Sashe 25
Hurriya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hamad ya girgiza kai.
“Aa ba soja nake so ba?”
Namra ta ce.
“To me kake so? Wannan zuciyar taka Hamad ai soja ya dace da kai”
“Aa ni Likitan idanu nake son zama, idan na kware zan yi ma Hurriya aiki ta, ita ma ta rika gani kamar kowa”
Tsit katon falon na Hajiya Kaltume yayi domin babu wanda ya za ci abun da zai fito daga bakin Hamad kenan. Hurriya ta yi murmushi tana masa kallo irin na so da kaunar dan'uwa, ita kanta ba yi zaton Hamad yana sonta kuma ya kula da damuwarta har haka ba.
“Come here my friend”
Yasir ya mika masa hannu, sai ya taso ya iso gurin Yasir din Yasir ya rumgume yana buga bayansa.
“Yayi kyau babban mutum”
Cikin jindadi da alfahari Appa ya kalli Hamad ya ce.
“Da yardar Allah da yardar Allah, Hamad ba zaka yi karatu a kasar nan ba, waje zan kai ka ka sha ilmin akan idanuwa har ka gaji, da ikon Allah wannan kudirin naka sai ya cika ko da bana raye”
Hajiya Kaltume da ta rasa abun da zata yi ta kalli Appa da murmushin dole.
“Za a karya dokar fitar da yara waje karatu kenan Alhaji akan Hamad?”
“In Shaa Allah, ba shi kadai ba Hurriya ma ba zata yi karatu a kasar nan ba, yadda take da kokarin nan waje ya kamata ta yi karatu, kuma ko ba ni ba Principal dinsu ya fada min suna sa ran da zarar ta gama secondary school zata samu scholarship mai kyau a manya kasasshe saboda kokarinta da yadda take cin gasa ta bangaren lissafi”
“Maa Sha Allahu, Allah ya nuna mana yara masu albarka Allahu akbar Allah dai yayi albar....ya bar zumunci”
Sai ta kasa karasa da Allah yayi albarka ta canja zuwa Allah ya bar zumunci, domin ta san hausawa sun ce addu'ar makiyi karɓaɓɓiya ce, ita ko ba zata so su yi albarka ba. Gashi abun da Appa ya fada cewar yaran Iyami za su karatu a waje ya daki zuciyarta mugun daka irin dakan da ace mashi ne, babu abun da zai hana ya bullo ta bayanta, yanayinta ma gaba daya sai ya sauya hankalinta yayi mugun tashi, ba dan ta yaki zuciyarta ba wata kila ma da ta rasa sukuninta har kowa ya gane halin da take ciki.
“Allah sarki dan'uwa mai kaunar yar'uwarsa, duk da fadan nan da kuke da rashin jituwa wannan soyayyar da kaunar tana nan a zuciyarsa, Allah ya kara hada kanku, ya shirya mana”
Kowa ya amsa addu'ar da Hajiya Binta ta yi da Ameen ban da Hajiya Kaltume da gume ma ya karye mata kamar wadda aka kwancewa zane a kasuwa. Daga bangaren Hajiya Kaltume Hajiya Binta ta fito ta shiga bangaren Momy suka gaisa sannan ta fito tana jin kewar Iyami. Sai addu'a take ma Appa idan dawowar Iyami alheri ce Allah ya daidaita tsakaninsu, ya kasa amsawa da ameen bayan kuma abun da yake nema kenan a zuciyarsa. Mota daya suka shiga Hurriya bayan ta dauko mayafinta, ita da Hajiya suka zauna a back seat, Appa da Hamad kuma suka shiga gaba, Appa yana jan motar suka fi daga gidan.
After mintuna goma da tafiyar Hajiya Binta, Momy ta fito tare da bakuwarta da kuma ɗanta da be ci komai ba a cikin abubuwan da Momy ta saka a shirya musu, Miwan na bayansu tare da dan'uwansa Musib sun yi ma bakuwar Momy da ďanta rakiya ban da Namra da har yanzu tana can bangaren Hajiya Kaltume.
“Captain ai yana yawan zuwa nan, duk lokacin da zai zo garin na ba ya tafiya sai ya shigo, ina jindadin haka Wallahi”
Hajiya Turai ta yi murmushi.
“Ai danki idan yana son mutum to ya huta, Allah ya hada jininku”
“Sosai kam, Allah dai ya nuna mana lokacin auren nan mu rakwashe”
Cewar Momy, Mutumen da aka ta maganar akansa be ce uffan ba ya fara sauko Entrance din hannu dafe a kirjinsa yana murza a hankali domin ba karamin zafi ya ji ba a lokacin da suka yi karo da Hurriya, taku daya biyu uku hudu yayi kamin ya ja ya tsaya yana kallon yadda tsaddadiyar motarsa ta yi ta kasa gaba daya, saboda tayun motar da aka succe duka hudu. Ya juyo ya kallesu.
“Waya taba motar nan?”
“Wace motar?”
Kusan a tare suka kalli motar Musib yayi sauri sauka ya karasa gurin motar da mamaki.
“Lafiya kalau kuka zo da ita?”
“Idan bata da lafiya zamu zo da ita ne? What kind of stupid question is this!”
“Subhanallahi, garin ya haka ta faru!”
Cewar Momy tana saukowa ta nufi gurin motar. Miwan ya ce
“Gaskiya wannan succe tayun aka yi”
“To waya aikata haka? Wannan dai rainin wayo ne da neman mutum yayi magana ace ya cika masifa”
Ya fada da karfi wani karin bacin dai na tunkarosa, cikin bakinciki ya sauka ta isa gurin motar. Momy ta kai hannu ta dafa karjikinsa.
“Kwantar da hankalinka Captain, a cikin yaran nan dai wani ba zai yi gigin yi maka haka ba, akwai dai matsalar da aka samu”
Momy na rufe Hajiya Turai ta miko masa hannu kamar wani karamin yaro dan yaye.
“Captain shigo ka zauna, sai mu shiga wata motar”
Ya sauke ajiyar zuciya tare da jan dagon numfashi ya fi sau goma, sannan ya shuri motar da kafarsa da karfi.
“Duk wanda yayi min haka da gangan yayi, saboda a bata min rai”
“Toh waye zai maka haka Captain? Dan Allah karka bata ranka, na gano, yanzu haka ba zai wuce bakar matar can ba Kaltume, domin na dade da lura da yar bakinciki ce ta karshe”
Momy tana maganar tana jin kamar ta yi tsalle taje ta shake wuyan Hajiya Kaltume.
“Oh kekam baki zaune cikin mutane kwarai Hajiya Nafisa, rayuwa a gidanku tana da wahala”
Momy ta amsawa Hajiya Turai tana kwafa.
“Barta na san yadda zan yi maganinta, da ni take zancen, Captain yi hakuri shigo ka huta sai ka dauki motata ku tafi da ita, idan an gyara wannan Musib zai kai maka ita gida”
Jameel ya juyo ya nufo hanyar falon, sai duk suka dugunzuma suka biyo bayansa, ban da Hajiya Turai da bata matsa daga inda take tsaye ba tun bayan da suka fito daga falon. Cikin natsuwa da kamala ya shiga falon, sai ka rantse ba shi ne ya gama bacin rai a waje ba, zaunawa yayi ya hade hannayensa ya sadda kai kasa ya rufe ido yana motsa bakinsa a hankali, kokari yake na ganin be bar bacin ransa ya ninku a zuciyarsa ba...
[10/20, 6:25 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣4️⃣
Namra ta dago ta dubi kofar shigowa falon tana amsa sallama, sai ta mike tsaye da sauri tana kallon Captain da mamaki, zuwansa a yanzu ya bata mamaki tsabanin baya da bata mamakin zuwansa domin ya saba zuwa gidan a duk lokacin aiki ya kawo shi ko ziya, tana mamakin zuwansa ne kasa da wata uku da faruwar abun da ya fusata shi, wato fasa masa tayun mota da Hamad yayi suke zaton Hajiya Kaltume ce ta saka aka aikata haka. Ba kasafai yake sake zuwa gurin da aka bata masa rai ba, idan ma zai sake komawa a gurin sai ya dauki lokaci mai tsawo har an manta da shi yake sake zuwa, wannan ya saka duk wani makusancinsa da yake son alaka da shi ta daure ko da iyayensa yake kokarin kiyaye duk wani abu da zai batawa dan gatan Ammy kuma ďa daya tilo ga Alhaji Aliyu Turaki. Wata kila haduwar jinin da Allah ya saka tsakanin Momy da ďan Yayanta ya wuce yayi mata haka. Fuska ba yabo ba fallasa ya shigo falon hannayensa duka biyu suna bayansa.
“Sannu da zuwa Ya... Captain”
Tunawa da ta yi baya son ace masa Yaya ya saka ta kasa karasa sai ta kiranshi da sunan da kowa yake kiransa.
“Yauwa hutawa kike?”
“Eh bari na kira Momy tana ciki”
Tana juyawa ya dakatar da ita.
“No Wait... Ina yarinyar nan take Namra?”
Ta juyo tana wara alamar bata fahimce wadda yake tambaya ba.
“Wata fara haka mai dan tsayi marar jiki, mai saka glasses”
“Oh Hurriya, tana bangaren Hajiya a kirata”
Ya daga mata kai, sai ta aje remote din hannunta ta nufi kofar fitar ta fice da sauri, da mamaki da tunanin dalilin kiran Hurriya ta isa bangaren Hajiya Kaltume, sai ta ci karo da Hurriya tana rike da tiyo tana watsawa motar Yasir ruwa, Hamad kuma na ta kada kumfa.
“Hurriya”
“Uhmm”
Ta juyo ta kalleta.
“Wai ki zo ana kiranki Captain...”
“Waye Captain...?”
“Ina wani wadda na ganku tsaye a bakin kofar Momy har na dauko miki glashinki da ya fashe? Kin tuna”
Hurriya ta yi shiru ta dan bata fuska, kuma ta kasa amsawa Namra da ta tuna ko ba ta tuna ba.
“Wanda ya mareki?”
Hamad ya tambaya, Hurriya ta daga masa kai Namra ta zaro ido domin bata saka ran marinta yayi ba, ta san dai akwai abun da yake faruwa.
“Au daman marinki yayi? Ikon Allah me kika masa?”
“Wucewa na zo yi ban gani ba muka yi karo shi ne ya mare ni har gilashina ya fashe”
“Ni kuma na fasa masa tayun mota duk biyu da wuka”
Namra ta rufe baki with mamaki. Hurriya ma masa kallon rashin jindadi fadar da yayi a yanzu.
“Daman kai ka fasa tayun nan? An kusan yaki a gidan nan fa saboda an fasa tayun Captain, Allah ya tsare ka Momy bata sani ba, da sai ka zama abun tausayi”
“Ni ina ruwana”
Ya fada yana turo baki.
“Captain akwai zafin zuciya ko shi zai iya maka hukunci babu ruwansa da alakarka a gidan nan, to yanzu dai shi ya ce a kiraki”
“Aa ba soja nake so ba?”
Namra ta ce.
“To me kake so? Wannan zuciyar taka Hamad ai soja ya dace da kai”
“Aa ni Likitan idanu nake son zama, idan na kware zan yi ma Hurriya aiki ta, ita ma ta rika gani kamar kowa”
Tsit katon falon na Hajiya Kaltume yayi domin babu wanda ya za ci abun da zai fito daga bakin Hamad kenan. Hurriya ta yi murmushi tana masa kallo irin na so da kaunar dan'uwa, ita kanta ba yi zaton Hamad yana sonta kuma ya kula da damuwarta har haka ba.
“Come here my friend”
Yasir ya mika masa hannu, sai ya taso ya iso gurin Yasir din Yasir ya rumgume yana buga bayansa.
“Yayi kyau babban mutum”
Cikin jindadi da alfahari Appa ya kalli Hamad ya ce.
“Da yardar Allah da yardar Allah, Hamad ba zaka yi karatu a kasar nan ba, waje zan kai ka ka sha ilmin akan idanuwa har ka gaji, da ikon Allah wannan kudirin naka sai ya cika ko da bana raye”
Hajiya Kaltume da ta rasa abun da zata yi ta kalli Appa da murmushin dole.
“Za a karya dokar fitar da yara waje karatu kenan Alhaji akan Hamad?”
“In Shaa Allah, ba shi kadai ba Hurriya ma ba zata yi karatu a kasar nan ba, yadda take da kokarin nan waje ya kamata ta yi karatu, kuma ko ba ni ba Principal dinsu ya fada min suna sa ran da zarar ta gama secondary school zata samu scholarship mai kyau a manya kasasshe saboda kokarinta da yadda take cin gasa ta bangaren lissafi”
“Maa Sha Allahu, Allah ya nuna mana yara masu albarka Allahu akbar Allah dai yayi albar....ya bar zumunci”
Sai ta kasa karasa da Allah yayi albarka ta canja zuwa Allah ya bar zumunci, domin ta san hausawa sun ce addu'ar makiyi karɓaɓɓiya ce, ita ko ba zata so su yi albarka ba. Gashi abun da Appa ya fada cewar yaran Iyami za su karatu a waje ya daki zuciyarta mugun daka irin dakan da ace mashi ne, babu abun da zai hana ya bullo ta bayanta, yanayinta ma gaba daya sai ya sauya hankalinta yayi mugun tashi, ba dan ta yaki zuciyarta ba wata kila ma da ta rasa sukuninta har kowa ya gane halin da take ciki.
“Allah sarki dan'uwa mai kaunar yar'uwarsa, duk da fadan nan da kuke da rashin jituwa wannan soyayyar da kaunar tana nan a zuciyarsa, Allah ya kara hada kanku, ya shirya mana”
Kowa ya amsa addu'ar da Hajiya Binta ta yi da Ameen ban da Hajiya Kaltume da gume ma ya karye mata kamar wadda aka kwancewa zane a kasuwa. Daga bangaren Hajiya Kaltume Hajiya Binta ta fito ta shiga bangaren Momy suka gaisa sannan ta fito tana jin kewar Iyami. Sai addu'a take ma Appa idan dawowar Iyami alheri ce Allah ya daidaita tsakaninsu, ya kasa amsawa da ameen bayan kuma abun da yake nema kenan a zuciyarsa. Mota daya suka shiga Hurriya bayan ta dauko mayafinta, ita da Hajiya suka zauna a back seat, Appa da Hamad kuma suka shiga gaba, Appa yana jan motar suka fi daga gidan.
After mintuna goma da tafiyar Hajiya Binta, Momy ta fito tare da bakuwarta da kuma ɗanta da be ci komai ba a cikin abubuwan da Momy ta saka a shirya musu, Miwan na bayansu tare da dan'uwansa Musib sun yi ma bakuwar Momy da ďanta rakiya ban da Namra da har yanzu tana can bangaren Hajiya Kaltume.
“Captain ai yana yawan zuwa nan, duk lokacin da zai zo garin na ba ya tafiya sai ya shigo, ina jindadin haka Wallahi”
Hajiya Turai ta yi murmushi.
“Ai danki idan yana son mutum to ya huta, Allah ya hada jininku”
“Sosai kam, Allah dai ya nuna mana lokacin auren nan mu rakwashe”
Cewar Momy, Mutumen da aka ta maganar akansa be ce uffan ba ya fara sauko Entrance din hannu dafe a kirjinsa yana murza a hankali domin ba karamin zafi ya ji ba a lokacin da suka yi karo da Hurriya, taku daya biyu uku hudu yayi kamin ya ja ya tsaya yana kallon yadda tsaddadiyar motarsa ta yi ta kasa gaba daya, saboda tayun motar da aka succe duka hudu. Ya juyo ya kallesu.
“Waya taba motar nan?”
“Wace motar?”
Kusan a tare suka kalli motar Musib yayi sauri sauka ya karasa gurin motar da mamaki.
“Lafiya kalau kuka zo da ita?”
“Idan bata da lafiya zamu zo da ita ne? What kind of stupid question is this!”
“Subhanallahi, garin ya haka ta faru!”
Cewar Momy tana saukowa ta nufi gurin motar. Miwan ya ce
“Gaskiya wannan succe tayun aka yi”
“To waya aikata haka? Wannan dai rainin wayo ne da neman mutum yayi magana ace ya cika masifa”
Ya fada da karfi wani karin bacin dai na tunkarosa, cikin bakinciki ya sauka ta isa gurin motar. Momy ta kai hannu ta dafa karjikinsa.
“Kwantar da hankalinka Captain, a cikin yaran nan dai wani ba zai yi gigin yi maka haka ba, akwai dai matsalar da aka samu”
Momy na rufe Hajiya Turai ta miko masa hannu kamar wani karamin yaro dan yaye.
“Captain shigo ka zauna, sai mu shiga wata motar”
Ya sauke ajiyar zuciya tare da jan dagon numfashi ya fi sau goma, sannan ya shuri motar da kafarsa da karfi.
“Duk wanda yayi min haka da gangan yayi, saboda a bata min rai”
“Toh waye zai maka haka Captain? Dan Allah karka bata ranka, na gano, yanzu haka ba zai wuce bakar matar can ba Kaltume, domin na dade da lura da yar bakinciki ce ta karshe”
Momy tana maganar tana jin kamar ta yi tsalle taje ta shake wuyan Hajiya Kaltume.
“Oh kekam baki zaune cikin mutane kwarai Hajiya Nafisa, rayuwa a gidanku tana da wahala”
Momy ta amsawa Hajiya Turai tana kwafa.
“Barta na san yadda zan yi maganinta, da ni take zancen, Captain yi hakuri shigo ka huta sai ka dauki motata ku tafi da ita, idan an gyara wannan Musib zai kai maka ita gida”
Jameel ya juyo ya nufo hanyar falon, sai duk suka dugunzuma suka biyo bayansa, ban da Hajiya Turai da bata matsa daga inda take tsaye ba tun bayan da suka fito daga falon. Cikin natsuwa da kamala ya shiga falon, sai ka rantse ba shi ne ya gama bacin rai a waje ba, zaunawa yayi ya hade hannayensa ya sadda kai kasa ya rufe ido yana motsa bakinsa a hankali, kokari yake na ganin be bar bacin ransa ya ninku a zuciyarsa ba...
[10/20, 6:25 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣4️⃣
Namra ta dago ta dubi kofar shigowa falon tana amsa sallama, sai ta mike tsaye da sauri tana kallon Captain da mamaki, zuwansa a yanzu ya bata mamaki tsabanin baya da bata mamakin zuwansa domin ya saba zuwa gidan a duk lokacin aiki ya kawo shi ko ziya, tana mamakin zuwansa ne kasa da wata uku da faruwar abun da ya fusata shi, wato fasa masa tayun mota da Hamad yayi suke zaton Hajiya Kaltume ce ta saka aka aikata haka. Ba kasafai yake sake zuwa gurin da aka bata masa rai ba, idan ma zai sake komawa a gurin sai ya dauki lokaci mai tsawo har an manta da shi yake sake zuwa, wannan ya saka duk wani makusancinsa da yake son alaka da shi ta daure ko da iyayensa yake kokarin kiyaye duk wani abu da zai batawa dan gatan Ammy kuma ďa daya tilo ga Alhaji Aliyu Turaki. Wata kila haduwar jinin da Allah ya saka tsakanin Momy da ďan Yayanta ya wuce yayi mata haka. Fuska ba yabo ba fallasa ya shigo falon hannayensa duka biyu suna bayansa.
“Sannu da zuwa Ya... Captain”
Tunawa da ta yi baya son ace masa Yaya ya saka ta kasa karasa sai ta kiranshi da sunan da kowa yake kiransa.
“Yauwa hutawa kike?”
“Eh bari na kira Momy tana ciki”
Tana juyawa ya dakatar da ita.
“No Wait... Ina yarinyar nan take Namra?”
Ta juyo tana wara alamar bata fahimce wadda yake tambaya ba.
“Wata fara haka mai dan tsayi marar jiki, mai saka glasses”
“Oh Hurriya, tana bangaren Hajiya a kirata”
Ya daga mata kai, sai ta aje remote din hannunta ta nufi kofar fitar ta fice da sauri, da mamaki da tunanin dalilin kiran Hurriya ta isa bangaren Hajiya Kaltume, sai ta ci karo da Hurriya tana rike da tiyo tana watsawa motar Yasir ruwa, Hamad kuma na ta kada kumfa.
“Hurriya”
“Uhmm”
Ta juyo ta kalleta.
“Wai ki zo ana kiranki Captain...”
“Waye Captain...?”
“Ina wani wadda na ganku tsaye a bakin kofar Momy har na dauko miki glashinki da ya fashe? Kin tuna”
Hurriya ta yi shiru ta dan bata fuska, kuma ta kasa amsawa Namra da ta tuna ko ba ta tuna ba.
“Wanda ya mareki?”
Hamad ya tambaya, Hurriya ta daga masa kai Namra ta zaro ido domin bata saka ran marinta yayi ba, ta san dai akwai abun da yake faruwa.
“Au daman marinki yayi? Ikon Allah me kika masa?”
“Wucewa na zo yi ban gani ba muka yi karo shi ne ya mare ni har gilashina ya fashe”
“Ni kuma na fasa masa tayun mota duk biyu da wuka”
Namra ta rufe baki with mamaki. Hurriya ma masa kallon rashin jindadi fadar da yayi a yanzu.
“Daman kai ka fasa tayun nan? An kusan yaki a gidan nan fa saboda an fasa tayun Captain, Allah ya tsare ka Momy bata sani ba, da sai ka zama abun tausayi”
“Ni ina ruwana”
Ya fada yana turo baki.
“Captain akwai zafin zuciya ko shi zai iya maka hukunci babu ruwansa da alakarka a gidan nan, to yanzu dai shi ya ce a kiraki”