Sashe 8
Hamshaƙiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jamila tana wanke wanke ni kuma ina wanke kayan su Jafar ina shanya yau asabar ce ba makaranta. Yaro ya shigo da sallama ya ce wai ana magana da Abbanku nace,ya tafi aiki. Jim ƙaɗan yaro ya zo Baby wai kizo a baki saƙo nace to.Nace inji wa? Yace wani mutumi ya fita. Na saka hijabi na fita zuciyata ta na zolayar wai ace inga Yaya. Me zai zo yi da safe nan. Tunanina ya tsaya cak, lokacin da mukayi ido huɗu da Yaya sanye da Jallabiya blue mai gajeran hannu sak irin alhazan birni idan ka kalleshi. Tsoro ya tsirga min me Yaya yazo yi yanzu? Ya katse ni da faɗin "Ƙaraso mana gurin Abba na zo ashe har ya fita?" Nace amma dai lafiya ko? Na tambaya idanu na ƙir a kansa. Yace "Lafiya ba lau ba." Na zaro idanu tare da faɗin Meyafaru. "Ƙara so mana Baby ." Na isa gurin shi a gigice,zuciyata na ayyana min yazo ya ba Abba haƙuri cewa aurenmu ba zai yi wu ba. Nace menene ban yi daidai ba Yaya?Wai kafasa ne? Yace "Mu fara da gaisuwa an tashi lafiya?" Nace lafiya ina kwana? Yace "Lafiya lau ya lura na fita hayyaci na yace "Ki daina damuwa ba wani abu bane, jiya da naje gurin maman Ogana shine ta ce tana son ta ganki wai yau ko gobe, ni kuma ina tunani nasan baza a barki kije ba,shine na zo in tambayi Abba da kai na, ko Allah zai sa ya yarda." Nace wai gaskiya ko da kuɗin ka a gidanmu hatta Umma baza ta bari ba bare kuma Abba, kan wannan maganar ma sai kaga an fasa auren nan,ka bata haƙuri kuma zata fahimta tunda itama Uwa ce kuma abinda ke faruwa a zamanin nan kowa ya sanshi.Kuma ka faɗa mata bamu daɗe ba.
Ya ɗan yi shiru, can ya ce "Baby akwai matsala ne, za a iya samun cikas in har baki je ba, saboda ita ta zata mun daɗe domin na jima ina ce mata ina da budurwa, kuma zata sanar da mai gida cewa ban kai ki ba, kuma maigidana shine jigon bikin nan,sai ki ga kan wannan yabar maganar nan inje ga wata to abin da nake tsoro kenan." Na zuba mishi ido cike da zargi,kodai cutar da ni zai yi ya dage haka,ƙila ma sai da yaga fitar Abbanmu sannan ya zo dan ya yaudare ni. Nace Humm Yaya ka yi haƙuri gaskiya ni kai na na soma zargin wani abu, dan Allah kar ka cutar da ni wallahi ina son ka da gaske... "Cutarwa kuma Amira? Me zai sa in cutar da ke kuma meye ribar hakan idan nayi? Ba ɗan iska bane ni ban taɓa zina ba ko lokacin da ina saurayi, kuma bazan fara a yanzu ba. Ko zan yi Baby ai ba zan yi da matar da zan aura ba." Na sauke lumfashi Yaya bazan hana zuciyata yin kowane irin hasashe ba,sai dai in ƙi gaskata abinda ta hasaso. Ka yi haƙuri ko ƙanwarka ce in ka mai da abin a kan ta zaka ga ba za ka amince da irin hakan ba. Ya sunkuyar da kai "Kin fini gaskiya ko ta wane fanni Baby amma taimakon da za kimin ciki harda sana'a ta. Mahaifiyar maigidana mace ce mai kirki da mutunci,ta ɗauke ni kamar ɗanta. To tana da irin nata ƙa'idojin dan Allah ki taimakawa mijinki." Zuciya ta ta soma tunanin munafurtar iyayena, amma ta Yaya kuma wane tabbaci ne da ni kan cewa bazai cutar da ni ba? Ya sake katseni "Nasan haka rashin kyautata ne musamman ga iyaye amma sadaukarwa a soyayya ibada ne, kuma ɗan gyaran babbar ɓarna yin ƙaramin kuskure ba aibu bane. Wallahi ki yarda da ni Rabi'atu wallahi ba zan cuce ki ba." Na zuba mishi ido wata ƙaunarshi na ke ji a zuciyata ga tausayin shi kamar inyi kuka. Na sauke a jiyar zuciya. Yaya Aliyu ban taɓa yi wa iyayena ƙarya ba, kuma ban taɓa munafurtar su ba, zan sadaukar kan so da ƙauna,zan munafurce su so ɗaya a yau kuma zan musu ƙarya, amma karka maida hakan ya zama nadama a gurina ka tabbatar da kyau tata maka zato da na yi. Na shirya sai ka tsara min yadda zan yi duk abinda kake so batare da sanin iyaye na ba.
Ya sauke wata ajiyar zuciya "Alhamdulillah! Kina da ƙawa wadda za kuje tare domin ki ƙara samun mutsuwa?" Na girgiza kai, ba ni da ƙawa. Yace, "To Jamila fa? Kiyi magana da ita matsayin ta na 'yar uwarki zata iya fahimtar ki sai kuje tare, matsalar ina zaki ce zaku?" Na ce Yaya komai zai faru da ni ni ce mai son ka don Allah banda Jamila. Yayi 'yar dariya kirata nace kibar wannan a hannu na zamu yi magana anjima a wayar Umma sai dai muje gobe kenan.
Yace yauwa daidai ke nan gobe bamu cika fita kasuwa da wuri ba,insha Allahu zan kira muyi magana. Mukayi sallama ya ce in shiga gida kafin nan ya wuce.
Jamila tana shara na shigo ta dube ni,"Lafiya Yaya Baby naganki sukuku haka? Nazo na leƙo naga saurayin ki da safen nan. Nace Umma bata tashi ba? Tace e kinsan sai gurin shaɗaya zata farka, na nufi ɗakinmu na dubi Jamila na ce,zo. Ta saki tsintsiya ta shigo cike da fargaba tana faɗin wai ya fasa ne Yaya Baby? Na ce zauna, muka zauna kan katifa, na ce Mahaifiyar maigidana ce ke son gani na, in ba haka ba zata bashi wata,kuma inya bijire zai iya rasa aikinsa. Jamila tace "To kije mana." Nace baki da hankali su Umma baza su bari ba, shine nike tunanin yadda za ayi ki raka ni batare da sun sani ba,sai muce zamu je gaida su Baba kinsan Abba zai yarda sai muje gidan daga can sai muje mu gaida su Baba ɗin ko? Jamila ta ce haka ne, amma kafin lokacin islamiyya zamu dawo gara ke maraja'ar sauka kuke yi." Na ce ba damuwa,zan faɗa masa, amma sai mun ji ta bakin su Umma. Bayan Isha'i ya kira ni na faɗa masa duk yadda muka yi,kuma na faɗawa Umma ta ce mu tambayi Abbanmu. Yace "Na gode sosai,amma ita Baba ɗin wacece? Nace ita ce ta riƙe Ummanmu har ta aurar da ita bayan rasuwar mahaifiyar ta,kuma mun jima bamu je ba,tana son mu sosai. Yace Ni ma ya kamata inje in gaisheta wata rana nace gaskiya ne. Yace "Wace unguwa take?" Nace Kurna ta ke, yace "To ba matsala gobe kamar ƙarfe nawa zaku fito?" Na ce kamar shaɗaya Ummanmu ta farka a bacci mu kuma mun gama aiki, ya ce haka yayi zan zo amma sai dai in tsaya can gurin ƙofar fanfo sai ku zo mu wuce." na ce to. Bayan mun yi sallama na damu sosai yadda zan ha inci iyaye na amma sai wata zuciyar tace khairan insha Allah. Abba yana cin abinci Jamila ta ce Abba zamu samu kuɗin mota gabe muje mu duba Baba tunda ta yi zazzaɓi nan Ummanmu bata samu zuwa ba muma haka, yace to zan sama muku, daga nan kwa bata labarin saurayin na Baby kar taji daga sama. Umma tace aiko aji murna gurin Baba,bata da burin da ya wuce auran Baby. Ni dai duk tausayinsu nake ji domin na ha'ince su.
Washe gari Abba ya bamu na mota sannan ya bamu ɗari biyar ya ce mu bata. Umma kuma ta bamu Naira ɗari ta ce mu sai mata goro. Jamila dama ta saƙe wayar Umma sai da muka fita ƙofa muna gefen babban titi sanna nace Jamila yanzu yaya za ayi Yaya yasan mun fito? Ta ciro wayar Umma ta miƙo min tare da faɗin "Taimakon farko." Na karɓa tare da faɗin na shiga uku,in Umma ta nema fa.? Jamila tayi dariya wa ke kiranta banda Abba sai kaɗan daga dangi, ƙila har mu dawo ba a kira ba, in ma an kira zamu ɗaga muce tana gurin mu. A zuciya ta nace in ma munga zai cutar damu sai mu kira Abba. Na kira shi na ce mun fito ya ce to ku samu keke kuce Janbulo ƙofa ta biyu ni sai zan jira ku a daidai BUK tsohuwa. Muka ce to.
Cikin sauri yake shiri tun jiya ya sanar da Hajiya cewa su Rabi"a za su zo yau da misalin shabiyu saboda islamiyya ta ce Allah ya kawo su, dan haka ta soma duk wani shirinta. Sun sake kira shi da suka zo inda ya kwatanta musu,sai yace Kuɗan jira,ko da yake ba mai adaidaita sahun mu yi magana." Na bashi ya yi masa kwatance ya ce ya gane,sai yace ya bani wayar,na amsa sannan yace zai kawo ku kusa da gida sai mu ƙarasa. Mun tsaya kusa da wata baƙar mota sai kiranshi ya shigo kune kuka tsaya yanzu naɗan leƙa ko zan ganshi ina fadin e mune. Sai naga ya buɗe motar ya fito yazo yace wannan motar tace ku biyomu. Na ce to cikin fargaba. Gaban wani damfareren gida muka tsaya ga wani ƙaton gate kamar ƙofar kasuwa, dan ƙareren masallacin da na kalla a jikin gida kuma fentinsu iri ɗaya shine ya sa na ɗanji sauƙin fargaba. Mai gadin ya buɗe,naga anyi masa magana daga motar sai ya nufo gurin mu yace da mai keke ya shiga. Muka shiga hamshaƙin gidan mai keke yace ashe zan shiga gidan Hajiya ZEENA a rayuwa. Nace kasan ta ne? Yace e mana masu ZEENA Foundation ina ne ba'a san su ba a ƙwaryar Kano.Har muna haɗa baki gurin faɗin muna jin tallolinsu a Radio muka tsaya nace nawa ne kuɗin? Yace bari Alhaji ya bani nan gidan ai ba 'a rowa. Nace Alhaji baya nan wannan yaro shagon sa ne. Daidai lokaci da Yaya yace Amira,na waiwaya, ya yafito ni da hannu naje gurin sa yace nawa ne kuɗinsa? Na ce yaƙi faɗa, yace to tsaya nan ina Jamilar kirata bari inje gunsa. Nace Jamila zo,ta fito shi kuma ya nufi gurin mai keke,abinda yake gudun shi ya faru,mekeke ya soma faɗin ranka ya daɗe ina gaisuwa Shamaki ya ciro kuɗi bai ƙirga ba ya bashi tare da faɗin jeka Allah ya tsare. Shiyasa ya yanke shawarar ƙin jiransu domin tabbas mutane za su gane shi kuma komai zai fallasa.Ya shiga gaba ku zo muje.
Ya ɗan yi shiru, can ya ce "Baby akwai matsala ne, za a iya samun cikas in har baki je ba, saboda ita ta zata mun daɗe domin na jima ina ce mata ina da budurwa, kuma zata sanar da mai gida cewa ban kai ki ba, kuma maigidana shine jigon bikin nan,sai ki ga kan wannan yabar maganar nan inje ga wata to abin da nake tsoro kenan." Na zuba mishi ido cike da zargi,kodai cutar da ni zai yi ya dage haka,ƙila ma sai da yaga fitar Abbanmu sannan ya zo dan ya yaudare ni. Nace Humm Yaya ka yi haƙuri gaskiya ni kai na na soma zargin wani abu, dan Allah kar ka cutar da ni wallahi ina son ka da gaske... "Cutarwa kuma Amira? Me zai sa in cutar da ke kuma meye ribar hakan idan nayi? Ba ɗan iska bane ni ban taɓa zina ba ko lokacin da ina saurayi, kuma bazan fara a yanzu ba. Ko zan yi Baby ai ba zan yi da matar da zan aura ba." Na sauke lumfashi Yaya bazan hana zuciyata yin kowane irin hasashe ba,sai dai in ƙi gaskata abinda ta hasaso. Ka yi haƙuri ko ƙanwarka ce in ka mai da abin a kan ta zaka ga ba za ka amince da irin hakan ba. Ya sunkuyar da kai "Kin fini gaskiya ko ta wane fanni Baby amma taimakon da za kimin ciki harda sana'a ta. Mahaifiyar maigidana mace ce mai kirki da mutunci,ta ɗauke ni kamar ɗanta. To tana da irin nata ƙa'idojin dan Allah ki taimakawa mijinki." Zuciya ta ta soma tunanin munafurtar iyayena, amma ta Yaya kuma wane tabbaci ne da ni kan cewa bazai cutar da ni ba? Ya sake katseni "Nasan haka rashin kyautata ne musamman ga iyaye amma sadaukarwa a soyayya ibada ne, kuma ɗan gyaran babbar ɓarna yin ƙaramin kuskure ba aibu bane. Wallahi ki yarda da ni Rabi'atu wallahi ba zan cuce ki ba." Na zuba mishi ido wata ƙaunarshi na ke ji a zuciyata ga tausayin shi kamar inyi kuka. Na sauke a jiyar zuciya. Yaya Aliyu ban taɓa yi wa iyayena ƙarya ba, kuma ban taɓa munafurtar su ba, zan sadaukar kan so da ƙauna,zan munafurce su so ɗaya a yau kuma zan musu ƙarya, amma karka maida hakan ya zama nadama a gurina ka tabbatar da kyau tata maka zato da na yi. Na shirya sai ka tsara min yadda zan yi duk abinda kake so batare da sanin iyaye na ba.
Ya sauke wata ajiyar zuciya "Alhamdulillah! Kina da ƙawa wadda za kuje tare domin ki ƙara samun mutsuwa?" Na girgiza kai, ba ni da ƙawa. Yace, "To Jamila fa? Kiyi magana da ita matsayin ta na 'yar uwarki zata iya fahimtar ki sai kuje tare, matsalar ina zaki ce zaku?" Na ce Yaya komai zai faru da ni ni ce mai son ka don Allah banda Jamila. Yayi 'yar dariya kirata nace kibar wannan a hannu na zamu yi magana anjima a wayar Umma sai dai muje gobe kenan.
Yace yauwa daidai ke nan gobe bamu cika fita kasuwa da wuri ba,insha Allahu zan kira muyi magana. Mukayi sallama ya ce in shiga gida kafin nan ya wuce.
Jamila tana shara na shigo ta dube ni,"Lafiya Yaya Baby naganki sukuku haka? Nazo na leƙo naga saurayin ki da safen nan. Nace Umma bata tashi ba? Tace e kinsan sai gurin shaɗaya zata farka, na nufi ɗakinmu na dubi Jamila na ce,zo. Ta saki tsintsiya ta shigo cike da fargaba tana faɗin wai ya fasa ne Yaya Baby? Na ce zauna, muka zauna kan katifa, na ce Mahaifiyar maigidana ce ke son gani na, in ba haka ba zata bashi wata,kuma inya bijire zai iya rasa aikinsa. Jamila tace "To kije mana." Nace baki da hankali su Umma baza su bari ba, shine nike tunanin yadda za ayi ki raka ni batare da sun sani ba,sai muce zamu je gaida su Baba kinsan Abba zai yarda sai muje gidan daga can sai muje mu gaida su Baba ɗin ko? Jamila ta ce haka ne, amma kafin lokacin islamiyya zamu dawo gara ke maraja'ar sauka kuke yi." Na ce ba damuwa,zan faɗa masa, amma sai mun ji ta bakin su Umma. Bayan Isha'i ya kira ni na faɗa masa duk yadda muka yi,kuma na faɗawa Umma ta ce mu tambayi Abbanmu. Yace "Na gode sosai,amma ita Baba ɗin wacece? Nace ita ce ta riƙe Ummanmu har ta aurar da ita bayan rasuwar mahaifiyar ta,kuma mun jima bamu je ba,tana son mu sosai. Yace Ni ma ya kamata inje in gaisheta wata rana nace gaskiya ne. Yace "Wace unguwa take?" Nace Kurna ta ke, yace "To ba matsala gobe kamar ƙarfe nawa zaku fito?" Na ce kamar shaɗaya Ummanmu ta farka a bacci mu kuma mun gama aiki, ya ce haka yayi zan zo amma sai dai in tsaya can gurin ƙofar fanfo sai ku zo mu wuce." na ce to. Bayan mun yi sallama na damu sosai yadda zan ha inci iyaye na amma sai wata zuciyar tace khairan insha Allah. Abba yana cin abinci Jamila ta ce Abba zamu samu kuɗin mota gabe muje mu duba Baba tunda ta yi zazzaɓi nan Ummanmu bata samu zuwa ba muma haka, yace to zan sama muku, daga nan kwa bata labarin saurayin na Baby kar taji daga sama. Umma tace aiko aji murna gurin Baba,bata da burin da ya wuce auran Baby. Ni dai duk tausayinsu nake ji domin na ha'ince su.
Washe gari Abba ya bamu na mota sannan ya bamu ɗari biyar ya ce mu bata. Umma kuma ta bamu Naira ɗari ta ce mu sai mata goro. Jamila dama ta saƙe wayar Umma sai da muka fita ƙofa muna gefen babban titi sanna nace Jamila yanzu yaya za ayi Yaya yasan mun fito? Ta ciro wayar Umma ta miƙo min tare da faɗin "Taimakon farko." Na karɓa tare da faɗin na shiga uku,in Umma ta nema fa.? Jamila tayi dariya wa ke kiranta banda Abba sai kaɗan daga dangi, ƙila har mu dawo ba a kira ba, in ma an kira zamu ɗaga muce tana gurin mu. A zuciya ta nace in ma munga zai cutar damu sai mu kira Abba. Na kira shi na ce mun fito ya ce to ku samu keke kuce Janbulo ƙofa ta biyu ni sai zan jira ku a daidai BUK tsohuwa. Muka ce to.
Cikin sauri yake shiri tun jiya ya sanar da Hajiya cewa su Rabi"a za su zo yau da misalin shabiyu saboda islamiyya ta ce Allah ya kawo su, dan haka ta soma duk wani shirinta. Sun sake kira shi da suka zo inda ya kwatanta musu,sai yace Kuɗan jira,ko da yake ba mai adaidaita sahun mu yi magana." Na bashi ya yi masa kwatance ya ce ya gane,sai yace ya bani wayar,na amsa sannan yace zai kawo ku kusa da gida sai mu ƙarasa. Mun tsaya kusa da wata baƙar mota sai kiranshi ya shigo kune kuka tsaya yanzu naɗan leƙa ko zan ganshi ina fadin e mune. Sai naga ya buɗe motar ya fito yazo yace wannan motar tace ku biyomu. Na ce to cikin fargaba. Gaban wani damfareren gida muka tsaya ga wani ƙaton gate kamar ƙofar kasuwa, dan ƙareren masallacin da na kalla a jikin gida kuma fentinsu iri ɗaya shine ya sa na ɗanji sauƙin fargaba. Mai gadin ya buɗe,naga anyi masa magana daga motar sai ya nufo gurin mu yace da mai keke ya shiga. Muka shiga hamshaƙin gidan mai keke yace ashe zan shiga gidan Hajiya ZEENA a rayuwa. Nace kasan ta ne? Yace e mana masu ZEENA Foundation ina ne ba'a san su ba a ƙwaryar Kano.Har muna haɗa baki gurin faɗin muna jin tallolinsu a Radio muka tsaya nace nawa ne kuɗin? Yace bari Alhaji ya bani nan gidan ai ba 'a rowa. Nace Alhaji baya nan wannan yaro shagon sa ne. Daidai lokaci da Yaya yace Amira,na waiwaya, ya yafito ni da hannu naje gurin sa yace nawa ne kuɗinsa? Na ce yaƙi faɗa, yace to tsaya nan ina Jamilar kirata bari inje gunsa. Nace Jamila zo,ta fito shi kuma ya nufi gurin mai keke,abinda yake gudun shi ya faru,mekeke ya soma faɗin ranka ya daɗe ina gaisuwa Shamaki ya ciro kuɗi bai ƙirga ba ya bashi tare da faɗin jeka Allah ya tsare. Shiyasa ya yanke shawarar ƙin jiransu domin tabbas mutane za su gane shi kuma komai zai fallasa.Ya shiga gaba ku zo muje.