Sashe 6
Gangar Jikinsa Na Aura Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
daga bacci basu yiba Inna Hauletayi dirar mikiya a bakin kofan dakinsu tana bugunkofar da karfi tana fadin a tashi haka baccin ya isaduk inda sati yayi an gama cin amarci bakunta ta kare kin zama 'yar gida fito ki dora dumame. Indozataje rafi debo ruwa.Firgigit Hanna ta mike ta dirodaga kan gado ta bude kofa ta fito. Ta durkusa harkasa ta gaishe da Inna Haule. A yatsune ta amsatace'' a tafi wajen murhu a dora dumame ga dawada gero can idan kuka karya kumallo keda indo ku surfa''. Bello yaji tamkar yayi ihu saboda takaiciyasan Hanna kuma ta shiga uku ta lalace kamanyadda amaryar Babansa Indo take dandana wahalakullum kamar baiwa.Ya tashi zaune ya rike kaitausayin Hanna zuciyarsa da tunani ina zai samomafita kafin ta zama baiwa, to amma babu wata mafita tunda har yau har waye war gobe innaHaule taki amince masa ya koma gidansa shidamatarsa. Da ya isheta ma da maganar sai tace dukranar daya sake rokonta akan wannan bukata tasaAllah ya isa kuma zata tsine masa, don haka Belloyaja bakinsa yayi gum. Haka hanna ta kasance tana yin iya kokarinta na ganin ta farantama uwarmijinta tana binta sau da kafa amma a banza innahaule bata gani. A koda yaushe zagin hanna taketana cewa.A yaushe zagin hanna take tana cewa aurendaba gara ma ai bai cika aure ba. Wai hanna tamallake mata da don da sai yayi sati biyu,uku baizogarin ba daga wajen aikimsa amma yanxu bayasati guda, zantuttuka barkatai marasa ma'ana daina nuna tsana tsagoranta. To wannan al.amari yasa hanna ta sake fitar da rai daga samun zaman lafiyaa rayuwarta, inna haule halinta daya da iya abukoma tafi iya abu ko uwarka ka yanka musu kadafa ka basu bazsu gode maka ba. Sai dai kawaiidan abun ya isheta ta shiga daki tayi kuka ta gaji.Idan bello madu ya dawo ya ganta a wannan hali sai ya shiga lallashinta yana bata hakurin nan nasababu abinda yake karama hanna banda takaici.Abu daya ya gano lagonta in har yana so tayidariya a duk halin bacin ran da take shine yacemata haisam. Haka yake sakata a gaba yace dolesai ta bashi labarin haisam. A koda yaushe hanna na kirga kwanikin yaushe bello zai dawo dagawaje aiki saboda dashine kawai take hira mai dadihar tayi dariya hirar ita ce hirar haisam.. Hanna daindo ne suke surfe a yau, inna haule ta fita unguwashine ma suka samu suna yar hira. Duk da indo tagirmewa hanna amma duk da haka bata fi shekaru ashirin da shida ba a matsayin suruka take a wajenhanna tunda matar baban mijinta ce. Amma doletasa suka zama kawaye. Hanna na bakace dusar,indo tana tikar dawa a turmi. Indo ta tsagaita dadakan tace'' hanna sai dai hakuri ni harna saba dawannan bauta haka Allah ya rubuto mana rayuwarmu. Hanna tayi ajiyar zuciya tace '' Allahyana barin bawanshi a halin daya so ya ganshi.Amma duk abubuwan da inna kemun bayadamuna irin duk abunda muke yi mata bata ganidubi fa irin aikin da mukeyi kamar zamu mutuyanzu idan tazo cewa zatayi munyi ha'inci bata surfu ba. Ga zagin da take yimin akan gara ni narasa yadda zanyi da rayuwata. Indo ta ajiye tabaryatace'' ai waike kina nufin duk abinda ake baki saniba a gidan nan yau? Hanna ta ajiye faifan dakehannunta ta tattara hankalinta gaba daya a wajenindo tana jiran taji me yake faruwa. Indo tace '' ko da yake kin tafi debo ruwa dazu da sassafe ni innahaule tasa na shifa dakinki na miko mataakwatinan aurenki guda biyu wadanda baki dinkakayan ciki ba tasa almajiri ya daukar mata wai zatakai wani gida ajiya tunda ba.ayi mii gara ba sumabaza ki daura lefansu ba. Daman wata uku ta daukar miki a kawo gara gashi yanzu kin shigawata hudu da aure . Don haka da zarar bello yadawo zata sa ya sakeki, lefen kuma ta kaiwa watayarinyar a daura masa aure da wacce zata kawomata gara. Kuma kinsan bello babu yadda zaiyiidan ta sashi a gaba tace '' ya sake ki . Hawaye ne sur yake zuba daga idanuwanta hanna ta mike dagudu ta shiga daki ta tara wayan an kwasheakwatina sai kwaya daya 'yar karamar kaya kalauku ne ta dinka a lefen su suka rage sai saurantsofaffain kayanta nada gasunan a kasa an watsarmata. Sai ta kwanta a kan gado ta fara rusar kuka hanna ta kware wajen iya kuka dan ko gasar masuiya kuka akaje ta duniya ina ganin ita zata zo tadaya. Can ba dadewwa inna haule ta dawo ta tarada indo ce kadai take aikin abincin rana tace'' inahanna? Indo tace'' ciwan ciki take tana daki. Taleka ta tarar da hanna sharkaf cikin kuka sai tace.'' babu wani ciwan ciki ba ciwan cikiba ko ciwannakuda kike kin bar gidan nan bazan iya ba harkartalauci anyi biki ko gara babu lefan dana dauke neshine yasa bakin ciki ya kwantar dake. Haka hannata yini cur a kwance babu ci babu sha sai kukaAllah cikin ikonsa sai ya jeho mata Bello da yamma kwanansa biyu ral da tafiya ba zato ba tsammanihanna taji sallamansa ya shigo, furgigit tayi ta tashizaune kallo daya yayi mata yasan akwai abindaaka yi mata har tasha kuka. Yaje da sauri ya zaunaa kusa da ita ya jawota jikinsa ya tambayeta mekedamunta take kuka. Ta amsa masa da ba komai . Ya ce yasan dole da wani abu kar ta boye masa ta fadamasa gaskiya, sai tace cikin tane ke ciwo, yayi shirushi dai ya jita ne kawai amma bai gamsu ba. Sai canaka jima hankalinsa yakai wajen akwatina yagabasa nan yace hanna ina akwatinanki suke? Tayishiru can tace inna ta kwashe takai ajiya wai tunda ba'yimin gara ba wata zata kaiwa ta aura maka itani ka sakeni. Sai ta rushe da kuka. Bello ya cije bakidon tsananin bakin ciki yayi shiru ya kasa maganasai yasa hannu yana goge mata hawaye ya nisayace. Daina kuka kece baki sani ba na baw ahmedkudin da zai saya mika gata kakaf yanzu ma cikon kudin da zai karasa sayyar na kawo masa. Damanyanzu zan koma wajen aiki tunda ina da aikin dare.Daman inna bata ganni ba ance tana makwabtabari inyi sauri in tafi baza ta san nazo garin bamaballe tayi min maganar sai ince Ahmed suyi kokarisu kawo garar gobe kinga an kashe bakinta kafin in dawo. Ya rungumeta hanna ya sambacikumatunta yace '' bazan sake kiba hanna ina sonkida yawa ki kwantar da hankalinki kinji ko, sannanya fice yana sauri ya tafi. Hanna ta bishi da kalloyayin da zuciya kece mata'' ba haisam kadai ba bello madu ma maisonki ne hanna ki kaunace shi.'' haka kuwa akayiwashe gari da misalin karfe uku na yamma saihanna taji an doso cikin gidan kamar a mafarkitaga kartan maza suna ta ajiye buhunhuna a kofar dakin inna haule . Mata suna ta shigowa dafantekun alkaki, nakiya dibulan da sauransu.Wannan al.amari ya bawa inna haule mamaki,nauyi da kunya saboda sunyi mata ba zata duk tabigari tana fadin ba.ayiwa hanna gara ba kuma bazasu iya yiba kwatsam sai ga gara wacce ko 'yayan attajiran garin ba'a taba yi musu gara mai yawanbuhunhunan haka ba. Nan dai inna haule ta haufara.ar borin kunya tana cewa ashe kuna tafe ku kaki sanar min nima in gayyato yan uwana suxo sutayani karbar irin wannan abin alhairi sannunku dazuwa ku shigo daki mana ya zaku zauna a waje. Hanna dibo tabarminki dana indo a shinfida baki.Ai da kun sanarmin zaku zo da nasa anyi mukugirke girke da soye soye irin wannan abin arzikihaka'' yan uwan hanna suka ce'' babu komai ai bazama muka zo yi ba mun kawo gara gata nan,zamu koma don yarmu ta sami salama a zamanta na aure da mijinta'' suma suka yaba mata ba dadi.Washe gari inna haule da sassafe taje ta debowahanna akwatinanta ta kawo mata amma ankwashe wasu kayan da yawa babu ta kumagargadi hanna kada ta sake ta fadawa danginta komijinta tayi shiru da bakinta. Da bello madu ya dawo faran faran inna haule ta kira shi ta nunamasa gara har tana cewa'' allah sarki ashe bakaramin shiri suke yiba shi yasa basu kawo dawuri ba irin wannan yawan gara sai kace yarsarkin noma ka auro '' bello yayi dariya ya ce'' Allahya sanya alheri ya bamu zaman lafiya'' ya nufi dakin hanna, bayan tayi masa sannu da zuwa ta kawomasa abinci da ruwa yasha sai ya jawo akwatinanya bude kamar yadda ya zarga tabbas mahaifiyarsazata kwashe wasu kayan haka kuwa ya gani takwashe kaya da yawa. Ya waiga ya kalli hanna saita sunkuyar da kanta kasa bata ce masa komai ba...