← Book details Dan Makaho Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 16 OF 20

BABI NA ASHIRIN DA SHIDDA 2⃣6⃣

Dan Makaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 25 min read

(BAIKO 💍)

Da yake duk sun sa ma kansu abun, cikin kwanaki biyu su ka binciki Juna, akwai wani Mutum a Benin City, shi Abban Jawad ya tura ma Details kan Alhaji Ahmad Dakata yayi mishi background check kan family dinnan kuma ya samu gamsasshiyar Amsa.
Yace mishi Mutumin babban mutum ne datijo kuma bai da matsala, gidan shi Gidan Mutumci ne.

Haka nan Baban Amira ya binciko Asalin su Jawad a Unguwan Alkali, kasancewar Family dinsu ba boyayye bane, babu wani abun Assha da ya ji game da Family din, ya kira Mahaifinshi ya sanar dashi, baban yace "to Alhamdulilah, kace su turo".
To kafin ma Baban Amira ya kira Yayan Jawad yace mai su turo sai ko ga dan Halak din ya kira ya sanar dashi cewa "Akwai wani Uncle dinsu da yazo Abuja, zai koma ran Friday, to sauk'i suke so ba sai an tado kowa daga Katsina ba a tura su chan Edo neman Izini why not su tafi gobe Alhamis? Ba tare da an wahalar da mutanen katsina ba? Amma fa sai in ba matsala a wurinku be san ko its a short notice ba?".

"Bakomai" Yaya Muhammadu yace, zan gaya musu suyi shirin tarban ku Gobe in Allah ya kaimu, suka rabu a mutunce don yin shirin tafiar su kuma da tarban bakin.

Yaya Abdulhafiz ya gaya ma Abbansu yanda sukayi da Yayan Labiba, shi kuma Abban ya kira k'aninshi ya gaya mishi, k'anen yace bakomsi suna iya tafia gobe su dawo goben Friday sai ya dawo Katsinan.
Abba yace "akwai stress, bari na aiki Abdulmajeed naga ko zamu iya samun tickets to Edo"
A hakan suka rabu.

Yaya Muhammadu ya kira Gida ya musu bayani cewa gobe zasu zo saboda wasu dalilai, Babansu Labiba yace "haba bakomai su zo, ita kuma ka saka ranar kawo min ita Gida, tunda dai ga Miji, a bar karatun haka nan".
Mallam Muhammadu yace "InshaAllah baba, bari dai suzo muga yanda zaayi ba zai gagara ba InshaAllah". A hakan suka rabu.

WASHEGARI EDO STATE

Kamar yanda Abba ya tsara su 5 suka ya tafiar zuwa Edo Benin City, Abba, Daddy Usman, Yaya Abdulhafiz, Yaya Abdulmajeed da shi kanshi Jawad din, a cewar Abba gwara su ga wanda zasu ba diyarsu tun yanzu.
Tafiya ce mai nisa, sun iso Edo after 12, kamar yanda aka umurcesu, Dan Achaba suka tsayar su ka bashi adireshin gidan yayi gaba suka bishi a baya har kofar Gidan Alhaji Ahmad Dakata.

Yana a bakin Gate din Gidanshi tare da Manyan Yaranshi su 4, suka tarbesu cikin mutunci,
Sukayi ma juna Musabaha cike da farinciki kafin Alhaji Dakata ya ja hannun Alhaji Abu Shamsu har cikin Parlo suka zauna.
Bayan 'yan gaishe gaishe, aka ci abinci don sosai Alhaji Dakata ya sa aka musu Abinci har kala 3, sunci sun gyaste.
Alhaji Abu Shamsu ya gabatar da Daddy Usman a matsayin kaninshi kuma waliyi madaurin auren 'yayanshi.
Ya gaya mishi yana da mata biyu da yara 4 Abdulhafiz shine babban danshi sai mai bi mishi Abdulmajeed sai auta a mazamai neman diyarshi kuma Jawad, sai miemee yar shekara 3.

Alhaji Dakata yace "MashaAllahu, Allah ya raya mana zuria, nima dai Matana 2, ko waccen su na da 'yaya takwas, ni mai tarin zuria ne, Babban yaro na shi ne Labiba ke gunshi a Katsina, wannan sunanshi Hamza, sai wannan sunanshi Faruk, ga Aliyu wannan kuma mai sunan babana ne Lawal.
Da faraa suka sake gaisawa.
Daddy Usman Abba yace yayi magana.
"Alhamdulilah kamar yanda ka sani munzo ne don muga tushen Yarinya kuma mu nemi a ba dan wurinmu Izini ya dinga zuwa gunta su fahimci juna".

Alhaji Dakata ya murmusa yace "Mallam Jawad, kai ne ke son Diyata Labiba? Fada min naji daga bakinka".
Jawad ya dago kai ya sauke da sauri irin kwarjinin da mutumin ya mishi.
"Eh nine".
Alhaji dakata yace "ka shirya aure?".
Jawad ya kalli Babanshi kafin yace "eh na shirya".

Alhaji Dakata yace "to MashaAllah, abu yayi kyau, Itama nayi magana da Yayanta yace tana sonka tunda ta barka kazo gida wannan alamace ta yarinya na sonka din, nikuma gaskia a tsarin gidana, ban yarda ayi ta zuwa zancen nan ba, in aka ce yaro na son diyata, in na bincike yaro na binciki halinshi da asalinshi, sai in kirasu a daura aure, bana son bacin lokaci, amma naji dadi yanda ka kwaso min Iyalinka na gani, naji dadi wannan ya nuna halin girma, na amince da ku dari bisa dari, na ba danku Labiba, kuzo duk lokacin da kuka shirya ayi auren".

Alhaji Abu Shamsu ya murmusa yace "Alhamdulilah mun ji dadi sosai da karamci, amma so muke ka gaya mana cewa ga ranar da kake so muzo ayi maganar Aure, diya taka ce, magana ma takace".

Alhaji Dakata yace "wallahi bakomai, ni da kuka nuna kuna son nawa? Ko yaushe kuke so sai ayi, ku dai da kun shirya kuzo".

Alhaji Abu yace "dagaske Alhaji kafada, mu fa a shirye muke, ko yaushe ne, Mu ko yanzu kace a daura ai sai a daura".
Daria sukayi gabaki daya.

Alhaji Dakata yace "to shikenan, faduwa tazo daidai da zama, akwai yaruwar Labiba wato Samira, an saka ranarta, auren nata nan da kwana 45, in babu matsala, ina so in hadesu su biyu na aurars".

Alhaji Abu ya fadada fara'arshi yace "ba wani abu InshaAllah, mu da aka ma gata? hakan ma yayi, ba amfanin raba biki biyu a shekara, gwara kawai a hadesu".
Dadi kamar ya faso zuciyan Jawad jin shi zai yi niyyar aure nan da kasa da wata 2.

Daddy Usman yace "aikam bari in bada kudin neman Aure"
Ya ciro naira dubu dari a Aljihu ya kawo ma Alhaji Dakata har gabanshi.
Ya sa hannu ya karba, yace "naira dubu dari? Ai tayi yawa Alhaji Usman".
Daddy Usman yace "aa bata yi ba, bikin Autan Umma ne fa".
Alhaji dakata yace "aa gaskia tayi yawa, nifa aladar nan wai ta bada kudin neman aure da ina da yanda zani yi dana hanata"

Daddy Usman yace "haha, to tunda dai anayi, shikenan muma munyi".
Alhaji Dakata yace "wallahi sunyi yawa, amma abunda zanyi, na dauki dubu hamsin na neman auren, dubu hamsin na sadakinta".
Alhaju Abu Shamsu yace "shikenan an raba gardama".
Duk sukayi daria suna masu ganin mutuncin juna.

Da zasu tafi aka cika musu booth da Doya da Makani da jarkan Manja, suka rabu suna sambarka da junansu.
Bayan tafiyansu ya kira Mallam Muhammadu ya sanar dashi duk yanda sukayi. Baban Amira yace "hakan yayi Abbanmu, ina kasuwa sai anjima zan koma gida na sanar dasu yanda akayi, MashaAllah abu yayi kyau".

Gidansu ya kachame da Abbansu ya sa bikin Labiba rana daya dana Samira, 'yan uba kam ba su ji dadi ba, balle da labarin yazo muso cewa gidansu mai son auren Labiba mai kudi ke, duk surukan gidan babu mai kudinsu mijin Labiban, a da suna ta jin dadi Samira zatayi aure Labiba batayi ba, yanzu ko ransu ya baci jin ta samu Miji dan Babban gida kuma.
Mamin Labiba kam godia take ma Allah da zai nuna mata bikin Labibarta.

K A T S I N A

A Masallacin Anguwar yayi Sallahr La'asar, Mallam shehu ya tareshi a hanya yana tambayarshi.
"Wai ni Mallam Muhammadu wannan k'anwa taka ya ma sunanta?".
Baban Amira ya murmusa yace "Labiba Sunanta".
Mallam Shehu yace "ita fa, ni ina mamaki, meye hadinta da wannan yaro dan gidan Alhaji Zaki"
Baban Amira bai gane zancen ba yace "wai wa?
Yace "wannan yaro mana DanMakaho"
Da mamaki yace "DanMakaho kuma? Ita fa ko saninshi batayi ba, me ko zai hadssu?".
Mallam Shehu yace "ya zakace ko saninshi batayi ba bayan kullum sai na gansu tare, jiya da tsaye na gansu a shagon Eskaley kuma suka ketaro Anguwa tare, duk wands ya gansu ya san masoya ne, kuma sai da suka tsaya kofar Gidanka sukayi zance kafin ta shige gida".

Mamaki duk ya bayyana a fuskarshi yace "Anya dai? Ba dai Labiba ba".
Mallam Shehu yace "hmm, baka yarda ba ko? Ka dai bincika ka gani, dama nace in gaya ma ne don ka san yanda zakayi ka datse Alakara su tunda dai kowa ya san DanMakaho dan Shaye shayene kafin ta zubar maka da mutunci gwara ka katse ma hanzarinsu gudu".
Baban Amira ya ma rasa abunyi don shifa bai yarda ba, haka ya k'ama hanyar gida jiki a sanyaye.
****

Fitowar ta kenan daga Gida, ta ganshi tsaye ya rungume hannu a kirji kafarsa daya kan bangon gidansu.
Suna hada idanuwa suka murmusa ma Juna, kusan a tare suka ce “Kinyi kyau, kayi kyau”.
Sukayi daria a tare yace “ai ban kai ki ba”.
Tace “ka fini mana”
Yace “ya makaranta? Are you stressed out?”
Tace “i was, amma ganinka ya sa gajiar duk ta tafi”.
Ya dago kai da murmushinshi kafin yace wani abu ya Hango Mallam Muhammad na nufosu.
Ya dan tsorata yace “Shiga Gida Biebbs” da mamaki ta kalleshi tace “meyasa?” Murya k’asa k’asa yace “ga Yayanki nan”.
Ta dan waiga ta ga shi dinne, ko a jikinta don ma murmushi take mishi da ya zo gabansu ya kallesu daya bayan daya.
Labiba tace “Yaya sannu da zuwa”
Baban Amira yace “DanMakaho mai kakeyi a kofar gida na?”.
Zaid ya dan fara in ina yace “bakomai, dama wucewa zanyi”.

Labiba tayi karaf tace “Yaya wurina yazo”
Mallam Muhammadu ya kalleta da mamaki yace “wato maganganun da ake fada game da ke a anguwa”.
“Gaskia ne” Ba tare da ta san me yake nufi ba ta amsa shi.
Mallam Muhammadu yace “Labiba shiga Gida”.
Tace “To Yaya”
Ta kalli Zaid tace “Barin shiga ciki, sai munyi waya”.
Zaid sadda kanshi k’asa kawai yayi, wai ya ta ke haka? Ta ya take iya fadan abunda ke ranta ba tare da ta sakayawa ba? Ai a irin yanayin nan k’arya ya kamata tayi, ansan bata k’arya, amma dai yanda bata ji nauyin yayanta ba ya sa shi jin wani iri.
Yana jira yaji Yayanta yace wani abu amma bai ce ba illa ce mishi sai anjima da yayi.

Ya shiga Gida ya ga Labiba tsaye, kwala ma matarshi kira yayi.
“Asiya, Asiya”.
Sai ko gata ta fito da sauri jin kiran Mijin nata
“Wai dama kinsan Yaron nan DanMakaho na zuwa gurin Labiba?” Ido ta bude tace “wallahi ban sani ba, DanMakaho kuma? Wani irin dan Makaho? Tare ka gansu?”. Ta tambaya tana kallon Labiba.
Labiba tace “Yaya fa bata sani ba”.
Yace “yi min shiru”.
Aunty Aseey tace “dagaske ne? Ke ko me zakiyi dashi?”.
Baban Amira yace “bude kunnenki kiji, kar na sake ganinki da Yaronnan, kuma an sanya ranar aurenki da Jawad, sadakinki dubu hamsin na gun Baba, dazun sukaje neman aure Baba kuma ya amince musu, tunda ya ansa sadakinki”.

Labiba jin abun take kamar Almara tace “Yaya chabda, lallai kam”.
Yace “kin dauka wasa nike?” Kallonshi ta tsaya yi tana karantarshi, iyakar gaskia ta karanto a idanunshi.
“Yaya ta ya akayi bansan shiryshiryen nan ba?”
Yace “kinyi waya da Jawad jiya zuwa yau?”
Tunawa tayi rabon da suyi waya tun ran Tuesday, kuma messages dinshi a whatsapp suna chan tayi hanging.

Tace “Huh, Yaya har kai baka min maganar ba”.
Yace “tunda kika kawo minshi Gida magana ta k’are”.
Ko a jikinta tace “nikam ba a daura ba ai? To ku mayar mai da sadakinshi, nikam DanMakaho nike so, kuma ni shi zan aura”.
Ta shige ciki ta barsu da mamaki, barin ma Baban Amira, Labiba bata taba mishi rashin kunya ba, shekara 26 ya bata, amma yanzu ita take mishi rashin kunya akan Namiji? Namijin ma DanMakaho?.

Zuwa yayi yana kwankwansa mata amma ta ki bude dakin, ran baban Amira ya baci, ya shige daki.
Itama Labiba ranta a jagule ta kira Mamarta ringing daya ta dauka tace “Mami, dagaske an kawo sadakina? Dagaske bikina rana daya dana samira?”.
Mami tace “Eh Labiba, aikam mutanen Kirki”.
Labiba tace “Mami nifa ba zan aureshi ba, so daya yazo nan gidan, kawai suka zagaya suka ma Yaya Muhammadu magana shine ya turasu chan gun Baba”.

Mami tace “Labiba mai kike son cewa? DonAllah nidai ki rufa min Asiri, bakiji me ake ta cewa a cikin Gida ba”.
“Mami su fada abunda suke so, nikam ba zan auri Jawad ba, ina da wanda nake so”.
Mami tace “Labiba kiyi hakuri donAllah, kinsan babanki kaifi daya ne, ya amince musu, ki rufa min asiri”.
Labiba ta lura Maminta ba zata gane ba yanzu tace “Mami zan kiraki, ina zuwa” ta kashe wayarta.

Sukuku ta karashe ranar Alhamis, ba wandata ma magana har yaran yayanta, da daddare ta sha zancenta da Zaid a waya ba tare da ta damu da komai ba, don ba mai mata auren dole so wannan ba matsala bace, ta cigaba da harkan gabanta.

F R I D A Y.

Daddy Usman yazo musu Sallama, Doya da makani damanja Galan Biyu da suka samo jiya a Edo AbdulMajid ya saka mai a booth, yayi breakfast, sukayi dan fira da Yaran Yayanshi kafin yayan ya fito, sannan yayi sallama yace "bari ya tafi".
Gabaki daya Iyalan Alhaji Abu Shamsu suka rakoshi har bakin Mota suka mishi fatan Allah ya sa a isa lafia suna mai mai fatan Alheri.
Daddy Usman ya kama hanyar ta dikko dakin Kara.
***
Tsautsayi ne ya faru da Alhaji Usman a hanyarshi ta komawa Katsina, yana daf da shiga Katsina a Charanci yayi hadari inda Shanu suka gitta mai garin kauce musu ya bige wani Mutumi tare da fadawa wani kwalbatin da ya sa shi buguwa a kai.
Mutanen Anguwa suka kawo dauki, da aka duba sai aka wanda Alhaji Usman din ya bige ya cika don ko shurawa beyi ba.

Da yawa kan idonsu abun ya faru sun san cewa ba laifin Alhaji Usman bane, nan da nan yan garin suka taimaka suka kai Alhaji Usman Asibiti mafi kusa.
Wayarshi wani ya ciri ya cire sim din ya saka a wayarshi don wayar Alhaji Usman din akwai Pattern.

Duba contact list yayi yaga dai ba wani suna Mama ko Baba, sai yaga Contact din My Son.
Da sauri mutumin ya latso numbern.

A B U J A

Abdulmajeed cike da shagwaba yace "Yanzu kai shikenan Abba ka yarda Jawad ya rigani Aure?"
Mancy tace "to tunda baka da niya ba gwara ya yi overtaking dinka ba?".
Abdulmajeed yace "fa Mancy ba laifina bane, ko dazun sai da nace ma Ya Abdulhafiz yama Daddy Usman magana a hada bikin da nawa da na Jawad Abba ya hana, wai ba ya so ya shiga hakkin Daddy, kuma wai karatu takeyi sai ta gama ND1, afterall wallahi cireta ma zanyi daga Poly, Haba Polyn lafia".

Abban ya harareshi yayi saurin sadda kai, Umma tace "gaskia Abbansu da ka bari an hadasu, ai ba shiga Hakkin Aisha diyarka ce kaine waliiyyinta, in ka yanke hukunci kanta ba mai ce maka don me?".

Shiru Abban yayi kafin yace "shikenan, bari Usmanun ya isa zamuyi waya, sai mu ji in zaa iya hadesu".
Abdulmajeed ya gallawa Zaid harara yace "mallam sai ka bar mi gwalo hakan nan, inshaAllah ba zaka rigani aure ba".
Jawad yace "hahah aiko zaka sha madaran mamaki".
Sukayi daria baki daya.

Suna cikin firansu mai dadi ne wayar AbdulMajeed yayi ringing,
Ya kallesu baki daya da murmushi a fuskancshi yace "Daddy Usman ne"
Jawad yace "kace sirikinka ne"
Ya jefeshi da harara.
Mancy tace "kai wani irin Gudu Daddy Usman keyi haka? Har ya isa kenan".
Jin tashin hankali sukayi a muryan Abdulmajeed.
"Inallilahi wa ina ilaihir rajiun, mai ya sameshi? Yanzu yana ina?".

Kowa na cikin parlorn ya fara tambaya mai ya sami Uncle
Usman.
Kasa magana yayi sai da Abban yace "Kai Abdulmajeed, ka gaya mana mai ya samu Daddyn naku?".
Abdulmajeed kamar yayi kuka yace "Abba hadari Daddy Usman yayi a Charanci, ya bige wani mutjmi har mutumin ya mutu amma shi Daddyn yana Asibiti ba abunda ya sameshi sai dai wai ya bugu a kai".

Tunda ya fara magana suke Salallami da Salati.
Abba cike da kidima ya ciro wayarshi ya kira chan Katsina gidan Iyayenshi ya sanar dasu, da su je Charanchi yanzu yana nan tahowa gobe InshaAllah.
Ya Kalli Iyalanshi da sukayi saye cirko cirko yace musu "ku shirya, gobe inshaAllah zamuje Katsina".
Amsa mishi sukayi duk jikinsu a sanyayye

K A T S I N A

Ai yayewa akayi a Unguwar Alkali harta Hajiarsu Alhajin suka kwasa suka nufa Charanci har su Aishan.
Kafin su je an gano Gidansu Mamacin, suka shiga akayi magana, Allah ya sa Saurayi ne, baida Iyali, Mahaifiyarshi kam taci kuka sosai amma ta yafe Wanda ya bamkeshi yayi kaffara, aka rufo mamacin.
Basu kwana a Charanci ba suka wuto Katsina.
Asibiti zaayi dashi yace shi dai donAllah a kaishi Gidanshi don ya tsorata sosai da abunda ya faru.
Tunda suka dawo Gida ake zuwa yi musu jaje ko wani lungu da sak'o, gidanshi ma bude ya kwana saboda masu shiga da fita, wasu sun kasa hakura safiya tayi su zo, abunku da 'yan dangi.
*

'Yan Abuja tun safe wurin 8 suka fito, Mota biyu sukayi, AbdulMajeed ke jan Abba da Matanshi Umma da Mancy, sai Abdulhafiz ke jan Matarshi Ummita da Jawad da Mimi, a tare suke taafiya ba'a gudu da Abba, shiyasa suke dadewa akan hanya, sai da suka tsaya a Zaria suka ci Abinci a Shagalinku kafin suka sake daukan hanya.

Sun iso Charanci wurin Karfe2, tambaya sukayi gidan da aka banke wani Jiya, har kofar Gidan aka kaisu, suka shiga, sai kallonsu ake tayi aka dai gaigaisa.
Abba yace "ina Mahaifan yaro?"
Aka gwada musu Uwarshi.
Yace "Uba fa?"
Akace ya dade da rasuwa.
Abba ya gabatar da kanshi a matsayin Yayan wanda ya banke mata da, ya roke su gafara, mahaifiyar yaro tace "wallahi Alhaji, lokacin Saminu ne yayi, K'anenka ne sila, amma lokaci yayi ba wata dabara da zai tsaida tafia".
Matar ta burgesu, nan aka musu karamci aka kawo musu ruwa fiya wota (pure water) da damammen fura.
Ba wanda bai sha furan nan ba sai mimi da bata shan fura, suka sha suka sake musu gaisuwan mutuwa kafin Abba ya cika Mahaifiyar yaro da Alheri.
Godia ta hau yi ta na kuka tace "Saminu ya tafi, amma sanadiyar shi sai samun Alheri nakeyi, Dazun ma Maidakin Mutumin tazo da tawagarta, wallah sun cika mu da abun Alheri, mungode mungode, Allah ya ji kanka Saminu".
Da kyar suka bata baki ta bar kuka, suka musu rakiya har bakin Mota kafin suka dau Hanyar Katsina kuma.

A Garin Katsina.

Zaune ta isketa a babban Parlo tana kallon dadin Kowa sabon Salo na karfe 3.
"Nene Jaje zanje Unguwan Alk'ali kafin yara su dawo Islamiya" Nene da ke tamnar cingam tace "Jaje na me? Me ya auku?".
Hajia Aisha tace "wallahi Mijin k'awata ne yayi hadari, yayi banka a hanyar charanci, har wanda ya banke ya Rasu".
Nene tace "Inalillahi wa ina ilaihir rajiun, Allah sarki, kije dani nima nayi musu jajen".
Hajia Aisha Lema tace "Eh sai muje Nene, abun ba dadi wallahi ".
***

Welcome to Katsina ta gani a tollgate, gabanta ya yanke ya fadi, Katsina...bayan ta auri Babansu Jawad tazo katsina so uku zuwa hudu, bata san meyasa wannan karan ta ji faduwar gaba ba, jikinta ya soma rawa, haka kurum ta ke jin faduwar gaba a zuciyarta, Zaid, Sadiya, ya kamata ta gansu, amma ina bata shirya ganinsu ba, ba yanzu ba, shiyasa kamar zuwanta na baya har taje ta dawo bama zasu san ta zo ba.
Straight Gidan Daddy Usman suka nufa.
Aisha ta rugo da gudu ta rungume Umma kafin ta rungumi Mancy.
Ta gaida Abba da yayyinta ba tare da ta kalli AbdulMajeed ba.
Suka karasa har Parlon Daddy Usman, Parlorn cike yake da mutane, aka gaigaisa aka ma Juna Jaje, Alhamdulilah jikin da sauki sai ciwon kai, akayi wa juna barka ba abunda ya samu Daddy Usman, Antisco tace "Abinci na Parlo na, ku muje kuci kun kwaso hanya".
Abba yace "ai mun tsaya Charanci gaisuwa sun bamu fura munsha".
Antisco tace "ai abun bai yi dadi ba, nima dazun da safe mukaje muka sake musu gaisuwa, duk da lokacinshi ne yayi harda sila dai".

Suka sake jajantawa juna kafin suka dunguma baki daya Parlon Antisco, Mancy ta shiga toilet din Parlorn.
Sai Ga Hajia Aisha da Hajia Nene sun shigo Parlon Antisco, Antisco ta musu maraba, suka tarbi juna suka zauna don yi ma juna Jaje da Barka, Alhaji Abu Shamsu ya gaida Nene ta mishi Jaje, Suka gagaisa duka harda Umman su Jawad, Antisco ta rakasu chan Parlon Daddy  suka mishi Allah kyauta, suka koma Parlornta don parlon Daddy cike yake da 'yan anguwan alkali.
Jawad da yayyinshi suka zuba Abinci suka fita waje wai Mota zasu.

Fitowar Mancy daga Toilet ta hada ido da Nene, tare suka zare ido suna mamakin ganin junansu, Mancy tace "Nene?".
Nene ko ta buga muguwar tsaki ta tashi ta fita daga Parlorn. Duk suka bi tsohuwar da ido Umma na ma Alhaju Abu magana da ido ya mata alamun baisan ko wacece ba.
Mancy da Hajia Aisha Lema suka bi bayan Nene.

Nene na daga kofar parlo a hakimce tana jiran Mamyn Rafeeq ta fito su wuce amma a zuciarta mamakin chanzawan Mancy take, da alamu duk inda take tana jin dadin Aurenta.
"Hajia Aisha Ina wuni? Ya yara? Ya wurin su Rafeeq da matarshi?" Mami ta amsa mata da fara'a, "lafiya lau Hajia Maryam ya bayan rabuwa?" Mancy tace "Alhamdulilahi".
Kallon Gogiyar tayi, gogarku sai tamnar cingam ake kachalkachal ana kallon gefe irin bata san akwai mutum a gurin ba.
Murmushi Mancy tayi tace "Haba Hajia Neneta" Nene bata amsata ba, tace "Hajajju Nene mutanen Makka, Allah ya sake hadani dake a Makka na goyaki bayana" yanzun ma ko kallonta bata yi ba, hannu Mancy ta sa ta na taba cinyar Nene ta na kiran sunanta.

"Nene, Nene, Nene, haba Nene" Nene ta mik'e cike da masifa tace "haba Mallama, ya zaki ta sani gaba kina min Noiiiiise? Is Stupid? Ke tsaya ma is no me ne? Nace is no me?".

Mancy ta murmusa tare da rik'o hannayenta biyu tace "I know you very well Nene" hannu Nene ta fizge ta bugar ma Mancy baki tace "Ni kike ma turanci? Dan iskancin kin sa k'afa kin bar Katsina, ba waya ba komai, kika maidani wata mara amfani ashe yanda na daukeki ba haka kika daukeni ba, kin take duk wani abunda ke tsakaninmu da k'afa, bayan shekara kusan 4 kinzo kina cika min kunne da surutu, har da karfin halin turanci, Allah ya tsine miki kika sake furta man kalmar turanci".

Mamin Rafeeq tace "kiyi hakuri Nene, kina daga Murya, kar 'yan Parlo suji" Nene ta sake bude murya tace "Su ji, nace Su Ji, ai gwara su ji".

Mancy ta murmusa ta sake rik'o hannun Nenen tace "kiyi hakuri donAllah, ban kyauta ba, nasani ni mai laifi ce wallahi, Nene banda zabi ne, abubuwa sun fara da sauri ne, wallahi a lokacin ban san me nayi ba, kuma ni wallah kunya ma nikeji, ki yi man hakuri donAllah, fushinki na sosa min rai donAllah Nene".

Nene ta dan sha mur tace "kinsan na gaji Yafiya wurin Mahaifina, na yafe miki, amma banji dadi yanda kika watsar dani ba, kika nuna ma duniya baki da gata a Katsina, ni yanda aka ci maki mutunci a garin Katsina da kin gaya man sai na sai miki mutunci kuma in ci uban mutum ko uban wa ya tsayar mai daga nan har gaban ko wani dan shegia amma kika tsallakeni, ke kika sani".

Mancy tayi ta kallon Nene da mamaki, ta san Nene bata da hakuri bata da ragowa amma yanzu ta ga Nene ta koma kamar wata 'yar Tasha.
Nene tace "yana ga kina kallona? Ko zagin uwata zakiyi?".
Mancy ta hau Girgiza kai tace "Nene ki rufa min Asiri, wai ba ma kince kin hakura ba?".
Murmushi tayi tace "oyoyo Maryama, nayi missing dinki".
Mancy tace "Hajia Aisha kinga Nene ko? Turanci tamin, nikuma in na mata a zageni".
Mamyn Rafeeq tace "ina ji dazu har tsine miki akayi".
Daria sukayi tare.

Nene tace "sai aje a ga su takwaran Zaidu bawan Allah ko?".
Mancy ta dan rage annashuwa tace "Aa Nene".
Nene ta sha mur nan da nan tace "bangane Aa ba? Ba zakije ki ga yaranki ba? Ke wai wace irin stupid ce? Me ke damunki? Baki da  zucia? Wace irin uwa ce ke? Wallahi ki guji haduwarki da Ubangijinki, Allah yace dukkanku Makiyayya ne, kuma sai Allah ya tambayeki yanda kikayi da naki Kiwon, ya kikayi da kiwonsu? Daya ya zama dealan Wall kobo biyar ba zaki saye shi ba, ta macen Allah ya tsare miki ita, wallahi jiya naji a radio wata ta kashe kanta saboda bakinciki, ke kiyi hankali, ke kin ma ci uwarki in kikaje ganinsu, ke Aisha wuce mu tafi".

Alhaji Abu Shamsu da Matarshi suka fito bakin Parlon da alama sun gama jin duk wani abunda suke tattaunawa.
Mancy tuni ta sha jinin jikinta
Alhaji Abu Shamsu yace "wallahi Mama, tun kafin na auri Hajia Maryama na nuna mata ina son rikon yayanta amma ta hanani, ta nuna min gwara ta barsu Gidan ubansu, na ce mata ko zata bar Namijin ta dauko Macen don Tarbiyar diya mace in ba Uwa to akwai Matsala".

Nene tace " kai k'yale sakarar, ai maryama da kake ganinta muguwar sakara ce"

Umman Jawad tace "ke ko Maryama har yau baki huce ba? Ai ba zaka dauki laifin uba ka shafa ma yaranka ba, wake fushi da 'ya'yan cikinshi, ke ko kije ki gansu ko so daya ne".

Nene tace "sai wani aiken da take musu duk wata na banza, ce miki sukayi suna Son abun hannunki? Sunfi bukatar ki, yaro na nan ya zabge ya tsure, a lokaci guda sai ya shanye kwalin sigari daya,ga tabar wiwi yana zukarta kamar ba gobe har wani suna yan jagaliya ke ce mishi wai Mankasss".

Mancy cike da kidima tace "ba dai Zaid ba".

"Aa Ubana" Nene ta fada cike da fada.
Mamyn Rafeeq tace "haba Nene kiyi shiru".
Ita ko Nene kira take "ban yin shiru, laifin wa? Wallahi lafinki ne, da kyar in baida ciwon k'ofa dan wallahi fari yke fayau, in ya mutu Kurani ke kika kashe danki".

Tuni Mancy kafa ya fara rawa, fitsari ya cika marar ta taf kamar ba yanzu tayi fitsari ba.

"Alhaji, donAllah ka min izinin zuwa ganinsu, Inalillahi wa ina ilaihir rajiun, na shiga uku na, Zaidda shaye shaye?"
Alhaji Abu yace "Maryama kinsan dai tun yaushe nake binki muje ki gansu ko? Kin san ba zan hana ba, ko yanzu kika ce su dawo Gidana ina maraba dasu".

Ba ta tsaya jinshi ba ta shiga ciki ta dauko gyalenta tace da Mimi je ki wurin Yaya Aisha, yarinya ta mak'e kafada, Mancy bata da lokacin yi gardama ta fito a hargitse.

Alhaji Abu yace "nima zanje" Umma tace "itama zata" haka Mancy ta shiga Motar Hajia Aisha Lema, su Alhaji Abu suna biye da motarsu a baya.
Dama Abdulmajeed ya zagaya zance wurin Aisha, Abdulhafiz ya gaji yace zai dan kwanta so ba tare da sanin inda zasu ba Jawad yace bari ya kaisu, Abba yace ka bi bayan motar nan yabi Umurni yana tuk'i.
"Abba ina zamu?"
Abba yace "just drive".
Bin bayan motar Mamyn Rafeeq yake, har ya ga Anguwar su Sanyin idaniyanshi ne, da niyyar in ya saukesu zaije ya ga Babynshi dama Allah Allah yake neman chance ya fito wayarta tun jiya kashe, duk ya damu.

Sun zo Daidai Bencin Eskaley Nene tace "dan tsaya nan, kinga Bencin chan, chan suke zaman kashe wando, barin lek'a inga Zaid din na nan, ta lek'a tace "Kai Takwaran Zaidu bawan Allah na nan?"
Master ya fara ganinta yace "Sai Nene".
Aiko hankalinsu tero yayo kan Motoci Biyun nan.
"Nene da me kika zo mana yau?" "da uwarku" nazo ta koma tace "baya nan, yana gida Muje Aisha" ita kam Mancy kallo daya ta ma Bencin Eskaley gabanta ya tarwatse wai Zaidunta ne ke rayuwa irin ta Mashaya, ta kasa yarda.

Master yace "Wallahi Nene Solo zata mana yau, gata chan ta tafi ta kai ma Mankas, shegen ba bamu zai yi ba, ku mu bita".
Nan fa Eskaley ya kulle shago suka biyan Motar Nene su hudu.
**
Gabanta ya tsananta faduwa da ta hango gidan Alhaji Ali Zaki, duk abunda ya faru a shekarun baya suka dinga dawo mata kamar a lokacin abun ke faruwa.
***

Yau Saturday, Mutanen Gidan sun tafi Daura Biki, Baba ma ya kaisu da kanshi, daga ita sai Uncle Hudu a gidan, Ya Zaid bata san ko yana daki ba, ta kira wayarshi bata shiga, Wani irin k'ishi takeji, amma bata son fita daga dakin, ta zabi tayi zamanta a daki hankalinta zaifi kwancia don har ga Allah bata son duk wani abu da zai hadata da Uncle Hudu.

Ya fara wuce gona da iri, ita tsoronta kar ya mata wani mugun abun, kar ya dakusar mata da rayuwa, ya goga mata Fenti da ba zai taba goguwa ba.
Saidai k'ishi takeji ba na wasa ba, har ta na ta shak'uwa, yanke hukunci tayi na tafia daukowa a kitchen ko ta diba a dispenser da ke parlo.

Kamar barauniya haka tayi Sando har parlo tayi amfani da Cup din wurin diban ruwa.
Ji tayi an mata wani irin chakulkuli a gefen cikinta wanda ya sakata sakin Ihu da k'arfi.
Da sauri ya sa hannunshi a bakinta tare da rik'o k'ugunta.

"Matsoraciya, meye abun Ihu"
Gani irin rik'on da ya mata ya sa ta fashewa da kuka tana fadin "ka sakeni donAllah, bani so fa Uncle Hudu, donAllah sakeni" tana k'okarin kwace kanta shikuma yana sake rik'ota tare da tariyota jikinshi.
**
Ya fito daga Dakinshi zai shiga ya ga Dalo kafin ya fita waje, ya ci karo da Nene da wasu mutanen da bai shaida ba, sai ‘yan Bencin Eskaley da mamaki yake binsu da kallo.
Yace “Nene ta ya kika shigo da su Master? Meye kuka cika mana Gida”.
Nene da bakinta ya dade a Bude tace “Takwaran Zaidu Bawan Allah, wannan wankan fa? Ina jallabiyar? Wa ya baka jamfa ka saka?”.
Zaidu ya kalli Jikinshi yana murmusawa kafin yace wani abu master yace “yo ai Nene mun zata kece kika mishi kika mana solo, kwana uku kenan yana sa kayan nan”.

Nene tace “Aifa kayan nan sun shiga uku, har sai sun fita hayyacinsu za a bar saka su”.
Hajia Aisha Lema ta girgiza kai, ita Nene wai ta manta mai ya kawo su ne? Zata biye musu suna wasu maganganu.

Jawad ya gane Zaid, Tsaf ya ganeshi, kallon kyama yake mishi.
Mancy da ta gama karantar danta tsaf, duk ya fita hayyacinshi, ba yaron da ta bari bane shekaru 4 da suka wuce, mai makon yayi K’iba, sai ya rame yayi duhu, a k’azance.
Baki ta cire ta kira sunanshi.
“ZAID”.
Inda ya ji kiran ya kalla, kallo daya ya mata ya shaidata.
Baki na rawa yace “MANCYYY”..
****
Kasa kama kansa yayi, ya fara kokarin kai mata kiss a baki ta dinga kwacewa amma rikon da ya mata ba na wasa bane, ganin kiss din zai bata mai lokaci ga dama ya samu, kokari yake kawai ya cire mata zani, ya ko ci nasarar cire mata Zanin, tana kiciniyar guduwa ya daga hannu ya kamtseta da mari, ya sake marinta a gefe dayan, tuni ta sheme a kan kujera, ya sa guiwan shi ya danne ta, yahau kiciniyar cire belt dinshi, dogon wandon shi ya fadi, ta ga daga shi sai Boxers ya rage, hankalinta ya tashi matuka, duk wani k'arfin dake gareta ta tattara ta hado Kalmar "YaaaaYaaaaa".

Duk wanda ya ji Ihun nan ya san ba na lafia bane,a sittin suka shige Parlorn har 'yan Bencin Eskaley, gani sukayi Hudu na niyyar haye Dalo da.

Wani Tsalle Zaid yayi ya dira gaban Hudu.
Mancy ta zube K'asa saboda gani take tata ta zo k'arshe.
Umman Jawad tayi saurin zuwa gun Dalo ta rufeta, kwata kwata bata motsi da alamun ta suma.
Zaid ya kai ma Hudu naushi yafi kala 10a baki lokaci guda.
Nene kam  ta shiga tsakaninsu tace kuje ku kai ta Asibiti ta juyo ga Hudu da yayi wik'i wik'i da ido charaf ta rik'e gaban Hudu tace "k'aikayi yake maka? Wallahi kaciya zan sake maka yanzu, gundule ka zanyi wallahi"
Master cike da tasha yace "ga Aska Nene,danuwarka Kanwarmu ka danne?"
Terro yace "yau sai ka bi uwarka Lahira".
Nene cikin Muryar 'yan Daba tace "ku zo ku danne min shi".
Kafin kace kobo yan bencin Eskaley sun yo kan Hudu.

#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode

Biebee Isa.
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO😉
Chapter 16 · 0% Book details