← Book details Yakanah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 13

Sashe 9

Yakanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Suna falo ita da Sulaiman misalin karfe sha daya na dare suna hira a nutse irin ta da da mahaifi, ta ce, “Wai ni mai sunan Malam me yarinyar nan kanwar Hadiza ta yi maka ko kallon ta ba ka yi? Dazu da safe ina kallo tana gayas da kai ka dauke kai ka fita, haka tun zuwana ban taba ganin ka yi mata magana ba, balle wasan nan irin na mijin ya da kanwarta. In kana wuri ta shigo sai ka tashi, in kana falo ta ganka sai ta koma ta yi ta zaman daki. Ita da ganin ‘yar uwarta sai in baka nan, mene ne manufar hakan?”

Ya juyo yana kallon Inna ya ce, “Wacce yarinya kike magana?”

Ta ce, “Fatima”.

Yace, “Fati wai?”

“Eh, ita”.

Ya rausayar da kai ya ce, “Raini ne bana so, kuma ni ban iya wani wasan kanin miji ko kanin mata ba”.

Ta yi sakale tana jin sa, ta ce, “Hala

wani laifi ta yi maka? Har Hadiza na lura ranta yana baci da irin halin ko in kulan da kake yiwa ‘yar uwarta. Ban san ka da bakar zuciya ba, kada ka a fara a kan Fatima, domin mutum ce cikin ‘yammatan da babu irin su a yanzu, wannan yarinyar tana da halayen ‘yan aljanna, ka yi a hankali baka sani ba ko waliyya ce”.

Shi abin ma sai ya ba shi dariya, ya ce, “A wannan kalatacciyar duniyar tamu dama akwai sauran waliyyai Inna?”

Ta harare shi ta ce, “Dariya ma kake min?”

Ya yi saurin cewa, “A’a, yi hakuri Inna”.

Ta ce, “To ka gyara ma’amalar ku, zai fi kyau a ce akwai kyakkyawar alaka a tsakanin ku saboda Hadiza, in ta gaishe ka ka dinga amsawa cikin walwala da sakin fuska, wanda ya rike ibada ba ya wulakanta a duniya da Jahira. Baka sani ba ko ta fi ka matsayi a wajen Allah, ka canza takun ka a kanta, ai ba haka na ga kana yiwa su

Ruma ba, to matsayin ta daya dasu a gare ka, ka ji na gaya maka”.

Bai ce komi ba ya jawo wata hirar, don dai a sauya wannan. He is not interested at all (Fati is not the kind of person) wato ba ta daga cikin irin mutanen da yake son yin mu’amala dasu. Haka nan jinin su bai hadu ba, don yana son Ya, ba dole sai ya yi wata kakkarfar alaka da kanwar ta ba, bayan wadda musulunci ya ce, ai ba sa’ar wasan shi ba ce kanwar shi ce. Kwana bakwai din da Inna Halima ta yi jinyar Hadiza suke ita da Fati, komai ta ci sai ta amayar, ga zazzabi da ciwon kai mai zafi, sai ta rike kanta idan ciwon ya motsa mata tana wani irin kuka mai keta zuciyar duk mai imani.

Sulaiman da farko bai sani ba, don ya dauka laulayin ciki ne irin wanda ta saba, kuma ciwon baya tasar mata da daddare lokacin da suke tare kenan. Ita ma Inna ta lura ta san laulayi ne na sabon ciki, amma wannan buga kan da

Hadiza take yi a jikin bango da kukan da take yi na azaba ta fahimci akwai dai wani abun, amma tana ganin dukkan su likitoci ne sun san abin da ke damun ta, kuma ta ga Hadiza tana shan magani, sai ba ta yi magana ba, amma dai ba ta taba ganin irin wannan laulayin cikin ba.

Don haka ta kara sati saboda lafiyar Hadiza wadda ta daina cin komai sai ruwan bakin lipton da ruwan tsamiya. Gaba daya ta rame ta fita hayyacin ta, ba ta taba yin cikin da yake wahalar da ita irin wannan ba.

Tun Sulaiman bai gane ba har ya fahimci Hadiza ba ta da lafiya sosai, wannan ya wuce laulayi kuma wannan (migrain) yana bukatar bincike.

A daren ya fito daga wanka yana tsane kanshi da dan kankanin towell, tana kwance rigingine a gefen gado, cikin doguwar rigar barci mai santsi mara hannu ruwan madara, kyawawan kafafunta da cinyoyin ta a mike sambal, a haka sai ka rantse lafiyar ta kalau ba ta

tare da wata lalura.

Son matarshi da kaunar ta na kara girgiza zuciyar sa, yana hargitsa gangar jikinsa. Ta kure fanka da A.C amma ba ta daina zufa (gumi) ba. Da sauri ya karasa zarga igiyar pyjamas din shi ya yiwa kanshi kyakkyawan matsuguni a bayan ta, ya daura hannu a kan goshin ta, zafi rau! Dole ya hadiye nashi bukatan ya soma ba ta kyakkyawar kulawa ta hanyar sanya karamin towell a ruwa yana goge mata kanta don zafin kan ya ragu. Sannan ya soma bin gabban jikinta da message don ta ji dadin kasusuwan ta. Ya juyo ta ya rungume ta yana furzar da numfashi da sauri da sauri, ya sake cewa,

“Cikin kowanne hali, INA SON KI HADIZAH!””

Ta bude idanunta a hankali, wadanda suka kankance suka yi jawur tana kallon abin son ta, shi ma kallon ta yake kallon yaya zan yi da raina? Ya ce a galabaice,

“Gobe zan dauko Dr. Bunza ya duba

ki”.

Gabanta ya yi wani irin faduwa, ta runtse idon ta da karfi ta ce,

“Bana so, kada ka dauko shi, idan kuma har ka dage sai ka dauko shi to zan koma Karkasara’”.

Ya girgiza ta da karfi ya ce, “What do you mean (me kike nufi)? In barki a gida kina ciwo ban nema miki magani ba? Ai Allah sai ya tambaye ni, tyayen ki da suka danka min ke su tuhume ni. Wannan ciwon kan bana wasa bane yana bukatar bincike”.

Ta ce, “Ai ba yau na fara ba, kuma da na sha magani shi ke nan _ yake lafawa”.

“Ina maganin? Dauko min in gani”.

Ta ce, “Ya kare dazu, da safe nake shirin in aiki Fati ta siyo wasu”.

Yace, “Wane magani ne?”

Ta yi shiru.

““Tambayar ki nake yi, ina maganin? Ya ya sunan sa?’

Ta ce,

“Panadol”.

A mamakance ya maimaita “Panadol?”

“Eh”.

Ya ce,

“You are silly ko in ce you are nonsense Doctor! I did not beliebe YOU… “(kina shirme, ke shashashar likita ce, ban yarda dake ba).

Ya tashi a fusace ya fizgi waya ya kira Dr. Bashir, ‘consultant’ na ‘psychiatrist’, Surayya ce ta dauka, bai ko amsa gaisuwar da take mishi ba ya ce, “Ina mijin ki?’

Ta amsa

“An kira shi a ‘emergency’ kuma ‘he is on call’ yanzu ya fita, ya manta wayar”.

Ya kashe wayar ya cillar ya zauna a gefen gado ya dafe kai, Hadiza na kuka a hankali tana kara hargitsa shi, ya ce a fusace,

“Enough…….is enough Hadizah! Ki gaya min fisabilillahi mene ne babbar matsalar ki?”

Ta ce,

A mamakance ya maimaita “Panadol?”

“Eh”.

Ya ce,

“You are silly ko in ce you are nonsense Doctor! I did not beliebe YOU… “(kina shirme, ke shashashar likita ce, ban yarda dake ba).

Ya tashi a fusace ya fizgi waya ya kira Dr. Bashir, ‘consultant’ na ‘psychiatrist’, Surayya ce ta dauka, bai ko amsa gaisuwar da take mishi ba ya ce, “Ina mijin ki?’

Ta amsa

“An kira shi a ‘emergency’ kuma ‘he is on call’ yanzu ya fita, ya manta wayar”.

Ya kashe wayar ya cillar ya zauna a gefen gado ya dafe kai, Hadiza na kuka a hankali tana kara hargitsa shi, ya ce a fusace,

“Enough…….is enough Hadizah! Ki gaya min fisabilillahi mene ne babbar matsalar ki?”

Ta ce,

“Nifa na gaya maka laulayin ciki ne, Sai migraine wanda ba yau na fara ba, kuma ka san shi dama ina da magungunan da nake sha a kan shi, wannan zazzabin da haraswa laulayin ciki ne irin wanda na saba, zan gaya maka karya ne? Yau da bakin ka Sulaiman kake cewa baka yarda dani ba?” Jikinsa ya dan yi sanyi, ya rage sauti ya ce, “To ta ya ya zan ce zan kira likita da ya san matsalar ki ya duba ki ki ce a’a? Sai in dauka wani abu ne daban kike boye mini”.

Ya yi mata wani irin murmushi da har abada ba zai gushe daga zuciyarta ba, ta dauke kai alamar ta yi fushi. Ya bi bayan ta a hankali ya kwanta, suna raba zazzabin tare. Akwai wani abu wai shi ‘hot kiss’ da Hadiza ba ta sani ba daga Sulaiman sai a yau, ya mantar da ita rashin lafiyar ta, ya dauke ta ya jefa a duniyar soyayya, ta manta cewa ita nakasasshiya ce, ta manta damuwar ta na cewa lafiyarta na hannun Allah, ta dauka cewa, tana a Dr. Hadiza ne ta

baya. Ba za ta mance da wannan ranar da Sulaiman ya zubar da hawayen shi a karo na biyu a kanta ba.

Na farko saboda ta nakasa, na biyu na dimbin soyayyar da yake yi mata. To wanne ne zai kasance na uku???

2K KK OK

I

nna ba ta koma Bakori ba sai bayan watanni biyu, lokacin laulayin Hadiza ya ragu, tana yi mata dabaru irin na manya har ta samu sauki.

A lokacin cikin ya shiga wata hudu, sannan ne laulayin ya tsaya. Sannan ciwon kanta ya jima bai tashi ba, saboda Dr. Bunza ya sauya mata magani, Fati ce ke zuwa ta karbo ba tare da sanin Sulaiman ba.

Ganin ciwon ya dade bai tashi ba sai Hadiza ta watsar da shawarar Fati ba ta gayawa Yaya ba, shi dama SuJaiman tuni ta binne shi ya kuma yarda cewa migraine take.

Cikin Hadiza wata bakwai, ya fito ya

yi tororo kamar watanni tara. Haka za ka ganta fus! A cikin wheel chair tasa cikin a gaba tana kallo tana mamakin sarautar Allah, wanda ya ga damar ta haihu a cikin halin da take ciki. So da kulawa wurin Sulaiman kamar ya yi mata nakuda.

Watan Aprilu ya kama, wanda ya yi dai-dai da EDD din ta, cikin dare wani azababben ciwon kai ya tashe ta, ta soma bubbuga kanta a jikin gado, kafin a yi haka ta yi dogo suma jini ya kece kamar da bakin kwarya.
Chapter 9 · 0% Book details