← Book details Hamshaƙiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 18

Sashe 7

Hamshaƙiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

🖊️🖊️🖊️
[6/16, 19:58] Ummi Tandama😇: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻*

*NA*

*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*

_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_

*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_

*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*

*Free Page 5*

Umma tana kaɗa miyar kuka ta bini da kallo, "Shine baki shigo gida ki sanar cewa kin dawo sannan ki canza kaya ki fita gunsa ba, sai kitsaya da kayan makaranta. Nace,to Umma ba zan sake ba amma cewa ya yi yana sauri. Naje na miƙa mata kuɗin da ya bani,ta amsa tare da faɗin "Wannan kuma na menene?" Nace wanda ya ce zai bani ne na walima. Umma tace "Ni Salmai wannan wane irin mutum ne ko sati guda fa ba kuyi da haduwa ba. Nace in na ce ya barshi sai ya haɗe rai. Jamila da ke alwalla tace, Umma kinsan wasu mutanan ma su yi ne, Yaya Baby ta yi dace. Umma ta ce "Allah ya zaɓa mafi alkhairi shinkafa 'yar gwamnati gata can amshi kuɗin nan ki kai ki adana a cikin wannan jakata. Allah ya sa kar Malam ya yi faɗa." Na ce to. Gaskiya na yi farin cikin ganin Yaya da rana, na ɗakko hodar Umma na kalli fuskata a madubi ko me yaya ya gani yake sona Ni ba dogo hanci ba, kuma ba manyan ido ba, amma ina da gashin gira sai ƙananan haƙora da kuma wushirya. Muryata ma ina jin ana fadinta, bazan ce komai ba game da surar jiki domin yanzu ne maƙerin ya ke ƙirar.
Shamaki ya yanke shawarar zuwa gurin Baby ne dan baya son Hajiya ta ci gaba da nuna damuwa tun a tashin farko. Ya fi son komai ayi cikin daɗin rai to kuwa dole ya danne zumuɗin shi game da Baby. Lokacin da ya shiga bayan ya kammala da mabuƙata suna cin abinci ta ji bai yi batun yarinyar ba sai ta ce, ɗazu Maman Umar ta ke faɗa min ta maka budurwa ko? Ya ce "Haka ta faɗa amma ta zo a makare, tunda mun gama magana da Baby har ta sanar da mahaifanta cewar zan turo, na ce a cikin satin nan in kun ga hakan ya dace." Hajiya ta yi shiru kamar bataji me ya ke faɗa ba, sai kusan minti biyu har ya gama yanke hukuncin bazata yi magana ba wanda yin hakan alamune na babbar matsala,sai yaji ta ce, "Yaushe za ka kawo ta in ƙara auna yiwuwar abin?" Ya ce yaushe ki ke so,amma ina tsoron ban jima da soma zuwa ba, iyayenta ba lallai su amince su barta ta zo ba. Sai dai zan jaraba yin magana da mahaifinta. Hajiya ta ce za a kai kuɗine bayan ta lashe jarabawar da zan yi mata. Shamaki ya kalli Hajiya sannan soma tunani wace jarabawar ita kuma za 'a yi mata?.
Chapter 7 · 0% Book details