← Book details Hurriya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 29

Sashe 11

Hurriya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ba zaki bada hakuri ba yar iskar yarinya? Idan kuma ba haka ba ne sai ki fadi yadda aka yi ai ko?”

“Appa Wallahi karya take min, yarinyar nan munafukace sai dai idan labe ta yi, ko kuma so take ta hada min sheri”

Tana rufe baki Yasir ya fara dukan bakin nata ya saka hannnunsaya kama lips din ya jan sai da ta ti ihu sannan ya rufe ta da duka gaba daya, Hajiya Kaltume ta fara kokarin kwatar yarta Appa kuma ya fice daga falon ba tare da ya hana Yasir dukan Khairi ba.

“Ai fa an taba yar gata yar gaban goshi yar lasa da halshe, kai dan Allah karka kashe min ƴa saboda ƴar wasu da ba zata amfana maka komai ba”

Hajiya Kaltume na masifa tana kwatar Khairi dake ta rusar ihu, Maama da Salma sai haushi suke ji saboda ana dukan yar'uwarsu Ruma ce kadai take jin abun da yayarta ta yi bata yi daidai ba.

A bangaren Hurriya Appanta na fita sai ta tsagaita kukanta ta share hawayen da suka ki tsaya mata ta saka gilashin da zai bata ganin kofar fita dakin daidai ta mike tsaye ta fito daga bangaren mahaifinta ta dawo na su bangaren tana tafe tana hawaye har ta isa. Sai ta ta tura kofar falon ta bude sai kuma ta kasa shiga domin jin take kamar Amma ma mutuwa ta yi ba barin gidan ba bata taba sanin haka kewa take ba sai yau da ta yi kewar mahaifiyarta. Kusan da ita da wanda ba shi da lakka a jiki duk daya domin tun a yanayin tafiyarta zaka fahimci zuciyarta ta karaya salulu ta shigo falon ta zauna kan kujera har lokacin Hamad na zaune a inda ta barshi, sai dai a yanzu fuskarsa na nuna danuwar dake zuciyarsa domin ya bata rai sosai ba kamar dazun ba d ya bar abun a cikin zuciyarsa. Fashewa Hurriya ta yi da kuka tana girgiza kai ji take kamar ace mata ba gaske ba ne, da ace ta san sakin Amma Appanta yayi babu abun da zai hana ta binta, da ba zata yarda ta zauna a gidan ba, a yanzu kam ta yarda ita wawuya ce da bata yi saurin ganewa ba, domin tana da saurin yarda idan aka fada mata abu dauka take ko da kuwa ba gaskiya ba ne. Kukanta ne ya saka Hamad hawaye yana ta dantse baki yana boye cikarsa domin zuciyarsa kawowa take kamar wani zaki, amman sai duk da hakan sai ya gagara rike kansa shi ma ya fasa kuka, ita da shi suka zama kamar wadanda aka cewa Amma ta mutu ta bar su.

“Hurriya Hamad”

Kusan a tare suka dago suka kalli kofar gefen Dinning din kofar da Appa ke tsaye, kofar cikin falon Amma ce dake basu damar shiga bangaren Appansu. Hurriya ta tashi da sauri ta nufi inda yake tana kuka sosai Hamad kuma ya dauke ido alamar baya son ganin Appa.

“Wannan kuka sai kace an yi mutuwa? Haba karku saka kanku a damuwa tsakanin halshe ra hokora ma ana basawa balle kuma mutum da mutum, dan tsabani muka samu shi ne Amma ta tafi gida, amman da zarar al'amurra sun daidaita zata dawo”

Hurriya ta kasa magana sai kuka take, Hamad kuma ya mike tsaye ya share hawayensa ya nufi sama.

“Karka shiga, ba a nan zaku kwana ba, na yi magana da Momynku a can zaku kwana ku zo muje”

Be jira cewarsu ba ya kama hannun Hurriya zuciyarsa na masa babu dadi, daman can shu baya son kukan wani ko ganin wani a damuwa balle kuma yaransa, sanin cewar shi ne silar damuwar ya saka shi jin babu dadi gaba daya abubuwan sun zo masa ta yadda be yi zato ba. Ganin Appa ya nufi kofar fita falon tare da Hurriya ya saka Hamad ya bi bayansu, sai da suka fita harabar gidan gaba daya, sannan Appa ya tsaya ya tsayar da yarsa ya daga kanta ta kalleshi.

“Haka zamu shiga bangaren Momynki kina ta kuka Hurriya? Dan Allah ku yi hakuri idan ba so kuke ni ma na yi kukan nan ba, ba ku san abun da yake cikin zuciyata ba, ina cikin wani irin tashin hankali da rudani marar misaltuwa”

Kai kawai ta iya daga masa ta saka hannayensa ta share hawayenta tana ta aikin hade kukan dake neman ya gagari tsayawa a iya bakinta da idonta.

“Ammanku ba mutuwa tayi ba, zaku iya zuwa ku ganta a duk lokacin da kuke so, ita zata iya zuwa ta ganku, Hamad na san kai ne mai zuciya ka sakawa kanka hakuri dan Allah ko dan yar'uwarka”

Ko saitin gurin da Appa yake tsaye Hamad be kalla ba, yadda ya dauke kai yana kallon wani gurin sai ka rantse da Allah ba da shi Appa yake magana ba, domin a yau kam ba shi da abokin tsana kamar Appansa saboda sanin cewar ya rabu da Amma, ko da kuwa ba zai iya fadar abun da ya faru tsakaninsu ba, hausawa suka ce mai lalabe a duhu balle an haska masa, a banza yayi fushi balle an taba shi. Appa ya dauke kai ya rika hannun Hurriya suka cigaba da tafiyar, da kansa ya shiga falon, be zarce ko ko'ina ba sai Stairs kai tsaye ya nufi dakunan da suke gefen bedroom din Momy kamar yadda suke a kowane bangare, ya san dakin Namra da na Musib da Miwan dan haka be taba dakunansu ba ya nufi wani dakin ba dabam ya tura kofar dakin sannan ya saki hannun Hurriya daki ne dake dauke da furniture na mutum daya domin Appa ya saka an zuba furniture an gyara ko wane daki duk kuwa da kasancewar wasu dakunan babu kowa, ba dan komai ba sai dan irin haka ko kuma idan an yi baki ko ma idan yaransa sun yi sha'awar canja daki daga wani zuwa wani. Hurriya ta daga kafarta ta shiga cikin dakin ta isa bakin gadon da zai wadaci mutum daya ta juyo ta zauna ta a hankali tana kallon Appanta dake jan kofar dakin. Gam... Kofar na amsawa gabanta ya yanke ya fadi, gaba daya sai ta ji kamar wata duniyar aka kawo ta, sai ta ji kamar wani gidan da bata san kowa ba kuma bata da gatan kowa a ciki aka kawota. Rabon da ta shiga bangaren Momy ma an dade, babu ruwanta da bangare sai da dalili ita ma Momy bata shiga nasu bangaren ita ta ware kanta dabam a gidan. Dayan dakin dake kusa da na Hurriya Appa ya budewa Hamad

“Nan zai mana Hamad?”

Ya daga kai sannan ya saka kai ya shige dakin da kansa ya turo kofar dakin ba tare da ya jira mahaifinsa ya rufe masa ba. Appa ya sauke ajiyar zuciya ya juya ya sauka, Namra da Musib suka hada ido suna mamakin yadda Appa ya shigo da Hurriya be ma bari ta zo da kanta ba.

“Musib ina Miwan?”

“Ya fita da magariba nan Appa”

“Namra da Musib dan Allah a zauna lafiya, yaran nan kanenku ne, jini daya ne ku da su, bana son na ji wani tashin hankali ko fada, Hamad dai kun riga kun san halinsa ba sai an fada muku ba, duk wani abun da zai yi ku kawar da ido ni kaina da nake mahaifinsa hakuri nake da shi, Hurriya kuma kun san babu ruwanta da fita dan Allah a zauna lafiya”

Nasiha yake musu amman zuciyarsa cike take da kunci da damuwa narar misaltuwa. Appa ya amsa cike da ladabi

“In Shaa Allahu Appa”

Ya dan motsa kansa kadan alamar gamsuwa sannan ya nufi kofar fita.

“Sai da safe Appa mu kwana lafiya”

“Allah yasa”

Ya amsa sannan ya fice. Yana sakin kofar falon Musib yayi kwafa ya mike tsaye ya nufi stairs Namra ta bi bayansa, ita ta shige dakin Momy Musib kuma ya nufi dakin da zuciyarsa ta raya nasa Hurriyya na ciki. Ya tura kofar dakin kamar abun arziki ya tsaya daga bakin kofa yana kallonta idonta shar da hawaye.

“Yar gatan Appa, da kansa ya riko hannunsa ya kawo ki, kuma saboda ke yayi ta fada da Momy”

Uffan Hurriya bata ce masa ba, har ya gaji da tsayuwa ya bar mata kofar a bude yayi tafiyarsa. Runtse ido ta yi tana jin wani sabon kuka na zo mata, ta dawo a rakube gurin ta ta san cewar zata sha azaba da wahalar zama, da ma ace bangaren Hajiya Kaltume aka ajeta ko ba komai zata samu sauki ta wani bangaren saboda Yasir, amman a na bangaren ta san babu mai sonta, gaba daya sai ta ji ta zama wata marainiya ashe ba sai da rashin uwa da uba ake maraici ba. Musib na barin kofar dakin Hurriya ya nufi dakin Hamad ya tura, kwance ya hango shi saman gadon ya baya kofar baya, kuma budewar da Musib yayi be saka Hamad juyo dan ya duba ko waye ba. Wani mugun kallo da tsana irin ta yan uba Musib ya jefi kanensa da shi, sannan ya bar kofar dakin shi ma be rufe masa ba, Hamad na jin alamar an tafi ya juyo ya sauko saman gadon ya iso gurin kofar ya rufe ta da karfi ya saka key, Musib da be jima da barin bakin kofar ba ya juyo ya kalli kofar jin yadda aka bugata da karfi.

“Zaka sha wahala yaro”

Yayi kwafa ya nufi dakin Momy sai wani huci yake kamar mace, daman shi ne mai kishin da matan ubansa a gidan sai dai yana boye abun a zuciyarsa, yadda yake jin kiyayyar Iyami da Hajiya Kaltume ko Momynsa bata jin kiyayyarsu haka domin ita sai idan kishin ya motsa mata ne take kula su ko kula wani abu da ya shafesu.
Chapter 11 · 0% Book details