← Book details Hariji Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 20

Sashe 4

Hariji Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Dady me yasa kaimun haka? Kaine gatana dady why...ka fada mun abunda kace kana son ka fada mun " kawai sai ya fara dukan goshinsa akan qirjinsa, da qyar aka 6an6are adnan a kan sa...tundaga nan adnan bai kuma sanin inda kanta yikeba har danginsu Na saudiyya sukazo .

Sarkin kano shi ya Kira mai unguwa aka shaida masa mutuwar quliya ,saidai ance ayi hankali da ummi kasantuwar tanada juna biyu.

Hajjo da uwale suka tafi gidan gaisuwar,ummi Kam tunda quliya ya rasu kamar ya tafi da cutar haukan ta ,ta dawo garau ,saidai wani azababben laulayi ke dawainiya da ita kullum barci ,sai son abincin gargajiya much more fatan tsaki ,Haka umma za tayi mata yaji zogale da tantaqwashi ,ta zuba ,manshanu ko kakide.

Saidai abu daya yike bata mamaki yanda Sam ,quliya tsawon kwana 3 bai kirata a waya ba ,amma ta kasa fadawa ummah saboda kunya,su kuwa matan gidan da suka tafi gaisuwa bata damu da sanin Ina suke ba ,tunda tasan ba mazauna bane da ma.

Saida akayi sadakan uku kafin Adnan ke iya Zama Ana kar6an makoki dashi ,Sunga kara da jama'a ba adadi qasa qasa ,saidai sofy dukda kasancewarta ba bahaushiya ba ita ta kasance mace a cikin gidan .

Su hajjo kuma suka zauna a dakin ummi suma suna kar6an makoki ,in anzo nemarta sai ace itama taje gida jinya ,har yanzu batasan rasuwar ba

***
Ranar da quliya ya kwana goma da rasuwa ,a ranar dangin Adnan ,dasu hajjo suka biyo jirgi suka taho gidan su gabadaya

Ummi tana zaune a falo tana cin dan wake da yajin tafarnuwa sai zan yaji take yi a bakinta tana shan ruwa ,saiga sallamar baqi ,cak ta tsaya ganin larabawan dangin mijinta harda wanda bata sani ba ciki kuwa harda adnan

Murmushi tayi tana masu barka da zuwa da turanci ,su kuma su hajjo nan da nan suka kawo masu ruwa da lemu aka baza masu sababbin tabarmi Na auren uwale da za ayi .

Sunji dad'in tarban da akayi masu

Sofy a nutse ta saka ummi akan cinyarta tana shafa bayanta

Shiru ummi tayi amma haka kurum taji zuciyarta yina tsinkewa,ya nagansu dukkansu amma ba Mijina ?

Qyam ta tsaida idonta akan adnan da taga kamar har ya fada ,kuma yayi zuru zuru kamar firgitacce

"Adnan Ina dady??" Ta fada kamar wanda aka tursasata ,ta qwato maganar a bakinta .

Kallon kallo aka fara yi ,ba mai zarran bata amsa .

Ganin dakin yayi tawai tawai yasa zuciyarta yankewa ya fadi

"Adnan kayi mun shiru!" Wannan karon cike da tsawa da kakkausar lafazi tayi maganar .

Sofy da bata fahimci komai ba face Kalmar "Dady" da kuma "Adnan ".sosai ta fahimci tana tambayar adnan ne

"Ummi, Accept our condolences anty , we're sorry on behalf of late Elkabeer Ahlan musannah's Relatives and family..." Ai kafin ta qarasa maganar ta ummi ta saki wani gigitaccen qara ta miqe tana fizge fizge kafin tayi yuuu ta fadi rim sumammiya.

Tabbas ta fahimci so ake a ce mata quliya ya mutu ,to kafin a fada mata hakan gwara ta bishi .

Adnan da kansa ya miqe ya 6alle hancin

Ruwan da ke a gefensa ya kamota yina shafa mata ruwan a fuska ,wani ajiyar zuciya tayi tana sambatu "saida su Adama ,Nnenna da Abike suka kashe mun miji ,sannan hankalin su zai kwanta,Ban yafe maku ba ,kun gotarmun da gatana ,kun maida yaron cikina maraya ,Allah..allah kabi mun haqqina a kan ku!"

Umma ra6ewa tayi tana kallon innocent yarintarta tana shararar da hawaye

"Ya Isa ummi,Ba wani ya kasha dady ba ,Allah da yafimu sonsa shi ya kar6esa to ya zamuyi sai haqury mu kuma raini abunda ya bari"

"Wayyo Allah Na,adnan kace mun bai mutu ba"

"Ya Rasu!"

"Ina yike ,zan masa magana ,inaso in masa magana xakuga ya tashi bazai tafi ya barni ba..."

"Sorry ummi ,Elkabeer yina kabarinshi over 10 dayz "

"Baku fada mun ba sai yau! Saboda ni ba kowa bane a wajensa!"

Ansha artabu da ummi kafin asha wo kanta ,da ance kaza zata juya tace kaza

**
Dangin quliya da adnan suka bar Nigeria,rabon gado sai ummi ta haihu anga abun da ta Haifa ,tunda quliya ya mutu ba da ba mata sai ummi kadai,iyayensa kuma sun rasu saura en uwa ,din haka dole a jira ta haihu aga mace ne zata Haifa ko namiji

***
Ummi Sam batada nutsuwa ,abinci ta daina ci. Kullum azumi ,in an magana tace ai ko bata yi azumin ba bazata iya cin abincin ba gwara ma tayi.
Tun Ana biye mata har suka qyaleta don sun San mutuwar mijinta ke ta6a ta.

A haka bikin su uwale ya qaraso ,saidai ummi Sam ta hana en gidansu sukuni da sun shirya zasu fita yawon barikinsu zata dauko makami ta coge a qofa ,dole fita ya fasu,tunaninsu hauka ya motsa Don haka mai wada a qagauce yake ayi ayi biki ko ya samu ya ke6e da uwale don kwana biyunnan ya wujijjiga da kewarta,gashi matarsa abun sai a hankali ,a cewarsa .

Hajjo Kam sau uku Ana daidaitawa da samari kamar za ayi aure sai en Gaza gani in sunji labari su soke,yanzu hakan ta tattaro ta dawo gidansu ,don wulaqancin gidan kawunsu ya isheta ,ashe zata hadu da masifar kullen ummi , da qaryan hauka!

***
Alhmdllh duk abunda aka sanya masa rana to la shakka zai zone

A yau jumu'a tururuwan jama'a suka shaida daurin auren Alhaji maiwada da Uwale akan sadaki naira dubu saba'in ,sai dai muyi masu fatan dawwamammen zaman lafiya

Da yike aure da tarewa ne a hade ,shi yasa aka zarce da yinin biki a gidan su uwale ,en Kai kara,suka wuce jere wanda kayan gadon da set din kujerun duk Na ummi ne.

Daki Kam ya qawatu ba qarya,tunda ba kowa ma zai gane ba sababbi bane ba

Qarfe 8 Na dare akazo daukan amarya , shikam maiwada yina zaune a sitting room din sa dake kallon waje ,shida abokansa yina kallon shedanun qawayen uwale da suketa shigowa gamida cika gidan da guda, harda en daudu,wannan kuwa tawagar hajjo ne ,suka gama bidirinsu ,masu rabon samun new catchers anan suka Dane motarsu suka warwatse ,zuwa qarfe Tara da rabi kowa ya watse ,tunda bikin na bazawara ne kowa yasan ba'a kwana .

Uwale Kam suna fita ta warware kayan jikinta ta daura towel ta fito sashen ta tundaga bakin qofa ta ringa binshi da kallo tana tasbihi a ranta "oh alhmdllh ,ni uwale ashe da rabon mu ta6a ,yau nine a wannan gida ! Me haquri ke cimma rabo " saida ta kakkawar da abubuwan da aka 6ata mata ta ,qalailaye ko Ina ta feffesa room freshener ,sannan taje ta zare maganin matsin da ta saka da auduga ta wanke da ruwan dimi,ta sillo wanka a qasaitaccen toilet dinta ,ta Dada matsa Virginie cream dinta ,ta fito ta mulke jikinta da lotion me qamshi ,ta murza turaren humrah masu qamshi ta saka chewing gum me kamshi

Wata damammen fitted gown din doguwar riga ta saka Na Atamfar ingilish ,ta tokaro daurin Ture kaga tsiya ,wanda yayi fadi sosai. Sannan ta fara ferfesa turare tundaga cikin pant dinta har sama ,wani juyo tayi a gaban mirrorn da ya kasance murfin drawern ta
"Wow uwale kinyi ne,allah dai ya bada zaman lafiya" ta shiga kuzanta kanta tana Dada cincida nononta da Tasha masu magani sukayi cif cif ,suka dad'a kumbura .ga mazaunanta sun bayyana sosai ,saboda yanayin style Din,dan matashin tumbinta ya lafe,kai dadai uwale natsatsace to da anyi mace a wajen.

Duqawa tayi tana neman mayafin da zai shiga Da kayanta sai jin turo qofa akayi

"Amarya..Amarya! ,Amarya kinsha qamshi" ya fad'a yina kwanto mata ta baya.

"Angona,nayi kewarka"

"Ba wani nan ,jiki har wani qiba kikayi ,an gama yimun Rowan Duri,to yanzu dai nawane ko? "

Tasowa tayi tana girgiza ta juyo gamida rungumosa sosai a jikinta ta tokaro masa nonuwanta a fuskarsa

"Hmmm wallahi munga jarabta,wato haukan ummi bayi tashi sai taji anyi sallama damu nan zata zare wuqa ta fita bakin qofa ,tana zare ido ,ka hareta ta luma maka...don wallahi rannan da kwadayin 🍌ya ishi hajjo ta Katanga ta haura tana kuka ,ta tafi yawon wanda zata rabawa taji dad'i "

Dariya ya saki "A'ah kuce gadinku ake yi haiqam,wallahi har Na tausayawa hajjo amma mudai yanzu kwana nan uni ,ko ya kika ce"

"Qwarai kuwa my one"

Jan hannunta yayi ta dakko mayafinta suka fito falo ,abokansa suka yi masu barkwanci aka Kira uwargida aka masu nasiha kan su hade Kansu ,daga nan ta miqe cikin dakiya zata fita ,lokacin da abokan suma sukayi yunkurin tafiya

"Ki jira inada magana daku in sun fita" ya kalli uwargidan tasa yina bata umurni

Jinjina kai tayi hawaye kwance a qwarar idonta"allah ya bani ikon yi maka biyyaya iyakan iya wata mijina". Ta ke addu'a a ranta

Cikin kwarkwasa uwale ta miqe ta kalli abokan nasa "baqinmu har xaku wuce ,to bari in Baku abun dakin amarya mana "

Ta shiga store ta ringa cicciko manyan jakan biki da abubuwan fulawa irinsu dubulan ,cake,cincin da su ridi sai ruwa da caparison

Kowanne ta mimmiqa masu suka wuce suna zumbuda masu godiya da addu'ar qazantar daki

Ita dai uwargida luf tayi ranta yina mata suya ,Sam sunma manta da ita,din haka ba wanda yayi mata sallama , shikuwa bai masu rakiya ba,saboda cewa sukayi sun hutashshe shi

Gyaran murya yayi ,to ku nannatsu inada en bayanai da zan maku

Fari tayi da Ido "to me gida zan iya kauda wa'innan plates din?"ta kashesa da idonta mai dauke da ruwan jaraba

Cikin mataccen jiki ya gyada mata Kai ,aikuwa ta wuce duwaiwanta suna sixteen , seventeen cikin matsetsen kayanta ,kallon ta ya ringa yi da tayi kwana haka yayi karka ta kansa ta bayan kujeran yana kallon ta

Ganin ya sha'afa gabadaya yasa tayi gyaran murya "Maiwada a ringa adalci don rashinshi ,shi ya halaka maza da yawa zuwa wutan jahannama"

"Ke bankaura ,karki 6ata mun rai da baqaqen maganarki,kina dai kallon yanda akaiyi ilimin ririta miji,ga kaya Kota Ina daidai hutawan ingarman miji kamana bakeba ,a bushe a qwanjale kamar muciya ,Ina maki addu'a,allah yasa albarkacin sweety Na ki gyara abunda kikeyi
Chapter 4 · 0% Book details