← Book details Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 18

Sashe 15

Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Zungureriyar motar ta tsaya a ƙofar gidan Yayan Abban su Baby, Bala direba bai manta gidan ba,dan haka ya fito yace bari ya yi sallama. Wani saurayi zai shiga gidan Malam Bala yace, yaro, dan Allah in kashiga ka yi mana sallama da mai gidan. Tare suka fito domin yasan da zuwansu bayan azahar kamar yadda Abban su Baby yazo ya sanar da shi tun jiya, dan haka ma bai fita ba, kuma ya sanar da ƙaninsu da kuma maƙotanshi kamar yadda suka saba duk lokacin da wani a cikinsu zai karɓi kaya irin haka. Suka gaisa da Malam Bala, sannan ya dubi yaronsa da ya yi sallama da shi, yace Halifa a fito da tabarmi ga baƙin sun iso bari kira Malam liman ya danna kiran maƙocin nasa yana faɗa musu sun iso, dama da suka yi azahar ya tuna musu. Ya kira Abban su Baby ya ce,kazo sun iso, ka taho da ruwa da Lemon kar ka manta. Nan suka hallara sai aka buɗe kujerar baya aka soma fito da akwatuna na zamani haka ma but ɗin motar. Guda shidda ne masu kyau daga gani an zuba kaya masu tsada. Abban su Zuhra ya ce, ba sai an buɗe ba, Allah ya sa albarka ya bada zama lafiya. Suka ɗakko ruwa katan biyu Lemo katan biyu suka ce gashi. Har kawun Aliyu yace su barshi,sai Abban su Zuhra ya ce, ko dai ya yi kaɗan ne?" Suka ce a a haba ba haka bane, Liman da suka zo dashi ya ce a karɓa Allah ya sa albarka.
Suna tafiya aka shiga da kaya ciki dama su Umman su Zuhra suna ciki sun ƙosa su gani koda abin arziƙi ita da yaranta. Nan kuwa jiki yayi sanyi domin Atamfa tirmi talatin ce ga lesuna ga Shadda da dogayen riguna abin dai na girma. Suka haɗa kaya suka aje,tace Hajara kije ki cewa Umman su Baby azo a ɗauki kayannan. Abbansu Zuhra ya ce, ina za a kai su tun yanzu, a bari mana 'yan uwa su gama gani." Tace a a kar wani abu ya ɓace gani da 'yar mata a zarge su, gara akai can kowa yaje can ɗin ya gani.
Ta ƙwarzaba dole yace su Halifa su ɗauka su kai. Suma 'yan lungu suna ganin ana shiga da akwatuna, nan da nan labari ya karaɗe kaffatanin lungun an kawo lefen Baby. Umman su Baby ta aika Jafar ta ce ya kira mata Umman Amina. Itace ta saka ido akan kayan saboda maƙota sun tsaya sai sun gani ba iyayen ba ba yaran ba. Kowa ya sha mamakin kayan Umma kasa magana ta yi saboda tunanin ta kayan ɗaki, suma sun fita kunya,ko da yace baya so shi dai a shiryen sa yake.
Bayan mutane sun watse Umman Amina tace, gaskiya wannan kaya babu batun haƙura da kayan ɗaki. Tashi za kiyi mu koma can gurin tallafi in ba haka ba za aji kunya. Umman su Baby ta ce sai gobe dai yanzu su Baby basa nan ga kayan mutane. Umman Amina tace "To goben dai ya zama da wuri fa insha Allah kamar ƙarfe goma.

Jamila ta yi ta murna da ta dawo makaranta ta ga lefe tace amma gaskiya Yaya Aliyu da tanadin sa, dubi kaya kamar kati!" Umma tace gaskiya ya bada mamaki ya yi mamaya.

Muna jiran mai kawo mana zani, jim kaɗan sai gashi muka karɓa muna dubawa,ya faɗa mana kuɗin. Cikin mamaki na kalli Zuhra kinsa Safara dubu da ɗari biyar ta ɗora akan duk turmin atanfa ɗaya. "Amina tace shiyasa Ummanmu bata yarda da siyan kaya a gida." Zuhra tace dubu da ɗari biyar ta isa ayi ɗinki. Yaron ya katse mu ga ruwa. Ya miƙo mana ruwan Paro mai sanyi. Nace harda ruwa ku ke bayarwa? Yace mai gida yace a baku don daga gani kun gaji. Zuhra ta kalli wanda ke kan teburin a zaton ta shine mai gidan ta ce mun gode.Sai nima na dube shi nace Allah ya saka da alkhairi. Na basu baya ina shan ruwan kamar yadda suma suka nutse a shan ruwa.

🖊️
[6/16, 19:58] Ummi Tandama😇: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻*

*NA*

*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*

_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_

*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_

*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*

*Free Page 9*

Na tuna da yadin su Jafar na cire robar ruwan daga bakina, na dubi wanda dai ya kawo mana atamfar nace, don Allah kuna saida yadikan maza masu sauƙi haka ko shadda irin ishirunka maraya ɗin nan? Yace "Bama sai dawa sai kun koma kan wannan layin nan."
Nace wai gashi mun gaji kyanshi daga nan mu fita. Na zaunen ya ce Ɗahiru zo mana. Yaje, jim ya dawo ya ce ƙanwata kawo a yanko miki yadin, nawa ne kuɗin kuma wace kalar kike so? Nace yadi huɗu ne kala kuma irin dai ta maza ƙanne na za a ɗinkawa. Ya amshi kuɗin ya fita. Abinda ya faru shine Shamaki ya tattara duk wani kallonshi ga motsinshi akan Baby data yi magana sai ya bugawa Hassan waya yana tambayar shi metake so, sai ya sanar dashi, sai yace ka sa Dahiru ya amshi kuɗin ko nawa tazo dashi ya je can shagon ya ɗakko mata shadda yadi biyar,amma karya sake ya ce mata komai, ya bata kawai ya amshi kuɗin. Hassan cikin mamaki ya ce,to Allaji. Muna zaune ya kawo shadda mai kyau, nace gaskiya wannan ta yi sauƙi, amma ka duba ko nawa na baka kuwa? Yace "Na gani ita kaɗai ta rage shiyasa aka bar miki a haka." Nace to mun gode. Muna fitowa bakin shagon sai ga wani mai adaidaita kamar mai jiranmu, nace ɗan agundi. Yace "Dai-dai ina?" Amina tace ko bakin ƙofa ma sai mu ƙarasa. Zuhra ta ce nawa zamu baka? Yace "Ku hau muje kawai. Muka kama hanya. Sai dai yana sauke mu ya wuce wai mubar kuɗin. Muka cika da mamaki sannan muka masa godiya tare da hasashen ko wata ya ke so a cikinmu, amma me yasa bai tambayi lambar waya ba. Haka dai muka wuce zuwa gida muna al'ajabin ɗan sahu. Tun da muka shiga lungun yara suke bamu labarin wai an kawo lefena. Gabana ya faɗi, muka shiga gidanmu har su Zuhra. Mun cika da al'ajabin kaya wanda hakan ni ma ya sa na fara tunanin kayan ɗaki ya wajabta aka iyayena.
Chapter 15 · 0% Book details