← Book details Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 18

Sashe 16

Hamshakiyar Uwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hajiya ta kalli ɗan 'uwanta bayan ya gama yi mata bayanin irin karɓar da akayi musu,yace dattawa ne gaskiya Allah ya sa alkhairi. Ta numfasa, "To sannunku da ƙoƙari kuma Allah ya ƙara zumunci." Yace amin ni zan koma,tace babu damuwa sai ka jini. Bayan fitar shi ta jingina tana nazari,ko shakka babu tunda ɗan uwannan nata ya ce dattawa ne ta tabbatar da hakan, domin da akasin hakanne ba abinda zai hana shi faɗa. A yadda ta karanci yarinyar a ranar da ta zo ta fito daga ƙaramin iyali, kuma kamar ba masu ƙwaɗayi bane, tasan cewa daga lokacin nauyin wannan iyalin zai iya hawa kansu, amma bata son abinda zai wuce gona da iri. Gidanta fadarta ce duk wanda ya shigo dole zai zama a ƙarƙashin ikon ta. Rawar kan Shamaki ya yi yawa a wannan auren ko na farko bai rikice haka ba bare sauran abinda ya ke bata haushi ma yadda yarinyar ta ke kamar an daurawa ƙashi fata, yaron ta lafiyayye ne kuma ta jima da fahimtar cewa shi ɗin mabuƙaci ne, ta yarda cewa ya yi haƙuri shi ne ya sa yanzu ta yarda da wannan auren na gaggawa duk idan ta dunƙule damuwar guri ɗaya tambayar ita ce yarinyar zata iya sama masa gamsashiyar natsuwa?" Bata da tabbacin wannan amsar dan haka dole ya sake aure ba da jimawa ba,domin samun ƙarin wadda zata tare wannan matsalar, zata yi tunani akan yarinyar da Maman Umar ta yi magana. Ta tashi zaune ta zuba wa Azima ido wadda ke zuba mata furar da Juma da dama mata aƙaramin firji da ke kusa da ita wadda ta ke sha bayan la'asar. Tana baiwa Azima duk wata kulawa da wasu ciye ciye na zamani domin amfanin ɗanta,amma har yanzu Azima yar shekaru sha huɗu ce, yar ƙaninta ce data ɗakko tun daga bakin yaye. Tana son Azima ta tashi da irin tarbiyyar da take son matar ɗanta ta kasan ce,sannan Malamin su ya faɗa mata cewa Azima ita ce zata haifi ɗa namiji tare da Shamaki. Sanin Shamaki ba zai jira ba shine yasa ta barshi ya yi duk auren da zai yi kafin Azima ta kawo,kuma Azima ce zata zama Hamshaƙiya a cikin matan sa. ƙaran da wayarta tayi ne ya maido da hankalinta ta kalli wayar wadda ta ware ce don yin magana da iya 'ya'yanta kaɗai. Maryam ce ɗaya daga cikin 'ya'yanta, Ta ɗauka sannan ta ɗaga, ta sa a kunne, acan ɓangaren Maryam cikin girmamawa tace,, "Hajiyarmu barka da yamma." Hajiya ta ce Maman Nana kun dawo ne?" Mun dawo Hajiya sai muka kaji biki kamar daga sama. Hajiya ta ce Allah ya kawo lokacin. Maryam Tace to Allah ya kai mu, zamu shigo anjima da Dadinsu Nana yace in gaisheku kafin mu zo. "To Allah ya muku albarka amma kice masa nace dan Allah kar a zo da wata gudunmawa domin nasan halinsa." Maryam ta yi yar dariya Ɗazu yake ce min ya yi oder wata mota wadda zai bawa autanki a saka lefe a ciki a baiwa Amarya. Hajiya ta yi yar dariya ƙasaita. Ai ba irin wannan yarinyar bace, wata 'yar tsuntsuwa ya samo gata nan dai, kuma gidansu in aka kai wani kayan tsorata za su yi suga kamar za a sayar musu da 'ya, bare a haɗa da mota. Maryam tace Tofa! Bana kuma 'yar talakawa ya samo kenan? Hajiya ta ce haka ne sai dai kuma suna da dattako a yanzu, ba mu san ya zasu nuna a gaba ba." Maryam tace Allah ya sa su ɗore, domin haka mutane suke, in sun samu guri sai su nemi wuce gona da iri. To zan kira Maman Iman in faɗa mata wai ta saka order ta wasu lesuka. "Ki faɗa mata har A'isha duk ki sanar da su, kar kowa ta ɗaga hancinta,ankan wata gudun mawa, lefen ma an kai shi ɗazu. Nan dai suka yi sallama bayan sun tattauna tana Allah ya sanya alkhairi.

Shamaki ya sakko su Hassan suna tsegumin ba susan ya sakko ba, sai yaji suna fadin. Maigida wa yake so a cikin yaran nan Ɗahiru ya ce abin da mamaki irin fa yaran geto ɗin nan ne wasu kyamusassu shi da za ayi auran sa kwanan nan. Hassan ya ɗago daga kallon laptop ɗin da ke gaban shi ya ce "Kaji yadda ya ke min magana a gigice kuwa. "Hassan! ku tabbatar kun samo musu Ɗansahu su bar kasuwar nan. Suka kwashe da dariya bayan Hassan ya kwaikwayi muryarsa. Shamaki ya yi gyaran murya, nan da nan suka haɗa hankalinsu cikin kunya suka yi shiru. Yace "Gara dana ji ku, wadda zan aura tana cikin waɗannan yaran da ku ke yi wa ba'a. Kuma za ku je kuna neman wata alfarma agurinta wata rana. Hassan ya ce tuba muke maigida Allah ya taimaki maigida ayi haƙuri ba mu sani ba,sai ya fasa maganar da zai yi ya juya ya barsu cikin zullumi da kunya.

Washe gari Abbanmu yana fita Umma ta ce Allah ka gani saboda fita kunya zan fita ba izinin Abban Baby Allah ka sa muyi nasara. Lokacin da suka je sakatariyar bata fito ba, suka zauna suna jira kamar yadda Umman Amina ta bada shawara. Sunfi ƙarfin awa ɗaya sannan sai ga ta ta iso a wata mota. Har da duƙawa suna gaisheta, a wulaƙance ta kalle su,sannan ta kauda kai tana tambayar lafiya? Umman Amina tace dan Allah ki taimaka mana a matsayinmu na mata 'yan uwanki, mune muka zo shekaran jiya don Allah ki taimaka.
Ummansu Baby tace, Ki rufa mana asiri abin nan ya ƙarato gashi... Matar ta ce dan Allah ki min shiru ,me zan muku? Inje in buɗe store ince ga kaya ku ɗiba?" "Me yake faruwa?" Suka ji an tambaya daga bayansu. Duk suka waiwaya. Hajiya A'isha ce wadda Shamaki ke bi mata a haihuwa, kodayake ta bashi shekaru kusan takwas. Itace mai kula da ɓangaren Foundation ta kalli su Umma sun tsugunna a gaban Raliya. Tace ba yin Allah ku tashi,ke buɗe Office su shiga. Ta ci gaba da faɗa,bansan so nawa zan faɗa miki ba, ki daina wulakanta mutane . Wannan Office ɗin saboda su ne muka buɗe shi,kema kuma aikin su ki ke yi. In ba masu buƙatar me za mu yi a nan kenan? Raliya ta shiga bada haƙuri tana faɗin jiyan nan suka kawo takardarsu kuma suna maganar bikinsu sati mai zuwa. Umma ta kalli A'isha tace Hajiya kamar yadda Allah ya rufa miki asiri muma ki rufa mana, ba mu da wata mafita ne bamu zo da wuri bane domin muna sa rai cewa zamu iya siyan kayan .Sai kuma akayi rashin dacen samun kudin. Ko iya gado ne a taimaka Hajiya Aisha tace, "'yar waye a cikinku?" "Yata ce, inji Umman Baby. "To ina mahaifinta?" Ta jeho tambayar. Yana nan amma bashi da ƙarfi wallahi leburane ya buga ko ina amma bai samu halin yi mata kayan ba, ko iya gado ne ku taimaka mana sai mu kaita. To Shikenan zan taimaka amma sai na ga mahaifinta,sannan zan san ya za ayi a saka takardar ku acikin jerin na wannan wata ukun, duk wata uku mutum goma mu ke ɗiba mutum talatin a shekara ai muna ƙoƙari bafa gwamnati bane mu. Su Umma suka ce gaskiya kuna ƙoƙari muna godiya Allah ya saka da alheri ta ce "Ba komai ku zo da mahaifin nata sai munyi masa tambayoyi sannan mu bashi takarda ya cike. Ta dubi Raliya "Dakko min takardar su." Haka suka yi mata sallama suka tafi.

Tunanin Umma tun a hanya shine yadda zata tunkari Abban Baby da zancan nan gani take ba zai yarda ba. Umman Amina ta ce ki bari zanzo in same shi da maganar sai muji me zai ce,ai in ba wai ya samu wata mafitar bane ina mai tabbatar miki da gudu zai yarda. Ummansu Baby tace Allah yasa.
Sun dawo gida suka tarar 'yan Kurna sunzo ganin lefe,ni kuwa dawowar su Umma ta min daɗi domin Yaya na ta kiran waya ina cewa ya yi haƙuri zan kira shi masu ganin lefe ne suka zo. Umma na zama suna gaishe gaishe ni kuwa na miƙe na shige ɗakin mu da sauri na kira Yaya sai da ta yanke zan kuma kira sai ga kiran shi ya shigo. "Baby." Muryar shi ta ratsa cikin kunnuwa na, cike da kasala nace na am. Yace zan miki wata tambaya nace ina jin. ka. "Ke budurwa ce? Gabana ya yake ya yi wata mummunar faɗuwa, cikin rawar murya na ce Yaya ban fahimta ba. Yace kawai ki bani amsa,ke budurwa ce ko kuwa wani abu ya taɓa budurcin ki? Tambaya ta biyu kin iya girki?" Na ce, Kaji wani labari ne game da ni? Yace "Banji ba, amma akwai wata al ada wadda Hajiyata take rayawa,na tabbatar zata yi wannan al "dar a kanki kamar yadda ta yi a sauran mata na,ina son ku faɗa min gaskiya domin in ne mi mafita kafin ranar, saboda Baby wallahi ni kaɗai nasan me nake ji a kanki bazan iya fassara wa ba ai game da son ki." Na numfasa Yaya ina da tabbcin cewa ni budurwace amma bani da tabbaci akan budurcina. "Kamar yaya?" Ya katseni. Nace to ni dai ban taɓa ko wasan banza da wani namiji ko wasan duka banayi har bare ya kai ni ga ashsha, amma wannan ba shine zai sa in yi tutiyar budurcina ba tun da ance yana samun matsala da kanshi. Game da girki kuma irin namu dai na iya nasan kuma shi ku ke ci. Fara da wake mai da yaji, irin su taliya ɗinnan da manya. Kuma na iya tuwo harda ɗan wake sosai,jalaf ma dai zan ɗan iya tunda mukan yi jifa jifa. Ya yi shiru har sai da na ce kanaji na kuwa Yaya?

🖊️🖊️🖊️
[6/16, 19:58] Ummi Tandama😇: *HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻*

*NA*

*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*

_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_

*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_
Chapter 16 · 0% Book details