Sashe 4
Yan Gidan Haya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya gyada mishi kai kawai tare da kara riko mai unguwa domin su tafi, fir mai unguwa ya dage lallai sai malam Isah yazo an tafe tare dashi duk da bayanin da ya yi mai, amma mai unguwa ya dage. Haushi ya kama Baban Dare yace "ke mai unguwa kina so mata namu ya yi kisa ne? Kina gani fa mun bershi shi kadai ya na fada ba meza a gida fa."
"Yo ina ruwana dasu? su kashe kansu mana, amma billahillazi sai kun kaini gidan Usaini dukkan ku."
"Haba mai unguwa taya kake tunanin dukkanmu mubar gidan? Kiran mu aka yi domin tsawatar musu, amma ganin halin da kake ciki muka zabi taimaka maka, shine kuma kake cewa su kashe kansu?" cewar Malam Isah.
"Esa berta ki shiga gida, nine kadai ze kaita gidana huseni tefi kawai" Baban Dare ya fadi.
Malam Isah ya wuce ba tare da sauraron abun da mai unguwa ke fadi ba.
Baban Dare ya kalli mai unguwa dake ta aikin sababi, ya nade hannun riga tare da daukar mai unguwa da nufin goyawa a bayan shi.
Ganin wannan aiki yasa mai unguwa daga hannun mai ciwo ya kaimai duka a baya, wanda yasa hannun kara amsawa sai kuma ya dafe tare da matsar kwalla don ciwo .Baban Dare ya kalli mai unguwa yace "ok asema hannun ki yana lafiya shine kince aje gidan huseni ko? To walah ba zen kaiki ko ina ba" ya juya ya yi shigewarshi cikin gida ya bar mai unguwa tsugunne ga hawaye nabin fuskar shi.
Makocin 'yan gidan haya ne ya tausaya ma mai unguwa tare da daukar shi a mashin suka nufi gidan mai dori.
*A CIKIN GIDAN' YAN HAYA*
Zage-zage akeyi tsakanin su, ko wacce na zagin wanda sukai fad'a tare. Ganin mazan sun dawo ya sanya sukai shiru aka koma hararar juna.
Baban Dare ya dubi Maman Dare cikin yarensu yace "Na gode da kika zubarmin da mutunci, kullum ina fada miki ki daina shiga abun da babu ruwanki kinki, to wallahi duk abun da ya faru babu ruwana" ya shige dak'i.
Tasan halin mijinta da zuciya, jikanta ya yi sanyi ta rufa masa baya ita ma.
Malam Isah ya kalle su yanda sukai tsaye suna jifan juna da mummunan kallo yace "Talatu kuna da masaniyar kun kar ya mai unguwa ko?"
"Kar ya shi kuma, ta ina?" ta tambaya a rikice.
"A'a wallahi Maman Dare ce ta buga mai icce" cewar Mairon Ado dake tsaye gefe.
"To wata shegiyar ce ma ta kira shi gidan nan?" Maman Ladi ta tambaya tana hararar Mairon Ado.
Takaici ya kama Malam Isah ganin mai makon su jajanta, amma suna kokarin mai da zuwan nashi ma abun fad'a, dan haka yace,
"Ko wacce ta kira mijinta kafin zuwan 'yan sanda gidan nan,kun san halin mai unguwa" ya shige dak'i.
Suna tsoran batun' yan sanda don haka ko wacce ta shige dakin ta, tare da neman mazajen su.
An hallarra a tsakiyar gidan.
*Kome zai faru???*
*Ina labarin mai unguwa???*
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:36 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱
. 👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*
*WANNAN SHAFIN KYAUTA NE GARE KI ZUWAIRA MADARA. AUNTY ZETTY NAYIN KI IRIN SOSAI DINNAN, TANA YI MIKI FATAN ALKAHAIRI, ALLAH YA RAYA HANEEFAH, KEDIN TA MUSAMMAN CE.*
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*30~35*
Mai Unguwa zaune gaban Hussaini mai gyara, yana jiran ayi gyaran hannunshi saboda azabar ciwon da yake ji. Hussaini ya kalle shi bayan ya taba hannun yace "Mai unguwa ka samu tsagewar k'ashi a kafadar ka, garin ya hakan ya faru?"
"kayi aikin ka ba tambaya ba malam "cewar mai unguwa a fusace.
Gyada kai Hussaini ya yi yana murmushi, ya dauko wani mai ya diba sannan ya kama hannun mai unguwa da karfin tsiya. Wani ihu mai unguwa ya saki wanda ya janyo hankalin yaran gidan, suka dinga leke suna dariya.
Cikin azaba mai unguwa yace "Allah ya isa Hussaini, billahillazi ban yafe maka ba duniya da lahira azzalumi kawai".
Kara shafa man Hussaini ya yi ba tare da ya kula mai unguwa ba, ya sake riko hannun ya matsa ya shafe da wannan mai. Mai unguwa ya kwalla kara yana hawaye yana zagin Hussaini, shi kuma Hussaini saiya kama kafadar mai unguwa sai ya fanshe zagin da yake yi mishi. Ganin azabar ta yi yawa ya sanya ya warce hannun shi tare da mikewa ya share kwallar idonsa yace "Zakasan ni mai unguwa Tanko ka yi ma wannan mugunta wallahi, har da kai 'yan sanda zasu hada yau." ya juya zai fita.
"Mai unguwa kudin aiki na fa?" cewar Hussaini.
"Na karfine kazo ka k'wata azzalumi kawai"
"Haba mai unguwa, wannan fa hakkina ne."
"Naci hakkin naka, kayi abun da zaka yi." ya juya ya fice. Yana isa tsakiyar gidan ya ga dandazon yara sai dariya suke ganin ya fito. Tsawa ya daka musu, amma ina sai fadi suke "Mai unguwa ya yi kukan gyara yeeee ra go, matsoraci mai unguwa Tanko" suna shewa.
Da gudu ya bisu ga hannu a rike, aikuwa suka k'wasa da gudu suna dariya. Ganin bazai ka masu ba ya sanya ya wuce yana aikin sababi yana fadin "Yau hatta iyayen ku suma sai sun kwana ofishin 'yan sanda, billahillazi tare da 'yan gidan haya. Yanzu ma can zani na kira su." jin hannun nashi namai ciwo idan yana tafiya, yasa ya k'wance rawaninsa ya daure hannun dashi yana cije baki. Sannan ya mike hanya sai station.
*********
*A TSAKAR GIDAN 'YAN HAYA*
Kowa dake gidan ya hallara wurin wannan taro, bayan an zauna ne malam Isah ya mike da bayani kamar haka.
"Ina fatan zaku mai da hankali ku fahimci ainahin abun da ya taramu anan? Dalilin wannan taro kuwa bazai rasa nasaba da fadace-fadacen dake yawan faruwa ba a gidan nan. Misali na yau wanda ya kai mizanin babu mai hankali a cikin matan mu, ko wacce kokari take na ganin ta yi fad'a badai ta raba fadan ba yau, mai unguwa da ya kasance uban al'umma kuma matsayin mai kula da wannan gida yau shima sun ji masa ciwo a hannu. Kuyi sani cewa mai unguwa bazai taba barin wannan magana ba face ya danganta ta da hukuma, shiyasa nace ko wacce ta kira mijinta domin sanin abun yi"
Cikin takaici Baban Dare yace " sunayi fad'a kaman kaji wada beci abinci ba".Dariya wasu suka yi dajin hausar shi. Mijin Maman Ladi ya mike yace" Tabbas abun da matan mu keyi kwata-kwata basu tsare mana mutunci, sai kace mu kadaine 'yan haya cikin wannan gari, kullum sai sun ja mana jaraba wurin mai unguwa. Ranar cewa ya yi wurin sarki zai kai karar mu a koremu domin ya gaji da masifar matan mu" ya karasa cikin bakin ciki.
Haka aka dinga mai da bayani kan halayyar matan gidan, inda aka hana matan magana. Kowa ya yi ma matarsa kashedi kan wannan halayyar tasu. Ana cikin wannan magana ne suka ji jiniyar motar 'yan sanda, cikin takaici mazan suka mike da niyar fita waje, amma sai ganin 'yan sanda suka yi tare da jagorancin mai unguwa dake sak'ale da hannu a wuya kai babu rawani.
Mazan ne suka yi musu tayin zaman sulhu, amma mai unguwa yace sam babu sulhu sai dai a tafi da Maman Dare ofishi tunda itace taji mai ciwo.
"Kwarankwatsi sai an tafi da ita, matsiyaciya ita ta bugamin icce kawai don nazo rabon fad'a, shi kuma shegen mijinta ya barni a waje harda cewa wai na mutu ai basu suka kirani ba."
"Haba me unguwa kiyi hakuri mana ki fadi gaskiya" cewar Baban Dare jin bayanin mai unguwa.
"Yauwa Usmanu kaji ba? Mace yake kirana shegen kwanon" Mai unguwa ya fadi yana nuna Baban Dare.
Dariya dan sandan da ya kira da sunan Usmanu ya yi yace "afuwan mai unguwa bai iya hausa bane shiyasa"
" Yo dama an fadi mai hausar kayan banza ce? Ai dole ya kasa tunda ba muhallinsa bace" Mai Unguwa kenan.
Sauran mazan ne suka shiga maganar don ganin ba a tafi da Maman Dare ba albarkacin mijinta, sunyi ma mai Unguwa Alkawarin biyan kudin jinyar hannun shi har ya warke. Jin haka dama gashi da masifaffen son kudi, take ya amince da wannan tayin.
Nasiha sosai 'yan sanda sukai musu, tare da basu hakuri ganin an zauna tare, sannan mai unguwa ma yace "Na daina zuwa gidan nan koda zaku kashe kanku." Dariya sosai suka yi, sannan kowa ya kama kansa.
*SHIGAR MAI UNGUWA GIDANSA*
Matan na zaune tare da Lado, Sani da Buba suna hira. suka ganshi kai babu rawani, da sauri yaran suka mike cike da mamaki suna yi mishi sannu da zuwa. Ko kallon su baiyi ba ya zauna cikin zafin ciwo yana fadin "Hanne kawo min ruwa"
"Malam meyasa meka a hannu?"
"Jummala! Jummala! Kar wata banza ta kuma tambayata abun da ya faru muddin nine mai gidan nan"
"To babu mai kara tambaya Malam, kayi hakuri." taja bakinta ta yi shiru tana binshi da ido.
Ruwa yasha sannan yace "wato Jummala mata matsiyata da ban suke". Banza ta yi da shi.
Cikin hassala yace" magana fa nake kuka shareni"
"Baba kayi hakuri"cewar Lado.
"Don uwar ka na saka bakinka ne a wannan maganar?"
"Yi hakuri Malam bazai kara ba" Hannatu ta fadi tana mikewa.
"Zauna ma za anan munahika kawai, za aje dak'in don ga bala'i ya dawo ko?"
"Abince zan kawo maka Malam " ta fadi ta yi hanyar dak'inta.
Abincin ta kawo mai, amma ko kallon kayan bai yi ba sai ma cewa da ya yi ta kwashe bazai ci ba. Ta kuwa kwashe a ranta tana fadin"Mun samu na karyawa da safe".
"Baba ga wannan ka sai magani, ni zan wuce sai da safe." cewar Sani ya mika mai dari biyu.
Amsa ya yi yana dariya yace "Sani dan albarka, yaro mai halin dattijai na gode sosai magaji na"
"Yauwa Baba had'ari kayi ne?" Sani ya tambaya.
"Yo ina ruwana dasu? su kashe kansu mana, amma billahillazi sai kun kaini gidan Usaini dukkan ku."
"Haba mai unguwa taya kake tunanin dukkanmu mubar gidan? Kiran mu aka yi domin tsawatar musu, amma ganin halin da kake ciki muka zabi taimaka maka, shine kuma kake cewa su kashe kansu?" cewar Malam Isah.
"Esa berta ki shiga gida, nine kadai ze kaita gidana huseni tefi kawai" Baban Dare ya fadi.
Malam Isah ya wuce ba tare da sauraron abun da mai unguwa ke fadi ba.
Baban Dare ya kalli mai unguwa dake ta aikin sababi, ya nade hannun riga tare da daukar mai unguwa da nufin goyawa a bayan shi.
Ganin wannan aiki yasa mai unguwa daga hannun mai ciwo ya kaimai duka a baya, wanda yasa hannun kara amsawa sai kuma ya dafe tare da matsar kwalla don ciwo .Baban Dare ya kalli mai unguwa yace "ok asema hannun ki yana lafiya shine kince aje gidan huseni ko? To walah ba zen kaiki ko ina ba" ya juya ya yi shigewarshi cikin gida ya bar mai unguwa tsugunne ga hawaye nabin fuskar shi.
Makocin 'yan gidan haya ne ya tausaya ma mai unguwa tare da daukar shi a mashin suka nufi gidan mai dori.
*A CIKIN GIDAN' YAN HAYA*
Zage-zage akeyi tsakanin su, ko wacce na zagin wanda sukai fad'a tare. Ganin mazan sun dawo ya sanya sukai shiru aka koma hararar juna.
Baban Dare ya dubi Maman Dare cikin yarensu yace "Na gode da kika zubarmin da mutunci, kullum ina fada miki ki daina shiga abun da babu ruwanki kinki, to wallahi duk abun da ya faru babu ruwana" ya shige dak'i.
Tasan halin mijinta da zuciya, jikanta ya yi sanyi ta rufa masa baya ita ma.
Malam Isah ya kalle su yanda sukai tsaye suna jifan juna da mummunan kallo yace "Talatu kuna da masaniyar kun kar ya mai unguwa ko?"
"Kar ya shi kuma, ta ina?" ta tambaya a rikice.
"A'a wallahi Maman Dare ce ta buga mai icce" cewar Mairon Ado dake tsaye gefe.
"To wata shegiyar ce ma ta kira shi gidan nan?" Maman Ladi ta tambaya tana hararar Mairon Ado.
Takaici ya kama Malam Isah ganin mai makon su jajanta, amma suna kokarin mai da zuwan nashi ma abun fad'a, dan haka yace,
"Ko wacce ta kira mijinta kafin zuwan 'yan sanda gidan nan,kun san halin mai unguwa" ya shige dak'i.
Suna tsoran batun' yan sanda don haka ko wacce ta shige dakin ta, tare da neman mazajen su.
An hallarra a tsakiyar gidan.
*Kome zai faru???*
*Ina labarin mai unguwa???*
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
[3/1, 12:36 PM] Beauty Queen: ⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜
*'YAN GIDAN HAYA*
🔱🔱⚜⚜🔱🔱⚜⚜🔱🔱
. 👨🏻💻👩🏻💻
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
©
*Badeeyerh Beauty Queen*✍🏼
Dedicated to
*AUNTY ZETTY MAMAN HANAN*
*WANNAN SHAFIN KYAUTA NE GARE KI ZUWAIRA MADARA. AUNTY ZETTY NAYIN KI IRIN SOSAI DINNAN, TANA YI MIKI FATAN ALKAHAIRI, ALLAH YA RAYA HANEEFAH, KEDIN TA MUSAMMAN CE.*
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*30~35*
Mai Unguwa zaune gaban Hussaini mai gyara, yana jiran ayi gyaran hannunshi saboda azabar ciwon da yake ji. Hussaini ya kalle shi bayan ya taba hannun yace "Mai unguwa ka samu tsagewar k'ashi a kafadar ka, garin ya hakan ya faru?"
"kayi aikin ka ba tambaya ba malam "cewar mai unguwa a fusace.
Gyada kai Hussaini ya yi yana murmushi, ya dauko wani mai ya diba sannan ya kama hannun mai unguwa da karfin tsiya. Wani ihu mai unguwa ya saki wanda ya janyo hankalin yaran gidan, suka dinga leke suna dariya.
Cikin azaba mai unguwa yace "Allah ya isa Hussaini, billahillazi ban yafe maka ba duniya da lahira azzalumi kawai".
Kara shafa man Hussaini ya yi ba tare da ya kula mai unguwa ba, ya sake riko hannun ya matsa ya shafe da wannan mai. Mai unguwa ya kwalla kara yana hawaye yana zagin Hussaini, shi kuma Hussaini saiya kama kafadar mai unguwa sai ya fanshe zagin da yake yi mishi. Ganin azabar ta yi yawa ya sanya ya warce hannun shi tare da mikewa ya share kwallar idonsa yace "Zakasan ni mai unguwa Tanko ka yi ma wannan mugunta wallahi, har da kai 'yan sanda zasu hada yau." ya juya zai fita.
"Mai unguwa kudin aiki na fa?" cewar Hussaini.
"Na karfine kazo ka k'wata azzalumi kawai"
"Haba mai unguwa, wannan fa hakkina ne."
"Naci hakkin naka, kayi abun da zaka yi." ya juya ya fice. Yana isa tsakiyar gidan ya ga dandazon yara sai dariya suke ganin ya fito. Tsawa ya daka musu, amma ina sai fadi suke "Mai unguwa ya yi kukan gyara yeeee ra go, matsoraci mai unguwa Tanko" suna shewa.
Da gudu ya bisu ga hannu a rike, aikuwa suka k'wasa da gudu suna dariya. Ganin bazai ka masu ba ya sanya ya wuce yana aikin sababi yana fadin "Yau hatta iyayen ku suma sai sun kwana ofishin 'yan sanda, billahillazi tare da 'yan gidan haya. Yanzu ma can zani na kira su." jin hannun nashi namai ciwo idan yana tafiya, yasa ya k'wance rawaninsa ya daure hannun dashi yana cije baki. Sannan ya mike hanya sai station.
*********
*A TSAKAR GIDAN 'YAN HAYA*
Kowa dake gidan ya hallara wurin wannan taro, bayan an zauna ne malam Isah ya mike da bayani kamar haka.
"Ina fatan zaku mai da hankali ku fahimci ainahin abun da ya taramu anan? Dalilin wannan taro kuwa bazai rasa nasaba da fadace-fadacen dake yawan faruwa ba a gidan nan. Misali na yau wanda ya kai mizanin babu mai hankali a cikin matan mu, ko wacce kokari take na ganin ta yi fad'a badai ta raba fadan ba yau, mai unguwa da ya kasance uban al'umma kuma matsayin mai kula da wannan gida yau shima sun ji masa ciwo a hannu. Kuyi sani cewa mai unguwa bazai taba barin wannan magana ba face ya danganta ta da hukuma, shiyasa nace ko wacce ta kira mijinta domin sanin abun yi"
Cikin takaici Baban Dare yace " sunayi fad'a kaman kaji wada beci abinci ba".Dariya wasu suka yi dajin hausar shi. Mijin Maman Ladi ya mike yace" Tabbas abun da matan mu keyi kwata-kwata basu tsare mana mutunci, sai kace mu kadaine 'yan haya cikin wannan gari, kullum sai sun ja mana jaraba wurin mai unguwa. Ranar cewa ya yi wurin sarki zai kai karar mu a koremu domin ya gaji da masifar matan mu" ya karasa cikin bakin ciki.
Haka aka dinga mai da bayani kan halayyar matan gidan, inda aka hana matan magana. Kowa ya yi ma matarsa kashedi kan wannan halayyar tasu. Ana cikin wannan magana ne suka ji jiniyar motar 'yan sanda, cikin takaici mazan suka mike da niyar fita waje, amma sai ganin 'yan sanda suka yi tare da jagorancin mai unguwa dake sak'ale da hannu a wuya kai babu rawani.
Mazan ne suka yi musu tayin zaman sulhu, amma mai unguwa yace sam babu sulhu sai dai a tafi da Maman Dare ofishi tunda itace taji mai ciwo.
"Kwarankwatsi sai an tafi da ita, matsiyaciya ita ta bugamin icce kawai don nazo rabon fad'a, shi kuma shegen mijinta ya barni a waje harda cewa wai na mutu ai basu suka kirani ba."
"Haba me unguwa kiyi hakuri mana ki fadi gaskiya" cewar Baban Dare jin bayanin mai unguwa.
"Yauwa Usmanu kaji ba? Mace yake kirana shegen kwanon" Mai unguwa ya fadi yana nuna Baban Dare.
Dariya dan sandan da ya kira da sunan Usmanu ya yi yace "afuwan mai unguwa bai iya hausa bane shiyasa"
" Yo dama an fadi mai hausar kayan banza ce? Ai dole ya kasa tunda ba muhallinsa bace" Mai Unguwa kenan.
Sauran mazan ne suka shiga maganar don ganin ba a tafi da Maman Dare ba albarkacin mijinta, sunyi ma mai Unguwa Alkawarin biyan kudin jinyar hannun shi har ya warke. Jin haka dama gashi da masifaffen son kudi, take ya amince da wannan tayin.
Nasiha sosai 'yan sanda sukai musu, tare da basu hakuri ganin an zauna tare, sannan mai unguwa ma yace "Na daina zuwa gidan nan koda zaku kashe kanku." Dariya sosai suka yi, sannan kowa ya kama kansa.
*SHIGAR MAI UNGUWA GIDANSA*
Matan na zaune tare da Lado, Sani da Buba suna hira. suka ganshi kai babu rawani, da sauri yaran suka mike cike da mamaki suna yi mishi sannu da zuwa. Ko kallon su baiyi ba ya zauna cikin zafin ciwo yana fadin "Hanne kawo min ruwa"
"Malam meyasa meka a hannu?"
"Jummala! Jummala! Kar wata banza ta kuma tambayata abun da ya faru muddin nine mai gidan nan"
"To babu mai kara tambaya Malam, kayi hakuri." taja bakinta ta yi shiru tana binshi da ido.
Ruwa yasha sannan yace "wato Jummala mata matsiyata da ban suke". Banza ta yi da shi.
Cikin hassala yace" magana fa nake kuka shareni"
"Baba kayi hakuri"cewar Lado.
"Don uwar ka na saka bakinka ne a wannan maganar?"
"Yi hakuri Malam bazai kara ba" Hannatu ta fadi tana mikewa.
"Zauna ma za anan munahika kawai, za aje dak'in don ga bala'i ya dawo ko?"
"Abince zan kawo maka Malam " ta fadi ta yi hanyar dak'inta.
Abincin ta kawo mai, amma ko kallon kayan bai yi ba sai ma cewa da ya yi ta kwashe bazai ci ba. Ta kuwa kwashe a ranta tana fadin"Mun samu na karyawa da safe".
"Baba ga wannan ka sai magani, ni zan wuce sai da safe." cewar Sani ya mika mai dari biyu.
Amsa ya yi yana dariya yace "Sani dan albarka, yaro mai halin dattijai na gode sosai magaji na"
"Yauwa Baba had'ari kayi ne?" Sani ya tambaya.