← Book details Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 18

Sashe 17

Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*

*Free Page 10 Karshen free Pages*

*DIJENGALA ENTERPRISE*
*07031121981*
*Ina Mata 'yan gayu masu son kayan gayu kuzo ga dama ta samu* *DIJENGALA ENTERPRISE ta kawo maku Kayan masu kyau da inganci indai mace tasan gayu to* *DIJENGALA ENTERPRISE ne wajen siyayyar ta.*
💯 London laces
💯 London lafaya
💯Switzerland laces
💯 Dubai laces & Lafaya
💯veils
💯 Atampha
💯 shadda
💯 Voile
💯yadika na maza
💯caps
💯 Necklaces etc...
*Kayan mu ba Wanda suka cika gari bane,bazaki gansu a ko ina ba shiyasa ake mana kirari da Auntyn Gayu ko me kika siya a gunmu zaki ji dadinsa* *07031121981 Ina Wanda zasuyi biki su rasa abinda zasu saka suna tunani kar suyi iri daya d wasu Don Allah ku tuntubeni* *07031121981 zaku Sha mamaki🤔sarkokinmu ba kowane wuri zaku samesu ba wlh sai wurin ya ansa sunansa, haka Laces dinmu ma na daban ne daga Company sai wajenmu💯🥰💞*
*DIJENGALA ENTERPRISE*

Umman Amina ta shigo ƙarfe goman dare ita da Amina, duk muna kwance tsakar gida saboda yanayin zafi. Abbanmu yana banɗaki, ta zauna suna ƙara tattauna yadda zasu yi wa Abba maganar. Ni kuma muna 'yar hira da Amina da Jamila,. amma hankalina baya tare da su, na kan tuno da Yaya ɗazu da muna waya. Bai kuma ce min ƙala ba ya kashe wayarsa, na kira bai ɗaga ba. Tambayoyinsa sun caza min kai kuma al adar da yace Hajiyarsa ta na da ita wadda ya tabbatar za ta gabatar a kai na, suma suna sani faɗuwar gaba. Zan so ya min bayani sosai, sai dai a yadda na soma karantar halinsa, ba lallai ya kuma ɗakko min maganar ba.

Jamila ta girgiza kafaɗa ta tana cewa Amina tana miki magana tunanin me ki ke yi? Na sauke ajiyar zuciya na dubeta me kika ce Amina? Tace Duk tunanin auren ne haka, ina tambayar ki ne za kiyi lalle a saukarku ne?" Nace a'a' ba zai fita ba har inyi na biki. Jamila tace gaskiya kam. Sam ban lura cewa Abba ya fito daga banɗaki ba,sai dai na ji muryarsa ya na faɗin gaskiya talauci na da lalacewata da rashin godiyar Allah na duk basu kai haka ba. Gara inci bashi domin nasan zan biya." Umma ta ce to amma kasan shima bashin ba a samun sa ko? Yace to in ba a samu ba sai mu kaita a haka domin shi yace baya buƙata,me zai sa mu ɗaga hankalinmu akan wannan. Har zuwa yanzu baya ga dubu hamsin kuɗinta da aka kawo bani da ko taro, kuma ban damu ba. Allah ne zai mata komai,amma bana son in kuma jin zancan neman tallafin nan,bayan mun karɓa sai munje 'yan jaridu sunyi hira da mu, an yaɗa a kafafen yaɗa labarai cewa gamu an ba mu, sannan mu yi godiya, ga Allah, shi mijin ya ji zai ɗauke mu da daraja ne?"

Umman Amina ta ce yanzu sai abarshi kenan Abban su Baby bayan ita mai gurin ta karɓi takardar... Ya miƙe tare da tsaki. "Ni kunga fita ta." Ya wuce abinsa. Umma ta ce kin gani ko wani Lokacin Abban su Baby hutsune, da ki ke ganinsa. Umman Amina tace da Abban su Amina zai yarda ai sai muje da shi a madadin Abban su Baby.Umma ta ce, da zai yarda ai da mun fita kunya. Ina jinsu abubuwan sun min yawa, banda ina jin wani mahaukacin son Yaya Allah da na fasa auren nan,kowa cikin damuwa da zullumi ga shi karatun saukar nawa ma duk na kasa nutsuwa inyi maraja'a a gida. Gashi daga gobe an gama sai kuma a filin sauka.

Shamaki ya yi jugum, bashi da wata mafita face ya gana da 'yan uwanshi matan nan su tattauna a samu mafita. Ya ɗaga waya ya kira Maman Umar ta ɗaga da faɗin autan Hajiya, yace Maman Umar fatan dai kina lafiya da yarana duka. Tace "muna lafiya Auta." Yace ba haushe dai yace Babbar ya Uwa ko? Tace "Tabbas." Yace to zan kawo kukana gurinku ku duka, ba ƙara zan kawo ba, fatan zaki banbance ko? Tace "Na banbance." Yace don Allah ki tara su zanzo da magariba gidanki zamu yi wani zama yau ɗaya a tarihi ba tare da Hajiya ta sani ba, kuma karma taji labari. Maman Umar tace "Baka da matsala auta yanzu duk zan kira su." Suna yin sallama ta kuwa kiransu ta sanar da su.
Tun biyar suka haɗu kowacce ta ɗauki mota ta zo. Suna ta hirar su abin gwanin ban sha'awa cikin wasa da dariya. Maman Umar tace "Ni yanzu ko ɗinki ban bayar ba bansan ma wane kayan zan ɗinka ba. Fatima tace naga wasu lessis da atamfofi na tashin kai, har nace zan kira Shamaki ya kamata su kawo irin su. Aisha tasan san Fatima da gayu ta ce Maman Iman a ina kika gansu? DIJANGALA ENTERPRISE Na sha mamaki kunsan ni duk inda kayan gayu yake zaku ganni a gurin kawai naga tallar kayan na duba naga laces yan London da lafaya da atamfofi abin dai sai kingani, naga Number wayar kamfanin, na kira da ta ɗauka mukayi magana ta turo min ke kinga atamfofi na tashin kai.Maman Umar tace kin gansu a hannu ne wasu fa duk hoto ne. Maman Iman ta ciro waya ta fara nuna musu kaya, tace sune na faɗawa Maman Nana cewa na saka Oder kayan London ai ba acan London ɗin na saka ba, gurin wannan kamfanin na sa, gobe zan karɓa. A'isha tace "In naga naki sai in siya nima amma dai in Hajiya taji zata ce duk irin kaya da muke da su a ZEENA baza mu bawa kanmu ƙaruwa ba. Maman Umar tace ai ko ita taga abinda ya birge ta ko muna dashi sai ta siya. Yasunan kamfanin ki ka ce? Maman Iman tace DIJANGALA ENTERPRISE Karki damu zan kawo muku kayan ku gani. Ni Ko tun a waya sun yi min. Suna ta labari har sai da sukaji kiran salla sannan biyu suka tashi suka tafi salla,biyun kuma suka ce basayi.

Umar ne ya shigo daga masallaci yake sanar da Momyn su tare da Uncle Shamaki suka yi sallar magariba a masallacin layinsu.Maman Nana tace har ya zo kenan. Umar yace e mana cikin massalacin. Suna cikin magana sai ga sallamarsa. Suka amsa suna yi masa sannu gami da sunan tsokanar da suke faɗa masa wato ƙaraminmu babbanmu. Yace ga ni nan a bi ni a hankali ko in ƙi sa wa kowa hannu a takardar. Suka sa dariya,ya zauna aka kawo masa abinci dana sha. Ruwa kawai ya ɗauka ya ɗaga robar ya sha kusan rabi sannan ya aje. Ya kalle su, halin da nake ciki bazai barni in iya jin yunwa ba.
Chapter 17 · 0% Book details