BABI NA ASHIRIN DA TARA 2⃣9⃣
Dan Makaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 25 min read
(ZAN RAYU DA KAI ❤ ZAN MUTU DA KAI 😭 )
A tasha tayi Sallahr Asuba, Motar Suleja ta hau, tunda ta shiga Motar suka fara tafia gabanta yake faduwa, fargaba da tsoro suka cika mata zuciya, kar suyi Accident fa, ji take kamar ta sauka, amma zuciyarta ta riga ta kitsa mata, bacci takeji amma bata ga ta bacci ba haka tayi zaune tana sak'e a ranta.
Allah ya kaisu Suleja Lafia, daga nan ta hau Motar Katsina.
A B U J A
Mancy na dakin Abba, Dalo ita kadai ke zaune a Dakin Mancy ta na neman wayar Zaid ta kasa samunshi, a duk lokacin da ta tuna Yasmin da Alherinta sai ta zubda hawaye, sallama yake tayi, bata ji ba, har yazo gabanta ya zauna.
Hannu ya tafa, ta dan firgita.
"Ina kwana?" Ta gaisheshi kanta a duk'e.
Bai amsa ba yace "tunanin me kikeyi?".
Murmushi ta dan kirkiro tace "bakomai".
Yace "Ba nace a daina kukan nan haka ba?".
Marairaicewa tayi tace "fa ba kuka nakeyi ba?".
Irin muryarta yayi yace "to me kikeyi?
Da sauri ta kalleshi jin yanda yayi magana kamar wani dan auta, au danauta ne ashe, dauke ido tayi saboda kallon da yake binta dashi.
Yace "Kin gaya min matsayin Yasmin a wurinku, zan sake gaya miki kamar yanda na gaya miki jiya, shi mamaci addua yake so fiye da komai, kuka baya kara musu komai sai nauyi, ki roka mata rahama, balle ita da muke sa ran inshaAllah tayi mutuwar Shahada, ki bar mata kuka please".
Duk jikinta ya mutu da yanayin maganarshi, shi haka yake? Haka yake magana? Muryarshi sanyi? Wannan in ta cigaba da sauraran muryarshi sai ya sa ta shiga wani yanayi".
Yace "dama Abba yace muje na miki register Catering School kafin a samo miki Admission a Nile University".
Cikin jin dadi tace "Dagaske?".
Ya langwabar da kai yace "eh dagaske".
Ta sa hannu ta rufe fuskanta, ta lura Ya Jawad na san zolayarta.
Ya mik'e tsaye yace "ina jiranki a waje".
Ya fita, ta bi bayanshi da Ido.
FIKRA Catering School ya mata register, maimakon su wuce Gida, sai ya shiga Yawon nuna mata gari, don ya san in suka koma Gida daki zata shige tayi ta kuka, shi kuma har ga Allah baya son Kukan nan.
Sai da ya ga tayi daria kafin ya daina k'okarin sanyata daria.
Akwai wani abu da yake ji a game da ita, yana ganin kamar Tausayi ne, amma cikin zuciyanshi ya san ba haka bane.
Na wani dan lokaci Dalo ta manta da damuwarta, yanda Jawad ke ji da ita ya sa take jin wani abu game dashi, ta san shi ba tsaranta bane Hmm, a dai bar maganar.
K A T S I N A
Tarin da Dr Ali ya ji Zaid nayi jiya ya tsaya mishi a rai, yana tsoron kar stage din TBC dinshi ya kai ga Liver Transplant, wayarshi ya dauka ya latso Zaid amma wayarshi is switched off, sak'e sak'e yayi tayi daga k'arshe ya yanke hukuncin zuwa ganin Zaid, daga nan ma ya zo ya mishi tests a ga yaua matsayin ciwonshi yake yanzu.
Maigadi ya tabbatar da cewa Zaid na cikin gida, ba tare da jiran komai ba Dr Ali ya nufi Boysquaters, yana shiga dakin ya ga Zaid kwance murus k'asa, da sauri ya karasa gunshi yana jijiga shi, da alamun ba yanzu yayi collapsing ba.
Da yake Dr Ali Giant ne, haka ya saba Zaid a baya ya fita don kaishi Asibiti, a kagauce yace da Maigadi "donAllah je ka fada cikin gida Zaid baya da Lafia, na tafi dashi General Hospital"
Bai jira cewar maigadi ba ya bude motar ya tura Zaid shi kuma ya shige motarr.
Maigadi yayi cikin da gudu don sanar da su.
Hannah kadai aka samu, Shafaa na chan gun Er Rabi.
Da aka gaya ma Hannah tabe baki kawai tayi yo su ina ruwansu da wani rashin lafian Zaid? Allah sa ma ya mutu.
A Asibiti tuni an kaishi Emergency Room Likitoci suka dukufa kanshi, abunda Dr Ali ke gudu shi ya faru, Kusan rabi da kwatar Hantar Zaid ta lallace, kuma in har baa mishi dashin Hantar ba, to Hantarshi zata fashe, ga Hak'ark'arinshi duk sunyi bak'i saboda hayak'i dake bi ta wurin.
Dr's suka yanke shawaran yi mishi aiki cikin gaggawa saboda kar lallacewan Hantar ya tabo Huhunshi.
Wani daki a ka kai Zaid don a kara mishi ruwa da jini saboda he is very weak.
Har ya farfado Dr Ali na dakin yana kallonshi cike da tausayawa.
Muryar Zaid baya fita, amma sai da yayi karfin halin cewa “Na kusa mutuwa ko?” Sai da ya kasa kunne kafin yaji abunda yake cewa.
Dr Ali yace “Zaid ba wanda ya san gawan Fari, zaka samu lafia”.
Zaid yace “kar ka boye min, ka gaya min”.
Dr Ali yace “Zaid, liver dinka is damaged, you will need a transplant”.
Zaid ya lumshe jajayen idanuwanshi yace “tawa ta kare kuma, zani bi Yasmin”.
“Aa donAllah, kar kace haka, zanje gidanku na samu babanku, an san wanda zai baka hantar a diba, da anyi transplant din shikenan inshaAllah, duk da your ribs are infected once you quit smoking, you will be fine by God”.
Zaid ya murmusa yace “ina kace zaka? Gidanmu? Waste of time, kar kaje, nikam da drip dinnan ya kare zan koma Gida”.
Duk da ya san abu ne mai wahala, but zai koma gida ne kawai ya jira ajalinshi
*****
E D O
Har Bayan Azahar Mami bata ga Labiba ba.
Abun ya k'ular da Maminta, don Ubanta fushi take don an mata fada? Shiyasa bata fito ta gaishesu ba? Bata tunani ko Sallah ma tayi, tashi tayi a fusace, ta kama Labiba sai ta mareta, bude labulen dakinsu Labiba tayi, sai gani tayi wayam ba kowa.
Mamaki ya kamata, tun dazun take Prlo, yaushe labeen ta fita? Haka kawai ta tsinci kanta da lek'a kasan gadon.
Da sauri ta bar dakin ta shiga dakinsu Samira, suna nan zaune duka.
"Samira ina Labiba?"
Samira tace "tab, yo ai ni duk yau banga Labee ba".
Mami tace "tashi duba man Gidansu Jamilu ko ta shiga".
Kuiwa garesu, sai da ta dan bata lokaci tana zumbura baki kafib ta fita.
Jim kadan ta dawo tace "mamarsu jamilu tace ba ma su san Labee ta dawo ba".
Mami tace "Ikon Allah".
Mamarsu Samira tace "fushi tayi fa, kila tana Gidan Zainaba, sai kunyi biko zata dawo."
Maminta tace "Aiko Zata ci Ubanta"
Ta koma dakinta ta dauki wayarta takira diyarta Zainaba.
Ko amsa gaisuwarta batayi ba tace "Maza kice Labee ta hau A daidaita sahu ta dawo Gida yanzu ina jiranta".
Zainaba tace "Mami wace Labeen? Labee ta dawo ne?".
Mami tace "bata Gidanki?".
Zainaba tace "ai ban ma san ta dawo ba".
Kit Mami ta kashe, kiran Mai bi ma Baban Amira tayi Hamza, tace "Hamza labee na gidanka?"
Hamza yace "Aa Mami, sai dai in gidan Zainaba".
Ruwa idon Mami ya kawo tace "Hamza Labee ba ta gida, bata gidan Zainaba, in ba gidan Zainaba ba, gidanka, in ba ta nan ban kuma san inda take zuwa ba".
Hamza yace "Kar ki daga Hankalinki Mami, kinsan Labee dai, ba zata wuce Gidajen Yayyinta ba, barin kira su Hashim, sai naci Ubanta in tana fita bata gaya miki ba".
Mami tace yauwa Kirasu.
Daya bayan daya Hamza ya kira Yayyinshi da Kannenshi masu aure, daga wanda ba su ma san Labeen ta dawo Edo ba, sai wanda suke ceea aa bata zo ba".
To shima fa nan Yaya Hamza ya kasa Zama, ya hau dan babur dinshi ya burko zuwa Gida, da niyyar in ya kama Labee, wallahi babu abunda zai hana shi zane ta da Belt din Jikinshi.
Abu kamar wasa Duk inda aka san Labiba zata iya zuwa sai da aka bincika amma ba alamun wani ya ganta, an kira wayarta a kashe.
Hayaniya ya firdo da Yaya Muhammadu da Abbansu
"Mai ya faru?" Suke ta tambaya
Maman Samira tace "kunga tun dazun ne muke neman Labiba ba mu ganta ba, ba inda ba mu dibata ba, duk gidan da muka san Labiba na zuwa munje bata ba alamunta, wayarta a kashe kuma".
Abba ya saka salati, ya ma rasa me zaiyi, baban Amira kam kwallah ya fara yana tunanin tana ina.
Ba mai zama, kowa aka barbazu neman Labiba, babu wanda ya kawo ta koma katsina.
A bayyane Abba yace "kina ina Labiba?Allah ka tsare min Labiba a duk inda take".
K A T S I N A
Farfadowa tayi ta bi masu zaune a dakin da ido.
Ganin ta bude ido ya sa su mikewa tare da matsowa bakin gadonta suna mata sannu, barin ma Shafa'atu da ta fi kowaccen su zak'ewa.
Er Rabi bata iya ce musu komai ba, ta cigaba da binsu da ido daya bayana daya kafin tayi yunkurin tashi, zasu riketa ta daga musu hannu.
Da kanta ta tashi ta zauna kan Gadon ta kalli ta gefenta tace "yau wace rana?".
Alhamis aka ce mata.
Murmushi tayi tace "yau kwanan Yasmin Uku da rasuwa? Ina nan kwance kamar gawa? Meyasa baku tadani ba?".
Ba wanda yace mata komai, sauka tayi da kan Gadon ta sa Slippers ta fita daga Dakin.
'Yan kwarakonta suka bi bayanta da gudu suna mata magana bata tsaya amsa kowa ba.
Sam na ganinta ya bude mata K'ofar Mota ta shiga ya Ja Motar zuwa Gida.
****
Dr Ali bai ji cewar Zaid ba ya nufi Gidansu, zuwa gidan ke da wuya ya ga Shafaatu da Iyalanta zaune a bukkan gidan, ya gaidata ta amsashi tana son jin ko waye.
Yace “Alhaji Ali na nan?”
Tace “aa baya nan, wake nemanshi?”.
Dr Ali yace “ni ne”
Tace “lafia?”
Yace “dama Zaidu ne baya da lafia sosai, yana chan kwance, emergency surgery zaa mishi inda zaa chanza mishi Hanta, shine ake son relative ya zamana shi zai bada hantarshi”
Galala take kallonshi kafin tace “oh ashe baida lafia, yo ai bamu sani ba, mu kwana runfa daya ace har yana Asibiti ace bamu sani ba? To ba ruwanmu, kar wanda ya sake zuwa mana gida batun Zaid”.
Dr Ali yace “ni babanshi na zo gani, in baya nan ku bani number dinshi in nemeshi”.
“Shafa ta harareshi tace ai bayyi nisa ba, Annah je ki kira min Daddynki”.
Annah ta tashi tana harare harare ta tafi cikin gida jim kadan sai gashi sun dawo tare.
Dr Ali dai na ganin ikon Allah.
Yana zuwa yace “ina wuni?”
Kafin ya amsa Shafaatu ta fara bambami
“Wai Zaid zaa ma dashin Hanta shine aka zo tafiya da kai a bude cikinka a farka ka a cire naka a saka mai kai kuma sai mutuwa”.
Dr Ali yace “Aa wallahi ba haka bane, Baba, Lafiyayyen Hanta kamar bishiya ne, in aka dibeshi bayan wani lokaci da kansji zai tsiro ya dawo normal form dinshi, ba duka ake cirewa ba, diba zaayi”.
Baba yace “me ya samu Zaid din ne?”.
Jin haka Shafaatu tace “Ya kashe hantar shi da Hayaki, ya lallace shine za a zo wurinka ka bada wani Hanta, kar ka sake ka yarda”.
Kamar wanda aka sa ma battery ya fara bambamin fada.
“Ni dan Iska ne? Ni zan bada Hanta na? Kar Allah ya sa ya warke in ni yake jira”.
Dr Ali kamar yayi Ihu yace “Baba Danka Ne fa”.
Baba yace “donUbanka ka fitar min A gida”.
Dr Ali ya kasa motsi, da gudu ya dauko wani gatarin da ake saran flowers ya bishi da gudu Dr Ali ya fita.
Nan Shafaatu ta samu fagen Aibata Zaid.
%%%%%
Er Rabi na zuwa ta ga Gidan kamar ba ayi zaman gaisuwa ba, ba kowa a gidan, ta shiga ta bada umurnin "kar wanda ya shigo mata Gida, tana son kasancewa ita kadai a wannan gabar".
Dakin Yasmin ta shiga, ta na shiga ta saka jam lock tare da sulalewa k'asa, kuka kawai takeyi, kuka mai taba zuciya, ashe Baban Yasmin na nan zaune kan Gadonta, ganin Er Rabi ta shigo ya sashi yin Lamo.
Sai da ta dau lokaci mai tsawo tana kuka kafin ta share hawayenta.
Wayarta ta shiga tana scrolling Messages din Yasmin.
Inda duka rok'o takeyi kar ta taba mata Zaid dinta.
Hajia Er Rabi ta yi mamakin irin wannan So da Yasmin ke ma Zaid, yanzu ta mutu kenan tana son cetar Zaid ko? Amma dai wannan ba.
Sumbatu take "wai ta yaya zata mutu? Ta yaya zata tafi ta barta? Bata san ta na sonta ba? Bata san tana sonta fiye da rayuwa da kanta ba? Ya take so ta rayu bayan ba ta a duniya? lallai duniya abun tsoro, ko daren rasuwarta sai da sukayi Chatting fa.
Kila ma ta bar mata message yau da safe, bata bude ma, data ta kunna,messages suna ta shigowa.
Karanta last chat dinsu take kafin taga Voice note kusan 7.
Na farkon ta bude.
"MUMMY, kinsan Zaid ne farincikina ko? Mummy ki rabu da Zaid, in kika mishi wani abu wallahi ba zan taba yafe miki ba, ".
Kuka Er Rabi ta sake tare da playing Voice note na biyu inda tace
"Mummy, Ina son Zaid fiye da rayuwa da kanta, ki ka kashe Zaid, daidai yake da kin rasani".
Duk sai da tayi playing Voicenotes dinnan tas, tana jin muryar diyarta tana kuka tana nadama.
Messages din ta cigaba da bi inda wani tace "Wai yanzu Aunty Shafa ce zata dinga juya ki, ba zaki bar Bokanci ba? Mummy har kin kai matakin Kisa? Waiyoni
Mummy i am driving and its raining heavily, kin ki daukan waya, in har dagaske ne kina so na, in har dagaske kina sona fiye da komai, in har komai don ni kikeyi, zaki tayani Son abunda nike so, zaki tayani kare abunda nake so, zaki tayani Son Zaid, in har dagaske kike Mummy, zaki min Alfarmar nan".
Ta karanta wannan last message din yafi so 20,
tana kuka sosai tana "Yasmin ki yafe min, na kasance banzan uwa, sakarya da bata san meke mata ciwo ba, lallai Shaidan ya kada min kidi na kuma tika rawa sosai, na tsani kaina, na raina kaina, tir da ni wallahi, duk karfina da ikona, na kasa baki abu daya da kike so a rayuwa. Zaid kadai na kasa baki a rayuwa, yanzu ina mai matukar nadama da na kasa baki Zaid.
Baban Labiba yace "Kayya Er Rabi, kaiconki, tir da ke kam
K'arfi? Iko? Wani karfi kike dashi da iko? Bokanci? Shirka? Wayace miki rayuwa a hannun ki take? Da har zaki zabi wanda zaki raya da wanda zaki kashe, gashi garin neman ran dan wani kin nema naki, Kin kashe diyarki da kanki, wallahi ke kika kasheta".
Tsinuwar Allah su tabbata a gareki hatsabibiyar Mace, wurin gaisuwa da yawa cewa sukeyi ashe Yasmin na da Uba, kin maidani wani hoto mara amfani, banda ikon amsa sunan Uban Yasmin, don ma Yasmin na So na, mutuwarta ce silar kubutata daga duk wani kaidinki, nayi imani duk wani asirin da kika min ya rushe, saboda daga ran da Yasminta koma ga mahallincinta naji na tsaneki, na bar tsoronki, na kuma bar shakkanki.
Kuma na san mutuwa hutu ce ga Yasmin, bata da yanda zatayi nayi imani da sai ta chanza Uwa, ke annoba ce, yanzu sai ta huta lafia.
Allah ya Isa Er Rabi, Allah ya isa da kika rabani da kowa, da dangina da asalina kika maidani kamar bawanki, Allah ya isana da kika dauki shekaru kina maidani Mace sai yanda kikayi dani Allah ya isa tsakanina da ke, duk da kin gama dani, na sakeki saki Uku, abu na karshe da zan ce miki, in kinga dama kar ki fasa, ki cigaba da neman ran abunda diyarki har ta mutu tana So".
Ya tsallaketa ya fita daga dakin Yasmin ya barta zaune kamar an dasata, ta kasa motsi, banda hawaye babu abunda ke sintiri a idaniyarta, yau itace duniya ta juya ma baya?".
*****
LABIBA FA?
Tunda ta shiga Motar Suleja ta ke kuka sosai, abu 3 take ma kuka.
Na farko Mutuwar Yasmin, in ta tuna ta Mutu sai ta ji ranta ya sosu wanda tunatan na zuwa mata da hawayen ido.
Na biyu kuwa rashin sanin halin da Masoyi yake ciki, ta kira ta kira wayar a Kashe.
Na Uku kuma fitowan da tayi ba tare da sanin Iyayenta ba, fitowar da tayi ita kadai, babu wani muharammi, tafiyan awa 12 tayi jiya, gashi ta dasa.
Awa 5 zuwa 6 ya kawo su Suleja don ita ta da fito tun asuba sai 12 suka isa, ta fara galabaita tun kafin su shigo Suleja. Tunda suka shiga ta nemi Abinci a Tasha ta ci kafin taji cikinta ya dan dauka.
Bayan awa daya suka tashi don tafia Katsina.
Da gangan ta kashe wayarta, don ta san ba zaa dade ba za a san bata gida, tafia suke ta ci sosai, idanunta duk sunyi luhuluhu saboda kukan da ta keci.
Tafian wani Awa 6 zuwa 7 ne daga Suleja zuwa Katsina, in ta tuna tsawon awannin da ya rage da zai kaita Katsina sai ta ji jikinta duk yayi sanyi.
Suna ta cin tafiya, ba sa tsayawa komai sai Sallah.
Karfe 3 suka tsaya don hada Sallah Azahar da Laasar.
Wata tafiyar awa 4 ce kuma, sa kai yafi bauta ciwo, haka suka sake daukan Hanya suna ta tafia, suna ta sharara gudu, Labiba ta cigaba da zikirinta.
Tsautsayi ya samu Motar, tayar su ta fashe gab da Maghrib a daidai Wajajen Gidan Mutum daya, an dauka minti kusan 40 ana gyara, karshe akace Motar ba zai gyaru ba, sai dai su kwana, matsalar Motar haya kenan, ya zata kwana a nan? Zaid fa? Wani hali yake ciki? Ya zata kwana cikin Maza? Matansu ba su wuce 3 ba, bata damu da tafiya ita kadai wani abu ya sameta ba, ta fara tafiyarta, ganin Signboard wanda ya nuna arrow din zuwa Charanci sai taji kamar dama ta iso Gida.
Tafiya kawai take, bata san adadin tafiyar da tayi ba, ita dai ta san ta dade tana tafiya har kafarta ya fara ciwo, amma bata tsaya ba, saboda ta bar inda mutane suke, ta shigo daji, ita ko tsoro bama ta ji, ba ruwanta, batayi nadama ba, ita dai ta ganta a Katsina gaban Masoyi.
Jefi jefi ta kan sa hannu don tsaida Mota don samun Lift, amma babu wanda ya tsaya da Motarshi, tsoro ya fara mamayeta a lokacin da duhu ya soma yi, kiran Sallahr Magrib taji, da sauri ta kara sauri don isa ga Masallacin.
Tun bata hango Masallacin har ya kai ga tana hangowa.
Ta ci uwar tafiya tana isa Masallacin Matan ta zube a k'asa, tana mayar da numfashi.
Wata mata na Sallah,yaranta biyu na zaune, daya ta idar da Sallah daya yarinya ce tana shan ruwa mai sanyi.
Labiba tace "ki tsanmin ruwanki in sha donAllah".
Yarinyar ta mak'e kafada alamun "aa".
Yayarta ta ma Labiba murmushi tare da ce ma kanwarta "Give her the water".
Yarinyar tace "No".
Labiba ta dan kwantar da kai tana ajiyar zuciya lokaci lokaci tace "Sweetheart, i am really thirsty, can you give me please?".
Yarinyan tace "Noo, its mine".
Labiba da dan karfi tace "Arrggh" tare da kwantawa rigingine tana kallon ceiling tana maida numfashi.
Daidai da Sallame Sallar Mamarsu ta kalli Labiba dake maida numfashi sosai.
Zahra duba Mota kiga sun idar da Sallah? Akwai Ruwan Sanyi ki dauko mata".
Yar budurwar ta tashi ta nufi Motarsu da ke waje ta dauko ma Labiba ruwan sanyi.
Tunda Labiba ta kafa kai a robar Faro, sai da ta shaye shi tas, ta aje tana mayar da numfashi, ta dade a wannan halin, kafin ta daidaita numfashinta.
Matar kam Kallon Labiba kawai takeyi.
Labiba tace "Ina wuni?".
Hajiar tace "Lafia lau Yanmata".
Labee tace "Wallahi tafia naci a k'asa, shine fa duk na gaji".
Hajiar tabi Labibs da ido, tana karantar ta, to ko dai 'yar kauyen ce? tace "Okay, ke 'yar nan ce?".
Labiba ta gyada kai tace "aa wallahi, Daga Edo nake motar mu ta lallace wai sai dai a kwana a hanya, nikuma Wallahi ba zan kwana da Maza cikin Mota ba, mu ka san abunda zasu mana in dare ya tsala? Allah ya tsareni daga masu warin baki sai masu warin hammata, nan kaina duk ya gama sarawa, ya fiye min na kwanta a Masallacin nan da safe in nemi Lift".
Hajiar ta kalleta tace "Ina zakije ne? Kaduna?".
Tace "Aa, Katsina".
Shiru tayi tana kallon Labiban dake danna k'irjinta, bata san wacece ba amma ita da ta barta a nan ta kwana gwara ta tafi da ita".
Matar tace "Katsina Zamu yanzu".
Labiba tace "lah ashe chan kuka nufa, sallah kuka tsaya kenan".
Matar tace "Eh daga Abuja nike nima, ni da Iyalina zamuje Bikin diyar Wa na"
Labiba tace "Allah sarki".
Hajiar tace "muna iya tafiya dake".
Farinciki ya mamaye Labiba tace "Allah Hajia? Ba zan takura ba?".
Tace "haba ba wani takura, kiyi Sallahr ke dai".
Da sauri Labiba ta fita ta doro Alwala tazo ta hada Sallahr Magrhib da Isha'i.
Motar High Lander ce.
Yaranta suka shige chan baya, ita kuma da Labiba suka shiga mai bi mishi.
Driver da Yaron Hajia suka zauna gaba.
Yar budurwar ta zunguri Labiba da Ledar takeaway tace "ga snacks".
Labiba ta murmusa ta amsa tare da amayo godia.
Dadi kasheta, yunwa takeji, rabonta da Abinci tun a Tasha.
Ham ham take cin Meatpie dinnan kamar mayunwaciya.
Sai da cinye da donut ta sha Cway Juice taji tayi k'at.
Sun danyi tafiya na minti 10, Hajiar duk na nazarinta, tace "Sunana Hajia Bilkisu, kinga wannan yara na ne, na gaya miki biki zamuje Katsina, tsakaninki da Allah mai ya kawo ki Katsina tun daga Edo ke kadai, guduwa kikayi ko?".
Labiba tace "aa wallahi,zan koma".
Hajiya Bilki tace "kinga, zakiyi saar babbar yarinyata, kuma ki gaya min gaskia, bana son karya, zan taimakeki in kika gaya min gaski, in kika min k'arya in sa driver ya saukeki a nan Dajin Allah".
Window Labiba ta kalla taga bata ga Gida ko daya ba sai Bishiyoyi tace "Wallahi Aunty nidai ba duniya na shiga ba, Katsina nake karatu, Wannan ne baya Lafia kuma wayarshi bata shiga,hankalina ya kasa kwantawa shiyasa nazo ganinshi".
Hajiya tace "Saurayinki?".
Labiba ta sadda kai ta dan murmusa.
Hajiyar tace "tsakaninki da Allah iyayenki sun san kin taho?".
Cike da rashin gaskia tace "Aa".
Matar tace "guduwa din dai kikayi, kika taho dubiyan saurayi, anya kuwa ba karya kike min ba lafiyarshi lau ba? Soyyaya zai sa ki zo wurinshi ku gudu ko?".
Da sauri Labiba tace "aa wallahi, wallahi ni ba mutuniyar banza bace, wallahi dan shaye shaye ne, sai mu fi hours a dakinshi amma ko hannuba bai taba tabawa ba".
Labiba kam ta gama kashe matar a zaune, baki a bude take bin ta da ido.
"Dan Shaye Shaye? Kike so? Har kike zuwa dakinshi?". Ta kalli diyarta dake back seat tace "yo in diyata ce ai da na yankaki naji kina shiga dakin namiji, meyasa kike kai kanki wurin namiji? Wallahi wasu matan su ke kashe kansu".
Da sauri ta girgiza kai tace "Aunty donAllah kar ki man Mummunar fassara da fahimta, tsaya kiji".
Tiryan tiryan ta kwashe duk wani labari da ta sani game da Zaid ta ba Aunty Bilki.
Da mai saurin kuka ce da tayi amma irin dakakkun matan nan ne, diyarta dai tana ta hawaye.
"Allah ka mana tsari da kishiyoyi irin Hajia Shafaatu, Allah ka mana tsari da mummunar kishi, Allah ka mana tsari da yi ma 'ya'ya mugun Alkaba'i, tabbas naga mutuwar Dr Yasmin a Social Media sosai kuwa, kila mutuwarta ce ya taba lafiyarshi.
Labarin Zaid abun taussyi ne amma Labiba what you did is very wrong, kowa ya ganki yanzu he will give you a bad impression na kin baro gida zakije Katsina gun Namiji, ba wanda ya ga niyyarki, kowa zai daukeki a matsayin mutuniyar banza, ba ma haka ba, yanda kika fito ba da sanin kowa ba, wani abu ya sameki a hanya Allah shi kyauta wa gari ya waya? Me zakice? Laifin waye? Duk laifinki ne".
Sosai ta ma ta fada da nasiha, ta kuma bata baki akan tausar zucia, don a dan labarin da taji ta lura she's an extrovert, tana fadan abunda take so a lokacin da take so babu dam sakayawa, saboda gatsau tace mata "Aunty ina sonshi don ni na fara furta mishi So".
Sosai Aunty Bilki ta yi ma Labiba fada har ta sha kuka.
Aunty tace "to wallahi da kinga lafiyarshi wallahi ki kama hanyar Edo gobe ki koma Gida, ki rok'i gafarar Iyayenki, ga dubu 10, ki mayar ma Maminki kudin da kika sata, sauran kiyi kudin Mota".
Labiba ta murmusa tace "inshaAllahu Aunty, na daukar miki Alkawari, nagode sosai".
Suka iso Katsina Lafia, har tudun matawalle suka kaita, har gaban gidan Alhaji Ali Zaki.
Labiba ta bude Mota.
Tace "Ba zaki shigo ku gaisa da Matar Yayana ba?"
Aunty Bilki ta girgiza kai tace "aa Labiba munyi dare".
To nagode kwarai, Allah ya saka miki da Alheri ya tsareki ya tsare miki 'ya'yanki, yanda kika taimakeni Allah ya taimakeki, inshaAllah yaranki zasu zama abun Alfahari a dunia baki daya".
Ta amsa da "Amin Amin nagode da adduoinki, naji dadinsu Allah ya amsa"
Labiba tayi sallama da yaran Hajia, har ta juya zaya tafi gida Hajia ta dakatar da ita.
Labiba ta dan Matso bakin window, Hajia tayi rubutu a wani takarda ta ba Labiba tace "Ina So na samo ma DanMakaho aiki, ina da hanyar Civil Defense, in yana da raayi ki bashi email address dina gashi nan ya tura min CV dinshi ko da secondary certificate ya samu ai yafi mishi zaman banzan nan, ga number nan kuma ki kirani inji ko kin koma Edon".
Hajia bata tsaya jin Godiar Labiba ba tayi whinning glass shi kuma Driver ya ja mota aka bar Labiba tsaye da mamakin Hajia Bilki.
Haka Allah ke abunshi, haka Allah ke sa jinin mutane haduwa ba tare da jini mai gudana ba.
Ita ta san haduwarta da Hajia Bilkisu Alkhairi ne.
"Hajia Bilkisu Beebbs nagodia, Allah ya baki farinciki a duk inda kike" mai makon ta shiga Gidansu kawai ta fada gidansu Zaid.
Yau ta Gate Beebs aka shiga Gidansu Zaid.
Ba ta tsaya ko ina ba sai dakin Zaid,
Wayam bashi ba alaminshi, wayarshi ta gani a k’asa da sauro ta dauka, tana kunnata ba charge, ta tura toilet taga baya ciki, yana ina? Ko yaje Bencin Eskaley, da sauri ta fita waje ta nufa Bencin Eskaley.
Suna ganinta suka mimmike, “Yayarmu ina wuni”
Bata amsa ba tace “donAllah ina Zaid?”
Sukace “Yo ai duk yau bamu ga Mankas ba”.
“Baku ganshi ba?”
Be fito ba gaskia, bamu ganshi ba, jiya dai mun ganshi har muka mishi Taaziyar Yasmin”.
Bata tsaya gama jin zancen ba ta koma Gidansu Mankas din.
Ba tsoro ta shiga Parlorn suna zaune.
Alhaji Ali tace “Ina wuni?”.
Zai yi magana Hajia Shafa tace “wacece ke?”.
Tace “sunana Labiba, ina neman Zaid ne”.
Shafaatu kamar an watsa mata garwashi tace “ba zaa bashi Hantar ba, ya mutu dole ne?ina ruwanmu”.
Labiba bata gane inda ya dosa ba tace “Mene? Ni Zaid na zo nema”.
Annah tace “Dallah Mallama ki fitar mana daga Gida”
Labiba ta kallesu tace “Ni fa ba wai zuwa nayi ku daga min jijiyoyin wuya ba, tambaya ce na muku, in baku san inda yake ba, ku gaya min, sai na je wani gu na tambayeshi”.
Annah tace “Karuwa har Gida kike biyoshi?”.
Sosai Labiba taji zafin zancen cikin fushi tace “Uwarki ce karuwa”.
Shafa’atu tace “kam bala’i uwarta ni kenan?”.
Labiba ta rausayar da kanta ta kalli Baban Zaid, sai taji ya bata tausayi”.
Fita kawai tayi a Parlon ta bar gidan, har zata shiga Gidan Yaya Muhammadu ta fasa ta dawo Gidan Alhaji Ali tace da Maigadi “DonAllah ko ka ga Fitar DanMakaho?”.
Maigadi yace “Eh, bai da lafia sosai wallahi dazun ni na kama ma wani abokinshi muka sashi Mota Abokin ya tafi da shi General.
Da gudu Labiba ta fita, bata shiga Gidansu ba tayi hanyar bakin Titi hankalinta a tashe.
Yan Bencin Eskaley nata mata magana tayi banza dasu.
Keke Napep ta tsaida tace a kaita General Hospital.
Ta na isa ta nufa Accident and Emergency, ta bada sunanshi gun reception akace anyi moving dinshi an bashi gado Amenity room 7.
Bata san ina ne Amenity ba amma bata ma tsaya tambaya ba.
Da taimakon Signboards ta gano Amenity, ta shiga ta fara neman dakuna.
Tana ganin room 7 ta karasa a guje ta bude da karfi.
Chan kan Gado ta hangoshi kwance kamar tabarma, da sauri ta karasa gunshi kamar zata daukoshi daga kan Gadon.
A hankali Zaid ya bude idonshi ya saukesu fes kan Labiba a wahalace da sauri yayi yunk’urin tashi, tayi saurin maida shi ta sakar mai murmushi mai ciwo, kauda kai yayi bai so ta ganshi cikin ciwo, bai so ta san weakeness dinshi.
Sannu ta shiga jera mishi, bya juyo ya kalleta yana niyyan magana bata ji meya ce ba, ta sa kunneta a daidai bakinshi yace “Yasmin ta tafi Beebs”.
Tace “Yasmin ta tafi Allah ya gafarta mata, lets focus on you now, you are sick”.
Yace “I am dying”.
Tace “shuttup gashi ana kara maka ruwa da jini inshaAllah kafin su kare ka warke”.
Murmushi kawai ya mata.
Socket ta nufa tace “Wayarka ba charge, daga gidanku fa nake”.
Da charger dinta ta jona mishi charge.
Ta dawo ta zauna a kan kujeran da ke gabanshi.
Tace “Sannu”
Yace “ya kamata ace kina Edo”.
Tace “Masoyin baida lafia”.
A hankali yace “Ta yaya kika zo?”.
Tace “in ka warke zan baka labari”.
A hankali aka bude Kofar.
Labiba ta juya ga k’ofar Drs ne su biyu suka shigo
Ta mike da fara’arta.
Tace “Sannunku”.
Dr Ali yace “Zaid bak’uwa akayi?”.
Zaid ya kanne idonshi yana so ya ma Dr Ali inkiya da kar ya gaya ma Labiba.
Labiba tace “Yauwa Dr, ya mai jiki? Stress ne ko?”.
Dr Habib yace “dama Stress ne da sauk’i, he is very sick wallahi”.
Tace “toufa, what exactly is wrong with him?”.
Dr Habib yace “Liver is damaged, he needs a transplant”.
A firgice tace “He Needs a Whatttt?”.
Zaid yui saurin runste Ido.
Da sauri ta kalli Zaid kafin ta kalli Dr Ali kafin ta kalli Dr Habib.
“Bangane ba Dr”.
A gajiye, a galabaice Zaid yace “Beebs”.
Ta san da kyar muryar ta budu, amma ta ki kallonshi tace “Dr kamin bayani?”.
Dr Habib yace “Are you a Family”.
A kagaucd tace “Ni zai aura, mun kusa aure, and i think i deserve to know what is wrong with my Fiance”.
Dr Habib yace “follow me”.
Bata jira komai ba ta bi bayanshi.
Zaid yace “Ali, donAllah ka hanashi magana”.
Ali yace “Budurwarka ce?”.
Zaid yace “it doesnt matter ka taimakeni kar ta san komai, tell her malaria ce kawai”.
Dr Ali ya fita ya bi bayansu, ko da ya shiga Labiba na zaune tana sauraron Maganganun da ke fita daga bakin Dr Habib.
Hawaye tuni sun wanke mata fuska, Zaid na dauke da ciwukka all this while bata taba sani ba? An fi shekara da akayi diagnosing dinshi amma ko da wasa bata taba sani ba? Ya Illahi, zuciyarta ta dafe dake barazanar fitowa.
Cikin Kuka tace “To a mishi surgery din mana me ake jira? Da bakinka kace Emergency ne”.
Dr Ali yace “Wallahi ba mai donating, naje Gidansu na gaya ma Babanshi baki ga wulakancin da suka min ba da gatari suka bini, Mamarshi kuma bata nan, nace zanyi contacting dinta yace baida contact din Mamanshi tunda suka rabu, nace kanwarshi yace “ta tafi Ghana wurin kakansu, nace dangin Babanshi ya ki magana tun dazun”.
Labiba tace “K’arya, yanzu what will happen in be samu Surgery din ba?”.
Dr Habib ya dauko Xray ya na nuna mata yace “he will slowly Die, dont forget his Ribs are Infected, and its close to the Heart, when he breathes in the Heart touches the veins of the liver, its risky”.
Da sauri tace “then mai ake jira, muna bata wani lokacin ne, lets have the surgery now”.
Sukace “who is donating?”
Tace “Me, prepare for the surgery now”.
Ta mike ta fita ta barsu su biyu suna binta da kallon mamaki.
Dakin ta koma.
Ta karasa da kallon tausayi tace “Kayi hakuri, duk wannan wahalar ka shata kai kadai, i am sorry you went through this alone, i am here for you now”.
Ko bata fada ba ya san me take shirin yi, yasan mai zatayi
Ya girgiza kai yace “Labiba Dont, karki yarda a budeki, mutuwa zanyi, theres a possibility ko an yi surgery din ba zan rayu ba, kuma donor din will be at risk, kar kiyi, ba zan yarda ba, i am dying”.
Murmushi take mishi mai tarin ma’anoni daidai ta digar hawayenta tace “ZAN RAYU DA KAI, ZAN MUTU DA KAI”.
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO😉
A tasha tayi Sallahr Asuba, Motar Suleja ta hau, tunda ta shiga Motar suka fara tafia gabanta yake faduwa, fargaba da tsoro suka cika mata zuciya, kar suyi Accident fa, ji take kamar ta sauka, amma zuciyarta ta riga ta kitsa mata, bacci takeji amma bata ga ta bacci ba haka tayi zaune tana sak'e a ranta.
Allah ya kaisu Suleja Lafia, daga nan ta hau Motar Katsina.
A B U J A
Mancy na dakin Abba, Dalo ita kadai ke zaune a Dakin Mancy ta na neman wayar Zaid ta kasa samunshi, a duk lokacin da ta tuna Yasmin da Alherinta sai ta zubda hawaye, sallama yake tayi, bata ji ba, har yazo gabanta ya zauna.
Hannu ya tafa, ta dan firgita.
"Ina kwana?" Ta gaisheshi kanta a duk'e.
Bai amsa ba yace "tunanin me kikeyi?".
Murmushi ta dan kirkiro tace "bakomai".
Yace "Ba nace a daina kukan nan haka ba?".
Marairaicewa tayi tace "fa ba kuka nakeyi ba?".
Irin muryarta yayi yace "to me kikeyi?
Da sauri ta kalleshi jin yanda yayi magana kamar wani dan auta, au danauta ne ashe, dauke ido tayi saboda kallon da yake binta dashi.
Yace "Kin gaya min matsayin Yasmin a wurinku, zan sake gaya miki kamar yanda na gaya miki jiya, shi mamaci addua yake so fiye da komai, kuka baya kara musu komai sai nauyi, ki roka mata rahama, balle ita da muke sa ran inshaAllah tayi mutuwar Shahada, ki bar mata kuka please".
Duk jikinta ya mutu da yanayin maganarshi, shi haka yake? Haka yake magana? Muryarshi sanyi? Wannan in ta cigaba da sauraran muryarshi sai ya sa ta shiga wani yanayi".
Yace "dama Abba yace muje na miki register Catering School kafin a samo miki Admission a Nile University".
Cikin jin dadi tace "Dagaske?".
Ya langwabar da kai yace "eh dagaske".
Ta sa hannu ta rufe fuskanta, ta lura Ya Jawad na san zolayarta.
Ya mik'e tsaye yace "ina jiranki a waje".
Ya fita, ta bi bayanshi da Ido.
FIKRA Catering School ya mata register, maimakon su wuce Gida, sai ya shiga Yawon nuna mata gari, don ya san in suka koma Gida daki zata shige tayi ta kuka, shi kuma har ga Allah baya son Kukan nan.
Sai da ya ga tayi daria kafin ya daina k'okarin sanyata daria.
Akwai wani abu da yake ji a game da ita, yana ganin kamar Tausayi ne, amma cikin zuciyanshi ya san ba haka bane.
Na wani dan lokaci Dalo ta manta da damuwarta, yanda Jawad ke ji da ita ya sa take jin wani abu game dashi, ta san shi ba tsaranta bane Hmm, a dai bar maganar.
K A T S I N A
Tarin da Dr Ali ya ji Zaid nayi jiya ya tsaya mishi a rai, yana tsoron kar stage din TBC dinshi ya kai ga Liver Transplant, wayarshi ya dauka ya latso Zaid amma wayarshi is switched off, sak'e sak'e yayi tayi daga k'arshe ya yanke hukuncin zuwa ganin Zaid, daga nan ma ya zo ya mishi tests a ga yaua matsayin ciwonshi yake yanzu.
Maigadi ya tabbatar da cewa Zaid na cikin gida, ba tare da jiran komai ba Dr Ali ya nufi Boysquaters, yana shiga dakin ya ga Zaid kwance murus k'asa, da sauri ya karasa gunshi yana jijiga shi, da alamun ba yanzu yayi collapsing ba.
Da yake Dr Ali Giant ne, haka ya saba Zaid a baya ya fita don kaishi Asibiti, a kagauce yace da Maigadi "donAllah je ka fada cikin gida Zaid baya da Lafia, na tafi dashi General Hospital"
Bai jira cewar maigadi ba ya bude motar ya tura Zaid shi kuma ya shige motarr.
Maigadi yayi cikin da gudu don sanar da su.
Hannah kadai aka samu, Shafaa na chan gun Er Rabi.
Da aka gaya ma Hannah tabe baki kawai tayi yo su ina ruwansu da wani rashin lafian Zaid? Allah sa ma ya mutu.
A Asibiti tuni an kaishi Emergency Room Likitoci suka dukufa kanshi, abunda Dr Ali ke gudu shi ya faru, Kusan rabi da kwatar Hantar Zaid ta lallace, kuma in har baa mishi dashin Hantar ba, to Hantarshi zata fashe, ga Hak'ark'arinshi duk sunyi bak'i saboda hayak'i dake bi ta wurin.
Dr's suka yanke shawaran yi mishi aiki cikin gaggawa saboda kar lallacewan Hantar ya tabo Huhunshi.
Wani daki a ka kai Zaid don a kara mishi ruwa da jini saboda he is very weak.
Har ya farfado Dr Ali na dakin yana kallonshi cike da tausayawa.
Muryar Zaid baya fita, amma sai da yayi karfin halin cewa “Na kusa mutuwa ko?” Sai da ya kasa kunne kafin yaji abunda yake cewa.
Dr Ali yace “Zaid ba wanda ya san gawan Fari, zaka samu lafia”.
Zaid yace “kar ka boye min, ka gaya min”.
Dr Ali yace “Zaid, liver dinka is damaged, you will need a transplant”.
Zaid ya lumshe jajayen idanuwanshi yace “tawa ta kare kuma, zani bi Yasmin”.
“Aa donAllah, kar kace haka, zanje gidanku na samu babanku, an san wanda zai baka hantar a diba, da anyi transplant din shikenan inshaAllah, duk da your ribs are infected once you quit smoking, you will be fine by God”.
Zaid ya murmusa yace “ina kace zaka? Gidanmu? Waste of time, kar kaje, nikam da drip dinnan ya kare zan koma Gida”.
Duk da ya san abu ne mai wahala, but zai koma gida ne kawai ya jira ajalinshi
*****
E D O
Har Bayan Azahar Mami bata ga Labiba ba.
Abun ya k'ular da Maminta, don Ubanta fushi take don an mata fada? Shiyasa bata fito ta gaishesu ba? Bata tunani ko Sallah ma tayi, tashi tayi a fusace, ta kama Labiba sai ta mareta, bude labulen dakinsu Labiba tayi, sai gani tayi wayam ba kowa.
Mamaki ya kamata, tun dazun take Prlo, yaushe labeen ta fita? Haka kawai ta tsinci kanta da lek'a kasan gadon.
Da sauri ta bar dakin ta shiga dakinsu Samira, suna nan zaune duka.
"Samira ina Labiba?"
Samira tace "tab, yo ai ni duk yau banga Labee ba".
Mami tace "tashi duba man Gidansu Jamilu ko ta shiga".
Kuiwa garesu, sai da ta dan bata lokaci tana zumbura baki kafib ta fita.
Jim kadan ta dawo tace "mamarsu jamilu tace ba ma su san Labee ta dawo ba".
Mami tace "Ikon Allah".
Mamarsu Samira tace "fushi tayi fa, kila tana Gidan Zainaba, sai kunyi biko zata dawo."
Maminta tace "Aiko Zata ci Ubanta"
Ta koma dakinta ta dauki wayarta takira diyarta Zainaba.
Ko amsa gaisuwarta batayi ba tace "Maza kice Labee ta hau A daidaita sahu ta dawo Gida yanzu ina jiranta".
Zainaba tace "Mami wace Labeen? Labee ta dawo ne?".
Mami tace "bata Gidanki?".
Zainaba tace "ai ban ma san ta dawo ba".
Kit Mami ta kashe, kiran Mai bi ma Baban Amira tayi Hamza, tace "Hamza labee na gidanka?"
Hamza yace "Aa Mami, sai dai in gidan Zainaba".
Ruwa idon Mami ya kawo tace "Hamza Labee ba ta gida, bata gidan Zainaba, in ba gidan Zainaba ba, gidanka, in ba ta nan ban kuma san inda take zuwa ba".
Hamza yace "Kar ki daga Hankalinki Mami, kinsan Labee dai, ba zata wuce Gidajen Yayyinta ba, barin kira su Hashim, sai naci Ubanta in tana fita bata gaya miki ba".
Mami tace yauwa Kirasu.
Daya bayan daya Hamza ya kira Yayyinshi da Kannenshi masu aure, daga wanda ba su ma san Labeen ta dawo Edo ba, sai wanda suke ceea aa bata zo ba".
To shima fa nan Yaya Hamza ya kasa Zama, ya hau dan babur dinshi ya burko zuwa Gida, da niyyar in ya kama Labee, wallahi babu abunda zai hana shi zane ta da Belt din Jikinshi.
Abu kamar wasa Duk inda aka san Labiba zata iya zuwa sai da aka bincika amma ba alamun wani ya ganta, an kira wayarta a kashe.
Hayaniya ya firdo da Yaya Muhammadu da Abbansu
"Mai ya faru?" Suke ta tambaya
Maman Samira tace "kunga tun dazun ne muke neman Labiba ba mu ganta ba, ba inda ba mu dibata ba, duk gidan da muka san Labiba na zuwa munje bata ba alamunta, wayarta a kashe kuma".
Abba ya saka salati, ya ma rasa me zaiyi, baban Amira kam kwallah ya fara yana tunanin tana ina.
Ba mai zama, kowa aka barbazu neman Labiba, babu wanda ya kawo ta koma katsina.
A bayyane Abba yace "kina ina Labiba?Allah ka tsare min Labiba a duk inda take".
K A T S I N A
Farfadowa tayi ta bi masu zaune a dakin da ido.
Ganin ta bude ido ya sa su mikewa tare da matsowa bakin gadonta suna mata sannu, barin ma Shafa'atu da ta fi kowaccen su zak'ewa.
Er Rabi bata iya ce musu komai ba, ta cigaba da binsu da ido daya bayana daya kafin tayi yunkurin tashi, zasu riketa ta daga musu hannu.
Da kanta ta tashi ta zauna kan Gadon ta kalli ta gefenta tace "yau wace rana?".
Alhamis aka ce mata.
Murmushi tayi tace "yau kwanan Yasmin Uku da rasuwa? Ina nan kwance kamar gawa? Meyasa baku tadani ba?".
Ba wanda yace mata komai, sauka tayi da kan Gadon ta sa Slippers ta fita daga Dakin.
'Yan kwarakonta suka bi bayanta da gudu suna mata magana bata tsaya amsa kowa ba.
Sam na ganinta ya bude mata K'ofar Mota ta shiga ya Ja Motar zuwa Gida.
****
Dr Ali bai ji cewar Zaid ba ya nufi Gidansu, zuwa gidan ke da wuya ya ga Shafaatu da Iyalanta zaune a bukkan gidan, ya gaidata ta amsashi tana son jin ko waye.
Yace “Alhaji Ali na nan?”
Tace “aa baya nan, wake nemanshi?”.
Dr Ali yace “ni ne”
Tace “lafia?”
Yace “dama Zaidu ne baya da lafia sosai, yana chan kwance, emergency surgery zaa mishi inda zaa chanza mishi Hanta, shine ake son relative ya zamana shi zai bada hantarshi”
Galala take kallonshi kafin tace “oh ashe baida lafia, yo ai bamu sani ba, mu kwana runfa daya ace har yana Asibiti ace bamu sani ba? To ba ruwanmu, kar wanda ya sake zuwa mana gida batun Zaid”.
Dr Ali yace “ni babanshi na zo gani, in baya nan ku bani number dinshi in nemeshi”.
“Shafa ta harareshi tace ai bayyi nisa ba, Annah je ki kira min Daddynki”.
Annah ta tashi tana harare harare ta tafi cikin gida jim kadan sai gashi sun dawo tare.
Dr Ali dai na ganin ikon Allah.
Yana zuwa yace “ina wuni?”
Kafin ya amsa Shafaatu ta fara bambami
“Wai Zaid zaa ma dashin Hanta shine aka zo tafiya da kai a bude cikinka a farka ka a cire naka a saka mai kai kuma sai mutuwa”.
Dr Ali yace “Aa wallahi ba haka bane, Baba, Lafiyayyen Hanta kamar bishiya ne, in aka dibeshi bayan wani lokaci da kansji zai tsiro ya dawo normal form dinshi, ba duka ake cirewa ba, diba zaayi”.
Baba yace “me ya samu Zaid din ne?”.
Jin haka Shafaatu tace “Ya kashe hantar shi da Hayaki, ya lallace shine za a zo wurinka ka bada wani Hanta, kar ka sake ka yarda”.
Kamar wanda aka sa ma battery ya fara bambamin fada.
“Ni dan Iska ne? Ni zan bada Hanta na? Kar Allah ya sa ya warke in ni yake jira”.
Dr Ali kamar yayi Ihu yace “Baba Danka Ne fa”.
Baba yace “donUbanka ka fitar min A gida”.
Dr Ali ya kasa motsi, da gudu ya dauko wani gatarin da ake saran flowers ya bishi da gudu Dr Ali ya fita.
Nan Shafaatu ta samu fagen Aibata Zaid.
%%%%%
Er Rabi na zuwa ta ga Gidan kamar ba ayi zaman gaisuwa ba, ba kowa a gidan, ta shiga ta bada umurnin "kar wanda ya shigo mata Gida, tana son kasancewa ita kadai a wannan gabar".
Dakin Yasmin ta shiga, ta na shiga ta saka jam lock tare da sulalewa k'asa, kuka kawai takeyi, kuka mai taba zuciya, ashe Baban Yasmin na nan zaune kan Gadonta, ganin Er Rabi ta shigo ya sashi yin Lamo.
Sai da ta dau lokaci mai tsawo tana kuka kafin ta share hawayenta.
Wayarta ta shiga tana scrolling Messages din Yasmin.
Inda duka rok'o takeyi kar ta taba mata Zaid dinta.
Hajia Er Rabi ta yi mamakin irin wannan So da Yasmin ke ma Zaid, yanzu ta mutu kenan tana son cetar Zaid ko? Amma dai wannan ba.
Sumbatu take "wai ta yaya zata mutu? Ta yaya zata tafi ta barta? Bata san ta na sonta ba? Bata san tana sonta fiye da rayuwa da kanta ba? Ya take so ta rayu bayan ba ta a duniya? lallai duniya abun tsoro, ko daren rasuwarta sai da sukayi Chatting fa.
Kila ma ta bar mata message yau da safe, bata bude ma, data ta kunna,messages suna ta shigowa.
Karanta last chat dinsu take kafin taga Voice note kusan 7.
Na farkon ta bude.
"MUMMY, kinsan Zaid ne farincikina ko? Mummy ki rabu da Zaid, in kika mishi wani abu wallahi ba zan taba yafe miki ba, ".
Kuka Er Rabi ta sake tare da playing Voice note na biyu inda tace
"Mummy, Ina son Zaid fiye da rayuwa da kanta, ki ka kashe Zaid, daidai yake da kin rasani".
Duk sai da tayi playing Voicenotes dinnan tas, tana jin muryar diyarta tana kuka tana nadama.
Messages din ta cigaba da bi inda wani tace "Wai yanzu Aunty Shafa ce zata dinga juya ki, ba zaki bar Bokanci ba? Mummy har kin kai matakin Kisa? Waiyoni
Mummy i am driving and its raining heavily, kin ki daukan waya, in har dagaske ne kina so na, in har dagaske kina sona fiye da komai, in har komai don ni kikeyi, zaki tayani Son abunda nike so, zaki tayani kare abunda nake so, zaki tayani Son Zaid, in har dagaske kike Mummy, zaki min Alfarmar nan".
Ta karanta wannan last message din yafi so 20,
tana kuka sosai tana "Yasmin ki yafe min, na kasance banzan uwa, sakarya da bata san meke mata ciwo ba, lallai Shaidan ya kada min kidi na kuma tika rawa sosai, na tsani kaina, na raina kaina, tir da ni wallahi, duk karfina da ikona, na kasa baki abu daya da kike so a rayuwa. Zaid kadai na kasa baki a rayuwa, yanzu ina mai matukar nadama da na kasa baki Zaid.
Baban Labiba yace "Kayya Er Rabi, kaiconki, tir da ke kam
K'arfi? Iko? Wani karfi kike dashi da iko? Bokanci? Shirka? Wayace miki rayuwa a hannun ki take? Da har zaki zabi wanda zaki raya da wanda zaki kashe, gashi garin neman ran dan wani kin nema naki, Kin kashe diyarki da kanki, wallahi ke kika kasheta".
Tsinuwar Allah su tabbata a gareki hatsabibiyar Mace, wurin gaisuwa da yawa cewa sukeyi ashe Yasmin na da Uba, kin maidani wani hoto mara amfani, banda ikon amsa sunan Uban Yasmin, don ma Yasmin na So na, mutuwarta ce silar kubutata daga duk wani kaidinki, nayi imani duk wani asirin da kika min ya rushe, saboda daga ran da Yasminta koma ga mahallincinta naji na tsaneki, na bar tsoronki, na kuma bar shakkanki.
Kuma na san mutuwa hutu ce ga Yasmin, bata da yanda zatayi nayi imani da sai ta chanza Uwa, ke annoba ce, yanzu sai ta huta lafia.
Allah ya Isa Er Rabi, Allah ya isa da kika rabani da kowa, da dangina da asalina kika maidani kamar bawanki, Allah ya isana da kika dauki shekaru kina maidani Mace sai yanda kikayi dani Allah ya isa tsakanina da ke, duk da kin gama dani, na sakeki saki Uku, abu na karshe da zan ce miki, in kinga dama kar ki fasa, ki cigaba da neman ran abunda diyarki har ta mutu tana So".
Ya tsallaketa ya fita daga dakin Yasmin ya barta zaune kamar an dasata, ta kasa motsi, banda hawaye babu abunda ke sintiri a idaniyarta, yau itace duniya ta juya ma baya?".
*****
LABIBA FA?
Tunda ta shiga Motar Suleja ta ke kuka sosai, abu 3 take ma kuka.
Na farko Mutuwar Yasmin, in ta tuna ta Mutu sai ta ji ranta ya sosu wanda tunatan na zuwa mata da hawayen ido.
Na biyu kuwa rashin sanin halin da Masoyi yake ciki, ta kira ta kira wayar a Kashe.
Na Uku kuma fitowan da tayi ba tare da sanin Iyayenta ba, fitowar da tayi ita kadai, babu wani muharammi, tafiyan awa 12 tayi jiya, gashi ta dasa.
Awa 5 zuwa 6 ya kawo su Suleja don ita ta da fito tun asuba sai 12 suka isa, ta fara galabaita tun kafin su shigo Suleja. Tunda suka shiga ta nemi Abinci a Tasha ta ci kafin taji cikinta ya dan dauka.
Bayan awa daya suka tashi don tafia Katsina.
Da gangan ta kashe wayarta, don ta san ba zaa dade ba za a san bata gida, tafia suke ta ci sosai, idanunta duk sunyi luhuluhu saboda kukan da ta keci.
Tafian wani Awa 6 zuwa 7 ne daga Suleja zuwa Katsina, in ta tuna tsawon awannin da ya rage da zai kaita Katsina sai ta ji jikinta duk yayi sanyi.
Suna ta cin tafiya, ba sa tsayawa komai sai Sallah.
Karfe 3 suka tsaya don hada Sallah Azahar da Laasar.
Wata tafiyar awa 4 ce kuma, sa kai yafi bauta ciwo, haka suka sake daukan Hanya suna ta tafia, suna ta sharara gudu, Labiba ta cigaba da zikirinta.
Tsautsayi ya samu Motar, tayar su ta fashe gab da Maghrib a daidai Wajajen Gidan Mutum daya, an dauka minti kusan 40 ana gyara, karshe akace Motar ba zai gyaru ba, sai dai su kwana, matsalar Motar haya kenan, ya zata kwana a nan? Zaid fa? Wani hali yake ciki? Ya zata kwana cikin Maza? Matansu ba su wuce 3 ba, bata damu da tafiya ita kadai wani abu ya sameta ba, ta fara tafiyarta, ganin Signboard wanda ya nuna arrow din zuwa Charanci sai taji kamar dama ta iso Gida.
Tafiya kawai take, bata san adadin tafiyar da tayi ba, ita dai ta san ta dade tana tafiya har kafarta ya fara ciwo, amma bata tsaya ba, saboda ta bar inda mutane suke, ta shigo daji, ita ko tsoro bama ta ji, ba ruwanta, batayi nadama ba, ita dai ta ganta a Katsina gaban Masoyi.
Jefi jefi ta kan sa hannu don tsaida Mota don samun Lift, amma babu wanda ya tsaya da Motarshi, tsoro ya fara mamayeta a lokacin da duhu ya soma yi, kiran Sallahr Magrib taji, da sauri ta kara sauri don isa ga Masallacin.
Tun bata hango Masallacin har ya kai ga tana hangowa.
Ta ci uwar tafiya tana isa Masallacin Matan ta zube a k'asa, tana mayar da numfashi.
Wata mata na Sallah,yaranta biyu na zaune, daya ta idar da Sallah daya yarinya ce tana shan ruwa mai sanyi.
Labiba tace "ki tsanmin ruwanki in sha donAllah".
Yarinyar ta mak'e kafada alamun "aa".
Yayarta ta ma Labiba murmushi tare da ce ma kanwarta "Give her the water".
Yarinyar tace "No".
Labiba ta dan kwantar da kai tana ajiyar zuciya lokaci lokaci tace "Sweetheart, i am really thirsty, can you give me please?".
Yarinyan tace "Noo, its mine".
Labiba da dan karfi tace "Arrggh" tare da kwantawa rigingine tana kallon ceiling tana maida numfashi.
Daidai da Sallame Sallar Mamarsu ta kalli Labiba dake maida numfashi sosai.
Zahra duba Mota kiga sun idar da Sallah? Akwai Ruwan Sanyi ki dauko mata".
Yar budurwar ta tashi ta nufi Motarsu da ke waje ta dauko ma Labiba ruwan sanyi.
Tunda Labiba ta kafa kai a robar Faro, sai da ta shaye shi tas, ta aje tana mayar da numfashi, ta dade a wannan halin, kafin ta daidaita numfashinta.
Matar kam Kallon Labiba kawai takeyi.
Labiba tace "Ina wuni?".
Hajiar tace "Lafia lau Yanmata".
Labee tace "Wallahi tafia naci a k'asa, shine fa duk na gaji".
Hajiar tabi Labibs da ido, tana karantar ta, to ko dai 'yar kauyen ce? tace "Okay, ke 'yar nan ce?".
Labiba ta gyada kai tace "aa wallahi, Daga Edo nake motar mu ta lallace wai sai dai a kwana a hanya, nikuma Wallahi ba zan kwana da Maza cikin Mota ba, mu ka san abunda zasu mana in dare ya tsala? Allah ya tsareni daga masu warin baki sai masu warin hammata, nan kaina duk ya gama sarawa, ya fiye min na kwanta a Masallacin nan da safe in nemi Lift".
Hajiar ta kalleta tace "Ina zakije ne? Kaduna?".
Tace "Aa, Katsina".
Shiru tayi tana kallon Labiban dake danna k'irjinta, bata san wacece ba amma ita da ta barta a nan ta kwana gwara ta tafi da ita".
Matar tace "Katsina Zamu yanzu".
Labiba tace "lah ashe chan kuka nufa, sallah kuka tsaya kenan".
Matar tace "Eh daga Abuja nike nima, ni da Iyalina zamuje Bikin diyar Wa na"
Labiba tace "Allah sarki".
Hajiar tace "muna iya tafiya dake".
Farinciki ya mamaye Labiba tace "Allah Hajia? Ba zan takura ba?".
Tace "haba ba wani takura, kiyi Sallahr ke dai".
Da sauri Labiba ta fita ta doro Alwala tazo ta hada Sallahr Magrhib da Isha'i.
Motar High Lander ce.
Yaranta suka shige chan baya, ita kuma da Labiba suka shiga mai bi mishi.
Driver da Yaron Hajia suka zauna gaba.
Yar budurwar ta zunguri Labiba da Ledar takeaway tace "ga snacks".
Labiba ta murmusa ta amsa tare da amayo godia.
Dadi kasheta, yunwa takeji, rabonta da Abinci tun a Tasha.
Ham ham take cin Meatpie dinnan kamar mayunwaciya.
Sai da cinye da donut ta sha Cway Juice taji tayi k'at.
Sun danyi tafiya na minti 10, Hajiar duk na nazarinta, tace "Sunana Hajia Bilkisu, kinga wannan yara na ne, na gaya miki biki zamuje Katsina, tsakaninki da Allah mai ya kawo ki Katsina tun daga Edo ke kadai, guduwa kikayi ko?".
Labiba tace "aa wallahi,zan koma".
Hajiya Bilki tace "kinga, zakiyi saar babbar yarinyata, kuma ki gaya min gaskia, bana son karya, zan taimakeki in kika gaya min gaski, in kika min k'arya in sa driver ya saukeki a nan Dajin Allah".
Window Labiba ta kalla taga bata ga Gida ko daya ba sai Bishiyoyi tace "Wallahi Aunty nidai ba duniya na shiga ba, Katsina nake karatu, Wannan ne baya Lafia kuma wayarshi bata shiga,hankalina ya kasa kwantawa shiyasa nazo ganinshi".
Hajiya tace "Saurayinki?".
Labiba ta sadda kai ta dan murmusa.
Hajiyar tace "tsakaninki da Allah iyayenki sun san kin taho?".
Cike da rashin gaskia tace "Aa".
Matar tace "guduwa din dai kikayi, kika taho dubiyan saurayi, anya kuwa ba karya kike min ba lafiyarshi lau ba? Soyyaya zai sa ki zo wurinshi ku gudu ko?".
Da sauri Labiba tace "aa wallahi, wallahi ni ba mutuniyar banza bace, wallahi dan shaye shaye ne, sai mu fi hours a dakinshi amma ko hannuba bai taba tabawa ba".
Labiba kam ta gama kashe matar a zaune, baki a bude take bin ta da ido.
"Dan Shaye Shaye? Kike so? Har kike zuwa dakinshi?". Ta kalli diyarta dake back seat tace "yo in diyata ce ai da na yankaki naji kina shiga dakin namiji, meyasa kike kai kanki wurin namiji? Wallahi wasu matan su ke kashe kansu".
Da sauri ta girgiza kai tace "Aunty donAllah kar ki man Mummunar fassara da fahimta, tsaya kiji".
Tiryan tiryan ta kwashe duk wani labari da ta sani game da Zaid ta ba Aunty Bilki.
Da mai saurin kuka ce da tayi amma irin dakakkun matan nan ne, diyarta dai tana ta hawaye.
"Allah ka mana tsari da kishiyoyi irin Hajia Shafaatu, Allah ka mana tsari da mummunar kishi, Allah ka mana tsari da yi ma 'ya'ya mugun Alkaba'i, tabbas naga mutuwar Dr Yasmin a Social Media sosai kuwa, kila mutuwarta ce ya taba lafiyarshi.
Labarin Zaid abun taussyi ne amma Labiba what you did is very wrong, kowa ya ganki yanzu he will give you a bad impression na kin baro gida zakije Katsina gun Namiji, ba wanda ya ga niyyarki, kowa zai daukeki a matsayin mutuniyar banza, ba ma haka ba, yanda kika fito ba da sanin kowa ba, wani abu ya sameki a hanya Allah shi kyauta wa gari ya waya? Me zakice? Laifin waye? Duk laifinki ne".
Sosai ta ma ta fada da nasiha, ta kuma bata baki akan tausar zucia, don a dan labarin da taji ta lura she's an extrovert, tana fadan abunda take so a lokacin da take so babu dam sakayawa, saboda gatsau tace mata "Aunty ina sonshi don ni na fara furta mishi So".
Sosai Aunty Bilki ta yi ma Labiba fada har ta sha kuka.
Aunty tace "to wallahi da kinga lafiyarshi wallahi ki kama hanyar Edo gobe ki koma Gida, ki rok'i gafarar Iyayenki, ga dubu 10, ki mayar ma Maminki kudin da kika sata, sauran kiyi kudin Mota".
Labiba ta murmusa tace "inshaAllahu Aunty, na daukar miki Alkawari, nagode sosai".
Suka iso Katsina Lafia, har tudun matawalle suka kaita, har gaban gidan Alhaji Ali Zaki.
Labiba ta bude Mota.
Tace "Ba zaki shigo ku gaisa da Matar Yayana ba?"
Aunty Bilki ta girgiza kai tace "aa Labiba munyi dare".
To nagode kwarai, Allah ya saka miki da Alheri ya tsareki ya tsare miki 'ya'yanki, yanda kika taimakeni Allah ya taimakeki, inshaAllah yaranki zasu zama abun Alfahari a dunia baki daya".
Ta amsa da "Amin Amin nagode da adduoinki, naji dadinsu Allah ya amsa"
Labiba tayi sallama da yaran Hajia, har ta juya zaya tafi gida Hajia ta dakatar da ita.
Labiba ta dan Matso bakin window, Hajia tayi rubutu a wani takarda ta ba Labiba tace "Ina So na samo ma DanMakaho aiki, ina da hanyar Civil Defense, in yana da raayi ki bashi email address dina gashi nan ya tura min CV dinshi ko da secondary certificate ya samu ai yafi mishi zaman banzan nan, ga number nan kuma ki kirani inji ko kin koma Edon".
Hajia bata tsaya jin Godiar Labiba ba tayi whinning glass shi kuma Driver ya ja mota aka bar Labiba tsaye da mamakin Hajia Bilki.
Haka Allah ke abunshi, haka Allah ke sa jinin mutane haduwa ba tare da jini mai gudana ba.
Ita ta san haduwarta da Hajia Bilkisu Alkhairi ne.
"Hajia Bilkisu Beebbs nagodia, Allah ya baki farinciki a duk inda kike" mai makon ta shiga Gidansu kawai ta fada gidansu Zaid.
Yau ta Gate Beebs aka shiga Gidansu Zaid.
Ba ta tsaya ko ina ba sai dakin Zaid,
Wayam bashi ba alaminshi, wayarshi ta gani a k’asa da sauro ta dauka, tana kunnata ba charge, ta tura toilet taga baya ciki, yana ina? Ko yaje Bencin Eskaley, da sauri ta fita waje ta nufa Bencin Eskaley.
Suna ganinta suka mimmike, “Yayarmu ina wuni”
Bata amsa ba tace “donAllah ina Zaid?”
Sukace “Yo ai duk yau bamu ga Mankas ba”.
“Baku ganshi ba?”
Be fito ba gaskia, bamu ganshi ba, jiya dai mun ganshi har muka mishi Taaziyar Yasmin”.
Bata tsaya gama jin zancen ba ta koma Gidansu Mankas din.
Ba tsoro ta shiga Parlorn suna zaune.
Alhaji Ali tace “Ina wuni?”.
Zai yi magana Hajia Shafa tace “wacece ke?”.
Tace “sunana Labiba, ina neman Zaid ne”.
Shafaatu kamar an watsa mata garwashi tace “ba zaa bashi Hantar ba, ya mutu dole ne?ina ruwanmu”.
Labiba bata gane inda ya dosa ba tace “Mene? Ni Zaid na zo nema”.
Annah tace “Dallah Mallama ki fitar mana daga Gida”
Labiba ta kallesu tace “Ni fa ba wai zuwa nayi ku daga min jijiyoyin wuya ba, tambaya ce na muku, in baku san inda yake ba, ku gaya min, sai na je wani gu na tambayeshi”.
Annah tace “Karuwa har Gida kike biyoshi?”.
Sosai Labiba taji zafin zancen cikin fushi tace “Uwarki ce karuwa”.
Shafa’atu tace “kam bala’i uwarta ni kenan?”.
Labiba ta rausayar da kanta ta kalli Baban Zaid, sai taji ya bata tausayi”.
Fita kawai tayi a Parlon ta bar gidan, har zata shiga Gidan Yaya Muhammadu ta fasa ta dawo Gidan Alhaji Ali tace da Maigadi “DonAllah ko ka ga Fitar DanMakaho?”.
Maigadi yace “Eh, bai da lafia sosai wallahi dazun ni na kama ma wani abokinshi muka sashi Mota Abokin ya tafi da shi General.
Da gudu Labiba ta fita, bata shiga Gidansu ba tayi hanyar bakin Titi hankalinta a tashe.
Yan Bencin Eskaley nata mata magana tayi banza dasu.
Keke Napep ta tsaida tace a kaita General Hospital.
Ta na isa ta nufa Accident and Emergency, ta bada sunanshi gun reception akace anyi moving dinshi an bashi gado Amenity room 7.
Bata san ina ne Amenity ba amma bata ma tsaya tambaya ba.
Da taimakon Signboards ta gano Amenity, ta shiga ta fara neman dakuna.
Tana ganin room 7 ta karasa a guje ta bude da karfi.
Chan kan Gado ta hangoshi kwance kamar tabarma, da sauri ta karasa gunshi kamar zata daukoshi daga kan Gadon.
A hankali Zaid ya bude idonshi ya saukesu fes kan Labiba a wahalace da sauri yayi yunk’urin tashi, tayi saurin maida shi ta sakar mai murmushi mai ciwo, kauda kai yayi bai so ta ganshi cikin ciwo, bai so ta san weakeness dinshi.
Sannu ta shiga jera mishi, bya juyo ya kalleta yana niyyan magana bata ji meya ce ba, ta sa kunneta a daidai bakinshi yace “Yasmin ta tafi Beebs”.
Tace “Yasmin ta tafi Allah ya gafarta mata, lets focus on you now, you are sick”.
Yace “I am dying”.
Tace “shuttup gashi ana kara maka ruwa da jini inshaAllah kafin su kare ka warke”.
Murmushi kawai ya mata.
Socket ta nufa tace “Wayarka ba charge, daga gidanku fa nake”.
Da charger dinta ta jona mishi charge.
Ta dawo ta zauna a kan kujeran da ke gabanshi.
Tace “Sannu”
Yace “ya kamata ace kina Edo”.
Tace “Masoyin baida lafia”.
A hankali yace “Ta yaya kika zo?”.
Tace “in ka warke zan baka labari”.
A hankali aka bude Kofar.
Labiba ta juya ga k’ofar Drs ne su biyu suka shigo
Ta mike da fara’arta.
Tace “Sannunku”.
Dr Ali yace “Zaid bak’uwa akayi?”.
Zaid ya kanne idonshi yana so ya ma Dr Ali inkiya da kar ya gaya ma Labiba.
Labiba tace “Yauwa Dr, ya mai jiki? Stress ne ko?”.
Dr Habib yace “dama Stress ne da sauk’i, he is very sick wallahi”.
Tace “toufa, what exactly is wrong with him?”.
Dr Habib yace “Liver is damaged, he needs a transplant”.
A firgice tace “He Needs a Whatttt?”.
Zaid yui saurin runste Ido.
Da sauri ta kalli Zaid kafin ta kalli Dr Ali kafin ta kalli Dr Habib.
“Bangane ba Dr”.
A gajiye, a galabaice Zaid yace “Beebs”.
Ta san da kyar muryar ta budu, amma ta ki kallonshi tace “Dr kamin bayani?”.
Dr Habib yace “Are you a Family”.
A kagaucd tace “Ni zai aura, mun kusa aure, and i think i deserve to know what is wrong with my Fiance”.
Dr Habib yace “follow me”.
Bata jira komai ba ta bi bayanshi.
Zaid yace “Ali, donAllah ka hanashi magana”.
Ali yace “Budurwarka ce?”.
Zaid yace “it doesnt matter ka taimakeni kar ta san komai, tell her malaria ce kawai”.
Dr Ali ya fita ya bi bayansu, ko da ya shiga Labiba na zaune tana sauraron Maganganun da ke fita daga bakin Dr Habib.
Hawaye tuni sun wanke mata fuska, Zaid na dauke da ciwukka all this while bata taba sani ba? An fi shekara da akayi diagnosing dinshi amma ko da wasa bata taba sani ba? Ya Illahi, zuciyarta ta dafe dake barazanar fitowa.
Cikin Kuka tace “To a mishi surgery din mana me ake jira? Da bakinka kace Emergency ne”.
Dr Ali yace “Wallahi ba mai donating, naje Gidansu na gaya ma Babanshi baki ga wulakancin da suka min ba da gatari suka bini, Mamarshi kuma bata nan, nace zanyi contacting dinta yace baida contact din Mamanshi tunda suka rabu, nace kanwarshi yace “ta tafi Ghana wurin kakansu, nace dangin Babanshi ya ki magana tun dazun”.
Labiba tace “K’arya, yanzu what will happen in be samu Surgery din ba?”.
Dr Habib ya dauko Xray ya na nuna mata yace “he will slowly Die, dont forget his Ribs are Infected, and its close to the Heart, when he breathes in the Heart touches the veins of the liver, its risky”.
Da sauri tace “then mai ake jira, muna bata wani lokacin ne, lets have the surgery now”.
Sukace “who is donating?”
Tace “Me, prepare for the surgery now”.
Ta mike ta fita ta barsu su biyu suna binta da kallon mamaki.
Dakin ta koma.
Ta karasa da kallon tausayi tace “Kayi hakuri, duk wannan wahalar ka shata kai kadai, i am sorry you went through this alone, i am here for you now”.
Ko bata fada ba ya san me take shirin yi, yasan mai zatayi
Ya girgiza kai yace “Labiba Dont, karki yarda a budeki, mutuwa zanyi, theres a possibility ko an yi surgery din ba zan rayu ba, kuma donor din will be at risk, kar kiyi, ba zan yarda ba, i am dying”.
Murmushi take mishi mai tarin ma’anoni daidai ta digar hawayenta tace “ZAN RAYU DA KAI, ZAN MUTU DA KAI”.
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO😉