← Book details Kida A Ruwa Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 19

Sashe 11

Kida A Ruwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Tunda Nabeeha ta shigo falon kowa ya saki baki yana kallonta. Mammah kam kallo ɗaya tai mata ta ɗauke kanta. Koda ta gaisheta ma a haka ta amsa hankalinta akan Nawal ɗin Aunty Mimi. Su Ma'aruff da suka zo wuya zasuyi magana Gwaggo Khadijah tai musu gargaɗi da idanu. Dole sukai shiru. Sarai Nabeeha ta lura da yanayinsu, amma ta danne dan a ganinta basu bane a gabanta. Idanunta akan Mu'azz ta tambayesa ina Dada yake.
Mu'azz ba komai ya sani game da lamarin Nabeeha ba. Duk da dai da wayonsa tabar gidan amma ba komai ya sani ba. Da hannu kawai ya nuna mata sama. Bakuwa ta sake magana ba, ba kuma kunyar kowa balle jin nauyi ta nufi stairscase ɗin tana taku ɗai-ɗai cike da gadara ita ga matar boss.
Aunty Ummi dake jin kamar ta amayo zuciyarta dan takaici taja hannun Aunty Mommy suka shige kitchen bayan tama Mimi signal da ido. Fakar idanun su Mammah tai itama tabi bayansu.
Basu wani jima ba suka fito, hannun Aunty Mimi da tray an haɗa kayan abinci akai. Cikin sa'a dai-dai nan Nimrah da Ruky da Biebah ke fitowa. Nimrah tayi wanka ta canja kayanta. Kuma wando ne fari daya kwanta a jikin nata da riga iya gwiwa Pakistan style na yadi mai taushi. Sai siririn gyale kalar yadin rigar. Babu wata kwalliya a fuskarta sai rosy lips data shafa daya saka lips ɗin taushi da santsi, yay pink sosai, ko daga nesa kake da ita zakaga hakan....
“Yauwa Nimrah zoki miƙama Dada abincinsa”. Aunty Mommy ta faɗa kai tsaye. Ɗagowa Mammah tai da sauri, ta buɗe baki zatai magana Gwaggo Alawiyya ta katseta da faɗin, “Dama yanzu zan yi magana kuwa. Amsa kinji ƴar albarka. Ruƙayya ke kuma zo nan na sakaki aiki”.
Haɗa ido Mammah da Gwaggo Khadijah sukai, Mammah tayi yanayin kai ƙara gareta, amma sai Gwaggo Khadijahn ma tai mata murmushi alamar tana goyon bayan abinda ƴan ta kife ɗin ƴaƴanta ke shirin yi. Kanta ta girgiza kawai tana kallon su Ma'aruff, a mamakinta suma duk sun washe fuskoki ba kamar yanda suka ciskule ba tun shigowar Nabeeha.
Received at 12:22 PM
reacted with ❤ Nimrah dai da ba sanin abinda ya faru sukai ba tuni ta shagwaɓe fuska zata fara langare. Aunty Ummi ta balla mata harara dole tazo ta amshi tray ɗin. Wucewa tai tana ɗan tuttura baki, dan harga ALLAH tana son yin ɗan nesa da shi har sai taji amsar tambayiyinta akan batun nan ɗaya tak daya zame mata ƙayar kifi a maƙoshi....

A wannan lokacin da Nabeeha tuni ta iso ƙofar ɗakin na Dada bayan ta hauro taci karo da Afeef dake fitowa a ɗakinsu shi da Mu'azz ta tambayesa ya nuna mata. Knocking tayi a hankali, sai dai shiru babu motsi balle ta samu amsa. Sanin halinsa yasa ta sake yi har sau biyu, daga nan ta buɗe Kofar kawai ta shiga dan ta kasa daurewa. Da wani irin ƙamshi ta fara cin karo, dan ƙamshin turaren wutar SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. na Maman Abdull ya gama kama lungu da saƙo na sashen Mammah. Sai da ta lumshe idanu ta buɗe tana sauke ajiyar zuciya kafin ta ƙarasa shiga ɗakin. Ko ina fes a gyare, babu tarkace kamar yanda ta sanshi mutum mara son hayaniya. Jin motsi a bayi yasata zama a bakin gadon tana murmushi, babu abinda take hangowa sai yanda zaiyi mamakin ganinta da farin ciki. Ta sake gyara zamanta da ƙyau. A dai-dai lokacin kuma Nimrah data iso itama tai knocking ƙofar. Sai dai jin shiru da sanin halinsa na in ba shi yaso ba bazai tanka ba yasata murɗa handle ɗin ƙofar kawai ta tura ta shiga da sallama.
Wani kalar zubo mata idanu Nabeeha da zuciyarta tai zallo cikin ƙirjinta tayi. Ta buɗe baki zatai magana tana ƙoƙarin miƙewa kawai aka buɗe ƙofar bathroom. Dada da bai san dasu ba su duka biyun ya ɗan yi tsaii yana kallonsu.
Nimrah kam jitai ƙirjinta ya buga, a lokaci guda tai saurin duƙar da kanta. Gaba ɗaya ji take ta daburce, a hakan ma ALLAH ya sota bathrobe ce a jikinsa ba towel ba. Sai dai kuma abinda bata taɓa gani bane daga garesa dole ta rikice. Dan bathrobe ɗin ma dai kaɗan ta wuce gwiwarsa.
Har cikin ransa bai ji daɗi ba shima. Idan Nabeeha ta ganshi a haka normal ne ai, amma Nimrah ina, da sauran lokaci. Jallabiya ya ɗauka batare da yayi magana ba ya juya cikin bayin. Babu jimawa ya sake fitowa da ita a jiki. Abinda ya bashi mamaki har lokacin Nimrah na'a inda ya barta. Kanta a ƙasa ga kaya a hannu kamar wadda aka dasa. Yayinda Nabeeha ke mata wani mugun kallo sai dai itama bata iya tayi magana ba saboda wani curarren abu daya dunƙule mata ƙirji ko numfashi bata fitarwa da ƙyau. Zuciyarta tsara mata take taje ta fisgi tray ɗin abincin ta kife mata shi a jiki, sannan ta kamata da shegen duka har sai ta daina numfashi. Kai itafa da tana da dama ko macen sauro bazata sauka mata a jikin miji ba..
Tana can tunanin ya kwasheta kawai sai hango Dada tayi a gaban Nimrah. Itama Nimrahn daba sanin isowarsa tai ba jin an riƙo tray ɗin hannunta ta ɗago da sauri alamar dawowa hayyaci, dan ya fahimci tsayuwar da tayi tunani ta tafi mai zurfi.
“Kina lafiya?”.
Ya faɗa cikin zurfin lafazi daya sakata jin wani sanyi ya dira tsakkiyar kanta yana bin jijiyoyin jikinta yana sauka har ƙafafunta. Slowly ta ɗago idanun da suka kaɗe sosai da ja a ciki, kasancewar shima ita yake kallo sai suka shige cikin nasan har sai da yaji wani dummmm a ƙirjinsa. Dai-dai lokacin Nabeeha ta matso kusa da shi, cike da salon daya ƙona ran Nimrah kawai ta rungume shi ta baya tana kwantar da kanta a faffaɗan bayan nasa. Cike da shagwaɓar iskanci ta furta, “I miss you baby”.
Gefe Nimrah tai da fuskarta tana lumshe idanunta da suka cika da ƙwalla. Dan wani suka da ƙirjinta yayi zata iya rantsewa tunda tasan kanta bata taɓa jin irinsa ba. Gaba ɗaya taji duniyar ta mata ƙunci, wani irin tsanar Nabeeha da haushin Dadan suka zagaye ƙirjinta batare data san dalili ba. Bata motsa ba a wajen da take balle nuna alamar zata fita tabar ɗakin kamar yanda ta fahimci Nabeeha naso, sai ma ji tai a ranta saita baƙanta mata rai itama, sannan wlhy bazata bar ɗakin nan ba yau sai da su zauna su ukun, in banda iskanci da ballagazanci miye na wani rungumeshi a gabanta, ai ko ba komai shi uba ne, yakamata itama ta mutunta kanta a gabansu dan su bata irin darajar da suke bashi koda bata da ita
Received at 12:22 PMa zahiri kamar shi. Amma tunda tace ita ta iya yanzu zata nuna mata shege ma da ubansa ba aruwa ake shawosa ba. ALLAH saita gogema matar nan hadda yanzun nan. Idan ita mijinta ne ai suma Babansu ne.........✍️

Tofa Madam Nimrah mutum da matarsa. Tunda kin yarda ita mijinta ne ku babanku ne basai ki fita ki barsu su jiƙa kansu ba🥱. Anya kuwa kikaji shine mijin ba akwai yaƙi ba? To bari muga ya wasan zai kaya a yanzu💃💃🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️☺️.
Received at 12:22 PM
[16/02, 10:58 pm] null: KIƊA A RUWA 3

13
Chapter 11 · 0% Book details