jin abin da
ya ce. Ya kai juice din bakinshi ya
kwankwade ya ajiye kofin a kasa.
Ya kalle ni na dauka madara ce, na
ce a'a ba madara ba ce, ya ce To
menene'? Na ce Juice din kwakwa
ne."
Ya sa cokali ya fara cin abincin
gaba daya muka yi shiru sai da ya
cinye abincin tas sannan ya ce, "To
masallah Allahu, na gode Hauwa u.
Allah ya yi miki albarka, ya kuma
ba mu zaman lafiyamai dorewa.
Abinci yayi kyau."
18
Nasa hannu na kwashe kwanukan
na fitar na kai kicin, sannan na dawo
na zauna. Ya fara magana, "Tunda ki
ka zo ban samu wani lokaci na zaunar
da ke don nayi miki magana dangane
da al'amuran gidana ba.
Amma duk da hakan dai nasan kin
ga abinda ki ka gani na zahiri. Akwai
mahaifiyata wacce idan kin lura za ki
gane ba ni da wanda nake girmamawa
nake kuma so fiye da ita.
A rayuwata ita kadai ce na mallaka
ina nufin mallakar da ban taba wayar
gari na gane na rasata ba.
Ina yi mata soyayyar da bana yiwa
kowa shi a duniya Hauwa'u, don
kuwa nasan itama tana yi mun fiye daa
hakan.
Babana ya rasu ne ya bar ni ban fi
shckaru biyar ba a duniya, amma
19
kuruciyarta bai sa ta barni zuwa wani
mijin ba.
Sai ta zauna da ni da Yata don ta
tarbiyyantar da mu, ta ilimantar da mu
ta hakura ta sadaukar da jin dadin
rayuwarta.
Don haka duk wani abu da ki ka ga
nayi a yau ko na zama a yau din nan
to da bazarta ne. Ina rokonki daki
taimake ni ki zauna lafiya da ita.
Zan iya yin hakuri idan ki ka saba
mun, amma ina da gajen hakuri ta
fannin sabawa mahaifiyata.
Sai abu na biyu, nasan kin ga yara
to ina so ki san ko ni da nake ubansuu
Hajiya bata yardar mun ta bani
yancin shiga harkarsu ba.
ldan kin ga wani abu da suka yi
miki da bai yi miki dadi ba, to na
roke ki da kiyi hakuri, idan kuma kin
20
ga ba za ki iya ba to ki jira ni na dawo
ko menene a lokacin sai ki fada mun.
Ina yi miki wannan maganar ne
saboda ni nasan kan gidana, na kuma
san matsalar da ke cikin shi. Ina so ki
taimake ni na samu nutsuwar da nake
bukata a cikin gidana."
Na yarda da duk abubuwan da
mijina ya gaya mun da kanshi ya
kuma roke ni a kai ina kuma iyakacin
kokarina wajen ganin na biya mishi
bukatunshi.
Gara nake shirya mishi kullum mai
dadi, daga cikin littafin girkina a
kullum kuma bai gajiya wajen yaba
mun.
Haka nan baya gajiya da yabon
kwalliyata, don kuwa kullum a cikinta
nake safe da yamma, matukar yana
gidan.
21
lna son mijina ina kuma son zama
da shi. Zama nake yi na yanci da
walwala. A yanzu ne kuma na gane
me ake nufi da zaman aure.
Zama na hakika ba mai cike da
kunci ba. Zama na sanin hakki da
yancin dan Adam.
A yanzu ne nasan so nasan abinda
kalmar take nufi don abinda nake ji a
game da Ahmad.
Shima burinshi a kullum bai wuce
na ganin ya faranta mun ba. Da
matukar wuya ya dawo gida ba tare
da ya riko mun wani abu ba, wanda
zan yi amfani da shi don kaina ba don
shi ko wani ba.
Iyayena kuwa yana mutunta su
tamfar nashi. To abinda nake so
kenan na kuma samu, zan kuma
jurewa zama da ya' yanshi da
22
mahaifiyarshi kamar yadda ya ce, don
na tabbatar mishi matsayin shi a
wurina.
Watana biyu cif, Ahmad ya ce na
shirya a kai ni gida wuni. Cikin doki
ranar na kama shiri. Tsaraba sosai
yayi mun wanda zan tafi dashi tamfar
wacce take nesa.
Nayi sallama a kofar dakin Hajiya
na shiga a gefe na durkusa na gaya
mata zuwana gida.
Ta ce, Eh mijin naki yazo ya gaya
mun. Allah ya kiyaye hanya, ki gaida
manyan naki. Na fito na shiga mota.
Bala direba ya tuka muka tafi.
Babu wanda bai yi murna da ganina
ba.
Umma ta ce, "Haka fa Allah ke
lamarinsa, ki duba ki gani wannan
auren naki nutsuwarshi ma daban. "
23
Wajen karfe uku Ahmad ya kira ni
a waya. Na dauka "Yaushe ki ke
shirin zuwa gida ne?
Na ce, "Ina ce wai ko za ka bari ne
na yi sallar Magriba tukuna daidai
lokacin dawowarka kenan."
Ya ce, "To abincina fa? Ko zan
zauna da yunwa ne yau tunda nayi
karambanin yi miki gwaninta?
Nayi maza na ce, "A'a yallabai
mu tafi." Ban iya tsayawa jiran
Babana ba na kama shiri.
Tasi'u ne yake ta magana yana
cewa, Zai bini yaje yaga gidana,
Umma ta ce, Aa a wane dalili ka
bari dai a kai ku wani lokacin." Ba
tare da wata fargaba ba na ce a hada
musukayansu shi da Sabi'u.
Wurin Hajiya muka fara shiga, na
gaisheta. Su Tasi'u ma haka, na mike
24
zan fito ta ce mun, "Zo mana. Na
dawo na sake tsugunnawa ta ce, Su
waye wadannan?
Tana nuna su da baki, na ce
Kannena ne. ziradat ta leko daga cikin
dakinsu ta kalli su Tasi'u ta ce, Wai!
Sannan ta kwashe da dariya.
Ta ce, Lallai kuwa. Na tashi bayan
ta bani umarnin tafiya, na dawo
sashena amma ina jin wani abu a
raina maras dadi.
Muka shigo falona sannan na kara
bin yaran da kallo wadanda tuni suka
bi lafiyar kujera suka zauna. Ni nasan
mu ba masu kudi ba ne.
Amma daidai gwargwado Umma
tana iyakacin tawajen ganin ta
tsaftace danta babu kazanta a tare da
shi.
25
Tsarguwar da nayi ita ce tasa na
leka na kira Bala direba na ba shi
kudi na ce ya sayo mun kaya daidai
nasu Tasi'u set bibbiyu wadanda zan
yi musu amfani da shi.
Aikina na fara yi gadan-gadan
saboda kada na makara. Abinci mai
kyau sosai nayi mishi. Sai da na gama
sannan nayi wa su Tasi'u wanka na
saka musu sababbin kayansu nima
nayi wankan nayi alwala, sannan nayi
kwalliyata.
Ka'idar Ahmad shi ne, yana
dawowa zai shiga wurin
Mahaifiyarshi, idan aka yi sallar
Magriba ya dawo zai shiga suyi hira.
Daga sallar Isha'i ne zai shigo
wajena, don haka yau ma hakan ya yi.
Yana ganin su Tasi'u ya sai
murmushi.
26
"A'a'a, ke ki ce yau muna da
manyan baki a gidan nan, amma ba ki
sanar dani ba, ai da na shigo da kayan
tsaraba. To yanzu me ki ka ba su na
saukan baki?"
Na bude baki zan yi magana ya ce,
"A'a bar su kawai su bani amsa.
Suka fara lissafa mishi abubuwan da
suka ci tun da suka zo.
Sai da suka gama ya ce, "Ba ta ba
ku sweet ba, ba ta ba ku Ice Cream ba
kenan kun ga bata iya karbar baki
ba."
Ya jawo wayarshi daga aljihu ya
kira Bala direba ya ba shi kudi ya ce
yaje ya siyo mishi Ice Cream da
candy.
Sannan ya kalleni, "To baiwar
Allah ya ya ki ka samu gida? Nayi
murmushi har cikin zuciyata na ce
27
"Lafiya lau yallabai, kowa yana
gaisheka tare da godiya mai yawa, sai
dai ban ga Baba ba saboda gudun
kadana makara."
Ya mike ya nufi hanyar sashen shi
ina bin shi har muka shiga. Ya tsaya a
bedroom din shi yana tube kayanshi,
ni kuma na wuce bayangida ina hada
mishi ruwan wanka a kwarmi.
Ya ce, Ki koma wurinki kawai
saboda yaran nan na ce to. Ban dawo
ba sai da na ajiye mishi dukkan abin
da zai bukata idan ya fito daga
wankan.
Na dawo dakin inda na bar su
Tasi'u suna nan inda suke, kallon
cartoon din da na saka musuna
Kiddies world suke yi har yanzu.
28
Ban dade da dawowa ba Bala ya
shigo da aiken da aka yi mishi babbar
leda cike da kayan kwalama.
Ya ajiye ya juya na kira shi na debi
mai yawa na ba shi saboda sanin da
nayi yana da yaya suna kuma zaune
ne a boys Quarters din gidan.
Godiya sosai yayi ya juya. Na bai
wa su Tasi'u wanda za su iya ci na kai
saura fridge na ajiye saboda Ice
Cream din kada ya narke.
Ganin da nayi hankalinsu ya yi nisa
yasa na koma wurin Ahmad ya gama
shirinshi har ya fito falon yana
kokarin fitowa na ce, "Ai abincinka
nazo na baka ya ce mu koma wurinki
na ci a can, na ce to."
A falona yaci abincin shi muka ci
gaba da hirar mu, su Tasi'u ma suna
harkokinsu har suka yi barci. Na
29
dauke su naje daya dakin nawa na
kwantar da su na dawo in da Ahmad
yake.
Ya jawo ni jikinshi ya kwantar da
ni a kan kafafunshi yana shafa gashin
kaina.
"Tun da ki ka zo gidan nan ina
kallon ki ba ki taba yin kitso ba." Na
ce, Ai ban san inda za a yi mun
kitson ba ne a unguwar nan."
Ya ce, "Eh mai yi ma su Zainab
tazo tayi miki gobe. Na ce, "To."
A dakinamuka kwana ya ce
saboda su Tasi'u kada a bar su su
kadai. Sammako sOsai yanzun nake yi
saboda karyawar Ahmad tunda na
lura ba son shayi da biredi yake yi ba.
Pizza na mishi na hada mishi da
ruwan lipton saboda complain din da
30
juice din da nayi mishi na fara mika
mishi.
Ya karba ya dan yi murmushi ya
ce, "Bismillah zan fara cin abincin
amarya. Nayi murmushin jin abin da
ya ce. Ya kai juice din bakinshi ya
kwankwade ya ajiye kofin a kasa.
Ya kalle ni na dauka madara ce, na
ce a'a ba madara ba ce, ya ce To
menene'? Na ce Juice din kwakwa
ne."
Ya sa cokali ya fara cin abincin
gaba daya muka yi shiru sai da ya
cinye abincin tas sannan ya ce, "To
masallah Allahu, na gode Hauwa u.
Allah ya yi miki albarka, ya kuma
ba mu zaman lafiyamai dorewa.
Abinci yayi kyau."
18
Nasa hannu na kwashe kwanukan
na fitar na kai kicin, sannan na dawo
na zauna. Ya fara magana, "Tunda ki
ka zo ban samu wani lokaci na zaunar
da ke don nayi miki magana dangane
da al'amuran gidana ba.
Amma duk da hakan dai nasan kin
ga abinda ki ka gani na zahiri. Akwai
mahaifiyata wacce idan kin lura za ki
gane ba ni da wanda nake girmamawa
nake kuma so fiye da ita.
A rayuwata ita kadai ce na mallaka
ina nufin mallakar da ban taba wayar
gari na gane na rasata ba.
Ina yi mata soyayyar da bana yiwa
kowa shi a duniya Hauwa'u, don
kuwa nasan itama tana yi mun fiye daa
hakan.
Babana ya rasu ne ya bar ni ban fi
shckaru biyar ba a duniya, amma
19
kuruciyarta bai sa ta barni zuwa wani
mijin ba.
Sai ta zauna da ni da Yata don ta
tarbiyyantar da mu, ta ilimantar da mu
ta hakura ta sadaukar da jin dadin
rayuwarta.
Don haka duk wani abu da ki ka ga
nayi a yau ko na zama a yau din nan
to da bazarta ne. Ina rokonki daki
taimake ni ki zauna lafiya da ita.
Zan iya yin hakuri idan ki ka saba
mun, amma ina da gajen hakuri ta
fannin sabawa mahaifiyata.
Sai abu na biyu, nasan kin ga yara
to ina so ki san ko ni da nake ubansuu
Hajiya bata yardar mun ta bani
yancin shiga harkarsu ba.
ldan kin ga wani abu da suka yi
miki da bai yi miki dadi ba, to na
roke ki da kiyi hakuri, idan kuma kin
20
ga ba za ki iya ba to ki jira ni na dawo
ko menene a lokacin sai ki fada mun.
Ina yi miki wannan maganar ne
saboda ni nasan kan gidana, na kuma
san matsalar da ke cikin shi. Ina so ki
taimake ni na samu nutsuwar da nake
bukata a cikin gidana."
Na yarda da duk abubuwan da
mijina ya gaya mun da kanshi ya
kuma roke ni a kai ina kuma iyakacin
kokarina wajen ganin na biya mishi
bukatunshi.
Gara nake shirya mishi kullum mai
dadi, daga cikin littafin girkina a
kullum kuma bai gajiya wajen yaba
mun.
Haka nan baya gajiya da yabon
kwalliyata, don kuwa kullum a cikinta
nake safe da yamma, matukar yana
gidan.
21
lna son mijina ina kuma son zama
da shi. Zama nake yi na yanci da
walwala. A yanzu ne kuma na gane
me ake nufi da zaman aure.
Zama na hakika ba mai cike da
kunci ba. Zama na sanin hakki da
yancin dan Adam.
A yanzu ne nasan so nasan abinda
kalmar take nufi don abinda nake ji a
game da Ahmad.
Shima burinshi a kullum bai wuce
na ganin ya faranta mun ba. Da
matukar wuya ya dawo gida ba tare
da ya riko mun wani abu ba, wanda
zan yi amfani da shi don kaina ba don
shi ko wani ba.
Iyayena kuwa yana mutunta su
tamfar nashi. To abinda nake so
kenan na kuma samu, zan kuma
jurewa zama da ya' yanshi da
22
mahaifiyarshi kamar yadda ya ce, don
na tabbatar mishi matsayin shi a
wurina.
Watana biyu cif, Ahmad ya ce na
shirya a kai ni gida wuni. Cikin doki
ranar na kama shiri. Tsaraba sosai
yayi mun wanda zan tafi dashi tamfar
wacce take nesa.
Nayi sallama a kofar dakin Hajiya
na shiga a gefe na durkusa na gaya
mata zuwana gida.
Ta ce, Eh mijin naki yazo ya gaya
mun. Allah ya kiyaye hanya, ki gaida
manyan naki. Na fito na shiga mota.
Bala direba ya tuka muka tafi.
Babu wanda bai yi murna da ganina
ba.
Umma ta ce, "Haka fa Allah ke
lamarinsa, ki duba ki gani wannan
auren naki nutsuwarshi ma daban. "
23
Wajen karfe uku Ahmad ya kira ni
a waya. Na dauka "Yaushe ki ke
shirin zuwa gida ne?
Na ce, "Ina ce wai ko za ka bari ne
na yi sallar Magriba tukuna daidai
lokacin dawowarka kenan."
Ya ce, "To abincina fa? Ko zan
zauna da yunwa ne yau tunda nayi
karambanin yi miki gwaninta?
Nayi maza na ce, "A'a yallabai
mu tafi." Ban iya tsayawa jiran
Babana ba na kama shiri.
Tasi'u ne yake ta magana yana
cewa, Zai bini yaje yaga gidana,
Umma ta ce, Aa a wane dalili ka
bari dai a kai ku wani lokacin." Ba
tare da wata fargaba ba na ce a hada
musukayansu shi da Sabi'u.
Wurin Hajiya muka fara shiga, na
gaisheta. Su Tasi'u ma haka, na mike
24
zan fito ta ce mun, "Zo mana. Na
dawo na sake tsugunnawa ta ce, Su
waye wadannan?
Tana nuna su da baki, na ce
Kannena ne. ziradat ta leko daga cikin
dakinsu ta kalli su Tasi'u ta ce, Wai!
Sannan ta kwashe da dariya.
Ta ce, Lallai kuwa. Na tashi bayan
ta bani umarnin tafiya, na dawo
sashena amma ina jin wani abu a
raina maras dadi.
Muka shigo falona sannan na kara
bin yaran da kallo wadanda tuni suka
bi lafiyar kujera suka zauna. Ni nasan
mu ba masu kudi ba ne.
Amma daidai gwargwado Umma
tana iyakacin tawajen ganin ta
tsaftace danta babu kazanta a tare da
shi.
25
Tsarguwar da nayi ita ce tasa na
leka na kira Bala direba na ba shi
kudi na ce ya sayo mun kaya daidai
nasu Tasi'u set bibbiyu wadanda zan
yi musu amfani da shi.
Aikina na fara yi gadan-gadan
saboda kada na makara. Abinci mai
kyau sosai nayi mishi. Sai da na gama
sannan nayi wa su Tasi'u wanka na
saka musu sababbin kayansu nima
nayi wankan nayi alwala, sannan nayi
kwalliyata.
Ka'idar Ahmad shi ne, yana
dawowa zai shiga wurin
Mahaifiyarshi, idan aka yi sallar
Magriba ya dawo zai shiga suyi hira.
Daga sallar Isha'i ne zai shigo
wajena, don haka yau ma hakan ya yi.
Yana ganin su Tasi'u ya sai
murmushi.
26
"A'a'a, ke ki ce yau muna da
manyan baki a gidan nan, amma ba ki
sanar dani ba, ai da na shigo da kayan
tsaraba. To yanzu me ki ka ba su na
saukan baki?"
Na bude baki zan yi magana ya ce,
"A'a bar su kawai su bani amsa.
Suka fara lissafa mishi abubuwan da
suka ci tun da suka zo.
Sai da suka gama ya ce, "Ba ta ba
ku sweet ba, ba ta ba ku Ice Cream ba
kenan kun ga bata iya karbar baki
ba."
Ya jawo wayarshi daga aljihu ya
kira Bala direba ya ba shi kudi ya ce
yaje ya siyo mishi Ice Cream da
candy.
Sannan ya kalleni, "To baiwar
Allah ya ya ki ka samu gida? Nayi
murmushi har cikin zuciyata na ce
27
"Lafiya lau yallabai, kowa yana
gaisheka tare da godiya mai yawa, sai
dai ban ga Baba ba saboda gudun
kadana makara."
Ya mike ya nufi hanyar sashen shi
ina bin shi har muka shiga. Ya tsaya a
bedroom din shi yana tube kayanshi,
ni kuma na wuce bayangida ina hada
mishi ruwan wanka a kwarmi.
Ya ce, Ki koma wurinki kawai
saboda yaran nan na ce to. Ban dawo
ba sai da na ajiye mishi dukkan abin
da zai bukata idan ya fito daga
wankan.
Na dawo dakin inda na bar su
Tasi'u suna nan inda suke, kallon
cartoon din da na saka musuna
Kiddies world suke yi har yanzu.
28
Ban dade da dawowa ba Bala ya
shigo da aiken da aka yi mishi babbar
leda cike da kayan kwalama.
Ya ajiye ya juya na kira shi na debi
mai yawa na ba shi saboda sanin da
nayi yana da yaya suna kuma zaune
ne a boys Quarters din gidan.
Godiya sosai yayi ya juya. Na bai
wa su Tasi'u wanda za su iya ci na kai
saura fridge na ajiye saboda Ice
Cream din kada ya narke.
Ganin da nayi hankalinsu ya yi nisa
yasa na koma wurin Ahmad ya gama
shirinshi har ya fito falon yana
kokarin fitowa na ce, "Ai abincinka
nazo na baka ya ce mu koma wurinki
na ci a can, na ce to."
A falona yaci abincin shi muka ci
gaba da hirar mu, su Tasi'u ma suna
harkokinsu har suka yi barci. Na
29
dauke su naje daya dakin nawa na
kwantar da su na dawo in da Ahmad
yake.
Ya jawo ni jikinshi ya kwantar da
ni a kan kafafunshi yana shafa gashin
kaina.
"Tun da ki ka zo gidan nan ina
kallon ki ba ki taba yin kitso ba." Na
ce, Ai ban san inda za a yi mun
kitson ba ne a unguwar nan."
Ya ce, "Eh mai yi ma su Zainab
tazo tayi miki gobe. Na ce, "To."
A dakinamuka kwana ya ce
saboda su Tasi'u kada a bar su su
kadai. Sammako sOsai yanzun nake yi
saboda karyawar Ahmad tunda na
lura ba son shayi da biredi yake yi ba.
Pizza na mishi na hada mishi da
ruwan lipton saboda complain din da
30