Sashe 10
Yan Gidan Haya Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read
*LADI GIDAN MAI UNGUWA*
Da safe suka tashi suka fara ayyukansu, Ladi nata baccin gajiya har suka gama hadin karin safe. Hannatu t taso ta, aikuwa t sanya kuka ita gida zata je, da kyar suka samu ta yi shiru t zauna suka kar ya. Mai unguwa na jinsu yana kwance dak'i duk jikin shi ciwo yake domin yaci duka ba kadan ba.
Suka zauna suna da janta da hira har ta sake dasu. Mai kura ya yi sallama suka shigo tare dasu Inno da Ladidi, Abule, Maman Dare, Maman Akintola, Inna Talatu, matar Malam da sauran matan gidan d makota.
Nan su Jummai suka yi musu tarba ta mutunci, mai kura ya jide musu kayan suka hau shiryawa. Ladi t dinga yi musu kuka tana cewa su tafi da ita. Hakuri suka dinga bata Maman Akintola tace " Ladi kana da iyaye fa a gida na me anguwa kayi hakuri kawai ka zona kaji ko." ta gyada mata kai tana kuka har suka gama jere suka tafi. Mai unguwa na dak'i yaki fitowa yana kunyar ya yi ido biyu dasu saboda dukan da ya sha jiya, sai da suka tafi sannan y fito yana hura hanci.
Yace"Jummala ruwan wanka"
"Babu." ta fadi a takaice.
"Allah ya hana ki muguwa kawai." ya fice yana hararar Ladi.
Nan Jummai ta dinga rarrashe tana nuna mata ta yi biyayya zata ji dadin zama tare dasu, ta gyada mata kai tana kuka suka shigar da ita dak'inta.
*'YAN GIDAN HAYA*
Suka koma suna bata labarin matan mai unguwa sun rike Ladi kamar yarsu, wannan yasa Maman Ladi ta saki ranta domin tasan matan nada mutunci ba kamar shi ba. Hankalinta ya dan kwanta ta rage fargabar diyarta zata cutu gidan mai unguwa. Mijin kuwa tun ranar bai dawo ba sai yau, ko kallon shi bata yi ba.
*Ya ya zaman Ladi zai kasance da mai unguwa kenan??*
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:45 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱
. 👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
_ALHAMDULILLAH SADAUKARWA GA DAUKACIN AHALIN ALHAJI ABUBAKAR SA'EED ARDO BORO, UBANGIJI YA TSARE MU YA KARE MU GA SHARRIN MAKIYA, ALLAH YA SHIRYA MANA ZURI'A DAYYIBA AMEEN._
🌹 *BAMU DACE DA JUNA BA*🌹
_UMMU BASHER_
*Allah sarki wasu iyayen basu san cewa kwanciyar hankali yafi kudi ba, shiyasa suke ganin 'ya'yansu sunfi karfin talaka. Amma ga Ummu basher ta fada mana cewa zaman lafiya, kwanciyar hankali, soyayya da sauransu duk ana samu koda babu kudi, zaa dace da juna. ina taya ki murna na kammala wannan littafi k'awas, Allah ya kara basira da zakin hannu hade da kwarin idanu. Ina yinki sosai dinnan. Muna biye a DANA SANI*
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
_Ma cherie ta mai unguwa Tanko ina kika kai mana SAADAT angon BUSHRA, kina kamshi muna miki feshin humra tawan more grease._
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*80~End*
Sosai gidan 'yan haya fad'a ya yi sauki, ko wacce na kokarin kare martabar sana'arta tun bayan dawowar Maman Usman taji duk abun da ya faru, nan ta nuna musu cewa muddin suna da sana'ar yi to ba zasu kasance suna ganin bakin juna ba. Hakan yasa suka dage kowa ya kama sana'a suna kuma kokarin ganin an zauna lafiya. Bata taba kai ma diyarta ziyara ba, sai dai tana samun labarinta wurin kawayenta.
*GIDAN MAI UNGUWA*
Sosai suka rike amanar Ladi, kasancewar yarinyar tana yi musu biyayya ta shammace su basu yi tsammanin zata yi hakuri ba duba da halayya ta gidan data fito. Suna kare ta sosai don ganin mai unguwa baici zarafinta ba, sun yarda duk abun da zai ma ta ya yi musu gudun magana cikin gari.
Sun hada kai suna ganinta kamar yaran su mata dake gidan aure.mai unguwa ya yi jarabar ya yi masifar hadin kansu yaga basu da niyar canzawa, gashi duk abun da suka ce shi Ladi keyi don haka yasa musu ido kawai yana kallon su.
Lokaci yaja kwanaki sun shude haka satittika haka watanni yau Ladi watan ta biyar gidan mai unguwa ba tare da taje gida ba. don haka yau take ta zumudin zuwa gidan su. Ta gama shiryawa ta fito da mayafinta a hannu tace"Maman Sani zan tafi."
"Lallai Ladi da safiyar nan zaki tafi?"
Rau-rau ta yi da ido kamar zata yi kuka tace"Maman Sani ina son ganin Mamana fa."
Dariya suka yi suna tsokanar ta ganin zata yi kuka. Da sauri mai unguwa ya fito yana gyara mashin dinshi yace " ke zo mu tafi ki bar wa'innan matan."
"To a dawo lafiya Ladi a gaida gida."
"Insha Allah za suji." ta fita suka tafi.
*GIDAN 'YAN HAYA*
Maman Usman na zaune cikin su suna hira, sai nishadi suke kamar basu ba. Maman Akintola tace " wallahi gida namu ya yi dadi fa kowa ya yi shiru ya yi hakuri kome ya wuce."
Suka sa dariya dukkan su, sai jin sallamar Ladi suka yi. Da gudu ta shigo ta rungume uwar sai kuma tasa kuka. Maman Ladi murna Sosai ta yi na ganin Ladi tace" To rigimatu kukan na menene?"
"Mama baki taba zuwa gidana ba."
Duk matan gidan sukai dariya, Maman Usman tace " Ladi sai kuma aga Maman ki gidan ki ba kunya ko?, kamar ba diyar fari ba."
"Kai mama kema sau daya kika je ai."
"To zan dinga zuwa kullum." ta fadi tana dariya.
Ladi ta rufe ido da hannayenta tace "Yana waje fa tare muke dashi."
Rankwashi matar Malam ta sakar mata akai" Ja'ira shine tun dazu baki fadi ba kika zauna shagwaba?"
Da sauri Maman Usman ta dauko tabarma ta shimfida tace "Maza jeki shigo dashi."
Tare suka dawo sai sunkuyar da kai yake yi alamun kunya, domin ya tuna abubuwa da yawa da ya faru cikin wannan gida, gashi kuma yau ya shigo matsayin sirikin su. Ya nemi wuri ya zauna, Ladidi ta kawo mai ruwa, matar Malam ta kawo mai fura. Suka zauna suna gaisawa a kunya ce.
Bayan sun gama gaisawa suka zauna.
Maman Usman tace "Alhamdulillah nayi farin ciki ganin wannan rana, domin ada can ba muyi tsammanin abu makamancin wannan ba, mai unguwa matsayin suriki cikin gidan haya. Lallai abun mamaki ne sosai da hakan ya faru amma sai gashi sanadin haka zaman lafiya da fahimtar juna ya dore tsakanin mu, ina fatan zamu kasance masu hakuri mu jure neman na kanmu mu guje ma rigima da tashin-tashina."
"Kwarai hakane Maman Usman domin kin dade kina nusar damu illar fad'a cikin gidan nan, amma bamu dai na ba sai gashi tun bayan auren Ladi da mai unguwa zaman lafiya yazo ya daure sosai, Allah yasa mu kasance koyaushe haka." cewar Inna Talatu.
Maman Ladi ta yi ajiyar zuciya tace "Gaskiya munyi zaman rashin hakuri da junan mu, mun kasance masu biye ma zuciya da rashin sanin meke mana ciwo muna fad'a da junan mu alhali Allah ya ri ga ya kaddara zaman mu tare, musamman ni na kasance mai daukar duk abun da diyata ta fadamin game da mutanen gidan nan koda bana nan, sai dai abun farin ciki shine bata dauki wannan hali taje gidan miji dashi ba, ina kira ga iyaye dasu dinga kwabar ya'yansu kan maganganu, su daina yarda da maganar yara koda suna tunanin gaskiya ce. ina fatan zamu yi hakuri mu kasance masu yafiya mu zauna lafiya."
"Gaskiya ne Maman Ladi mun kasance masu kyashi da hassada, mun dauki mugun hali na fad'a da juna mun yafa, mun tsane junan mu kan bambamcin ra'ayi, ina fatan zamu cire kyashi a ranmu mu rungume zaman lafiya." cewar Ladidi.
Maman Dare ta yi dariya tace "To a madadin yan'uwana da basa jin hausa sosai, muna mika namu hakurin gare ku da fatan zamu cigaba da kasance wa cikin farin ciki da zama lafiya gaba dayan mu duk kuwa da bambanci yare da addini da muke dashi."
" Tabbas auratayya na daya daga cikin abun da ke haddasa zaman lafiya, domin sanadin auratayya ne zaman lafiya da farin ciki suka wanzu cikin gidan nan, ina fatan kowa zai maida hankali wurin bada aure tsakanin al'umma domin hakan na bada gudunmawar zaman lafiya." cewar Inna Talatu.
Mai unguwa ya kalle su yace " Lallai haka ne maganar ku gaskiya ce, domin dukkan mu masu laifi ne, mun kasance mutane marasa hakuri a rayuwa, komai muna sanya ido kanshi, mun kasance mutane masu addini da ban da kuma harshe wanda mu kammu muka kasa hade kai mu zauna lafiya, amma ina fatan yanzu zamu yi hakuri mu duba akasin da muka fuskanta a baya mu hadu mu gyara da kanmu. Mu gudu tare mu tsira tare domin zaman lafiya yafi zama dan sarki."
Kowa ya yi na'am da zancen su aka hadu aka nemi yafiyar juna aka yi addua aka tashi. Mai unguwa ya yi musu sallama ya dau matarsa suka wuce gida cikin farin ciki da annashuwa.
*GIDAN MAI UNGUWA*
Bayan sun dawo aka zauna hira bayan magriba. Mai unguwa yace " Ina fatan zaku yi hakuri da halina muci gaba da zaman lafiya daku, kuyi hakuri ku yafe min duk abun da nayi muku."
Cikin farin ciki suka dinga murna suna jin dadin canjin da aka samu daga mai gidan nasu.
Rayuwa kenan yau mai unguwa ne ya bada ijiyar mabudin rumbu a hannun matanshi saboda tsananin zaman lafiya.
Yau gashi duk sun fahimci juna sun yanke duk wani abu da zai haddasa masu rashin fahimta, sai fatan daurewar zaman lafiya.
Ina fatan madaukakin sarki Allah ya cigaba da zaunar damu lafiya, da kasar mu lafiya. Allah ya bamu ikon fahimtar amfanin zaman lafiya, mu rungume zaman lafiya fiye da tashin hankali mu hade kanmu cikin aminci da salama ameen.
Alhamdulillah tammat bihamdi, nan na kawo karshen wannan littafi na 'YAN GIDAN HAYA, ina fatan Kuskuren dake ciki ubangiji ya yafe mun, wanda nayi dai-dai Allah ya karbi niyyata na fadakar d al'umma muhimmancin zaman lafiya ya sanya muyi tarayya cikin ladan da dukkan masoya.
*Ina yi muku fatan alheri masoya duk inda kuke, Allah ya sada mu da alheri, na gode ma kowa da kowa duk masu jumurin bibiyar littafi na tunda ga kan BADDEEYERH, GIDAN MARAYU, SANADIN K'AWATA, SAI KUMA 'YAN GIDAN HAYA.*
*Ku kasance dani cikin TUSHE MAFARI domin yanzu wasan ya fara, tare da daukacin members dake rubutu kan _TUSHE MAFARI_ . Ga Fauziyya Lawal Ammany muna tafe muku da wani sabon littafi mai suna _BAHAGON TUNANI_ nan ba da dadewa ba insha Allah fans fatan alheri.*
_Allah ya daukaka zamani writers ya kara mana zumunci tsakanin mu ameen_
Da safe suka tashi suka fara ayyukansu, Ladi nata baccin gajiya har suka gama hadin karin safe. Hannatu t taso ta, aikuwa t sanya kuka ita gida zata je, da kyar suka samu ta yi shiru t zauna suka kar ya. Mai unguwa na jinsu yana kwance dak'i duk jikin shi ciwo yake domin yaci duka ba kadan ba.
Suka zauna suna da janta da hira har ta sake dasu. Mai kura ya yi sallama suka shigo tare dasu Inno da Ladidi, Abule, Maman Dare, Maman Akintola, Inna Talatu, matar Malam da sauran matan gidan d makota.
Nan su Jummai suka yi musu tarba ta mutunci, mai kura ya jide musu kayan suka hau shiryawa. Ladi t dinga yi musu kuka tana cewa su tafi da ita. Hakuri suka dinga bata Maman Akintola tace " Ladi kana da iyaye fa a gida na me anguwa kayi hakuri kawai ka zona kaji ko." ta gyada mata kai tana kuka har suka gama jere suka tafi. Mai unguwa na dak'i yaki fitowa yana kunyar ya yi ido biyu dasu saboda dukan da ya sha jiya, sai da suka tafi sannan y fito yana hura hanci.
Yace"Jummala ruwan wanka"
"Babu." ta fadi a takaice.
"Allah ya hana ki muguwa kawai." ya fice yana hararar Ladi.
Nan Jummai ta dinga rarrashe tana nuna mata ta yi biyayya zata ji dadin zama tare dasu, ta gyada mata kai tana kuka suka shigar da ita dak'inta.
*'YAN GIDAN HAYA*
Suka koma suna bata labarin matan mai unguwa sun rike Ladi kamar yarsu, wannan yasa Maman Ladi ta saki ranta domin tasan matan nada mutunci ba kamar shi ba. Hankalinta ya dan kwanta ta rage fargabar diyarta zata cutu gidan mai unguwa. Mijin kuwa tun ranar bai dawo ba sai yau, ko kallon shi bata yi ba.
*Ya ya zaman Ladi zai kasance da mai unguwa kenan??*
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:45 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱
. 👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
_ALHAMDULILLAH SADAUKARWA GA DAUKACIN AHALIN ALHAJI ABUBAKAR SA'EED ARDO BORO, UBANGIJI YA TSARE MU YA KARE MU GA SHARRIN MAKIYA, ALLAH YA SHIRYA MANA ZURI'A DAYYIBA AMEEN._
🌹 *BAMU DACE DA JUNA BA*🌹
_UMMU BASHER_
*Allah sarki wasu iyayen basu san cewa kwanciyar hankali yafi kudi ba, shiyasa suke ganin 'ya'yansu sunfi karfin talaka. Amma ga Ummu basher ta fada mana cewa zaman lafiya, kwanciyar hankali, soyayya da sauransu duk ana samu koda babu kudi, zaa dace da juna. ina taya ki murna na kammala wannan littafi k'awas, Allah ya kara basira da zakin hannu hade da kwarin idanu. Ina yinki sosai dinnan. Muna biye a DANA SANI*
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
_Ma cherie ta mai unguwa Tanko ina kika kai mana SAADAT angon BUSHRA, kina kamshi muna miki feshin humra tawan more grease._
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*80~End*
Sosai gidan 'yan haya fad'a ya yi sauki, ko wacce na kokarin kare martabar sana'arta tun bayan dawowar Maman Usman taji duk abun da ya faru, nan ta nuna musu cewa muddin suna da sana'ar yi to ba zasu kasance suna ganin bakin juna ba. Hakan yasa suka dage kowa ya kama sana'a suna kuma kokarin ganin an zauna lafiya. Bata taba kai ma diyarta ziyara ba, sai dai tana samun labarinta wurin kawayenta.
*GIDAN MAI UNGUWA*
Sosai suka rike amanar Ladi, kasancewar yarinyar tana yi musu biyayya ta shammace su basu yi tsammanin zata yi hakuri ba duba da halayya ta gidan data fito. Suna kare ta sosai don ganin mai unguwa baici zarafinta ba, sun yarda duk abun da zai ma ta ya yi musu gudun magana cikin gari.
Sun hada kai suna ganinta kamar yaran su mata dake gidan aure.mai unguwa ya yi jarabar ya yi masifar hadin kansu yaga basu da niyar canzawa, gashi duk abun da suka ce shi Ladi keyi don haka yasa musu ido kawai yana kallon su.
Lokaci yaja kwanaki sun shude haka satittika haka watanni yau Ladi watan ta biyar gidan mai unguwa ba tare da taje gida ba. don haka yau take ta zumudin zuwa gidan su. Ta gama shiryawa ta fito da mayafinta a hannu tace"Maman Sani zan tafi."
"Lallai Ladi da safiyar nan zaki tafi?"
Rau-rau ta yi da ido kamar zata yi kuka tace"Maman Sani ina son ganin Mamana fa."
Dariya suka yi suna tsokanar ta ganin zata yi kuka. Da sauri mai unguwa ya fito yana gyara mashin dinshi yace " ke zo mu tafi ki bar wa'innan matan."
"To a dawo lafiya Ladi a gaida gida."
"Insha Allah za suji." ta fita suka tafi.
*GIDAN 'YAN HAYA*
Maman Usman na zaune cikin su suna hira, sai nishadi suke kamar basu ba. Maman Akintola tace " wallahi gida namu ya yi dadi fa kowa ya yi shiru ya yi hakuri kome ya wuce."
Suka sa dariya dukkan su, sai jin sallamar Ladi suka yi. Da gudu ta shigo ta rungume uwar sai kuma tasa kuka. Maman Ladi murna Sosai ta yi na ganin Ladi tace" To rigimatu kukan na menene?"
"Mama baki taba zuwa gidana ba."
Duk matan gidan sukai dariya, Maman Usman tace " Ladi sai kuma aga Maman ki gidan ki ba kunya ko?, kamar ba diyar fari ba."
"Kai mama kema sau daya kika je ai."
"To zan dinga zuwa kullum." ta fadi tana dariya.
Ladi ta rufe ido da hannayenta tace "Yana waje fa tare muke dashi."
Rankwashi matar Malam ta sakar mata akai" Ja'ira shine tun dazu baki fadi ba kika zauna shagwaba?"
Da sauri Maman Usman ta dauko tabarma ta shimfida tace "Maza jeki shigo dashi."
Tare suka dawo sai sunkuyar da kai yake yi alamun kunya, domin ya tuna abubuwa da yawa da ya faru cikin wannan gida, gashi kuma yau ya shigo matsayin sirikin su. Ya nemi wuri ya zauna, Ladidi ta kawo mai ruwa, matar Malam ta kawo mai fura. Suka zauna suna gaisawa a kunya ce.
Bayan sun gama gaisawa suka zauna.
Maman Usman tace "Alhamdulillah nayi farin ciki ganin wannan rana, domin ada can ba muyi tsammanin abu makamancin wannan ba, mai unguwa matsayin suriki cikin gidan haya. Lallai abun mamaki ne sosai da hakan ya faru amma sai gashi sanadin haka zaman lafiya da fahimtar juna ya dore tsakanin mu, ina fatan zamu kasance masu hakuri mu jure neman na kanmu mu guje ma rigima da tashin-tashina."
"Kwarai hakane Maman Usman domin kin dade kina nusar damu illar fad'a cikin gidan nan, amma bamu dai na ba sai gashi tun bayan auren Ladi da mai unguwa zaman lafiya yazo ya daure sosai, Allah yasa mu kasance koyaushe haka." cewar Inna Talatu.
Maman Ladi ta yi ajiyar zuciya tace "Gaskiya munyi zaman rashin hakuri da junan mu, mun kasance masu biye ma zuciya da rashin sanin meke mana ciwo muna fad'a da junan mu alhali Allah ya ri ga ya kaddara zaman mu tare, musamman ni na kasance mai daukar duk abun da diyata ta fadamin game da mutanen gidan nan koda bana nan, sai dai abun farin ciki shine bata dauki wannan hali taje gidan miji dashi ba, ina kira ga iyaye dasu dinga kwabar ya'yansu kan maganganu, su daina yarda da maganar yara koda suna tunanin gaskiya ce. ina fatan zamu yi hakuri mu kasance masu yafiya mu zauna lafiya."
"Gaskiya ne Maman Ladi mun kasance masu kyashi da hassada, mun dauki mugun hali na fad'a da juna mun yafa, mun tsane junan mu kan bambamcin ra'ayi, ina fatan zamu cire kyashi a ranmu mu rungume zaman lafiya." cewar Ladidi.
Maman Dare ta yi dariya tace "To a madadin yan'uwana da basa jin hausa sosai, muna mika namu hakurin gare ku da fatan zamu cigaba da kasance wa cikin farin ciki da zama lafiya gaba dayan mu duk kuwa da bambanci yare da addini da muke dashi."
" Tabbas auratayya na daya daga cikin abun da ke haddasa zaman lafiya, domin sanadin auratayya ne zaman lafiya da farin ciki suka wanzu cikin gidan nan, ina fatan kowa zai maida hankali wurin bada aure tsakanin al'umma domin hakan na bada gudunmawar zaman lafiya." cewar Inna Talatu.
Mai unguwa ya kalle su yace " Lallai haka ne maganar ku gaskiya ce, domin dukkan mu masu laifi ne, mun kasance mutane marasa hakuri a rayuwa, komai muna sanya ido kanshi, mun kasance mutane masu addini da ban da kuma harshe wanda mu kammu muka kasa hade kai mu zauna lafiya, amma ina fatan yanzu zamu yi hakuri mu duba akasin da muka fuskanta a baya mu hadu mu gyara da kanmu. Mu gudu tare mu tsira tare domin zaman lafiya yafi zama dan sarki."
Kowa ya yi na'am da zancen su aka hadu aka nemi yafiyar juna aka yi addua aka tashi. Mai unguwa ya yi musu sallama ya dau matarsa suka wuce gida cikin farin ciki da annashuwa.
*GIDAN MAI UNGUWA*
Bayan sun dawo aka zauna hira bayan magriba. Mai unguwa yace " Ina fatan zaku yi hakuri da halina muci gaba da zaman lafiya daku, kuyi hakuri ku yafe min duk abun da nayi muku."
Cikin farin ciki suka dinga murna suna jin dadin canjin da aka samu daga mai gidan nasu.
Rayuwa kenan yau mai unguwa ne ya bada ijiyar mabudin rumbu a hannun matanshi saboda tsananin zaman lafiya.
Yau gashi duk sun fahimci juna sun yanke duk wani abu da zai haddasa masu rashin fahimta, sai fatan daurewar zaman lafiya.
Ina fatan madaukakin sarki Allah ya cigaba da zaunar damu lafiya, da kasar mu lafiya. Allah ya bamu ikon fahimtar amfanin zaman lafiya, mu rungume zaman lafiya fiye da tashin hankali mu hade kanmu cikin aminci da salama ameen.
Alhamdulillah tammat bihamdi, nan na kawo karshen wannan littafi na 'YAN GIDAN HAYA, ina fatan Kuskuren dake ciki ubangiji ya yafe mun, wanda nayi dai-dai Allah ya karbi niyyata na fadakar d al'umma muhimmancin zaman lafiya ya sanya muyi tarayya cikin ladan da dukkan masoya.
*Ina yi muku fatan alheri masoya duk inda kuke, Allah ya sada mu da alheri, na gode ma kowa da kowa duk masu jumurin bibiyar littafi na tunda ga kan BADDEEYERH, GIDAN MARAYU, SANADIN K'AWATA, SAI KUMA 'YAN GIDAN HAYA.*
*Ku kasance dani cikin TUSHE MAFARI domin yanzu wasan ya fara, tare da daukacin members dake rubutu kan _TUSHE MAFARI_ . Ga Fauziyya Lawal Ammany muna tafe muku da wani sabon littafi mai suna _BAHAGON TUNANI_ nan ba da dadewa ba insha Allah fans fatan alheri.*
_Allah ya daukaka zamani writers ya kara mana zumunci tsakanin mu ameen_