← Book details Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 10

Sashe 4

Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yar da bawon shi ko kuma su bar
kwanon a wurin ko da wacce irin
shara ko gyara na yi wa gun.
Ban taba daga ido na kalli abin da
suke yi ko na gaji nayi musu magana
ba.
Abin dai da na sani shi ne, ya kusa
wucewa tunda maigidan ya dawo a
jiya da daddare bayan tafiyar da yayi
ta wajen sati biyu.
Na gama aikina tas da yamma na
gyara dakina da na Ahmad na duba
babu wani abin da zan yi.
Don haka nayi wanka na gyara
kaina, nayi kwalliya ta burgewa
sannan na dawo falona da yake ta
kanshi na zauna ina kallon
programme din (Ask Huda) da ake yi
a Huda TV.

44

Kan wata tambaya dangane da jinin
Haila da ake amsa ta wacce ta dade
tana daure mun kai.
Sai kawai Zinatu ta shigo dakin
nan da sauri ta dauki remote ta canza
zuwa kidsco wai zata ga cartoon.
Wani gululun takaici ya taso min,
ban san yadda aka yi na daka mata
tsawa ba.
Na ce, "Meye haka? Dalla can
mayar mun inda ki ka same shi."
Iyakacin abinda na ce kenan yarinyar
nan ta tayi jifa da remote dinnan ya
daki bango ya wargaje.
Sannan ta falla a guje tana kurma
wani irin ihu, sai ka ce wacce ya
yanke wa wata gaba a jikinta.
Wani sabon takaicin ya sake kama
ni, ganin remote din ya ki aiki na
tattara shi na aj1ye.

45
Na shiga dakina na bi lafiyar gado
ina 'yan sake-sakena.
Larai ce tayi sallama ta shigo, wai
in je Hajiya tana kirana. Na fito bayan
na lullube jikina da gyale.
"Me ya hada ki da Zinatu ki ka
bugeta?" Na kalli yarinyar yadda ta
takure a jikin kujera har yanzu kuka
take yi.
Na ce, "Hajiya ban bugeta ba." Na
fara kokarin yi mata bayanin abin da
ya faru.
Ta ce, "Dakata! Kin ga yadda muka
fara zama cikin fahimtar juna? To ba
na so wani abu ya shigo daga baya,
don idan nayi niyyar daukan mataki
akan mutum abin ba ya yi mishi kyau.
Kada na sake jin an ce ko kallon
banza kin yi wa wani da a cikin gidan

46
nan, ballantana har ta kai ga kin saka
hannu a jikinsu.
Ki zauna a matsayinki su zauna a
matsayinsu. Ni bana dukan yarana
tunda ubansu ma a haka na
tarbiyantar da abina.
Duk wanda ya ce ba zai yi hakuri
da su a haka har kafin su fahimci kan
al'amarin duniya ba, to sai yasan
nayi.
Ba na so, kada kuma na sake jin
don sun je wurinki sai kiyi mata haka
har tana sulewa saboda razana? Ai
nan gidan ubanta ne tana da ikon
shiga duk inda take so ta wala."
Na dawo dakina nayi alwala nayi
sallar magriba har aka yi Isha'i ban
tashi daga wurin ba.
Don haka na mike nayi sallar Isha'i
tare da shafa'i da wutiri. Motsin

47
Ahmad naji a wurin shi ne na dauki
abincin shi na kai mishi.
Ina ajiyewa ya ce, "Me ya hada ki
da Zinatu ki ka yi mata irin wannan
dukan? Wato kin gane ko? Ni da ki ke
gani ina matukar tsoron tashin
hankali.
A waje ban huta ba, babu abin da
nake bukata irin na shigo gida dan
hutun da zan yi da iyalina na yishi
cikin kwanciyar hankali da farin ciki
ba.
Menene haka? Tun farko na gaya
miki kiyi kokarin zama ba tare da
wani abu ya hada ki da wani yaro ba,
saboda nima hakuri nake yi da su.
Hajiya kuma ina matukar kokarin
ganin bacin rai, bai same ta ba
ballantana a ce sanadina ne,"

48
Naga fadan nashi zai yi yawa
saboda wani abu bai taba hada ni da
shi makamancin haka ba, a tsawon
zaman da nayi a gidan na watanni
shida.
Na ce, Ban fa bugeta ba." Ya
watso mun ido "Ba ki bugeta ba? Na
ce "Na rantse maka ban bugeta ba."
"Me ki ke nufi kenan? Kina so ki
ce mun Mahaifiyata tayi miki karya?"
Nan da nan na fara kuka saboda jin
inda ya mayar da abin.
Nan take kuma fadan yafi na dah
wai na karyata mishi uwa. Ga gaskiya
nan kiri-kiri jikin yarinya ya rure har
zazzabi ya rufeta amma kina karyata
mahaifiyata.
Mara kunyar yarinya, tashi ki ba ni
wuri."

49
Na tashi na dawo dakina nayi kuka
har na gaji, idanuna suka yi luhu-luhu
saboda rashin barcin da ban yi ba.
Na gama abin karyawa kamar ba
zan shiga sashen nashi ba, tunda
korata ya yi jiya sai naga kada na
karawa kaina matsala.
Na dauka na kai mishi na ajiye na
juyo abina, tunda a da wannan damar
tayin gaba da wani ina dai bin doka
ne kawai. To da haka wanna ya wuce.
Ba karamin taka tsantsan nake yi
da yaran Ahmad da mahaifiyarshi ba,
saboda ina son aurena.
Gashi kuma cikin kankanin lokaci
sai na mallaki abubuwan kadara irin
Su,gold da zinari saboda yawan
tafiyar da yake yi.
Kuma shi mai sakin hannu ne.
matsalata a kullum ba daga shi ba ne

50

sannan babu fashi sai dai idan bai yi
tafiya ya dawo ba sai an ce nayi kaza
nayi kaza.
Ita kuma Hajiya ta ce aja mun
kunne, to garin aja kunnen sai ya
zama tashin hankali, ina batawa
mahaifiyarshi rai.
Sannan babu damar nayi musun
ban yi ba sai laifin nawa yayi yawa,
na karyata mahaifiyarshi, don haka
kullum a haka muke.
A daidai wannan lokacin ne ta
bayyana ina dauke da juna biyu har
na shiga wàta na uku.
Hakan ne ya matukar takura ni naa
kasa yin Azumin watan Ramadana,
saboda tsananin laulayin da nake yi.
Ba Ahmad ba ma har Hajiya a
wannan lokacin ta sassauta mun, don

51

haka babbar matsala a yanzu
laulayina ne da kuma yaran.
Tunda yanzu ba barina suka yi da
karata wurin Babansu duk da laulayin
da nake yi bai hana ni kiba na murje
ba.
Shirin sallah sosai ake yi don kuwa
gidan ma a cike yake da mutane 'yan
uwan su da suka zo daga kauye da
kuma babban dan Ahmad Zubair.
Wanda yanzu ne muka san juna da,
shi.
Shi kam babu laifi yana da hankali
don Aunty ma yake kirana. Haka nan
nima duk da sanin da nayi suna buda
baki a wurin Hajiya hada mishi nake
yi da Babanshi.
Sannan ganin shi yasa hatta Zainab
ta saurara da wasu abubuwan
ballantana su Ziradat.

52

Zama yazo yayi yana gaya mun
abubuwan da yake so nayi mishi, na
sallah saboda bakin abokanshi da za
su kawo mishi ziyara.
Na ce, To ka bari mana idan nayi
na Babanku sai na diban maka a ciki.
Yayi godiya sosai, take kuma farin
cikinshi ya bayyana, ya tashi ya tafi.
Bai dade da fita ba na fita don
zuwa sashen Hajiya kai mata farfesun
kodar da Ahmad ya aiko ya ce nayi
mata da hannuna.
Na isa bakin kofar tun kafin nayi
sallama naji Ziradat tana cewa, "Ai
munafuka ce tunda gashi har Hajiya
ma yanzu ba ta yarda idan mun ce
mata tayı mana wani abu.
Ni a matan da Babanmu ya aura
duk ita nafi tsana. Hajiya ta ce,

53

"Um'um Ziradat na fa kwabe ki da
irin wannan maganganun."
Shi kuma Zubair cewa ya yi "Ni
banä son irin wadannan maganganun
ban san abinda yasa Baba yake biye
muku ba.
Menene laifin wannan matar? Ko
harkar mutum bata shiga ba za ku
taba barin Baba ya zauna lafiya da
mata ba. Shi kuma ku ke sakawa a
matsala."
Sallama nayi na ajiye mata na fito
na dawo wurina, a raina na ce kwaji
da shi, ni kam nawa auren daram in
Allah ya yarda.
Shiri sosai nayi na sallah mutanen
gidan kaf na basu abinci da abinsha
da su kek din da nayi ba tare da nayi
la'akari da Hajiya tayi ba.

54

Makwabta baki daya sai da na
zagaya su da abinci. Ahmad ne kuma
ya taso keyar su Zainab suka kai mun
rabon.
Gidanmu ma duk da ya aike musu
da nama cikin babban baho saboda
yankan da yayi da kuma shinkafa da
tumatur kwando.
Bai hana ni kai musu abincin sallah
ba wannan kuwa Bala direba na aika.
Da yamma ne baki abokan harkar
Ahmad suka zo gidan hakan ne yasa
sashenshi ya cika dankam ba kadan
ba.
Nima gagarumar liyafa na shirya
musu sinasir da farfesun kafar saniya
sai dambun nama da kek da manyan
donghnut na asali mai ridi.
Sai kwalayen juice wanda na hada
musu duka a cikin wani madaidaicin

55

kwando na Rafia da nayi rafin
dinshi da wata 'yar leda da aka rubuta
iyalan gidan Alhaji Ahmad Rufa'i
suna muku barka da Edil Fitr.
Kuma gaba dayansu ya wadace su.
Shima abin yayi mishi dadi ba kadan
ba.
Ya shigo dakina lokacin da nake
shirin shiga wanka har yanzu
fuskarshi a washe take ya sa hannu ya
dauke ni yana cewa bari nima na taya
ki wankan irin wannan gajiya da ki ka
yi haka.
Duk da dai ni da yunwa ki ka bar ni
na ce, "Haba yallabai na dauka ai
yau ba za ka ji yunwa ba."
Dariya yayi ya fita bayan ya gaya
mun yana jirana idan na gama shiri.
Doguwar riga na saka mai gyale na
dauko abincin a babban tire na nufi

56
falon shi na waje don a nan na jiyo shi
alamar ya sake yin wasu bakin.
Ni kuma ba zan iya jiran tafiyar su
ba tunda na gane yana 1in yunwa.
Wani irin santsi ne ya debe ni gaba
daya na zame na kife a kasa tire yayi
nesa ya kife abubuwan ciki suka
tarwatse.
Karar fashewar abu da salatin da
nayi ne yasa Ahmad tahowa wurin
cikin sauri har ya karaso inda nake.
Ba iya motsawa ba sa hannu yayi
ya dauke ni zuwa cikin dakinshi
tunda daga inda nake nan dinne ya fa
kusa.
"Sannu Hauwa'u."
Sai dai ko amsawa na kasa yi
saboda wani irin gigitaccen ciwo da
nake jiwowa daga gadon bayana yana
hadowa har gabana zuwa marata.
57
Chapter 4 · 0% Book details