← Book details Bakin Rijiya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 32

Sashe 23

Bakin Rijiya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hafsat kuwa tunda yan kai Amarya suka watse wuraren karfe goma na dare seta soma jin tsoron zaman gidan ita kadai, shi kuwa be leqo bama se sha daya da rabi, Abinci ya kawo mata sannan ya sanya hannu ya yane mayafin dake jikinta ya ajiye gefe ya kalleta, "Kina bazawara wani kunya zakiji,zaki wani lullub'e fuska" sosai maganar sa ya doki qirjinta amma bata nuna masa komai ba kurun dai murmushi tayi masa,ganin haka ya sanya yace "Kici abinci kazane da drinks ga youghurt da ice cream idan zaki sha" kallon su tayi tace "Gaskia Alhamdulillah na koshi,sedai zuwa safiya" miqewa yayi be wani damuba,kizo ki kulle kofofin gidan ni zan tafi seda safe" ko motsawa batayi ba daga inda take sabida mamakin daya bata,to gidan uban wa ze kwana?" ta tambayi kanta,ganin fa tsorone ze hallakata ya sanya harya kai parlor ta rugo ta riqe masa hannu,da mamaki ya kalleta tace dashi

"Yaa muhammad zan bika dan Allah" juyowa yayi yabfuskance ta gaba daya "Ina zaki bini hafsat?"

"Inda zakaje mana"

"Ba inda zani fa, gidan zainab zanje na kwana,kishiyarki" tafi minti uku tana kallanshi, juyawa yayi ze fita ta riqe masa hannu again "Bazan iya kwana anan ni kadai ba,tsoro nakeji" murmushi yayi

"Ni ban aureki danna tayaki kwana ba hajiya,ko mun rubuta haka acikin agreement namu?" gaba ki daya tsoro ne ya taso mata ta kalleshi sosai tace cikin dakiya idanta yayi ja sosai amma batasan tayi kuka "Na tuna kuwa babu wannan acikin rubutaccen auren mu,na manta bayan signing takardar yarjejeniya da mukayi ta aure,wurin daurin auren ma mun rubuta cewar kalar auren namu na dabanne ba wanda musulunci ya tsara ba,Kaje amma karka qara kawomun komai daya shafi rayuwar aure,idan bazamu kwana a tare ba babu wani abu dazakamun na aure,na yarda haka tsarin namu auren yake,kaje plss" tafad'a tana me d'addage hannayenta duka biyu alamar naci ka fam, matsowa yayi daf da ita ya sanya hannunsa asaman waist nata yamatse ta sosai da jikinsa yace "Ni kike gayawa magana hafsa? Sabida kin samu sake ko? Yanzu ma idanta ta dago sukayi kaura dana juna tace cikin jin haushin sa

"So nake muyi sighning wani yarjejeniya kanka tafi" sakinta yayi yace yana murmushi muje gayamun wane iri ne?" zama sukayi a kujerun parlor tace

"Sona ke mu kwana a roof daya,muci abinci atare,mu sake wa juna soyayya,mu aminta mudin masoya ne,idan har akayi watanni shida kaci cewar baka buqatar tarawa dani,kuma bakaji sona ko daya a ranka ba,to ka rabu dani,kuma tsakani da Allah zamuyi" kallonta yayi ya kwashe da dariya ya sani yanajin tausayinta amma sam baya santa wlhy, yakuma san baze taba san taba,da wannan ya aminta suka rubuta suka ajiye.....

Hafsat ta kuma yin wauta a karo na biyu,yaya kuke zanin wannan zaman? Ze dore kuwa?" anya hafsat bata kirawa kanta zawarci na biyu ba bayan shaam ya aure fara me gashi abinshi? Muje zuwa dai.....

Votes pls
[2/13, 9:28 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅

Love story 2018

Billy galadanchi

*HASKE WRITER'S ASSO.*(home of expert and perfect writers.)

Wattpadd@ 68billygaladanchi

*Sadaukarwa gareki qawar alkhairi ummie Aisha*

27

Muhammad a d'akinsa ya kwana yayinda hafsa ta kwana a nata d'akin,wata hatsabibiyar rigar bacci ta saka iya cinya,da saninta ta cire bra,pant kawai ne ajikinta se wannan rigar,sumar kanta datasha gyara ta gama barbajewa har saman goshinta daga bed room nata tafito zuwa kitchen,a parlor ta hangoshi zaune duk da zuciyarta takad'a qirjinta se dokawa yakeyi amma haka ta daure,tasani idan bata koyawa kanta rashin tsoron shiba akwai matsala,kallon ta yayi sosai ya raya aranshi so take taja ra'ayinshi wanda baze tab'a faruwa ba har gaban abada, bata ko kalli inda yake ba tayi gaba abinta zuwa kitchen,d'an guntun tsaki yaja ya mayarda dubanshi zuwaga film dayake kalla, Ha d'adden break fast tabshirya musu,finger sandwichs da chocolate sandwich,se kuma coffee amor da vegetable potatoe, tun yana daure wa har qamshin yasoma jan hankalinsa,ogar bata baro ktchn ba sanda ta hada samosa, jere komai tayi a fankacecen dining table,ta bude dining shelf ta baje komai da komai da ake buqata,bata wani kalleshiba sabida sam ma yi tayi tamkar bata kula dashi ba,dakinta ta wuce tasha wanka da wata doguwar rigar dress maroon color ta tufke gashin kanta da farin ribon,se flat shoe data saka shima fari qal, har tsakiyar falon ta sameshi kusa dashi sosai ta zauna ta kalleshi dauke da fara'a sosai a fuskarta,tana bude bakinta qamshi alawar datakesha ya daki hancin sa dauke kanshi yayi gefe d'aya

"Barka da safiya yaa muhammad da fatar ka tashi lapiya?" dan juyar da kanshi yayi gefe daya sannan yace

"Barka dai,kin tashi lapiya" Murmushi tayi

"Breakfast kai kadai yake jira oga muhammad kose kayi wanka ne?" dagowa yayi dukda beso ba kasancewar tunda yayi aure da zainab,be taba tashi tabgayar dashi ba kuma yauce rana ta farko da mace ta gabatar masa da abinci,sedai kuku ne yake dafa masa,miqewa yayi yace muje dining d'in" kai tsaye tayi kokarin shiga gabanshi dauke da tafiya me daukar hankali gabaki daya gogan seya shagala da kallon mazaunan ta,susucewa yayi ya wani zama tamkar wani soko,sanda tace dashi "ka zauna plss" zama yayi yaga irin abubuwan data girka acikin lokaci qanqanin,yakuma san be rigada ya kawo cook a gidan ba dama niyyanshi yau da rana ze gabatar mata dashi "Mezan saka maka?" ta katse masa tunani da wannan tambayar

"finger sandwich and veg potatoe zansha wancan abun kuma" batayi musu ba ta zuba masa komai da yace ta matso kusa dashi sosai wai bashi zatayi,kallon ta yayi ya d'an had'e fuska "Meye hakan hafsat?" kafe shi tayi da idanta "Yaa muhammad da kaina zan baka mana" a yanayin yanda tayi magana seya ganta kamar wata yar sha biyu kasa cewa komai yayi se bude bakin dayayi ta aika masa sanwch din ya gutsura,sosai yaji dadin abuncin yama manta inda yake har samosa seda yaci yasha coffee Amor dinshi sosai sannan ya daga mata hannu a lamar ya qoshi,kallon shagwab'a ta masa

"Saura ni ka bani" dan mur ya qara sha "Na baki kuma me kenan?" Take ta hado shagwababbiyar fuska "Abuncin mana" tsaki yaja ya miqe kawai tashi tayi ta bi ta gabanshi tana doddoka kafa wanda ilahirin jikinta motsi yake tana kuma qunquni akan bazata maci abuncin ba yau gaba daya...bin bayanta yayi da kallo harta wuce ned room nata,girgiza kanshi yayi ya dawo parlor ya zauna ganin tafi 1 hour bata fito ba ya sanya ya bita ciki da kanshi, a kwance ya taddata rubda ciki takalmin kafarta kurin ta cire da zata kwanta amma komai najikinta nanan,mazaunan ta sun qara bajewa a yananyin kwanciyar datayi ji yayi tamkar ya sanya hannun sa ya taba wata zuciyar ta haneshi gyaran murya yayi yace

"Hafsa mesa bazakiyi breakfast ba?" tana daga kwancen bata juyo ba tace "Bakai bane kace wai baraka feeding na da kanka ba,ni Allah bazan ciba idan baraka bani ba" shiru ya danyi kanyace

"Naji muje zan baki" mirginowa tayi ta kiqa masa hannun ta waiya dagata,badan yaso ba ya miqa nasa hannun ya dagota,laushin hannunta kawai ya sanyashi runtse idansa cikeda kasala,a parlor kuwa seda ta koshi sannan tace dashi wai ita atabau seya dagata zuwa cikin parlor cikinta ya mata nauyi bazata iya tafiya ba, kallonta yayi yanaso yace kin cika rigima amma ya kasa,dagatan yayi ta wani lafe jikinsa har sukaje parlo ya direta ya zauna saman 3 siter zuwa tayi ta kwanta ta daura kanta saman cinyar sa tace dashi "Ka sosamun kaina zanyi bacci" bece da ita komai ba,aka soma knockin na gidan,dagata yayi yaje ya bude,kukun da yake jirane,koda aka nuna wa hafsat shi masifa ta saka akan itace da kanta zatana girka abunci,dole kuwa ya kyaleta ya sallami kukun, kallon ta yayi bayan fitar kukin yace da ita

"Hafsat mesa kin cika rigima ne? Idan ma bakya buqatar sa mesa zakimun haka a gabansa? Seki bari idan ya tafi ko? Karki qara mun haka nan kina jina ko?" dan kallonshi tayi sekuma ta dake "Idan kayi hakuri kome zanyi ai na 6 month ne ka jira idan matar daba ta yarjejeniya ba tazo ka murza mata iko" sororo yayi yana kallonta ita harta wuce part dinsa, gyara masa dakin tayi ta kwashe kayansa ta wurga a loundry basket sannan ta yaye boxers nashi da singlet data ga ya cire ta wanke su ta shanya a toilet nasa, towel dinsa ta daura tayi wanka,tana fito wa ta ganshi asaman gadon dauke kanta tayi daga dubansa,tazo tana rawar sanyi, kusa dashi ta zauna ta rungumoshi gaba d'aya ta gabanshi "Yaa muhammad ka rufeni da jikinka akwai sanyi wlhy" gabaki daya ta gama da matsalar malam muhammadu,kasa ko motsin kirki yayi sanda taji daidai sannan ta miqe bayanta ya qurawa ido,taje mirror ta dakko wani mai tazo ta zauna,shidai yau ta gama rufe masa baki,shafa manta ta zauna tayi kamar kuma wacce aka tsikara ta laquto man ta janyo hannunshi ta saka aciki,juyawa tayi ta rage towel nata zuwa tsarar ta tace "Hannuna baze kaiba nika shafamun" shiru yayi dole ya murza man ya shiga shafe bayanta dashi,se wani lumshe ido yakeyi soft skin nata na daukar masa hankali sosai.....

Da yamma yace da ita tazo su shiga bangaren zainab,ba musu ta caba ado suka wuce part din na zainab, suna zuwa parlor ya kalli wata yarinyar yace "Ki mata iso wurin zeezee" ya juya abinshi wani bangaren.....A zaune suka taddata ana mata gyaran kai,da alama wasune daga salon sukazo mata aiki a gida,har kafafuwanta ake wanke mata,kallo daya hafsat ta mta taji ta tsaneta,matar ma kallon sheqeqe tawa hafsat

"Sannu" shine abunda tace dasu babu wanda ya koda kalleta acikinsu har masu aikin, duban su tayi tace Aunty zainab sannu" dagowa matar tayi cikeda isa tace

"Kan mijin naki yakawoki gaidani be sanar dake ba'a gaidani a tsaye ba? Kuma ba'a saka ido acikin nawa sannan kuma ba'a kiran sunana hajiya zakice" kallonta hafsa tayi ta baki,ta juya abinta kawai aranta tace "qanin uwarki zanci ni kam wlhy,kajimun masifafgiyar mata,kinjawa kanki dani kuwa rashin mutun cine,gidan kika tarar...

Kumun uzuri kaina ke ciwo
[2/14, 9:00 PM] Billy Galadanchi: *💅BAKIN RIJIYA....ba wurin wasan makaho bane*💅

Love story 2018

Billy galadanchi
Chapter 23 · 0% Book details