← Book details Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 10

Sashe 8

Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

97
Na ce, "Ta meye?" Ya ce, "Abinci
nake so ki samar mun wanda zan ci,
yunwa ta dame ni."
Tashi nayi a daren nayi wa Ahmad
dan girki mai sauri yaci sannan muka
kwanta.
Tun daga nan na samu sassaucin
damuwa, sai dai Hajiya ta daina amsa
gaisuwata, duk da haka kuma ban
daina zuwa gaisheta ba.
Zan zauna na kai mintina goma
bata saurare ni ba. Shi ma na lura
yana da 'yar matsala amma tunda dai
bai bude bakinshi ya fada mun ba sai
ban tambayar shi ba.
Na dai tsaya tsayin daka wajen
ganin bai kuntata da yawa ba, don
nasan matsalar ba ta wuce ta Hajiya
ba.

98
Ba a fi wata daya zuwa kwanaki
arba'in ba sai shirin Ahmad ya
kammala na bude babbar harkarshi ta
kasuwanci a Kano.
Har yaje ya yi sati daya a can don
ya tabbatar komai ya daidaita, sannan
ya dawo.
Muna kwance a dakinshi yana bani
labarin yadda abin yazo cikin
gagarumar nasara, ni kuma dokina sai
karuwa yake yi zai bar zama da su
Hajiya da 'yan fitinannun jikokinta,
zan koma Kano tare da mijina.
Ina ta ayyano irin tattalinshi da zaan
kara yi da irin abubuwan da zan yi na
ci gaba don kaina.
Don kuwa nima yanayin
kasuwancin Ahmad yana ba ni
sha'awa, har nima na kan yi tunanin a

99

matsayina na mace idan zan gwada
babu mamaki nayi nasara.
Na ce, Kaga idan muka koma ni ma
sai na gwada kasuwancin mata na
cikin gida.
Kallona ya yi cikin mamaki.
"Kasuwanci kuma Hauwa'u?
Na ce, "Eh mana, na zannuwa da
gwala-gwalai irin naku ba."
Shiru yayi yana kallona, ya ce
"Ashe kina sha'awar kasuwanci?"
Na ce, "Eh, zama da kai ne yasa
hakan, da can ba na yi."
Ya ce, To bari kayan da nayi oda
wannan watan su zo sai na diban miki
a ciki ki gwada muga irin taki nasarar.
Kin san mata da yawa suna karban
kaya a hannuna kuma suna samun
riba ba kadan ba.

100

Amma abin da na lura da shi shi ne,
sai wacce ta iya rikici saboda siyan
kayan gida yawanci bashi ne.
Ke kuma ban ga wannan a tare da
ke ba."
Ba mu yi bacci ba sai karfe daya
saboda 'yan hirarrakin da muke yi.
Washegari bai kintsa da wuri ba
saboda bakin da yayi abokan
kasuwancinsa.
Sai kusan sha daya na rana. Ya
shigo dakina rike da mukullin
motarshi yana ba ni sakon da zan bai
wa Bala direba idan yazo, saboda
haihuwar da matarshi tayi.
Sannan ya shiga wurin Hajiya.
Kwanciya nayi don na dan yi barci
kafin Azahar tayi. Sai dai ban ko yi
nisa ba naji sallamar Larai.

101

Daga cikin dakin na daga murya
ina tambayarta ko lafiya? Ta ce,
Lafiya kalau Hajiye ce take kiranki.
Gabana ne ya fadi, to menene
kuma? Ba dai naje na gaisheta ba.
Nayi sallama a kofar dakin na shiga.
Har yanzu Ahmad yana nan bai fita
ba, yana zaune can gefe a asa,
kanshi kamar zai dunguri kasa saboda
irin sunkuyon da ya yi.
Jikina a sanyaye na zauna a gefe
nesa da inda yake.
"Ina ce dai ita ce wannan?"
Hajiya ta fara magana.
"Yarinyar da ko darajar sauran
matanka bata kai ba. A kanta ne kuma
nake baka umurni ka ke kin bi.
Abinda ban taba zaton zaka iya yi
ba shi ne take umurnina. Na kyale ku

102

na zuba muku ido amma gaba
dayanku ba ku fahimci hakan ba.
Nan wurin nan kazo mun da
maganar za ka kaita Hajji a bana na
ce a'a banyarda ba, don ina ta binka
ka biya wa Lado dan kanina har
yanzu ba ka biya ba kana daga
tafiyar.
Sai ka dawo min da maganaar
zuwan ku Dubai wanda wannan ma
duk wani salo ne na kin bin umurnin
da na bayar din.
Ka dai nuna mun a yanzu kai ma ka
girma. Ba a wani dauki lokaci mai
tsawo ba yarinyar nan ta zo har dakin
nan ta zage ni.
Na gaya maka ban ji ka dauki
matakin komai a kai ba. A jiya kuma
abinda ka zo da shi shi ne za ka daukec
ta ku koma Kano da zama ko Amadu?

103

To bari ka ji wata magana, idan ba
mantawa nay1 ba, ko a ranar da na
haife ka, nayi nakudar ka ne ni kadai
a dakina na haife ka na yanke maka
cibi da kaina.
Sannan ne nayi maka wanka kafin
wasu ma daga gidan suka san na
haihu, kenan ka gani babu wanda ya
taya ni.
Don haka ba zan haifi da nayi
tarbiyyarshi da irin abubuwan dadi da
wahala da dawainiyar da nasha wata
tazo ta kwace mun shi rana tsaka ina
kallo ba, babu ita.
Zagina da tayi ba ka ce komai ba
saboda ka daina gudun bacin raina sai
nata, to na yafe maka amma ko don
na yi wa tufka hanci ya zama hakan
bai sake faruwa ba.
104

Ga takarda da biro nan na baka
rubuta takardar sakin aurenta
yanzunnan ka bata, auren nata ya ishe
ni haka."
"Inna lillahi wa inna ilaihir raji'un."
A bayyane na furta saboda firgitan da
nayi. Saki kuma? Wannan wacce irin
musiba ce?
Na kalli Ahmad wanda har yanzu
yake a yadda na same shi, sannan na
kalli Hajiya.
Kamar kullum tana zaune ne a kan
dardumarta ta sallah, sanye da
zurmemen hijabinta.
Zan iya cewa a tsawon zaman da
nayi a gidan na watanni ashirin ban
taba ganin ranar da na ganta babu
hijabinta ba.
Sai nayi sha'awar ace ita din mata
ce mai sassauci da rangwame a kan

105

al'amuranta, tunda kowa ya shaideta
mace ce mai yawan Ibada.
To me yasa ita din halinta ya zama
haka. Danta da yake matukar
kokarinsa wajen ganin yayi mata
biyayya ya kaucewa bacin ranta ya
batawa wanda ya bata mata.
Danta da a kullum yake fadin irin
alherinta da dawainiyar da tayi da shi
wajen ganin bai yi maraicin uba ba.
Danta da a kullum yake fadin cewa
ita ce abinda ya fi so da girmamawa a
duniya shi ta ke yi wa irin wannan
kuntatawar da kuma rashin sassauci?
Lallai halinta sai ita.
Take na fara kokarin rarrashin
zuciyata don ta samu sassaucin
tsananin da zata fuskanta a gaba.

106

Na rinka tunanin abubuwan da zan
yi wadanda za su taimaka mun a
rayuwata da zan shiga nan ba da
dadewa ba.
Tunda nasan babu makawa Ahmad
zai aikata abinda Hajiya ta umurce shi
tunda da bakinshi ya tabbatar mun
cewa ita din bata taba bashi wani
umurni da ya ketare ba, face ya
aiwatar da shi komai tsananin shi.

** ** **
Ina kwance a kan shimfidaddiyar
katifata da ta sha lallausan shimfidan
zanin gado na yadin (American bed
sheet) dan asali da bargonshi.
Na kai hannu na shafa yadin zanin
gadon tare da tuna ranar da na fara
shimfida shi a kan gadona, lokacin da

107
nake ganiyar cin amarcina a gidan
Ahmad.
Na runtse idanuwana da karfi
saboda wasu tunane-tunane da suke ta
kawowa zuciyata ziyara.
Tunanin abubuwan da suka zo suka
kuma wuce tamfar a mafarki tamfar
dai ace wani barci kawai nayi mai
dadi na kuma farka.
A da can, ban taba tunanin haka
al'amurana za su kasance ba. A
matsayin shekaruna a yanzu ashirin
da uku kacal a duniya.
Amma har an fara kirga mun
aurena. Yanmata da yawa sa'o'ina ba
su ma yi auren ba, ballantana har ace
ya kare.
Take kuma nayi hanzarin yin
Istigfari da na tuna akwai wasu mata
kuma da suke zuwa duniya su gama

108
rayuwarsu a cikinta su koma ga
mahaliccinsu ba tare da sun yi auren
ba.
Don haka ba zai yiwu nayi wa
Ubangijina butulci ba, a kullum zan
kasance mai yawan godiya a gare shi
bisa irin yawa-yawan n imomin da
ya yi mun a rayuwata.
Ban kuma dauka wannan
mummunan jarrabawa ba ce sai na
dauka cewa ni kuma tawa kaddarar
kenan ba kuma zai yiwu na tsallake
wata kaddara tawa ba face kawai na
roki Ubangijina da kowacce ta tashi
zuwa mun, to ta zamto mai sauki.
Ya kuma ba ni ikon dauka don
Imanina ya zamto cikakke tun da aan
gaya mana cewa Imaninmu ba zai
cika ba sai mun yarda da kaddararmu
ta alkairi ko wanin alkairi.

109
Bai kuma jarraba ni da ciwo ba ko
wanina ko kuma ya jarrabe ni da rashi
na wata gaba a jikina ba.
Sannan da aurena ya mutu a farko
sai ya bani wanda ya fi mun na
farkon, to ina rokon shi a yanzu ma
ya bani wanda ya fi mun na biyun.
Sai dai tunanina yana kawowa
daidai nan sai naji gabana ya yanke ya
fadi ras!
Kenan na rabu da Ahmad ba zan
sake komawa gidanshi ba? Ina son
mijina shima kuma yana sona.
Mahaifiyarshi ce matsalarmu, don
kuwa idan ba don shigarta cikin
lamarin ba to don ta ya'yanshi zan
iya zama da su a yadda suke, tunda
ina son ubansu.
Sabanin matsalata da Ishak wanda
a lokacin da aka yi aurena da shi

110
shekaruna goma sha bakwai ne a
duniya.
Ba komai yasa a ka yi auren ba
face rashi da mahaifina yake ciki ga
kuma kwadayinshi a kaina na ganin
ni din nayi karatu.
Ya dauke ni ya ba shi ni ba tare da
wani dogon nema ko bincike ba,
saboda jin irin alkawuran da yayi a
kaina.
Alkawuran da suka zamo shi ne
sanadin faruwar auren da kuma
rugujewarshi.
Idan kuma da ace zaman da yayi da
ni akwai adalci a ciki ko kuma
sassauci ko tausayawa wadanda
wadannan abubuwa sune suka hadu
suka zamo soyayya da kauna to duk
da da sauki.
Chapter 8 · 0% Book details