Sashe 9
Yan Gidan Haya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin fusata Maman Ladi ta nufo Inna Talatu ta hauta da duka, sai dambe. Kaya-kaya ana kokarin rabawa sunki rabuwa domin a zuciye Maman Ladi take sai jibgar Inna Talatu take yi, ganin haka yasa Inno shigarwa Inna Talatu dama tare suke adawa da wannan aure. Aikuwa hadasu Maman Ladi ta yi t dinga jibga tana gwara kawunansu.
Ladidi dake tsaye gefe ta kalli Mairon Ado tace"Ke Mairo zo ki tayani dibar abinci idan kina so."
Abule dake zaune tana kallon fad'a ta dubi su Mairo "Walle Mairo ta karkije wanga cin amana ta zata yi."
"Wani shegen yace miki cin amana zanyi?"
"Ke na shegiya." cewar Abule.
Mari Ladidi ta kawo ma Abule, Mairon Ado ta tare tana hararar Ladidi"Kika tabata sai na sabautaki wallahi matsiyaciya kawai mai..." bugun bakinta da Ladidi ta yi yasa ta yi shiru ba tare data shirya ba.
Abule na ganin haka ta hau Ladidi da duka baji ba gani. Suma suka hau fad'an su uku, gefe kuma gasu Maman Ladi. Gudar masu daukar amarya ne y dakatar da wannan rikice, aka shiga kallon-kallo.
"Munzo daukar amaryar mai unguwa."Cewar Maimounath makociyar mai unguwa da ya roka suzo dauko amarya tunda yan'uwan shi sunki zuwa. Ita kuma Maimounath dama da biyu tazo saboda basa ga maciji da 'yan gidan haya.
Shewa Inno data gama dokuwa gurin Maman Ladi tasa tana fadin"Gaya musu su fito muku da amarya ku cika umarnin mai unguwa."
"Aikuwa dai yar'uwa abamu amarya a mutunce mu kaita dak'in ango a mutum.." wani duka taji ya sauka a kanta wanda yasa ganinta ya dauke na 'yan sakanni.
"Bari naji' yar iskar data kara cewa na bada diyata akai gidan mai unguwa." cewar Maman Ladi dake tsaye rike da muciya.
Nan fa 'yan koren Maman Ladi ko wacce t dauko abun duka.'Yan daukar amarya na ganin haka ga Maimounath durkushe a kasa, ai sai suka sanya gudu suka barta. Ladidi ta kalle ta ta tuntsire da dariya tana fadin "Su yan daukar amarya ansha wahala, ina bakin fadin amarya yake?"
Cikin karfin hali Maimounath ta mike ta shake wuyan Ladidi ta fara jibga, ganin haka Maman Ladi da sauran suka rufeta da duka, sukai mata lilis suka barta kwance.
*WURIN MAI UNGUWA*
Sauran da suka koma suka fadi ma mai unguwa abun dake faruwa, aikuwa ya mike ya saba riga shida abokin shi Kallah da baban Ladi suka nufi gidan.
Yana fadin " Wallahi yau Lawal matar ka zata san Tanko take raina wa."
" Ayi hakuri don Allah Ranka-ya-dade."
Matan naji Hannatu t dinga dariya "Maman Sani yau zaki ga angon da daukar amarya, Allah yasa Maman Ladi ta mai dukan tsiya."
" Uhm Uhm Hannatu mijin kine fa."
"Maman Sani ayi sha'ani kawai wallahi."
Nan suka dinga tattaunawa suna kara jajantawa kansu aikin da ya dauko musu.
*CIKIN GIDAN 'YAN HAYA KUWA*
_MEZAI FARU DA ZUWAN MAI UNGUWA_
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:45 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱
. 👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*WANNAN SHAFIN NA MUSAMMAN NE GAREKU DOMIN KU DIN NA MUSAMMAN NE, KODAYAUSHE INA YI MUKU FATAN ALHERI*
_BRO HUSSAIN ATK_
-BRO HASSAN ATK_
_AUNTY HASSANA ATK_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*70~75*
Maimounath kwance ko motsi bata yi saboda ta daku, su mai unguwa suka doka sallama suka shigo. Ganin ta kwance yasa sauran matan suka nufeta da sauri suna tambayar lafiya. Inna Talatu dake tsaye kofar dak'inta ta bude baki da karfi tace"Su Maman Ladi ne suka jibgeta wallahi."
Mai unguwa ya kalle su fuskannan a daure yace " ku dauketa ko kaita kemis ina zuwa."
Suka dauketa su uku suka fice.
Ya kalli Maman Ladi dake tsaye bakin kofarta, inda ta rufe Ladi dake aikin kuka ita batasan mai unguwa. Yace" Nazo daukar matata da kai na."
"Sai dai idan uwar matar ka zaka dauka."ta bashi amsa.
Ya kalli Baban Ladi, ai kuwa da sauri ya matso jiki na kakkarwa yace"Haba Maman Ladi don Allah ki bari a tafi da ita wallahi yanzu bamu da iko da ita."
"Algungumi ba inda zata indai nina haifeta, kuma wallahi naga uban da zai dauketa."
"Nine kuwa uban da zai dauketa billahillazi."cewar mai unguwa.
"To kana iya zuwa ka dauketa ai matsiyaci."
"Kece dai matsiyaciya shegiya me bakin hali."
Da sauri Kallah yace" Ranka-ya-dade surukar kace fa yanzu a tauna kalamai."
Wani kallo ya buga ma Kallah wanda yasa Kallah tsugunnawa yana fadin "Tuba nake Yallabai."
"Wallahi yau zaa bani matata ko kuma na yi bala'i billahillazi,kuma wannan mai kama da buhun fulawar ta yi kadan na kira ta da suruka."
"Kana iya zuwa ka dauketa ai idan kai ka haifa min yarinyar, mai kama da sauro."
Karasawa kofar dak'in ya yi yana kokarin shiga, aikuwa Maman Ladi da mutanen ta suka rufe shi da duka ga makota nata shigowa kallo. Dukan shi suke suna karawa shikuma kokarin ceton kansa ya ke don kuwa baisan tsiyar da suka shirya mai ba kenan.
Kallah da Baban Ladi nata rokon su dai na amma sunki don haka Kallah ya ranta ana kare yana fadin"Naji bayanin yanda aka kare idan mun hadu, domin wa'innan matan babu alamun tausayi tare dasu."
Makota na leke suna bada hakuri wasu kuma suna kara zuga wa.
Jiniyar motan 'yan sanda suka jiyo, aikuwa suka sake mai unguwa da sauri suka shige dakunan su.'Yan sanda suka shigo su biyar uku mata biyu maza cikin gidan. Mai unguwa na ganin su ya sanya ya mike da kyar yana goge jinin bakin shi yace"Kuci uban su sosai ku tafi dasu setation don Allah, billahillazi bazan yafe musu ba kuma a fito min da matata."
"Kayi hakuri mai unguwa zamu dauki mataki insha Allah."
Nan aka sanya 'yan sanda matan suka shiga dakunan duk aka tarkato su waje.
Maman Usman ce kadai bata nan, domin ta yi tafiya bata gari duk wannan bidirin da ake yi. Gaba daya matan gidan aka tasa su gaba zuwa ofishi, mai unguwa yace a taho masa da mata, aka kuwa fito da ita sai kuka take.
Aka tasa keyarsu hada 'yan biki sai setation.
*Ofishin' yan sanda*
Suna zaune Dpo ya shigo, ganin mai unguwa manne da bandeji a Hannunsa da gefen kunne yasa ya karaso da sauri.
"Mai unguwa maiya same ka haka ne, ba dai hatsari kayi ba?"
"Bari Ddo waccan tsinanniyar matar ce ta jimin ciwo wallahi."
Sai lokacin Dpo Muhammad Abubakar ya lura da matan dake tsaye gefe guda. Da mamaki ya kira sajan yana tambayar meyafaru, nan suka fada mishi tun daga kiran da akayi musu da kuma yanda suka tadda mai unguwa ga Maimounath ma sun daketa.
"Dankari! Kenan menene matsalar?"
"Ranka-ya-dade sai dai a kira mai unguwa ya yi bayani."
"Kirashi su."
"Yes sir." ya fita ya kira mai unguwa suka shigo tare.
Nan ya zaiyane komai da ya sani dangane da fad'an da kuma dukan da suka yi mishi da Maimounath. Nan Dpo ya fito ya tara su wuri daya ya fara tambayar ba'asi. Wasu su fadi gaskiya wasu akasin haka, dukka ya tattara ya hada ya yi tagumi yana kallon su. Duk sukai shiru suna kallon shi yace "Aba mai unguwa matarsa su tafi."
Kuka Maman Ladi ta sa tana fadin" Wallahi bazan yarda diyata taje gidan shi ba, domin da farko ai basu fadamin gaskiya duk munafukai ne."
Tsawa ya daka mata ta yi shiru tana kallon shi. Ya yi musu dogon sharhi kan boye mata da suka yi sannan ya yi umarnin Maman Ladi da sauran duk zasu bada dari biyar-biyar na dukan mai unguwa da Maimounath kudin magani. Haka suka bayar suna Allah ya isa a zuci. Haka ya dinga musu nasiha yana ankarar dasu illar abun da suke yi, daga bisani ya sallame su suka fito. Maman Ladi na kuka Ladi nayi suka rabo ta hau mashin din mai unguwa suka tafi. Su kuma matan gidan da 'yan biki ko wacce ta yi hanyar gidan ta.
Maman Ladi na koma wa ta dinga rabawa 'yan gidan duk kayan bikin data hada tana cewa "Wallahi dana kai gidan mai unguwa gara na zubar dashi." Ta kira almajirai ta dinga rabo.
*GIDAN MAI UNGUWA*
Yana tsayar da mashin ta sauka ta tirje taki shiga, juyin duniya Ladi taki shiga gidan. Mai unguwa ya fusata ya dinga zaginta. Hayaniyarshi ta sanya matan lekowa jin yana surfa zagi, aikuwa ganin Ladi tsaye kikam kamar gunki yasa Jummai dauko mayafi ta fito,tana zuwa ta riko hannun Ladi, aikuwa bata yi gardama ba ta bita suka shiga gidan.
Takaicin hakan yasa mai unguwa gunduma musu ashar yana cewa"Ban aurota don ku zauna da ita ba, billahillazi kar wacce ta koya mata bakin hali." basu kula shi ba suka shige dak'in Jummai dukkansu.
Zaunar da Ladi ta yi tana rarrashi Hannatu ta debo mata abinci suka saka ta gaba suna ta bata hakuri. Da kyar ta yi shiru yana ajiyar zuciya taci abincin tasha ruwa ta haye gadon Jummai ta kwanta. Kallon juna suka yi Hannatu tace "To yanzu ya zaki yi taje dak'inta?, kuma fa dak'in ba komai basu kawo kaya ba."
"Barni dashi Hannatu zai gane kuranshi ya sake ya shigo da sunan tafiya da yarinyar nan dak'inta."
Duk suka zauna suna dakon zuwan mai unguwa, kamar ya sani kuwa yaki zuwa ya shige dak'i ya kwanta yana jinyar jikin shi.
*WASHEGARI GIDAN HAYA*
Maman Ladi ta tashi zuciya tunkushe da bakin ciki, ta kira Inno tace "Inno ki kwashe kayan gadon nan ki siyar dasu ki ban kudina ko nawane gara nayi asara dana kai ma mai unguwa."
"Haba Maman Ladi kiyi domin diyar ki mana, kinsan dai mai unguwa bazai kula da ita yanda ya dace ba, kiyi hakuri ki kai mata."
Shiru Maman Ladi ta yi tana tunani, can tace "Shikenan ku shirya kukai kayan to." ta shige dak'i. Gyada kai Inno ta yi domin ta tausaya wa Ladi da auren mai unguwa dama dan basu san waye angon ba yasa suke bakin ciki.
Haka kuwa rana na yi aka kwashe kaya sai gidan mai unguwa.
Ladidi dake tsaye gefe ta kalli Mairon Ado tace"Ke Mairo zo ki tayani dibar abinci idan kina so."
Abule dake zaune tana kallon fad'a ta dubi su Mairo "Walle Mairo ta karkije wanga cin amana ta zata yi."
"Wani shegen yace miki cin amana zanyi?"
"Ke na shegiya." cewar Abule.
Mari Ladidi ta kawo ma Abule, Mairon Ado ta tare tana hararar Ladidi"Kika tabata sai na sabautaki wallahi matsiyaciya kawai mai..." bugun bakinta da Ladidi ta yi yasa ta yi shiru ba tare data shirya ba.
Abule na ganin haka ta hau Ladidi da duka baji ba gani. Suma suka hau fad'an su uku, gefe kuma gasu Maman Ladi. Gudar masu daukar amarya ne y dakatar da wannan rikice, aka shiga kallon-kallo.
"Munzo daukar amaryar mai unguwa."Cewar Maimounath makociyar mai unguwa da ya roka suzo dauko amarya tunda yan'uwan shi sunki zuwa. Ita kuma Maimounath dama da biyu tazo saboda basa ga maciji da 'yan gidan haya.
Shewa Inno data gama dokuwa gurin Maman Ladi tasa tana fadin"Gaya musu su fito muku da amarya ku cika umarnin mai unguwa."
"Aikuwa dai yar'uwa abamu amarya a mutunce mu kaita dak'in ango a mutum.." wani duka taji ya sauka a kanta wanda yasa ganinta ya dauke na 'yan sakanni.
"Bari naji' yar iskar data kara cewa na bada diyata akai gidan mai unguwa." cewar Maman Ladi dake tsaye rike da muciya.
Nan fa 'yan koren Maman Ladi ko wacce t dauko abun duka.'Yan daukar amarya na ganin haka ga Maimounath durkushe a kasa, ai sai suka sanya gudu suka barta. Ladidi ta kalle ta ta tuntsire da dariya tana fadin "Su yan daukar amarya ansha wahala, ina bakin fadin amarya yake?"
Cikin karfin hali Maimounath ta mike ta shake wuyan Ladidi ta fara jibga, ganin haka Maman Ladi da sauran suka rufeta da duka, sukai mata lilis suka barta kwance.
*WURIN MAI UNGUWA*
Sauran da suka koma suka fadi ma mai unguwa abun dake faruwa, aikuwa ya mike ya saba riga shida abokin shi Kallah da baban Ladi suka nufi gidan.
Yana fadin " Wallahi yau Lawal matar ka zata san Tanko take raina wa."
" Ayi hakuri don Allah Ranka-ya-dade."
Matan naji Hannatu t dinga dariya "Maman Sani yau zaki ga angon da daukar amarya, Allah yasa Maman Ladi ta mai dukan tsiya."
" Uhm Uhm Hannatu mijin kine fa."
"Maman Sani ayi sha'ani kawai wallahi."
Nan suka dinga tattaunawa suna kara jajantawa kansu aikin da ya dauko musu.
*CIKIN GIDAN 'YAN HAYA KUWA*
_MEZAI FARU DA ZUWAN MAI UNGUWA_
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:45 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱
. 👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*WANNAN SHAFIN NA MUSAMMAN NE GAREKU DOMIN KU DIN NA MUSAMMAN NE, KODAYAUSHE INA YI MUKU FATAN ALHERI*
_BRO HUSSAIN ATK_
-BRO HASSAN ATK_
_AUNTY HASSANA ATK_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*70~75*
Maimounath kwance ko motsi bata yi saboda ta daku, su mai unguwa suka doka sallama suka shigo. Ganin ta kwance yasa sauran matan suka nufeta da sauri suna tambayar lafiya. Inna Talatu dake tsaye kofar dak'inta ta bude baki da karfi tace"Su Maman Ladi ne suka jibgeta wallahi."
Mai unguwa ya kalle su fuskannan a daure yace " ku dauketa ko kaita kemis ina zuwa."
Suka dauketa su uku suka fice.
Ya kalli Maman Ladi dake tsaye bakin kofarta, inda ta rufe Ladi dake aikin kuka ita batasan mai unguwa. Yace" Nazo daukar matata da kai na."
"Sai dai idan uwar matar ka zaka dauka."ta bashi amsa.
Ya kalli Baban Ladi, ai kuwa da sauri ya matso jiki na kakkarwa yace"Haba Maman Ladi don Allah ki bari a tafi da ita wallahi yanzu bamu da iko da ita."
"Algungumi ba inda zata indai nina haifeta, kuma wallahi naga uban da zai dauketa."
"Nine kuwa uban da zai dauketa billahillazi."cewar mai unguwa.
"To kana iya zuwa ka dauketa ai matsiyaci."
"Kece dai matsiyaciya shegiya me bakin hali."
Da sauri Kallah yace" Ranka-ya-dade surukar kace fa yanzu a tauna kalamai."
Wani kallo ya buga ma Kallah wanda yasa Kallah tsugunnawa yana fadin "Tuba nake Yallabai."
"Wallahi yau zaa bani matata ko kuma na yi bala'i billahillazi,kuma wannan mai kama da buhun fulawar ta yi kadan na kira ta da suruka."
"Kana iya zuwa ka dauketa ai idan kai ka haifa min yarinyar, mai kama da sauro."
Karasawa kofar dak'in ya yi yana kokarin shiga, aikuwa Maman Ladi da mutanen ta suka rufe shi da duka ga makota nata shigowa kallo. Dukan shi suke suna karawa shikuma kokarin ceton kansa ya ke don kuwa baisan tsiyar da suka shirya mai ba kenan.
Kallah da Baban Ladi nata rokon su dai na amma sunki don haka Kallah ya ranta ana kare yana fadin"Naji bayanin yanda aka kare idan mun hadu, domin wa'innan matan babu alamun tausayi tare dasu."
Makota na leke suna bada hakuri wasu kuma suna kara zuga wa.
Jiniyar motan 'yan sanda suka jiyo, aikuwa suka sake mai unguwa da sauri suka shige dakunan su.'Yan sanda suka shigo su biyar uku mata biyu maza cikin gidan. Mai unguwa na ganin su ya sanya ya mike da kyar yana goge jinin bakin shi yace"Kuci uban su sosai ku tafi dasu setation don Allah, billahillazi bazan yafe musu ba kuma a fito min da matata."
"Kayi hakuri mai unguwa zamu dauki mataki insha Allah."
Nan aka sanya 'yan sanda matan suka shiga dakunan duk aka tarkato su waje.
Maman Usman ce kadai bata nan, domin ta yi tafiya bata gari duk wannan bidirin da ake yi. Gaba daya matan gidan aka tasa su gaba zuwa ofishi, mai unguwa yace a taho masa da mata, aka kuwa fito da ita sai kuka take.
Aka tasa keyarsu hada 'yan biki sai setation.
*Ofishin' yan sanda*
Suna zaune Dpo ya shigo, ganin mai unguwa manne da bandeji a Hannunsa da gefen kunne yasa ya karaso da sauri.
"Mai unguwa maiya same ka haka ne, ba dai hatsari kayi ba?"
"Bari Ddo waccan tsinanniyar matar ce ta jimin ciwo wallahi."
Sai lokacin Dpo Muhammad Abubakar ya lura da matan dake tsaye gefe guda. Da mamaki ya kira sajan yana tambayar meyafaru, nan suka fada mishi tun daga kiran da akayi musu da kuma yanda suka tadda mai unguwa ga Maimounath ma sun daketa.
"Dankari! Kenan menene matsalar?"
"Ranka-ya-dade sai dai a kira mai unguwa ya yi bayani."
"Kirashi su."
"Yes sir." ya fita ya kira mai unguwa suka shigo tare.
Nan ya zaiyane komai da ya sani dangane da fad'an da kuma dukan da suka yi mishi da Maimounath. Nan Dpo ya fito ya tara su wuri daya ya fara tambayar ba'asi. Wasu su fadi gaskiya wasu akasin haka, dukka ya tattara ya hada ya yi tagumi yana kallon su. Duk sukai shiru suna kallon shi yace "Aba mai unguwa matarsa su tafi."
Kuka Maman Ladi ta sa tana fadin" Wallahi bazan yarda diyata taje gidan shi ba, domin da farko ai basu fadamin gaskiya duk munafukai ne."
Tsawa ya daka mata ta yi shiru tana kallon shi. Ya yi musu dogon sharhi kan boye mata da suka yi sannan ya yi umarnin Maman Ladi da sauran duk zasu bada dari biyar-biyar na dukan mai unguwa da Maimounath kudin magani. Haka suka bayar suna Allah ya isa a zuci. Haka ya dinga musu nasiha yana ankarar dasu illar abun da suke yi, daga bisani ya sallame su suka fito. Maman Ladi na kuka Ladi nayi suka rabo ta hau mashin din mai unguwa suka tafi. Su kuma matan gidan da 'yan biki ko wacce ta yi hanyar gidan ta.
Maman Ladi na koma wa ta dinga rabawa 'yan gidan duk kayan bikin data hada tana cewa "Wallahi dana kai gidan mai unguwa gara na zubar dashi." Ta kira almajirai ta dinga rabo.
*GIDAN MAI UNGUWA*
Yana tsayar da mashin ta sauka ta tirje taki shiga, juyin duniya Ladi taki shiga gidan. Mai unguwa ya fusata ya dinga zaginta. Hayaniyarshi ta sanya matan lekowa jin yana surfa zagi, aikuwa ganin Ladi tsaye kikam kamar gunki yasa Jummai dauko mayafi ta fito,tana zuwa ta riko hannun Ladi, aikuwa bata yi gardama ba ta bita suka shiga gidan.
Takaicin hakan yasa mai unguwa gunduma musu ashar yana cewa"Ban aurota don ku zauna da ita ba, billahillazi kar wacce ta koya mata bakin hali." basu kula shi ba suka shige dak'in Jummai dukkansu.
Zaunar da Ladi ta yi tana rarrashi Hannatu ta debo mata abinci suka saka ta gaba suna ta bata hakuri. Da kyar ta yi shiru yana ajiyar zuciya taci abincin tasha ruwa ta haye gadon Jummai ta kwanta. Kallon juna suka yi Hannatu tace "To yanzu ya zaki yi taje dak'inta?, kuma fa dak'in ba komai basu kawo kaya ba."
"Barni dashi Hannatu zai gane kuranshi ya sake ya shigo da sunan tafiya da yarinyar nan dak'inta."
Duk suka zauna suna dakon zuwan mai unguwa, kamar ya sani kuwa yaki zuwa ya shige dak'i ya kwanta yana jinyar jikin shi.
*WASHEGARI GIDAN HAYA*
Maman Ladi ta tashi zuciya tunkushe da bakin ciki, ta kira Inno tace "Inno ki kwashe kayan gadon nan ki siyar dasu ki ban kudina ko nawane gara nayi asara dana kai ma mai unguwa."
"Haba Maman Ladi kiyi domin diyar ki mana, kinsan dai mai unguwa bazai kula da ita yanda ya dace ba, kiyi hakuri ki kai mata."
Shiru Maman Ladi ta yi tana tunani, can tace "Shikenan ku shirya kukai kayan to." ta shige dak'i. Gyada kai Inno ta yi domin ta tausaya wa Ladi da auren mai unguwa dama dan basu san waye angon ba yasa suke bakin ciki.
Haka kuwa rana na yi aka kwashe kaya sai gidan mai unguwa.