Sashe 10
Hurriya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hurriya ta dauki plate ta bude manya warmers din ta ta dauki mulmular tuwon da aka nade a leda ta raba uku ta zuba daya a plate ta rufe ta bude dayan ta zuba miyar kubewa ďanye ta saka nama da man shanu sannan ta rufe ta ja kujera har ta zauna ta tuna bata wanke hannu ba ta tashi ta shiga bandakin dake falon ta wanke hannunta ta dawo ta zauna ta fara cin tuwon, sai da ta yi nisa da cin abincin sannan Khairi ta kalleta.
“Hurriya”
Hurriya ta dago a hankali ta kalli yayarta Khairi wadda ta kira sunanta.
“Na'am?”
“Me Appa yace miki da ya aiko a kira ki?”
“Tambayarmu yayi ina muke son zama”
“Toh ina kika zaba?”
“Ni dai na ce gurin Gwaggo ko Hajiya, amman yace aa sai dai gurin Momy”
Khairi ta yi fuskar tausayi.
“Allah sarki, Wallahi na tausaya muku babu dadi rayuwa gidan babu uwa a gida, da ma dai Appa zai yi hakuri da ya dawo da Amma, Hurriya na ga Appa yana jin maganarki why not ki roke shi ya dawo da Amma idan ma wani laifin ta yi masa ya yafe mata”
Hurriya ta yi mata wani kallo na rashim fahimtar inda zancenta ya dosa.
“Amman zata dawo idan ta haihu ai”
“Toh Allah yasa ya maida ita, wata kila akwai gyara ai Wallahi duk ban jidadi ba dazun har da kukana”
Hurriya na jin haka sai kwakwalwarta ta dauka sarai ta gane karatun Khairi a take wani irin tashin hankali ya same ta, idonta dake cikin farin gilashi suka cika da hawaye ta kasa hade lomar tuwon dake bakinta. Slowly ta mike tsaye taja kujera baya ta fara tafiya zuciyarta na buga kamar zata fasa kirjinta ta fito, tana fita falon ta watsa da gudu bangarensu da karfi ta tura kofar falon Amma ta shiga. Hamad na kwance kan kujera yana kallon remote a hannunsa.
“Hamad wai Appa sakin Amma yayi? Wai rabuwa suka yi? Yaya Khairi ta fada min”
Tana maganar yana kuka even though bata gama tabbatarwa ba. Hamad ya tashi zaune yana kallonta.
“Ai ke ce mahaukaciya shiyasa baki gane ba”
A nan Huriyya ta samu damar fashewa da kuka mai karfi, ta juya da sauri ta nufi bangaren mahaifinta.
*** *** ***
“Ah Ah Alhaji ina ce Kaltume ce Babba a gidan nan? Me zai hana su zauna a bangarenta?”
Appa ya mike tsaye.
“A nan nake son su zauna, kuma nan za su zauna ko kin yarda ko baki yarda ba, domin ke da su duk a karkashin ikona kuka kuma a gidana”
“Aa Alhaji gaskiya ban ci ƙashi ba ba zan ci aman tsoka ba! Har ina? Yara da girmansu da komai a kawo min su? Da wani abun arziki ne ai matarka take tarewa ta karbe sai a yanzu da yake wahala ce za a kawo min”
Appa ya nuna kansa.
“ƴaƴane wahala Nafisa? Ke dai har abada ba zaki taba zama matar kirki, har abada mai hali be taba fasa halinsa ba, kowa yana girma yana kara hankali da hali na gari amman ban da ke”
“Daman ni ban taba haske a idonka ba, masu haske Iyami ce da Kaltume, ka san ni ka san halina ni bana son a shiga sabgata ina bangarena babu ruwana da kowa, akan me yanzu za a dauko yayar sarauniyar gida mace da ta hana ka ganin martaba a kawo min”
Alhaji Haruna ya nuna ta da yatsansa.
“Sau daya tak bakinki ya sake furta wata magana marar dadi akan Iyami da yayanta sai mugun saba miki, ni na zabi su zauna a nan kuma a nan din za su zauna, idan baki son zama da ƴaƴana jinina ƙofar gidan a bude take..!”
Momy ta aje numfashi da karfi.
“Bismillah ga dakuna nan su zabi wanda suke so su zauna, gidan naka ne yaya naka ne ni ma taka ce Allah ya ba mu hakurin zama”
Fuuuu! Appa ya fice daga falon nata cikin mugun bacin rai. Namra da Musib suka bishi da kallo su kansu sun manta when last su ga mahaifinsu a cikin bacin rai irin wannan sai yau.
“Tsakani da Allah takurawa ce dawowarsu a nan, musamman ma dan iska yaron nan Hamad ni ubansa zan ci Wallahi”
Cewar Musib yana jin haushin hukuncin da mahaifinsu ya yanke. Bakinciki ya hana Momy sake cewa komai ta kai hannu ta dauki sarkar zinarinta dake kan aje a hannun kujera ta mike tsaye ta nufi upstairs, kamin ta isa dakinta ma wani aiki ne saboda izza da isa kamar wadda bata son taka kasa haka take tafiya.
Bakin gadonta ta zauna ta rike da sarkar sai cika take tana batsewa, ita dai ta san tana daga kafa akan kishi da matan Alhaji Haruna domin ganin take babu sa'arta a cikinsu Hajiya Kaltume dai yar talakawa ce arzikin na Alhaji Haruna Mai Yadi ne, Iyami ma haka rufin asirinsu na Alhaji Haruna ne domin har gidan da iyayenta suke ciki a yanzu shi ya siya musu shi yake dauke da nauyinsu.
Kuma Iyami ba sa'arta bace a shekaru, kuma ta fi Hajiya Kaltume zama makaskanciya a idonta domin ita ga aiki ta zo yi a gidan ta aure Alhaji Haruna, ba dan ma da kaddarar aure ta hana ba kuma yara sun shiga tsakani ba wata kila da ba zata iya hakurin sharing miji daya da yar aikin gida ba, kallon da take yi ma Amma bata da ajin da zata yi kishi da ita sai idan abun ya motsa.
Ita dai abun da ta fi tsana shi ne a shiga sabgarta, idan ta shiga sha'aninta na masu arziki har mantawa take da Hajiya Kaltume da Amma, a yanzu kuma kawo mata Hurriya da Hamad da Appa ya dage sai shi ne abun bacin ranta a yanzu, domin da su zauna a gurinta kara ya dawo da uwarsu ta rainin abunta, sam sam Momy bata son yayan kowa idan ba nata ba, bata mutanta kowa sai masu kumbar susa, idan baka da arziki har ganin take kamar baka cika mutum ba.
[10/18, 5:34 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: https://chat.whatsapp.com/GJ9hOtbWbfDKmq8NrKsDIG
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 6️⃣
Da tunanin Amma Appa ya dawo apartment dinsa, tsansar biyayyarta da yadda take gujewa bacin ransa da nuna kulawa akan duk wani abu da ya shafe shi. Ya tabbatar da ita ce ba sai ya bukaci a bawa Hurriya abinci ba, matukar ta san uwar yaran bata gidan zata yi kokarin kwatantan kyautata musu kuma ta ja su a jiki, haka ma da ita ce ya zo mata da zancen dawowa ƴaƴan abokiyar zamanta a bangarenta zata yi marhabun ta karba da hannu biyu ko da kuwa bata son haka ba zata nuna har ya gani ba, duk wani abu da Amma ta san Appa yana son kokarin raya shi kaunar abun take ba ta bata masa rai ba.
Hannayensa hade a bayansa yake tafiyar fuskarsa a yanutse zuciyarsa a hargitse yana jin kamar ya fashe da kuka gaba daya ya rasa me ke samunsa ya rabu da matarsa rabuwar ta haifar masa da rashin kwanciyar hankali da bacin rai, zamanta a gidan kuma masifa ce a gidansa masifar da be san ta micece ba domin shi dai ya san matarsa bata masa laifi ba, be san dalilin da ya saka ya tsane ta ba. Kukan Hurriya ne abun da ya fara masa maraba da zuwa a lokacin da ya kunna kai cikin falonsa, kuka take sosai irin kukan nan da ya hana gilashin idonta tsaya saboda hawayen da ke cika shi, ta rike gilashin a hannu lipa dinta da jikinta sai rawa suke, dishe-dishe ta ga alamar shigowar mutum bata bukatar saka gilashi domin tantance waya shiga, ta san tsayinsa da yanayin tafiyarsa ta haddace komai. Shi ya taho da sauri ita ma ta nufo inda yake da sauri tana rike da gilashin dayan hannunta kuma yana lalabensa.
“Appa. ..apa... Appa... Appa wai ka rabu da Amma?... Sakin Amma ka yi?”
“A gurin wa kika ji wannan maganar Hurriya? Waya fada miki haka cikin daren nan?”
“Yaya Khairi.... Appa da gaske? Appa why? Yanzu mu kadai ne zamu rasa uwa a nan Appa! Me Amma ta yi?”
Tambaya take tana wani irin kuka numfashi na fitar mata da karfi kamar ranta zai fita. Idon Appa ya cika da hawaye
“Bata yi komai ba Hurriya, be kamata ki shiga cikin magana irin wannan ba, zauna a nan ina zuwa”
Ya nufi kujera da ita ya zaunar da ita, ya juya ya fita gaba daya abubuwa sun rike masa har ji yake wani abu na juya masa cikin kai, kamar za a haukata shi haka yake ji. Bangaren Hajiya Kaltume ya nufa tun a tsakar falon ya fara kiran Khairi rai a matukar bace daman ciwon sakin Amma da ya kama shi, ga bacin ran da Momy ta saka masa yanzu kuma Khairi ta kara masa wani ta hanyar batawa Hurriya. Umm Khairi ta fito daga dakin Hajiya tare da Maama Umm Ruman na biye da su a baya, Umm Salma da Yasir kuma suka fito a nasu dakuna duk suka sauko kasa.
“Alhaji Lafiya?”
Cewar Hajiya Kaltume da ta riga su saukowa gabanta har faduwa yake.
“Akan wane dalili Umm Khairi zata fadawa Hurriya sakin mahaifiyarta aka yi? Ita mahaifiyar bata fada ba sai ke yar iya? Wannan ba rashin hankali da rashin tarbiya ba ne? Ki shiga cikin maganar iyayenki?”
Ya juya gurin Hajiya Kaltume.
“Kin ga abun da kika hanyo ko? Kin maida yaran nan kawayenki da maganar da ya dace da wanda be dace ba duk fada kike a gabansu, har suna jin sun isa sun kai su saka baki a zaman takewar mahaifinsu, sai na koya miki hankali sai na koya miki hankali Ummul Khairi”
Jikinta ya dauki rawa domin ta san halin Appansu idan hau yana wuyar saukowa. Yasir ya karbawa Appa.
“Iskanci ne da rainin hankali, ta fi uban kowa baki da bakin iyayi a gidan nan kamar wata babbar mace, yau sai kin fadi wanda ya aike ki”
Hajiya Kaltume na jin haka ta yi saurin zunguje Khairi.
“Hurriya”
Hurriya ta dago a hankali ta kalli yayarta Khairi wadda ta kira sunanta.
“Na'am?”
“Me Appa yace miki da ya aiko a kira ki?”
“Tambayarmu yayi ina muke son zama”
“Toh ina kika zaba?”
“Ni dai na ce gurin Gwaggo ko Hajiya, amman yace aa sai dai gurin Momy”
Khairi ta yi fuskar tausayi.
“Allah sarki, Wallahi na tausaya muku babu dadi rayuwa gidan babu uwa a gida, da ma dai Appa zai yi hakuri da ya dawo da Amma, Hurriya na ga Appa yana jin maganarki why not ki roke shi ya dawo da Amma idan ma wani laifin ta yi masa ya yafe mata”
Hurriya ta yi mata wani kallo na rashim fahimtar inda zancenta ya dosa.
“Amman zata dawo idan ta haihu ai”
“Toh Allah yasa ya maida ita, wata kila akwai gyara ai Wallahi duk ban jidadi ba dazun har da kukana”
Hurriya na jin haka sai kwakwalwarta ta dauka sarai ta gane karatun Khairi a take wani irin tashin hankali ya same ta, idonta dake cikin farin gilashi suka cika da hawaye ta kasa hade lomar tuwon dake bakinta. Slowly ta mike tsaye taja kujera baya ta fara tafiya zuciyarta na buga kamar zata fasa kirjinta ta fito, tana fita falon ta watsa da gudu bangarensu da karfi ta tura kofar falon Amma ta shiga. Hamad na kwance kan kujera yana kallon remote a hannunsa.
“Hamad wai Appa sakin Amma yayi? Wai rabuwa suka yi? Yaya Khairi ta fada min”
Tana maganar yana kuka even though bata gama tabbatarwa ba. Hamad ya tashi zaune yana kallonta.
“Ai ke ce mahaukaciya shiyasa baki gane ba”
A nan Huriyya ta samu damar fashewa da kuka mai karfi, ta juya da sauri ta nufi bangaren mahaifinta.
*** *** ***
“Ah Ah Alhaji ina ce Kaltume ce Babba a gidan nan? Me zai hana su zauna a bangarenta?”
Appa ya mike tsaye.
“A nan nake son su zauna, kuma nan za su zauna ko kin yarda ko baki yarda ba, domin ke da su duk a karkashin ikona kuka kuma a gidana”
“Aa Alhaji gaskiya ban ci ƙashi ba ba zan ci aman tsoka ba! Har ina? Yara da girmansu da komai a kawo min su? Da wani abun arziki ne ai matarka take tarewa ta karbe sai a yanzu da yake wahala ce za a kawo min”
Appa ya nuna kansa.
“ƴaƴane wahala Nafisa? Ke dai har abada ba zaki taba zama matar kirki, har abada mai hali be taba fasa halinsa ba, kowa yana girma yana kara hankali da hali na gari amman ban da ke”
“Daman ni ban taba haske a idonka ba, masu haske Iyami ce da Kaltume, ka san ni ka san halina ni bana son a shiga sabgata ina bangarena babu ruwana da kowa, akan me yanzu za a dauko yayar sarauniyar gida mace da ta hana ka ganin martaba a kawo min”
Alhaji Haruna ya nuna ta da yatsansa.
“Sau daya tak bakinki ya sake furta wata magana marar dadi akan Iyami da yayanta sai mugun saba miki, ni na zabi su zauna a nan kuma a nan din za su zauna, idan baki son zama da ƴaƴana jinina ƙofar gidan a bude take..!”
Momy ta aje numfashi da karfi.
“Bismillah ga dakuna nan su zabi wanda suke so su zauna, gidan naka ne yaya naka ne ni ma taka ce Allah ya ba mu hakurin zama”
Fuuuu! Appa ya fice daga falon nata cikin mugun bacin rai. Namra da Musib suka bishi da kallo su kansu sun manta when last su ga mahaifinsu a cikin bacin rai irin wannan sai yau.
“Tsakani da Allah takurawa ce dawowarsu a nan, musamman ma dan iska yaron nan Hamad ni ubansa zan ci Wallahi”
Cewar Musib yana jin haushin hukuncin da mahaifinsu ya yanke. Bakinciki ya hana Momy sake cewa komai ta kai hannu ta dauki sarkar zinarinta dake kan aje a hannun kujera ta mike tsaye ta nufi upstairs, kamin ta isa dakinta ma wani aiki ne saboda izza da isa kamar wadda bata son taka kasa haka take tafiya.
Bakin gadonta ta zauna ta rike da sarkar sai cika take tana batsewa, ita dai ta san tana daga kafa akan kishi da matan Alhaji Haruna domin ganin take babu sa'arta a cikinsu Hajiya Kaltume dai yar talakawa ce arzikin na Alhaji Haruna Mai Yadi ne, Iyami ma haka rufin asirinsu na Alhaji Haruna ne domin har gidan da iyayenta suke ciki a yanzu shi ya siya musu shi yake dauke da nauyinsu.
Kuma Iyami ba sa'arta bace a shekaru, kuma ta fi Hajiya Kaltume zama makaskanciya a idonta domin ita ga aiki ta zo yi a gidan ta aure Alhaji Haruna, ba dan ma da kaddarar aure ta hana ba kuma yara sun shiga tsakani ba wata kila da ba zata iya hakurin sharing miji daya da yar aikin gida ba, kallon da take yi ma Amma bata da ajin da zata yi kishi da ita sai idan abun ya motsa.
Ita dai abun da ta fi tsana shi ne a shiga sabgarta, idan ta shiga sha'aninta na masu arziki har mantawa take da Hajiya Kaltume da Amma, a yanzu kuma kawo mata Hurriya da Hamad da Appa ya dage sai shi ne abun bacin ranta a yanzu, domin da su zauna a gurinta kara ya dawo da uwarsu ta rainin abunta, sam sam Momy bata son yayan kowa idan ba nata ba, bata mutanta kowa sai masu kumbar susa, idan baka da arziki har ganin take kamar baka cika mutum ba.
[10/18, 5:34 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: https://chat.whatsapp.com/GJ9hOtbWbfDKmq8NrKsDIG
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 6️⃣
Da tunanin Amma Appa ya dawo apartment dinsa, tsansar biyayyarta da yadda take gujewa bacin ransa da nuna kulawa akan duk wani abu da ya shafe shi. Ya tabbatar da ita ce ba sai ya bukaci a bawa Hurriya abinci ba, matukar ta san uwar yaran bata gidan zata yi kokarin kwatantan kyautata musu kuma ta ja su a jiki, haka ma da ita ce ya zo mata da zancen dawowa ƴaƴan abokiyar zamanta a bangarenta zata yi marhabun ta karba da hannu biyu ko da kuwa bata son haka ba zata nuna har ya gani ba, duk wani abu da Amma ta san Appa yana son kokarin raya shi kaunar abun take ba ta bata masa rai ba.
Hannayensa hade a bayansa yake tafiyar fuskarsa a yanutse zuciyarsa a hargitse yana jin kamar ya fashe da kuka gaba daya ya rasa me ke samunsa ya rabu da matarsa rabuwar ta haifar masa da rashin kwanciyar hankali da bacin rai, zamanta a gidan kuma masifa ce a gidansa masifar da be san ta micece ba domin shi dai ya san matarsa bata masa laifi ba, be san dalilin da ya saka ya tsane ta ba. Kukan Hurriya ne abun da ya fara masa maraba da zuwa a lokacin da ya kunna kai cikin falonsa, kuka take sosai irin kukan nan da ya hana gilashin idonta tsaya saboda hawayen da ke cika shi, ta rike gilashin a hannu lipa dinta da jikinta sai rawa suke, dishe-dishe ta ga alamar shigowar mutum bata bukatar saka gilashi domin tantance waya shiga, ta san tsayinsa da yanayin tafiyarsa ta haddace komai. Shi ya taho da sauri ita ma ta nufo inda yake da sauri tana rike da gilashin dayan hannunta kuma yana lalabensa.
“Appa. ..apa... Appa... Appa wai ka rabu da Amma?... Sakin Amma ka yi?”
“A gurin wa kika ji wannan maganar Hurriya? Waya fada miki haka cikin daren nan?”
“Yaya Khairi.... Appa da gaske? Appa why? Yanzu mu kadai ne zamu rasa uwa a nan Appa! Me Amma ta yi?”
Tambaya take tana wani irin kuka numfashi na fitar mata da karfi kamar ranta zai fita. Idon Appa ya cika da hawaye
“Bata yi komai ba Hurriya, be kamata ki shiga cikin magana irin wannan ba, zauna a nan ina zuwa”
Ya nufi kujera da ita ya zaunar da ita, ya juya ya fita gaba daya abubuwa sun rike masa har ji yake wani abu na juya masa cikin kai, kamar za a haukata shi haka yake ji. Bangaren Hajiya Kaltume ya nufa tun a tsakar falon ya fara kiran Khairi rai a matukar bace daman ciwon sakin Amma da ya kama shi, ga bacin ran da Momy ta saka masa yanzu kuma Khairi ta kara masa wani ta hanyar batawa Hurriya. Umm Khairi ta fito daga dakin Hajiya tare da Maama Umm Ruman na biye da su a baya, Umm Salma da Yasir kuma suka fito a nasu dakuna duk suka sauko kasa.
“Alhaji Lafiya?”
Cewar Hajiya Kaltume da ta riga su saukowa gabanta har faduwa yake.
“Akan wane dalili Umm Khairi zata fadawa Hurriya sakin mahaifiyarta aka yi? Ita mahaifiyar bata fada ba sai ke yar iya? Wannan ba rashin hankali da rashin tarbiya ba ne? Ki shiga cikin maganar iyayenki?”
Ya juya gurin Hajiya Kaltume.
“Kin ga abun da kika hanyo ko? Kin maida yaran nan kawayenki da maganar da ya dace da wanda be dace ba duk fada kike a gabansu, har suna jin sun isa sun kai su saka baki a zaman takewar mahaifinsu, sai na koya miki hankali sai na koya miki hankali Ummul Khairi”
Jikinta ya dauki rawa domin ta san halin Appansu idan hau yana wuyar saukowa. Yasir ya karbawa Appa.
“Iskanci ne da rainin hankali, ta fi uban kowa baki da bakin iyayi a gidan nan kamar wata babbar mace, yau sai kin fadi wanda ya aike ki”
Hajiya Kaltume na jin haka ta yi saurin zunguje Khairi.