Sashe 8
Juyin Kwado Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ke kanki ta musamman ce, ballantana kuma aje ga kalamanki na nutsuwa, yanayin yanda kike magana, yanayin da kike tafiya, da duk wani abu da ya shafeki na musamman ne”
A wannan karon murmushi ta yi me faɗi, har haƙwaranta na bayyana.
“Kin yarda ke nan? Tun ga shi har kina murmushi”
Sai ta rufe bakinta, tana mamakin yanda aka yi ya san ta yi murmushi, tun da murmushin ba me sauti ta yi ba.
“Zan sauƙa daga kan layi. Ina fatan sake haɗuwa da ke”
“Sai anjima”
“Na gode da lokacinki”
Uwais ya sauƙe wayar, a lokacin da mahaifiyarsa ta shigo katafaren falon gidansu. Murmushi ta yi tana kallon ɗanta, tana zama kusa da shi ya kama hannunta ya sumbata. Ita kuma ta shafa kansa tana sanya masa albarka.
“Da wa kake waya? Ko yarinyar da zata zama sirikata ce?”
Ya faɗaɗa murmushinsa yana kallon mahaifinsa da shi ma ya shigo falon.
“Ai da gani ba sai an faɗa ba. Tun da kika ga yana yin irin wannan murmushin.”
Mahaifinsa Inayat Fazil ya faɗa yana nasa murmushin. Ƙudsiyya mahaifiyarsa tace.
“Wace ce?”
“Wata ce”
Ya basu gajeriyar amsar yana kwasar wayoyinsa, sannan ya bar living arean yana murmushi me kama da dariya.
*House No. 34, Street 12, Al Mankhool, Bur, Abu Dabhi, Dubai.*
ADAM POV.
Tsaki ya ja yana ci gaba da danna system ɗinsa, sakamakon binciken wurin da ya kamata ace ya je ya ɗauki hotunan da aka saka shi da yake. Amma ya shafe sama da awa uku bai samu wurin da ya kwanta masa ba. Arman dake zaune a gefensa yana cin tuwon da Maama ta ba shi ya ce.
“To wai duk wannan tsakin da kake wa mutane na miye?”
Adam ya juyo ya kalle shi, sai lomar tuwon shikafa miyar kuka yake, kamar wani bahaushe, ko irin ya saba da cin abincin nan. Kuma dan tsabar yana son tuwon yasa a wasu lokutan yake tattaki ya zo gidansu Adam, dan kawai Maama ta ba shi tuwo, yace a cikin abincin hausawa tuwo ya fi komai daɗi.
“Ya zalame (Man) na rasa wurin da ya kamata ace na je na ɗauki hotunan da za su ja hankalin mutane, irin hotunan da ba'a saba gani ba ka gane?”
Armaan ya gyara zaman glasses ɗinsa, sannan yace.
“Ka je ka ɗauko hotunan Creek harbor, ko Dubai Fountain show, ko Museum of the future...”
“Ina maganar abin da ba'a saba gani ba kana lissafo min wuraren da babu wanda bai sansu ba a Dubai. Duka waɗannan wuraren da ka lissafo ɗaiɗaikun mutanen garin nan ne kaɗai ba su taɓa zuwa ba, in ma ba su je ba sun san wurin. Kuma me zan nunawa mutane a wurin da suka riga suka sani?”
Adam ya katse shi. Arman ya gyara zama yana aje bowl ɗin hannunsa a kan center table.
“To ka je Bastakia, Deira, ko ka ɗauko gaba ɗaya Palm Jumeirah...”
“Dakata Arman, hotunan wuraren nan tuntuni an riga an ɗauke su, imfact ba na son ɗaukan hoton wani abu a Dubai, na fi son na fita wajen Dubai dan na zo musu da sabon abu.”
“Ina za ka je to?”
Ya tambaya yana gyara zaman glasses ɗinsa. Adam ya yi shiru kawai, dan har yanzu ya kasa tsayar da shawarar inda ya kamata ace yaje.
“Me zai hana ka je Nigeria, ka ɗauki hotunan masarautun gargajiya da al'adun Hausawa?”
Maama dake tsaye a kitchen, tana sauraron duka hirarrakinsu ta bada shawarar. Kusan a tare suka juya suka kalleta.
“Kyakkyawar shawara... Idan za ka je zan rakaka, dan ban taɓa zuwa ƙasarku ba, ko ba komai ka ga ni ma zan buɗe ido”
Adam ya yi murmushi.
“Zan duba na gani”
Arman ya kai masa dukan da a ɗan ƙanƙanin lokaci ya sa ya razana. Dan sam bai zaci dukan Arman ɗin a wannan lokacin ba.
“Miye ne?”
Ya tambaya yana zaro ido.
“Me za ka duba ka ga?. Ai tun da Maama ta riga ta bada shawarar nan ta karɓu, ko kai ba ka karɓa ba ni na karɓa maka, dan haka ni zan ɗauki nauyin tafiyarmu Nigeria. Dan a private jet ɗin Alhadi za mu tafi”
Adam ya yi dariya.
“To ya kamata mu sanar da Ivana, dan ita ma ba za ta kasa zuwa ba”
“Zan faɗa mata”
Arman ya faɗa yana ɗaukan wayarsa dake ruri, alamun shigowar kira, ganin lambar kakarsa ‘Jadda Nahila’ (Kaka Nahila) yasa ya ɗaga kansa yana girgizawa. Dan tun da har ya ga kiranta ya san wani abin aka ce mata ya aikata.
“Shu sar (Me ya faru?)”
Adam dake rufe system ɗinsa ya tambaya.
“Jadda ce ke kirana”
Ya faɗa yana nuna masa wayar.
“To ka ɗaga mana”
Sai ya girgiza kansa yana miƙewa.
“Babu amfanin sai na ɗaga, na san cewa za ta yi duk inda nake, duk abin da nake na bari na tafi gidanta”
Adam ya yi dariya yana kallon Arman ɗin da ya nufi kitchen, ya wanke hannunsa, sannan ya dawo falon ya ɗauki Denim jacket ɗinsa ya saka. Sannan ya ɗauki keyn motar da ya fito da ita.
“Na tafi... Maama na tafi”
Ya musu sallama yana nufar ƙofar fita daga gidan, wadda ta kasance ita ce ƙofar falo.
“To Arman ka gaida Imminka”
“Za ta ji”
Daga haka suka fita tare da Adam. Motarsa silver color ƙirar RR (Rolls-Royce) sweptail. Na fake a ƙofar gidan. Kallon motar kawai idan ka yi za ta baka labarin kuɗinta. Dan sam motar ba ta yi kama da ta ƙananun masu kuɗi ba. Shi kansa Arman ba ya hawa mota ɗaya, idan yau ya hau Bugatti La Voiture Noire, gobe za ka ganshi da Lamborghini Venone Roadster.
“Idan na dawo daga gidanta zan kiraka a kan maganar tafiya Nigeria ɗin nan”
Arman ya faɗa yana buɗe ƙofar motarsa. Adam ya amsa masa da to, suka yi sallama, sannan Arman ya ja motar zuwa gidan kakarsa, wadda ta haifi mahaifinsa, dan duka 'yan uwan mahaifiyarsa suna can Lahore, Pakistan.
Salma Ahmad Isah ✍️
_______________
_Shin a ganinku me Arman zai yi ifan jar ya san abin da iyayensa ke shiryawa?._
_Wata alaƙa kuke hasasowa tsakanin Uwais da Ivana?._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
. 🪄 ...JUYIN KWAƊO...🪄
©️Salma Ahmad Isah
SalmaAhmadIsah @ArewaBooks
SalmaAhmadIsah @Wattpad
Page-5
A ƙofar gidan ya faka motarsa, sannan ya fito yana kallon kyakkyawan gidan da tsohuwar ke ciki, dan kakansu ya daɗe da rasuwa, ita Jaddan ce kaɗai ta rage, sai jikokinta da kan zo tayata zama jifa-jifa. Dan bayan mahaifinsa da Anwar Jadda na da 'ya'ya mata huɗu, waɗan da suka kasance ƙannen mahaifinsa.
Ba tare da knocking ko danna door bell ba ya buɗe ƙofar gidan ya shiga, a ɗan hall ɗin dake bakin ƙofa ya tsaya ya cire takalmansa, ya saka wasu da ya ga a wurin, sannan ya shiga falo yana dube-dube. Bai ga kowa ba bayan wata kyakkyawar budurwa da ta fito daga ƙofar da ya san cewa kitchen ne. Hannunta riƙe da tray, wanda kallon kyanta bai sa ya san miye a ciki ba. Da alama ta ji buɗe ƙofar tasa ne shi yasa ta fito dan ganin wanda ya zo.
“Marhaba”
Ta faɗa tana kallonsa da murmushi, dan ita ta san shi, shi ne dai alamu suka nuna cewa bai santa ba. Kansa ya jinjina kawai yana ƙare mata kallo, ba zai yi ƙarya ba, yarinyar tana da kyau.
“Aina Jadda” (Ina Jadda)
“Bi gurfatah, kallini nadilah. (Tana ɗakinta, bari na kirata)”
Ta amsa da muryarta me daɗin saurare. A living room ya zauna yana ci gaba da kallon matashiyar, har ta nufi corridor ɗin da zai sadata da upstairs. Sai a lokacin ya ɗauke idonsa a kanta, yana zaune a wurin har ta dawo, ta sanar masa ga Jaddan na sauƙowa, sannan ta koma kitchen ɗin.
Tun da Jadda ta fito take wurga masa harara, har ta iso living room ɗin, ta zauna a gefe da shi tana kallonsa a kaikaice. Kuma duk da ya lura da hakan bai sa ya fasa dariya ba.
“Masa'ul khair ya Jadda. (Barka da yamma Jadda)”
Jadda ta masa banza ta ɗauke kai tana girgiza ƙafa.
“Ƙira nawa na maka?”
Ta tambaya bayan wani lokaci.
“A ƙalla goma”
Arman ya amsa.
“To me yasa ba ka ɗaga ba?”
“Saboda na san maganar da za ki faɗa, shi yasa na zo tun kafin ki ce na zo”
Jadda ta kuma yin shiru.
“Arman zo nan”
Ya dubeta, sai ya miƙe ya koma gefenta ya zauna.
“Magana nake so mu yi...”
Ya jinjina mata kai, yana kallon yarinyar nan da ta dawo falon ɗauke da kayan taɓawa, ta aje a kan center table, sannan ta juya ta koma kitchen.
“Jadda wace ce wannan?”
Ya tambaya. Jadda ta harare shi, dan ta lura tun da ta shigo falon yake kallonta har ta koma inda ta fito.
“Gufran sunanta, ita ce yarinyar gwaggonka Bilƙisa, wadda ke Qatar.”
“Ohh na gane. To ina jinki”
Ya amsa yana jinjina mata kai.
“Da Anwar da Iƙbal duka 'ya'yana ne. Da kai da Faisal jikokina ne, haka Gulzar da Sakina. Amma Wallahi har cikin raina na fi son ka zamto magajin Alhadi fiye da Faisal Arman...”
Arman ya yi murmushi, dan ya san tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi.
“Jadda me yasa kowa yake son na zama shugaban Alhadi?”
Ya matambaya.
“Saboda kai kafi cancantar zama shugaba... Alhadi kamfanin mahaifinka ne, Anwar hannun jari kawai yake da shi!”
Jadda ta ba shi amsa, ya girgiza kansa yana murmushi.
“Jadda bani da suffofin shugabanci, saboda inada nakasar gani, ba zan iya shugabanci ba”
“Arman! Ka ga wannan kujerar dake cikin office ɗin Iƙbal? Ka ɗauketa tamkar kujerar wata babbar masarauta a zamanin baya. Wadda ake yaƙi da zubar da jini duk domin a mallaketa, wannan kujerar na dai-dai da kujerar katafariyar fada a zamanin baya!”
“To wai duk me ya kawo wannan zancen?”
Jadda ta yi murmushi.
“Saboda ba ma so ka bamu kunya. Nan da kwana uku zagayowar ranar da aka haifeka. Iyayenka na shirya maka babban shagalin taya murna. Kuma a wurin shagalin mahaifinka ya ɗauki niyyar baka takardun shugabancin gamayyar kamfanunuwan Alhadi, domin ka sa hannu a matsayinka na shugaba na gaba. Kuma ba na fatan ka bamu kunya Arman!.”
A wannan karon murmushi ta yi me faɗi, har haƙwaranta na bayyana.
“Kin yarda ke nan? Tun ga shi har kina murmushi”
Sai ta rufe bakinta, tana mamakin yanda aka yi ya san ta yi murmushi, tun da murmushin ba me sauti ta yi ba.
“Zan sauƙa daga kan layi. Ina fatan sake haɗuwa da ke”
“Sai anjima”
“Na gode da lokacinki”
Uwais ya sauƙe wayar, a lokacin da mahaifiyarsa ta shigo katafaren falon gidansu. Murmushi ta yi tana kallon ɗanta, tana zama kusa da shi ya kama hannunta ya sumbata. Ita kuma ta shafa kansa tana sanya masa albarka.
“Da wa kake waya? Ko yarinyar da zata zama sirikata ce?”
Ya faɗaɗa murmushinsa yana kallon mahaifinsa da shi ma ya shigo falon.
“Ai da gani ba sai an faɗa ba. Tun da kika ga yana yin irin wannan murmushin.”
Mahaifinsa Inayat Fazil ya faɗa yana nasa murmushin. Ƙudsiyya mahaifiyarsa tace.
“Wace ce?”
“Wata ce”
Ya basu gajeriyar amsar yana kwasar wayoyinsa, sannan ya bar living arean yana murmushi me kama da dariya.
*House No. 34, Street 12, Al Mankhool, Bur, Abu Dabhi, Dubai.*
ADAM POV.
Tsaki ya ja yana ci gaba da danna system ɗinsa, sakamakon binciken wurin da ya kamata ace ya je ya ɗauki hotunan da aka saka shi da yake. Amma ya shafe sama da awa uku bai samu wurin da ya kwanta masa ba. Arman dake zaune a gefensa yana cin tuwon da Maama ta ba shi ya ce.
“To wai duk wannan tsakin da kake wa mutane na miye?”
Adam ya juyo ya kalle shi, sai lomar tuwon shikafa miyar kuka yake, kamar wani bahaushe, ko irin ya saba da cin abincin nan. Kuma dan tsabar yana son tuwon yasa a wasu lokutan yake tattaki ya zo gidansu Adam, dan kawai Maama ta ba shi tuwo, yace a cikin abincin hausawa tuwo ya fi komai daɗi.
“Ya zalame (Man) na rasa wurin da ya kamata ace na je na ɗauki hotunan da za su ja hankalin mutane, irin hotunan da ba'a saba gani ba ka gane?”
Armaan ya gyara zaman glasses ɗinsa, sannan yace.
“Ka je ka ɗauko hotunan Creek harbor, ko Dubai Fountain show, ko Museum of the future...”
“Ina maganar abin da ba'a saba gani ba kana lissafo min wuraren da babu wanda bai sansu ba a Dubai. Duka waɗannan wuraren da ka lissafo ɗaiɗaikun mutanen garin nan ne kaɗai ba su taɓa zuwa ba, in ma ba su je ba sun san wurin. Kuma me zan nunawa mutane a wurin da suka riga suka sani?”
Adam ya katse shi. Arman ya gyara zama yana aje bowl ɗin hannunsa a kan center table.
“To ka je Bastakia, Deira, ko ka ɗauko gaba ɗaya Palm Jumeirah...”
“Dakata Arman, hotunan wuraren nan tuntuni an riga an ɗauke su, imfact ba na son ɗaukan hoton wani abu a Dubai, na fi son na fita wajen Dubai dan na zo musu da sabon abu.”
“Ina za ka je to?”
Ya tambaya yana gyara zaman glasses ɗinsa. Adam ya yi shiru kawai, dan har yanzu ya kasa tsayar da shawarar inda ya kamata ace yaje.
“Me zai hana ka je Nigeria, ka ɗauki hotunan masarautun gargajiya da al'adun Hausawa?”
Maama dake tsaye a kitchen, tana sauraron duka hirarrakinsu ta bada shawarar. Kusan a tare suka juya suka kalleta.
“Kyakkyawar shawara... Idan za ka je zan rakaka, dan ban taɓa zuwa ƙasarku ba, ko ba komai ka ga ni ma zan buɗe ido”
Adam ya yi murmushi.
“Zan duba na gani”
Arman ya kai masa dukan da a ɗan ƙanƙanin lokaci ya sa ya razana. Dan sam bai zaci dukan Arman ɗin a wannan lokacin ba.
“Miye ne?”
Ya tambaya yana zaro ido.
“Me za ka duba ka ga?. Ai tun da Maama ta riga ta bada shawarar nan ta karɓu, ko kai ba ka karɓa ba ni na karɓa maka, dan haka ni zan ɗauki nauyin tafiyarmu Nigeria. Dan a private jet ɗin Alhadi za mu tafi”
Adam ya yi dariya.
“To ya kamata mu sanar da Ivana, dan ita ma ba za ta kasa zuwa ba”
“Zan faɗa mata”
Arman ya faɗa yana ɗaukan wayarsa dake ruri, alamun shigowar kira, ganin lambar kakarsa ‘Jadda Nahila’ (Kaka Nahila) yasa ya ɗaga kansa yana girgizawa. Dan tun da har ya ga kiranta ya san wani abin aka ce mata ya aikata.
“Shu sar (Me ya faru?)”
Adam dake rufe system ɗinsa ya tambaya.
“Jadda ce ke kirana”
Ya faɗa yana nuna masa wayar.
“To ka ɗaga mana”
Sai ya girgiza kansa yana miƙewa.
“Babu amfanin sai na ɗaga, na san cewa za ta yi duk inda nake, duk abin da nake na bari na tafi gidanta”
Adam ya yi dariya yana kallon Arman ɗin da ya nufi kitchen, ya wanke hannunsa, sannan ya dawo falon ya ɗauki Denim jacket ɗinsa ya saka. Sannan ya ɗauki keyn motar da ya fito da ita.
“Na tafi... Maama na tafi”
Ya musu sallama yana nufar ƙofar fita daga gidan, wadda ta kasance ita ce ƙofar falo.
“To Arman ka gaida Imminka”
“Za ta ji”
Daga haka suka fita tare da Adam. Motarsa silver color ƙirar RR (Rolls-Royce) sweptail. Na fake a ƙofar gidan. Kallon motar kawai idan ka yi za ta baka labarin kuɗinta. Dan sam motar ba ta yi kama da ta ƙananun masu kuɗi ba. Shi kansa Arman ba ya hawa mota ɗaya, idan yau ya hau Bugatti La Voiture Noire, gobe za ka ganshi da Lamborghini Venone Roadster.
“Idan na dawo daga gidanta zan kiraka a kan maganar tafiya Nigeria ɗin nan”
Arman ya faɗa yana buɗe ƙofar motarsa. Adam ya amsa masa da to, suka yi sallama, sannan Arman ya ja motar zuwa gidan kakarsa, wadda ta haifi mahaifinsa, dan duka 'yan uwan mahaifiyarsa suna can Lahore, Pakistan.
Salma Ahmad Isah ✍️
_______________
_Shin a ganinku me Arman zai yi ifan jar ya san abin da iyayensa ke shiryawa?._
_Wata alaƙa kuke hasasowa tsakanin Uwais da Ivana?._
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
. 🪄 ...JUYIN KWAƊO...🪄
©️Salma Ahmad Isah
SalmaAhmadIsah @ArewaBooks
SalmaAhmadIsah @Wattpad
Page-5
A ƙofar gidan ya faka motarsa, sannan ya fito yana kallon kyakkyawan gidan da tsohuwar ke ciki, dan kakansu ya daɗe da rasuwa, ita Jaddan ce kaɗai ta rage, sai jikokinta da kan zo tayata zama jifa-jifa. Dan bayan mahaifinsa da Anwar Jadda na da 'ya'ya mata huɗu, waɗan da suka kasance ƙannen mahaifinsa.
Ba tare da knocking ko danna door bell ba ya buɗe ƙofar gidan ya shiga, a ɗan hall ɗin dake bakin ƙofa ya tsaya ya cire takalmansa, ya saka wasu da ya ga a wurin, sannan ya shiga falo yana dube-dube. Bai ga kowa ba bayan wata kyakkyawar budurwa da ta fito daga ƙofar da ya san cewa kitchen ne. Hannunta riƙe da tray, wanda kallon kyanta bai sa ya san miye a ciki ba. Da alama ta ji buɗe ƙofar tasa ne shi yasa ta fito dan ganin wanda ya zo.
“Marhaba”
Ta faɗa tana kallonsa da murmushi, dan ita ta san shi, shi ne dai alamu suka nuna cewa bai santa ba. Kansa ya jinjina kawai yana ƙare mata kallo, ba zai yi ƙarya ba, yarinyar tana da kyau.
“Aina Jadda” (Ina Jadda)
“Bi gurfatah, kallini nadilah. (Tana ɗakinta, bari na kirata)”
Ta amsa da muryarta me daɗin saurare. A living room ya zauna yana ci gaba da kallon matashiyar, har ta nufi corridor ɗin da zai sadata da upstairs. Sai a lokacin ya ɗauke idonsa a kanta, yana zaune a wurin har ta dawo, ta sanar masa ga Jaddan na sauƙowa, sannan ta koma kitchen ɗin.
Tun da Jadda ta fito take wurga masa harara, har ta iso living room ɗin, ta zauna a gefe da shi tana kallonsa a kaikaice. Kuma duk da ya lura da hakan bai sa ya fasa dariya ba.
“Masa'ul khair ya Jadda. (Barka da yamma Jadda)”
Jadda ta masa banza ta ɗauke kai tana girgiza ƙafa.
“Ƙira nawa na maka?”
Ta tambaya bayan wani lokaci.
“A ƙalla goma”
Arman ya amsa.
“To me yasa ba ka ɗaga ba?”
“Saboda na san maganar da za ki faɗa, shi yasa na zo tun kafin ki ce na zo”
Jadda ta kuma yin shiru.
“Arman zo nan”
Ya dubeta, sai ya miƙe ya koma gefenta ya zauna.
“Magana nake so mu yi...”
Ya jinjina mata kai, yana kallon yarinyar nan da ta dawo falon ɗauke da kayan taɓawa, ta aje a kan center table, sannan ta juya ta koma kitchen.
“Jadda wace ce wannan?”
Ya tambaya. Jadda ta harare shi, dan ta lura tun da ta shigo falon yake kallonta har ta koma inda ta fito.
“Gufran sunanta, ita ce yarinyar gwaggonka Bilƙisa, wadda ke Qatar.”
“Ohh na gane. To ina jinki”
Ya amsa yana jinjina mata kai.
“Da Anwar da Iƙbal duka 'ya'yana ne. Da kai da Faisal jikokina ne, haka Gulzar da Sakina. Amma Wallahi har cikin raina na fi son ka zamto magajin Alhadi fiye da Faisal Arman...”
Arman ya yi murmushi, dan ya san tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi.
“Jadda me yasa kowa yake son na zama shugaban Alhadi?”
Ya matambaya.
“Saboda kai kafi cancantar zama shugaba... Alhadi kamfanin mahaifinka ne, Anwar hannun jari kawai yake da shi!”
Jadda ta ba shi amsa, ya girgiza kansa yana murmushi.
“Jadda bani da suffofin shugabanci, saboda inada nakasar gani, ba zan iya shugabanci ba”
“Arman! Ka ga wannan kujerar dake cikin office ɗin Iƙbal? Ka ɗauketa tamkar kujerar wata babbar masarauta a zamanin baya. Wadda ake yaƙi da zubar da jini duk domin a mallaketa, wannan kujerar na dai-dai da kujerar katafariyar fada a zamanin baya!”
“To wai duk me ya kawo wannan zancen?”
Jadda ta yi murmushi.
“Saboda ba ma so ka bamu kunya. Nan da kwana uku zagayowar ranar da aka haifeka. Iyayenka na shirya maka babban shagalin taya murna. Kuma a wurin shagalin mahaifinka ya ɗauki niyyar baka takardun shugabancin gamayyar kamfanunuwan Alhadi, domin ka sa hannu a matsayinka na shugaba na gaba. Kuma ba na fatan ka bamu kunya Arman!.”