BABI NA GOMA SHA TARA___19
Babban Goro Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Zaune ta tararda shi jingine da kujerar, ga duk kan alama tunani yake dan baiji saukowar taba,
Sai kawai ganinta yayi tsaye akan sa tana wani kumburi. Murmushi ya sakar mata ya Hannunta ya rik'a da niyar zaunar da ita, sai kawai ta fisge hannun ta kara haɗe fuska
“Saif wacece wannan.? Mi tazo yi?”
Ya ɗan daɗe yana kallonta kamin ya bata amsa
“Wacece ita ina ganin ita ya kamata kiyi ma wannan tambayar. Mi tazo yi kuma, tazo ne akan maganar Minal”
“Minal”
Gabanta ya faɗi,
“Kamar ya maganar Minal nifa ban gane ba”
“Naje nayi mata magana ne akan yanayin shigar ta da kuma rayuwar turawa da take”
Zama tayi kusa dashi,
“Saif har yanzu baka daina zancen Minal ɗin nan ba ina kace min ba zaka sake kula ta ba?
Mi kuma ya kaika gurinta yanzu Saif yarinya ance ba yarinyar kwarai bace ba shaye-shaye take yi kuma ance bata da Uba kai baka ma jin kunya a ganka da mace irinta.?”
Dariya, “Huddallah kenan toh ai ni sonta nake ba, kuma dan an ganni da ita ai ba wani abun bane tunda mutunci yar uwata kuma musulma.
Faɗa min waya ce miki bata da Uba kuma tana shaye-shaye.?”
“Ina zama na aka zo aka faďa min ai kasan abun duniya baya 6oya”
“Toh duk wadda ya faďa miki karya yake yi bata da Uba aka haifeta! Shaye shaye kuma a da ne tayi yanxu ta daina”
“Kare ta dai kake son yi Saif amman nasan wadda ya faďa min ba xai min karya ba, kuma ni banga abunda ta fini dashi ba da har zai ďauki hankalinka gurinka”
Hannu ya kai ya shafa fuskarta,
“Kina wahalar da kanki Huda, na faďa miki ba son Minal nake ba ni kwata kwata bata cikin tsarin rayuwa ta”
“Amman mi yasa kake kula ta?”
Duk yadda zai mata ba yarda zatayi ba dan yasan halin Huda da naci indai akan kishi ne, amman shi kan har cikin zuciyarsa Minal bata cikin tsarin rayuwarsa, Hancinta ya lakata ya tashi ya Upstairs.
Yana shiga ďaki ya cire kayan dake jikinsa ya ďaura dan karamin tawul ya shiga badroom,
Koda ya fito jikinsa da sanyi da alama wanka yayi, a gaggauce ya shirya cikin kananan kaya black jean da farar T-shirt, ya feshe jikinsa da turare, sannan ya ďauki Atm ďinsa da makullin mota ya fice.
Har lokacin Hud na zaune inda ya barta tana tunane-tunane, sam zuciyarta taki yarda da Saif ba son Minal yake ba, indai har da gaske ba sonta yake ba toh ina ruwansa da duk wata rayuwa da zata shiga.
Tana wannan tunanin ya sauko downstairs, kallo ďaya yayi mata ya ďauke kai yana murmushi, yasan har yanzu abun ne take tunani ganin yadda tayi nikin nikin da fuska babu Annuri. Baice da ita komai ba ya nufi kofar fita, itama bata ce dashi ba dan haushin sa ne ya karu ganin yadda ya ďauki wanka zai fita, har ya fice kallonsa take zuciyarta na raya mata can zaije.
Sai da taji tashin motarsa sannan ta nufi harabar gidan tana kwalama masu gadi kira, jiki na rawa suka iso suna mata gaisuwar girmamawa,
Bata amsa musu ba ta hau su da masifa.
“Wai miye aikin ku a gidan nn ba gadi ba kuna me wannan yar iskar yarinyar ta shigo min har cikin gida?”
“Hajiya tace ita yar Ibrahim Ahlam ce shiyasa muka barta ta shigo”
D'aya daga cikinsu ne ya bata amsa,
“Ina ruwana da waye ubanta nan gidana ne ba nata ba karku sake bari wata mace ta shigo min cikin gida ba tare da izinina ba duk kuka sake haka wallahi ba kin aikin ku”
Hakuri suka rika bata, ita kuma sai wani kumburi take bata sake ce musu wani abun ba ta juya ta koma cike da gadara.
**** **** ****
A hankali taji ana buga kofar falon, tashi tayi ta nufi kofar tana tambayar waye, Ba a bata amsa ba har ta buďe kofar.
Murmushi ya sakar mata
“Kaiyrat”
“Na'am Saif”
Ita ta mayar masa da murmushin tana kara wangale kofar.
“Shigo mana Saif a gidan ba bakinka bane”
Bai shigo ba sai kawai yasa hannayensa aljihu ya sakar mata ido har sai da idanuwansu sukayi taraiya, da sauri ta sauke nata idon cike da kunya ta ɗanja baya.
Hakan da tayi sai ta burgeshi dan shikan yana son mace da kunya da kuma kamun kai, Murmushin dake fuskarsa ne ya faɗaɗa.
“A'a bazan shigo ba har sai Qawarki tayi min izini”
“Yar'uwarta zaka ce ba qawata ba tana can Garden zaune”
Ta karasa maganar tana nuna masa hanyar Garɗen ɗin, Girarsa ya haɗe akamar tambaya,
“So.?”
“Sai kaje ka bata hakuri”
Kai ya kaɗa, ya ɗga daga jikin kofar ya nufi hanyar Garɗen.Tsaye tayi tana kare masa kallo, ita kan raywarsa tana bugerta bai ɗauki kansa wani ba, kuɗi dake tare dashi basu rufe masa ido ya wulakanta kowa ba, rayuwarsa so simple gashi kyakkyawa. Ya iya zama da kowa,
Sai da ta daina hango shi sannan ta rufe kofar falon tana sauke ajiyar zuciya.
Zaune take saman doguwar kujera tana rubuce-rubuce da biro kamar wata karamar yarinya sai yage takarda take tana zubarwa,
Dariyar da taji anyi yasa ta ɗago kai ta kalli gurin da Saif yake tsaye, Kara haɗe fuska tayi ta mayarda kanta gurin rubutun da take, wai ita ala dole tana fushi,
Karawo yayi kusa da ita da fuskar zolaya,
“Har yanxu baki hakura ba kenan yanxu daga faɗar gaskiya shi kenan na zama mai laifi.?”
Bata ce dashi komai ba sai rubutunta take kamar ma bata san dashi a gurin ba, ganin hakan yasa ya fisge biron dake hannunta ya jefar,
“Zuwan nan da nayi dan ki kawai nayi shi Minal nasan na ɓata miki rai but am sorry bazan sake ba”
Tashi tayi tsaye ba tare data kalleshi ba tace,
“Na hakura”
Sai ta juya da nufin tafiya,Da sauri ya riko ta ya juyo da ita.
“Wanna hakurin ai na dole ne”
Sai a lokacin ta ɗan kallesa ta ɗauke ido,
“Toh mi kake son nace maka?
“Ba wani abun nake son kice min ba kawai hakuri nake son gani a fuskarki, Minalina son ki fahimci wani abu. duk abunda nayi miki nayi ne dan ina kishinki Minal ina bakin cikin yadda kike sakin surar jikinki ga mazan da ba muharramanki na suna kallonki, Minal bana son yadda kike kwaikwayar rayuwar turawa fan abanga abun burgewa a rayuwarsu ba Kishinki ne kai ni ga furta miki kalmomin da suka ɓata miki rai, ina fatar zaki min uzuri ki fahimce ni yanzu”
Shiru tayi kamar mai nazari, Ganin hakan yasa ya riko hannayenta yana kallon fuskarta dan ta tabbatar da gaskiyar maganar sa.
Har cikin birnin zuciyarta taji sanyin tafukan hannayensa, Nan take kanshin turarensa ya shiga kai ma hancinta hari. Bata an karaba taji faɗuwar gaba sakamakon haɗa ido da tayi dashi. Cikin taku ta kawarda nata idon, da murya mai kamar kuka kamar shagwaɓa tace,
“Amman Saif miyasa kace tirrrr dani? wanna kalamar ita tafi min zafi kuma na kasa gane dalilin furta min ita da kayi Miyasa ba zaka fahimci halin da nake ciki ba?”
Idonta cike da ruwan hawaye ta karasa maganar, fuskarta na kallon gefe. Bakimsa ya cika ma iska, dan yasan duk yadda yake son ta fahimta ba fahimta zatayi ba. Hannu ya kai ya shafa gashin kanta, yaja zuwa kirjinsa ya rugumta.
“Kiyi hakuri Minal nayi miki alkawarin bazan sake ba”
Kara kamkamesa tayi ta lumshe ido tana shakar daɗadɗen kanshin dake tashi daga jikinsa, Ta hakan ya gane ta hakura daman yasan idan ba hakan yayi mata ba, baxata hakura ba.
Jikinsa ne ya bashi ana kallonsa. hakan yasa ya ɗago kai ya kalli windon dake fuskantarsu, Kairat ce tsaye jikin windo tana kallonsu fuskarta ɗauke da murmushi.
Daga inda yake tsaye ya aika mata da sakon lafiyayyen murmushi wadda zan iya cewa har cikin zuyarsa yake.
Ita kuma ta ɗago masa babban yatsanta alamar well done tana murmushi, sannan taja windon ta rufe zuciyarta a rike. Jinginawa tayi jikin windo gumɗe da baki.
Can kuma naga ta rumtse ido ta sulale kasa zaune, tana girgiza kai kamar mai magana da wani.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.
NA
KHADEEJA CANDY
Candynovels.wordpress.com
WATTPAD @khadeeja_candy
Sai kawai ganinta yayi tsaye akan sa tana wani kumburi. Murmushi ya sakar mata ya Hannunta ya rik'a da niyar zaunar da ita, sai kawai ta fisge hannun ta kara haɗe fuska
“Saif wacece wannan.? Mi tazo yi?”
Ya ɗan daɗe yana kallonta kamin ya bata amsa
“Wacece ita ina ganin ita ya kamata kiyi ma wannan tambayar. Mi tazo yi kuma, tazo ne akan maganar Minal”
“Minal”
Gabanta ya faɗi,
“Kamar ya maganar Minal nifa ban gane ba”
“Naje nayi mata magana ne akan yanayin shigar ta da kuma rayuwar turawa da take”
Zama tayi kusa dashi,
“Saif har yanzu baka daina zancen Minal ɗin nan ba ina kace min ba zaka sake kula ta ba?
Mi kuma ya kaika gurinta yanzu Saif yarinya ance ba yarinyar kwarai bace ba shaye-shaye take yi kuma ance bata da Uba kai baka ma jin kunya a ganka da mace irinta.?”
Dariya, “Huddallah kenan toh ai ni sonta nake ba, kuma dan an ganni da ita ai ba wani abun bane tunda mutunci yar uwata kuma musulma.
Faɗa min waya ce miki bata da Uba kuma tana shaye-shaye.?”
“Ina zama na aka zo aka faďa min ai kasan abun duniya baya 6oya”
“Toh duk wadda ya faďa miki karya yake yi bata da Uba aka haifeta! Shaye shaye kuma a da ne tayi yanxu ta daina”
“Kare ta dai kake son yi Saif amman nasan wadda ya faďa min ba xai min karya ba, kuma ni banga abunda ta fini dashi ba da har zai ďauki hankalinka gurinka”
Hannu ya kai ya shafa fuskarta,
“Kina wahalar da kanki Huda, na faďa miki ba son Minal nake ba ni kwata kwata bata cikin tsarin rayuwa ta”
“Amman mi yasa kake kula ta?”
Duk yadda zai mata ba yarda zatayi ba dan yasan halin Huda da naci indai akan kishi ne, amman shi kan har cikin zuciyarsa Minal bata cikin tsarin rayuwarsa, Hancinta ya lakata ya tashi ya Upstairs.
Yana shiga ďaki ya cire kayan dake jikinsa ya ďaura dan karamin tawul ya shiga badroom,
Koda ya fito jikinsa da sanyi da alama wanka yayi, a gaggauce ya shirya cikin kananan kaya black jean da farar T-shirt, ya feshe jikinsa da turare, sannan ya ďauki Atm ďinsa da makullin mota ya fice.
Har lokacin Hud na zaune inda ya barta tana tunane-tunane, sam zuciyarta taki yarda da Saif ba son Minal yake ba, indai har da gaske ba sonta yake ba toh ina ruwansa da duk wata rayuwa da zata shiga.
Tana wannan tunanin ya sauko downstairs, kallo ďaya yayi mata ya ďauke kai yana murmushi, yasan har yanzu abun ne take tunani ganin yadda tayi nikin nikin da fuska babu Annuri. Baice da ita komai ba ya nufi kofar fita, itama bata ce dashi ba dan haushin sa ne ya karu ganin yadda ya ďauki wanka zai fita, har ya fice kallonsa take zuciyarta na raya mata can zaije.
Sai da taji tashin motarsa sannan ta nufi harabar gidan tana kwalama masu gadi kira, jiki na rawa suka iso suna mata gaisuwar girmamawa,
Bata amsa musu ba ta hau su da masifa.
“Wai miye aikin ku a gidan nn ba gadi ba kuna me wannan yar iskar yarinyar ta shigo min har cikin gida?”
“Hajiya tace ita yar Ibrahim Ahlam ce shiyasa muka barta ta shigo”
D'aya daga cikinsu ne ya bata amsa,
“Ina ruwana da waye ubanta nan gidana ne ba nata ba karku sake bari wata mace ta shigo min cikin gida ba tare da izinina ba duk kuka sake haka wallahi ba kin aikin ku”
Hakuri suka rika bata, ita kuma sai wani kumburi take bata sake ce musu wani abun ba ta juya ta koma cike da gadara.
**** **** ****
A hankali taji ana buga kofar falon, tashi tayi ta nufi kofar tana tambayar waye, Ba a bata amsa ba har ta buďe kofar.
Murmushi ya sakar mata
“Kaiyrat”
“Na'am Saif”
Ita ta mayar masa da murmushin tana kara wangale kofar.
“Shigo mana Saif a gidan ba bakinka bane”
Bai shigo ba sai kawai yasa hannayensa aljihu ya sakar mata ido har sai da idanuwansu sukayi taraiya, da sauri ta sauke nata idon cike da kunya ta ɗanja baya.
Hakan da tayi sai ta burgeshi dan shikan yana son mace da kunya da kuma kamun kai, Murmushin dake fuskarsa ne ya faɗaɗa.
“A'a bazan shigo ba har sai Qawarki tayi min izini”
“Yar'uwarta zaka ce ba qawata ba tana can Garden zaune”
Ta karasa maganar tana nuna masa hanyar Garɗen ɗin, Girarsa ya haɗe akamar tambaya,
“So.?”
“Sai kaje ka bata hakuri”
Kai ya kaɗa, ya ɗga daga jikin kofar ya nufi hanyar Garɗen.Tsaye tayi tana kare masa kallo, ita kan raywarsa tana bugerta bai ɗauki kansa wani ba, kuɗi dake tare dashi basu rufe masa ido ya wulakanta kowa ba, rayuwarsa so simple gashi kyakkyawa. Ya iya zama da kowa,
Sai da ta daina hango shi sannan ta rufe kofar falon tana sauke ajiyar zuciya.
Zaune take saman doguwar kujera tana rubuce-rubuce da biro kamar wata karamar yarinya sai yage takarda take tana zubarwa,
Dariyar da taji anyi yasa ta ɗago kai ta kalli gurin da Saif yake tsaye, Kara haɗe fuska tayi ta mayarda kanta gurin rubutun da take, wai ita ala dole tana fushi,
Karawo yayi kusa da ita da fuskar zolaya,
“Har yanxu baki hakura ba kenan yanxu daga faɗar gaskiya shi kenan na zama mai laifi.?”
Bata ce dashi komai ba sai rubutunta take kamar ma bata san dashi a gurin ba, ganin hakan yasa ya fisge biron dake hannunta ya jefar,
“Zuwan nan da nayi dan ki kawai nayi shi Minal nasan na ɓata miki rai but am sorry bazan sake ba”
Tashi tayi tsaye ba tare data kalleshi ba tace,
“Na hakura”
Sai ta juya da nufin tafiya,Da sauri ya riko ta ya juyo da ita.
“Wanna hakurin ai na dole ne”
Sai a lokacin ta ɗan kallesa ta ɗauke ido,
“Toh mi kake son nace maka?
“Ba wani abun nake son kice min ba kawai hakuri nake son gani a fuskarki, Minalina son ki fahimci wani abu. duk abunda nayi miki nayi ne dan ina kishinki Minal ina bakin cikin yadda kike sakin surar jikinki ga mazan da ba muharramanki na suna kallonki, Minal bana son yadda kike kwaikwayar rayuwar turawa fan abanga abun burgewa a rayuwarsu ba Kishinki ne kai ni ga furta miki kalmomin da suka ɓata miki rai, ina fatar zaki min uzuri ki fahimce ni yanzu”
Shiru tayi kamar mai nazari, Ganin hakan yasa ya riko hannayenta yana kallon fuskarta dan ta tabbatar da gaskiyar maganar sa.
Har cikin birnin zuciyarta taji sanyin tafukan hannayensa, Nan take kanshin turarensa ya shiga kai ma hancinta hari. Bata an karaba taji faɗuwar gaba sakamakon haɗa ido da tayi dashi. Cikin taku ta kawarda nata idon, da murya mai kamar kuka kamar shagwaɓa tace,
“Amman Saif miyasa kace tirrrr dani? wanna kalamar ita tafi min zafi kuma na kasa gane dalilin furta min ita da kayi Miyasa ba zaka fahimci halin da nake ciki ba?”
Idonta cike da ruwan hawaye ta karasa maganar, fuskarta na kallon gefe. Bakimsa ya cika ma iska, dan yasan duk yadda yake son ta fahimta ba fahimta zatayi ba. Hannu ya kai ya shafa gashin kanta, yaja zuwa kirjinsa ya rugumta.
“Kiyi hakuri Minal nayi miki alkawarin bazan sake ba”
Kara kamkamesa tayi ta lumshe ido tana shakar daɗadɗen kanshin dake tashi daga jikinsa, Ta hakan ya gane ta hakura daman yasan idan ba hakan yayi mata ba, baxata hakura ba.
Jikinsa ne ya bashi ana kallonsa. hakan yasa ya ɗago kai ya kalli windon dake fuskantarsu, Kairat ce tsaye jikin windo tana kallonsu fuskarta ɗauke da murmushi.
Daga inda yake tsaye ya aika mata da sakon lafiyayyen murmushi wadda zan iya cewa har cikin zuyarsa yake.
Ita kuma ta ɗago masa babban yatsanta alamar well done tana murmushi, sannan taja windon ta rufe zuciyarta a rike. Jinginawa tayi jikin windo gumɗe da baki.
Can kuma naga ta rumtse ido ta sulale kasa zaune, tana girgiza kai kamar mai magana da wani.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.
NA
KHADEEJA CANDY
Candynovels.wordpress.com
WATTPAD @khadeeja_candy