← Book details Yakanah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 13

Sashe 5

Yakanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Ina ganin idan Dr. Hadiza ta ji sauki, za ta iya ci gaba da aikinta ta hanyar amfani da wheel chair, idan har za’a samu wanda zai juri kawo ta da mai da ita”.

Kiris! Ya rage ya lailayo ashar ya antaya mata, amma da ya tuna Malam na wajen Sai ya balla mata harara, a zuciyar shi ya ce,

“Uwar ki za a sa a wheel chair ba uwar Munib ba”.

Samson ya ce,

“Shawarar Ruth abar dubawa ce, hakan zai debe mata kewa fiye da ta zauna a gida ba abin da take yi. Ko ba don zuwa aiki ba dole za a nema mata wheel chair ko da a gida ne”.

Ba shi da abin cewa, don duk likitocin abin da suke cewa kenan. Malam dai baya ji saboda cikin harshen turanci suke maganar. Sulaiman ya tashi ya fita ya nufi ICU inda aka kwantar da Hadizah.

A bayan kofa ya tsaya ya rabe, yana leken ta, ya kasa karasawa, ya kura mata ido yana ta’ajjibin yadda kwana daya rak! Allah ya_ jirkitar da kyakkyawar fuskar Hadiza, ko ina a jikinta rauni ne, nan plasta can plasta. Barci take sadidan, sai dai da gani ba na Allah da Annabi bane (na karfin allurai ne).

Rabin fuskarta nade cikin bandeji, wadda ta kumbura ta yi sumtum kamar an hura (baloon). A hankali ya soma taku ya isa ga gadon da take kwance, ya ja kujera ya zauna dai-dai fuskarta yana fuskantar ta.

Ya kai hannu bisa goshin ta wanda ke nade cikin bandeji, kamar an ce da ita bude idon ki. Suka yi ido hudu da Sulaiman din ta, ta dubi dakin ta dubi kanta, ta tabbatar a kwance take a gadon asibiti. Ta maido duban ta ga Sulaiman wanda ke binta da ido, da zuciya, ta ce cikin kankanuwar murya, “Accident na yi ko?”

Ya daga mata kai. Ta dora hannunta

mai rangwamen raunika bisa nashi dake goshin ta, ta sauke, don ji take kamar ya dora mata Dala da Gwauron Dutse.

Ta yunkura da niyyar ta tashi zaune amma ta ji kamar ba jikinta ba, ya mike ya kama ta ya mikar da ita zaune. Ya janyo pillow ya tusa mata don ta ji dadin jinginar, ya tabbatar dai da gaske ne Hadizar shi ta zama disabled (nakasasshiya), sai jikinsa ya soma kyarma.

Duk dauriyar da yake yi abin ya ci tura, da sauri ya rungume ta, cikin shesshekar kuka ya ce,

“Cikin kowanne hali, INA SON KI HADIZAH””

Kuka suke dukkanin su babu mai rarrashin wani, don ita Hadiza ta tabbatar abin da zai sa Sulaiman kuka, to tabbata ba karamin abu bane, wannan shi ya gigita ta, ita ma ta fashe da kuka.

Fati a gaba, Yaya, Malam, Hamza da babban Yayan su Mukhtar suka shigo, daga Hadiza har Sulaiman babu wanda ya san da shigowar su, shessehekar kukan Fati ne ya ankarar da Sulaiman cewa akwai mutane a dakin.

A hankali ya zare jikinsa daga na Hadiza ya juya ya fita daga dakin ba tare da ya iya hada ido da surukansa ba.

Malam Ja’afar ya karasa jikin gadon Hadiza ya kama hannun ta inda babu ciwo, ya ce, “Ki yi tawakkali Hadiza, ki zamo mai YAKANAH a dukkanin al’amuran ki, ki zamo mai godiya ga Allah a duk yanayin da kika tsinci kanki. Wannan ba shi ne karshen rayuwar ba, yarda da kaddara dole ne ga duk musulmin kwarai”.

Cikin kuka mai tsanani ta ce, “Na ji Baba, amma don Allah ku fada min me ke faruwa dani? Sulaiman bai gaya min komi ba, sai kuka yake yi, kukan shi ya daga min hankali, ku fidda ni a duhu. Wani abu ne ya faru dani?”

Malam ya sa habar babbar rigar sa ya share hawayen da suka ciko mishi ido cikin dabara wai kada Hadiza ta ga shi ma kukan yake, amma ta ganin. Hadiza ta musamman ce ko a cikin ‘ya’yansa, yana son ta son da bal yiwa su Mukhtar, ganin Babanta yana kuka sai ta kara tsananta kukan ta.

Cikin tausasawa Mukhtar ya ce, “Cool down Hadiza, take it easy……. Ya shiga rattabo mata al’amarin da ya samu rayuwarta, ya kare da cewa, ““Wannan shi ne ya dagawa Sulaiman hankali, amma kamar yadda Baba ya ce ne, ki yi tawakkali, ki zamo mai YAKANAH! Wannan ba shi _ ne karshen rayuwar ba!”

A matsayinta na cikakkiyar likita, tuni ta gano mummunan nakasun da ya samu rayuwarta wanda babu wani likitan duniya da zai iya maganin shi. Ta nemi hawaye a kwayar idonta ta rasa, ta nemi miyau don ta hadiya a kan harshen ta ya kafe karaf! Kamar

Fati a gaba, Yaya, Malam, Hamza da babban Yayan su Mukhtar suka shigo, daga Hadiza har Sulaiman babu wanda ya san da shigowar su, shessehekar kukan Fati ne ya ankarar da Sulaiman cewa akwai mutane a dakin.

A hankali ya zare jikinsa daga na Hadiza ya juya ya fita daga dakin ba tare da ya iya hada ido da surukansa ba.

Malam Ja’afar ya karasa jikin gadon Hadiza ya kama hannun ta inda babu ciwo, ya ce, “Ki yi tawakkali Hadiza, ki zamo mai YAKANAH a dukkanin al’amuran ki, ki zamo mai godiya ga Allah a duk yanayin da kika tsinci kanki. Wannan ba shi ne karshen rayuwar ba, yarda da kaddara dole ne ga duk musulmin kwarai”.

Cikin kuka mai tsanani ta ce, “Na ji Baba, amma don Allah ku fada min me ke faruwa dani? Sulaiman bai gaya min komi ba, sai kuka yake yi, kukan shi ya daga min hankali, ku fidda ni a duhu. Wani abu ne ya faru dani?”

Malam ya sa habar babbar rigar sa ya share hawayen da suka ciko mishi ido cikin dabara wai kada Hadiza ta ga shi ma kukan yake, amma ta ganin. Hadiza ta musamman ce ko a cikin ‘ya’yansa, yana son ta son da bal yiwa su Mukhtar, ganin Babanta yana kuka sai ta kara tsananta kukan ta.

Cikin tausasawa Mukhtar ya ce, “Cool down Hadiza, take it easy……. Ya shiga rattabo mata al’amarin da ya samu rayuwarta, ya kare da cewa, ““Wannan shi ne ya dagawa Sulaiman hankali, amma kamar yadda Baba ya ce ne, ki yi tawakkali, ki zamo mai YAKANAH! Wannan ba shi ne karshen rayuwar ba!”

A matsayinta na cikakkiyar likita, tuni ta gano mummunan nakasun da ya samu rayuwarta wanda babu wani likitan duniya da zai iya maganin shi. Ta nemi hawaye a kwayar idonta ta rasa, ta nemi miyau don ta hadiya a kan harshen ta ya kafe karaf! Kamar

bai taba gudana a cikin bakinta ba.

Ta runtse idonta da karfi, tsawon mintuna biyar ba ta bude ba. Ita kadai ta san radadin da take ji a zuciyarta, ita kadai ta san azabtuwar da ruhinta ke yi, al’amarin ya shallake tunanin ta. Ba ta yi tsammanin al’amarin ya yi kamarin haka ba, lallai dan adam ba a bakin komai yake ba.

Yau ne kake mai rai, gobe ne kake gawa. Yau ne kake da amfani, idan Ubangiji ya so, gobe ne ka zama tarihi. A rayuwar Hadiza ba ta taba tsammanin wata kaddara makamanciyar wannan za ta taba shafar rayuwar ta ba. To ina ruwan Allah!

Ta bude idon a hankali tana kallon iyayen ta da ‘yan uwanta wadanda dukkanin su ke sharar hawaye, sai ta soma lallashin su cikin muryar ban mamaki, tamkar ba ita ba. Ta fi su karfin zuciya, ta fi su tawakkali, ta fi su YAKANAH. Ta karbi kaddarar ta da hannu bibbiyu, tana fatan Allah ya sa hakan ya zamo kaffara a gare ta, in

kuma jarrabawa ce ya sa ta cinye jarrabawar ta.

36 KOK

Dole kanwar naki, Sulaiman ya sayo ma Hadiza wheel chair ana i gobe za a sallame su daga asibiti. Don duk raunin dake jikinta ya kame sai karfin jiki da dan abin da ba a rasa ba.

Yaya ta so Sulaiman ya ba ta Hadiza ta wuce da ita gida inda za ta fi samun kulawar iyaye da ‘yan uwa, amma sai ya sa musu kuka. Da me zai ji ne? Da lalurar da ta kashe masa rayuwa, ko da rashin Hadiza a cikin gidan, wadda ta zamo wani bangare na rayuwar sa, kundin farin cikin sa, sannan barin jikinsa?

Dole suka kyale shi da matar shi, amma sun ce Fati ta koma gidan ta zauna tare dasu, don ta dinga taimaka masa kula da Hadiza, musamman kasancewar sa ba mazauni ba.

Sulaiman bai so ba, don shi tun fil’azal Allah bai sa mishi son Fati ba, saboda

son da Hadiza ke mata. Yana kishin Fati, a ganin sa Hadiza ta fi son Fati a kanshi. Sannan zubin ta na zuhudu (gudun duniya) ya yi yawa, bai fiya son mutane irin ta ba, kasancewar shi (sociable).

A tsarin halittar dan adam (personality), tana cikin rukunin al’ummar da ake kira (introbert). Ba ta iya hada ido da shi, kai da kowa ma, saboda kunya. Da wuya ka ga hakoranta, sai dai in guri ya kure ta yi murmushi, ‘dimple’ din da ‘cleft’ su lotsa, wanda shi ne muhimmin al’amarin da ke daukar hankalin dubban maza a kanta, sai dai kuma bai isa ya tsallake hukuncin da Yaya ta yanke ba.

Haka Fati ta hado kayan ta tsaf, ta dawo gidan ‘yar uwarta da zuciyar ‘yan uwantaka. Zuciyarta cike fal da so da kaunar ‘yar’uwar ta, karatun da ta taso shekara da shekaru da burin yin sa, gashi ta samu, amma ta jingine shi ta sadaukar da rayuwarta kacokam da

lokacinta ga rayuwar, ‘yar uwarta. Sulaiman ya ciccibo Hadiza ya fito da ita daga mota, Fati ta bude (boot) ta fiddo wheel chair a nade, cikin sauri ta warware, Sulaiman ya sanya ta a ciki ya tura a hankali zuwa cikin gida.

Fati ta fiddo kayansu daga cikin motar ta rufe motar, ta soma diban kayan daya bayan daya tana shiga dasu cikin gida.

Malam Ilu maigadi, ya yi sallama a falon, a lokacin Sulaiman na kici-kicin aza Hadiza a daya daga cikin kujerun falon, ba tare da ya juyo ba ya amsa masa.
Chapter 5 · 0% Book details