BABI NA GOMA ASHIRIN DA D'AYA__21
Babban Goro Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
“Miyasa kika rufe laptop ɗin.?”
“Ba komai na gama abinda zanyi ne ya akayi.?”
“Ba komai Mummy tace na tambaye ki ina kika je min Sarka.?”
Kairat ta tashi tsaye,
“A'a ba wani sarkanki ni tace ta siyo ma”
“A'a-a'a tace ni ta siyo ma ke sai ta sake zuwa”
“Dan can ji kanta aje a tambayi mummy ďin”
“Ae aje ďin”
Da gudu Minal ta fice tana arigaggan zuwa gurin mummy, Ta riga Kairat isa ďakin sai ta rika yima mummy wink da ido.
“Mummy bani kika siyo ma wannan Sarkar ba.?”
Murmuahi Mummy tayi dai-dai lokacin da Kairat ta shigo ďakin tace,
“A a Kairat na siya ma ke nace sai wani satin”
Dariya Kairat tayi mata tana mata gwalo,
“Allah na gode maka yarinya kinji kunya”
Kukan shagwa6a Minal tasa,
“Gaskiya ni mummy kina gwada min banbanci Ni barin gidan ma zanyi”
“Sai kin dawo Allah ya kiyaye Hanya”
Mummy ta faďa da fuskar zolaya tana murmushi,
Tashi tayi ta bar d'akin tana hararar Kairat, Nan Kairat ta rufa mata baya tana zolayarta,
BAYAN AWA D'AYA.......
Duk zaune suke falo suna fira suna cin Tofin da Talatu tayi musu, Kairat sai santi take wai ya ake yinsa. Duk dariya suka sama, har Mummy Minal tace
“Da madara ake yinshi”
“Dan can ji kanta kena tambaya ne sai kace iyawa tayi”
“Wallahi Mummy ta daina ce min aji kaina kona mata ďan banzan duka”
Tashi mummy tayi,
“Idan ba gurin na bar muku ba ba zaku barni na huta ba kullum faďa kuke kamar kananan yara”
“Ai itace ta fara jana”
Minal ta faďa tana hararta, Kairat taja tsaki
“Ji kanta dana jaki saina kaiki ina?”
“Kinji ko mummy baza ta daina ba”
Mummy dai bata sake ce musu komai ba da nufi ďakinta, Haushin hakan yasa Minal ta ďauki Filo ta jefe Kairat dashi, Nan Kairat ta sake ce mata
“Dan Allah can ji kanta an faďa ance ji kanta”
Banza tayi da ita ta cigaba da matsar rimot tana cin tofin,
“Idan kinji ma na sake miki magana kice min ba Minal ba”
Dariya Kairat tayi zatayi magana, Jafar ya turo kofar falon ya shigo da sallama,
“Amin wa alaikassalam”
Talatu ta amsa masa, sai da ya gaidasu sannan yace
“Wai Saif yace a kira masa Kairat”
Dimmm gaban Minal da Kairat ya faďi, suka haďa ido kamin daga bisani Minal.ta janye nata,
“Kodai Minal yace.?”
Kairat ta tambaya,
“A'a kedai yace a kira masa yana nan waje”
Rasa tayi abunda zata ce dashi, idan tace baxata ba Minal zatayi tunanin wani abun ne idan kuma taje Minal zatayi tunani wani abun ne kuma, toh ya zatayi.?
Minal ce ta katse mata hanzari, da faďar
“Jeki kace gata nan zuwa”
“Toh”
Da sauri ya tashi ya fice. Kairat ta kalleta
“Haba Minal nace miki zani ne?”
“Amman kinsan Saif yafi karfin wulakanci ko.?”
“Lallai kan Kuma baki san abunda yake tafe dashi cikin daren nan ba”
Talatu ta faďa tana kokarin tashi. Tashi itama Kairat tayi ta nufi hanyar ďakinta, Ta daďe tsaye kamin ta saka hijabinta ta fito.
Tsaye ta hangosa jikin mota sanye da bakar jallabiya ya rumgume hannayesa yana kallon sama kamar mai kidayar taurari,
da sanyin jiki ta karasa kusa dashi, cikin sallama. a hankali ya sauke idanunsa akanta ya kamar mata murmushi.
Bata jira ya amsa tambayar ba ta aika masa da tambayoyi,
“Me kazo yi yanxu da dare nan Saif.? Minyasa kace akira maka ni ? mi zanyi maka.?”
Ido ya kura mata,
“Wace Tambayr zan fara amsa miki”
“Mi kazo yi da dare haka.?”
“Daga gurin Abbah nake wasu file na kai msa shine nace bari na biyo kinsan kusa ne”
Kai ta ďaga masa tana kallon windon falo kamar mai jin tsoro,
“Miyasa kace a kirani Bayan ga Minal.?”
“Ke naga damar kira”
Cikin kakkausar murya ya bata amsa, Nan ta kallesa,
“Abunda kake bai kamata ba Saif”
“Ke kina yin abunda ya dace ne.?”
“Ba haka bane yanzu Minal zatayi tunanin ko wani abun ne”
“Toh sai me dan tayi tunanin kina tsoronta ne?”
“Bana tsoronta”
“Miyasa kike gudun 6acin ranta.?”
“Saboda ina son farin cikinta”
Kai tsaye yake mata tambayoyin tana bashi amsa. A hankali ya gyara tsayuwarsa fuskarsa ba yabo ba fallasa yace,
“Bari na faďa miki wani abu da baki sani ba a kaina Kaiyrat, Bana yin abu a tambaye ni dalili, bana tambaya a maida min tambaya, bana cewa A ace min B ba mai kallon tsakar idona ya faďa min bakar magana, Bana kira a kashe idan bani na kashe ba. Duk abubuwan nan dana faďa kin aikata su na kyale ki ne dan kawai ina mutunta ki and i have something behind your heart, so don't try me again”
Nan ya jefa mata gift ďin dake hannunsa,
“Bana kyauta a mayar min idan kinga dama ki ďauka ko ki jefar”
Bai jira cewarta ba ya buďe motarsa ya shiga, da wani karfi ya fisgeta ya fice gidan kamar kyaftawar walkiya.
Sai a lokacin ta iya yin tsotsin kirki, dan tunda ya fara maganar tayi saranda tana saurarensa. Dukawata tayi ta ďauki gif ďin da aka naďe cikin jar fefa mai zanen heart, ta nufi kofar falo, jikinta sayyaye.
Tana turo kofar falon Minal ta kalleta, Murmushi Kairat ta sakar mata tabkaraso da sauri kusa da ita kamar ba ita ba,
“Minal kinsan meye.?”
Kai ta girgiza mata, Kusa da ita ta zauna tana mika mata Gif đin
“Wai kiran da yayi min danki ne fa kinga abunda ya siyo miki wai tsoron baki yake ji karki watsa masa kasa a ido.”
Da sauri Minal ta mika hannu ta kar6a zuciyarta cike da farinciki,
“Tsorona sai kace wata dodo miye a ciki.?”
“Ai bai yarda na buďe ba wai sai na kawo miki kuma yace na gaishe ki”
Da karfi Minal ta fixge fefar. Kairat gabanta sai faďuwa yake kar Minal.tqga wani abun da zai sa tayi tunanin yana sonta Allah allah take idan bai rubuta sunan ta ba ko wani abu daya danganceta, Da farko batayi niyar bata ba sai kuma tayi tunani idan bata bata ba toh me xata ce mata Saif yazo yi a gida kuma gurinta.
Cake ne cikin kwali mai ganen heart guda shida guri ďaya, ďaya ta ďauka tabkai bakinta ta lumshe idon tana murmushi. Can kuma ta buďe idon ta rumgume Kairat, Dariya Kairat tayi wadda zan iya cewa bata kai ciki ba, tace
“Minal kin jidaďi ko.?”
“Sosai ma”
“Minal kina son Saif ko.?!”
D'agowa tayi daga jikinta tayi kasa da kanta,
“Amman ina jin tsoron kar shima ya juya min baya Bana sin daga baya wata matsalar ta fito yace ba zai zauna dani ba”
Hannu Kairat ta kai ta rika fuskarta, tana murmushi
“Zai soki Minal ba zai barki ba Saif ya banbanta da sauran maza Ba zaki sake bakin ciki ba Minal no more sad, no more tears wadda kikayi a baya is enough idan mutun bai faranta miki ba Minal toh bazai bakanta miki ba”
Sake rumgume ta Minal tayi ta rumtse ido tana sauke ajiyar zuciya,
“Na gode sosai Kairat”
“Don't mention you deserve more”
Kairat ta faďa tana lumshe ido,
“Kuma shima kamar yana sona ko Kairat.?”
Kai ta ďaga mata tana share hawayen da suka zubo mata,
“Sosai ma Minal yana sonki sosai”
Kara rumgumeta tayi cike da jindaďi.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.
NA
KHADEEJA CANDY
Candynovels.wordpress.com
WATTPAD @khadeeja_candy
“Ba komai na gama abinda zanyi ne ya akayi.?”
“Ba komai Mummy tace na tambaye ki ina kika je min Sarka.?”
Kairat ta tashi tsaye,
“A'a ba wani sarkanki ni tace ta siyo ma”
“A'a-a'a tace ni ta siyo ma ke sai ta sake zuwa”
“Dan can ji kanta aje a tambayi mummy ďin”
“Ae aje ďin”
Da gudu Minal ta fice tana arigaggan zuwa gurin mummy, Ta riga Kairat isa ďakin sai ta rika yima mummy wink da ido.
“Mummy bani kika siyo ma wannan Sarkar ba.?”
Murmuahi Mummy tayi dai-dai lokacin da Kairat ta shigo ďakin tace,
“A a Kairat na siya ma ke nace sai wani satin”
Dariya Kairat tayi mata tana mata gwalo,
“Allah na gode maka yarinya kinji kunya”
Kukan shagwa6a Minal tasa,
“Gaskiya ni mummy kina gwada min banbanci Ni barin gidan ma zanyi”
“Sai kin dawo Allah ya kiyaye Hanya”
Mummy ta faďa da fuskar zolaya tana murmushi,
Tashi tayi ta bar d'akin tana hararar Kairat, Nan Kairat ta rufa mata baya tana zolayarta,
BAYAN AWA D'AYA.......
Duk zaune suke falo suna fira suna cin Tofin da Talatu tayi musu, Kairat sai santi take wai ya ake yinsa. Duk dariya suka sama, har Mummy Minal tace
“Da madara ake yinshi”
“Dan can ji kanta kena tambaya ne sai kace iyawa tayi”
“Wallahi Mummy ta daina ce min aji kaina kona mata ďan banzan duka”
Tashi mummy tayi,
“Idan ba gurin na bar muku ba ba zaku barni na huta ba kullum faďa kuke kamar kananan yara”
“Ai itace ta fara jana”
Minal ta faďa tana hararta, Kairat taja tsaki
“Ji kanta dana jaki saina kaiki ina?”
“Kinji ko mummy baza ta daina ba”
Mummy dai bata sake ce musu komai ba da nufi ďakinta, Haushin hakan yasa Minal ta ďauki Filo ta jefe Kairat dashi, Nan Kairat ta sake ce mata
“Dan Allah can ji kanta an faďa ance ji kanta”
Banza tayi da ita ta cigaba da matsar rimot tana cin tofin,
“Idan kinji ma na sake miki magana kice min ba Minal ba”
Dariya Kairat tayi zatayi magana, Jafar ya turo kofar falon ya shigo da sallama,
“Amin wa alaikassalam”
Talatu ta amsa masa, sai da ya gaidasu sannan yace
“Wai Saif yace a kira masa Kairat”
Dimmm gaban Minal da Kairat ya faďi, suka haďa ido kamin daga bisani Minal.ta janye nata,
“Kodai Minal yace.?”
Kairat ta tambaya,
“A'a kedai yace a kira masa yana nan waje”
Rasa tayi abunda zata ce dashi, idan tace baxata ba Minal zatayi tunanin wani abun ne idan kuma taje Minal zatayi tunani wani abun ne kuma, toh ya zatayi.?
Minal ce ta katse mata hanzari, da faďar
“Jeki kace gata nan zuwa”
“Toh”
Da sauri ya tashi ya fice. Kairat ta kalleta
“Haba Minal nace miki zani ne?”
“Amman kinsan Saif yafi karfin wulakanci ko.?”
“Lallai kan Kuma baki san abunda yake tafe dashi cikin daren nan ba”
Talatu ta faďa tana kokarin tashi. Tashi itama Kairat tayi ta nufi hanyar ďakinta, Ta daďe tsaye kamin ta saka hijabinta ta fito.
Tsaye ta hangosa jikin mota sanye da bakar jallabiya ya rumgume hannayesa yana kallon sama kamar mai kidayar taurari,
da sanyin jiki ta karasa kusa dashi, cikin sallama. a hankali ya sauke idanunsa akanta ya kamar mata murmushi.
Bata jira ya amsa tambayar ba ta aika masa da tambayoyi,
“Me kazo yi yanxu da dare nan Saif.? Minyasa kace akira maka ni ? mi zanyi maka.?”
Ido ya kura mata,
“Wace Tambayr zan fara amsa miki”
“Mi kazo yi da dare haka.?”
“Daga gurin Abbah nake wasu file na kai msa shine nace bari na biyo kinsan kusa ne”
Kai ta ďaga masa tana kallon windon falo kamar mai jin tsoro,
“Miyasa kace a kirani Bayan ga Minal.?”
“Ke naga damar kira”
Cikin kakkausar murya ya bata amsa, Nan ta kallesa,
“Abunda kake bai kamata ba Saif”
“Ke kina yin abunda ya dace ne.?”
“Ba haka bane yanzu Minal zatayi tunanin ko wani abun ne”
“Toh sai me dan tayi tunanin kina tsoronta ne?”
“Bana tsoronta”
“Miyasa kike gudun 6acin ranta.?”
“Saboda ina son farin cikinta”
Kai tsaye yake mata tambayoyin tana bashi amsa. A hankali ya gyara tsayuwarsa fuskarsa ba yabo ba fallasa yace,
“Bari na faďa miki wani abu da baki sani ba a kaina Kaiyrat, Bana yin abu a tambaye ni dalili, bana tambaya a maida min tambaya, bana cewa A ace min B ba mai kallon tsakar idona ya faďa min bakar magana, Bana kira a kashe idan bani na kashe ba. Duk abubuwan nan dana faďa kin aikata su na kyale ki ne dan kawai ina mutunta ki and i have something behind your heart, so don't try me again”
Nan ya jefa mata gift ďin dake hannunsa,
“Bana kyauta a mayar min idan kinga dama ki ďauka ko ki jefar”
Bai jira cewarta ba ya buďe motarsa ya shiga, da wani karfi ya fisgeta ya fice gidan kamar kyaftawar walkiya.
Sai a lokacin ta iya yin tsotsin kirki, dan tunda ya fara maganar tayi saranda tana saurarensa. Dukawata tayi ta ďauki gif ďin da aka naďe cikin jar fefa mai zanen heart, ta nufi kofar falo, jikinta sayyaye.
Tana turo kofar falon Minal ta kalleta, Murmushi Kairat ta sakar mata tabkaraso da sauri kusa da ita kamar ba ita ba,
“Minal kinsan meye.?”
Kai ta girgiza mata, Kusa da ita ta zauna tana mika mata Gif đin
“Wai kiran da yayi min danki ne fa kinga abunda ya siyo miki wai tsoron baki yake ji karki watsa masa kasa a ido.”
Da sauri Minal ta mika hannu ta kar6a zuciyarta cike da farinciki,
“Tsorona sai kace wata dodo miye a ciki.?”
“Ai bai yarda na buďe ba wai sai na kawo miki kuma yace na gaishe ki”
Da karfi Minal ta fixge fefar. Kairat gabanta sai faďuwa yake kar Minal.tqga wani abun da zai sa tayi tunanin yana sonta Allah allah take idan bai rubuta sunan ta ba ko wani abu daya danganceta, Da farko batayi niyar bata ba sai kuma tayi tunani idan bata bata ba toh me xata ce mata Saif yazo yi a gida kuma gurinta.
Cake ne cikin kwali mai ganen heart guda shida guri ďaya, ďaya ta ďauka tabkai bakinta ta lumshe idon tana murmushi. Can kuma ta buďe idon ta rumgume Kairat, Dariya Kairat tayi wadda zan iya cewa bata kai ciki ba, tace
“Minal kin jidaďi ko.?”
“Sosai ma”
“Minal kina son Saif ko.?!”
D'agowa tayi daga jikinta tayi kasa da kanta,
“Amman ina jin tsoron kar shima ya juya min baya Bana sin daga baya wata matsalar ta fito yace ba zai zauna dani ba”
Hannu Kairat ta kai ta rika fuskarta, tana murmushi
“Zai soki Minal ba zai barki ba Saif ya banbanta da sauran maza Ba zaki sake bakin ciki ba Minal no more sad, no more tears wadda kikayi a baya is enough idan mutun bai faranta miki ba Minal toh bazai bakanta miki ba”
Sake rumgume ta Minal tayi ta rumtse ido tana sauke ajiyar zuciya,
“Na gode sosai Kairat”
“Don't mention you deserve more”
Kairat ta faďa tana lumshe ido,
“Kuma shima kamar yana sona ko Kairat.?”
Kai ta ďaga mata tana share hawayen da suka zubo mata,
“Sosai ma Minal yana sonki sosai”
Kara rumgumeta tayi cike da jindaďi.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.
NA
KHADEEJA CANDY
Candynovels.wordpress.com
WATTPAD @khadeeja_candy