← Book details Kadangarun Bariki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 10

Sashe 3

Kadangarun Bariki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Rond ɗin D ɗin sa ya fara massaging har zuwa..... Ya na yi ya na sauke ajiyar zuciya, lokaci guda ya haɗa gumi kamar wanda ya haɗi kunama.
Tsawon lokaci kafin ya samu nutsuwa,wayar ya ajiye ya na mai furta "Astagfirullah!mi nayi kenan zina? Innalillahi wa'inna iley raji'un!aikin mi kake yi Ibrahim har sheɗan ya rinjaye ka?shikenan ka fara yin ɗabi'un matasan zamani masu biyawa kansu buƙata da hannu da kuma kallon finafinain turawa wanda haramci ne da idon musulmi yayi duba da irin wannan Film ɗin"
A sanyaye ya tashi ya shiga toilet ruwa masu ɗumi ya haɗa cikin bawon wanka ya shige,sai da ya gama sannan yayi wankan tsarki ya fito.
Zanen gadon ya canza ya jefa wacan cikin mashine ɗin wanki,wayarsa ya ɗauka ya goge videos duka sannan ya latsa kiran Mamy.
A sanyaye ya kira sunanta kafin tace wani abu ya tambaye ta "lafiya?wa kuma ya taɓa Daddy naji ya na masifa?"can ɓangaren Mamy tace "Imane ce ya gani a mota Jabeer su na zance shine fah"tsuki Ibrahim ya ja yace "to wai miye matsalar Daddy ne?koko shi zai aure su?haba yara sun girma ya basu dama mana can su ƙarasa karatun gidan miji"murya Daddy ya ji ya na cewa "an ƙi a basu damar karatu za su yi kuma sai sun ida,kai ba an baka damar ba amman ka ƙi fitowa da matar auren ba?"dafe kai Ibrahim yayi sam bai san a haut parleur (hand free)wayar ta ke ba.
Cikin kwantar da murya yace "Daddy ba haka ba ne su fah mata ne,rayuwar su ƴar gajera ce ba kamar namiji ba kuma tunda sun nuna auren su ke so fiye da karatu ka yi masu mana"cikin masifa Daddy yace "toh Baba wai har ku dawo daga yawan shaƙatawa sai ayi bikin ko?"ran Ibrahim ne ya ɓace yace "Allah baka haƙuri Daddy abun bai kai haka ba,amman kar ka manta Allah zai yi maka tambaya a kan su domin kuwa ta dalilin ƴaƴa dayawan iyaye za su shiga wuta"
"Innalillahi wa'inna iley raji'un ! Ibrahim ni kake kira da ɗan wuta?to yayi ka nuna min ka girma,yanzu na gane abinda yasa kai ba ka son aure ƴaƴan turawa kake lalata da su shiyasa ka zaɓi zuwa gari-gari kamar mai raba katin biki"ƙittt ya kashe wayar.

"Ya Salam!"Ibrahim ya furta ya na mai dafe kansa,shi sam bai san wane irin uba ne Mamy ta zaɓar masu ba.Sam Daddy bai da wani halin ƙwarai wanda za a iya kiransa da nagartacen uba, Istigfari ya fara saboda ya na yaye dukan wasu launuka na masifun duniya.

★★★

A nan gida Niger kuwa ganin babu mafita yasa Imane yiwa Jabeer sallama ta shiga gida.A bakin ƙofa ta tsaya ta na sauraren ruwan masifar da Daddy ke zubawa kuma da dukan alamu da Babban magajin su ne ya ke to ina ga ita wacce ita ce mafarin?
Shahada tayi ta shiga,ko ida shigo ba ta yi ba ya ɗauke ta da wani gigitacen mari wanda yasa ta ganin taurari ko kafin ta ida kuma dawowa hayyacinta ta kuma jin wani a ɗayan kumcin wanda yasa jinta da ganinta ɗaukewa.
Kafin ta tuna duniya ta ke ko lahira ya kwashe mata ƙafafu ta faɗi ƙasa nan ya fara shurar ta ya na dukanta ta ko ina sai zaginta ya ke ya na tsine mata albarka.
"Ke ga ƴar iska mai son maza shine kika hakimce a cikin motar shi a gidan gaba ku na kallon juna kamar wasu tantabaru,uwar mi ce kuke yi?miyasa ba ku shigo cikin gida ba kamar yadda kuka saba,kenan wani munafurcin ne kuka kitsa"Alhaji Mudi ke faɗa bayan ya yiwa Imane liƙis duk ya tara mata gajiya.

Ihsane da Munira tuni suka shige ɗaki suna kuka saboda ba za su iya kallo ba, Mamy ta sunne kai ta na jin zuciyarta na ƙuna sai dai babu yadda ta iya doli ta zuba ido.
Munir kuwa waya ya ɗauka ya na ɗaukar komi a sace ya na gamawa ya turawa Ibrahim ta WhatsApp,shi ma ya na jin babu daɗi sai dai babu bakin magana dan Alhaji Mudi har ƴan unguwa shayin sa suke saboda rashin mutumci bai ragawa kowa shiyasa duka gidan suke tsoron sa dama-dama Ibrahim wani sa'in ya kan ɗan tirza.

A can wajen bakin get kuwa Baba Garbati ne ke faman yiwa Alhaji Mudi addu'ar shiriya saboda kukan Imane ya game duka gidan.Ɓangaren su ya nufa inda su ke da ɗaki wanda aka kewaye da zana,Mamu na ganin shi ta shimfiɗa masa tabarma ya zauna ya na mai cewa "kai Allah shirya,sam wannan ahali ba sa cikin walwala in Alhaji ya shigo"Mamu tace "su dai suka sani duka gidan ba su da mutumci gwara ma dai wannan marar magana shi bai saka babba aiki sannan ya san darajar ƴan Adam "Baba Garbati yace "Allah yiwa Ibrahim albarka duk da yayi karatu a waje bai sa ya ɗauki kansa wani abu ba"
Mamu ta canza zancen da "Halimatu na nan tafe cikin satin nan tace sun kusa yin hutu" yace "eh haka Kawun ta ke faɗa min yace jibi da kansa zai kawota nan tunda ba ta san gidan da mu ka kuma samun wani aikin ba"
Mamu tace "Allah sarki rayuwa ni wlh ban so mu ka baro gidan su Hajiya ba dan dai kawai ka nuna mata halin na ku na Fulani taurin zuciya ka ƙi bata haƙuri"cikin fushi yace "matar da ba ta san ƙaddara ba daga an banke ni da mota shikenan sai ta yi min zamiyar kuɗin albashi ?kuma Alhaji Mudi duk rashin mutumcin shi in ka yi masa aiki ya na biyan ka kan lokaci kuma da ya banke ni da kansa ya kai ni asibiti in wani ne ai sai dai ma ya gudu"
Mamu ba tace komi ba sai ma abincin sa da ta ɗauko masa.

★★★ *DAKORO*

Wani yanki ne da ke cikin garin Maradi,ba birni ne ba sosai haka ba za'a kirasa da ƙauye ba saboda akwai wuta da ruwa.
Wata ƴar matashiyar budurwa ce baƙa mai ɗan jiki,fararen kayan Fulani ne sanye a jikinta.A ido za ka fahimci zallar kyawu da dirin da Allah ya yi mata,tsoron gaban goshinta wanda ya ke reto ta kama kafin ta riƙe ƙugu ta fara taka rawa ta na ɗan matsowa kusa da masu buga ƙwarya.

"Halimatu ga Kawu nan zuwa wlh ki fito ni dai na tafi gida"da sauri Halimatu ta fita daga filin rawar ta ɗauki bokitin da take talar ƙanƙara da gudu ta cimma,Haule wacce ke saɓe da ƙwaryar fura hannunta kuma tarmus ɗin nono.
Dariya ta tuntsire da ita ta samu wata innuwa ta zauna har Halimatu ta iso ta na cewa "Allah ya isa tsakanina da ke Haule yanzu hakan da kika yi kin gyara?"dariya Haule ta kuma tace "yi haƙuri ƴar uwa na ban kwana ne,jibi warhaka fah ki na Maradi"haka kawai Halimatu taji gabanta ya faɗi, murmurshi tayi tace "ki shirya mu tafi tare" Haule ta miƙe tace "Kawu ba zai bari ba"
"Ki dai bari mu gwada tambayarsa"cewar Halimatu da sauri tace "a'a rufan asiri"daidai nan suka kawo gida.
A zaune suka tarar da Inna matar Kawu ta na naɗe kayan Halimatu da suka bushe,zama su ka yi suka fara ƙirga kuɗin da suka yi ciniki.

A can *MAROC* kuwa sosai hankalin Ibrahim ya tashi ganin irin dukan da Daddy ya yiwa Imane ,ba tare da ya tsara komawarsa gida ba ya fara shiri.
Duk wasu takardunsa masu muhimmanci ya tattara ya zuba a trolly ya ɗauki aniyar zai yi zamansa a can ko da na 5mois ne,bayan ya gama ya zuba kayansa su ma a ɗayan akwati.

Bayan 2days

Numfashi ya ja lokacin da ya fito daga cikin Bus ɗin da ta kawo su daga Niamey zuwa Maradi .
Da sauri Munir ya ƙarasa inda ya ke ya rungumesa,kafin su ja akwatunan zuwa mota.
A hanya Munir ke ta baiwa Ibrahim labarin rayuwar gidansu,shi dai bai ce komi ba har suka kawo.
Horne Munir yayi amman tsawon minti biyu an ƙi buɗewa,daga can cikin banɗaki Baba Garbati yace "Halimatu je ki buɗe masu babbar ƙofar"
Da ɗan gudu ta fito ta nufi get ta duƙa ta na zage kubar ƙasa,idonsa ne suka sauka kan dogon tsoron kitsonta wanda ke lilo kamar zai taɓo ƙasa.Get ɗin ta wangale ta na mai komawa gefe ta riƙe porte,Munir ya danno hancin motar ciki yayinda Ibrahim ya waiga ya na mai sake kallon ta.......

Comment
and share please
[29/04 à 21:57] MRS SADAUKI 💫: *ƘADANGARUN BARIKI*💅🏻💅🏻💅🏻
```

Romantic story```👌🏻

*☀️FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATIONS ☀️*

```MRS SADAUKI 💫✍🏻```

_______________________

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR
Call 08066268951*

*PAGE* 7_8

Munir na gama parking ya fito tare da zagayawa baya dan fiddo kaya, Ibrahim kuwa ta mirror ya cigaba da kallon Halimatu wacce ta rufe get ta nufi sashen su ta na ɗan gudu hakan ya baiwa dukiyar Fulaninta yin ƙasa da bisa tamkar an busa balan-balan haka suka cika mata riga,da sauri ya janye idonsa ya na jin D ɗin sa na ɗan halbawa.
Sai da yayi kamar minti biyu sannan ya fito tuni kuma Munir ya fiddo trollyn,nan suka jera suka shiga ciki.Da murna Mamy ta tarbe sa ta na cewa "lale marhaban da Babana"ƙarasawa yayi gunta yayi mata pic a goshi kafin yace "miss You Mamyna"kumatunsa ta shafa tace "je kayi wanka ka zo na zuba maka abinci" da "toh Mamy"ya amsa kafin ya nufi part ɗin sa wanda aka gyara.Kayan jikinsa ya rage sannan ya shiga toilet ya sakarwa kansa shower,da saurin ya lumshe ido sanyin ruwan na ratsa fatar shi da sauri kuma ya buɗe su sakamakon hoton fuskarta da kuma yanayin ƙirarta ya faɗo masa "Black baby"ya furta a zuci ya na jin wani sonta ya shige sa lokaci guda.
Ya na gamawa ya fito,sai da yayi sallar Zuhur sannan ya fito falo inda ya tarar da duk iyalan gidan in ka fidda Imane wacce ke ɗaki ta na jinyar kanta.
Chapter 3 · 0% Book details