Sashe 4
Yakanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ji yake in zai iya ba ta ranshi, to zai ba ta. Balle duniyar da abin da ke cikinta. Bai tambaye ta me za ta yi dasu ba, ko adadin da take so, ya kwaso duk abin da ke cikin aljihun shi ya zuba a jakar ta.
Allah sarki! Kamar ba za su rabu ba, a lokacin har duhun dare ya shigo, likitoci uku ne da ke karkashin sa suka kwankwasa suka turo kofar suka shigo. Dole Hadiza ta dau jakarta da lab-coat hadi da gilashinta ta fita, yana kara jaddada mata ta yi tuki da kula. Dan banzan go slow ne ya tare ta a titi, ba ta isa gidansu ba sai tara da rabi, Maman su da suke kira Yaya, tana zaune a tsakar gida da rediyo a hannun ta tana sauraron Jakar Magori. Autan su Abdulyassar yana gefe yana hada motar kara.
Yaya Babar su Hadiza ba wata tsohuwa ba ce cancan, don irin auren wurin nan aka yi mata, shekarun ta
arba’in kenan.
Hadiza ta yi sallama Yaya ta amsa, Abdulyassar ya watsar da _ kayan wasan shi da gudun shi ya kwaso ya rungume ‘yar uwar shi, kasancewar ta mai jan su a jiki tare da nuna musu kauna. Yana tambayar ta ina Munib? Daga can dakinta na ‘yammatanci, wanda a yanzu ya zan mallakin Fati, sautin Abdurrahaman Sudais ke tashi a hankali cikin suratul Al-Imran, wannan ya tabbatar mata Hafiza Fati Ja‘afar na gida.
Ta samu gefen Yaya ta zauna, Yaya ta mike daga kwanciyar da ta yi bisa tabarma. Kai da ganin kyakkyawar fuskarta ka san ta ji dadin ganin diyar tata, ta ce, “Da daddaren nan Hadiza?’ Ta ce, “Wallahi Yaya, Dr. ne ya tare ni, na kawo ma Fati kudin ne”.
Ta ce, “Amma kin kyauta, don da ta yi ma Yayan ku maganar ta waya ya ce ba zai samu zuwa Kano wannan satin ba, ga shi baban ku kwanan nan kasuwar ta ja baya, kuma ta ce daga
wannan satin za a rufe”.
Ta ce, “Baba bai dawo bane?”
Yaya ta ce, “Ya dawo tun yamma, ya tafi dubiyar dan gidan Malam Abdu ne babur ya buge shi dazu”.
Ta ce, “Allah ya sauwake, Fati na ciki ko”.
Yaya ta ce, “Yanzu ta gama cin abinci ta shige ciki tana rehearsal, jibi za su yi musabakar jiha kuma ita za ta wakilci jihar Kano, kin san Fati ba daga nan ba”.
Cikin alfahari da kanwar tata a zuciyarta, Hadiza ta tura kofar dakin cikin sallama, Fati ta diro daga gado ta rungume ‘yar uwarta tana yi mata oyoyo.
Hadiza ta dubi Fati sama da kasa, ta zama cikakkiyar budurwa sosai. Ta kama baki “Fati girma haka?”
Fati ta yi murmushi, kumatunta duka suka lotsa gwanin sha’awa, wushiryarta ta fito siririya da ita.
Hadiza ta ce, “Wane course aka samu?”
Ta ce, “Course din da na nema ne (Islamic Studies)”.
Ta ce, “Masha Allah, da an je kuma sai a Samo saurayi, irin wannan girma haka Fati?”
Ta ji kunya ta boye fuskarta cikin tafukanta, ta ce, “Ai hijabi zan ke zumbulawa irin mai hannun nan, kada ace ana so na”.
Hadiza ta ce me za ta yi ba dariya ba, duk girman Fati baka raba ta da wauta.
Ta kirgo kudi a jakarta naira dubu ishirin ta ba ta, Fati ta yi godiya ta ce, “Allah Yaya Hadiza kwana biyu ba’a kawo su Munib ba”.
Ta ce, “Makaranta ta boye su, amma da anyi hutu suna nan tafe insha-Allah”. Sai sannan ne ta ga hakoran Fati. Ta ce, “Ashe kuma musabaka za a yi Fati ba labari? To Allah Ya ba da sa’a”.
Ta yi murmushi ta ce,
“Ameen”,
Tana shirin fita Baban su na shigowa,
ya ce, “A’ah, manyan likitoci ne yau a gidan namu? Ina matas da abokin?” Ta yi murmushi ta tsuguna har kasa ta gaida tsohon ta, ta ce, “Suna nan lafiya basu samu hutu bane, da sun samu za su ZO”. Yace, “Kinga kafar nan tawa kwanan nan bana jin dadin ta, har na gaji da hadiyar magani”. Ta ce, “Wane magani ne Baba? Likita ne ya rubuta?” Ya ce, “A‘a, maganin ciwon kashi ne kawai nake saya a wajen masu talla”. Ta kama baki, “Baba irin wadannan magungunan ba masu kyau bane, yawanci ma sun yi edpiry don Allah ka daina sha. Yanzu bari in rubuta maganin Fati ko Hamza su je su siyo”. Yace, “To na gode”.
Ta baro Karkasara karfe goma daidai na dare, dauke da tazbihi a bakinta domin ba abu ne da ta ke so ko ta saba
ba, wato (night dribing) tukin dare.
Ta biyo ta titin Court Road ta hawo titin Gandu, ta yi kwana ta hau titin B.U.K Road. Ta iso Kabuga ta dau titin New-site wanda zai sadata da Janbulo. Babu wadatar motoci a titin. Daga gefen ta wayarta ta yi kara, sunan Sweetypie ya soma yawo a screen din. Ta yi murmushi ta mika hannun damanta ta dauka, ta rike sitiyari da hannun hagu cikin sanyin sauti ya ce,
“Ya ya? Hope for now kina gida?”
Ta yi ajiyar zuciya cikin karyayyar murya ta ce, “Na kusa dai, ina kan Iya abin da ya ji ke nan sai wata irin kara da ta fi kama da fashewar taya, ya yi kira “Hello!…..Hello….Hadizah!” Amma ba amsa.
Motar ta hantsila ta shige karkashin wata trailer da ke cike da buhunhunan abinci, duk da kokarin da direban ya yi wajen kauce mata hakan bai samu ba, motocin da ke gabansu da bayan
su duk suka yi birki cikin salati, tsirarun mutanen da ke gefen titi suka runtumo don kawo agaji.
T
a hanyar katin shaida (ID Card) jami’an tsaro suka gano ko wace ce Hadiza. Don haka ba su sha wahalar samun nombar wayar mijinta ba, wanda ke can cikin gigicewa. Nan asibitin aka taho da ita cikin jinni, rai a hannun Allah.
Likitoci biyar ne a kan Hadiza, sai Sulaiman cikon na shida, wanda ya manta wani abu wai shi karatun likita, komawa ya yi tamkar bai taba halarta
aji ba. Shi da Hadiza da ke kwance babu maraba, illa shi a tsaye yake, sai dai jingine da garu (bango), wanda ya taimaka masa wajen daukar nauyin gangar jikinsa. A lokacin da za ka tsaga ba za ka samu ko digon jini a cikin jikinsa ba.
Tashin hankali ba a sa maka rana! Haka wannan mummunan labari ya iske iyayen Hadiza da ‘yan uwanta ta hanyar Dr. Surayyah.
A daren Mukhtar ya baro Kaduna zuwa Kano, a daren suka dungumo baki dayan su suka taho, sai dai basu samu ganin Hadiza ba. Har zuwa lokacin likitoci na tsananta bincike a kanta, haka suka kwana a barandar asibiti cikin tsananin sanyi. Fati sai kuka take kamar ranta zai fita tunda suka taho, Yaya na lallashin ta.
Sai washegari da safe result din Hadiza ya iske Sulaiman da iyayen ta, bayan raunuka da ba za su kirgu ba, babu karaya ko daya a jikinta. Babban tashin hankalin wanda ya _ girgiza
kowa shi ne, jijiyar bayanta wadda ta hada daga wuya zuwa bayan ta (spinal cord) ta tsinke, wanda ke nufin Hadiza ba za ta kara iya mikewa ba, ba za ta kara iya tafiya ba a gaba daya sauran rayuwar ta.
Dr. Sulaiman ya mike tsaye ya nuna Dr. Samson da dan yatsa, “Ka san abin da kake fada, ban san cewa baka san aikin ka ba sai yau. Kuma shi ke nan daga yin accident sai ka nakasta min mata? Uwarka ce ba za ta kara iya mikewa ba, amma ba Hadiza ba……” Kai da ganin yadda yake maganar, kwayar idanun shi a juye, ka san ba a hayyacin sa yake wannan furucin ba. Samson ya sunkuyar da kai, duka likitocin babu wanda ya kara magana. Tausayi ne fal a zukatan su. Dr. Hadiza abar so ce ga kowa, suna jin dadin tarayya da ita, marasa lafiyan ta na yaba kokarin ta. Wannan accident da ya yi mata karan tsaye da kuruciyar ta, ya zamo nakasu ga dimbin taimakon da take bai ma al’umma.
Malam Ja’afar mahaifin Hadiza da ke gefe shi ya soma tausar Sulaiman da kalami masu dadi da sanya imani, yana tuna masa muhimmancin yarda da kaddara.
Sulaiman ya yi shiru, ya koma ya zauna a kujerar sa. Ya kifa kai cikin cinyoyin sa, amma har yanzu ya kasa yarda da abin da kunnuwan sa suka jiye masa.
Wai Hadiza ta zama sai dai a kwantar a tayar ba za ta kara amfanuwa ba, ba za ta kara moruwa ba. Balle ta amfanawa kanta komai. Ita da ‘ya’yanta da mijinta sai dai gani da ido. Abin da suke gani kullum yana faruwa da al’umma yau Allah As-Samadu ya juyo da shi kansu. Dimbin ilimin su, karfin aljihunsu da tunanin su babu abin da zai iya a kai, domin ita wannan jijiya ba ta doruwa. Sai ya fashe da kuka.
Malam Ja’afar ya mike daga kujerar sa ya isa ga Sulaiman, ya mikar da shi
tsaye ya rungume.
“Haba Sule! Kamar ba namiji ba? Namijin ma, likitan likitoci. Ba ka yi kuka a kan sauran al’umma da kuke kwana da yini kuna fama dasu ba sai a kan matar ka kadai? Su Allah ba ya son su ne yake dora musu lalura? Allah da ya halicci Hadiza ya fi mu son ta, shi kadai ya san dalilin sa na hukunta hakan a gare ta.
Yau in Hadiza mutuwa ta yi me zamu iya ban da mu yi mata addu’a? Amma tana raye, a kalla muna ganin ta muna jin dadi, ka yi tawakkali ka barwa AIlah, ka zamo mai YAKANAH, sai ya yi maka tukuici da abin da baka zata ba.
Kai za ka ba ta kwarin gwiwa, ta rungumi kaddarar da Allah ya dora mata. Amma idan ka fita karaya, wane ne zai karfafa wani?”
Ya mika hannu yana share masa hawayen da suka kasa daina ambaliya daga kyawawan idanun sa.
Dr. Ruth ta yi gyaran murya, ta dubi
Dr. Sulaiman ta sunkuyar da kanta, kana ta dago ta ce,
Allah sarki! Kamar ba za su rabu ba, a lokacin har duhun dare ya shigo, likitoci uku ne da ke karkashin sa suka kwankwasa suka turo kofar suka shigo. Dole Hadiza ta dau jakarta da lab-coat hadi da gilashinta ta fita, yana kara jaddada mata ta yi tuki da kula. Dan banzan go slow ne ya tare ta a titi, ba ta isa gidansu ba sai tara da rabi, Maman su da suke kira Yaya, tana zaune a tsakar gida da rediyo a hannun ta tana sauraron Jakar Magori. Autan su Abdulyassar yana gefe yana hada motar kara.
Yaya Babar su Hadiza ba wata tsohuwa ba ce cancan, don irin auren wurin nan aka yi mata, shekarun ta
arba’in kenan.
Hadiza ta yi sallama Yaya ta amsa, Abdulyassar ya watsar da _ kayan wasan shi da gudun shi ya kwaso ya rungume ‘yar uwar shi, kasancewar ta mai jan su a jiki tare da nuna musu kauna. Yana tambayar ta ina Munib? Daga can dakinta na ‘yammatanci, wanda a yanzu ya zan mallakin Fati, sautin Abdurrahaman Sudais ke tashi a hankali cikin suratul Al-Imran, wannan ya tabbatar mata Hafiza Fati Ja‘afar na gida.
Ta samu gefen Yaya ta zauna, Yaya ta mike daga kwanciyar da ta yi bisa tabarma. Kai da ganin kyakkyawar fuskarta ka san ta ji dadin ganin diyar tata, ta ce, “Da daddaren nan Hadiza?’ Ta ce, “Wallahi Yaya, Dr. ne ya tare ni, na kawo ma Fati kudin ne”.
Ta ce, “Amma kin kyauta, don da ta yi ma Yayan ku maganar ta waya ya ce ba zai samu zuwa Kano wannan satin ba, ga shi baban ku kwanan nan kasuwar ta ja baya, kuma ta ce daga
wannan satin za a rufe”.
Ta ce, “Baba bai dawo bane?”
Yaya ta ce, “Ya dawo tun yamma, ya tafi dubiyar dan gidan Malam Abdu ne babur ya buge shi dazu”.
Ta ce, “Allah ya sauwake, Fati na ciki ko”.
Yaya ta ce, “Yanzu ta gama cin abinci ta shige ciki tana rehearsal, jibi za su yi musabakar jiha kuma ita za ta wakilci jihar Kano, kin san Fati ba daga nan ba”.
Cikin alfahari da kanwar tata a zuciyarta, Hadiza ta tura kofar dakin cikin sallama, Fati ta diro daga gado ta rungume ‘yar uwarta tana yi mata oyoyo.
Hadiza ta dubi Fati sama da kasa, ta zama cikakkiyar budurwa sosai. Ta kama baki “Fati girma haka?”
Fati ta yi murmushi, kumatunta duka suka lotsa gwanin sha’awa, wushiryarta ta fito siririya da ita.
Hadiza ta ce, “Wane course aka samu?”
Ta ce, “Course din da na nema ne (Islamic Studies)”.
Ta ce, “Masha Allah, da an je kuma sai a Samo saurayi, irin wannan girma haka Fati?”
Ta ji kunya ta boye fuskarta cikin tafukanta, ta ce, “Ai hijabi zan ke zumbulawa irin mai hannun nan, kada ace ana so na”.
Hadiza ta ce me za ta yi ba dariya ba, duk girman Fati baka raba ta da wauta.
Ta kirgo kudi a jakarta naira dubu ishirin ta ba ta, Fati ta yi godiya ta ce, “Allah Yaya Hadiza kwana biyu ba’a kawo su Munib ba”.
Ta ce, “Makaranta ta boye su, amma da anyi hutu suna nan tafe insha-Allah”. Sai sannan ne ta ga hakoran Fati. Ta ce, “Ashe kuma musabaka za a yi Fati ba labari? To Allah Ya ba da sa’a”.
Ta yi murmushi ta ce,
“Ameen”,
Tana shirin fita Baban su na shigowa,
ya ce, “A’ah, manyan likitoci ne yau a gidan namu? Ina matas da abokin?” Ta yi murmushi ta tsuguna har kasa ta gaida tsohon ta, ta ce, “Suna nan lafiya basu samu hutu bane, da sun samu za su ZO”. Yace, “Kinga kafar nan tawa kwanan nan bana jin dadin ta, har na gaji da hadiyar magani”. Ta ce, “Wane magani ne Baba? Likita ne ya rubuta?” Ya ce, “A‘a, maganin ciwon kashi ne kawai nake saya a wajen masu talla”. Ta kama baki, “Baba irin wadannan magungunan ba masu kyau bane, yawanci ma sun yi edpiry don Allah ka daina sha. Yanzu bari in rubuta maganin Fati ko Hamza su je su siyo”. Yace, “To na gode”.
Ta baro Karkasara karfe goma daidai na dare, dauke da tazbihi a bakinta domin ba abu ne da ta ke so ko ta saba
ba, wato (night dribing) tukin dare.
Ta biyo ta titin Court Road ta hawo titin Gandu, ta yi kwana ta hau titin B.U.K Road. Ta iso Kabuga ta dau titin New-site wanda zai sadata da Janbulo. Babu wadatar motoci a titin. Daga gefen ta wayarta ta yi kara, sunan Sweetypie ya soma yawo a screen din. Ta yi murmushi ta mika hannun damanta ta dauka, ta rike sitiyari da hannun hagu cikin sanyin sauti ya ce,
“Ya ya? Hope for now kina gida?”
Ta yi ajiyar zuciya cikin karyayyar murya ta ce, “Na kusa dai, ina kan Iya abin da ya ji ke nan sai wata irin kara da ta fi kama da fashewar taya, ya yi kira “Hello!…..Hello….Hadizah!” Amma ba amsa.
Motar ta hantsila ta shige karkashin wata trailer da ke cike da buhunhunan abinci, duk da kokarin da direban ya yi wajen kauce mata hakan bai samu ba, motocin da ke gabansu da bayan
su duk suka yi birki cikin salati, tsirarun mutanen da ke gefen titi suka runtumo don kawo agaji.
T
a hanyar katin shaida (ID Card) jami’an tsaro suka gano ko wace ce Hadiza. Don haka ba su sha wahalar samun nombar wayar mijinta ba, wanda ke can cikin gigicewa. Nan asibitin aka taho da ita cikin jinni, rai a hannun Allah.
Likitoci biyar ne a kan Hadiza, sai Sulaiman cikon na shida, wanda ya manta wani abu wai shi karatun likita, komawa ya yi tamkar bai taba halarta
aji ba. Shi da Hadiza da ke kwance babu maraba, illa shi a tsaye yake, sai dai jingine da garu (bango), wanda ya taimaka masa wajen daukar nauyin gangar jikinsa. A lokacin da za ka tsaga ba za ka samu ko digon jini a cikin jikinsa ba.
Tashin hankali ba a sa maka rana! Haka wannan mummunan labari ya iske iyayen Hadiza da ‘yan uwanta ta hanyar Dr. Surayyah.
A daren Mukhtar ya baro Kaduna zuwa Kano, a daren suka dungumo baki dayan su suka taho, sai dai basu samu ganin Hadiza ba. Har zuwa lokacin likitoci na tsananta bincike a kanta, haka suka kwana a barandar asibiti cikin tsananin sanyi. Fati sai kuka take kamar ranta zai fita tunda suka taho, Yaya na lallashin ta.
Sai washegari da safe result din Hadiza ya iske Sulaiman da iyayen ta, bayan raunuka da ba za su kirgu ba, babu karaya ko daya a jikinta. Babban tashin hankalin wanda ya _ girgiza
kowa shi ne, jijiyar bayanta wadda ta hada daga wuya zuwa bayan ta (spinal cord) ta tsinke, wanda ke nufin Hadiza ba za ta kara iya mikewa ba, ba za ta kara iya tafiya ba a gaba daya sauran rayuwar ta.
Dr. Sulaiman ya mike tsaye ya nuna Dr. Samson da dan yatsa, “Ka san abin da kake fada, ban san cewa baka san aikin ka ba sai yau. Kuma shi ke nan daga yin accident sai ka nakasta min mata? Uwarka ce ba za ta kara iya mikewa ba, amma ba Hadiza ba……” Kai da ganin yadda yake maganar, kwayar idanun shi a juye, ka san ba a hayyacin sa yake wannan furucin ba. Samson ya sunkuyar da kai, duka likitocin babu wanda ya kara magana. Tausayi ne fal a zukatan su. Dr. Hadiza abar so ce ga kowa, suna jin dadin tarayya da ita, marasa lafiyan ta na yaba kokarin ta. Wannan accident da ya yi mata karan tsaye da kuruciyar ta, ya zamo nakasu ga dimbin taimakon da take bai ma al’umma.
Malam Ja’afar mahaifin Hadiza da ke gefe shi ya soma tausar Sulaiman da kalami masu dadi da sanya imani, yana tuna masa muhimmancin yarda da kaddara.
Sulaiman ya yi shiru, ya koma ya zauna a kujerar sa. Ya kifa kai cikin cinyoyin sa, amma har yanzu ya kasa yarda da abin da kunnuwan sa suka jiye masa.
Wai Hadiza ta zama sai dai a kwantar a tayar ba za ta kara amfanuwa ba, ba za ta kara moruwa ba. Balle ta amfanawa kanta komai. Ita da ‘ya’yanta da mijinta sai dai gani da ido. Abin da suke gani kullum yana faruwa da al’umma yau Allah As-Samadu ya juyo da shi kansu. Dimbin ilimin su, karfin aljihunsu da tunanin su babu abin da zai iya a kai, domin ita wannan jijiya ba ta doruwa. Sai ya fashe da kuka.
Malam Ja’afar ya mike daga kujerar sa ya isa ga Sulaiman, ya mikar da shi
tsaye ya rungume.
“Haba Sule! Kamar ba namiji ba? Namijin ma, likitan likitoci. Ba ka yi kuka a kan sauran al’umma da kuke kwana da yini kuna fama dasu ba sai a kan matar ka kadai? Su Allah ba ya son su ne yake dora musu lalura? Allah da ya halicci Hadiza ya fi mu son ta, shi kadai ya san dalilin sa na hukunta hakan a gare ta.
Yau in Hadiza mutuwa ta yi me zamu iya ban da mu yi mata addu’a? Amma tana raye, a kalla muna ganin ta muna jin dadi, ka yi tawakkali ka barwa AIlah, ka zamo mai YAKANAH, sai ya yi maka tukuici da abin da baka zata ba.
Kai za ka ba ta kwarin gwiwa, ta rungumi kaddarar da Allah ya dora mata. Amma idan ka fita karaya, wane ne zai karfafa wani?”
Ya mika hannu yana share masa hawayen da suka kasa daina ambaliya daga kyawawan idanun sa.
Dr. Ruth ta yi gyaran murya, ta dubi
Dr. Sulaiman ta sunkuyar da kanta, kana ta dago ta ce,