Sashe 6
Hamshaƙiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[6/16, 19:58] Ummi Tandama😇: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕ðŸ»*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*
_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_
*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_
*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*
*Free Page 4*
Ta amsa gaisuwarsa tamkar ba wani abu, suka ci gaba da lissafin da ya kamata ace sun yi a jiya. Ya saki jiki ya karya duk da ta gano cewa ya yi ne domin ta huce daga saɓa matan da take ganin ya yi, amma ta ji daɗin hakan. Ya so matuƙa ta tambaye shi wani abu game da Baby domin ya faɗa mata yana son a tura a cikin satin amma ta ƙi maganar sam,wanda hakan ya sa dole ya bari sai zuwa yamma, duk da tana son taji yadda suke ciki amma ta bari sai ta ji daga Malam. Su Meema suka shigo da gudu duk suka nufi Hajiya suka tsugunna suka gaisheta, ta shafa kansu tare da yi musu addu'o'in da ta saba,sannan suka nufi jikin Dadin su suka gaida shi,ya amsa tare da sa musu albarka Rahin ta fito da kwandunan su da jakunkuna Azima ta kama musu hannu suka wuce suna ɗagawa Dadinsu da kakarsu hannu. Shamaki ya sallami Hajiya ya koma ɗaki don ya shirya ya fita kasuwa. Komai ya ke yana tuna Baby so biyu yana ɗaukar wayar sai ya danna kiran layin Umman su sai kuma ya katse. Ana ukun ya jure tayi ta ringin aka ɗaga tare da sallama. Ya amsa Umma ce, ya gaida ta cikin ladabi, ta amsa cike da jin kunya.ta ce "Sun tafi makaranta kasan ita jarabawa ta ke yi ta fita." Ya ce e ta faɗa min Umma, Allah ya bada nasara, dama na kira ta ne mu gaisa a gaishe su. Umma ta ce "Ba komai a gaida magabatan da kyau don Allah" Yace za suji, ya kashe wayar ya shirya ya fita. Hajiya tun tana sallar walaha wayarta ke ƙara, sai da ta idar ta yi addu'a sannan ta miƙa hannu ta ɗakko wayar Malam ne,don haka sai ta danna kiran shi,ya ɗauka suka gaisa ta tambaye shi abinda ya fuskanta game da binciken, yace "To alal haƙiƙa Hajiya abinda na gani shine, abu na farko dai aure babu fashi, abu na biyu kuma taurarin yarinyar masu haske ne sosai tana tare da arziƙi irin su ko matsiyaci suka aura albarkacin su yana ganin faraga, mai arziƙi kuma tamkar wuta ce sai a zuba mata fetur a bin nufi akwai alkhairi tare da ita,abu na uku Allah ya ɓoye min ban fuskance shiba amma shima ina zaton alkhairi ne,sannan yana sonta sosai irin wanda in ya rasata zai cutu kuma irin wannan son ba zai taɓa ganin aibunta ba ko da ita bata son shi. Wannan sune abubuwan da na gani." Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce Malam kuma an bincika ba wani asiri ta yi masa ba? Malam yace "Abinda na fara dubawa kenan ita yarinya komai nata a rufe ya ke abin nufi bata taɓa ziyarar wani malami ba domin wani aiki. Sam babu kuma wata niyya ta cutar da shi ko kaɗan." Hajiya ta sauke ajiyar zuciya,shike nan Malam a tayamu da addu'a ita ma ta kamu da son shi fiye da wanda yake mata, yace "Wannan mai sauƙi ne in har za taci abin da zan kawo." Hajiya tace ina zan ganta har wani taci wani abu? Amma ka kawo ɗin sai muga ya za ayi. Yayi yar dariya "Hajiya ko gida zaku iya aikawa,kuma koda kowa yaci bazai yi aiki akan saba sai ita da akayi da sunanta sai dai matsalar in har wata mai irin sunanta ta ci to ita ma zata kamuwa da sonsa." Hajiya tace babu damuwa ka aiko ɗin zan san yadda za ayi amma shi abin menene? Yace,Dabino ne ƙwaya bakwai da za a samu ta ci duka zai wahala in bata zo ta tare a gidan ba kafin bikin kamar tai masa sujada haka zaki ga tana yi. Hajiya ta ce na gode sosai Suka yi sallama. Hajiya ta lushe ido ta nutsa cikin tunani, tabbas zata barshi ya auri yarinyar amma dole ta so shi da yawa domin bata buƙatar ta janye masa hankali. Duk da hakan kuma zata sa shi ya kawo mata yarinyar ta ga wace irin wayewa ce da ita wadda har ta ɗaukar masa hankalin yaro haka. Dole sai ta gano wasu abubuwa game da yarinyar domin ta saita mata sahunta don bata son rawar kai. Kuma ta gane ba a mulki sarakuna biyu aka karaga ɗaya. Sam bataji sallamar Anty Zainab ba sai gaisawa da taji suna yi da Juma. Ta buɗe ido ta kai kallo inda taji muryar Zainab ɗin, ta ɗago ta gyara zama tana faɗin yaushe kika shigo Maman Umar? Anty Zainab dake zaune can gefe cikin girmamawa tace "Naga kuna ɗan gyangyaɗi ne shiyasa na yi shiru." Ta gaida Hajiya cikin girmamawa. Hajiya tana tambayar yara, tace duk suna makaranta. Anty Zainab ta kira Juma tace ki zo ki ɗau ledar can ki wanko wa Hajiya tuffa da Inibi har gwabar da fiyar sai ki haɗo mata. Juma ta ɗauki ledar ta fita. Hajiya ta kalli babbar 'yartata tace Maman Umar Allah ya yi albarka har Fiya ta shigo kenan ta ce "Ta shigo nima jiya naje Store in duba jadawalin abinda ake buƙata shine naga sunsa harda Fiya a ɓangaren 'ya'yan itatuwa." Shine nace bari inje in duba miki a wani gurin." Hajiya ta ce Allah ya jiƙan mahaifinku. Zainab ta ce "Ameen Hajiya Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana. Sannan ta gyara zama ta ci gaba da magana. "Hajiya wata yarinya na gani na yiwa autanki shi'awa yarinyar tana da hankali sosai kuma tana da ilmi duka biyu,kuma iyayen ta dattawa ne, Babanta Farfesa ne a BUK." Hajiya ta ce,to ki kira shi ki faɗa masa in ya amince sai yaje ya ganta. Kira shi yanzu kiji amsar da zai baki.
Zainab ta kira wayar Shamaki na farko ta katse na biyu ya ɗauka tare da faɗin "Anty Maman Umar ya gida ya yara?" tace lafiya lau autan Hajiyarmu ƙaraminmu babbanmu. Suka yi 'yar dariya ya saba da wannan kirarin nasu, musamman tunda shike sa hannu a duk wani kuɗi in zai fita daga ko wane sashen ZEENA. Tace Shamaki mata na samo maka mai hankali,ga kyau 'yar gidan ilimi. Yayi 'yar dariya "Kin makara Anty,dan cikin satin nan za a kai kuɗina an bada ni Anty." ya kai ƙarshen maganar cikin tsokana. Ta ce bafa wasa nake ba, shima yace"Allah da gaske na ke yi kuma dama na daina auren haɗi abarni in gani da kai na." Tace shikenan amma duk da haka ka zo gidana zan sa a kira ta sai ka ganta,dama ban musu magana ba, bari na yi inji ta bakinka. Yace Ba sai na ganta ba, domin bazata kai Amira a komai ba, na gode da kulawa zanzo mu yi maganar yadda za a haɗa min lefe irin na yar manyan mutane,dattijai." Tace shike nan sai na jika suka yi sallama. Ta dubi Hajiya ,ashe ya samu? Hajiya ta ce shiyasa na ce ki kira shi,saboda wata irin soyayya naga ya fara mai ban tsoro ku taya shi da addu'a, bana son ya kawo macen da soyayyar ta zata kawo mana hari a cikin gidan nan, ina nufin ta yi amfani da hakan ta cutar damu, Shamaki shine jigon gidan kin san dai abinda nake nufi."Anty Zainab ta ce haka ne,to anyi bincike a unguwar su? Hajiya ta ce na kammala da duk wani bincike bana buƙatar inji me mutanen unguwarsu za su faɗa, yanzu kawai ina son ya dawo in faɗa masa,ya kawo min ita ne in yi mata jarabawar ƙarshe in ta haye shike nan in yana buƙata sati ɗaya kacal za a iya ɗaura musu aure in haka ya yi wa iyayenta. Zainab ta san Hajiya ta ƙare magana don haka ta ce Allah ya sanya alkhairi. Ameen Hajiya ta amsa tare da saka yankar fiya da aka jere mata a cikin tire. Anty Zainab ta tashi bari in shiga kicin ko akwai abinda zan iya ci a abincin gidan. Hajiya dai ta maida kanta ga TV inda wani malami ke nasiha ga 'yan mata masu fitowa suna fitsara a manhajar TikTok. Anty Zainab ta fito ɗauke da plate ta zubo kuskus ta kalli TV tace ai gaskiya yara suna fitsara a wannan TikTok ɗin. Hajiya ta ce "Wai Ni menene shi TikTok ɗinnan?" Zainab ta ɗakko wayarta tana nunawa Hajiya. Taga yadda 'yanmata kyawawa suke tallar tsiraici,da kuma yadda ƙananan yara da iyayen suke ɗora su suna maganganu na aure da haihuwa yaran da ko magana ba su gama iyawa ba. Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Allah ya kyauta wannan zamani, to wannan me za a kira su,ta yaya ɗanka zaka bari ya auro maka irin wannan yarinyar ya kawo maka gidanka! Wannan dai na tabbata harga Allah dole ta juya namiji da iri wannan karuwancin,dan su mazan irin abinda suke so kenan."Anty Zainab ta ce Allah ya shirya mana zuri'a kuma akwai Malamai ma su wa'azi da masu tallata abubuwa. Hajiya ta ce Allah dai ya tsare mana zuri'a gaba ɗaya da duk ɗan musulmi baki ɗaya. Anty Zainab ta a amsa da ameen ta kama cin abincinta tabar Hajiya da tunanin dole ma ta ga yarinyar ko dai ita ma tana cikin masu irin wannan rawar.
Ƙarfe shidda mun taso daga makaranta ina tafe ina tunanin kayan da zan sa yau in Yaya Aliyu ya zo. Turus na yi a ƙofar gidanmu ganin shi tsaye da wani ɗan buhu a gefen sa,sai kuma na soma kallon jikina duk da kayan makaranta ne a jikina amma ba su da guga kuma ƙafata duk tayi ƙura. "Ya kika tsaya Baby ki ƙaraso mana. Ya yi kamar bai lura da abinda na yi ba. Nace Yaya bari in cire kayan makaranta. Yace "Karki damu ba ruwana da kayan jikinki, dama na zo ne don in ganki da yamma sosai, ido na ganin ido." Na ɗan haɗe fuska alamun fushi na ce amma sai ka faɗa min ko? Yace to kiyi haƙuri,kinfi kyau a hakanki na ɗaga ido ina kallon shi, yana 'yar dariya ashe harda haƙorin maka fari tas a bakinsa, inda akwai maza masu kyau to ba shakka za a saka Yaya Aliyu a ciki yana da tsawo da kuma 'yar ƙiba harma da wani ɗan tumbin irin na matasan masu kuɗi, tsarinsa ya min ƙwarai. Ya katse ni Kin gama nazarin nawa? Na?" Na ja hijabi na rufe fuska, sannan nace bari to in ɗakko tabarma. Yace a a nan zaki dawo kawai ki zauna ni kuma ina nan a tsaye, ba jimawa zanyi ba dan kar anjima banzo ba ki fara lissafa rashin cika alƙawarina. Zanje aiken maigidana, baya gari ni ke kula da buƙatun mahaifiyarsa." Nace gaskiya na amshi uzrinka babbane,lamarin amana sai masu gaskiya. Ya dube ni, "Har kin bani lambar gaskiya Baby to ina godiya Allah ya sa hakan na ke." Nace haka ne ma insha Allahu. Na isa inda ya nuna min na zauna daidai lokacin da su Jamila suka iso da su Jafar, suka gaida shi,sannan na basu jakata nace su shigarmin da ita ciki, ya nuna wa Jamila ɗan buhun da ya zo dashi ya ce "Zaki iya ɗauka?" Ta kalle ni, nace "Me ka kawo min Yaya zaka ja min faɗa. Ya ce "Ɗauki kinji, shinkafa ce kwano uku ba yawa ki yi girkin walima." Ta ɗauka tana masa godiya ta shiga, nace Allah ya saka da alkhairi Yaya. Ubangiji ya sa a mizani. Yace "Amin mata ta ina godiya." Fatin Maman Fati mai awara ta zo wucewa ta kalle ni ta kalli Yaya,sai ta ɗan taɓa baki ta wuce.Na kalli Yaya ko ya kula sai naga shi ni kawai yake kallo, na yi ɗan fari tare da faɗin ya dai Yaya? Ya yi murmushi bari inzo in tafi gida kar a kira magariba nace har zaka tafi, yanzu fa ka zo. "Ya yi ɗan murmushi sai kin min uzrin zuwa zance, yanzu kawai in zanzo zan kira ki, ya kamata in sai miki waya ko 'yar ƙarama ce." Nace kana ta ƙirƙiro kashe kuɗi don Allah ka barshi. Ya ce "To na bari, tashi ki shiga gida." Na miƙe ya ce "Ga dubu ukunki." Na mai da hannuwana baya na maƙe su, ka barshi ga shinkafa ka sai min. Ya ɗaure fuska sannan yace karɓa, da sauri na miƙa hannu biyu na risina na amsa ina ta godiya da addu'a. Yace shiga gida kawai, na wuce ina waiwayen shi.
[6/16, 19:58] Ummi Tandama😇: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕ðŸ»*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*
_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_
*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_
*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*
*Free Page 4*
Ta amsa gaisuwarsa tamkar ba wani abu, suka ci gaba da lissafin da ya kamata ace sun yi a jiya. Ya saki jiki ya karya duk da ta gano cewa ya yi ne domin ta huce daga saɓa matan da take ganin ya yi, amma ta ji daɗin hakan. Ya so matuƙa ta tambaye shi wani abu game da Baby domin ya faɗa mata yana son a tura a cikin satin amma ta ƙi maganar sam,wanda hakan ya sa dole ya bari sai zuwa yamma, duk da tana son taji yadda suke ciki amma ta bari sai ta ji daga Malam. Su Meema suka shigo da gudu duk suka nufi Hajiya suka tsugunna suka gaisheta, ta shafa kansu tare da yi musu addu'o'in da ta saba,sannan suka nufi jikin Dadin su suka gaida shi,ya amsa tare da sa musu albarka Rahin ta fito da kwandunan su da jakunkuna Azima ta kama musu hannu suka wuce suna ɗagawa Dadinsu da kakarsu hannu. Shamaki ya sallami Hajiya ya koma ɗaki don ya shirya ya fita kasuwa. Komai ya ke yana tuna Baby so biyu yana ɗaukar wayar sai ya danna kiran layin Umman su sai kuma ya katse. Ana ukun ya jure tayi ta ringin aka ɗaga tare da sallama. Ya amsa Umma ce, ya gaida ta cikin ladabi, ta amsa cike da jin kunya.ta ce "Sun tafi makaranta kasan ita jarabawa ta ke yi ta fita." Ya ce e ta faɗa min Umma, Allah ya bada nasara, dama na kira ta ne mu gaisa a gaishe su. Umma ta ce "Ba komai a gaida magabatan da kyau don Allah" Yace za suji, ya kashe wayar ya shirya ya fita. Hajiya tun tana sallar walaha wayarta ke ƙara, sai da ta idar ta yi addu'a sannan ta miƙa hannu ta ɗakko wayar Malam ne,don haka sai ta danna kiran shi,ya ɗauka suka gaisa ta tambaye shi abinda ya fuskanta game da binciken, yace "To alal haƙiƙa Hajiya abinda na gani shine, abu na farko dai aure babu fashi, abu na biyu kuma taurarin yarinyar masu haske ne sosai tana tare da arziƙi irin su ko matsiyaci suka aura albarkacin su yana ganin faraga, mai arziƙi kuma tamkar wuta ce sai a zuba mata fetur a bin nufi akwai alkhairi tare da ita,abu na uku Allah ya ɓoye min ban fuskance shiba amma shima ina zaton alkhairi ne,sannan yana sonta sosai irin wanda in ya rasata zai cutu kuma irin wannan son ba zai taɓa ganin aibunta ba ko da ita bata son shi. Wannan sune abubuwan da na gani." Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce Malam kuma an bincika ba wani asiri ta yi masa ba? Malam yace "Abinda na fara dubawa kenan ita yarinya komai nata a rufe ya ke abin nufi bata taɓa ziyarar wani malami ba domin wani aiki. Sam babu kuma wata niyya ta cutar da shi ko kaɗan." Hajiya ta sauke ajiyar zuciya,shike nan Malam a tayamu da addu'a ita ma ta kamu da son shi fiye da wanda yake mata, yace "Wannan mai sauƙi ne in har za taci abin da zan kawo." Hajiya tace ina zan ganta har wani taci wani abu? Amma ka kawo ɗin sai muga ya za ayi. Yayi yar dariya "Hajiya ko gida zaku iya aikawa,kuma koda kowa yaci bazai yi aiki akan saba sai ita da akayi da sunanta sai dai matsalar in har wata mai irin sunanta ta ci to ita ma zata kamuwa da sonsa." Hajiya tace babu damuwa ka aiko ɗin zan san yadda za ayi amma shi abin menene? Yace,Dabino ne ƙwaya bakwai da za a samu ta ci duka zai wahala in bata zo ta tare a gidan ba kafin bikin kamar tai masa sujada haka zaki ga tana yi. Hajiya ta ce na gode sosai Suka yi sallama. Hajiya ta lushe ido ta nutsa cikin tunani, tabbas zata barshi ya auri yarinyar amma dole ta so shi da yawa domin bata buƙatar ta janye masa hankali. Duk da hakan kuma zata sa shi ya kawo mata yarinyar ta ga wace irin wayewa ce da ita wadda har ta ɗaukar masa hankalin yaro haka. Dole sai ta gano wasu abubuwa game da yarinyar domin ta saita mata sahunta don bata son rawar kai. Kuma ta gane ba a mulki sarakuna biyu aka karaga ɗaya. Sam bataji sallamar Anty Zainab ba sai gaisawa da taji suna yi da Juma. Ta buɗe ido ta kai kallo inda taji muryar Zainab ɗin, ta ɗago ta gyara zama tana faɗin yaushe kika shigo Maman Umar? Anty Zainab dake zaune can gefe cikin girmamawa tace "Naga kuna ɗan gyangyaɗi ne shiyasa na yi shiru." Ta gaida Hajiya cikin girmamawa. Hajiya tana tambayar yara, tace duk suna makaranta. Anty Zainab ta kira Juma tace ki zo ki ɗau ledar can ki wanko wa Hajiya tuffa da Inibi har gwabar da fiyar sai ki haɗo mata. Juma ta ɗauki ledar ta fita. Hajiya ta kalli babbar 'yartata tace Maman Umar Allah ya yi albarka har Fiya ta shigo kenan ta ce "Ta shigo nima jiya naje Store in duba jadawalin abinda ake buƙata shine naga sunsa harda Fiya a ɓangaren 'ya'yan itatuwa." Shine nace bari inje in duba miki a wani gurin." Hajiya ta ce Allah ya jiƙan mahaifinku. Zainab ta ce "Ameen Hajiya Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana. Sannan ta gyara zama ta ci gaba da magana. "Hajiya wata yarinya na gani na yiwa autanki shi'awa yarinyar tana da hankali sosai kuma tana da ilmi duka biyu,kuma iyayen ta dattawa ne, Babanta Farfesa ne a BUK." Hajiya ta ce,to ki kira shi ki faɗa masa in ya amince sai yaje ya ganta. Kira shi yanzu kiji amsar da zai baki.
Zainab ta kira wayar Shamaki na farko ta katse na biyu ya ɗauka tare da faɗin "Anty Maman Umar ya gida ya yara?" tace lafiya lau autan Hajiyarmu ƙaraminmu babbanmu. Suka yi 'yar dariya ya saba da wannan kirarin nasu, musamman tunda shike sa hannu a duk wani kuɗi in zai fita daga ko wane sashen ZEENA. Tace Shamaki mata na samo maka mai hankali,ga kyau 'yar gidan ilimi. Yayi 'yar dariya "Kin makara Anty,dan cikin satin nan za a kai kuɗina an bada ni Anty." ya kai ƙarshen maganar cikin tsokana. Ta ce bafa wasa nake ba, shima yace"Allah da gaske na ke yi kuma dama na daina auren haɗi abarni in gani da kai na." Tace shikenan amma duk da haka ka zo gidana zan sa a kira ta sai ka ganta,dama ban musu magana ba, bari na yi inji ta bakinka. Yace Ba sai na ganta ba, domin bazata kai Amira a komai ba, na gode da kulawa zanzo mu yi maganar yadda za a haɗa min lefe irin na yar manyan mutane,dattijai." Tace shike nan sai na jika suka yi sallama. Ta dubi Hajiya ,ashe ya samu? Hajiya ta ce shiyasa na ce ki kira shi,saboda wata irin soyayya naga ya fara mai ban tsoro ku taya shi da addu'a, bana son ya kawo macen da soyayyar ta zata kawo mana hari a cikin gidan nan, ina nufin ta yi amfani da hakan ta cutar damu, Shamaki shine jigon gidan kin san dai abinda nake nufi."Anty Zainab ta ce haka ne,to anyi bincike a unguwar su? Hajiya ta ce na kammala da duk wani bincike bana buƙatar inji me mutanen unguwarsu za su faɗa, yanzu kawai ina son ya dawo in faɗa masa,ya kawo min ita ne in yi mata jarabawar ƙarshe in ta haye shike nan in yana buƙata sati ɗaya kacal za a iya ɗaura musu aure in haka ya yi wa iyayenta. Zainab ta san Hajiya ta ƙare magana don haka ta ce Allah ya sanya alkhairi. Ameen Hajiya ta amsa tare da saka yankar fiya da aka jere mata a cikin tire. Anty Zainab ta tashi bari in shiga kicin ko akwai abinda zan iya ci a abincin gidan. Hajiya dai ta maida kanta ga TV inda wani malami ke nasiha ga 'yan mata masu fitowa suna fitsara a manhajar TikTok. Anty Zainab ta fito ɗauke da plate ta zubo kuskus ta kalli TV tace ai gaskiya yara suna fitsara a wannan TikTok ɗin. Hajiya ta ce "Wai Ni menene shi TikTok ɗinnan?" Zainab ta ɗakko wayarta tana nunawa Hajiya. Taga yadda 'yanmata kyawawa suke tallar tsiraici,da kuma yadda ƙananan yara da iyayen suke ɗora su suna maganganu na aure da haihuwa yaran da ko magana ba su gama iyawa ba. Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Allah ya kyauta wannan zamani, to wannan me za a kira su,ta yaya ɗanka zaka bari ya auro maka irin wannan yarinyar ya kawo maka gidanka! Wannan dai na tabbata harga Allah dole ta juya namiji da iri wannan karuwancin,dan su mazan irin abinda suke so kenan."Anty Zainab ta ce Allah ya shirya mana zuri'a kuma akwai Malamai ma su wa'azi da masu tallata abubuwa. Hajiya ta ce Allah dai ya tsare mana zuri'a gaba ɗaya da duk ɗan musulmi baki ɗaya. Anty Zainab ta a amsa da ameen ta kama cin abincinta tabar Hajiya da tunanin dole ma ta ga yarinyar ko dai ita ma tana cikin masu irin wannan rawar.
Ƙarfe shidda mun taso daga makaranta ina tafe ina tunanin kayan da zan sa yau in Yaya Aliyu ya zo. Turus na yi a ƙofar gidanmu ganin shi tsaye da wani ɗan buhu a gefen sa,sai kuma na soma kallon jikina duk da kayan makaranta ne a jikina amma ba su da guga kuma ƙafata duk tayi ƙura. "Ya kika tsaya Baby ki ƙaraso mana. Ya yi kamar bai lura da abinda na yi ba. Nace Yaya bari in cire kayan makaranta. Yace "Karki damu ba ruwana da kayan jikinki, dama na zo ne don in ganki da yamma sosai, ido na ganin ido." Na ɗan haɗe fuska alamun fushi na ce amma sai ka faɗa min ko? Yace to kiyi haƙuri,kinfi kyau a hakanki na ɗaga ido ina kallon shi, yana 'yar dariya ashe harda haƙorin maka fari tas a bakinsa, inda akwai maza masu kyau to ba shakka za a saka Yaya Aliyu a ciki yana da tsawo da kuma 'yar ƙiba harma da wani ɗan tumbin irin na matasan masu kuɗi, tsarinsa ya min ƙwarai. Ya katse ni Kin gama nazarin nawa? Na?" Na ja hijabi na rufe fuska, sannan nace bari to in ɗakko tabarma. Yace a a nan zaki dawo kawai ki zauna ni kuma ina nan a tsaye, ba jimawa zanyi ba dan kar anjima banzo ba ki fara lissafa rashin cika alƙawarina. Zanje aiken maigidana, baya gari ni ke kula da buƙatun mahaifiyarsa." Nace gaskiya na amshi uzrinka babbane,lamarin amana sai masu gaskiya. Ya dube ni, "Har kin bani lambar gaskiya Baby to ina godiya Allah ya sa hakan na ke." Nace haka ne ma insha Allahu. Na isa inda ya nuna min na zauna daidai lokacin da su Jamila suka iso da su Jafar, suka gaida shi,sannan na basu jakata nace su shigarmin da ita ciki, ya nuna wa Jamila ɗan buhun da ya zo dashi ya ce "Zaki iya ɗauka?" Ta kalle ni, nace "Me ka kawo min Yaya zaka ja min faɗa. Ya ce "Ɗauki kinji, shinkafa ce kwano uku ba yawa ki yi girkin walima." Ta ɗauka tana masa godiya ta shiga, nace Allah ya saka da alkhairi Yaya. Ubangiji ya sa a mizani. Yace "Amin mata ta ina godiya." Fatin Maman Fati mai awara ta zo wucewa ta kalle ni ta kalli Yaya,sai ta ɗan taɓa baki ta wuce.Na kalli Yaya ko ya kula sai naga shi ni kawai yake kallo, na yi ɗan fari tare da faɗin ya dai Yaya? Ya yi murmushi bari inzo in tafi gida kar a kira magariba nace har zaka tafi, yanzu fa ka zo. "Ya yi ɗan murmushi sai kin min uzrin zuwa zance, yanzu kawai in zanzo zan kira ki, ya kamata in sai miki waya ko 'yar ƙarama ce." Nace kana ta ƙirƙiro kashe kuɗi don Allah ka barshi. Ya ce "To na bari, tashi ki shiga gida." Na miƙe ya ce "Ga dubu ukunki." Na mai da hannuwana baya na maƙe su, ka barshi ga shinkafa ka sai min. Ya ɗaure fuska sannan yace karɓa, da sauri na miƙa hannu biyu na risina na amsa ina ta godiya da addu'a. Yace shiga gida kawai, na wuce ina waiwayen shi.