Sashe 3
Gidan Yan Bariki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
saida ta lumshe idanu, Kamal na gaba tana bayansa, har suka ƙarasa parlo zama sukayi kana ya kira wayar Sultan, sai ringing ɗinta yaji kan kujerar da Suhana take zaune, yace "Ashe yana kusa ma ina zuwa." Yacewa Suhana kana ya fita parlon Bar ya nufa dake cikin hotel ɗin a chan ya same shi zaune yana shan maltina,
Kamal yace "Sultan mun ƙaraso tana ciki." beyi magana ba sai da ya kammala abinda yake yi kana ya tashi yana gaba Kamal na bayansa har suka shiga ciki lokacin Suhana ta ɗauko wayarta tana waya da Jamal ya dawo be sameta ba sai rigima sukeyi sai ta faɗa mai inda taje ya zo ya sameta,
faɗa sukayi sosai ta kashe wayarta, Sultan kuwa zama ya yi kan kujera ya ɗora ƙafarsa kan teburin dake parlon, ya rufe idanunsa, yana jiran suyi magana Suhana kuwa sai lokacin ta kula da Sultan ne, wani dukan uku-uku ƙirjinta ya yi, amma ta basar kamar bata san shi ba , saboda ta kula ɗan jan aji ne,
Kamal ne ya ga shirun ya yi yawa kana yace "Sultan ga Suhana munyi magana da ita nayi mata bayanin komai , yanzu sai ku tattauna akan yadda za'a yi auren." Shiru Sultan ya yi na lokaci kafin ya buɗe baki da kyar kamar wanda akayiwa dole ya fara magana cikin muryarsa mai daɗin sauraro,
yace "kamar yadda Kamal ya miki bayani inason yin aure na wani lokaci maybe na shekara ɗaya ko wata uku zuwa 7 mouth, ki faɗi ko nawa kike so zan biyaki duk abinda kike so zan yi miki, amma fa dole kiyi min biyayya, duk abinda nikeso shi zakiyi, cikin gidanmu zan ajeki, nan kowa da kowa yake,
banaso ki ragawa duk wanda ke cikin gidan kiyi duk abinda kikeso duk wanda ya taka ki kema ki taka shi ko wanene ban ɗauke miki kowa ba, karki yarda da kowa duk yadda akayi karki aminta da ko ɗaya, abinda na saka ki shi zakiyi, idan lokacin da na ɗiba ya cika zan sakeki.!"
shiru Suhana tayi saida Kamal yace "Hana kiyi magana." Kana tace "Ni yanzu matsalata shine bansan inda iyayenka zasuje neman aurena ba saboda banda kowa!." Sultan yace "Okey Kamal ka kaita gidanku, wurin Umma, saina zo anjima zamu yi magana yanzu ku tafi ta tattara kayanta gaba ɗaya,
ku wuce bana son a samu matsala, gobe da safe zan turo ILiya ya zo ya kwashe kayanku zaku koma cikin gidana guda dake Unguwar, baifas." Cikin jindaɗi Kamal yace "Badamuwa yadda kace haka za'ayi." Sultan be koma magana ba, sai ma tashi da ya yi tare da ɗaukar wayarsa ya riga su fita,
Suhana kuwa tace "Kamal yanzu ya zanyi da Jamal wallahi idan yaji wannan zance bazai taɓa bari ayi auren nan ba.!?" Kamal yace "Ai wannan mai sauƙi ne, yanzu idan muka tafi ki kwashe komai naki kosu Lili da Afiya karki gaya ma wannan zance sai bayan aure, ki sanar da su, anjima zan siyo miki sabon sim card,
ki cire wannan, kega babu yadda za'a yi Jamal ya gano inda kike." Suhana tace "Kamal baka san waye Jamal bane amma bazan ƙi shawarar ka, yanzu dai mu tafi, nasan yanzu haka ya fita zuwa GIDAN ƳAN BARIKI yana jiran dawowa ta." Kamal yace "mutafi."
haka suka tafi ta kwashe kayanta gaba ɗaya, suka wuce gidansu Kamal zaune suka tarar da Umma tana jan chalbi, saida ta kammala kana Suhana ta gaida ta cikin girmamawa, Umma ta amsa cikin sakin fuska, gyara zama Kamal ya yi kana yace "Umma Sultan ne yace na kawo miki ita ki kula mai da ita,
matar da zai aure ce bata da Iyaye gidan marayu ya ɗauko ta kesan na gaya miki matslar gidansu da halin da yake ciki, shine ya ce don Allah ki riƙe mai ita a matsayin ƴar ki, gobe Yaronsa zai zo ya kaimu gidansa dake baifas, nan zamu ci-gaba da zama har lokacin da za'a yi auren."
Umma tace "Ai ko kare Sultan ya kawo a gidan nan dole na kula da shi bale yarinyar da zai aure, gaskiya naji daɗin wannan labari ashe ina da rabon ganin auren Sultan, Allah ya kaimu lokaci lafiya, ya sa iyakar wahalar da yashi kenan!." Kamal yace "Amin Umma."
sunjima suna hira kafin Kamal ya fita, Umma kuwa sai Jan Suhana takeyi ajiki har sun saba da juna, Umma najin Suhana kamar ƴar da ta haifa, Kamal ne kawai ɗan da Allah ya bata, shine kuma yanzu Allah ya saka mata ƙaunar Suhana,
Jamal kuwa ya yi ta kiran wayar Suhana a kashe haka ya gaji da zama gidan ƴan barki ya koma gidansa da tunanin ta dawo amma shiru, ko da ya duba babu kayanta da ke gidan ko tsinke bata bari ba, hankalinsa ne ya yi masifar tashi to ina Suhana ta tafi kar dai gudawa tayi ta bi wani,
fita ya koma yi wurinsa Afiya idan sun san inda Suhana take amma shiru sosai suka shiga ruɗani ina taje gashi wayarta a kashe ba'a samu, haka ya yi ta yawo a gari duk inda yasan tana zuwa sai da yaje amma babu labarinta, washegari, da safe
Writer ✍️ *Bey PINKY DARLING MRS JAY*
Following this link to join my WhatsApp Channel https://whatsapp.com/channel/0029VawsLxR65yDI5tHjxh2e
*GIDAN ƳAN BARIKI*
(*Hot love and Romantic Story*)
Story and Writer ✍🏻 bey
*Zainab Abdullah Usman*
(*PINKY Darling Mrs Jay*
*PAID BOOK*
₦500 only account number 7060577995
*Zainab Abdullah Opey*
Evidence of payment 👇
09033580667
__________________________________
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
*DIAMOND 💎 STAR 🌟 LADIES🧝♀️*
(*we stand together*)
🤝🤝🤝
*Bissmillahi Rahamanin Raheem*
*PAGE* 7️⃣▶️8️⃣
Yaron Sultan ya so da mota aka kwashe kayan su Kamal gaba ɗaya aka mayar da su Unguwar baifas, sabon gida, akwai duk wani abu na buƙatar jin daɗin rayuwa da sauransu, Suhana kuwa gaba ɗaya kwana ɗayan nan da tayi babu Jamal taji babu daɗi, gaskiya bata kyauta mai, ba
amma ai bashi da niyar aurenta, zaman bariki kawai yake so su cigaba da yi, yanzu kuma ta samu damar yin aure dole tayi shi, ƙarfe biyu na rana Sultan ya zo gidan lokacin ta fito wanka ta shirya cikin riga da siket na atamfa blue, da fari ɗinkin ya zauna jikinta sosai, tayi kyau ma sha Allah,
sai zuba ƙamshi takeyi, parlo ta fito, tana danna wayarta bayan ta saka sabon sim card ɗin da Kamal ya siyo mata, sam bata san da zuwan Sultan ba, ƙamshin turarensa da cika paroln ne ya tabbatar mata da zuwansa, tana ɗgowa, sukayi ido huɗu da shi, wani irin ƙwarjini ya yi mata gaba ɗaya ya cika mata idanu,
bazata iya jurar kallon ƙwayar idanunsa ba, sunkuyar da kanta tayi haka kawai ta tsince kanta da faɗar "Sannu da zuwa Yallaɓai." tana nufar wurin firij ta ɗauko mai madara mai sanyi da ruwan gora ta ajiye tare da cop, sai lokacin yace "Lafiya." bedroom ɗin Umma ta shiga
lokacin ta idar da sallah tace "Umma ga Sultan nan yazo." Addu'ar da Umma keyi ta shafa kana tace "Kai ma sha Allah bari nazo mu gaisa." Ta faɗa tana tashi tsaye, ita kuma Suhana ta fito tace "Umma na zuwa." Ta bar parlon, ta kula yau kamar ransa a ɓace yake, ai kuwa ta chanka dai-dai
Umma na fitowa tace "Me nike gani haka waye ya taɓaka Sultan lafiya dai ko.?" Ta jero mai waɗannan tambayoyi tana shafa kansa, da ba hula, rungumeta ya yi kana yace "Umma wai Abba ne be yarda nayi wani aure ba sai dai na mayar da Farida, nikoma wallahi har abada ko mai sunanta bazan koma aure ba."
shiru Umma tayi kana ta zauna kusa da shi tace "Gaskiya wannan maganar bata taso ba yarinyar da aka haɗa kai da ita a kashe ka shine za'ace ka maida ta gidanka, ni yanzu shawarar da zan baka kaje wurin Alhaji Abubakar ka sanar dashi ya yiwa Abbanka magana,
Ya bari ka aure wacce kakeso." Sai lokacin Sultan ya saki ranshi yace "shiyasa nike sonki Umma yanzu daga nan zan wuce gidansa na sanar da shi duk yadda akayi zan dawo gobe na sanar da ke." Umma tace "Yauwa ɗan albarka, Allah ya shige muna gaba." Yace "Amin ni zan wuce." Addu'a tayi mai kana ya wuce,
duk abinda suke tattaunawa Suhana ta jinsu, Wai dama Sultan ya taɓa aure har matarsa ta nemi kashe sa? Yana fita Unguwar Bado ya nufa, gidan Yayan Abbansa, har bar gida ya same shi zaune yana duba jarida cikin fara'a ya tarbe Sultan bayan sun gaisa cikin girmamawa Sultan ya kora mai bayani,
ya samu wata yarinya gidan marayu ya ɗauko ta, aurenta za shiyi saboda suna son juna amma Abba ya hana sai dai ya maida Farida, Alhaji Abubakar najin wannan magana ransa ya ɓaci yace "Wai har yanzu Yusuf beyi hankali to wallahi ƙarya yake ni nan zan ɗaura ma aure da ita, ko yaƙi ko yaso,
ai nima Mahaifinka ne barni da shi kawai yanzu ina yarinyar take.?" Sultan yace "Tana gidan Umman Kamal." Alhaji yace "Ma sha Allah kace yarinyar zata ƙara samun tarbiyya, mai kyau gaskiya kayi tunani mai kyau da ka ajeta gidan Fateema, yanzu ka tafiyarka gobe zan kiraka."
godiya Sulatn ya yi mai sosai kana ya bar gidan Alhaji ya rakasa da idanu, cike da tausayin Sultan,
Niko nace wai menene ya samu Sultan haka kowa kejin tausayinsa? Muje dai zuwa,
Umma ya kira a waya ya sanar da ita yadda suka yi,
Jamal kuwa da Afiya sun karaɗe garin Sokoto wurin neman Suhana amma shiru kakeji tsabar iskanci har da Kamal ake yawon nemanta,hhhhh gaba ɗaya hankalinsu yafi tafiya akan Suhana bata garin ta koma Abuja, dole suka haƙura da nemanta,
Washegari Alhaji Abubakar ya kira Sultan ya sanar da shi, zaije wurin Umma ya ga yarinyar kana ranar juma'a a ɗaura auren a babban masallacin juma'a, Abbansa yace dole sai dai ya haɗa biyu, da Suhana da Farida saboda haka ya yi haƙuri ta mayar da Farida kawai a ɗaura aurnsu da ita ranar assabar,
Kamal yace "Sultan mun ƙaraso tana ciki." beyi magana ba sai da ya kammala abinda yake yi kana ya tashi yana gaba Kamal na bayansa har suka shiga ciki lokacin Suhana ta ɗauko wayarta tana waya da Jamal ya dawo be sameta ba sai rigima sukeyi sai ta faɗa mai inda taje ya zo ya sameta,
faɗa sukayi sosai ta kashe wayarta, Sultan kuwa zama ya yi kan kujera ya ɗora ƙafarsa kan teburin dake parlon, ya rufe idanunsa, yana jiran suyi magana Suhana kuwa sai lokacin ta kula da Sultan ne, wani dukan uku-uku ƙirjinta ya yi, amma ta basar kamar bata san shi ba , saboda ta kula ɗan jan aji ne,
Kamal ne ya ga shirun ya yi yawa kana yace "Sultan ga Suhana munyi magana da ita nayi mata bayanin komai , yanzu sai ku tattauna akan yadda za'a yi auren." Shiru Sultan ya yi na lokaci kafin ya buɗe baki da kyar kamar wanda akayiwa dole ya fara magana cikin muryarsa mai daɗin sauraro,
yace "kamar yadda Kamal ya miki bayani inason yin aure na wani lokaci maybe na shekara ɗaya ko wata uku zuwa 7 mouth, ki faɗi ko nawa kike so zan biyaki duk abinda kike so zan yi miki, amma fa dole kiyi min biyayya, duk abinda nikeso shi zakiyi, cikin gidanmu zan ajeki, nan kowa da kowa yake,
banaso ki ragawa duk wanda ke cikin gidan kiyi duk abinda kikeso duk wanda ya taka ki kema ki taka shi ko wanene ban ɗauke miki kowa ba, karki yarda da kowa duk yadda akayi karki aminta da ko ɗaya, abinda na saka ki shi zakiyi, idan lokacin da na ɗiba ya cika zan sakeki.!"
shiru Suhana tayi saida Kamal yace "Hana kiyi magana." Kana tace "Ni yanzu matsalata shine bansan inda iyayenka zasuje neman aurena ba saboda banda kowa!." Sultan yace "Okey Kamal ka kaita gidanku, wurin Umma, saina zo anjima zamu yi magana yanzu ku tafi ta tattara kayanta gaba ɗaya,
ku wuce bana son a samu matsala, gobe da safe zan turo ILiya ya zo ya kwashe kayanku zaku koma cikin gidana guda dake Unguwar, baifas." Cikin jindaɗi Kamal yace "Badamuwa yadda kace haka za'ayi." Sultan be koma magana ba, sai ma tashi da ya yi tare da ɗaukar wayarsa ya riga su fita,
Suhana kuwa tace "Kamal yanzu ya zanyi da Jamal wallahi idan yaji wannan zance bazai taɓa bari ayi auren nan ba.!?" Kamal yace "Ai wannan mai sauƙi ne, yanzu idan muka tafi ki kwashe komai naki kosu Lili da Afiya karki gaya ma wannan zance sai bayan aure, ki sanar da su, anjima zan siyo miki sabon sim card,
ki cire wannan, kega babu yadda za'a yi Jamal ya gano inda kike." Suhana tace "Kamal baka san waye Jamal bane amma bazan ƙi shawarar ka, yanzu dai mu tafi, nasan yanzu haka ya fita zuwa GIDAN ƳAN BARIKI yana jiran dawowa ta." Kamal yace "mutafi."
haka suka tafi ta kwashe kayanta gaba ɗaya, suka wuce gidansu Kamal zaune suka tarar da Umma tana jan chalbi, saida ta kammala kana Suhana ta gaida ta cikin girmamawa, Umma ta amsa cikin sakin fuska, gyara zama Kamal ya yi kana yace "Umma Sultan ne yace na kawo miki ita ki kula mai da ita,
matar da zai aure ce bata da Iyaye gidan marayu ya ɗauko ta kesan na gaya miki matslar gidansu da halin da yake ciki, shine ya ce don Allah ki riƙe mai ita a matsayin ƴar ki, gobe Yaronsa zai zo ya kaimu gidansa dake baifas, nan zamu ci-gaba da zama har lokacin da za'a yi auren."
Umma tace "Ai ko kare Sultan ya kawo a gidan nan dole na kula da shi bale yarinyar da zai aure, gaskiya naji daɗin wannan labari ashe ina da rabon ganin auren Sultan, Allah ya kaimu lokaci lafiya, ya sa iyakar wahalar da yashi kenan!." Kamal yace "Amin Umma."
sunjima suna hira kafin Kamal ya fita, Umma kuwa sai Jan Suhana takeyi ajiki har sun saba da juna, Umma najin Suhana kamar ƴar da ta haifa, Kamal ne kawai ɗan da Allah ya bata, shine kuma yanzu Allah ya saka mata ƙaunar Suhana,
Jamal kuwa ya yi ta kiran wayar Suhana a kashe haka ya gaji da zama gidan ƴan barki ya koma gidansa da tunanin ta dawo amma shiru, ko da ya duba babu kayanta da ke gidan ko tsinke bata bari ba, hankalinsa ne ya yi masifar tashi to ina Suhana ta tafi kar dai gudawa tayi ta bi wani,
fita ya koma yi wurinsa Afiya idan sun san inda Suhana take amma shiru sosai suka shiga ruɗani ina taje gashi wayarta a kashe ba'a samu, haka ya yi ta yawo a gari duk inda yasan tana zuwa sai da yaje amma babu labarinta, washegari, da safe
Writer ✍️ *Bey PINKY DARLING MRS JAY*
Following this link to join my WhatsApp Channel https://whatsapp.com/channel/0029VawsLxR65yDI5tHjxh2e
*GIDAN ƳAN BARIKI*
(*Hot love and Romantic Story*)
Story and Writer ✍🏻 bey
*Zainab Abdullah Usman*
(*PINKY Darling Mrs Jay*
*PAID BOOK*
₦500 only account number 7060577995
*Zainab Abdullah Opey*
Evidence of payment 👇
09033580667
__________________________________
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
*DIAMOND 💎 STAR 🌟 LADIES🧝♀️*
(*we stand together*)
🤝🤝🤝
*Bissmillahi Rahamanin Raheem*
*PAGE* 7️⃣▶️8️⃣
Yaron Sultan ya so da mota aka kwashe kayan su Kamal gaba ɗaya aka mayar da su Unguwar baifas, sabon gida, akwai duk wani abu na buƙatar jin daɗin rayuwa da sauransu, Suhana kuwa gaba ɗaya kwana ɗayan nan da tayi babu Jamal taji babu daɗi, gaskiya bata kyauta mai, ba
amma ai bashi da niyar aurenta, zaman bariki kawai yake so su cigaba da yi, yanzu kuma ta samu damar yin aure dole tayi shi, ƙarfe biyu na rana Sultan ya zo gidan lokacin ta fito wanka ta shirya cikin riga da siket na atamfa blue, da fari ɗinkin ya zauna jikinta sosai, tayi kyau ma sha Allah,
sai zuba ƙamshi takeyi, parlo ta fito, tana danna wayarta bayan ta saka sabon sim card ɗin da Kamal ya siyo mata, sam bata san da zuwan Sultan ba, ƙamshin turarensa da cika paroln ne ya tabbatar mata da zuwansa, tana ɗgowa, sukayi ido huɗu da shi, wani irin ƙwarjini ya yi mata gaba ɗaya ya cika mata idanu,
bazata iya jurar kallon ƙwayar idanunsa ba, sunkuyar da kanta tayi haka kawai ta tsince kanta da faɗar "Sannu da zuwa Yallaɓai." tana nufar wurin firij ta ɗauko mai madara mai sanyi da ruwan gora ta ajiye tare da cop, sai lokacin yace "Lafiya." bedroom ɗin Umma ta shiga
lokacin ta idar da sallah tace "Umma ga Sultan nan yazo." Addu'ar da Umma keyi ta shafa kana tace "Kai ma sha Allah bari nazo mu gaisa." Ta faɗa tana tashi tsaye, ita kuma Suhana ta fito tace "Umma na zuwa." Ta bar parlon, ta kula yau kamar ransa a ɓace yake, ai kuwa ta chanka dai-dai
Umma na fitowa tace "Me nike gani haka waye ya taɓaka Sultan lafiya dai ko.?" Ta jero mai waɗannan tambayoyi tana shafa kansa, da ba hula, rungumeta ya yi kana yace "Umma wai Abba ne be yarda nayi wani aure ba sai dai na mayar da Farida, nikoma wallahi har abada ko mai sunanta bazan koma aure ba."
shiru Umma tayi kana ta zauna kusa da shi tace "Gaskiya wannan maganar bata taso ba yarinyar da aka haɗa kai da ita a kashe ka shine za'ace ka maida ta gidanka, ni yanzu shawarar da zan baka kaje wurin Alhaji Abubakar ka sanar dashi ya yiwa Abbanka magana,
Ya bari ka aure wacce kakeso." Sai lokacin Sultan ya saki ranshi yace "shiyasa nike sonki Umma yanzu daga nan zan wuce gidansa na sanar da shi duk yadda akayi zan dawo gobe na sanar da ke." Umma tace "Yauwa ɗan albarka, Allah ya shige muna gaba." Yace "Amin ni zan wuce." Addu'a tayi mai kana ya wuce,
duk abinda suke tattaunawa Suhana ta jinsu, Wai dama Sultan ya taɓa aure har matarsa ta nemi kashe sa? Yana fita Unguwar Bado ya nufa, gidan Yayan Abbansa, har bar gida ya same shi zaune yana duba jarida cikin fara'a ya tarbe Sultan bayan sun gaisa cikin girmamawa Sultan ya kora mai bayani,
ya samu wata yarinya gidan marayu ya ɗauko ta, aurenta za shiyi saboda suna son juna amma Abba ya hana sai dai ya maida Farida, Alhaji Abubakar najin wannan magana ransa ya ɓaci yace "Wai har yanzu Yusuf beyi hankali to wallahi ƙarya yake ni nan zan ɗaura ma aure da ita, ko yaƙi ko yaso,
ai nima Mahaifinka ne barni da shi kawai yanzu ina yarinyar take.?" Sultan yace "Tana gidan Umman Kamal." Alhaji yace "Ma sha Allah kace yarinyar zata ƙara samun tarbiyya, mai kyau gaskiya kayi tunani mai kyau da ka ajeta gidan Fateema, yanzu ka tafiyarka gobe zan kiraka."
godiya Sulatn ya yi mai sosai kana ya bar gidan Alhaji ya rakasa da idanu, cike da tausayin Sultan,
Niko nace wai menene ya samu Sultan haka kowa kejin tausayinsa? Muje dai zuwa,
Umma ya kira a waya ya sanar da ita yadda suka yi,
Jamal kuwa da Afiya sun karaɗe garin Sokoto wurin neman Suhana amma shiru kakeji tsabar iskanci har da Kamal ake yawon nemanta,hhhhh gaba ɗaya hankalinsu yafi tafiya akan Suhana bata garin ta koma Abuja, dole suka haƙura da nemanta,
Washegari Alhaji Abubakar ya kira Sultan ya sanar da shi, zaije wurin Umma ya ga yarinyar kana ranar juma'a a ɗaura auren a babban masallacin juma'a, Abbansa yace dole sai dai ya haɗa biyu, da Suhana da Farida saboda haka ya yi haƙuri ta mayar da Farida kawai a ɗaura aurnsu da ita ranar assabar,