← Book details Yan Gidan Haya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 10

Sashe 7

Yan Gidan Haya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana fita Ladidi tace" Tabdijam! Kunga atamfar da Inno ta saka kuwa?"
"Uhm Ladidi aini mamaki ya hanani magana, yaushe Inno ta yi kudin siyan wannan atamfa?" cewar Inna Talatu tana tafa hannu.

Shewa Mairon Ado tasa suka tafa da k'awarta Abule da suke zaune kullum tare. Tace "Mijinta ya siya mata ai tun wancan watan ta nuna min."
"Kwarankwatsi bari yallabai dawo dole nima ya siyamin."Ladidi ce ke wannan magana.

" Ayerere ina mijin ki yaga kudin siyan wannan atamfa?"
"Haba Maman Ladi wallahi kinsan dai yafi mijin Inno samun kudi."
"Amma bai fi shi zuciya ba ko?"Mairon Ado ta tambaya.

A hasale Ladidi ta juyo tana kumfar baki "Ke Mairo idan ina magana ki daina saka min baki kwarankwatsi kona miki shegen duka."
"Da shike an hwadi miki ina barin ki ki taba Mairo kawata ko?" Abule ta fadi tana hararar Ladidi.

Maman Ladi ta yi dariya tace "A'a fa dama kwana biyu mai unguwa bai shigo ba, da alama yau zai shigo."

Dariya suka sanya dukkansu sanin cewa ko wacce da tanadin dake ranta game da mai unguwa.
" Inno ta saka atamfa mai tsada, idan kuna da zuciya gobe kuma ku siya."cewar matar Malam dake fitowa daga dak'inta.
"Fadi ma mai zuciya zuwa biki ba mai abun kai wa ba matar Malam, domin ina da kudin da zan siya sofa waz wallahi."cewar Maman Ladi don tasan da ita matar Malam take.

Dariya ta kama Inna Talatu ta dinga yi, suna ta kallon ta har ta tsagaita tace "wallahi Maman Ladi kina burgeni super wax ake cewa fa ba sofa waz ba"
"Yo sai me dan ban iya fadi ba, na dai san nafi wasu kidahuman."

Nan ko wacce ta daure fuska, ita kuma Inna Talatu ta dinga dariya tana tsugunne kusa da injinta.

"Mairon Ado hala ke baki taba yin boko bane?"
"Babana ya hanani matar Malam, da yanzu na wuce wulakanci."
"Ke Mairo walle ni kuwa nayi boko har aji biyu walle kafun ankayi mun amre da Haladu."
"Iyye ashe Abule anyi boko har aji biyu?" Inna Talatu na dariya.

"Talatu zanci ubanki idan baki daina ma mutane dariya ba, matsiyaciya kawai kin tasa mu gaba kina dariya kamar wacce hau ya hau kanta." cewar Maman Ladi.
"Banda zagin iyayena Maman Ladi bana san wulakanci."
"Na zage ki din, ko za ki rama ne Talatu?"

"Ku dakata haka, abun raha ne ba fad'a ba sababbu."cewar Ladidi.
"Ina raha anan Ladidi ana zagin iyayen ka?"
"Abar maganar haka don Allah ya wuce babu fad'a."

Haka kuwa ko wacce ta kama aikin ta.

*GIDAN MAI UNGUWA*

Yana zaune kofar gida ya yi tagumi. Abokin shi malam Kallah yazo ya zauna kusa dashi yana fadin "Ranka-ya-dade fatan dai lafiya kayi tagumi haka?"
"Ina fa lafiya Kallah?"
"Ashsha Allah ya sauwaka, mai ya faru?"
"Wato Kallah idan Allah ya baka mata irin nawa, na tabbata mutuwa zaka yi."
"To babbar magana kenan dai mata ne suka tasa ka gaba Ranka-ya-dade?"
"Kwarai kuwa matan gidana Jummala da Hannatu duk munafukai ne, don yanzu zakai fad'a da wannan idan kaje wurin dayar to billahillazi ita ma fad'a zaku yi."
"toh na gane, kenan sun hade kai?"
"Kamar kashin awaki kuwa."
"wannan ai abune mai sauki, kawai aure zaka kara."

Da sauri mai unguwa ya dubi shi yana zare idanu "Aure fa kace Kallamu?"
"Kwarai kuwa aure zaka kara, kuma yarinya zaka auro."

Shiru mai unguwa ya yi can kuma yace "To ina zan samu matar auren Kallamu idon gari?"
"Don wannan ai mai sauki ne, Ladi kawai zaka samu ka aure ta."
"Wacece Ladi kuma?"
"Diyar Maman Ladi ta gidan 'yan haya."

Zabura mai unguwa ya yi yace "Kallamu baka kaunar farin ciki na billahillazi, ban da haka ta ina zaka hadani da wannan matar mai kirar samudawa kace na aure diyarta?, matar da ko mutuncina bata gani?"

Kallah ya dubi mai unguwa yana dariya" Ranka-ya-dade ai uban yarinyar yana iya komai kan kudi"
"Kenan zai bada diyarsa don kudi?"
"Na rantse maka zai bayar, amma ga wata shawara." ya matsa sosai kusa da mai unguwa sukai kus-kus, dariya suka sanya. Mai unguwa na fadin "Haka za a yi Kallah shawara mai kyau, nagode sosai Kallamu idon gari zan same ka gobe."
"To Allah ya kaimu."

Sukai sallama ya wuce, shi kuma mai unguwa ya shiga gida cike da farin ciki.

*Tabdijam! Wata sabuwa kenan, muje zuwa..*

*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:45 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱

. 👨🏻‍💻👩🏻‍💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.

©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼

Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*

📚 ​​Zaku iya samun littafan mu a Facebook​​ 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 ​​Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu​​ 👇🏽
[email protected]

Dedicated to
*GSS Dr. Ahmad makarki hayin Banki kawo. Ina mutukar alfahari daku sosai duk inda kuke, Allah ya kara ilmi. One love 2013*

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*

*55~60*

Mai unguwa na shiga gida ya nemi wuri kan turmi ya zauna, yana cika yana batsewa shi ga mai gida sai zare ido yake. Ya dubi matan ba wacce ta kalle shi ya yi kwafa yace "Na kusa kawo karshen wulakanci a gidan nan."

Babu wacce ta kalle shi sai aikin su suke ta yi.

" Jummala zan kara aure kwananan nan billahillazi."

Duk suka kalle shi cike da farin ciki kwance kan fuskar su, Hannatu tace "Kai amma naji dadi wallahi, yaushe ne bikin Malam?"

Harara ya daka mata" Munafuka mai bakin hali kawai, harda murna ko?, to billahillazi ba da wasa nake ba."
"Malam ai murna muke yi zaka kara aure shiyasa muke tambaya." cewar Jummai.
"Lallai matan nan iyayen ku sun koya muku mugun hali, inace idan za ayi ma mace kishiya haushi take jin, amma ku don tsabar algungumai ne wai murna kuke ko?"
"Malam kenan mai hali bai canzawa."
"Ke Jummala alqur'an ki fita idona, bazan canza halin ba inga uban da zai can zani."
"Allah ya baka hakuri." ta shige dak'i, ganin haka Hannatu ma ta shige dak'i tana hararar shi.

"Duk zaku gane kuranku billahillazi bari na auro yarinya danya sharkaf ku gani." ya kakkabe rigarsa ya fice daga gidan yana sababi.

*CIKIN GIDAN 'YAN HAYA*

Kwana biyu anyi sauki da fad'a, ana zaman lafiya gidan yasha iska. Ko wacce na sana'arta cikin lumana, mazan su na cikin kwanciyar hankali.

Gashi an fara wahalar ruwa kuma babu na fanfo, da kyar ake samu a rijiya. Da asubar fari suke rige-rigen fitowa dibar ruwa a rijiyar, kowa na kokarin ya ri ga wani diba, idan ka ri ga tashi ka diba sai a dinga hararar ka ana yada habaici.

Yau duk suna dak'i basu fito ba, sai matar Malam tana zaune tana wanke-wanke hanyar fanfo ita kadai, kawai taga an kawo ruwan fanfo. Da sauri ta karasa ta kashe fanfo tana waige kar wani ya ganta, ta ruga dak'i ta kwaso robobinta masu yawa ta nufi fanfo. Ta dinga tarawa tana cikawa. Jin karar zuban ruwa yasa Maman Dare lekowa, aikuwa tana ganin ruwan fanfo ne ta koma dak'i da sauri ita ma ta debo kayanta harda tukwane ta nufi fanfo, daga ita sai matar Malam ke jidar ruwa suna kai wa dak'i.

Abule ta fito zata bandaki ita ma taga wannan al'amari, amma maimakon ta yi yanda sauran suka yi na yin shiru, it kurma guda ta yi tana sanar da mutan gidan an kawo ruwan fanfo. Da sauri suka dinga fitowa da manyan robobi suna rige-rigen bin layi. Haushi ya kama Maman Dare ganin gayyar da Abule ta yi musu tace "Shegiya mai hankali a hannun riga." matar Malam ta fashe da dariya "Banza ce ai bata da nutsuwa."

Ba wacce ta kula su, kowa so yake ya samu ruwa. Maman Ladi ta ga alamun za a raina mata hankali ganin harda tukunya ake diban ruwa, gashi bata da ruwan ko kadan dan haka tace "Yakama ta kusan me kuke yi, kubari muma mu diba gaskiya."
"Maman Ladi a dai bi layi sannu a hankali zamu samu." cewar Inno.
"A'a Inno duba fa ki gani harda tukwane dan bakin ciki ake dibar ruwa."
"An saka ayi yanda za ayi damu." cewar matar Malam.

Shiru Maman Ladi da Inno suka yi basu kara magana ba, ganin Iya beji na hararar matar Malam. Can dai da suka ga zasu iya rasa ruwan, Iya beji ta kutsa ta warce tukunyar hannun Maman Dare ta yi jifa dashi ta aza nata robar. Maman Dare ta kalle ta ta kalli tukunyarta dake yashe a kasa tace " iya beji nawane fa bana matar Malam ba kika yadda."

*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:45 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱

. 👨🏻‍💻👩🏻‍💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.

©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼

Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*

📚 ​​Zaku iya samun littafan mu a Facebook​​ 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 ​​Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu​​ 👇🏽
[email protected]

*Wannan shafin na kune hazikan masana, jagororin adabi, _MARUBUTA GROUP_ gaskiya bani da group a whatsapp dake ilmantar da al'umma da kuma koyar da zallar adabi irin ku, ina alfahari daku a kodayaushe fatan alheri ga ilahirin al'ummar wannan gida, Allah ya kara daukaka ya bar zumunci mun gode.*

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*

*60~65*

Harara Iya beji ta zabga nata, "Ai nasan na kine shiyasa na yarda shi."

"Lallai ma Iya beji, mun ri ga ki zuwa layi ai." cewar Inno.
"Baku damu ku samu ruwa ba, ai wuri kuka samu ku ka tsaya."
"Dalla can matsa min." Maman Ladi ta bige robar hannun Iya beji ruwan y zube, ta sanya nata robar.
Chapter 7 · 0% Book details