← Book details Babbar Sakayyah Takun Farko Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 11

Sashe 5

Babbar Sakayyah Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dayar wadda ke sanye da hijabi baki itace zainab kallon ta tayi tace,"ya Salam NINEE meyake damunki ne Haka ,ki tashi muyi tunanin yadda zamuyi mugudu" kukan da NINEE ke tarewa ne yaci karfin tashi ga rusa kuka tana cewa "zainab bazaki gane bane ni yanzu ina tuna kanwata NABEHA nasan har zuwa yanzu ABBO FAHIMNA bazata Bata abinciba har sai na koma yanzu yazanyi kenan ni tsorona kar wani ta cutar da ita nasan ita kadai zata Bari ta kwana a dakin mu nashiga uku wannan Wace iriyar kaddarace meyasa rayuwarmu zata zo a Haka, dafarko bama da kowa muka rasa mahaifinmu gashi ankawo mu wata duniyar da bamusan aina muke ba bamu da tabbbacin zamu fita sabi da bamusan me suke aykatawa a nan ba " NINEE ta karasa maganar hawaye n'a bin kuncin ta,

Ayna,u ta kalli su idonta ya kada yayi jajur Tace"uhm kukan dadi kukeyi anty NINEE ni da bani da kowa fa Babu wan da zai nemi in da nake ko da ace zasu kasheni' anan Babu me bimin hakki ko ace za a dau mataki saï dai in ubangiji ya nuna musu BABBAR SAKAYYAH, Nina sani Allah Yana tare damu kudaina jin komai insha Allah RAYUWAR mu bazata wulakan ta ba.

Suna tsaka da wannan maganar sukaji an banko kofar dakin ,gaba kidayansu a tsorace suka Mike suna raba idanu don ganin wane', wasu mazane guda uku manyan basake masu kama da samu dawa jikinsu n'a sanye da Kaya bakake fuskar nan tasu kuwa a daure kamar wadan da sukaga mala'ikun mutuwa, Tun da su NINEE suka ga wadannan mutanen hanjin cikinsu yashiga kadawa kowacce acikinsu sai zare Ido take tana bin su day kallon cikin tsoro da fargaba ,basuyi aune ba sukaga mutanen sunyo kansu kaitsaye hannayen Ayna,u suka rurruke tare da janta ta karfi tana kuka tana Basu hakuri Amma Ina Basu kulata ba Haka suka fita da ita sannan aka Kara garkame su NINEE ,tun da aka fita da ayna,u NINEE da zainab suka zube a gurin kowacce idanunta cike tab da hawaye zuciyoyin su kuwa sai harbawa suke da saure daker suke iya bude baki suna furta kalmar innalillahi wa'inna ilaihirraju,un "shin Ina zasu kaita "Nan take zainab ta fado kirjin NINEE tasake fashewa da wani sabon kukan abin tausayi ,itako NINEE tun da take a duniya Bata taba ganin irin wadannan mutanen ba mugaye azzalumai yanzu ya zasuyi kenan dolene sunemi mafuta , Haka dai sukai ta sakesake a zukatansu....

Tun da aka fita da ayna,u ake tafiya acikin gidan har suka Isa wani tsibiri me duhun gaske batare da ayna,u tayi auneba taga an shiga da ita wannan gurin inda ta soma ganin "yan mata kala kala kamar wadan da ake safara wasu suna kuka, wasu kuwa kukan zuci suke wadan suma duk idan ma gansu saika zata sun mutune,abun dai abin tausayi gashi yawancin su bazasu huce 20 ,18 ba idanuwan su ta dunga bi da kallo na tuhuma suma kallon ta suke cikin tausayin kaddarar da ta kawota wannan guri ,wata kofa dake hannunsu na hagu suka shiga ko sallama Babu suka dureta tare da juyowa sufito , ayna u kuwa tsawatai tana karewa katafaren dakin ido yadda yaji komai da kayan alatu na more rayuwa tun da take Bata taba ganin irin wannan aljannar duniyar ba, ayanzu kuwa tagama tabbatar wa RAYUWAR ta tazo karshe tun da Allah yayi acikin gidannan zata mutu, tana tsaka da tunanin Nan taji an turo kofa..

DOGUWA

Amra wadda kukasani da asalin kyau da kwalliya da iya ado iri daban daban duk ta lallace ta tashi daga amra Takoma irin Yar asalin kauyenan ,a Rana idan tatashi sai ta girka Awara kusan kwano biyu sainan ta yanka tafita titi tasayar,kullum bata da ayki saï wanan ,to kana da gatama Ruwan Awara idan yaxuba ajikinka yake batamaka fata balle ita mata gata.

Yau talata Amra zaune ita da "yan ,uwanta ga jarin Awara ya karye saka makon yan shaye shayen anguwardu da suka mata hauka suka cinye suka Hana kudin ,baiwar Allah tayi kuka har ta gaji ga yau abin cin da zasuci ma gagarar su yake innalillahi wa'inna ilaihirraju,in wani tashin hankalin baba me gidan da suke zaunane ya debo yaran unguwa Wai azo a fito musu da kayansu sufita su barmasa gida tun da Babu gado, Amra kamar zatayi hauka ita Abu daya takeji shine mahaifiyar ta Bata da lafiya sai yanzu tayi danasanin barin Abdul ya koma garinsu wayyo Allah na "sun Batu take kamar ma haukaciya tana ganin yadda suke hulla kayansu a waje har da wata ya gulalliyar katifar su ,ummanta kuwa tana daga zaune amma hawaye ke zuba a kuncin ta domin ita kadai tasan abin da yakemata zafi da kuna acikin zuciyarta gashi Babu damar magana ,kallon Yar Tata take cike da tsananin tausayin ta da danasani akan irin wanan rayuwa da ta jefa yaranta aciki amma bubu komai ta saka aranta ko yanzu ta mutu ta bar wadda zata kula da sauran yaranta..

Kuka take tana binsu tana rurukesu taga bazasu daina ba hakan yasa tanufi gurin baba da gaggawa ta rurruke yadin jikinsa mekama da ishirinka maraya tana kuka tana cewa" kayi wa girman Allah kayiwa iyayen da suka haifeka kataimake mu Dan girman allah kada ka tozarta mu wallahi wallahi idan ka koremu bamusan inda zamuje ba kataisaya mana kada rayuwata da ta kannena ta wulakanta " wani bugu da yayiwa Amra sai da yasa ta hantsila tayi baya ta fasa baki dakyr ta iya tashi duk da abin da yayi mata hakan bé hanata komawa ta rokeshi ba hakan taitayi tana rike kafarsa kamar wan da zai Bata aljanna tana kuka Amma yaki saurararta ,mutanen unguwar kuwa ansamu abin kallo Babu me taimakon su Amma anzuba Ido ana kallon ikon Allah kamar wadda suke kallon film .

Batare da wani Bata lokaciba baba yasa Aka Shiga Aka ciccibo umma Aka hurgota waje sauran kannen AMRA kuwa suma tini yasa anfito dasu waje abin dai Babu kyan gani duk Mai imani idan yaga wanan cin mutuncin da aka musu sai ya tausaya musu bakadan ba duk da ance ciwon "yamace na "ya macene amam dai wadannan matan dake tsaye agurin Basu nuna hakaba saima dariya da wasu suke wasu Kuma su tabe Baki suce allah ya kyauta Ahaka kuwa ya watse babama ya sa kwado ya rufe gidansa yabarsu agurin..

Kuka amra take sosai tanajin zafi da kuna acikin zuciyarta can Kuma sai ta tsaya cak ta juya tana kallon yadda mahaifiyar ta da kannanta ke kuka sabi da ganin da sukai tana zubar da hawaye, cikin sauri ta goge hawayen fuskarta ta Shiga kakaro murmushin karfin hali tana musu, allah sarki da sauri ta wara hannunta suka zo suka rungumeta tana bubbuga bayansu tana Basu hakuri can Kuma tayi luff tana tunanin inda zasu nufa gashi yanzu yamma ta soma Yi....

4
*KAWO*

Yau kam gidan alaji muktar cike yake da tarin jama,a yaransa da jikoki harma da su nafisa da dan,uwanta auwal kowa kagani jimami yake Akan alhaji zaitashi ko,a,a gaba ki dayansu sunyi jigum suna jiran fitowar doctor ,cikin mintina kalilan doctor ya fito dauke da wasu takkaddu a hannunsa Kai tataaye babban Dan alhaji yanufa ya damka Masa takar dar tare dayimasa bayani akan rashin lafiyar mahaifinsu , sannan ya Kara dacewa "sai dai kuyi hakuri Amma alaji Allah ya karbi abinsa "what mekake cewa? "Eh kamar yadda kaji ciwonsa yayi tsananin da yawa har ya bula masa hanji babu dama muyi masa ayki sai dai afita dashi kasar india nanne suke da kayan ayki masu kyau" Faisal ne ya dafe Kay tare da runtse ido yace "innalillahi wa'inna ilaihirraju un shikkenan dady ya tafi yabarmu .

Nan danan fa gida ya rude da koke koke da salati wasu suna rarrashi wasu suna kuka, musamman matar alaji tayanzu wato mahaifiyar nafisa taci kuka har tagaji Haka dai daker aka rarrasheta tayi shiru...

To bayan sati guda da rasuwar alhaji yaransa suka tada husuma akan raba gado Babu yadda aka iya Haka aka raba gado aka bawa kowa nasa ,hatta gidan da suke ciki sai daaka raba dashi hakan yasa mahaifiyar nafisa da yarta ikiram suka komo gidan Inna da zama .

Tashin hankali masifafa takaru Daman da ya aka cika Babu abin ci da ker ake samu balle kuma yanzu da suka kara yawa, Tun da umman nafisa ta dawo gidan batajin dadin zaman gidan gaba daya musamman ma yadda ake hantarar nafisa agaban idonta ,nafisa kuwa abin duniya yamata yawa har takai takawo tafara tunanin yadda za ai takashe kanta .

Yau litinin nafisa da kawarta Fatima sun koma makaranta suna zaune a harabar makarantar BAYAN an fito Tara, abakin wata bishiyar darbejiya suke nafisa na kuka tana hawaye domin ban Gama tabbatar da abin da ke dakinta ba , Can kuma naji Tace " Fatima an tsaneni ban San menayiwa RAYUWAR duniya ba bansan menayiwa mutane ba kowa yabi ya tsaneni kullum cikin kera da muzgunamin ake ya kikeso nayi Ina zansaka Raina Allah nafara zargin su Inna karya sukemin bana da mahaifi ni shegiyar ce da gaske" dasauri Fatima ta saka hannu ta rufewa nafisa bakinta Tace" kina da hankali kuwa ya Isa Haka banason jin wadannan kalaman daga bakinki ki daina kinji ko insha Allah kedin "Yar wanice akasarnan " uhm uhm ! Fatima kenan bazaki gane ba kawai bakisan menakeji a zuciyata ba Dan Allah ki fadamin yazanyi na kashe kaina na huta " suna tsaka da wannan maganar sai ga ta yarinya ta taho dawata takadda a hannunta tana rabawa dalubai, binta sukayi da Ido har ta karaso in da suke Tace "kunga gashi inji sir yace na raba muku ,gobe za azo karfe 9 ashirya tsab zamuyi bako "kar ba sukayi tare da sakar mata murmushi karfin hali sukace "nagode ",daga Haka ta huce gurin .
Chapter 5 · 0% Book details