← Book details Hamshaƙiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 18

Sashe 14

Hamshaƙiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

*NA*

*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*

_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo evidence ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_

*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_

*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*

*Free Page 8*

Abubuwa sun kankama lokaci yana ta ƙaratowa Munafinci ba ga maƙota ba ba kuma ga dangi ba. Umman su Fati har gida ta zo wai Allah ya sanya alkhairi amma harda cewa Umma ashe ku da tanajin ku,auren Fati sai bayan Babbar salla mu masu ƙaramin ƙarfi. Umma tace Allahn da ya kawo mijin a lokacin da masu gori suke gori shine zai kawo abinda zamu kai mata. Ina jinsu Umman su Fati aka wuce ana borin kunya. Umma tace Allah kai zaka yi mana wannan lamari Allah ka taimake mu. Sauran kwana huɗu walimarmu kwana biyar kuma a ɗaura mana aure. Yaya ya aiko min da katan Lemo guda biyar wai na walima a daran ranar ne ya zo gurin Abba ya nemi alfarmar a ɗaga aurenmu zuwa wani satin. Walimarmu da sati ɗaya kenan. Abba yace ba damuwa, ya shiga ciki ya sanar da Umma sannan ya ce in fito. Mun gaisa yake faɗa min wai gyaran banɗakin gidan za'ayi shine dalili. Na ce to Allah ya kaimu, amma banso haka ba,yace kamar yau ne. Yanzu ki faɗa min me da me kike buƙata a gurina. Na dube shi, kamar na me? Yace "Kuɗin lalle da pati ko baza ki yi ba?" Nace zanyi amma kana da kuɗin ne? Yace Inkinji makaho yana cewa a yi wasan jifa ai ya taka dutse ne ko? Ki lissafa min duk abinda ki ke so na biki zan miki daidai ƙarfina." Nace to kana son mu kira DJ ko baka son kiɗa? Ya yi 'yar dariya. Kinga Baby zan kama miki ɗan wuri ku yi party da ƙawayanki amma banda maza." Na zaro ido karka matsa wa kanka, kila Abba ma ya ce baza a fita party ba. Kawai zan yi DJ na a can filin,na nuno mishi da hannu. Ya kalli gurin "Shikenan zan sa a zo a sa kujeru." Na ce to na gode Ubangiji Allah ya bada yadda za ayi. Yace Ameen ina jin daɗin addu'o'in ki. Zan tafi ki tura min sauran abubuwan ta text,sai in kawo miki ko?" Na ce to yawwa dama zan tambaye ka ko zan iya buɗe Whatsapp? Yace wannan ki bari sai an kawo ki zan buɗe miki da kai na." Na yi murmushin tare da faɗin na gode. Na ce yawa jira ni ina zuwa. Na shiga gida da sauri,na ɗakko katin saukarmu na ɗakko na kawo masa, nace ga shi don Allah ka zo, tunda ma an ɗaga bikin ai dai zaka zo ko? "Insha Allah zan zo, ki shiga gida zan aiko miki da katin auren shima sai na party ki rubuto min yadda ki ke son ya kasance." Zan yi magana ya ɗaga min hannu,kar ki ce komai shiga gida." Na ce to sai da safe.Har na juya yace, yawa na tuna "Baby!" Na waiwayo, ki faɗawa Abba za a kawo lefe zuwa jibi." Zan dawo ya kuma cewa shiga gida kawai." Dole na wuce ina waiwayen sa. Fatana Allah ya sa ba bashi zai ci ba.
Jamila sai murna su ke yi ita da Ummu za a.kawo lefe, ni kam ba ta wanna na ke ba,ɗaga bikin shine abinda yafi komai bani takaici. Saidai ba ni da damar in yi maganar da wani, tunda duk ba su fahimta ta. Ashoben Walimarmu shi aka maida ashoben biki wannan ɗagawar sai ya bada damar zuwa a siyo musamman 'yan uwa da 'yanmatan lungunmu waɗan da suka bayyana kansu a matsayin ƙawayena harda su Fati. Kullum sai sun shigo muna tattauna yadda za ayi party. Tare da taimakon Jamila na rubuta wa Yaya abubuwan da nake buƙata. Kuɗin lalle da wankin kai. kuɗin Party kuɗin kwalliya. Ina tura masa ya rubuto cewa,kin manta da na gyaran jiki. Na yi 'yar dariya shidai Yaya baya rabo da ɗorawa kansa ɗawainiya. Umma ta tashi hankalinta game da kayan ɗaki da safe ta aiki Jamila a kira mata aminiyar ta Umman Amina. Jamila bata jima da da wowa ba Umman su Amina ta shigo, ina jin su daga ɗaki Umma tana faɗa mata zancen kawo lefe, ta ce tunda sunyi lefe maganar kaya katako muma dole mu dage ko ba masu tsada bane. Ummansu Amina ta ce, "Haka ne, dama abinda yasa na ce abar batun kayan katako a sai ka tifa da kayan girki saboda ya ce ba matsala kuma ba shi halin lefe akwai wata mafita guda ɗaya in har Abban su Baby zai yarda, akwai masu bada taimako na kayan ɗaki wani foundation mai suna Zeena. Umma tace ina jin su a Radio suna yi wallahi. Umman su Amina ta ce Da sai a rubuta takarda a tafi da yarinyar a kai musu in so samu ne yau ɗinnan. Umma tace ai damuwar da ƙyar Abbansu ya yarda Umman su Amina ta ce " Akwai mafita, Baby ba tana nan ba, tazo yanzu in faɗa mata abinda zata rubuta ni sai in sata a gaba mukai takardar." Na ɗan zaro ido a inda nake a laɓe, Zeena sune waɗanda Yaya ke yiwa yaron shago fa. Ƙwalamin kira Umma ta yi, na amsa naje a kace in ɗako takarda da biro na ɗakko. Muka zauna Umman Amina tana faɗamin ina rubutawa. Neman taimako ne dan Allah an saka bikin har ana ta ɗaga wa saboda. ba'a samu kayan ɗaki ba, har ma maganar tana nema ta lalace. Wai in sa cewa ni marainiya ce. Sai na rubuta iyayena basu da hali gashi an saka auren kusa. Da na gama aka sa lambar wayata da ta Umma. Ummansu Amina ta ce shirya maza bari inje in barwa Amina sallahun girki, tana fita nace A
Umma Hajiya Zeena ita ce Uwar ɗakin Yaya fa, Mahaifiyar mai gidansa da muka je. Tace "Tofa!" Wannan shine ga ƙoshi ga kwanan yunwa, bari ta zo inji ya za ayi." Data dawo Umma ta faɗa mata halin da ake ciki, sai ta ce ai mu ofishin su na Foundation ɗin zamu je,baza su sani ba ma bare yaji labari. Muka hau Adaidaita sahu zuwa titin Ɗanbare muka je wata Zeena plaza mun shiga ofishin muka gaida wadda muka samu, sannan muka faɗa mata buƙatarmu tace yaushe ne bikin mukace kwana shabiyu, ta ce shine zaku kawo takarda yanzu? Umman Amina ta ce 'yarnan ku yi haƙuri da muna sa rai cewa zamu iya sayen kayan ne sai kuma muka ga ba wata mafita. Ta amshi takardar ta buɗe ta karanta,ta yatsina baki, ku ba ma marainiya ba ce kenan? Kuma gashi babu sa hannun ta bare na mahaifinta. Umman su Amina ta lankwashe murya kamar marainiya tace mana a taimaka mana. Matar ta ce gashi nan an rubuta iyaye na basu da ƙarfi." Umman Amina ta kalle ni, na sunkuyar da kai, tace Hajiya ita ce ta rubuta bata iya rubutun bane a taimaka. Ta yatsina fuska. "Sai ku haifi yara ku kasa amfana musu komai,Hajiyar bata shigo ba,in ta shigo zan bata amma bana sa ran zaku samu domin an cire list na wannan wata." Ta kalli Umman Amina "Kamar kun bada ajiya sai a ƙurarren lokaci irin wannan." Umman Amina sai haƙuri take bata tana roƙonta, ita kuma sai yaɓa mana magana ta ke yi. Baƙin ciki kamar in fice ko in hau matar da duka,ta kalle ni, wannan ce mayar kenan Umman Amina tace ita ce. Ta taɓa baki. "Kada kiji haushina yarinya laifin iyayenki ne, zan bawa Hajiya takardar ku in ta shigo suma suna da bikine bata zuwa sosai. Nan dai mukayi godiya muka fice.
Na ce da Umman Amina wallahi dama a kyale su, dubi yadda sai wulaƙanci ta ke mana. Umman Amina tace ai haka suke irin waɗannan aiki fa aka ɗauke ta karɓar takardar neman taimako, amma sai kace itace ta ce zata bada sai irin wannan rashin mutunci ta ce yi.
Umma bata faɗa wa Abbanmu ba, musamman da taji rashin tabbacin abin. Umman Amina tace in shirya in raka Amina kasuwa zata sai anko da mayafi. Nace to sai dai muje da kyalle tunda mu namu a gurin Safara aka siya. Tace bana son kayan Safara dan zata bada bashi saita Linka kuɗin ga rashin haƙurin bashi. Nace Umma da da kuɗi da kin bada na Jamila da yadin da kika ce zaki sai wa su Jafar da Habu. Tace sai in bada a kuɗin gudunmawar da 'yan Kurna suka aiko jiya, Allah ya rufa asiri kar in Lodi bashin Safara bayan biki ta uzzira min naji da naki saura dubu biyu da naira hamsin. Nace to maje gobe,ranar da za 'a kawo lefena kenan. Gidan su Zuhra za akai, gidan wan Abbanmu. Na shirya nasa doguwar baƙar riga da mayafi Amina ta zo har zamu wuce Umma tace kije gidansu Zuhra jiya Ummansu ta aiko tana tambayar inda za a samu anko.
Muka biya, nan "yan matan gidan aka taso, amarsu mai magar zuma, yau zamu sha lefe. Na ce ku ta lefe kuke. Ina Umma zamu kasuwane sayen anko. Murja tace Zuhra ce zata siya. Umman su ta fito muka gaisheta,ta taɓe baki, "Kaga 'ya'yan aminai to Zuhra ta baku saƙo ko kuwa ta biku?" Nace ta zo muje mana tafiyar zata fi daɗi. Dama tsararmu ce Tare mukayi Candy sai dai makarantarmu ba ɗaya ba, domin su ta kuɗi suke zuwa kasancewar Abbansu ya fi namu ƙarfi.
Muka hau adaidaita muka nufi kwari nace kai gabana sai faɗuwa ya ke yi, bansan ina ne gefen su Yaya ba, fatan karya ganni,sai ƙara kaɗe ƙura nake. Muna ta yawo sai wani ya amshi kyallen yace wannan kayan Zeena plaza ne. Gabana ya faɗi. Na tsaya cak, nace bari in baku kuɗi kuje ku siyo harda ta Jamila. Zuhra tace "Me yasa?" Nace a ɗaya daga cikin irin waɗannan kantunan ya ke yaron kanti. Amina ta ce to ai ba lallai shi a wannan yake ba. Nace to muje. Muna shiga wanda ya kawo mu ya tambaya ko akwai sauran wanna kayan?" Wani ya amsa ya duba yace akwai, muka shiga ƙaton kantin wani yace mu zauna a kawo mana saboda nan ba a bada ɗai ɗai sai dozin bari ya karɓo a ɗaya shagon.
Shamaki ya ɗaga robar ruwan paro ya sha ya aje yana sake juya katin hannun shi, ko shakka babu wannan katin daga makarantar su Baby aka kawo masa gayyata da kuma takardar neman taimako. Yanzu a yaya zaije, ya mata alƙawarin zaije mata yaga karatunta kuma zata so ta ganshi a gurin ƙila ma har ta nuna wa ƙawayen ta cewa ga wanda zan aura. Sannan a ɗaya gefen Hajiya bata son yana wasa da zuwa irin waɗannan wuraren da ake bawa Allah rance. Ya kuma ya jingina bayansa da kujerar ya lumshe ido dan neman mafita. Ya buɗe idanu ya zuba a kan fuskar laptop ɗin dake gaban shi wadda ta ke hasko mishi ko ina na Kantin sama da ƙasa. Ya tsura ido akan wasu 'yan mata dake zaune kan wasu kaya. Ya ɗauki wayar kantin ya danna kira Ɗahiru ya ɗaga, yace suwaye zaune akan kayan nan wasu "yan mata su uku?" Yace Atamfar nan mai ganye suke so, Hassan yaje kawo musu. Shamaki ya ce in yazo kace ya zo ina kiranshi kafin ya sallame su.
Chapter 14 · 0% Book details