← Book details Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 10

Sashe 3

Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yake yi akan tebar shi da take kara
habaka.
Duk da na gaya mishi ni bana
ganinta. Sai da na sallame shi ya tafi
sannan na dawo na shirya su Tasi'u
cikin sababbin kayansu muka karya
muna 'yar hirarmu cikin raha da ban
dariya suna bani labarai.
Su na tambaya abinda zan girka
musu suka fadaa na shiga nayi musu
muka ci tare sannan na dauko Ice
Cream din su na jiya na ba su suka
sha suka ce mun za su je wasa a waje.
Kamar na hana su sai dai naga kada
na takura su tunda yara ne.
Tashi nayi na nuna musu wurin da
yara suke wasa sannan na dawo
dakina na hau gado na kwanta.
Ban dadc sosai da kwanciya ba sai
ga dan aika daga kasuwa Ahmad ya

31

aiko shi da sakon su Tasi'u. Na karba
ina dubawa.
Kaya ne masu asalin kyau yan
kanti set uku-uku, sai takalma sandals
na asali.
Na ajiye kayan na leka don na kira
su daga nesa na hango su a kan lilo,
don haka na dawo na bar su suka ci
gaba da wasan su.
Ni kuma na shiga kicin don fara
shirin abincin dare. Ihun da nake
jiyowa ne yasa ni saurin fitowa, don
kuwa ya yi mun kama da na Tasi'u.
Sai dai kafin na fita waje har sun
shigo dakin cikin tsananin rudewa na
kwallara kara tare da fadin "Inna
lillahi wa inna ilaihi raj1'una."
Jini ne kawai har ya rine rigarshi
gaba daya. Waje nayi da gudu saboda
rudewa.

32

Daga nesa Bala direba ya hango ni
ya taho cikin sauri "Lafiya, lafiya? 99
Na ce, Zo ka gani. Na taho dakin
har ya zauna a kasa cikin saurin shi
ya sunkunci Tasi'u nima na bishi a
mota ya saka shi zuwa asibiti.
Ban jira dawowansu ba bin su nayi.
Ba karamin jin ciwo Tasi'u ya yi
ba, don kuwa sai da aka yi mishi
dinki a keyarshi a ka yi dressing din
wurin aka yi mishi allurai sannan
muka dawo gida wajen karfe shida da
rabi na yamma.
Har dakina Bala direba ya kawo shi
kan kujera ya ajiye shi. Muryar shi
har ta dishe saboda kuka. Na tsaya a
kanshi ina kallon shi saboda tausayin
da ya bani.
Na koma bandakina na dauko
sandar goge-goge na goge duk jinin

33
da ya mannu a tayels din na saka
dettol na sake gogewa sannan na
shiga kicin cikin sauri don na dan yi
wa Ahmad abincin da zai ci.
Sai dai ko dorawa ban yi ba sai ga
motarshi ta shigo gidan, duk da haka
ban fasa ba saboda nasan ba wurina
zai wuto ba.
Cikin kankanin lokaci na yi mishi
fried rice da coleslaw salad, sannan na
dawona dauki Tasi'u da barci ya riga
ya dauke.
Naje nayi mishi wanka da ruwa
mai zafi saboda ya ji dadin jikinshi,
na hada mishi tea na ba shi sannan na
ba shi magungunan da Likita ya ba
shi.
Naje na kwantar da su ban wani bar
su suka tsaya kallo ba.

34

Ahmad ya shigo lokacin ne nake
wanka amma kafin na fito ya tafi
dakinshi, don haka sai kawai na bi shi
can.
Shi ma wankan na samu yake yi
don kuwa dabi'arshi ce vin wanka, da
zarar ya idar da sallar Isha'i yana cin
abincin shi yana dan kallona.
Zuwa can dai ya kasa yin shiru ya
ce, "Menene ya faru ne amarya?
Na ce "Me ka gani? Ya ce, "Ba
haka na saba ganinki ba. Kamar nayi
shiru don kuwa abin da zuciyata take
ta gaya mun kenan sai dai na kasa.
Abin kawai da na sani shi ne,
Sabi'u ba zai yi mun karya ba, don
kuwa yana wurin da abin ya faru ya
kuma tabbatar mun da Ziradat ce ta
wurgar da Tasi'u akan liie ya ji
wannan ciwon.

35

Na share hawayena da na gama yi
mishi bayani, ya ce "Yanzu yana
ina? Na ce, Ya yi barci. Mikewa
yayi ya taho dakin da nake kwantar
da su har yanzu wata irin ajiyar
zuciya yake yi.
Duk da nisan da barcin shi ya yi ya
zuba mishi ido yana kallon lafcecen
bandejin da aka toshe ciwon da shi,
ya juya ya fita.
Shiru naji bai dawo ba, na mike
zan fita sai na hango shi yana tahowa
daga sashen Hajiya, duk da ban san
me ya faru ba gabana ne ya fadi da na
kalli fuskarshi.
Na kauce na ba shi hanya ya shige
daki ya kwanta, ni ma kwanciyar nayi
ban ce mishi komai ba, tunda shi ma
bai ce mun ba.

36

Washegari sai da ya gama shiri zai
fita ne ya kalle ni.
"Kiyi hakuri Hauwa'u, zan so ki
dauke shi a matsayin tsautsayi duk da
dai nasan ganganci ne kawai irin na
yara."
Na ce, "Babu komai." Ya fita, Na
shirya kamar kullum na shiga sashen
Hajiya don na gaisheta.
Kallon kawai da ta yi mun ne ya y1
matukar sanyaya mun jikina.
Na gaisheta ta amsa sannan ta ce,
Ko da wasa kada ki kuskura ki kara
kai karar yaran nan wurin Babansu na
gaya miki kada ki kara.
Ba a yi mun haka, kada ki shiga
gonata saboda bana son abinda zai sa
na saba miki. Tashi ki bani wuri."
37

Dawowa dakina nayi, nayi
sumukwi nayi tsit saboda sanyin da
jikina ya yi.
Ban yarda na mayar da su Tasi'u
gida ba kamar yadda naso nayi sai da
ya ji sauki sosai har aka cire mishi
bandejin.
Ahmad kuwa siyayya ya yi musu
mai ban sha'awa har da Kekuna ya ba
su, sannan yasa Bala ya mayar da su
gida.
Na riga na saba duk ranar Litinin
da Alhamis Hajiya tana Azumin
nafila, tunda nazo kuma duk da cewar
da tayi na daina saka mata abinci idan
nayi bai sa na fasa yi mata girkin
abincin buda baki a wadannan
ranakun ba.
Tun tana hanawa har tayi shiru,
kasancewar yau Alhamis sai na shirya

38

mata farfesun danyen kifi mai hadi
sannan nayi mata lafiyayyen alcle na
ganye da kunun gyada na danyar
shinkafa.
Na hada wuri daya ina nufin dauka
na kai sai ga wayar Ahmad ya aiko
dan aike na ba shi takardar da ya bari
a kan bed side din shi da ke cikin
dakinshin.
Hakan ne yasa nayi waya sashen su
don Larai tazo ta dauki abincin, sai
aka ce bata nan, don haka na ce
Zainab tazo ta dauka.
Na shiga na dauko wa dan aiken
sakon shi na ba shi, sannan na dawo
na ci gaba da harkokin abincina.
Sai da na kammala komai nayi
wanka nayi kwalliya tare da sallar
Magriba sannan na fito wurin Hajiya
don nayi mata sannu da shan ruwa.

39

Ina shiga Ahmad yana fita saboda
sallamar da aka yi da shi a waje.
Na durkusa gefe na gaisheta tana
amsawa kamar kullum yanayinta ta
kuma yi mun sannu. Na mike zan fito
sai naji an kira sunana.
Na waiwayo da sauri don ganin
mai maganar. Tun da nazo gidan yau
ne naji Zainab tayi magana da ni.
Tana rike da kofar dakinsu da
hannu daya yayin da dayan kuma
take nuno ni da shi.
"Kada ki kuskura ki sake yin waya
ki ce a turo ni ki aike ni kin ji na gaya
miki. Ba na daukan raini idan kin lura
za ki gane tunda ki ka zo gidan nan
ban taba shiga harkarki ba.
Idan me aika ki ke so, to gayawa
wanda ya ajiye ki ya nemo miki." Ta
juya ta koma dakin da ta fito.

40

Ina tsaye a bakin kofar dakin ko
ina a jikina sai tsatsafo da gumi yake
yi.
Murmushi Hajiya tayi ta ce "Kai
Zainab kenan, ina dai yi miki addu'a
Allah ya shirye ki. Je ki abin ki
Hauwa'u rabu da ita."
Na juyo na dawo daki raina a
cushe. Har lokacin da Ahmad ya
shigo na rasa yadda zan yi na saki
raina.
Duk wani abinda na saba yi mishi
na mishi sai dai da muka kwanta
Juyawata nayi na rabu da shi, don
kuwa abin har yanzu yana cina.
Yayi tambayar har ya gaji wai na
gaya mishi abinda ke damuna na ce
babu komai. Ya ce, haka kawai ki ke
mun irin wannan abin.

41

Nayi shiru naga zai ja mun wata
matsala na ce mishi ba ni da lafiya, ya
ce Idan ba ki da lafiya ba za ki yi
magana ba sai kawai ki juya mun
keya?
Juyowa nayi na ba shi hakuri,
sannan aka zauna lafiya.
Duk wani kokari da nake yi na gani
ban shiga sabga r 'ya'yan Ahmad ba
nayi shi, amma hakan bai sa sun bar
ni ba tare da su suna shiga tawa
harkar ba.
Babu ma dai shaidaniya irin
Ziradat, haka kawai yarinyar bata
kwanta mun ba. Gara Zainab bata
kallon inda nake bata yi mun magana
amma ita ko baki nayi to sai tasan
yadda tayi ta yi musu abinda ransu ya
6aci.

42

Duk wanda tayi wa rashin
mutuncinta hakuri nake ba shi tunda
ko a gaban Hajiya ne hakurin zataa
bayar sai ko bin su da take yi da
addu'ar shiriya.
Ba ni da wata matsala daga wurin
mijina, muhimmmin abu kenan a
wajena.
Wata irin iska mai karfin gaske aka
yi da daddare, wacce ta bugo satelite
dish din sashen su ya fado kasa.
A lokacin nan Ahmad baya nan,
don haka ba a gyara ba. Tun da abin
nan ya lalace sai suka dawo kallon su
Wurina.
Ziradat da Zinatu safe, rana da dare
a dakina suke wuni, ba na sawa ba na
hanawa.
Sannan ga su da ciye-ciye duk
abinda suka ci kuma to a wurin za su

43
Chapter 3 · 0% Book details