← Book details Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 18

Sashe 10

Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

"Islamiyya fatan dai kina zuwa?" Mu ne zamu yi sauka a makarantarmu nan da sati uku. Na bata amsa nima kamar ina jiran tambayar. Sai na ga ta kalle ni, daidai lokacin Shamaki ya Turo ƙofa tare da sallama. Ya kalle ni sannan ya tsugunna a ɗaya gefen na Hajiya yana mata sannu da hutawa. Ta amsa a ƙasaice ba tare da ta kalleshi ba. Na kafa mishi ido ina son ya kalle ni in masa alamar zamu tafi,amma sai ya ƙi kallo na,ya juya yana faɗin "Kunƙi cin komai ko Amira? Nan ma fa gida ne." Na ce ni naci dabino kuma ga ruwa. Jamila ce bata ci ba. Ya kalli dabinon a gabana, ya dauki ƙwaya biyu ya jefa ɗaya a baki ya fara taunawa tare da faɗin nima dai bari in ci dabinon. Hajiya ta ɗago da sauri ta kalle shi. Tuni ya fito da ƙwallon na farko har ya jefa na biyun. Ta ce na baka ne ka ci? Yace Afwan Hajiya zan kawo dabino na tuna kin ce ya ƙare jiya ko? Sai kuma ya tuna zai tona kanshi dan haka ya miƙe da sauri ina zuwa bari in zo ku tafi. "Zauna." Ta furta fuskanta ba walwala. Ni kuma mamaki na ke yadda ta yi masa a game da dabino,bisa ga dukkan alamu bata so ya ci ba. "Wace sana'ar mahaifinki ya ke yi?" Lebura ne magini. Ta ɗan taɓa baki. "Allah ya bada Sa'a. Ta dube shi, ka yi magana da Juma a kwashe musu kayan marmarin nan su yi tsaraba. Da sauri na ce a'a Hajiya ki yi mana afwa za a yi mana faɗa. Ta ce "Haka ne domin ba'a san kunzo ba ki ka ce ko? " Ya kalleni cike da mamaki kuma da alamu bai ji daɗin hakan ba, ni ko da a kalli iyayena ƙanana gara ace ni ce bani da mutunci. Tace "Ba haka kika faɗa ba?" Na ce haka ne amma yanzu in har muka je da wannan kayan iyayenmu baza su haƙura da haƙurin da zamu basu na laifin ƙarya da muka yi ba, domin za su zargi ko mun canza hali ne mun zama kwaɗayayyu." Ta tsira min ido, sannan ta kalli Aliyu. "Sai ku sake yin ƙaryar da kuka yi a farko ku faɗi wani wanda in shine ya baku baza'ayi faɗa ba." Ai bamu da shi a dangin mu kaf, kuma ba mu yi nasarar ƙaryar farko ba kenan. Ki yafe mu Hajiya watarana zamu sa da kanmu mu ci insha Allahu. Yace gaskiya ne ranar da na kai musu Lemon ɓawo Abbansu yana ta faɗa. Tace "To shike nan Allah ya yi muku albarka za ku iya tafiyar ku yanzu." Sai lokacin ya kalle ni, muje ko? Na ce to na miƙe ina gyara mayafina Hajiya kuwa idanunta ƙyar a kaina. Jamila ta mata sallama ya nuna mana ƙofar da muka shigo ku bi nan muje. Muka fita har falon ƙarshe bai fito ba. Jamila tace gaskiya baki da hankali wallahi Yaya Baby. Daga zuwa gidan mutane kinji sanyin AC kin kama kina ta zuba,to meye sai kin faɗa mata cewa ba'asan munzo ba,ina ruwan ta da sanin su?" Na ce Dalla banza baki san mekefaruwa ba,amma zan wayar miki da kai bari mu hau keke napep. Yace fito Muje in kaiku can inda zaku ta bani mota aro." Yace in hau gaba Jamila ta hau baya. Maigadin yana faɗin adawo lafiya ranka ya daɗe Allaji. Na kalle shi. Ya yi saurin faɗin su wai mutane suna ƙaunar su kai mutum inda bai je ba, daga zuwa wurin ta wai raina ya daɗe kullum haka ya ke faɗa in dai Nazo gidannan." Na sauke ajiyar zuciya nace ai fatan alkhairi ya yi maka.
Chapter 10 · 0% Book details