← Book details Yan Gidan Haya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 10

Sashe 8

Yan Gidan Haya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haushi ya kama Iya beji ita ma ta kifar da ruwan Maman Ladi. Nan fa fad'a ya kaure tsakanin su, Abule ganin yawanci hankalin su na wurin rabon fad'a yasa ta dinga jidar ruwan tana kaiwa dak'i. Maman Dare ta yi dariya ita ma rabi sahun Abule, lura da hakan da Inna Talatu ta yi ne yasa ita ma ta tara robarta bakin fanfo, aikuwa Matar Malam ta kifar da shi tana fadin"Algungumai kun wani zo kuna jidar ruwa kamar.." Mari aka sauke mata wanda ya tilasta mata yin shiru. Inna Talatu ce rike da robarta tsaye tana hararar matar Malam, "Kece dai algunguma bani ba, banza kawai mai halin matsiyata."
"Talatu ni kika mara?"
"Kina da abun yi ne?"

Haba sai fada kuma ya tsarke, suna yi suna jifar juna da robobin ruwa. Maman Ladi ta yarda Iya beji kasa gashi wurin duk ruwa ne, aikuwa ta bugu sosai ta kasa tashi. Maman Dare nasan shiga kuma tana tsoro don haka ta je taimakon daga Iya beji wanda ya yi dai-dai da Matar Malam ta jeho bokitin karfe ya sauka kuwa kan Maman Dare ta zube kasa jikin Iya beji. Kuka Iya beji tasa tana tsine masu Maman Ladi, da kyar Maman Dare to mike tana dafe da kanta ta taimaka ma Iya beji ta mike.

Hayaniya da fad'a sosai suke yi a bakin fanfo. Shigowar Malam Lawal mijin Maman Ladi ne ya sanya Maman Ladi barin wurin da sauri ganin shi da manyan ledoji a hannu, ta amsa tana mai sannu da zuwa. Washe baki ya yi yace " ke kam kin iya haihuwa wallahi, wannan arzikin duk dalilin haihuwa ne."ya fadi tare da shigewa dak'i.

Gudar da Maman Ladi tasa ce ta dakatar da fad'an da matan gidan ke yi, suka juyo suna kallonta. Yara suka dinga shigowa da kayan abinci suna zubewa kofar Maman Ladi.

Ladidi ta karaso tana fadin " Maman Ladi wannan kayan fa?"
"Ahayye duniya Ladidi gulma, to bari naje dak'i na tambayi wanda ya kawo sai nazo na baki satonri (story)" ta shiga dak'i ta same shi.

"Baban Ladi ina ka samu kaya haka?"
"Kedai bari uwargida kayan toshen Ladi ne, wani attajiri ya ganta shine dazu y kirani ya ban wa'innan kayan."ya fadi yana kirgo kudi a aljihun 'yan dari biyu. Maman Ladi t warce kudin tana cewa"Wannan rabo na ne kenan ko?, nasan dai an baka naka."
"Kayya Maman Ladi kina da gajen hakuri baki zanyi dama wallahi, yanzu yaushe zamu sanya bikin?"
"Sati biyu kawai za a saka saboda mahassada malam."cewar Maman Ladi.
Gyada kai ya yi yana gyara aljihun shi wanda ke damke da kudi.

Galala matan gidan ke bin kayan da kallo kamar makafi sun warke makanta, nan suka fara kus-kus aka manta da batun fad'an ruwa. Fitowar Maman Ladi daga dak'i tana washe jajayen hakoranta yasa suka marmatso kusa da ita domin jin kanun labarai.

"Ladi ce zata auri wani attajiri shine aka kawo wa'innan kayan, ku duba harda su buhun shinkafar waina wallahi na samu karin jari."

"Yanzu Ladi nawa take da zaki aurar da ita?"
"A'a Talatu kardai kina bakin ciki kan wannan abun arzikin dana samu ne?"
"To wani mai arziki kenan zata aura?" matar Malam ta yi tambayar.
"Sai ranar auren zaku sani, nan da kwana goma sha hudi zaa yi bikin."

Nan aka dinga cafta ana duba kayan arziki, Inno da Inna Talatu muraran suke nuna bakin ciki kan kayan, yayin da Maman Dare wacce har gefen goshinta ya kumbura sanadin wannan bokiti ke nuna ma Maman Ladi illar auran. Iya beji dama data samu ta tashi dak'i ta wuce da alwashin sai ta rama.

Maman Ladi kuwa sai rawar kai take tana nuna isa da takama diyarta zata aure mai arziki.

*MAI UNGUWA*

Matan mai unguwa sai murna suke ganin ana gyara dak'in amarya, suna fatan zasu huta da wannan masifar tashi. Sun tambayeshi wacece amaryar yaki fadi musu wai kada suje suyi mai munafuncin da suka saba, shiyasa suka saka mai idanu suna kallon duk abun da yake yi.

Mai unguwa zaune a cikin zaure tare da Baban Ladi.

"Kai Lawal nawa ne sadakin?, sannan ka tabbata wannan shegiyar matar taka bata san ni zan auri diyarta ba." cewar mai unguwa.
"Ka bada jaka goma Ranka-ya-dade, kuma na rantse maka bata sani ba ce mata nayi wani attajiri ne."

Haka ya kirga ya mika yana washe baki ya kusa zama ango.

Shikuma Malam Lawal gida y nufa ya damka ma Maman Ladi kudin sadakin, ita kuma ta mika ma Inno dillaliya data kawo mata kayan gado da dorowa. Ana ta shirye-shiryen aure sai gyara amarya Maman Ladi take, yayin da matan gidan wasu ke bakin ciki wasu kuma suna taya ta murna.

Sosai Maman Ladi ta shirya ma wannan aure ganin kudin sadaki jaka goma wanda a tarihin unguwar ba wanda aka taba ba irin wannan kudin matsayin sadaki. Hidima sosai matan gidan ke ta yata kama daga kan alkaki, dubulan, nakiya, da sauransu.
*RANAR AURE*

Ranar gidan 'yan haya ya cika sosai, domin gayyata Maman Ladi ta yi na auren tilon diyarta. A nata hidimar girki, amarya ansha atamfar batik cikin kayan auren da mai unguwa ya aiko.

Karfe biyu aka daura auren Zainab wato Ladi da ango Nasiru Tanko mai unguwa.

Maman Ladi anci kwalliya ana tsakiyar jama'a wannan sakon the isketa, a hargitse take tambayar "wani mai unguwa aka ba auren Ladi?"
"Wanne kuwa bayan mai unguwa Tanko."cewar Inna Talatu dake tsaye bakin kofa.

Ai a tamanin Maman Ladi ta fito tana kwallo da duk abun da tagani a hanya, tamkar zararra tana kwalla kiran sunan Baban Ladi. Mutane da aka gayyata suka dinga kallonta domin basu san komai ba, matan gidan kuwa sai yamadidi suke da ita suna dariya.

Shigowar su kenan daga wurin daurin mazan gidan, Baban Ladi na gaba suna biye dashi a baya.
Yana sako kai yaji an shake shi sosai ba da wasa ba, kokari yake ya ya kece daga rikon amma ya kasa. Maman Ladi data yi shakar ta wanke shi da mari tana fadin " munafuki macuci kace min wani attajiri zai auri Ladi, ashe wancan shegen ne to wallahi sai an warware auren nan muddin kana bidar zaman lafiya dani."

Juya kai kawai yake yana kokarin kwace wa daga rikonta, mazan nata aikin bada hakuri inda matan dake wurin suka maidata tamkar talabijin suna ganin ikon Allah.

Da kyar ta sake shi, aikuwa yana jin yasha ya sa kafa sai hanyar waje yana fadin "Na rantse da Allah aure ya auru naga uban da zai kwance shi mahaukaciya kawai."
" Zaka dawo ai wallahi zaka san da Hajara uwar Ladi ka yi a gidan nan".

*INA LABARIN ANGO MAI UNGUWA TANKO??*

*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:45 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱

. 👨🏻‍💻👩🏻‍💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*

​​Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร​.

©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼

Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*

📚 ​​Zaku iya samun littafan mu a Facebook​​ 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION

📩 ​​Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu​​ 👇🏽
[email protected]

No matter the Distance between
Us.. I am as Close To U today
As I was Yesterday.. For as
Long As U are In my Heart..
We are Never Truely Far Apart.! I love you fan's of 'YAN GIDAN HAYA. One love to you.

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*

*65~70*

*GIDAN MAI UNGUWA*

Suna zaune suna hira da yaran su da makota da suka zo biki. Lado ya shigo yana sharce zufa ranshi a hade yace "Mama zo kiji wai diyar gidan haya baba ya aura."

Salati Hannatu ta sanya tana dafe kirji" Diyar gidan haya fa kace Lado?"
"Wallahi ita ce ya aura wannan yarinya karama da ita, wacce wallahi ko ni ta yimin kankanta da aure wai ita baba ya aura."

Zugum suka yi suna jimamin wannan masifa da mai unguwa ya kwaso musu. Sai gashi ya shigo yana saba babbar riga, yasha fararen kaya yana ta bude hakora. Makota sukai mishi fatan alheri suka fita. Ya kalle su yanda duk sukai shiru kamar masu zaman makoki yace "Lafiya kuwa kuke zaune da tagumi kamar ance iyayen ku sun mutu?"

Cikin takaici Hannatu tace " cewa akayi mai unguwa Tanko ya mutu shine muke jimami."
"Ubankine ya mutu billahillazi bani ba, munafukai kawai duk kishi ne na sani."

Jummai ta kalli yanda yaran ke zaune rai a hade tace" Ko wacce ta wuce gidanta, kuma ku tafi wurin sana'ar ku an gama taro."

"Allah sarki Jummala ayi hakuri dai aure ne nariga nayi ko da taro ko babu taro sai amarya tazo." ya fice daga gidan.

Haka kuwa yaran jiki a sabule suka yi musu sallama duk suka fita. Suka bar iyayen cikin jimamin wacce mai unguwa ya debo musu matsayin kishiya.

Yana fita ya hadu da da baban Ladi yana haki kamar dan tsere.

"Kai Lawal meye haka kake ta haki, lafiya dai ko?"
"Ina lafiya Ranka-ya-dade Maman Ladi ta gane kai ne mijin, tace wallahi ba zata bada amarya ba."

Shekeke mai unguwa ya bishi da kallo "Yo ita shegiyar matar taka an gaya mata tana da ikon kan matar dana biya sadaki ne?, to billahillazi ka koma ka fada mata anjima a bani amaryata ko wallahi taga kalar nawa haukan, banzaye bayan na biya kudi na sai ace za'ayi min iko."
"Ranka-ya-dade wallahi shakeni ta yi bazan iya komawa ba."
"Aikuwa zata san waye Tanko billahillazi a garin nan." ya shige gida a fusace.

*CIKIN GIDAN HAYA*

Maman Ladi da 'yan korenta zaune kofar dak'inta, suna kara zugata kan kada t yarda akai diyarta gidan mai unguwa.
"Nifa da hankali na wallahi bazan ba Tanko Ladi ba, kuma yazo ya gani."
"Wallahi Maman Ladi gidan shi babu abinci, babu suturar arziki."cewar Ladidi.
"Nifa nasan waye Tanko, domin munyi artabu da shi watarana ana fad'a gidan mu yazo rabo y dinga tsine mana" cewar wata kawar Maman Ladi mai suna Atuwa.

"Ayererre a dade anayi, aure dai the auro dole a ba Tanko matarsa."
"Ke Talatu wallahi ko Ubankine bazan bayar ba, kuma ki daina shiga sabgata Maman Ladi nake."
"Aifa yau ko uwata zaki zaga bazan damu ba ai dama duk wanda y shiga motar kwadayi yasan inda zata kaishi."
Chapter 8 · 0% Book details