Sashe 2
Yakanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haduwar su haduwa ce _ special kuma haduwa ba ta dadi ba. Yana tare da patient da ya yiwa aiki satin da ya wuce, Hadizah Ja’afar, da wasu abokan karatun ta suka shigo domin daukar lacca. Ko kallon su bai yi ba, balle ya tantance kamannin su, kasancewar Allah bai dora mishi lalurar yiwa mata kallon kurilla ba. Tsakanin
shi da kowacce diya mace, kallo daya ne, da kau da kai.
Suka samu_ kujeru. suka zauna, kowacce da jotter din ta da biro a hannu. Yana ta yi musu bayani cikin lafiyayyen turancinshi na _ Birtaniya mara surki, wani zubin ya yiwa mara lafiyar tambaya ta ba shi amsa.
Wata amsa da patient din ta bayar ta sanya su murmushi dukkanin su (ban da Hadiza), cikin kalaman ta za ka fahimci kwakwalwarta ta tabu sakamakon bacin zuciya da damuwa.
Ta ce,
“Likita nifa ‘yar sarauta ce ba mara lafiya ba!”.
(Wannan ne ya sanya su yin murmushi). Ya ce,
“Wacce sarauta gare ki don mu fara girmama ki?”
Gaba daya daliban suka yi dariya don yadda yake biye ma shirmen matar dole ya baka dariya. Ta ce,
“Sarautar Kano gare ni”.
Yace, “Wacce ke nan?” Ta ce,
“Nice ‘yar ruwatan Kano”.
Gaba daya suka yi murmushi, wannan karon ma ban da Hadizah, wadda a lokacin hankalinta baya tare dasu, yana ga halin da ta baro Mamansu a ciki na rashin lafiya mai tsanani.
Ba zato Dr. Bakori ya jefo tambaya, “Mene ne delusion?” Ya kuma nuna Hadiza da ya lura hankalinta ba ya tare da shi matsayin wadda za ta amsa mishi tambayar shi.
Ya yi mata magana ya kai sau uku ba ta san yana yi ba. Hadiza ta damu da Mamanta sosai, kasancewar ta jarumar Uwa mai hidimtawa rayuwar su, tun daga yarinta har a girman su. Yaya, (Sa’adatu), ba ta huta da dawainiyar su ba. Don haka jin ciwon ta suke tamkar a gangar jikin su.
Duka kawayen ta babu wadda ta zungure ta, don sun san da ta ji za ta ba da amsa a yabe ta kamar yadda manyan likitoci suke yabon ta a kullum saboda kokarin ta.
Ya buga tebir din gaban shi da karfi
har ta razana, ya nuna mata hanyar waje ya ce, ‘You can go out….. in kin gama tunanin kya dawo”.
Ta mike sumi-sumi ta fita, murna gun su Hafsat kamar su yi yaya, yau Allah ya nuna musu likitan da ya yi maganin ‘yar gaban goshin likitoci. Ya yi (referring patient) din zuwa psychiatric, su kuma ya sallame su.
Ya koma gida a wannan ranar, bayan ya gama duk abubuwan da ya saba na al’adar rayuwar shi kamin ya kwanta, kamar shan fruit da edcercise saboda shi da daddare yake edcercise din sa kasancewar da safe ba shi da lokaci.
Amma abin mamaki ya kasa runtsa idonsa, tunanin fuskar dalibar da ya kora a yau ke gilma mishi, ya hana shi sakat, ya hana shi sukuni, ya yi duk kokarin da zai yi don ya samu barci amma hakan ya faskara. Ya ko kasa runtsa idon sa, wani bakon al’amari ne mai takura zuciya da bai taba tsintar
kansa a ciki ba.
Hadiza ba wata muguwar kyakkyawa ba ce cancan, tana da kyau dai-dai nata, sai dai kuma yarinya ce mai aji na karshe. Fuskarta zagayayya mai dauke da dara-daran fararen idanu masu sheki da walainiya, hancinta kamar an sanya ruler an ja shi an daidaita shi a kan (obal -shaped) fuskarta. Bakinta dan karami kamar cokali baya shige ba. A kan tsinin hancinta tawwadar Allah ce da aka haife ta da ita, fara ce sol! Irin farin nan da wadataccen ilimin boko ke taimakawa wajen zahharar sa.
Bai taba ganin yarinyar da (lab-coat) ta yi ma kyau kamar Hadizah ba. Ba Sai ya tsaya wahalar da kanshi wajen tunanin abin da ke faruwa da shi ba, ya tabbata son Hadiza ne ke ratsa kowanne sako a jikinsa.
Abin haushin ko sunan ta bai sani ba, zuciya ta kwashe shi ya yi abin da ya zo ya dame shi. Bai taba tsintar kansa a kwatankwacin irin wannan yanayin
ba, a kan diya mace.
Sai dai shi a ce ana son sa yana hura hanci, kada hakan ya janyo raini, baya fatan hakan ya kasance sakayya ce Allah ya yiwa dimbin matan da ke binsa agindi-agindi don ya so su yana yakice su. Tare da yi musu wulakancin da ko a hanya suka ganshi bazasu yi fatan ace sun san shi ba.
Ya fahimci dalibar (obstetric and gynaecology) ce, daga (ID Card) din ta. Yadda ya ga rana haka ya ga dare, ko na second daya bai runtsa ba. So da kaunar student (daliba) Hadiza na narkar mai da zuciya.
Abin kamar sihiri, daga ranar bai kara ganin Hadiza ba, bai kuma san ya zai yi ya tambaya ba, tunda ko sunanta bai sani ba. A matsayinsa na babban likita, mai juya sauran likitocin bangaren su, ba karamin zub da kima bane a ji shi yana tambayar wata yarinya cikin masu daukar darasi a wurin su. Duk da haka bai fidda rai ba, yana da yakinin watarana Allah zai
sake hada shi da yarinyar ko da a mafarki ne.
Ita kuwa Hadiza ba ta dawo TH ba sai bayan sati uku, tana gida tana Jinyar Maman su da suke kira Yaya, da ke fama da ciwon hanta. Tana ganin likita a Murtala, har suka kwantar da ita sati guda.
Kawarta Surayya ke daukar musu Jacca tana kuma sanar da ita duk abin da ke faruwa ta waya. Ranar monday Maman su ta ji sauki sosai, don haka ta shirya ta dawo.
Ba zato babu tsammanin shi, yana ganawa da wata patient din suka shigo ita da Surayyah, ya zare gilashin idonsa a hankali, ya saki wata sassanyar ajiyar zuciya irin ta wanda ke neman abu, ya wahala ya dade, kamin ya samu. Duk hankalin sa da attention din sa sai ya koma kanta, ya manta abin da ke gabansa, ya samu kansa da rudewa. Abin da bai taba yi ba a kan diya mace, akwai wani sassanyan
kallo cikin kwayar idon Hadizah, da ba duk mata Allah ya mallakawa ba. Suka gaishe shi cike da girmamawa, sannan suka samu kujeru suka zauna. Hadiza dai a darare take, ko kanta ba ta dago ba. Daga gefe-gefen idon ta take satar kallon likitan da ya hargitsa mata tunani ‘yan kwanakin nan. Tunda ya kore ta ba ta kara samun nutsuwar zuciyarta ba, har zuwa yau da ta sake tozali da shi a karo na biyu.
Ta tambayi kanta, shin ko mutane nawa ne a duniya irin Dr. Bakori? Yana da wasu ilhamomi na musamman a tare da shi da ba ta taba ganin su a da namiji ba, ko yadda yake duban mutane daban ne da na sauran likitocin da ta sani. Tsarin maganar sa cikin seriousness shi ne babban abinda ke burge ta da shi, ga kamun kai da sanin mutuncin kai, hadi da rashin son wasa ta ko’ina. Dr. Sulayman Bakori, ya shiga cikin rukunin wasu mutane da take ganin matukar kima da mutuncin su, sannan kuma ya bi ya
manne a zuciyarta, ta yadda dai-dai da minti daya ta kasa manta shi cikin satittikan da ta yi tana jinyar Mamanta.
A gurguje ya basu laccar ya kuma sallami mara lafiyar da suke tare da ita. Suka mike da nufin su tafi, baya fatan wannan damar da kubuce masa, don haka bai yi kwauron baki ba, ya yi ta maza (in ji mata) ya ce da Hadiza cikin wata irin lallausar murya da ya kasa yarda cewa tashi ce.
“Wato fushi kika yi? Kika daina halartar karatun ki sabida na kore ki a kan kin yi min laifi?”
Ta yi ajiyar zuciya a hankali ba tare da ta juyo ba, ta ce,
“A haba Doctor! Wane ni in yi fushi? Mum dina aka kwantar a_ hospital kuma ni nake jinyar ta sai jiya aka sallame mu”.
Ya nuna tausayi tsantsa a_ kan kyakkyawar fuskarsa, ya ce, “Ayya!
Ta juyo ta yi mishi murmushi, suka yi
ido hudu da dan Inna Halima, wani chemistry yayi aiki cikin ‘yan dakikai, ya kimsa wani al’amari mai GIRMA a zuciyoyinsu mai wuyar bayyanawa. Gwiwoyinta suka yi sanyi, zuciyarta ta karye, duk wata soyayya da Allah ya halitta a zuciyarta ta hadu ta tattare waje daya. To haka shi ma. Jikin shi ya ba shi wannan ita ce matar auren shi, wadda za ta samar mishi da ‘ya’yan da zai yi alfaharin fitowar su daga tsatson ta. Ya ce
“A bani address zan zo in duba Mamar mu”.
Daga ita har Surayyah sai suka yi mutuwar tsaye, domin abune da ko da wasa basu taba kawowa ba. Kowa ya san shi da halin ko in kula da yake nunawa a kan mata, wanda ke burge kowa. Don haka sun sha mamaki.
Ita Hadiza ta kasa magana, sai Surayyah ce ta rairayo mishi adireshin Hadiza. Ya ce,
“Idan na zo wa zan ce?”
Ta ce,
“Hadizah!””.
Ya ce,
“Hadizahh, am I welcome?”
Ta yi murmushi ta ce, ”
You are welcome!!”.
Tun daga ranar kakkarfar soyayya ta kullu, kullum suna tare, a gida ne ko a ofis. Abin ya soma bayyana ga abokan aikin shi da abokan karatun ta, da manyan likitoci mata da ke yi mishi asirtacciyar soyayya.
Wannan ya janyo ma Hadiza hassada karara a wajen mafi yawan abokan karatun ta, to ita ma sai ta share su, saboda ta san Surayyah kadai ke kaunar ta saboda Allah.
A
uren su, wani abu ne da ya bar dimbin tarihi a asibitin Malam Aminu Kano, domin mafi akasarin likitocin cardiology kabilu da Hausawa sun halarta. Ba a taba ganin daurin auren da ya tara ‘yan boko tsantsa, likitoci ziryan a unguwar Karkasara irin na Hadiza ba. Suka tare a gidan Sulaiman da ke cikin asibiti, cikin wata irin soyayya mai wuyar fassarawa.
Aure ne auren soyayya mai tsabta, wanda babu ha’inci, yaudara ko karya a cikin ta. Ya sha mamakin samun Hadizah a cikakkiyar mace (birgin) musamman in aka yi la’akari da matakin karatun ta. Ba gaskiya bane
zargin da ake yiwa ‘yammatan (medicine), kawai dan iska dan iskan kansa ne, amma da yawa abin da ya kai su shi ne a gabansu.
shi da kowacce diya mace, kallo daya ne, da kau da kai.
Suka samu_ kujeru. suka zauna, kowacce da jotter din ta da biro a hannu. Yana ta yi musu bayani cikin lafiyayyen turancinshi na _ Birtaniya mara surki, wani zubin ya yiwa mara lafiyar tambaya ta ba shi amsa.
Wata amsa da patient din ta bayar ta sanya su murmushi dukkanin su (ban da Hadiza), cikin kalaman ta za ka fahimci kwakwalwarta ta tabu sakamakon bacin zuciya da damuwa.
Ta ce,
“Likita nifa ‘yar sarauta ce ba mara lafiya ba!”.
(Wannan ne ya sanya su yin murmushi). Ya ce,
“Wacce sarauta gare ki don mu fara girmama ki?”
Gaba daya daliban suka yi dariya don yadda yake biye ma shirmen matar dole ya baka dariya. Ta ce,
“Sarautar Kano gare ni”.
Yace, “Wacce ke nan?” Ta ce,
“Nice ‘yar ruwatan Kano”.
Gaba daya suka yi murmushi, wannan karon ma ban da Hadizah, wadda a lokacin hankalinta baya tare dasu, yana ga halin da ta baro Mamansu a ciki na rashin lafiya mai tsanani.
Ba zato Dr. Bakori ya jefo tambaya, “Mene ne delusion?” Ya kuma nuna Hadiza da ya lura hankalinta ba ya tare da shi matsayin wadda za ta amsa mishi tambayar shi.
Ya yi mata magana ya kai sau uku ba ta san yana yi ba. Hadiza ta damu da Mamanta sosai, kasancewar ta jarumar Uwa mai hidimtawa rayuwar su, tun daga yarinta har a girman su. Yaya, (Sa’adatu), ba ta huta da dawainiyar su ba. Don haka jin ciwon ta suke tamkar a gangar jikin su.
Duka kawayen ta babu wadda ta zungure ta, don sun san da ta ji za ta ba da amsa a yabe ta kamar yadda manyan likitoci suke yabon ta a kullum saboda kokarin ta.
Ya buga tebir din gaban shi da karfi
har ta razana, ya nuna mata hanyar waje ya ce, ‘You can go out….. in kin gama tunanin kya dawo”.
Ta mike sumi-sumi ta fita, murna gun su Hafsat kamar su yi yaya, yau Allah ya nuna musu likitan da ya yi maganin ‘yar gaban goshin likitoci. Ya yi (referring patient) din zuwa psychiatric, su kuma ya sallame su.
Ya koma gida a wannan ranar, bayan ya gama duk abubuwan da ya saba na al’adar rayuwar shi kamin ya kwanta, kamar shan fruit da edcercise saboda shi da daddare yake edcercise din sa kasancewar da safe ba shi da lokaci.
Amma abin mamaki ya kasa runtsa idonsa, tunanin fuskar dalibar da ya kora a yau ke gilma mishi, ya hana shi sakat, ya hana shi sukuni, ya yi duk kokarin da zai yi don ya samu barci amma hakan ya faskara. Ya ko kasa runtsa idon sa, wani bakon al’amari ne mai takura zuciya da bai taba tsintar
kansa a ciki ba.
Hadiza ba wata muguwar kyakkyawa ba ce cancan, tana da kyau dai-dai nata, sai dai kuma yarinya ce mai aji na karshe. Fuskarta zagayayya mai dauke da dara-daran fararen idanu masu sheki da walainiya, hancinta kamar an sanya ruler an ja shi an daidaita shi a kan (obal -shaped) fuskarta. Bakinta dan karami kamar cokali baya shige ba. A kan tsinin hancinta tawwadar Allah ce da aka haife ta da ita, fara ce sol! Irin farin nan da wadataccen ilimin boko ke taimakawa wajen zahharar sa.
Bai taba ganin yarinyar da (lab-coat) ta yi ma kyau kamar Hadizah ba. Ba Sai ya tsaya wahalar da kanshi wajen tunanin abin da ke faruwa da shi ba, ya tabbata son Hadiza ne ke ratsa kowanne sako a jikinsa.
Abin haushin ko sunan ta bai sani ba, zuciya ta kwashe shi ya yi abin da ya zo ya dame shi. Bai taba tsintar kansa a kwatankwacin irin wannan yanayin
ba, a kan diya mace.
Sai dai shi a ce ana son sa yana hura hanci, kada hakan ya janyo raini, baya fatan hakan ya kasance sakayya ce Allah ya yiwa dimbin matan da ke binsa agindi-agindi don ya so su yana yakice su. Tare da yi musu wulakancin da ko a hanya suka ganshi bazasu yi fatan ace sun san shi ba.
Ya fahimci dalibar (obstetric and gynaecology) ce, daga (ID Card) din ta. Yadda ya ga rana haka ya ga dare, ko na second daya bai runtsa ba. So da kaunar student (daliba) Hadiza na narkar mai da zuciya.
Abin kamar sihiri, daga ranar bai kara ganin Hadiza ba, bai kuma san ya zai yi ya tambaya ba, tunda ko sunanta bai sani ba. A matsayinsa na babban likita, mai juya sauran likitocin bangaren su, ba karamin zub da kima bane a ji shi yana tambayar wata yarinya cikin masu daukar darasi a wurin su. Duk da haka bai fidda rai ba, yana da yakinin watarana Allah zai
sake hada shi da yarinyar ko da a mafarki ne.
Ita kuwa Hadiza ba ta dawo TH ba sai bayan sati uku, tana gida tana Jinyar Maman su da suke kira Yaya, da ke fama da ciwon hanta. Tana ganin likita a Murtala, har suka kwantar da ita sati guda.
Kawarta Surayya ke daukar musu Jacca tana kuma sanar da ita duk abin da ke faruwa ta waya. Ranar monday Maman su ta ji sauki sosai, don haka ta shirya ta dawo.
Ba zato babu tsammanin shi, yana ganawa da wata patient din suka shigo ita da Surayyah, ya zare gilashin idonsa a hankali, ya saki wata sassanyar ajiyar zuciya irin ta wanda ke neman abu, ya wahala ya dade, kamin ya samu. Duk hankalin sa da attention din sa sai ya koma kanta, ya manta abin da ke gabansa, ya samu kansa da rudewa. Abin da bai taba yi ba a kan diya mace, akwai wani sassanyan
kallo cikin kwayar idon Hadizah, da ba duk mata Allah ya mallakawa ba. Suka gaishe shi cike da girmamawa, sannan suka samu kujeru suka zauna. Hadiza dai a darare take, ko kanta ba ta dago ba. Daga gefe-gefen idon ta take satar kallon likitan da ya hargitsa mata tunani ‘yan kwanakin nan. Tunda ya kore ta ba ta kara samun nutsuwar zuciyarta ba, har zuwa yau da ta sake tozali da shi a karo na biyu.
Ta tambayi kanta, shin ko mutane nawa ne a duniya irin Dr. Bakori? Yana da wasu ilhamomi na musamman a tare da shi da ba ta taba ganin su a da namiji ba, ko yadda yake duban mutane daban ne da na sauran likitocin da ta sani. Tsarin maganar sa cikin seriousness shi ne babban abinda ke burge ta da shi, ga kamun kai da sanin mutuncin kai, hadi da rashin son wasa ta ko’ina. Dr. Sulayman Bakori, ya shiga cikin rukunin wasu mutane da take ganin matukar kima da mutuncin su, sannan kuma ya bi ya
manne a zuciyarta, ta yadda dai-dai da minti daya ta kasa manta shi cikin satittikan da ta yi tana jinyar Mamanta.
A gurguje ya basu laccar ya kuma sallami mara lafiyar da suke tare da ita. Suka mike da nufin su tafi, baya fatan wannan damar da kubuce masa, don haka bai yi kwauron baki ba, ya yi ta maza (in ji mata) ya ce da Hadiza cikin wata irin lallausar murya da ya kasa yarda cewa tashi ce.
“Wato fushi kika yi? Kika daina halartar karatun ki sabida na kore ki a kan kin yi min laifi?”
Ta yi ajiyar zuciya a hankali ba tare da ta juyo ba, ta ce,
“A haba Doctor! Wane ni in yi fushi? Mum dina aka kwantar a_ hospital kuma ni nake jinyar ta sai jiya aka sallame mu”.
Ya nuna tausayi tsantsa a_ kan kyakkyawar fuskarsa, ya ce, “Ayya!
Ta juyo ta yi mishi murmushi, suka yi
ido hudu da dan Inna Halima, wani chemistry yayi aiki cikin ‘yan dakikai, ya kimsa wani al’amari mai GIRMA a zuciyoyinsu mai wuyar bayyanawa. Gwiwoyinta suka yi sanyi, zuciyarta ta karye, duk wata soyayya da Allah ya halitta a zuciyarta ta hadu ta tattare waje daya. To haka shi ma. Jikin shi ya ba shi wannan ita ce matar auren shi, wadda za ta samar mishi da ‘ya’yan da zai yi alfaharin fitowar su daga tsatson ta. Ya ce
“A bani address zan zo in duba Mamar mu”.
Daga ita har Surayyah sai suka yi mutuwar tsaye, domin abune da ko da wasa basu taba kawowa ba. Kowa ya san shi da halin ko in kula da yake nunawa a kan mata, wanda ke burge kowa. Don haka sun sha mamaki.
Ita Hadiza ta kasa magana, sai Surayyah ce ta rairayo mishi adireshin Hadiza. Ya ce,
“Idan na zo wa zan ce?”
Ta ce,
“Hadizah!””.
Ya ce,
“Hadizahh, am I welcome?”
Ta yi murmushi ta ce, ”
You are welcome!!”.
Tun daga ranar kakkarfar soyayya ta kullu, kullum suna tare, a gida ne ko a ofis. Abin ya soma bayyana ga abokan aikin shi da abokan karatun ta, da manyan likitoci mata da ke yi mishi asirtacciyar soyayya.
Wannan ya janyo ma Hadiza hassada karara a wajen mafi yawan abokan karatun ta, to ita ma sai ta share su, saboda ta san Surayyah kadai ke kaunar ta saboda Allah.
A
uren su, wani abu ne da ya bar dimbin tarihi a asibitin Malam Aminu Kano, domin mafi akasarin likitocin cardiology kabilu da Hausawa sun halarta. Ba a taba ganin daurin auren da ya tara ‘yan boko tsantsa, likitoci ziryan a unguwar Karkasara irin na Hadiza ba. Suka tare a gidan Sulaiman da ke cikin asibiti, cikin wata irin soyayya mai wuyar fassarawa.
Aure ne auren soyayya mai tsabta, wanda babu ha’inci, yaudara ko karya a cikin ta. Ya sha mamakin samun Hadizah a cikakkiyar mace (birgin) musamman in aka yi la’akari da matakin karatun ta. Ba gaskiya bane
zargin da ake yiwa ‘yammatan (medicine), kawai dan iska dan iskan kansa ne, amma da yawa abin da ya kai su shi ne a gabansu.