Gabatarwa
Dan Makaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 200 min read
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na D'aya1⃣
('YAN ZAMAN KASHE WANDO)
3/05/2013
Kamar kullum, zaune suke kan Benchi daidai shagon Eskaley dake farkon layi, zaman banzan da suke yi ke nan duk bayan Sallar La'asar, daga gefenshi Haruna ne ke shan Sigari.
Haruna ya mik'o mishi Sigarin da ke dab da k'arewa, ya karba ya sa a baki zai zuk'a ke nan suka hada idanuwa da halitta daya da yake jin kunya duk duniya, da sauri ya tura karan sigarin cikin doguwar hannun rigarshi ya kawar da kai kamar ba wani abu.
K'arasowa ya yi bakin shagon ya musu sallama. Haruna kadai ya amsa tare da gaishe shi sai Eskaley, shi dai gudan kawar da kansa ya yi.
Naira Dari ya fiddo daga Aljihun gaban rigarshi ya ce da Eskaley "Barka dai! Maggi za ka bani Mai Star da Farin Maggi" karban kudin Eskaley yayi, ya hada mishi kayan daya bukata ya ba shi chanjin Naira Goma Sha Biya(15) bai amsa ba sai cewa ya yi a bashi Ashana da sauran. Sallama ya sake yi musu ya wuce cikin layin don tafiya gidan shi.
Haruna ne ya lura da Zufar da abokinshi ke yi, d'an zungurar shi ya yi da hannu yace "Ya dai Mankas?" Da sauri wanda aka kira da Mankas ya zura hannun shi cikin doguwar hannun rigarshi ya zaro karan Sigari, ya jefar kasa tare da sa kafa ya murjeshi. kafin kuma ya hau nannade hannun rigar. Haruna da mamaki yace "Mankas? Kana da hankali kuwa? Sigari mai wuta ka tura cikin rigarka? Mtss! gashi nan har ya taba fatarka".
Mankas ya kauda kai daga kallon fatar hannunshi da ya yi bororo lokaci guda saboda wutan da ya taba fatar, abunka da farin fata, tuni wurin ya yi Ja.
Garin wata hoda Eskaley ya wurgo ma Haruna ya ce "jik'a ka shafa mai a wurin" Haruna ya bude 'yar takardar, ya dauki fasasshen ruwan ledan da ke gefenshi ya dan jik'a ya kamo hannun Mankas zai shafa, Mankas ya janye hannunshi, da k'yar ya iya cewa "Ka barshi, ba damuwa".
Haruna cike da damuwa ya ce "kai fa Mankas gardama gare ka, ka tsaya don Allah."
Bai ce komai ba, sai ya mik'a masa hannun. Hakan ya ba Haruna daman Shafa masa Powdern a wurin da ya fara tashi.
Suna fira jefi-jefi sauran Abokan zaman kashe wandon suka karaso, nan unguwar ya kaure da hayaniyan yan benchin Eskaley , rabi da kwata duk gardama ce.
Da Sallama ya shiga Gidanshi, Ameera da Sabit suka rugo wurin Mahaifinsu dan taren shi "Baba Sannu da dawowa" kansu ya shafa ya ce "Yauwa sannu, ya makaranta?" suka amsa mi shi, "Barka da Dawowa Yaya" ya kalleta da fara'a ya ce "Barka dai Labeeba, ya Makaranta?" murmushi ta mishi tace "Alhamdulilah" shiga ciki tayi ta dauko Tabarma ta shimfida mi shi, ya cire takalminshi ya hau kai, Sabit ya zauna kan kafar Babanshi Amira kuma ta jingina da jikinshi yana musu tambayoyi suna amsawa.
Aunty Asiya ta fito daga Toilet da Buta a hannu, ta ce "Barka da dawowa Baban Amira" wani murmushi me k'ayatarwa suka ma junansu, da ba dan idon yara ba da sun rungume juna, da kallon kauna ya ce "Asee, ya Gida ya Yaran?" ta ce "lafiya lau, ya Kasuwan?" ya ce "Kasuwa Alhamdulilah, kin san sai da na bar kasuwa na ga message dinki? Sai da na shigo Unguwa na tsaya shagon Eskaley dinnan na siyo Magunan" ya k'arashe tare da mik'a mata ledar Maggin.
Murmushi tayi ta ce "Maggin ke nan nayi amfani dashi a Abincin rana, shi ya sa na ce bari na maka text ka taho mana da shi" ta karba tare da isa kitchen inda ta iske Labeeba na jera Cooler din Abincin Baban Amira a Tray, karban Tray din tayi ta ce "Fasa k'ankarar nan cikin Sobon" Labeeba ta amsa mata da "To" ta bude dan firij din da ke kitchen din ta dauko kankarar ta fasa ta juye a Jug.
Duk da su Sabit sunci Abinci sai da suka taya Babansu cin na shi. Ya ce "Wai ya ba a je Islamiya ba yau?" Ameera ta ce "Baba yau fa Alhamis" yace "Afuwan na shafa'a, to ina Homework dinku, na tabbata an baku" Amira ta ce "Sai da daddare zanyi nawa" Baban Amira ya ce "Aa, kuyi yanzu tun ido na ganin ido, ba sai dare ya yi ba, ba wuta a rasa yadda za'ayi" Aunty Asiya ta ce "tashi ku dauko Aunty Labeeba ta koya muku" Rige-rigen tashi suka yi suka shiga dakinsu.
Baban Ameera ya ce "Labeeba to ya Makarantar?" ta ce "Wallahi Yaya Ranar tsiya, kaji zafi, ga nisan tsiya" Aunty Asiya tace "nan ta shigo min kamar zata kife" dariya ya yi yace "Haha, yarinya yanzu kika fara, baki ga komai ba" tace "Wai Allah!" duk suka yi daria.
Ta danyi kewar Gida, tana kewar Mamarta, da yanuwanta, sosai take kewan mahaifarta inda ta girma, amma tana jin dadin zaman Gidan Yayanta sosai, tana sha'awar yadda Yayanta ke tafiyar da Gidanshi, bata da damuwar komai, to damuwar me za ta yi tana gidan Ɗan'uwanta Shak'iki, ga kuma Matarshi da ko kusa ba ta da matsala, ga Yaran Yayanta masu matuk'ar kaunarta, zama da su kan dauke mata duk wata kewa. Haka yanzu ta zauna ta ci gaba da koya ma Amira Homework dinta, sai da ta gama kafin ta ma Sabit da yake shi Tracing ne.
***
6:35pm
Baban Amira ya tashi ya shiga bandaki ya fito tare da daura Alwala, ya kalli Sabit ya ce "Mallam Sabit muje Masallaci ko?" Sabit ya mik'e da murna ya yi alwalarshi duk da ba daidai bane, ya rik'o hannun babanshi. Aunty Asiya da ke kitchen tana tuk'a tuwon dare Baban Amira ya lek'a ya ce "Asee, mun tafi Masallaci, sai bayan Isha'i in Allah ya kaimu" fatan dawowa lafiya ta musu, Labeeba ma haka suka fita daga gidan rik'e da hannuwan Juna.
Suna nan zaune har aka kira Sallar Maghrib, cikinsu babu wanda ya yi yunkurin tashi zuwa Sallah duk da Massalacin na gefensu.
Har Baban Amira ya ketara su ya dawo baya ya ce "Dan Makaho, kuna ji ana kiran Sallah, kuna nan zaune, haba kuji tsoron Allah mana" Tero yace "kai Mallam kaga an Sallame Sallar ba muyi ba ne?" Baban Amira ya ce "ai gani nayi baku da niyya shi ya sa na ce bari na muku tuni" Haruna yace "Zamu yi anjima" Baban Amira yace "Haba, da hankalinku? Anjima? Yanzu me kukeyi? Kun san hukuncin masu Tarrikus Salat? Jinkiri wurin yin Sallah? Kunsan fallalar Jam'i" Master yace "Kaga ba ruwanka da mu, in kai ke karban Sallahn kar ka karbi namu".
Dan Makaho ya mik'e yana kallonshi da mak'allelen idonsa da k'yar yace "Yanzu za mu tafi".
Baban Amira ya kalli Master yace "Aa bani ke karban Sallar ba, tuni ne nawa, Allah ya shirya" ya ja hannun Sabit suka wuce tare da k'etara Titi suka wuce Masallaci.
Cikin muryan yan shaye-shaye Master yace "Kai Mankas naga sai wani lallaba Gayen nan kake, daka barshi dan uwattai, kallon kafirai yake mana" Dan Makaho yayi tsaki yace "Eskaley bani Ruwa leda biyu" Eskaley ya mik'o mai Ledar Pure water dan gefe ya matsa ya fara Alwala.
Haruna yace "kai ma dai Master, bak'ar magana ka gaya mishi, ni ban ga laifinshi ba" Tero yace "Yan Unguwanan Gulma buroba ne dasu, Master ka min daidai" Haruna ya mik'e shima ya karbi ruwan ya matsa inda Dan Makaho yake shima yayi Alwalarsa. Master kuwa da Tero zamansu sukayi, suna kuna Sigari. Har Eskaley ya fito ya kulle Shagonsa, Master da Tero suna nan zaune.
Su uku suka nufi Masallacin Unguwansu da ake ma lak'abi da Sharp-Sharp.
Vote and Comment line by line
#1love
#DM
#anatare
#FWA
#nagode
Biebee Isa.
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Biyu 2⃣
(SHARRI)
4/05/2013
Kan'nannen Idonshi ya dago ya kalli Sady da ta ke zaune a gaban dakinshi, da alama shi take jira, ya dan k'araso da sauri yace "Ya akayi ne Sadiya" ya tambaya fuska cike da damuwa, kamar ba zata amsa ba tace "Barin Gidan nan zanyi" ido ya dan ware kafin ya murza Idonshi yace "me ya faru?" bata amsa shi ba, ta sake jadadda mai da "Gidan nan zan Bari" dan mur ya sha kafin yace "ba inda zaki, ba ki da inda yafi nan, ni a matsayina na miji ban bar gidan nan ba, kema ba zaki bar gidan nan ba" kuka ta fashe dashi ya matso gareta ya janyota jikinshi ya rungume yana shafa bayanta alamun lallashi, ya sama magana a hankali "Sady, komai zi wuce--" Be karashe maganar da ya so mata ba sukaji ana rafka sallati a bayansu "Inallillahi wa ina ilaihir rajiun, DanMakaho kanwarka kake runguma haka? Kana shafa mazaunanta?" cike da tashin hankali suka sake juna suna kallon Aunty Shafa'atu Matar Babansu. Bambamin da ta hau yi ne ya sa mutanen Gidan suka firfito, Aunty Shafa bata bar tafa hanaye tana jefansu da mugayen kalamai ba.
Jikin Sady na bari ta karasa gunta tace "Aunty Shafaatu donAllah kiyi shiru, wallahi ba wani abu bane, kin manta Yaya Zaid Yayana ne Muharramina Shakikina?" hannu Aunty Shafa'atu ta sa ta buge bakin Sady tace "yi min shiru Munafuka, yau kuka fara shafar juna kuna iskanci? Shegia Yar Shegia Karuwar Yayanta.".
Ran Mankas ya baci ainun, be san lokacin da yayi wani tsalle ba ya shak'o wuyan Aunty Shafa'atu ba ya danganata da bango, k'aninta Hudu ya yo kanshi, be saketa ba, k'ak'arin mutuwa take tana jin azaba tace "DanMakaho kasheni zakayi? Hudu ci man ubanshi" kamar umurninta yake jira, nan ya fara dukkanshi yana kai mai naushi ko ta ina, ko motsi beyi ba illa kara matse hannunsa da yayi a wuyanta.
Fati da Annah suka rufe Sadiya da duka durkusawa tayi tana kuka ba su bar dukanta ba, kukanta yaji ya tsananta, ar yanzu su Hudu ba su bar dukkanshi ba kuma be saketa ba, kukan da Sadiya keyi ne ya sa shi sakin Anty Shafaatu ya karasa gun su Fati ya finciko su yana kai musu duka ko ta ina,.
Sarkin yawa ya fi sarkin karfi, nan suka hadu gabaki daya suka ma Sadiya da Mankas dukkan tsiya.
****
Bangon Kantangarsu daya, ko meke faruwa a cikin Gidan Alhaji Zaki musamman ta wurin BQ suna ji kamar a cikin Gidan akeyi, suna zaune baki daya kan darduma sukaji muryar Hajia Shafa'atu na cewa "Inallillahi wa ina ilaihir rajuun, DanMakaho kanwarka kake runguma haka? Kana shafa mazaunanta?" zumbur suka mik'e tare da matsawa kusa da bangon Gidan.
Suna nan tsaye jigum-jigum, sunji komai kamar gabansu ake, jikinta sai bari yake, baki na rawa tace "Aunty Asee kar su kashesu, muje mu rabasu DonAllah" Aunty Asee tace "hmm, Labiba ina mu ina shiga fadan Gidan Alhaji Ali Zaki? Haka suke, ai sun dade ma basuyi ba, haka suke wallahi".
Muryar Alhaji Ali sukaji yana fadin "Me ke faruwa a gidan nan ne? Da alamu yanzu ya shigo Gidan, da sauri suka tashi daga jikinsu Mankas. Anty Shafaatu ta fashe da kuka ta matsa kusa dashi cike da kissa "Nagaji Alhajina, nidai ka sakeni, ba zan iya ba, har sai yaushe Dan Miji zai bar dukana? " Hankali tashe yake tambayarta me ya faru, ta ja majina tace "Zuwa nayi baya naga DanMakaho na ta latsar Sadiya yana mata wasu abubuwan da na kasa hakuri sai da na mishi magana na nusar dashi Kanwarshi ce Muharamma, in kuma aure yakeso ya fada sai a mai, bansan ya akayi ba sai dai kawai naga ya kaini k'asa yana dukana Sadiya na tayashi da kyar su Hudu suka zo suka karbeni daga hannunshi".
Labiba ta bude baki tana kallon Aunty Aseeyah tace "Laah Aunty Karya takeyi, wallahi karya take musu, ba abunda ya faru ba kenan, karya ne" Aunty Aseeyah ta tabe baki ta koma kan dardumanta ta zauna tace "Labiba, meye naki? Sharri ai ba yau ta saba k'ala musu ba, In Allah ya tashi saka ma DANMAKAHO da k'anwarsa wallahi sai Hajia Shafa'atu ta wulakanta ta shiga hakkinsu sosai, wata irin Mata ce da muke neman tsarin Allah daga garesu".
Jin muryar Alhaji sukayi yana cewa "Allah ya tsine maka Zaid, matar tawa ka buga? Allah ya tsine ma ban yafe ba, watsatsse kawai" Labiba ta fashe da wani irin kuka, kamar ita a ka tsinemawa Aunty Aseeyah ta kallota tace "Labiba" cikin kuka tace "Aunty Asee Mahaifinshi ya tsine mai, Mahaifinshi ya laanceshi, be san gaskiar abunda ya faru ba, ya hau kan maganar matarshi, zanje in gaya mai gaskia, wallahi zan gaya mishi matarshi k'arya takeyi" ta zabura Aunty Asee ta taso don kamota, amma bata ci nasara ba, har ta kusa k'ofar Gidan Baban Sabit ya shigo, hakan ya sa tayi turus.
"Ina zakije?" kamar bata cikin hayyacinta tace "K'arya Auntynshi take mishi, wallahi ba haka akayi ba, ina bakin katanga, naji komai, yaya Babanshi tsine mishi yake" Baban Ameera ya kalli Aunty Aseeya, girgiza mai kai, ya sa hannu ya rik'o Labeeba ya jawota har tsakar gida ya zaunar kan tabarma yace "me ya faru" a hankali Aunty Aseeya ta bashi labarin abunda suka ji, jinjina kai yayi yace "to ke me zai dameki?" Majina ta ja kafin tace "Yaya, wallahi Allah sharri suka mishi, k'arya suke" ganin tana magana kamar me shirin fita hayyaci, ya ma matarshi alamu da ta shiga da ita ciki.
Aunty Aseeya ta kamo hannunta ta ja ta zuwa daki, bakin Gado ta zauna ta rafka uban tagumi, Aunty Aseeyah ta fita gun Mijinta, Kubra ta rasa me ke mata dadi, bata da kuzari, ko da suka zo bacci, hakan tayi ta juyejuye, haka Labeeba ta k'arashe darenta.
Washegari da safe idanunta sunyi luhuluhu saboda kukan da taci, bata san shi ba, amma abunda aka mishi ya tsaya a ranta, to shi wani iri ne da ba zai iya kare kanshi ba? Meyasa ba zai iya furta k'arya ake mishi ba? Shi sakarai ne? Haka ta tashi tayi shirin Makaranta, ta shiga ta gaida Aunty Aseeyah, Baban Ameerah ya kai yara Makaranta, Aunty Aseeya tace mata ta tsaya ta yi kalaci amma tace sauri take ta makara, adduan samun nasara ta mata, ta rakota har bakin k'ofar gidan, Adduan fita daga Gida Labiba tayi ta fice ta bi dogon hanyar unguwarsu ta Tudun Matawalle inda zata neman abun hawan da zai kaita National inda zata hau Motar Makaranta (School Bus).
Kasancewar Safiya ce, Unguwar bata cika sosai ba kamar yanda take cika wurin k'arfe 11 na rana, tafiya take cikin dan sauri, unguwar sai an fito bakin Titi ake samun abun hawa.
Daga chan nesa ta ke hango wani zaune na busar sigari, da sauri ta zaro wayarta don ganin lokaci, 8;17am, mamaki ya cikata, wanene ke banka ma cikinshi hayak'i da sassafe haka, da ta k'araso gurin sai ta ga matashin saurayine, daidai nan ya murje guntun da k'afa ya sake kyasta wani da ya zaro daga aljihun gaban rigarshi ya fara zuk'a.
Labiba ta dan yi jim tana kallon bawanAllahn nan, Zuciyarta na tunzurata kan taje ta mishi magana. Har tazo ta gabanshi ko kallonta beyi ba, haka ta tsallaka titi tana waigenshi har ta samu kekenapep da zai kaita National don tafia Hassan Usman Polythecnic.
#1love
#DM
#SonSo
#anatare
#Fikrawriters
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Uku3⃣
('YAN MAKARANTA)
Har lectures din ya k'are Labeeba bata fahimci komai ba, a hanyarsu na zuwa Masallaci yin Sallahr Azahar, Aisha Usman K'awarta take tambayarta lafiya yau ta ganta wani sukuku da ita, jim tayi kafin tace "Kaina ne yake dan ciwo amma ya bari yanzu" Aisha tace "haba ni dai ince, yau na ganki ga ki nan, Allah ya sauwak'e" murmushi Labiba tayi tana kara k'allon k'awarta.
Kafin su k'arasa Masallaci suka ji ana k'wala musu kira ta baya, dakatawa suka yi tare da dan waigawa, cikin hanzari ya k'araso yana me sakin su da k'ayattacen murmushi.
"Aisha, Labeeba, ya kuke?" a tare suka amsa masa da Ina wuni Captain Abu Sideeq? Ya amsa tare da cewa "kun gama lectures din yau ai?" Aisha ta gyada kai, Labeeba tace "eh mun gama" yace "Good, to kuje kuyi Sallahr, ku sameni a Ajinmu, sai mu duba karatun yau ko na 1hr ne" amsawa suka yi tare da wuce shi don nufar Masallacin.
Aisha tace "Son ki yake" Murmushi Labiba tayi, tace "na sani" da doki Aisha tace "I knew it, kema kina sonshi?" Labeeba ta sake wani murmushin kafin tace "ina dai ganin mutuncinshi, yana kuma burgeni, ina son naga mutum me k'wazo da basira" Aisha ta dan tafa hannuwanta tace "a sannu kema zaki fara son shi, ai ya hadune ya hada komai, ga bokon, ga addinin, ga kuma Kyaun".
Labiba tace "ba k'arya".
Daidai nan suka iso Masallaci, ko waccen su ta d'auki buta ta nufi Fampo.
Sun idar da Sallah suka nufi ND2 inda AbuSideeq yake, yana ganinsu ya k'araso yana jefan Labiba da wani irin kallon da shi kawai ya san ma'anarsa.
Murmushi kawai Labiba tayi, yace "muje daga k'arshen Ajin, yana gaba suna bin shi a baya, daga can suka samo Bench suka zauna, shi ne a tsakiyarsu, ba bata lokaci suka hado masa Jotting din Lectures Biyu da suka yi yau, dubawa ya yi kafin ya shiga yi musu bayani cike da k'warewa.
K'arfe 2:30 ya ce su dakata haka. Godiya suka masa me tarin yawa, ganin yadda AbuSideeq ke bin Labiba da wani irin kallo ya sa Aisha ta dan mik'e ta ce "bari na dan amsa waya".
Ganin haka yasa AbuSideeq fara magana "Labiba..." sai kuma ya yi shiru, ya sake fadin "Labiba ina... ina..." sai ya sake yin shiru, sai da, mintuna kusan 4 suka wuce kafin ya ce "bansan ya zaki dauki maganar nan ba, amma ina so in fada miki wani abu, amma kuma dai na kasa, k'ila rashin faden shi ne Alheri, bari kawai in bar shi, tashi muje na rakaku ku samu abun hawa".
Dago idanuwanta tayi ta kalle shi, kafin ta saukar da kai ta fara magana cikin sanyinta ta ce "So na kake yi, kana jin nauyi na, kana tsoron yadda za ka gaya mini, kana gudun kar hakan ya zaman silar bacewar kyakyawar Alak'ar da ke tsakaninmu?" da sauri ya kalleta.
Kai ya fara gyadawa kamar k'adangare. "Haka ne, wallahi haka ne Labiba, tun farkon haduwarmu a office din HOD, lokacin da Yayanki ya rakoki Registeration na kamu da sonki" Labiba ta danyi murmushi ta ce; "Ban yi mamaki ba, its obvious ai".
K'arfin guiwa ya samu, ya ce "Ina fatan zaki amince mini?" murmushi tayi ta ce "wallahi ban sani ba, bansan me nake ji a kanka ba, bansan me zanji nan gaba a kanka ba, amma nasan cewa ina matuk'ar ganin girmanka, sosai kake burgeni Captain, bansan ko nan gaba wata alak'a da ta wuce wannan zata shiga tsakaninmu ba, amma ko me ke nan, Allah ya zaba mana abin da yafi Alheri a rayuwarmu".
Kallonta kawai ya tsaya yi, sosai ta burgeshi, sonta na k'ara ruruwa a zuciyarshi, bai taba ganin irinta ba, bai taba sanin Matan Katsina na iya kallon Namiji haka su gaya masa gaskaya ba tare da wani 6oye-6oye ba, ba ta rufe mishi komai ba, ta gaya mishi iyakar gaskiyarta, hakan da tayi ta matukar burge shi, yana da tabbacin da wata ce, yaudarar shi za ta yi, ko ta ce mishi eh itama tana sonshi ko don wani abu, ko kuma ta bata mishi lokaci, ko kuma ta ja mishi aji, haka yake so Mata su kasance Straightforward, in ana haka, da ba a samu Yaudara da cin amana a cikin Soyayya ba.
Mik'ewa yayi yace "tashi muje na nema muka abun hawa" murmushi tayi tare da sa6ar jakkarta, ta bi bayanshi, a bakin kofa suka ga Aisha, tace "muje ko?" Labiba ta gyada kai, a haka har suka fita bakin makaranta ya tsaida musu keke Napep, fadin inda zasu sukayi, mai Keke Napep yace "ke ta tudun Matawalle ciki zaa shiga?" Labiba tace "eh ciki ne ta wurin Makarantar Hope" yace "150 ne kudinki, ke kuma ta k'ofar k'aura layout ki bada 250" da yake hakan suke badawa ba su tsaya ciniki ba.
Aisha ta fara shiga kafin Labiba, Labiba na ganin AbuSideeq ya sa hannu cikin Aljihu tace ma Adaidaita sahu, mu tafi kaji" ba tare da bata lokaci ba ya ja Kekenshi, ta dan juyo ta daga ma Captain hannu, shi ko yatsarshi ya nuna mata alamun "ke ko" kafin suka sakar ma juna murmushi.
Aisha tace "Bawan Allah, be gajia" Labiba ta gyara zamanta tace "kullum cikin Hidima yake".
**
Abu Sadeeq Abu, dan Department of Engineering HUK Poly, wani irin Yaro ne me matuk'ar k'okari, HND2 yake, a nan ya gama ND ya jona HND dinsa, a Dept din kowa na sonshi sabida kyakyawar Alak'ar da yake dashi da Malamai da Dalibai, k'okarinshi be daura mai Girman kai ba.
So da yawa in ana darasi, kace ma Mallami ba ka gane darasin yau ba, zai ce "ka sa min AbuSideeq a HND2 ya ma bayani zaka fi ganewa" hakan ne ya faru da Labiba a ranar da suka samu Mallama Amina bayan darasi, tace "ta sake mata bayanin wani fannin da bata fahimta ba" mallamar tace "Wallahi sauri nake, amma kije HND, ki samu a AbuSadeeq a HND2, kice ni na aiko ki, ya miki bayanin topic din". Labiba ta mata godia ta ja Aisha suka tafi inda Mallama ta mata kwatance.
Ko da sukaje sukayi tambaya, nuna musu shi akayi, yana tsakiyar maza biyu da mata 3 daga gani 'yan ND2, yan gaba da ajinsu Labiba, yana ta faman musu bayani. Aisha tace "mu jira ya gama, ko muje mu dawo" Labiba ta girgiza kai ta musu Sallama" suka amsa tace "ina wuninku? DonAllah Abu Sadeeq muke nema" kallonta yake yi sosai, yarinyar nan ce da Yayanta ya kawota office din HOD ranar da yake ciki, murmushi ya mata yace "Ga wani Abu Sadeeq nan"
Murmushi tayi sosai, ta ganeshi, shine HOD yace mata in tana da matsalar karatu ta zo gurinshi zai mata bayani".
"Sannu da Aiki, Mallama Amina ce tace na sameka, wani abu ne ya shige min duhu a course dinta, shine nakeso in kana da lokaci ka dan min bayani" Agogo ya kalla, kafin yace "Alright ba damuwa, amma ga yayyinki nan muna karatu, saidai in mun gama" tace "lahh dama ai sai kun gama" yace "to nam da 30mins InshaAllahu" murmushi ta sakar masu duka, sosai ta burge duk na wurin, tace "bari mu dawo" ta ja hannun Aisha da ba tace ma kowa komai ba.
Ya musu bayani yanda ya kamata, Labiba da Aisha sun fahimta, suka mishi godia sosai, yace musu daga yau duk bayan ko wane lectures suzo ya sake musu bayani, hakan zaisa su fi fahimta. Godia suka sake mishi, tare da exchanging numbers.
Tun zuwansu Poly Aisha ke tare da ita, tana son Labeeba sosai, duk da a Ajin Maza sunfi Mata yawa, matan basu wuce sha biyar (15) amma Aisha bata da k'awar da ta wuce Labiba, ko wata daya basu rufe a Makarantar ba, amma Aisha na jin Labiba har ranta.
Labeeba za ta iya rantsuwa Aisha na sonta matuk'a, kodayake ita dai haka take, indai ta zauna a wuri, to tana da farin jinin mutane, kowa na sonta, ba za a ce don Kyau ba, don ba fara ba ce, a'a, don kyauwun zuciyarta ake sonta, ta iya zama da jama'a, kowa nata ne, bata da zabin mutane da take mu'amala dasu.
Wannan kenan.
Labari suke da Aisha kafin a shiga layin Unguwarsu Labiba, Aisha ke hada ta da Allah tazo gidansu don Mamarta na son ganinta, har k'arya ta mata cewa Mamar ta ce in ita Labiban bata je ba to ita za ta zo gidansu Labiban da kanta, duk dai don taje Aishar ta ce mata haka.
Dariya Labiba ta yi tace "Insha Allahu zanzo wannan Satin, ki ce Mama tayi hakuri.
"Allah ya sa kana da chanjin dubu daya" cewar Labiba, mai Adaidaita ya buga tsako yace "Hajia sai kiyi magana tun wuri ni banda chanji" Aisha tace "nima wallahi dubun ne" mai A daidaita ya fara mita da ya san Chanji ne da be dauko su ba, gashi har ya kusa shiga Tudun Matawalle, Labiba tace "Afuwan, akwai shago a ta wurin zasu samu Chanji" mai Napep yace "ga unguwanku ba dadin shiga, balle jiya anyi ruwa" Labiba dai hakuri ta sake bashi, Aisha dai tsaki tayi tace "ya cika mita".
Daidai Shagon Eskaley ya ci burki, Aisha ta mik'a mishi dubu daya tace "gashi ka samo chanji ka cire duka" ko waigowa beyi ba yace "Yo Anguwarmu ne? ko sani na sukayi da zasu bani chanji?" Labiba ta lura Mai Keke Napep dinnan dan tijara ne, ta sauka tace "bari na samo" Aisha ta bude baki tace "ya za'ayi kije gurin 'yan Shaye-shayen chan? Haba Labiba ba mutuncinki bane a ga kinje chan shagon, ki bari ya samo" Labeeba ba ta tsaya ba, illa ta karasa bencin Eskaley da Sallama.
*
Zaune yake kan plastic chair, cikin wata longsleeve shirt da 3 quartern Sojoji, face cap dinshi wanda ya rufe kanshi har wurin idonshi ruf ma irin wandon ne, kayanshi kenan duk dunia, ya dora k'afa d'aya kan d'aya, Idonshi lumshe. Yana shak'ar k'amshi, yana jin dadin yanayin da World ke sashi,
World shine sunan da 'yan bencin Eskaley ke kiran Tabar Wiwi, a cewarsu, Ita Wiwin Duniya ce, ma'ana komai, in suka zuk'eta, jin kansu suke daidai da Saraki, Sarauta Wiwin ke sasu. In ka zuk'i World, kafi kowa, wannan ma ya sa Zaid zama shi kadai tare da ba su Master baya, wanda suke fama buga Whot ko na Sigari basu dashi.
Duk k'ullin Worlda naira dari biyu Eskaley ke saidawa, yana bada bashin Sigari, amma be yarda ya bada bashin World ba.
Tunda suka ga ta nufosu suka k'ura mata ido, Eskaley ya amsa yana washe hak'oranshi jajjaye, da murmushi ta kallesu tace "Ina wuninku, DonAllah chanji naira dubu nake son ka taimaka min dashi" ta maida hankalinta gun na cikin shagon, Eskaley yace "Ahhh, chanjin dubu da sauk'i, basu kai ba wallahi" Labiba tace "akwai Credit? Mtn?" "Aa wallahi ya k'are" dubu dayan ta mik'a mishi tace "to DonAllah ka dan ara min #350 na ba me keke Napep" Eskaley yayi daria yace "Hajia yau wallahi da sauk'i, yau ba ciniki"
"Oh Allah!" ta fada a gajiye, ta musu Godia ta juya.
"Ga 350" taji an fada murya a dakushe, ta juyo ta ga wa ke magana, bata samu kallon fuskarshi ba sai gani tayi wani ya fincike kudin da aka mik'a mata.
"Shege Mankas, kana da kudi a aljihunka kasa Eskaley ya hana ni World, kai mik'o min World dinnan" ran mankas 6ace yace "donuwarka bata kudin" master ya kalleshi yace "mankas ni zaka ma wulakanci don nace ka siya min World, don ni ba mace ba ce, banda kayan dadi ko? to ranta min uku da hamsin dinnan, zan baka" daidai nan mai Napep ya sake buga horn, Labiba dai ikonAllah take kallo.
K'yallararen idonshi ya dago ya kalli Master bece komai ba, Master ya buga tsaki ya matsa kusa da Labiba yana cewa "Danmakaho ya ga Chikala" da sauri Labiba ta kalli mazauna gurin don ganin dan Makaho, amma bata samu nasarar ganinshi ba don ya juya mata baya, dubu dayan ta mik'a ma Master, tace "ka bashi, na biyo shi chanji, zan zo na amsa" master ya yashe jajayen hak'oranshi yace "Yayata, donAllah ki bar min chanjin mana" tace "aa gaskia ni ba zan baka kudina ka k'ona su ba" da sauri Master yace "wallahi ba Sigari zan sha ba, abinci zanci Yunwa nakeji". Labiba tace "ban yarda ba, nidai ka ba DanMakaho chanjina".
"Haba Babbar yaya kin fi k'arfin dari bakwai da hamsin, nidai Godia nake" Horn mai Napep ya sake buga mata har yana mata masifa, da k'arfi master yace "dallah ware Mallam, zaka ishemu da Oda, ka bita a hankali ko na ci uwarka, Yayarmu Allah ya kiyayeki" Mai Adaidaita tuni ya shiga taitayinshi, kar ya sha duka a banza, Labiba na shiga ya ja Napep dinshi suka shiga cikin Unguwa.
"Master, bani" cewar DanMakaho, "me zan baka?" master yayi kamar be san me yake nufi ba, Haruna yayi wuf yace "kai Master, muna gani fa ta baka 1k, kuma muna ji tace ka ba DanMakaho chnajinta, kawai kawo kowa a bashi world daidaiya" DanMakaho ya dago k'yallararen idonshi yace "ku bani nan" Master yace "haba Mankas, yawa kakeyi wallahi, kai ma fa World dinnan ka taba, kuma ka hanani, ka bari mana Eskaley ya bamu daidaya".
"DonAllah Mankas ka bar mana kudin nan, haba mana yawa kake" mik'ewa yayi ya fizge kudin, tare da cewa "In tazo k'arbar chanji ta uwar me kuke so na ce mata?" Master yayi wuf yace "ta fa bani" DanMakaho ya zira kudin Aljihun gaba inda Kwalin Sigari ke ciki, tare da fadin, "in na bata ta baku".
Barin gurin yayi, ya shiga cikin unguwa, su Master suka bishi da Ashar kala-kala ransu bace.
**
5:20pm
Baccin Awa 2:30 yayi, yana farkawa World ta sakeshi, ko da yake be shak'eta duka ba, Kewaye ya shiga ya dauro alwala, yazo ya hada Azahar da La'asar, rigarshi ya shinshina yaji tana warin zufa da rana ga kuma k'aurin hayak'i, guntun tsaki yayi, be yarda ya zauna da dauda ko k'azanta ba, duk da wadan nan sune suturunsa, sai wata bak'ar jallabiya da yake sawa a duk lokacin da zai wanke riga da wandonshi yana iya k'okarinshi wurin tsaftace su, be son shiga cikin Gida amma dole ya shiga ya dauko sabulu, ya ga dan Shegiar da zai hanashi.
Straight ciki ya shiga, da Hudu ya ci karo ya fito kamar mara gaskia, yana zare ido, da sauri ya wuce boysquaters, da dan mamaki DanMakaho ya kallesh yana mamakin saurin da yakeyi kamar wanda yayi k'arya, amma da yake ba damuwarshi bane sai yayi gaba ya shige Store ya dauko Klin.
Ya na fitowa daga Store yaji Aunty Shafa na cewa "Uban wa ya dauke min Naira Dubun da na aje kan Center Table" Annah ta fito daga daki tace "nidai Wallahi Aunty bani bace, tun dazun ina daki" Fati tace "ni kuma wallahi ban ma san kin aje kudi ba" "duk dauke dauken da ake min bana magana, yau abun ya isheni, daga in aje kudi in shiga in fito sai na nema kudi na rasa? ina Sadiya?" Fati tace "tana cikin dakinta ko?" Aunty shafa tace "na san itace, ya zaayi dama ku dauka, aiko ko ta bani kudina ko na mata mugun bugu, kuma Ubanta yazo ya biyani kudina"
Mankas be gama jin sauran zancen ba ya banko labulen Parlo ya shigo, ya na bude idonshi ganin ina Sadiya, ganin bata cikinsu ya kutsa cikin dakin ya ganta chan gefen gado me kama da na 'yan boarding durk'ushe tana karkarwa, ga dukkan alamu ta ji zantuttukan su Aunty Shafa, kuma ta tsorata, be tsaya kwantar mata da hankali ba ya finciko hannunta ya ja ta har Parlo gaban Aunty Shafa ya tsaya.
"Uwar da ta fasa taba ta, ta raina Uwar da ta haifeta" duk suka yi cirko-cirko ba me motsi, ya juya ga Annah da Fati, yace "duk randa kuka sake daga mata hannu, sai na sassareku" Aunty Shafa tace "Dubu daya ta ta dauka, kuma sai an biyani, DanMakaho ka fita idona, ni ba sa'arka bace, Uwarka ma bata fara yi dani ba, wallahi ku firdo min Kudina kafin Daddynku ya dawo, kaga duk inda yake yana daf da Gida, ku bani kudina, ba zai ji komai ba".
Baki na rawa Sadiya tace "Wallahi Aunty bamu dauka ba" Mankas ya daka mata tsawa yace "dallah kyaleta, munje mun dauka, ba za kuma a bayar ba, in ya dawo me zaiyi? Tsine min? Wani irin tsinuwa ne zai min wanda be min ba? Mtswww" ya buga tsoki kafin ya ja hannun kanwarshi suka fita daga Parlorn.
Daidai nan Hudu ya shigo yana zare ido, "Wai meye ke fariwa nake jin Hayaniya Hajia?" Kwafa Aunty Shafaa tayi tace "dani Dan Makaho yake cikin Gidan nan, wallahi zaman Gidan nan sai ya gagareshi fiye da yanzu, bari Alhaji ya dawo".
*
Zaunar da Sadiya yayi gaban k'ofar dakinshi ya dan bata baki, tare da kwantar mata da hankali ta hanyar gaya mata zai rok'i Babansu kan ya barta taje Gidan Mamansu hutu, sai da ya ga ta saki ranta kafin ya koma daki ya dauko Bak'ar jallabiyarshi ya zura, ya kwaso Riga da Wandon da zai wanke tare da bucket a toilet, cire abubuwan gaban Aljihunshi yayi, da Mukulli, da kwalin Sigari, da Naira dubu daya ya ajiye k'asa, Klin ya Jik'a ya fara tsoma rigar ya fara cudawa.
Be gama wanke Rigar nan ba yaji muryan Daddynshi yana fadin "Ina Dan Makahon yake?" dago idonshi yayi ya kalli Daddynshi da ya nufosu kamar Zakin da ya kwana 7 be ci abinci ba, duk 'yan Gidan sun rufa mai baya, kafin ya ankara Daddynshi ya sakar mai nushi kala biyu a gefen baki, ko motsawa beyi ba, Sadiya ta fashe da kuka.
" Sata? A gidana DanMakaho? Dama duk sace-sacen da akeyi kai ne? Yau dubun ka ya cika, yau wallahi sai ka kwana bayan Kanta" wayarshi ya dauko ya latso DPO, Sadiya ta zube gabanshi tare da rikon kafarshi, tace "Daddy Wallahi ba shi ya daukar mata Dubu dayanta ba, wallahi bashi bane, Daddy, Klin kawai ya shigo ya dauka, Daddy ka yarda damu" Haurinta yayi dai da ta matsa gefe, da sauri Mankas ya karasa gunta ya durkusa tare da dagota yana watsa ma 'yan Gidan mugun kallo, ya tsaida kallonshi ga Mahaifinshi ido cikin ido yake kallonshi.
"Zaid Mahaifinka ne, Zaid kar ka manta Soyayyar da ya wanzu tsakaninku, Zaid kar ka sake ka yi ma Mahaifinka ba daidai ba, duk yanda zuciya ke tunzuraka kan ka mishi wani abu, Zaid ba zan yafe ma ba, kar ka ga tsinuwan Mahaifinka kamar baya tasiri a kanka, Zaid a ranar da zan juya ma baya, Zaid ka rasa Lahirarka wanwar, Zaid Mahaifinka ne, ba komai tsakaninku sai k'auna da kyautatawa" muryar Mahaifiyarshi yaji na mai kuwa kamar a lokacin take magana.
Runtse ido yayi sosai, muryar Hudu ta katseshi inda yake cewa "Lahhh, ga Dubu daya chan" da sauri ya bude idonshi, ya ga Hudu har ya durkusa ya dauka, da azama ya karasa shima ya rik'o kudin, idonshi duk biyun ya bude su yace "Sake min kudi".
Aunty Shafaa ta karade da "Wallahi dubu daya tace, ashe dama kai ka dauka, in kace kana so ai DanMakaho dubu daya ba komai bace, zan baka, amma meyasa zaka daukar man kudi?".
Daddy yace "Zaka sake kudin nan ko sai ranka ya baci?" sai da Daddy ya sake maimaitawa kafin ya sakar, ran Daddy a bace yace "Shege Barawon Banza, kaji haushi" halbi Zaid yayi da Bokitin Wanki, ya shige daki rai a dagule.
***
Zaune suke gaba ki daya , Fira sukeyi har Yara suna dariya, daga bisani sukaji an fara iface iface, sosai su ke jin abunda ke faruwa daga kan tabarmar da suke zaune,
Labiba ta mik'e da sauri ta k'arasa jikin Bangon Gidan, nan taji komai,
Girgiza ka ta farai kamar k'adangaruwa, "Wallahi ba sata yayi ba, Aunty Aseeyah wallahi dubu daya ta ce, kudina ne, ni na bashi, Aunty DanMakaho ba Barawo bane, Ya Illahi".
°°°°°°°
Kindly Vote and Comment Line by Line
#1love
#DM
#anatare
#™SonSo
#FWA
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DANMAKAHO 😉
4⃣
Rikota tayi da hannu biyu, "Labiba, ki yi min magana". Naunayar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta bata labarin abun da ya faru dazun.
Aunty Aseeyah tace "Labiba, akwai abubuwa da yawa dake faruwa gidan Alhaji Ali Zaki, tun kafin zuwanmu Unguwar nan, ba zaki gane ba, amma akwai 6oyayyen alamari tsakanin duk wani rai da ke cikin gidan, wanda ba hurumin mu bane, ba mu da wata alak'a dasu da ta wuce makwafataka".
Labiba ga kalli Matar Yayanta " Aunty, Hakkin Makwaftaka fa? wannan babban hak'k'i ne, ya kamata a yi wani abu a kai, so biyu ina jin Makirar Matar nan na hada makircinta, ba zata tsaya a nan ba, ba za kuma ta bari ba, ya kamata Aunty a tari Alhaji Zakin".
"Hmm, Labiba, fadan da ya fi k'arfinka sai ka maida shi wasa, ba abunda za mu iya yi. Hajia Shafa, ta zarce tunaninki, bana son matsala da Hajia Shafa, yanda ba abunda ya taba hada mu, bana son komai ya hadamu, amma tabbas Dan Makaho da k'anwarshi na buk'atar Addu'a, shi kawai zamu taya su".
Hannu ta sa ta ja dankwalinta baya, murya k'asa k'asa tace " Sakarai! Kamar ba namiji ba, ba ya iya kare kanshi? Meyasa be iya k'aryatasu in sun mishi sharri? Mts"
Aunty Aseeyah tace "Magana kike?" girgiza kai tayi tare da mik'ewa ta shige daki
5/5/2013
1:30pm
Tunda garin Allah ya waye zuciyarta ke mata kitse-kitse, DANMAKAHO k'wak'walwarta ke kwada ma kira, baza ta iya shaidashi a hanya ba don ba saninshi tayi ba, dalili take so ya sa ta ga DanMakaho, kamar shekaran jiya, da tunaninshi ta tashi, ta damu da lamarinshi, abu kamar a film ko a littafan hausa, so take ta shiga rayuwarshi, so take taji damuwanshi, abun da kamar wuya, amma sosai take so ta hadu dashi, haduwarsu ta farko in brief ne, ko ganin fuskarshi ba ta samu tayi ba, gashi yau ba ta zuwa Makaranta balle ta sa ran ganinshi a Waje, haka kurum ta tsiri zuwa Gidansu Aisha.
Yara na Tahfiz, Parlo ta iske Yayanta da Matarshi, a gefen Kujera ta zauna tana musu murmushi "Yaya, ina neman izinin zuwa Gidansu Aisha Usman, Mamarsu ke son ganina, har cewa tayi in ban zo ba, ita zata zo".
Dan dariya sukayi kafin Yayan yace "Kinsan Gidan ne?" Girgiza kai tayi alamun aa kafin tace "kwatance ta min" yace "to bari naci Abinci na saukeki" tace "to shikenan nagode".
*
Da kwatance suka gano Gidansu Aisha, dari biyu ya bata yace " ki hau Adaidaita sahu, kuma kar ki kai Maghrib"
Godia ta mishi, Aisha ta gaisheshi sannan suka shiga Gida.
Ina za'a saka Labiba don murna, tunda ta tako cikin gidansu Aisha ta ke cin karo da Soyyayar mutanen gidan, har Mai aikinsu ta san Labeeba, da kaunar da ke tsakaninsu.
Ya Illahi, haka suke sonta? Barin ma Mamar Aisha da take ji kamar ta goyata, kayan mak'ulashe a ka cika gabanta, daga bisani a ka kawo mata Abinci mai rai da lafia, ita dai Labiba daria take tayi, tana cikin cin Samosa Aisha ta k'atseta da cewa "Zo muje ki gaida Daddy".
Kunya ya kama Labiba, "DonAllah ki bari sai anjima" Aisha bata saurareta ba, sai jan hannunta tayi don ta mik'e tsaye tare da janta ta na gaba Labiba na bin ta a baya.
Har k'asa ta durkusa ta gaida Daddy, Daddy ya amsa cikin kulawa ya dauko dubu biyu ya bata, bata iya amsa ba sai dai Aisha ta amsar mata sukayi Godia suka koma dakinsu Aishan. Sai da Laasar yayi suka yi Alwala don yin Sallah.
Labiba na adduointa ta ji kamar ihu daga waje, sai da ta kasa kunnuwanta sai taji ashe Ihun murna ne da alamun bak'i sukayi, tashi tayi ta ninke Darduma, ta zauna gami da tsiyayo kunun Aya a Cup. Aisha ce ta shigo fuskarta dauke da murna. "Besty kinsan me? Cousins dinmu ne sukazo daga Abuja wallahi dadi kamar ya kasheni".
Labiba tace "Inye, fatan sunzo Lafiya" "Lafiya lau wallahi, taso muje ku gaisa" hararar wasa ta jefeta dashi, ta dan muskuta tace "tafiya zanyi ni, banason marace yayia ina waje, kuma dai zaun daura Sanwar dare" Aisha ta san ta mata tunda tun bayan Azahar tazo, don tace zata tafi yanzu ba wani abu ne. Mikewa tayi tace to "barin sanar da Mama".
Labeeba tace "ke dai jira mu tafi tare, katon gyalenta Khashka me kauri ta yafa, Aisha kuma ta janyo wata yar gyale bayan ta mata packaging su Samosa da Springrolls tace a kai ma su Ameera.
Ba ta Parlor inda ta barsu, ba dai har sun tashi ba? Da sauri ta ja hannun Labeeba sukayi tsakar Gida, inda ta gansu tsaitsaye, kallo ta bisu dashi kafin tace "Yaya Hafeez ba dai kun fito ba". "wallahi kuwa A'i, gwara muje mu gaida Hajia Kaka kafin ta kira Abba tace Munfi Awa 8 a katsina bamuje mun gaisheta ba".
Dariya sukayi gabaki daya, Mama tace za kuci Gidanku, Sirrikar tawa kuke ma iyashege?" daria suka sakeyi. Mama tace "Af! Labeeba ba dai kin fito ba" ta dan k'araso garesu cikin takunta tace "Wallahi Mama gwara na tafi, Marece yayi" Mama tace "eh Gaskia ne".
Dukkansu Maza Ukun idanuwansu suka zuba ma Labeeba, idanuwa taji a kanta, ta dan dago ta kallesu su ukun a lokaci daya tace "Ina wuninku? Kunzo lafiya?" amsawa sukayi a tare suna kallonta sosai, Aisha tace "Besty, wadannan sune yanuwana rabin Jikina, kika tsaga tsokata Jininsu kawai zaki gani".
Dariya Labeeba keyi wanda ke k'ara ma fuskarta kyau, ta cigaba da sauraron Aisha, "ga Yaya AbdulHafiz ga Yaya Abdulmajeed kuma ga Yaya Jawad, yau yau dinnan suka zo daga Abuja don Sada zumunci" wani murmushin ta sakeyi, tace "Barkanku da zuwa Katsina ta dikko Ya Abdulhafiz Ya Abdulmajeed da Yaya Abdul-" ta dan yi shiru tana son tuno sunan gudan, wanda suka kurawa junansu ido shi da ita, murmshi ya mata ya girgiza kai yayi yace "ba Yaya Abdul bane, Yaya Jawad ne" kamar bitar karatu ta maimaita "Yaya Jawad".
Aisha ta katsesu tace "Brothers, ga Besty ta, Labiba Ahmad" a tare sukace "Labiba" Mama ta dan murmusa tace "cikinku wa zan ba Diyata?" ta fada tana dafa Labibar da tayi saurin sadda kai k'asa".
Yaya Abdulmajeed yayi karaf yace "Ni zaki ba Antisco, Yaya Hafiz na da Mata, dama nine online, kinga sai in hada da Aminiyarta na aure, kinga no kishi".
Aisha ta harareshi, tace "sai me don na hada Miji da Besty ai ba wani abu bane, ba dai kai bane Mijin"
Dariya Ya Majeed yayi yace "to ni nace ke na ke nufi ne? Nidai Antisco ina so" Mama ta yi Daria, ta maida dubanta ga wanda take ma Labiba kwadayi tace "Jawad fa?" murmushi kawai yayi da ya sake kallon Labiba.
Ya Hafiz yace "nifa bangane ina da Mata ba, don ina da Mata sai aka ce ba zan iya sake ta biyu ba?".
Antisco tayi daria tace "to zan raba gardama, kuzo ayi tseren gudu, wanda ya riga zuwa bakin Gate, shi zan ba damar daidaitawa da Diyata Labiba".
Kafin ta rufe baki tuni Jawad ya ruga a guje ya isa bakin gate daria suka sa baki dayansu, Abdulmajeed yace "Cheating! Ni fa Mancy ban shirya ba, gaskia a sake" Mama tace "Wani ya hanaka shiri da wuri? Ni Jawad na ba dama" Ya Majeed ya cubune fuska yace "dama Antisco na lura kin fi san Jawad" Daria suka sa baki daya.
Labiba tayi saurin katsetsu da cewa "barin tafi, yamma na k'arayi" Mama tace "ki tsaya su Jawad su sauke ki sai Aisha ta raka ki" Labiba tace "Baban Amira Zaiyi fada, bari dai in samu Keke Napep" duk sai ta burgesu duka.
Mama tace "Gaskia ne, to besty mungode, mungode Allah saka da Alheri, ki gaida Aunty Aseeyar da yaranta" Labiba tayi murmushi jin sunan da Mama ta kirata dashi wai 'Besty' tace "sai anjimanku" tayi Gaba Aisha ta bita a baya.
"Nidai Antisco wallahi tayi min ina so" Jawad ke fadin maganar nan, Antisco tace "dagaske Jawad?" "wallahi Antisco" Mama tace "maza je ka karbo numberta, gwara ta baka da hanunta" da dan gudugudu ya bi bayansu, har sun fita bakin gate, k'arasawa yayi gunsu yana dan haki, Aisha tace "Ya Jawad ya akayi ne kake gudu?" wani kallo me wuyar fassaruwa yabi Labiba dashi tare da cewa, "Zuciyata na biyo, zuciyata, ta tafi dashi" tafi Aisha tasa, ita kuma Labiba ta rufe fuskarta da hannu biyu.
Dan gefe Aisha ta tsaya don basu wuri su dan tautana.
Kallonta yake cikin ido, duk jarumta irin tata sai da ta kasa jure kallon, sadda kanta tayi k'asa, cike da shauk'i Jawad yace "Labee" da sauri ta dago ta kalleshi, jin sunan da ya kirata dashi, murmushi mai nuna jin dadi ta mishi.
"Ba zan tsayar da ke ba, Yamma nayi, ki bani numbernki DonAllah" "ka karba gurin Aisha" girgiza kai yayi da sauri yace "Haram, ke zaki bani da hannunki, in kuma hanani zakiyi shikenan" yayi fuskan tausayi kamar mai shirin kuka.
Dan daria tayi me k'ayatarwa tace "be maka kyau ba" ya dan kallota yace "mene?" tace "shagwabar mana" dan bubbuga k'afa ya fara yi kamar dan yaro, da sauri tace "Ya hakuri Baby kar ka tara min jama'a kawo wayar na sa ma".
"Baby,Wow, sunan da aka bani yayi dadi" da sauri ta girgiza kanta da hannuwanta bibbiyu kamar mai yin bye bye tace "ni fa ba wannan Babyn nake nufi ba, naga kana abun yara ne shiyasa na kiraka da Baby". Kafadunshi ya daga " Oho, nidai zan dauka a matsayin Dayan, yanzu dai gashi ki samin number" karba tayi ta sa Numberta.
Tsaida mata Keke Napep sukayi, Jawad ya bude mata k'ofa yace "kin k'i yarda na kaiki Gida ko?" murmushi tayi tace "Bye Ya Jawad" lumshe ido yayi ya bude "Good bye Labee" Aisha ta bude baki ganin yanda Bestynta da danuwanta suka shagala da aika wa junansu sak'onni, "Hello! An manta dani ko? To ina wurin besty?" Kunya ya sa Labeeba rufe fuska tana daria, ta umarta mai Keke Napep da su wuce.
***
5:45pm
Tuk'i Yaya Hafiz keyi cike da nutsuwa, sun fito daga Unguwar Alk'ali Gidan Kakarsu, zasu tafi su aje Sak'o kafin su wuce Masauki don Gobe zasu wuce Abuja.
Yaya Hafiz yace "Yauwa Majeed, kira Yaron Mancy mu biya mu kai mai sak'on nan don ni gaskia nagaji ni da fita sai gobe".
AbdulMajid ya ciro wayarshi daga Aljihu ya latso numbern da Mancy ta bashi, har wayar ta katse ba a dauka ba, sake dialing yayi nan ma ba answer.
"Ba ya dauka fa" cewar Majeed, Hafiz yace "Kira Mancy ka gaya mata" dialing Numbern Mancy din yayi ringing na biyu ta dauka.
"Assalam Majeed" ta fada cike da Murna, "Hello Mancy ina wuni, dama mun ta kiranshi dan mu bashi sak'on be dauka ba" "Oh Allah, sorry na wahalar daku, ko ku barshi" Majeed yace "haba Mancy, har muzo gari kuma mu juyo da sak'o? Ba wani abu bari na sake kira InshaAllah zamu sameshi".
"Nagode sosai, bari nima in kira k'anwarshi in ba ya nan sai ta amsa" nan suka katse wayar.
Tudun Matawallen suka nufa kamar yanda Mancy ta gaya musu.
Majeed be fasa trying numbern shi ba, Jawad har ya k'ulu, shi fa be son bacin lokaci, tsaki ya sake yi, shi ba Fan din Mancy bane, be kuma k'inta, kawai dai bata cikin 'yan kayanshi kamar yanda yayyunshi biyu ke yinta.
Sun fi minti 10 a cikin Tudun Matawalle basu san inda zasu ba, sake kiran Mancy Majeed yayi tace "kuyi hakuri, wallahi wayar k'anwar tashi kashe take, na kuma ta kiranshi be dauka ba wallahi, kuyi tafiarku kawai Majeed".
"To Mancy ya sunan Maigidan sai muyi sallama mu bada a ajiye musu" dan jim tayi na wasu sakwanni kafin tace "kawai Majeed ku dawo ba wani abu" ba ya so ya matsa sai cewa yayi "to Mancy, amma banji dadi ba" ya kashe wayar ya ce masu "tace a bari kawai, amma banji dadi ba wallahi".
A k'ufule Jawad yace " to ya zamuyi, nan zamu lallace? Ya Hafiz mu tafi please" ta Mirror Hafiz ya kalli k'aninshi da harara yace "Jawad!!!" kawar da kai yayi, Hafiz yace "Majeed sake kira" Majeed yace "for the 14th time, Allah ka sa ya dauka".
Bencin Eskaley
World DanMakaho ya zuk'a, sarauta ta sa mai, k'afa daya kan daya ya daura, yana kallon kowa a dage, me tsautsayi kawai zai shiga harkanshi yau, yanda yake jin kanshi tsaf zai kakarya mutum.
Master da su Haruna ke buga Whot, suna yi suna busar sigari, yau ma basu da arzikin siyan World,sunyi ma Eskaley Magiya amma fir ya k'i basu".
"Wai Mankas ba wayarka ke k'ara ba tun dazun, kusan so 10?" Haruna yace "yo ina zai iya dauka, World fa ya ta6a" Master yace "yo in baka dauka ka kashe shegia mana, ni nan ta cikan kunne"
Tsaki Eskaley ya buga ya mik'e ya nufa Mankas hannu ya sa a Aljihun gaba inda Wayar ke k'ara, dauka yayi kafin ya amsa da "Hello?".
"Eh Hello, Zaid?" daga bangaren Eskaley yace "Eh to ba Zaid din bane" daga dayan bangaren a ka ce "DonAllah gamu a Tudun Matawalle, sak'o aka bamu daga Abuja mu kawo ma Zaid, don Allah ina zamu sameshi?" Eskaley yace "kuna ta ina?" "mun dan shiga cikin Anguwar" "Ayya, ku dawo farkon Anguwar, akwai wani kiosk nan Yellow".
Eskaley ya kalli su Master yace "Daga Abuja aka aiko wasu gun Mankas, gashi Mankas na birnin Sin ya zaayi?" Master yace "to ya fa? Uban kowa ya san Mankas na eh ya ne".
Horn sukaji na wani mota bak'a k'irar 507, duk suka tashi don yau kakarsu ta yanke sak'a.
Wayar Mankas ta sake ringingin Eskaleh ya dauka " Hello? Kaine a bakar Mota? Eh nan ne, barin zo" Eskaley yayi gaba, su Master na binshi a baya.
Ta Window suke kallon masu tunakaro su, "'Yan Shaye-Shaye ne" cewar Jawad "Mai ya hada yaron Mancy da Shaye-Shaye?" inji Hafiz, ba su da wannan amsar illa fitowa da sukayi gabaki dayansu.
Musabaha sukayi da dukkansu harda Jawad da ya mik'a musu hannu a kyamace, su ko 'yan bencin Eskaley kamar su musu Sujjada don biyayya, Hafiz ya kallesu daya bayan daya, ya lura duk ba na kirki cikinsu, duk warin Sigari suke, daurewa dai yayi magana yace "Ina Zaid?" Master da Haruna suka kalli juna suna tunanin waye Zaid? Shaf sun manta da wani Zaid".
Kafin Master yace "au Mankas? Gashi chan baya, in sak'o ne ku kawo a bashi" Majeed yace "Aa, hannu da hannu zamu bashi" Haruna yace "Ai Mankas ya hau network, ba zai gane bayanin da zaku mishi ba, mune Aminnanshi".
" DanUwarku Mahaukaci ne ni da ba zan gane bayani ba?" gabaki dayansu suka juya, Mankas ne ke tunkaro su, tuni Master da Haruna suka matsa mai ya k'araso yana k'are musu kallo duk a dage, ya tsaya kan Jawad mai kallonshi a k'yamace, Mankas ya wurga mishi mugun kallo shima kafin ya kalli su Master yace Duk ku ware?".
Hafiz ya mik'a mishi hannu, k'in amsa yayi, ran Jawad ya mugun baci, Majeed yace "Zaid, Mancy ce ta bamu sak'o mu baka".
Runtse ido yayi da k'arfi ya bude, tuni ya dawo hayyacinsa, Hafiz ya nufa da sauri ya dan durkusa " DonAllaj kayi hak'uri babban Yaya kuyi hakuri, wallahi akasi aka samu" daga yanda yake magana sun san a buge yake, yana dai k'okari ya dawo hayyacinsa ne.
Hafiz ya girgiza kai yace "Zaid, Mancy Mutuniyar kirki ce, donAllah ka bar Shaye-Shaye" da sauri Zaid yace "Wallahi na bari, ba zan k'ara dama yau na fara" sun san ba gaskia ya fada ba amma dai suka share" Majeed ya bude Booth ya dauko Ghana MustGo dan k'arami ya mik'a mishi.
Karba yayi, yace "nagode, Allah tsareku, ko uban wa ya tabaku ku gayan naci uwar mutum, duk garin Katsina, ko da kuwa Sarkin Katsina ne".
Takaici ya sa Jawad saurin fadawa Mota, Majeed ya girgiza kai yana mai fatan shiriya, shiko Hafiz da yake Ustazu ne sai da ya sake masu Mankas da abokanshi nasiha kan su bar Shaye-Shaye.
Nan suka fara mishi rantsuwar kaffara kan sun daina ba za su sake ba. Master har yana k'arawa da cewa dama don rashin abun yi ne ya sa suke Shaye-Shaye. Hafiz kudi ya ciro kusan 10k ya basu.
Master yayi wuf ya amshe tare da zuba Godia kamar zasu goyasu. Addua suka dinga zuba musu har Hafiz ya shige Mota ya ja suna mishi byebye.
Mankas be tsaya bin ta kudin da aka basu ba ya dauki ghanar nan ya danna a guje yayi Gida kamar wani zararre.
Su ko su Master yau take Sallah, World suka siya kowa qulli biyar biyar.
Washegari
5/05/2013
Tashi sukayi yau ba ruwa a Gidan, Drums dinsu empty, dama da k'yar suka samu Ruwan Alwala da Asuba, ko ruwan da zasu dafa suyi kalaci basu dashi.
"Oh ni Labiba ya zamuyi? Gashi Baban Amira bacci yake yi balle yaje nemo mai ruwa, bansan tadashi wallahi" Labiba tace "to Aunty Aseeyah ko in fita inga in zan samu mai Ruwan?" dan shiru tayi tace "Oh, ko zaki dan lek'a Gidan Alhaji Zaki ki samo mana a Kettle? Naga su borehole garesu".
Ba tare da wani tunani ba tace "eh wallahi barin shiga, ina zuwa" da sauri ta fita.
Aunty Asee mamakin Labiba take kawai ta ga fuskarta da walwalwa daga cewa taje Gidan Alhaji Zaki debo ruwa.
Maimakon Kettle wani Plastic Bucket na fenti taga ta dauko.
"Aa Labiba, ina zaki iya daukan wannan Bokitin, ki dibo a Kettle din zai isa kafin Yayanki ya tashi, ya nemo mai ruwa". Da murmushi tace "Anty Aseeyah kar ki damu, zan debo daidai ni" bata tsaya jin me zatace ba, tafita da sauri tana jin wani annashuwa a tattare da ita burinta daya, Allah ya sa ta Hadu da DanMakaho.
**
Tun jiya da ya kwanta bayan Maghrib be farka ba sai yanzu, fitowa yayi don ruwa be zuwa a toilet dinshi, Alwala zaiyi ya hade sallah tun Maghrib din jiya zuwa Asubar yau.
Fitowa yayi zuwa Babban Tankin Gida.
"Hajia masu Gidan bacci suke, nikuma banda hurumin barin ki diban ruwa, aikina Gadi kawai".
"Yauwa ga DanMakaho nan" karasowa yayi gunshi yace ya akayi ne Manu?" yauwa wannan yarinyar Gidan Baban Amira take, ruwa suke so a tsammasu" juyawa yayi ga Labiba da ta shagala tana kallonshi, da kannennen idonshi ya kallota yace "ki shigo ki diba, Manu barta ta diba".
Kamar sakara ta bi bayan dan Makaho har bakin Tank din gidan, karban Bucket din Labiba yayi ya tara a Fampo ya bude fampon, hankalin Labiba na gun karantarshi,
fari ne, amma wahalar rayuwa ta maida Fuskarshi bak'i, bayan hannunshi da dan haske amma tafin hannun da duhu, bakinshi ma yayi duhu, ganin kallon k'urillan da Labiba ke mishi ya sashi cewa " Chanjinki na nan, in na chanza zan kawo miki".
Wani irin kallon da be san na meye ba take binshi dashi, ji yayu ta fara magana tace "Meyasa?" dan kallonta yayi da kannenen ido me kama da bacci yace "Meyasa sai nayi chanji zan baki chanjinki?".
Da sauri ta girgiza kai tace "Meyasa baka iya kare kanka? Meyasa kake tsayawa ana daura maka laifin da ba naka ba? Meyasa kake daukan laifin wasu? Duk a zatona DanMakaho nakasasshene da ba zai iya tabuka ma kanshi komai ba, a zatona Dan Makaho bai da karfi da ikon kare kanshi, ashe ba haka bane, ashe kawai Dan Makaho Matsoraci ne, ashe dan Makaho ba zai iya tsayawa garkuwa ma k'anwarshi ba" baki bude yake kallonta cike da dumbin mamaki.
"Yanzu ba lokacin bude baki bane ka kalleni kamar Photo, ina jinka jiya da aka ce ka dauka naira dubu dayan da na baka, ba sai ka min k'arya ba, na san baka da ko sisi, ina kuma ji ranar da akace kana iskanci da k'anwarka, ina son sanin dalilin da ya sa baka iya kare kanka".
Da k'yar yace "Wacece ke?"
••••••
Yay!!! Late night post
Afuwan
Dont forget to vote and comment line by line
#1love
#DM
#anatare
#FWA
#SonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Biyar (RUWAN SAMA)
Barka da Sallah Bibilicious freaking fans, da fatan anyi Sallah Lafia? Allahu ya maimaita mana na badin badada.
Okay, please, before you start reading Vote first, number of Votes na decreasing, ku bani barka da Sallah ta hanyar voting kafin karatu Nagode.
"Dan Makaho ba tambayar da zaka min ba kenan, ka gaya min mene dalilin da ya sa ba ka iya kare kanka?" shiru yayi be da niyyar amsata.
"ba fa shiru zaka min ba, amsa nake so ka bani, meyasa kake daukar laifin da ba naka ba?"
Hannu ya sa ya shafi sumar kanshi "first of all ki daina min magana kamar wata uwata, secondly ba zaki ta6a ganewa ba, everything is beyond your expectations (komai ya zarce zatonki)" wani kallon mamaki take bin shi da shi, turancinshi mai kyau ne kalar na turawa.
Mamaki ya gani a fuskarta "Oh wow! kallon jakki, dak'ik'i kike min. I'm a Graduate Miss, thank you very much for asking, in kinaso zo in daura miki ruwan a kai, in ba kya so kuma sauri nake Sallah zanyi".
Bata gama mamakin da yace shi Graduate ba ne kuma taji wai Sallah zaiyi da mamaki tace "Asuba?" ba tare da jin komai ba yace "da Maghrib da Isha'i ba".
"Auzubillahi, haba Dan Makaho, me kake yi haka da ya hanaka Sallah? Me kakeyi da ka tara Sallah haka? Kai banji dadi ba wallahi, ka bari bana so" fada ta fara mishi sosai.
Cike da Mamaki ya dubeta kafin yace "To Hajia Maryam, zaa bari". Kallonshi ta danyi tace "wacece Hajia Maryam? Ni sunana Labiba?".
"To ai naga kin tasani gaba kina ta min fada, in ba uwata ba, ba uwar da ta isa ta tasani gaba tana min fada, kuma ni bandamu da sanin sunanki ba, kuma ki daina labe kina jin gulma, duk randa kika sake tsareni kika titsitseyeni da tambaya sai naci Uwarki".
Ya dauki Bokitinshi yayi gaba ya barta tsaye cike da mamakinshi, dan bude murya tayi yanda zai jiyota tace "ai dai ban tsoronka, zamu sake haduwa kuma" ba tare da ya juyo ba yace "aiko zakici Uwarki".
Da sanyayyar guiwanta ta dauki handle din bokitinta ta fita guiwa a sage.
Tana shiga Gida ta diba ruwan a tukunya ta kunna Risho.
Aunty Asee na lura da ita, yanayinta ya chanza, ba kamar da ta fita ba "Labiba? Wulakanci suka miki halan?" da k'yar ta girgiza kanta, tace "kai na ke dan ciwo" "ki shiga ki dan kwanta zai bari" kamar jira take ta fada daki, ta zube kan Gado kafin ta mik'e zumbur ta zauna.
K'wak'walwarta ta shiga tana sak'a da warwara.
Gidan Alhaji Ali Zaki Babban Gida ne, duk Anguwar ba Gidan da ya kai Gidanshi Girma da kyau.
Zaid na da k'anwa Sadiya? To ina Mamarsu? Ko ta rabu da Alhaji Ali ko kuma ta rasu.
Tabbas Hajia Shafa Matar Ubansu ce? Sauran muryoyin da take ji kuma na yaranta ne, ta san 'yan uba da matar uba, don ta na dasu, Gidansu gidan yawa ne, amma tsakani ga Allah ba sa irin zaman Gidan Alh Zaki.
To shi DanMakaho tunda Iliminshi meyasa ba zai nemi aiki ba? Meyasa yake shaye-shaye? Meyasa ya bata rayuwarshi haka?.
A baiyane tace "Ya Rabb! Ina son sani, nasan ba hurumina bane, amma ina son sani" Wayarta ne ya katse mata tunanin da takeyi.
Jawad ne, murmushi ya dan su6uce mata kafin ta dauka da Sallama.
"Labee nah, ina son ganinki kafin na koma Abuja" abunda ya fara ce mata kenan.
Murmushi ta saki mai laushi kamar tana gabanshi, kafin tace "Ina kwana? Ka tashi lafiya?".
Da sauri ya katseta "Wallahi ba Lafia ba, ina ta tunaninki, let me see you please".
Sausauta murya tayi tace "kayi hakuri, ni bansan me zance ma Baban Ameerah ba, amma nan gaba zan mishi maganarka, sai kazo Gida ko?".
Jim ya danyi kafin yace "Alright, Zamu biya ta Gidansu k'awarki kafin mu dau hanya, i will call you later, Ina Sonki Labiba".
Bata taba sanin ana shiga irin wannan yanayin ba, ba ta taba saurayi ba, da yawa nace mata suna Sonta, ba ta taba samun kalaman da sukayi tasiri a zuciyarta ba kamar na Jawad, Ina Sonki Labiba.
Maganar ta sake dawo mata katseta yayi "kinyi Shiru" tace "to me zan ce?" "kice kema kina So na" murmushi tayi tace "ka cika shagwaba, kai dan Auta ne?" yace "Ehmana, ashe ana ganewa, OK gotta go, zan kiraki in na isa Abuja".
"Allah ya tsare ya kaiku lafiya" ya amsa mata da Ameen.
Gab da zasu katse wayar.
Yace "Labiba, a hankali zan koya miki So na, I love you".
Kaste wayar sukayi, Ruf da ciki ta kwanta, wani irin yanayi ta shiga, wannan ne yanayin da ma'abota soyayya ke shiga? Wannan ne yanayin da ke ta6a zuciya. Pillow ta janyo ta rungume a k'irjinta tare da lumshe ido,
Mantawa tayi da duk wani abu, ta manta da komai, har DanMakaho, ba abunda zuciyarta ke aiyana mata sai JAWAD.
Shin Son so ne?.
Jawad da Yayyinsa sai da suka biya Gidan Kakarsu, kafin sukaje Gidan k'anin Babansu suka musu sallama. Jawad ya sake jadadda ma Aisha son da yake ma Labiba don ta kafa mishi Fada a wurin kawarta, yayi alk'awarin dawowa ba da dadewa ba, daga Gidansu Aisha ba su tsaya ko ina ba sai a Shagalinku Restaurant dake Zaria sukaci Abinci sukayi Sallah kafin suka sake daukan hanyar Abuja.
ABUJA
Da Marece suka iso Garin Abuja, Gidansu da ke Garki suka nufa, a tare suka fito daga Motar, Autarsu Mimi ta hangosu, da gudu ta kwasa ta na musu Oyoyo, AbdulMajeed ya dagata sama yana chafewa, Jawad shafa kanta yayi kawai ya shige ciki ya barsu, yarinya ce 'yar shekara uku, amma akwai surutu da shiga rai, cikin muryarta tace "Yaya Ina kukaje? Mancy tace kunje Katsina, ni meyasa bakuje dani ba?" Abdulhafiz yace "Sorry Mimi, da mu ka fita bacci kikeyi next time OK?" gyada kai kawai tayi.
A jikin AbdulMajeed suka k'arasa cikin gidan. A main Parlor duka zube, sai ga Jawad ya fito daga wani Daki, Mahaifiyarsu na biye dasu, bakinta har kunne saboda murmushi. "Sannunku da zuwa Boys" a tare suka gaisheta da "mun same ku lafiya Hajia? Ya gidan" da murmushi ta amsa musu da "Lafiya lau, ya mutanen KT?" suka amsa mata, tayin abinci ta musu.
AbdulHafiz ya mik'e yace "bari dai na k'arasa Gida Hajiya, Ummita ta min Waina" Hajia tace "to ba matsala ka gaidasu, muje na rakaka ma" ta k'arasa gunshi tana dan turashi kamar mai gudun kar yaga wani abu ko kuma kar ya tsaya yin wani abu, ranta ne ya dan sosu da taji yace "bari na Gaisheda Mancy" AbdulMajeed ma yace "Mimi sauka muje mu gaida Mancy" yarinya ta k'i sauka, haka ya dauketa a jikinshi, ya bi bayan yayanshi suka wuce Hajiyarsu da Jawad da je tsaye suka nufa hanyar dakin Mancy.
Abunda bata so kenan, abunda take gudu kenan, bata so yaranta suna ba Kishiyarta muhimmanci, suna nan tsaye sai ganin fitowarsu sukayi su duka har bakunansu na motsi da alamu wani abun ta basu, ranta ya baci, don me suka maida zuwa gaishe da kishiyarta Wajibi, itace Uwarsu ba Mancy ba, amma don me zasu dinga raba musu matsayi? Har suna cin abun hannunta?.
Muryan Mancy sukaji "Jawad, ashe an dawo, ya hanyan?" ba yabo ba fallasa yace "lafiya lau" tace 'Abdulhafiz, Allah ya huta gajia, a gaida Ummita, ke kuma zo nan ki bar Yaya Majeed yaje ya huta" Mimi ta mak'e kafada. Abdulhafiz ya musu sallama ya fita don tafiya Gidanshi, AbdulMajeed ya ba Mancy Mimi da k'yar shima ya wuce daki, Jawad ya ja Hajiyarshi suka shige daki, ita kuma Mancy ta ja hannun diyarta suka wuce daki.
Jawad ya zauna kusa da cinyar Mamanshi, ya na mai bata labarin Labiba, da irin son da yake mata, da kuma gaskia shi aurenta yake sonyi, Hajia Luba tayi mamaki matuk'a, ita ta san yaronta Miskili ne a wani fanni, ta san halinshi da kyale mutane, so da yawa kawayenta ke so su hadashi da 'yaransu amma fir yake nuna ba ya da raayi, tayi mamakin yanda ya furta da bakinshi kan cewa ya samu Mata.
Hajiya tace "to zan kira Antisco din na tambayi hallayar yarinyar" Jawad yace "to Hajia, bari ma na kira miki ita ku gaisa" Hajia tayi murmushi ganin zumudin Jawad.
KATSINA
Labiba ta lek'a dakin Yayanta inda matarshi ke kishingide tace "Aunty Asee barin je in siyo kati, duk yau bamuyi waya da su Mami ba" mik'ewa tayi "tace yauwa nima siyo min na dari" Labiba tace "to" fita tayi tana gyara zaman mayafinta.
Daidai da fitowarshi daga Gida, karaf suka hada idanuwa, dauke kai ya fara yi, ya fara tafiya, da sauri ta bi bayanshi tana fadin "DanMakaho Chanjina, zanyi amfani dasu" chak ya tsaya ya dan juyo, kafin yace "wai ba kince kin san Kudin be wurina ba? Ban dasu yanzu ban da dalilin samun su, na san inda kike, da na samu zan kawo miki har Gida"
Yana kai wa nan ya juya ya cigaba da tafiyarshi, dan jim tayi kafin tayi saurin binshi tana cewa "Dan Makaho, tsaya tsaya DonAllah" dan dakatawa yayi "ka rakani wurin siyan Kati, kaga dai shagon Oga kulle yake, dole sai chan Bencin Eskaley, kuma 'yan shayeshaye ke wurin, nikuma ban san zuwa, ka sansu ban so su ci mutunci na, ko su min magana bana son magana da su wallahi, ni tsoron su ma nakeji, donAllah ka rakani" ta k'arashe kamar me niyyan kuka.
Ya harzuk'a yace "wai ke don Uwarki me kika daukeni? Zan fa ci uwarki, zan babbala ki, ki fita harkana" fuskarta ya dan chanza amma murmushin be gushe da ga kan fuskarta ba tace "dazun da safe ka zagi Uwata so biyu, yanzu ka sake Zaginta, shin me ta maka? Ba ma fa ta sanka ba? Amma kake ta zaginta, don nace ka raka ni?".
jikinshi yayi dan sanyi, shafa kai yayi da hannu kafin yace "to ai duk cikin 'yan bencin Eskaley na fisu shaye-shayen don me zakice na rakaki, ba kya tunanin na miki wani mugun abun yanda kike shishige min haka?". Kallonshi tayi ta ga yanda yake kallonta da kannennen idonshi tace "I'm safe with you, na sani, in zaka rakani muje". Gaba tayi da sauri ya cin mata suna tafiya kafada-kafada ba mai ce ma wani komai har suka iso shagon Eskaley.
Tuni su Master da Haruna suka fara shewa "Shege Mankas, wo kai Mankas" Master yace "Yayar mu ina wuni, ya kwana biyu? A dan dari biyu inci abinci donAllah" Tero yace "amma wallahi kin hadu fa, kina da kyau, Labiba ta kawar da kanta kawai tana mai da na sanin zuwa shagon nan, ina ma yaro ta samu ta aikoshi nan, kamar tayi kuka, jin irin maganganun da suke mata.
"Zan ci uwarku ku ka sake mata magana, danuwarku kalarku ce? To danuwarku waninku ya sake cewa wani abu game da ita, zai kwana Asibiti billahilazi" Tero yace "Kai ji Mankas, yo kai ka shiga wurin sai ka hanamu shiga, indai ba kalarmu bace kaima ba kalarka bace, ai tunda muka ganta tare da kai, ai mun san 'yar hannu ce, Eskaley bata World, dan na san shi tazo saye, ba sai an tsaya mana wani kwane kwane ba, mun san kina Eh-Yaneh Malama".
Kafin Labiba ta gama gano inda Zancen Tero ya nufa, tuni DanMakaho ya kai Tero k'asa ya na kai mai nushi ko ta ina, ba wanda yayi yunk'urin rabasu don sun san halin Mankas, Labiba da tashin hankalin yayi yawa sai ta rasa me zatayi, tana waigawa inda zata ga jama'a don a samu mai rabasu, kowa harkan gabanshi yake , sai da Mankas ya ma Terro Ha6o kafin ya barshi, ya tashi ya nuna su da yatsa yace "duk daniskan da ya sake mata magana sai na ci uwarshi" fizge kudin hannun Labiba yayi yace "Eskaley bamu Kati" Tero ya mik'e a wahalce yace "Wallahi Mankas sai na rama, ko ba yau ba" Mankas yace "zo rama dan uwarka" ya nufoshi da gudu Tero ya bar gurin.
Be ko kalleta ba ya amshi Katin daga wurin Eskaley, gaba yayi ganin haka ya sa ta bishi a baya, sai da suka zo har k'ifar Gidajensu kafin ya mik'a mata katin, amsa tayi tace "Nagode, meyasa kayi Fada?" kallonta yayi ya kawar da kai, tace "Fada be kamace ka ba, be maka kyau ba, komai be maka kyau, ka bari donAllah " a fusace tace "Danuwarki bana ce ki bar shiga harkata ba" shiru tayi ta sadda kanta kasa, sai daga baya yayi laakari da zaginta da ya sakeyi.
Hannu ya sa ya murza idonshi na hagu, yace "kinga ke ke sa ina zaginki, kiyi hakuri, ki kyaleni, ki fita harkata" kallonshi take sosai kafin ta daura hannunta saitin k'irjinta tace "bansan menene ba, Zuciyana daidai nan, na min Zafi, bansan meyasa nake son saninka ba, ba son meyasa na damu da lamuranka ba, dagaske banson meyasa ba, amma dagaske Zuciyana na min Zafi, yana azazzala min, yana tafasa, zakayi mamakin don me ko? Nima mamakin nake, don me, so ka taimakeni, ka gaya min, ko zan samu sausauci".
Kafin yayi maganar Wayarta ta fara ruri, dubawa tayi taga Jawad ne, har ya katse bata dauka ba, ya sake kira DanMakaho yace "ki dau ka wayanki, zan sake ganinki, za kuma ki san ko Ni Waye, ban taba maganar nan da kowa ba, amma zanyi dake, ki shiga ciki, zamu sake Haduwa".
Da duk wata kalmar da ta fito bakinshi suka samu zama a Zuciyarta, samun kanta tayi da bun umurninshi, ba tare da ta ce mishi komai ba ta shige Gida tare da amsar Wayar Jawad.
"Haba Labee nah, ina kika aje waya ina ta kira?" dan guntun murmushi tayi "sorry na fita siyo Kati ne" "God, laifina ne, by the way, Hajiyata zaki gaisar" Dakinta ta fada, tace "Haba Jay, is too early" wani darian farinciki taji yayi, yace "Zamuyi maganan sunan da kika bani Anjima, amma ga Hajiar" kafin tace wani abu ya sadata da Hajiarshi.
Da Sallama ta amsa "Hello Assalam Alaikum" Labiba ta saki murmushi kamar tana gabanta "Ummanmu ina wuni?" dama a handsfree wayar take dadi ya kama Jawad, "Lafiya lau Labiba, ya kike ya su mamanku?" Labiba ta amsa mata, Umma ta tambayeta ya Makaranta, kafin ta mata addua sukayi Sallama.
"Ameen Ummanmu, Nagode Allah ya k'ara Girma ya kuma ja Kwana".
Labiba mai Farinjini tuni Umman Jawad taji ta na sonta sosai, tace "Jawad, Labiba wayayya ce, ba ruwanta" Jawad yace "sai ma kin ganta a fili" Umma ta kai mai dukan wasa tana cewa "wuce ka zubo abinci Ja'iri".
ALHAJI ABU SHAMSU
Asalinshi dan Garin Katsina ne, Alhaji Abu Shamsu na da k'ani daya rayyaye, sauran duk sun Rasu, Alhaji Abu Shamsu fitattacen dan Kasuwa ne mai zaman kanshi wanda ake damawa dashi a k'asa, Hajiya Lubabatu itace Uwargidanshi tun auren saurayi da budurwa, itama 'yar Katsinar ce, tun Abu Shamsu na 'yan buga-buganshi sukayi Aure har Allah ya mishi budi.
Alhaji Abu Shamsu da Hajiya Luba na da yara Uku, duk Maza, Abdulhafiz shine babba, sai AbdulMajeed sai auta a cikinsu Jawad.
Amaryar Alhaji Abu Shamsu wacce basu rufe Shekara 4 da aure ba Sunanta Hajia Maryam, diyarta daya Aminatu ana ce mata Mimi.
Wannan kenan
Ruwan Sama akeyi ba k'ak'autawa, tun k'arfe 10 dare, har wayewar Gari, da Asuba Baban Amira ya fito don yin Alwala don tafiya masallaci yin Sallahr Asuba, gabanshi ne ya fadi ganin bangon da ke tsakanin gidanshi da Alhaji Ali Zaki ya rushe, "Subhanallah, Inallillahi wa ina ilaihir rajiun" ya furta, da kyar ya daure ya shiga kewaye ya dan zagaya tare da yin alwala ya fita masallaci.
Bayan Sallahr Asuba suka hadu da Alhaji Ali Zaki, Baban Amira ya karasa wurinshi sukayi musabaha cikin mutuntawa.
Alhaji Ali yace "Mallam ya Iyali?" Baban Amira yace "Alhamdulilah, sai ga tsautsayi kuma" Alh Ali yace "Subhanallah, me ya auku?" be yi mamakin rashin sanin da yayi ba saboda bangon ta baya ne, ta inda Boysquaters yake, Baban Amira yace "jiya Ruwa yayi Gyara, Bangon da ke hade dade da Gidanka ne ya fadi".
Alhaji Ali yace "Subhanallah, IkonAllah, wallahi ban gani ba, ko don ban lek'a bayan ba, ta wurin DanMakaho ne kenan, InshaAllahu zaa gyara, bari gari ya waye" Baban Amira yayi Godia suka taho Gida tare, "ai Alhamdulilah tunda bangon be fado ma wani ba" "Ai don dare ne, amma wurin Iyalina suke shimfida don wurin akwai inuwa" Alhaji Ali yace "IkonAllah, Allah ya k'ara tsarewa"
A haka suka iso Gida, Baban Amira ya shigar dashi ta Gidanshi ya gani, suka sake jajantawa juna Alhaji Ali kuma ya tabbatar mishi da cewa da Safe zaiyi waya a siyo Bulo da k'asa da Siminti sai a gyara. Godia ya sakeyi kafin ya bi ta dan hanyar ya shige Gida.
Aunty Aseeyah haka ta tashi ta ga Ikon Allah, da mamaki, Baban Ameera ya mata bayani, ya kuma gaya mata yanda sukayi da Alhaji Ali, jinjina lamarin tayi kafin ta k'ara da Allah ya tsayar nan, dan tautaunawa sukayi, Baban Amiran ya yanke Shawaran su fita gabaki daya, sai ita Asiyar ta tafi Gidansu, in Yara sun tashi daga Makaranta sai a kaisu gidansu Aseeyar, Labiba
Sallah tayi ta shiga dakin Labiba da Yara, Labiba na fashin Sallah. Aunty Aseeya ta fara tada yaran don suyi shirin Makaranta yau Monday.
Labiba ta farka ta gaida Aunty Aseeyah, ta amsa tace "sai kika ga Bango ya fadi ko?" Wuf Labiba ta mik'e zaune tace " "Bango? Na ina? Inallillahi, ya akayi?" Aunty Aseeyah ta mata bayani, Labiba ta jajanta abun, Aunty Asiya tace "to yanzu dai k'ofar k'aura zamu yini, zuwa anjima InshaAllahu anyi gyaran. In kin tashi daga Makaranta ki wuce chan, yayanki yace zai gaya ma Mai Adaidaita sahun su Ameera da ya kaisu chan in sun tashi" Labiba tace "to shikenan Allah shi kyauta ya tsare".
Yara suka fara tafiya Makaranta, kafin Baban Amira ya fita Kasuwa, Aunty Aseeyah tace "karfe nawa kike da lectures?" Labiba tace "9 ne" "Ohh, na zata yanzu ne, bari na jiraki sai mu fita tare" Labiba tace "ki tafi kawai Aunty, in na gama sai na kulle Gidan ko?" sai da suka danyi mahawara kafin Aunty Aseeyah ta amince.
Itama 8 daidai ta shiga wanka, ta fito ta shirya cikin riga doguwar Riga Bak'a, Jan gyale medium ta sa ta yane kanta, ta kulle kofar Dakin, dama Aunty Asiya ta rufe Dakinta da Parlo da kitchen. K'ara saba jakkarta tayi ta yi hanyar fita, bata san dalilin juyawa ba, sai juyawa tayi ta hada Ido da k'ofar dakin da ke kallonta na Gidan Alhaji Zaki, kuma tana da tabbacin daya daga Ciki na DanMakaho ne,
Kila ko Sallahr Asuba beyi ba cewar zuciyarta, har tayi gaba, zuciyarta ta tunzurata da ta je ta kwankwasa mai, ya tashi yayi Sallah, samun kanta tayi da bin umurnin Zuciyarta, tsallake rusassun bulo din ta dinga yi har sai da ta dangana da Gidan Alh Ali Zaki, amsa kuwar zuciyarta take yi , duk da faduwan gaban da take jin zuciyarta nayi, bata fasa tafiya ba
har ta k'arasa gaban k'ofar dakin.
K'wank'wasawa tayi amma ba amsa, Zuciyarta na harbi da sauri sauri, gabanta na tsananta faduwa, ta lek'a ta window, kwance ta ganshi ruf da ciki.
Sake k'wankwasawa tayi, tare da murda handle din k'ofar.
"A bude take, k'ofar a bude take, ki shiga ki tadashi yayi Sallah" cewar Zuciyarta
Girgiza kai tayi tare da runste ido, amma zuciyarta na sake tunzurata.
Ki kiyaye mutuncinki Labiba, ki tsare mutuncinki, a kullum maganar Maminta kenan a duk lokacin da sukayi waya.
Ta san abunda take shirin yi is wrong, babu Macen arzik'in da zatayi hakan, ba Macen da zata shiga dakin Namiji Baligi ba Muharamminta ba, duk abunda ya faru da ita, ita ta jawa kanta, ita ta kai kanta, ko dakin Yayyinta Mahaifinta ya masu iyaka da shiga sashensu, balle wannan da ba zatayi shaidarshi a kan komai ba, bata san menene ke sa tana biyewa zuciyarta a 'yan kwanakin nan, ba halinta bane, amma bata san yanda zata tsayar da abun ba,
Bude k'ofar tayi tare da sa Kanta, tattaro Natsuwarta tayi kafin ta bubbuga kan Katifar da yake kwance tace "DAN MAKAHO"
Firgigit ya tashi, k'anannen idonshi ya dago ya kalleta da mamaki, kafin ya mik'e tsaye kyam yana binta da wani irin kallo, cikin Labiba ya bada k'ulululu, ta zabure zata ruga a guje, da sauri ya sha gabanta fuska daure yace "Ina kuma Zaki?".
Yayyyyyy people, Labiba ta kawo kanta fa.. Ba shi ya kirata ba, ita ta kawo kanta
Yau Mankas zai Angwance Rengyem
Me kuke tunanin zai faru?
Drop your thoughts here
Biko Vote Vote and Vote.
#1love
#DM
#SonSoFWA
#anatare
#nagode
Biebee Isa.
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Shidda (WACECE KE?)
Vote before reading please don ku kai karshe kun manta da wani zancen voting, just vote now. Thanks
"Saurin me kikeyi? Ina zaki ba wurina kika zo ba? To ina kuma Zaki? Ba so kike ki san ko ni waye ba, to yau ko zaki sanni, ba ke 'yar iska ba, kin san yanda ake zuwa dakin Namiji ko? Aiko zaki gaya musu, kwanta dan ubanki, yau sai na miki lagalaga" ya fada yana me yunk'urin tu6e riga don ya tsorata ta.
Runtse ido tayi cike da kidima, hawayenta su ka soma kwaranyowa, tana girgiza kai da k'yar ta lalubo kalmomin nan "ni Sallah na zo tadaka kayi, kuma wallahi ni ba 'yar iska bace".
Hanayenshi ya rungume a k'irjinshi, yana kallon yanda take rantsuwan ita ba 'yariska bace, iyakar gaskiyarta ya gano, daurewa yayi yace "yanzu in zagi uwarki kiji haushi, ni yaro ne da zakizo tadani yin Sallah? Bude ido tayi a tsorace, bata son ganinshi ba riga, amma da rigarshi.
Baki na rawa tace jiya fa naga sai daga garin Allah ya waye ka hada Salloli har Maghrib da Isha'i, shine nayi zaton ko bakayi ba, shine nace barin zo na tadaka ,ko zan samu lada, in ba haka ba, ba abunda zai kawo ni nan, saboda na damu da kai, ina so mu tsira tare ranar gobe k'iyama".
Kallonta sosai yake yana nazarinta, daga bisani yace " kin damu dani? Ni k'anin uwarki ne ko na ubanki?".
Kai ta girgiza tace "Aa, kai ba daya daga cikinsu bane, k'annen Mahaifana ba haka suke ba, kuma na lura Zagi kamar a jininka yake, na san na maka shishigi, ina kan maka shishigi a rayuwarka, amma ina rok'onka, wannan ya zama karo na k'arshe da zaka Zageni, kar ka k'ara zagina DanMakaho, babu mai ganin Mutuncinka a duk Unguwar nan, ni kam Ina ganin mutuncinka, inshort ni kadai ke ganin mutuncinka, so be kamata ace kana danno min Ashar ba" ta fada cike da sanyi, murmushi be kauce daga fuskarta ba.
DanMakaho ya kalleta sosai, yana mamaki, be taba sanin a Arewacin Nigeria akwai Mata masu Confidence irinta ba, be taba sanin akwai Matan da zasu iya expressing kansu kamarta ba a Katsina ba, yana mamakinta sosai.
Kallo ya bita dashi a hankali yace "WACECE KE"
Ta amsa mai da "Labiba Ahmad".
Ya Girgiza kai yace " Aa, wacece ke, kamar yanda kike son sanin Ni wanene haka nake so ki sanar dani ke wacece, sai na san ko ke wacece kafin zan iya sanar da ke ko ni waye".
Murmushi tayi tace "Makaranta zanje, nidai kaje kayi Sallahr Asuba".
Jim ya danyi, yace "Nayi" ta kalleshi da alamun rashin yarda, yace "ke ni fa bana k'arya, ba Bango ya fadi ba?nagani da Asuba". Murmushi ta sakar mai tace " tabbas kayi Sallah, to ni na tafi School".
Bai ce da ita komai ba, ta raba shi ta wuce, har ta kai bakin k'ofan ta dakata, zuciyarta na kitsa mata da ta tsaya suyi magana, opportunity ne ta samu, k'ila daga yau ba zata sake samun irin damar nan ba.
Dakata wa tayi ta juyo gareshi tace "lets talk Dan Makaho".
Ya dan waigo yana mamakin rashin tafiyarta yace " lectures din fa?".
Wuri ta samu daga gefe ta zauna, ta dago ta kalleshi, ta sakar mishi da murmushi tace "We are going to have our lectures here".
Bata jira yace komai ba ta fara magana;
Alhaji Ahmad Dakata
Alhaji Ahmad Dakata dan asalin k'asar Nijar ne, Maraya ne, baya da kowa, ya zo ya fara 'yan bugabuganshi a Garin Katsina, da yake yana kaifin basira da fasaha, nan ya fara shigeshige yana samun k'anannun kwangiloli.
Baiwa gareshi, yana da Ilimin Hak'a Rijiya da gina mugudanun ruwa, da ilimin Quantity surveyor amma be taba shiga Aji ba ma'ana beyi karatu ba, a shekaru da yawa a baya saboda kwarewarshi ya sa ake daukan shi gari gari don yin Aiki,
Da ya dan samu kudi yake zuwa Maradi gurin Tsohon da ya tashi a gidansa, a nan ne aka aura mishi Wata buzuwa Zaharau, marainiya ce itama, ya taho da ita Katsina.
Da Likafa ta cigaba mai, a ka dinga fita dashi garuruwa don yin kwangilar Tituna da Hak'on rijiyoyi, da janyo ruwa daga wani kauye zuwa babban Birni.
Babban kwangila ta sameshi inda zaiyi aikin kusan Shekara a Garin Edo Benin City da Zara'u ya tafi, lokacin tana da jaririn ciki, nan ya dan kama musu dan karamin Gida, ya hau aikinshi. Ganin aikinshi ba ha'inci, ya sa shi kafin ya gama wannan aikin ya samu wani aikin, haka zaman Edo ya kamashi, sai ya zama ya fara jin dadin Edo fiye da duk wani garin da yake zuwa, a nan ya kafa Iyalinshi.
Alhaji Ahmad Dakata Yana da Mata Biyu, Hajia Zahara'u, da Hajiya Jamila wacce ya aura bayan dawowanshi Edo kwatakwata, ko wacce da iya adaddin yaranta don Haihuwa suke MashaAllah.
Hajiya Zaharau itace UwarGida ta haifi yara Sha daya amma Uku ke da rai Mata 2 namiji daya , Yaya Muhammadu, Yaya Hajara, sai Auta Labiba daga kanta Mami kamar yanda suke ce ma Mahaifiyarsu bata sake haihuwa ba.
Hajiya Jamila itace Amaryar Alhaji Ahmad, Yaranta 7, 3Maza Yaya Aminu, Yaya Muntari, Mata Yaya Salisu, Yaya Fadime, Yaya Zaliha itace tsarar Yaya Hajara, sai Samira tsarar Labiba duk da ta girmi Labiba da 'yan watanni sai Auta Halisa.
Gidan Alhaji Ahmad kamar yawancin Gidaje ne Masu mata biyu maana mai Kishiyoyi, akwai kishi tsakaninsu, sa'anan akwai 'yanubancin.
Alhaji Ahmad yana tsayawa tsayin daka akan hade kawunan iyalanshi, amma abun da kamar wuya, a cikin kaso Dari, suna zaman lafiya kashi Tamannin, amma dai ana iya cewa na ciki na ciki, akwai ganin k'yashi da hassada musamman wanda 'yan wannan dakin ke ma wanchan.
Muhammad da Aminu suna da Shekaru 18 aka haifi Samira ba da dadewa ba aka haifi Labiba.
Sun taso kamar 'yan biyu, amma Labiba ta faye wayau, ganin tana da Wayau sosai, ga Shegen tambaya Muhammadu yayanta ya kwadaitu da son autar mamanshi ta shiga boko, don ba zai bari Babansu ya ma yarinya mai saurin daukan abu kamar Labiba abunda ya musu ba.
Alhaji Ahmad Dakata be damu da sanya yara a Makarantar Boko ba yana dai sanya su a Islamiya, in Namiji ne in ya kai shekara 10 yake fita dashi wurin aiki ya koya musu Aikinshi, in kuma Mace ce, da kin samu Miji zai maki aure, .
Daga Samira sai Labiba da Auta Halisa ne kawai basuyi aure ba, yawanci ba Hausawa suke aure ba, amma Maza kuwa daga Yaya Muhammad da Yaya Aminu wanda ke zaune cikin Gidan Alhaji Ahmad Dakata da matarshi.
%%%%%%
Da yaje wurin Baban da bukatar sanya kanannun yaran Makaranta, Baban fir yak'i, bayan Muhammadu ya kwantar da kai ya ma Baban bayani sosai kan Muhimmancin Karatu musamman ga 'ya Mace, sai suka tafka muhawara, daga k'arshe Baban ya amince. Aka sanye Labiba da Samira wani Private school.
Samira bata da passion din karatu, Labiba kuwa tana son k'aratu sosai, har suka gama Primary School. A lokacin ne Zamani ya fara dakushe tauraron Alhaji Ahmad Dakata, sai ya rage samun Kwangiloli, a nan ya Umurci yaranshi da su fita su samu Aikin hannun da zai ma kowannensu, ko wanne ya kama gabanshi, Muhammadu ne yayi Arewa a garin Katsina, yanemi izinin Babanshi da ya bashi hayar Gidan da yake Katsina zai zauna Baban yace yaje dai ya zauna in ya mutu a sa Gidan a Gado. hakan kuwa akayi amma hakan ya taba zuciyar yan uba. Muhammad ya tafi katsina da ya fara 'yan bugabuga, ko shekara baayi ba da zamanshi Katsina, ya samu mata ya aura a Katsina, har Allah ya sa mishi Albarka a kasuwancinshi ya bude dan madaidaicin Provision store a Kasuwa.
Samira ta tsani karatu, daga JSCE tayi ta zillewa bata son karatun, Mamanta ta biye mata, shi kuma Alhaji Dakata tunda be da damuwa kan Karatun boko, be matsa mata ba.
Amma Labiba ta dage da bada himma a karatunta ta shiga Senior Secondary School. Labiba ta ke kutsawa cikin 'Yayan kudun nan ta dau ilimi, bata fiye k'awaye Mata ba saboda gulma da fada, yawancin abokanta Maza ne kuma Kiristoci, don Musulmai basu fiye yawa ba, a nan ne ta koyi tambaya akan komai, ta iya mu'amala da kowa, tun tana primary ake fita Debate da ita, bata jin komai Magana gaban dubannin mutane, ba kuma ta kunyar tambaya.
Labiba tafi so ta sanya dogon Wando budadde, da rigar da ta wuce mazaunanta, tana da burin zaman Injiniya saboda duk abokanta Maza da tunanin zama Engineer suka tashi, duk tunanint irin na Maza ne amma ko so daya bata taba tunanin kwace hanyarta ba, tana da ilimin addini, bata wuce gona da iri ta fanin nan, ko hannu namiji ya bata sai ta galla mishi harara.
Wayon Labiba ya girmi shekarunta, shiyasa take samun laifi da Mama kamar yanda suke cema Mamansu Samira, Mama tana son lak'afa mata sharri, ita kuma in ta san batayi abu ba, ba zata taba amincewa ba, ko me zaa mata.
A lokacin da ta gama Secondary School Samari suka mata chaaa, ba sa gabanta, in sun zo zata fita ta sha hira dasu, amma kar take gaya musu ba wanda zata aura cikinsu, burinta dai tayi karatu ta zama Injiniya, in har suna sonta su jirata in ta zama Injiniya zata dawo, sai ko wannensu ya gwada bajintarshi, a hakan ta samu suke shafa mata lafia .
Result sun fito, duk sunyi kyau, ta kira yayanta Muhammad ta na kuka sosai kamar ranta zai fita, ta nuna mai tana son cigabawa da Makaranta amma tasan Babansu ba zai taba bari ba. Yayan ya kwantar mata da hankali ya shaida mata zaizo k'arshen Wata..
Bata gaya ma kowa ba burin son cigabawa da karatu, harta Maminta bata sani ba, sai da Yaya Muhammad yazo da Iyalanshi, Aunty Asiya da Ameera da Sabit, murna wurin su baa magana don sai sufi shekara 3 ba suzo Edo ba sai dai waya,
Aunty Asiya na san Mami don bata surukkuta da ita, tana son k'annen Mijinta, Labiban ma na sonta, da ta shiga gaida Mama, a dage ta amsa, gani take kamae Muhammad yafi yaranta kudi da arziki.
A lokacin da Muhammad ya shiga da bukatar son Labiba ta cigaba da karatu, ran Baban ya baci, yace shi aure zai musu karatun da tayi a baya Allah ya amfana. A nan ma wata Muhawarar suka sake tafkawa amma Baban yace shi sam Diyarshi ba zatayi Jami'ar Edo ba, ba zatayi karatun gaba da Secondary cikin Arna ba, muma shi tsakani ga Allah aure yake son musu, ya lura kan Labiba na rawa, wai rannan nan har tistitsiyeshi tayi da tambaya don me be sa sauran yaranshi Makaranta ba.
Muhammad dariya yayi, yace in zai yarda zai tafi da ita Katsina ya sanyata a Polytechnic, kuma ya mishi Alkawari da ta samu Miji, zai dawo da ita a mata Aure da k'yar Baban ya yarda, tara su yayi gabaki daya ya shaida musu hukuncin da ya yanke, nan Mama ta fara jin zafi, tace "Haba Alhaji, anya kuwa? Duk cikin 'ya'yanka, Maza da Mata, ba wanda ya taba karatu sai Labiba yanzu kuma kace zaka kaita wani gari tayi karatun Jami'ah? Ina guje maka dana sani Alhaji, Wallahi AbdulFatah ya nuna ya na sonta, gwara ka mata aure".
Labiba tace "Allah ya sauwak'e in auri mai shan taba, ki aura mishi Samira" Mami ta wurgeta da harara, Samira tace "Kinga Labiba Mama na ba tsaranki bane, wallahi ki daina maida mata magana in tayi" Alhaji Dakata yace "to nidai na amince Muhammad ka tafi da Labiba, amma idan Labiba ta kwaso abun kunya, ko tayi wani abun da zai kunyatani a idanun jama'a, to ba ruwana da kai da ita da Mahaifiyarku" Mami ta kalleshi cikin tashin hankali, Labiba kuwa ko a jikinta dom ta san ba zata taba basu kunya ba, dadi ya rufeta tace "Niko wallahi sai na baka Mamaki Abbah, zan zama abun alfaharinku, da Allah, ba zakayi dana sani ba, Mami karki damu, wallahi karatu kawai zani Katsina, sai na kula muku da jikokinku" wasu sukayi dariya wasu ko sukayi fuska.
Hakan kuwa akayi, Muhammad ya koma Katsina ya mata Appying HUK poly, don bin sharrudan uban, tunda Diploma Shekara 2ce, kuma akwai sharadin in ta samu Miji za tayi aure. Labiba na daga cikin wanda aka dauka da farko, saboda ko Jamb dinta Mark din yan jami'ah ne, ya gama mata preparation nan da wata biyu zata zo katsina fara lectures.
Abbansu ya kirata daki, ya mata nasiha sosai, ya bata kudi Naira dubu ashirin yace kuma InshaAllahu zai dinga turo mata ko da dubu uku ne duk wata, godia tayi sosai, ta rungume Abbanta.
Maminta ta ki rata daki tace "Na zauna a Katsina shekaru da yawa, na san yanda suke, yanda suke ma'amala da mutane ya sha bamban da yanda mukeyi a nan, baki taba barin Edo ba, Arewa zaki Labiba, dole ki koma halaiyar 'yan Arewa, kije kasuwa ki dinko atamfa da ankara, ki dinga shigan Hausawan usul, ba zasu miki uzurin ba a chan kika taso ba, zasu miki fassara in kikayi wani dabi'ar da ba tasu ba, ke ke son Karatu, dole ki zama irinsu ba zan so ki fito da wani penti duk kankantashi ba, kingane? Labiba ta gyada kai, Mahaifiyarta ta dade ta na mata nasiha kan kare Mutuncinta.
Tana son karatu, tana son fidda mahaifiyarta kunya, zatayi komai don ganin ta cimma burinta, ta shiga kasuwa ta siyo manyan gyaluluwa da atamfofi, ta dinka su. Lokacin zuwa Katsina Yaya Muhammad ya zo da kanshi don tafiya da ita, kowa na alhinin tafiyar Labiba, don tana da shiga rai, harta Samira da ba sa shiri tayi kukan rabuwa da ita, haka suka ma Edo Sallam suka taho Katsina ta dikko dakin Kara.
Gidan Yaya Muhammad dakuna biyu ne sai Parlo, da kitchen da toilet a waje, k'aramin Gida ne, Dakinta Aunty Asiya ta bar mata da Amira babban diyan Yaya Muhammad, ita kuma Aunty Asiya da Sabit suka koma dakin Yaya Muhammad.
Yaya Muhammad ya raka Labiba Registeration ba wai don ya san yanda ake ba, Sati guda ya kashe yana kaita Makaranta, ta hanyar bin School Bus, ya kuma koma ya daukota, ce mishi tayi ya bari hakan nan, ta gane hanya, zata iya zuwa ta dawo da kanta, a sati na biyu ne ta fara zuwa da kanta a lokacin har tayi k'awa Aisha Usman.
Wannan kenan.
Zaid ya gama jinta lokacin da ta gama bashi tak'aiceccen labarinta da murmushi dauke a fuskanta, kallon da yake binta da shi ne ya sa tace "ya akayi ne?" mur Zaid ya sha "are you stupid?" kallon mamaki ta mai tace "me ya faru?".
Hannu ya sa ya murza idonshi "wai ke lafiyar ki lau? Alk'awarin da kika daukar ma Maminki kenan? Don me zaki shigo dakina? Kare mutuncin kenan? Kinsanni ne? Yanzu in na danne ki, na miki abunda ba kya zato, me zakice mata? Kin san me kikayi risking? Farincikin ki, na Yayanki, na Mahaifiyarki wanda barazana ne ga aurenta, to kinyi risking kin shigo dakina, for what? Is it worth it?".
Labiba tayi shiru "nasan ban yi daidai ba, but kamar yanda nace ma, wallahi kamar ana controlling dina, bansan meyasa when it comes to you, nake yin abubuwa da yawa, i am just curious, Ya Rabb, amma kasan me? Wallahi banyi dana sanin shigowa dakinka ba, bansanka ba, bansan what you are capable of ba, amma na san ka san abunda kayi, shi za'ayi ma, na san kana da k'anwa Sadiya, na san in ka shiga gonan da ba taka ba, itama zaa shiga tata, nasan ba zaka min abunda ka san ba zaka ji dadi ba in an mata ba, na san fandarewarka a busa ma ciki hayak'i ne, kuma ina da tabbacin kai ba mazinaci bane".
Idon ya sake murzawa ya kwantar da murya, kamar zaiyi kuka, damuwa taji a muryarshi yace"Labibaah, you cant be so sure, ba a gane daniska a fuska, baki san abun da wani zai miki ba, ba kowa ke da irin zuciyar da kike tunani ba, wasu suna da abun ban mamaki, baki gane bak'in halinsu, nidai please kar ki kara shiga dakin kowanne namiji, ina tsoron abunda wani zai miki".
Ido ta lumshe ta bude ta sakar mai murmushi, tana me jin dadin muryar nan, tace "ka damu dani?" hannu ya sa a cikin gashi kafin ya daure yace "ke dallah, tashi ki tafi School" raurau tayi kamar me shirin kuka, nifa ba inda zani, already an fito 1st lecture, kawai na baka labarina sai kuma kace zaka koreni, ai ba haka mukayi ba?".
Tsaye yayi yana kallonta, itama kallonshi takeyi, sun dau mintuna fiye da uku suna kallon kallo, ko wannensu fa da abinda yake sak'awa, Wayarta ne ya katse su.
Aisha ce, dauka tayi "Hello Aisha? Ya kike, eh wallahi Ruwan Jiya ya mana gyara. Bangon Gidanmu ya fadi, shiyasa banzo ba, Ayyah Allah sarki, ya lectures? Ok to".
Ashe Aisha na tare da Abu Sadeeq, bashi wayar Aisha yayi suka gaisa ya mata jaje, ya shaida maya da yana missing Dimta, murmushi ta mishi kawai ta kashe wayar.
Har yanzu be fasa kallonta ba, wani kiran ya sake shigowa, kallon screen din wayar tayi taga Jay mamaki ta ba kanta da ta kasa daga wayar har wayar ta tsinke, don me zata k'i daukar wayar? ta tambayi kanta, kafin ta ba kanta amsa wayar ya sake ringing, sai ta daga ido a hankali ta kalli DanMakaho da sauri ta ajiye idonta k'asa tana wasa da hanayenta, wayar na kan Katifa tana ruri.
Wayar ta katse ta sake ruri, DanMakaho ya cire idonshi daga kanta, ya ga Jay a screen din, da kyar yace "Saurayinki na kira".
Da sauri ta daga kai ta kalleshi da kuma sauri ta sauke kanta kasa ta kawar da kai gefe, "Oh baki iya dauka a gabana?bari na fita" ta san in ya fita nan zai barta, ganinshi aiki ne tayi saurin cewa "aa, donAllah ka tsaya zan iya dauka".
Da sauri ta dauka "Hello Jay, zan kiraka, ina lectures ne" tayi saurin katse kiran, DanMakaho ya kalleta da mamaki.
Da murmushin mugunta yace "Lectures? Seriously? Wow, ashe kin iya k'arya" itama tayi mamakin k'aryan da ta sharara amma sai ta dake ta daure fuska tace "Ina Jinka, ka gaya min wanene kai?"
Wuri ya samu ya zauna daga gefe a sanyaye yace "Labarina bai da dadin ji" gyara zama tayi tace "zan iya saurarenka" yace "Labarina akwai tsawo" ta gyara zama tace "i have the whole day. (Ina da dukkan rana).
Murmushin takaici yayi
Yace "Sunana Zaid, Zaid Aliyu Zaki"
Da sauri tace "Meyasa ake ce maka DanMakaho? Meyasa ake kiranka da Mankas?"
A fusace yace "Zaki man shiru ko kuwa? in azarbabi zaki min tashi ki fita".
Hannu ta sa ta kama bakinta "Afuwan, nayi shiru".
A hankali ya soma Magana.
°°°°°°°
Wa zai iya mana hasashen Labarin Zaid?
Vote Vote Vote please.
#1love
#DM
#SonsoFWa
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Bakwai (ASALIN SU)
Alhaji Aliyu Umar Zaki tsohon dan Siyasa ne da yayi tashe a Da.
Yana da Shekaru 28 ya auri Shafa'atu 'yar mutanen Jos. Ya hadu da Shafa'atu ne lokacin da yaje Gaisuwar Mamar wani Abokinshi.
A GURGUJE
A lokacin, Mamar Shafa'atu na da Gidan Abinci, kafin Ali yaje Gidan Rasuwan ya fara zuwa Shagonsu Shafa'atu dake bakin hanya don cin Abinci.
Shafa'atu ce ta zo ta same shi, a natse ta gaishe shi ta tambayeshi abunda za'a kawo mishi, kallonta yayi yace "ki kawo min Shinkafa da Miya da Wake, sai kan Kifi" Shafa'atu ta dago ta kalleshi da mamaki tace "babu kan Kifi, saidai gangar Jiki da Bindi".
Ya dan tuburne fuska yace "ni kuma Kan Kifin nakeso" ta dan sa yatsar ta a baki tana nazari, su ba sa ba Customers kan kifi, amma wannan ya buk'aci da a bashi, tace "ka dan bani mintuna na soya maka" murmushi yayi don sosai 'yar budurwar ta burgeshi.
Bayan wasu 'yan mintuna ta dawo da abunda ya buk'ata, sosai ya ci Abincin nan, don ya sha tafiya, rabonshi da abinci tun kafin ya baro Katsina, sai ruwan da ya sha a Tasha, tambayar kudin Abincin yayi, tace mishi "kudinka naira dari da hamsin ne" cirowa yayi ya bata.
Ali sai ya manta da abunda ya kawo shi garin Jos, ya ja Shafa'atu da fira, haka ta biye mishi, da yaga Maghrib na neman yi baije yayi abunda ya kawo shi ba, ya ciro takardan da aka rubuta Adireshin Gidan Rasuwan, ya gwada mata "ko kin san Anguwar nan?" tace "eh ba nisa" nan ta sake mai kwatance.
Sallama sukayi tare da shaida mata zai dawo Gobe, murmushi suka sakar ma junansu, Ali ya tafi kwatancen da ta mishi da taimakon wani mai a kori kura ya gane Gidan. Sosai Abokinshi yaji dadin ganinshi, ya mishi godia sosai.
Washegari Ali ya koma Shagon su Shafa'atu, tun wurin k'arfe 10 na safe, dama da tunaninshi Shafa'atu ta kwana, taji dadin ganinshi yau, nan suka zauna suna ta fira, ba abunda ke tadata sai in Customers sunzo da ta basu abincinsu take dawo gurin Ali, Mamarta bata damu ba in dai kudi na shigo musu bata da matsala.
Maimakon kwana 1 da Ali yayi niyyan yi, sai gashi har kwana Uku be koma Katsina ba, duk da yayi Sallama da Abokinshi.
A cikin 'yan kwanakin nan Shak'uwa mai k'arfi ya shiga tsakanin Ali da Shafa'atu don Soyayya har ta shiga tsakaninsu kamar Almara.
Ranar da yace zai koma kar hankalin 'yan Gida ya tashi, Shafa'atu ta sha kuka sosai, a cewarta in ya tafi ba zai dawo ba, shi kuwa ya mata Alkawarin dawowa nan bada jimawa ba don zuciyarshi na wajenta a k'arshe ma ya tabbatar mata da cewa da labarin Aure zai dawo Mata.
Da wannan batu suka rabu Ali ya dawo Gida Katsina.
Ali ne Babba a Gidansu, yana da k'anne Maza da Mata.
Yayi karatun Arabi da Boko a Kano, be da wani aiki takamaime, amma yana da shige-shige da kutse-kutse, in yaje wuri sai ya tabbatar da an san shi a wajen kafin ya bar gurin, shiyasa abokan shi ke mai Inkiya da Ali Zaki ko suce Zaki kawai.
Tunda ya dawo Katsina yake ta tunanin Shafa'atu, hankalinshi dungurugum na gurinta, zuciyarshi na gaya mai ya koma Jos, nan ya bi zuciyarshi, ya sanar da Mahaifiyarshi zai koma Jos don ya samu Mata a chan, Mamarshi tayi mamaki sosai, amma sai tace "yanzu Ali duk Matan da ke garin nan da k'auyen garin nan basuyi maka ba sai ka dangana da Jos? Da dai ka bar maganar ta Jos ka zo ka bincika cikin Dangi, kasan Babanku dai" nan ya hau mata Magiyan donAllah ta goya mishi baya, zai samu amincewar Baban in har ta goya mishi baya, bayan ya dan sha wahala ya ci nasarar convicing dinta daga k'arshe.
Bayan 'yan kwanaki ya Koma Jos da Babanshi da k'anenshi sukaje ma Maman Shafa'atu da maganar Aure. Ta amince da hannu bibbiyu, Baban Shafaatu be da ta cewa don sai abun da Mamar tace, abu dai kamar wasa aka daura Auren Shafa'atu da Aliyu Zaki.
Bisa Alada aka rakota nan Gidansu Ali da ke Katsina inda a ka kaita dakin Ali.
Sosai Ali ke Son Shafa'atu, itama haka take sonshi, tana kyautata ma Mahaifiyanshi da k'anenshi, zaman lafiya sukeyi sosai.
Ali na dan fita yayi 'yan buga buganshi ya samu na cefane, ya kawo Gida a dafa kowa ya ci, zama suke na tsakani da Allah.
Bayan wasu yan Shekaru
Har Shafa'atu tayi shekara 3 a gidan bata taba ko da bari ba, wannan ya ja hankalin Dangin Mijinta gareta, abun ya soma damunta. Alin ne ke kwantar mata da hankali yana sake tunatar da ita kan Haihuwa ta Allah ce, yana ba wanda ya so a duk lokacin da ya so.
A lokacin ne Ali ya fara Shiga Siyasa, da yake yana da baki, ya iya magana sai hakan ke jawo mai Alheri daga Manyan 'yan siyasa, nan ya siya fili dan madaidaici ya fara gini, don su koma tare Matarsa duk don ya kwantar mata da hankali don ya lura rashin haihuwar nan, na damunta sosai.
Har wasu Shekarun suka k'ara shudewa, Shafa'atu bata yi ko da batan wata ba, abubuwa da yawa sun faru, Baban Ali ya rasu, duk nauyin Gidansu ya dawo kan Ali.
A Lokacin Ali ya shiga Siyasa tsundum don a yanzu ya wuce dan kwarako, a nan ta buk'aci da ya kaita Jos don a ganinta bata da Lafiya, ya kan ce mata "ta bar irin maganganun nan, don Haihuwa ta Allah ce, k'ila lokacin Haihuwar beyi ba" bata saurarenshi sai tayi ta kuka don danginshi sun sanga mata udo, habaibaici sukeyi mata, don Matan k'anenshi daga mai yara daya sai biyu, ita dai ya taimaka ya kaita ta samu magani".
Ba don ya so ba, ya kaita Jos da Motarshi, ya barota chan, nan Mamarta ta shiga dirka mata magungunan samun ciki.
Watanta daya a Jos Ali ya dawo daukarta don yayi kewar Matarshi sosai.
K'ulle mata magungunan akayi, har da na hayak'i, a ka kuma hadota da k'aninta Hudu dan shekara 4, Ali bai damu ba, don zai iya yin komai don Matarsa..
Shiru-Shiru bayan Watanni babu wata alama, hankalinta yayi mugun tashi da taga ba sarki sai Allah, sai ta bar yin maganin ta zubawa sarautar Allah ido.
BAYAN WASU 'YAN WATANNI
Alhaji Ali yayi suna, ya lula cikin siyasa tsundum, a lokacin shine Dan Majalissar dake wakiltar Katsina a Birnin tarayyah Abuja. Tunda Allah ya buda mishi yake kai danginshi aikin Hajj.Ya hada da Mahaifan Shafa'atu.
Wata rana, Alhaji Ali na hanyar zuwa Katsina daga Abuja shi da Drivernshi, suka tsaya a Masallacin Matafiya da ke Zaria. a gidan mai Masallacin yake. Bayan sun idar da Sallah ya hadu da wani Abokinshi Alhaji Usman Shehu da suka yi Karatu a Kano tare.
Da Murna suka rungume juna, bayan sunyi gaisuwa, Alhaji Ali yace "Haba Abokina ka boye" Alhaji Usman yayi dariya yace "Ina talaka zai ganka kana dan majalissa, ai ka zarce ni" Dariya sosai Alh Ali yayi yace "kai har yau baka bar iskanci ba" sukayi dariya baki daya. "Daga ina zuwa ina?" Alh Usman yace "daga zariya zamu koma Kano , chan nake zaune da wallahi iyalaina" Alhaji Ali yace "yaranka nawa?" "su 3 ne muje ku gaisa na san sun idar da sallah suna Mota" Tare suka je inda yayi parking Motar shi, ya bude yace ma matarshi ta fito su gaisa da abokinshi, fitowa tayi daga mota yaran suka fito su ma suka gaisheshi, daya bayan daya ya daukesu yana tambayan sunayensu yana mai sha'awarsu, sosai yake son yara, barin ma na k'annenshi, so yake ya dauki wasu daga cikin yaran k'annen nashi, amma da yake suna da yawa be son daukan dan wani ya bar na wani, kar ace ya nuna bambanci ko fifiko ga wani da kuma be so Shafa'atu taji an mata ba daidai ba don ita bata haihu ba, shiyasa be taba bijirowa da son rike 'ya'yan kanenshi ba.
"Kaifa yaranka nawa?" dan murmushi yayi yace "tukunna dai Allah bai kawo ba" Alhaji Usman sai yayi nadamar tambayarshi don kar yaga kamar yana son ci mai fuska ne, Alhaji Ali ya lura da yanayin da abokinshi ya shiga yace "kai daniska, kar ka damu, haihuwa ai ta Allah ce, idan da rabona zan samu D'an cikina ko ba dade ko ba jima zan samu, kawai ka tayani da Addu'a" InshaAllah Abokina inji Alh Usman.
Alhaji Usman ya kalli matarshi yace "wai ina Maryama ne?" dan murmushi tayi tace "ta na cikin masallacin mata muka barota bata idar ba" da mamaki Alhaji Usman yace "k'assarun?" tayi dariya tace "shi fa, ka santa da dadewa gun sallah" yace "danAllah je kirata muna kan hanya kar muyi marece" kafin waninsu ya sake magana hankalin Alhaji ya kai bakin Masallaci da wata halitta fara ta fito daga ciki tana gyara zaninta wanda shine matsayin mayafi.
Yauwa gata nan ta fito cewar matar, bude baki yayi yace "sallatu yi sauri ko?" da murmushi ta k'araso, ta kalli Alh Usman da ya shagala wurin kallonta tace "ina wuni" kasa amsa mata yayi sai da abokinshi ya lura dashi ya sa hannu ya zunguro shi kafin ya amsa mata. Oya a shiga mota, ya umurce su.
Alhaji Ali yace "Abokina wacece wannan?" yace "Maryama ce kanwata ko" dan shiru yayi kafin yace "indai har baku yi mata miji ba ina so, zan aureta".
#############
Dariya Alhaji Usman yayi "kai wallahi Ali ba ka rabuwa da shiririta" tamk'e fuska Alhaji Ali yayi yace " kai ni wallahi dagaske nake, in dai wallahi ba kuyi mata Miji ba, ina so".
Kallonshi Alhaji Usman yayi sosai yaga iyakar gaskiarshi kenan, yace "in har dagaske kake, to wallahi ka samu Maryam, kai dai kawai ka zo Gida, sai mu sake tautaunawa".
Hannunshi ya rike yace "Wallahi zanzo, kawai ka bani full address dinka." Alhaji Usman yace "ba damuwa".
Paper ya fallo a cikin Motarshi ya rubuta mishi Adireshin Gidanshi a Kano, shi ko Alhaji Ali hannu ya sa a Aljihu ya ma yara Alheri suna ta Godia, a nan ne kowanensu ya shiga Mota suka ma juna Oda kafin suka wuce.
Tunda ya zauna yake lumshe ido yana sake hasaso ma kanshi Maryama, haka Driver ya ta shatata gudu Alhaji Ali na ta begen Marayama a zuciyarshi.
Ya iso Katsina lafiya, sai da ya fara zuwa Gidansu ya gaida Mahaifiyarshi, kafin ya sauke mata tsarabar da yayi mata, ya ma Matasan Gidan Alheri kafin ya wuce Gidansi.
Shafa'atu ta tarbeshi kamar yanda ta saba, cikin shiga ta alfarma, suka rungume juna don sunyi kewan juna, sai da ta kaishi yayi wanka, kafin ta zubo mishi Abinci suka ci tare.
WasheGari, ya dauki hanyar Kano.
Alhaji Usman Aminin Alhaji Ali ne tun suna Makaranta, Maryama k'anwarshi ce, kasancewar Mahaifansu sun Rasu, Alhaji Usman ne ke rik'on Maryama tun bayan Rasuwar Mahaifiyarsu, yana kula da ita sosai don har makarantar Unguwanzomanci ya sakata(Midwifery).
Da Azahar suka karbi bak'uncin Alhaji Ali, Alhaji Usman yayi mamakin ganinshi, don beyi zaton zai zo nan kusa ba, lallai ya nuna mai dagaske yake. Abinci Matar A. Usman ta gabatar mai da shi, ya ci sannan ya gabatar mai da buk'atarshi,
Alhaji Usman yace "ba damuwa, shi dai ya bashi ita, kuma ya san yarinya ba zata bashi kunya ba, don Matsayin Uba yake a gunta" ya mik'e tare da cewa "bari ya turo mishi ita".
A daki ya isketa tana zaune kan wata kujera tana duba wani littafi, zama yayi a dan nesa da ita, tana ganinshi ta gyara zamanta tare da kulle littafin da ke hannunta.
"Maryama, ina so ki Saurareni, a Parlo, akwai abokina Alhaji Ali, wanda muka hadu jiya a Zariya a Masallaci! Na san kin ganeshi, to shine ya zo neman aurenki gurina, ni kuma na bashi ke, saboda na san kyawawan halaiyanshi, na san ba zaki watsa min k'asa a ido ba".
Shiru tayi batayi magana ba, yace "Maryama, ba dai bijiremin zakiyi ba ko?" da sauri ta girgiza kai tace "Yaya, kai ne Uwana kai ne Ubana duniya banda sama da kai, na san ba zaka zaba min abinda zai cutar dani ba, Nagode da zabinka gareni, Allah ya shige mana gaba". Da fara'a ya amsa da "Ameen, ni na san ba zaki bani kunya ba, ina Alfahari da ke Maryama, maza tashi, ki sanya Mayafi kije gareshi yana jiranki". Kanta a k'asa ta ciro Zaninta ta yafa ta fita waje.
Da Sallama ta shiga Parlorn kanta a k'asa, zama tayi a kan kujera daga farko, kafin ta dan rusuna ta gaisheshi, shi ko da kallon So da Kauna ya bita, ya amsa gaisuwarta cikin shaukin soyayya, a hankali a hankali ya ke tambayarta tana bashi amsa, sun dau lokaci suna zantawa, daga bisani yace "ta shiga ciki ta turo Yayanta".
Alh Ali ya gaya ma Alh Usman shifa ya samu Mata, ba bata lokaci yace "suje ya gabatar dashi wurin Kawun su".
Alhaji Ali be bar Kano ba sai da ya tabbatar an bashi Maryama.
Da farinciki ya koma Katsina, ya je ya sanar da Mahaifiyarshi yana neman Aure, ta sa mishi Albarka, Danginshi ko sunfi kowa Murna don su na son su ga gudan jininshi, k'ila Auren Rabo ne ke zuwa, nan fa aka fara shirin Biki.
Ba wanda ya sanar da Shafa'atu game da Auren.
Kudade ya biya masu dimbin yawa aka fara gina Mishi Katafaren Gida a wani Anguwa da kusan shi kadai ya fara Gini a wurin wato Tudun Matawalle,
Shafa'atu kuwa tausayinta yake sosai, yana shakkar gaya mata maganar Aurenshi, be so taji kamar zai kara aure ne saboda haihuwa, baya so ta ga kamar ya gaji da ita ne, baya son bata mata sam, karshe dai ya biya mata kudin Umra ta tafi Makka, kuma ya siya mata 190, a lokacin da wuya kaga Mace na tuk'a mota, amma ita ya mallaka mata Motar kanta, Bayan tafiyarta Makka ya samu ya fara shirin bikinshi a tsanake.
Ana saura Sati 3 Biki
Shafa'atu taje Gidan Surikanta da Akushi dauke da Tuwo Miyan Kubewa busassa dominos uwar Mijinta, tunda ta shiga ta ji gabanta ya fadi, da Sallama ta shiga k'urya, zaune k'annen Alhaji Ali suke su 9 suna diba kaya, da alamu lefe ne, akwati 2 manya, da fara'arta ta gaishesu, da Hajiyarsu, Hajiya ta amsa tana dan jin nauyinta, basu san zata zo ba.
Shafa'atu ta kallesu tace "to, lefe ne ake kallo? Karime wa aka kawo wa lefe bamu sani ba?" Karime ta dan kawar da kai gefe tana yak'e ta rasa me zata ce mata, Shafa'atu ta sa hannu tana daga kayayyakin tana gani tana yabawa "wai Kayan waye? Wa aka kawo mawa?" Ladidi tace "wa dai zaa kai ma wa ko?"
Karime ta zungurota da hannu, da yake Ladidi ta fi ki jinin Shafa'atu tace "har sai yaushe zaa boye mata? Ke Shafa'atu lefen Yayanmu ne, za'a kai Kano Gobe in Allah ya kaimu" Shafa'atu da dan yak'e a fuskarta tace "Ahh, Yaya Shehu Aure zai sake? Waiyo Allah shi kaimu, ashe muna da biki".
Ladidi tace "Iyeeee, wato Shehu kadai ne yayanmu? To babban Yayanmu nake nufi" Hajia tace "Ladidi kiyi shiru" Shafa'atu da bata fahimci komai ba tace "bangane ba, Babban yayanku? Wanne kenan?" Ladidi tace "baki gane ba? To Yaya Ali nake nufi" tsalle Shafa'atu tayi ta dire tace "Ba ku da hankali, kun ga dai bana san irin wasan nan" Asabe tace "wake miki wasa? Tunda kin kasa haihuwa, zaa auro me haihuwa".
Karamin bori Shafa'atu ta hau, ta hau facali da kayan cikin Akwatunan, kafin ta wawuri Akushin Miya ta bude Miyan ta juye a jikin kayayakin, nan suka yo kanta, ta dire ta yi kan Hajiyarsu. "munafuka, ke kikace yayi aure ko?" aiko su Ladidi sukayo kanta, suka hau dukanta wai ta zagar musu mahaifya da k'yar Hajia ta hanasu dukanta, har tace "zata tsine musu in suka sake bugunta"
Ina bakin shafa bai mutu ba, ta dinga surfa musu Zagi, tana laantarsu, tana cewa itace Ajalinsu, shegu k'azamai, talakawan banza, duk kyautata muku da nakeyi? Ni zakuyi wa butulci, biye nake da ku kamar na muku sujadda shine zaku saka min da wannan? Aiko zaku sha mamaki, ayi auren mu gani, ta fita fuuu, ko zaninta bata dauka ba, ta ci karo da Ali a hanya ko kallonshi bata yi ba ta fada motarta ta danna a guje, Ali ya ji gabanshi ya fadi. Ya shiga Gidan da sauri
Hajia ce tace "ta ga kayan lefen ne, ka bita ka lallasheta" kallon kayan yayi yace "meye wannan kamar miya?" Ladidi ta chafe tace "Wai baka ga ruwan wulakanci da tayi a gidan nan ba, har ta na zagin Hajia, kanta farau kishiya?" ran Ali ya baci yace "Ta zageki Hajia?" Hajia ta girgiza kai tace "aa ba fa ta zageni ba ladidi" tana wurgar Ladidin da harara, kai dai ka je ka san me za ka ce mata kasan mata ba sa son Kishiya.
Tashi yayi jiki a sabule ya nufi Gida, ya jima a bakin gate kafin ya shiga, zaune ya ganta har ta bashi tsoro don ta ci kuka har ta gaji, k'arasawa yayi a tsorace, be san ta inda zai fara ba, yana karasowa ta ci kwalarshi, tana jijigashi tana dukanshi ko ta ina, ni zaka yaudara Ali don kayi kudi, ni da nake zaune da kai tun baka da komai, ni zaka ci amanata Ali? Kasa magana yayi, ya kasa motsi, ta cigaba da dukanshi kafin ta fashe da wani irin kuka, rungumeta yayi tsam tun tana motsi har tayi lamo a jikinshi tana mayar da ajiyar zuciya, sai da ta daina motsi kafin ya soma magana.
"Shafa'atu na san ban kyauta miki ba da na boye miki maganar Auren nan, amma ki san cewa ina sonki fiye da zatonki, duk wata Macen da zan aura a bayanki take, kar ki manta irin Son da nake maki, ki dauka wannan Auren k'addara ce, ki bani goyon baya nayi auren nan, wallahi ba zan taba wulakantaki ba, wallahi Shafata kin fi karfin wulakanci a wurina, Shafa'atu ba ayi macen da take karshena da zata wulakantaki ba, in naga ba zata girmamin ke ba, wallahi ina iya rabuwa da ita, ki taimaka min" abun mamaki hawaye ta gani kwance a idanuwanshi tana son Mijinta sosai, kalamanshi sun darsu a zuciyarta, bata da wani zabi illa ta danne zuciyarta.
Bayan ta gama kumburinta ta sauko, hakan ya bashi kwarin guiwa ya cigaba da sabgarshi, amma walwalarta sam bata dawo ba, da tsanar danginshi da ya darsu a ranta, danne zuciyarta kawai take.
***.
Ba wai don tsoronta yake ba kawai don a zauna lafiya ya sakar mata ragamar bikin gaba ki daya, sai yadda tace ake yi, harta dakin da Amarya zata zauna ita ta za bar mata, ya so ta ba Amarya daki biyu, amma tace nata ne kawara daya ne na amarya, be damu ba don ya san da ya gama gininshi zasu koma sabon Gida kowa da Dakinshi da Parlornshi, shiyasa be ce mata komai ba.
A ka zo jere, da katifa da kujera da kayan kitchen duk aka jera a daki daya kasancewar dakin k'ato ne.
Tun daga jere dangin Maryama suka gano matsala daga gun Abokiyar zaman Maryama, amma basu ce komai ba gudun sa mata tsoro da fargaban kishiya, kuma sun lura Dangin Ali na son Abun.
"Kinsan Shafa'atu, ki bi a sannu, kinsan Mijinki yana daidai gwargwado gurin kyautata miki, to in kika faye zak'ewa kika kureshi, zai bar bi takanki, ke dai kawai ki bi ta bayan fage ki kori amaryar nan, ki mata zagon k'asa, kishin mimik'e zakiyi, kar ki yarda a gane ba kya sonta kin gane?" ta jinjina kai tana kwasan karatu gurin Aminiyarta Hajiya Er Rabi,
Nan ta kwantar da kai ta bi har Gidansu Hajiar Ali ta basu hakuri, kan haukan da tayi sharrin shaidan ne, Hajia tace ba komai ya wuce dama an san mata da kishi, balle ita da aka boye mawa.
Jumu'ah na zuwa aka daura Auren Alhaji Ali Zaki da Maryama Adamu a garin Kano ta dabo, an kawo Amarya dakinta.
Uwar Dakinta Matar Yayanta ta dade tana jadadda mata nasihan da yayanta ya mata, kafin suka bar Katsina, Maryama ta sha kuka kamar idanuwanta zasu fadi.
Murmushi ya mata yace "nagode Allah ya miki Albarka Maryama"
Shafa'atu kamar ta fashe amma sai ta hau yak'e tace "bari ta dauko musu Abinci".
Da sauri ta mik'e ta fice hanyar kitchen, Ali ya dinga bin Maryama da kallo ita ko kunya ma yake bata.
Tare sukaci abinci kafin suka gama, Shafa'atu tace bari ta shiga ciki ta musu sai da safe.
Shiga daki tayi ta dinga gwala kanta a bango, tana kukan bakinciki, anya hanyar nan mai bullewa ce? Anya zata cigaba da nuna komai lafiya lau ne alhalin ba haka bane? Gaskia da sake.
Su ko maaurata tuni suka shige dakinsu.
A GURGUJE
Bayan wasu 'yan Satittika
Zaman lafiya suke kadaran kadahan, Maryama dama sanyi gareta, biye take da Shafaatu, sun raba kwana bibbiyu, ko wacce burinta ta zama tauraruwa wurin Mijinta, sosai Shafa'atu ta danne zuciyarta don su zauna lafiya da Maryam, barin ma da ta ga bata da matsala.
****
Ta gane tana da ciki, saboda sauyin da ta ji jikinta nayi, bata ce ma kowa komai ba ta cigaba da harkokinta.
Sosai Mijinta ke nuna mata k'auna, a gaban Shafa'atu ya kan nuna kawaici, amma in suka kebe kamar ya hadiyeta.
Sannu a tashi alamun Ciki ya fara bayyana a jikin Maryam, tara miyau a baki, da amai in taji tashin zuciya, daga Shafa'atun har Alin ba su dago cikin bane don ba sani sukayi ba.
Ita dai Maryam ta san ciki ne da ita, in ta fara kwarara Amai kamar ta amayo hanjin cikinta.
Wata Rana Hajia Er Rabi, k'awar Hajia Shafa'atu tazo gidan, Maryam ta fito don gaisheta, kallo daya ta mata ta san cewa tana da shigar ciki, da ta shiga ciki, tace "kawata, ashe mutuniyar har ta dau ciki" Shafa'atu ta mata kallon rashin fahimta. Er Rabi tace "kar ki ce baki san tana da ciki ba?" ta dan zamo daga kujera tace "kar ki ce man ciki gareta, wallahi ban sani ba, shima Alin bai sani ba" Er Rabi tace "lallai kam, ban yi mamaki ba don ko bari baki ta ba yi ba, ba ki san yanda ake gane ciki ba, to Kishiyarki Ciki ne da ita".
Dam gabanta ya fadi "yanzu Maryam ciki ne da ita? Bata gaya mani ba?" Er Rabi tace "ke ya ma fi haka, kinga yanzu da kika sani, sai mu 6arar da cikin ba tare da kowa ya sani ba, balle mu shiga zargi" ido ta zaro tace "a barar da shi fa kika ce?" ta girgiza kai da sauri, tana da kishi sosai amma rashin imaninta bai kai nan ba, ta san Mijinta ya dade yana neman haihuwa, kuma amfanin Maryaman kenan ta haihu, bata ji dadin cewa ba ita zata haifa ma Ali 'ya'ya masu kama dashi ba, amma ba za ta taba halaka dan Cikin Maryama ba.
Ta kalli k'awarta tace "ba wannan maganar, duk da bana so ta haihu, ba abunda zan mata gaskia, Cikin Mijina ne, farincikinshi nake so, don gaskia be rageni da komai ba" baki sake take kallon Shafa'atu tace "lallai Shafa'atu, kina tafka wauta, wayace miki Dan Miji Da ne? Kinga zaki tafka kuskure, a duk ranar da Maryama ta haihu musamman Namiji ti kashin ki ya bushe, ba mai kara kallonki da daraja, ke ce Uwargida, amma gida zai koma nata. Dangin Mijinki kuwa dama sun tsaneki da ta haihu sunanki abar tausayi".
Hajiya Shafa'atu tace "nidai gaskia a bar maganar zubda cikin" Er Rabi tace "an bari, amma zakiyi kuka da kanki, ni kinga tafiyata" ta mik'e ranta a bace "haba kawata ina zaki?" tace "yo zaman me zanyi? Ana gwada maki annabi kina runtse ido".
Hajiya Er Rabi ta fita, Shafa'atu ta bi bayanta tana magiyar ta tsaya amma tak'i.
Da daddare wurin cin Abinci, suna zaune su uku kamar yanda suka saba, Shafa'atu tace "Alhaji, Albishir ne dani me zan samu" ya tsaya da cin tuwo ya kalleta yace "Shafata duk abunda kike so zan baki, gaya min" Maryama ta zuba mata ido, tana tunanin abunda Shafa'atu ke tafe dashi, murmushi tayi tace "Maryama Ciki gareta, akwai danka a Mahaifarta" mamakin ya sa Maryama kallonta, shi ko Gogan wani Yammm yaji a kunnenshi, ba zai iya fasalta abunda yakeji a tattare da shi ba a cikin wannan lokacin, duk suka zuba ido don ganin halin da zai shiga.
Mamaki ya basu duka, da k'yar yayi murmushi yace "Allah Sarki, to Allah ya raba lafiya" ya mik'e tare da cewa bari ya wanko hannunshi, Shafa'atu ta bishi da ido, a matsayinshi na wanda baa taba mishi irin wannan Albishir din ba, tayi mamakin yanda ya karbi zancen, to ko baya son Haihuwan ne shiyasa bai taba mata k'orafi kan rashin Haihuwar ta ba, tunaninka da yawa suka darsu a zuciyarta.
Ita ko Maryam ba ta ji dadin yanda Mijinta ya karbi Zancan ba, ko da ace ya saba haihuwa aka ce tana da ciki ya kamata a nuna farincikinshi, ita da take da burin haihuwa duk shekara don ta cika mishi Gida da 'ya'ya, amma ba komai, ta tashi ta kwashi kwanonin ta kai kitchen ta dauraye kafin ta koma daki.
Alh Ali Zaki na shiga dakinshi ya fada kan Kujera tare da fashewa da wani irin kuka, kuka ne mai dauke da ma'anoni da dama, shi ne Zai haihu? Shi Allah ya azurta matarshi da ciki? Shekara fiye da bakwai da aure? Yau shi matarshi ke da ciki? Farincikinshi ba mai fassaruwa bane. Alwala yayi ya jera nafilfili don nuna farinciki ga Allah SWT.
Watanni sun shude
Tun Safe ta ke jin nak'uda, amma sai ta daure, ganin ciwon na k'aruwa yana sake yawa ya sa ta fitowa ta kwankwasa dakin Shafa'atu tana cije baki.
"Yaya Cikina kamar zai balle, mutuwa zanyi" da sauri Shafa'atu ta kamota tace "gashi Alhajin be nan, ko zaki sake daurewa har ya dawo?". Maryam ta riko hannunta tace "ki taimakeni, wallahi mutuwa zanyi, nidai ki kira Unguwanzoma".
Kamar daga sama sukaji Sallamarsu Ladidi da Asabe, Shafa'atu ta manta rashin jituwarsu ta karasa gunsu tace "yauwa ina jin Maryama nak'uda takeyi" Ladidi tace "to da me zaki mata? Ke zaki karbi haihuwar ki danna kan yaro ya koma?" ran Shafaatu ya baci "ai da banson a haihun da tun lokacin da take da ciki na barar da shi" Ladidi tace "ai ko ba ki fada ba na san bakincikin cikin nan kikeyi, to ta Allah ba taki ba, sai an haifeshi munci moriyar Magajin Yaya Ali da yardan Allah". Asabe tace "kinga muje mu taimaka mata, tana cikin mawuyacin hali".
A daddafe suka kaita dakinta, haihuwar ce dama, bayan yan mintuna ta santalo danta jazur dashi, bayan Ladidi ta gyara Da da Uwan ta aiki Asabe zuwa chan GidanGandunsu taje ta fadi haihuwar.
Shafa'atu na nan tsaye gefe tana jin kukan jariri tsoro ya mamayeta, kasa shiga dakin tayi sai ta wuce dakinta ta fashe da wani kukan da bata san ko na meye ba, fargaba ne fal ranta.
Kamar daga Sama sai ga Alhaji Ali da Kanenshi, yana Gidansu Asabe ta je ta fado haihuwar, Shafa'atu na jin muryan Mijinta ta fito waje,
"Alhaji sannu da dawowa" be ko kalleta ba ya wuce ya barta tsaye, gabanta ya fadi, me kenan? Ta tambayi zuciyarta, bayanshi ta bi da ido, kafin ta rufa mai baya.
Yana shiga ya amsa Jaririn daga hannun Ladidi ya rungumeshi tsam a k'irjinshi, tsigar jikinshi suka mimike, wani yanayin da be taba shiga irinshi ba ya shiga, hawaye suka soma kwaranyowa daga idanuwanshi, hamdala yake yi yana godewa Allah, addua ya ma yaronshi, kafin ya karasa gun Maryama yana ta jero mata sannu yana sanya mata Albarka.
Duk a kan Idon Shafa'atu, hawayen bakinciki ta fara ta fita daga dakin da sauri.
Labarin Haihuwa ya Zagaye Gari, sai zuwa barka akeyi, ana taya Alhaji Ali murna, kullum Gidan ceike yake da Danginshi da yan barka.
Shafa'atu ta zama kamar bakuwa, don da ta zo wuri ake mata habaici, ita Maryama bata da ta cewa sai yanda dangin Miji sukayi da ita don ma suna sonta, kowa so yake ya burgeta, daga masu dafa mata abinci, sai masu ina zaa saka da ita.
Alhaji Usman da Iyalanshi da Dangin Maryama sunzo barka, da yawa sun tsaya Suna.
An san Alhaji Ali da kyauta, amma tunda akayi haihuwar nan, ya Soma kyauta kamar baya son kudadenshi, kyautata ma Makwaftanshi yake.
Ranar Suna aka radawa yaro Suna ZAID ALI ZAKI.
Zaid ya sha kyaututuka daga manyan 'yan siyasa.
Anyi babban liyafan Sunan da baa taba yin irinshi ba a Anguwar.
Wani sabon kulawa Alh Ali ke ba Zaid da Mahaifiyarshi, dan kawaicin da yake ma Shafa'atu a da yanzu babu shi, gabanta yake nuna tsantsar soyayarshi ga danshi, in yana tare da Zaid ba ya da lokacin kowa da komai, Abujan da yake yawan zuwa yanzu ya bari, in ko Zaid na kuka da kanshi yake zaro Nono daga Jikin Maryama ya ba Zaid ko gaban waye.
Ba ya kawaici ko shariya wai don Zaid ne dan fari, mutane na mai uzuri ganin be taba haihuwa ba.
Shafa'atu ta fara jin ba daidai ba, Alhaji Ali ya rage damuwa da ita, kacokam hankalinshi ya koma kan Zaid, tun tana daurewa har ta tare shi wata rana da maganar a parlo.
Yana rike da Zaid a k'irjinshi "Alhaji, magana nake so muyi" ya dan kallota amma be fasa ma Zaid wasa ba, hakan da yayi ya nuna mata yana sauraronta tace "Alhaji, wai kai baka da lokacin kowa da komai sai na Zaid? Kai ko dan kawaicin Dan fari bakayi? Alhaji, ba ka gudun bakin mutane? Komai Zaid komai Zaid?" baki sake yake kallonta yace "Shafa'atu wace irin magana ce wannan kike? To in banyi lokacin Zaid ba lokacin wa zanyi? Don mutane kar suce banda kunya, ko kuma kar suce banda kawaici sai na k'i nuna ma yarona So, Kauna da kulawa? To mutane sun dade ba suyi magana ba, aj dade baa zageni ba, banda kamar Zaid wallahi, kuma zan iya rabuwa da kowa ta kan Zaid ko da Mahaifiyarshi ce balle ke".
A tsorace ta kalleshi, mamakinshi take, tace "Alhaji Ni? Sai ka rabu dani ta kan Zaid? Me na mishi?" yace "Yo sai na rabu da ke nana Shafa'atu, haka kurum kinzo min da wani soki burutsu, ni da Dana? Duk mai son ganin bacin raina to ya kawo kushe ga Zaid, kika cire Mahaifiyata, Wallahi na fi sonshi fiye da kowa a Duniyar Yanzu, to ki bi a hankali".
Hankalinta ya tashi sosai, sum sum ta tashi ta shige dakinta tana fashewa da kuka Sosai.
Haka ta kwanta zuciyarta na k'una, tunaninka kalakala, washegari ta ma Gidan Hajia Er Rabi diran Mikiya,
Matsalarta ta karanto mata.
Er Rabi tayi dariya, "ba ke dadi Miji ba? Ba yanda banyi dake kan a barar da cikin nan ba ki ka ki, gashi ya zame miki ciwon Ido, mai makon ace kinyi Kishi da Kishiyarki, kin kare da kishi da Dan Mijinki, ai wallahi kuka yanzu kika far yinshi, ba zaki san tsakanin Mahaifa da Gudan jininsu ba tunda ba haihuwa kika taba yi ba".
Bata rai tayi tace "abun 'yar gori ce?" tace "aa, ina dai gaya miki ne, kashin ki zai k'ara bushewa a duk lokacin da Maryama ta sake haihuwa, in ko ta cika mishi Gida da yara to wallahi zaki zama Almajira a cikin gidan aurenki, kar ki yarda ta sake haihuwa, ki tashi tsaye Shafa'atu, ki kwatar ma kanki 'yanci".
Jin saukar maganganun Er Rabi take kamar Darma mai zafi, dole ta tashi tsaye, da ta bisu ta arziki ba abunda ya kare ta dashi, zata bisu ta tsiya, duk sai ta ci uwarsu, nan Hajia Er Rabi tayi ta zugata tana gaya mata abubuwan da ya kamata tayi.
Tun daga ranar Hajia Shafa'atu ta chanza ma Maryama, a gaban Mijinsu kamar ta goya su ita da Zaid, amma a bayan idonshi Kashi ya fisu daraja.
Zaid na da Wata 5 Maryama ta sake daukan Ciki, hankalin Shafa'atu ya tashi ya a ka k'are da Zaid balle an yi mishi kanwa, kila Alhaji Ali ba zai samu lokacin yi mata magana ba.
Samun Er Rabi tayi, ta gaya mata ai Maryama na da ciki, wani magani ta bata tace ta zuba mata a cikin Abinci.
Ta ko ci saa cikin ya zube, bayan Maryama ta sha bak'ar wahala. Tun daga lokacin nan, ciki ya bar Zama a jikin Maryama, da tayi da cikin ya zube, kusan bari 9 tayi a shekara 4.
A cikin Shekarun nan Hudu da suka shude, Alhaji Ali yayi wani irin kudi mai ban tsoro, ya koma Sabon Gidanshi da ke Tudun Matawalle, Gidan Sama ne, a Sama akwai Dakuna 3 daya na Maryama daya na Alhaji Ali, daya na Shafa'atu, sai a k'asa Akwai K'aton Parlo da dakuna biyu, sai k'aton Kitchen din da duk mai sanwa take shiga.
Sai kuma ya na da masu dafa Abinci a baya inda Boysquaters suke, Gidajen da ke kusa dashi kullum suna da kwanon Abinci a Gidanshi, tunda ya dawo Anguwar kullum yana da 'yan maula masu jiranshi a k'ofar Gida, bai taba gajia ko kosawa da su ba, yana musu ihsani.
Kullum hannunshi rik'e da na Zaid, duk inda ya sa k'afa to Zaid na biye dashi, mutane kuwa sai su dinga wasa Zaid da kirari ko don ya musu Alheri, Zaid na da matuk'ar wayau, baya da k'uiwa, duk yan Unguwa na sanshi, yana da son mutane kamar Mahaifinshi, yana da shekara 4 yayi wani irin wayau.
Shafa'atu tsanar ta ga Maryama da yaronya karuwa yake.ta yi ruwa tayi tsaki dai gun hanata sake haihuwa, duniya ba abunda ta k'i jini irin Zaid, abunda ke bak'anta ranta, sai ta dage tayi abinci domin Mijinta, sai Alh Ali ya kira Zaid wai tare zasuci, ko kuma ya kwashe mishi namomin yace "maza cinye Zaiduna" abun nan na ci mata tuwo a kwarya, ji take ta na iya harbeshu da bindiga.
In ko ranar Girkin Maryama ne sai tayi sanadin bata mata sanwa, ko ta k'ara mata gishiri, ko yaji, don dai suyi fada da Alhaji, amma bata taba jin kansu ba.
Yaran Yayan Maryama na zuwa mata hutu sosai, in har Alhaji Ali baya nan, to Abinci a cikin Samira take ba Maryama wai da ita da bak'inta, ta kuma kulle kitchen din CIkin Gida don kar Maryama ta dafa komai a cewarta ai ana abincin gandu, zai zama albazaranci ayi ta dafuwa kalakala. Maryam bata taba kaima Mijinsu k'orafi ba.
Da ta hadu da Zaid to sai fa ta hada shi da wani Rankwashi, ko tsunguli, in ko yana bacci har razor ta ke sawa ta fasa mishi jiki dan k'eta.
Ran da ya ba kowa mamaki, randa suke zaune gabaki daya su hudu suna cin Abinci, Zaid na kan cinyan Babanshi yana sa mishi doya a baki kamar an tsunguleshi yace "Yauwa Baba, kaga kullum mama sai ta tsunguleni ta min haka akai" ya Rankwashi baban a kanshi a hankali yace "amma ni mai zafi takeyi min, me na mata baba?".
Mama kamar yanda yake ce ma Shafa'atu, kowa ya san ita kadai ce Mama don Maryama Minyama ya ke ce mata.
Alhaji Ali ya kalli Shafa'atu, Maryama kuwa kau da kanta tayi, yace "Shafa'atu? Ke kin Rankwashi shi da tsungulinshi? A kan mene?" Shafa'atu da tayi zaune kamar gawa ta kasa motsi, mamaki ta hanata motsawa.
Sai da ya daka mata tsawa kafin ta fara borin kunya, haba Alhaji, kai ka san yanda na dauki Zaidu kamar dan cikina, don me yaro dan shekara hudu zai ma magana ka hau kai? In tsunguleshi inji me? Daga jin maganar nan an san kitsa mai a kayi, kuma ban yafe ba, Zaid ni na san ba kayi wayon hada maganganun nan ba, na san gaya maka akayi, ba wani abu, don ban taba haihuwa ba shine ake ta min abubuwa a gidan nan".
Jikin Alhaji Ali yayi sanyi, shi ya san Yaronshi beyi wayon yin karya ba, amma kuma maganganun da Shafa'atu tayi sun shiga ranshi. Sai dai ya share ya cigaba da cin Abincinshi, amma ya kudurta a ranshi duk wanda ya matsa ma Zaid shima zai matsa mishi.
Wannan kenan
Vote and Comment line by line pls
#1love
#DM
#anatare
#SonSoFWA
#nagode..
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Takwas (WANENE SHI?)
Bibilicious freaking fans, Vote before reading please, thank you.
Ya kalli Labiba yace "A zaman Gidan Kishiyoyi, ko a auro Amarya tazo ta takura ma Uwargida, ko kuma Uwargida ta takura ma Amarya, a gidanmu ba haka bane, Matar Ubana , ni ta takura mawa, da yaron Gidan take kishi, ni ta sanya wa Ido".
Idan har ta bude idonta ta ganni, ji takeyi kamar ta kasheni.
Ba zan manta ba wata rana Baba ya tafi Lagos wani Taro, a lokacin ina da shekara 5, na shiga Makarantar Boko, ranar da Baba zai dawo Mama ke Kitchen, ta dade tana hada Abincicika kala 2 masu dadi, da farko tuwo miya taushe, sai na biyu Shinkafa da ya ji kaza ko ta ina, kuma don rowa sai tayi don cikinshi kadai.
Kamshin Abincin ya cika Gidan gabaki daya, har na kasa hakuri na bita har kitchen nace "Mama zanci Abinci" kora na tayi har da dan biyoni da gudu.
Fadawa nayi daki kan Minyama, ta kasance ta na jina da Mama a kitchen, rik'oni tayi tace "Zaid, ba fa yunwa kakeji ba" nace "Ni Abincin Mama nake son ci, kuma ta hanani, bakomai, ai da Baba ya dawo tare zamuci"
Minyama ta kalleni sosai kafin ta rik'o hannayena duka tace "Zaid, kana ja min matsala, DonAllah in Babanka ya dawo kar kaje wurin ci Abincinshi, zan maka irinshi ranar Girkina kaji DanAlbarka?" sai da Minyama ta dade tana lallashina kafin na amince ba zanje gun Babana ba in yana cin Abinci.
Da Baba ya dawo, kamar ko da yaushe da tsarabata ya shigo, ya dauke ni ya tillani sama ya chafe "Farincikina" kamar yanda ya saba ce min, ni ko na mak'alk'aleshi ina dariya, yace "Kayi Kewana?" nace "Sosai ma".
Ina kallon Mama ta galla min harara, da yake ita ce ta biyoshi daki, tuni na shiga taitayina na dan zame na bar musu dakin.
Nan suka sake gaisawa, sai da yayi wanka kafin suka fito Parlo tare, ta gabatar mishi da shagalin da tayi dominshi, ta zuzzuba mishi a Plate.
Baba ya lumshe ido yace "wai kin san yanda nayi kewan Girkinki Shafata?" Murmushi tayi tace "ai gaka ga shi, sai kaci ka k'oshi, nayi dominka kai kadai" Baba yayi murmushi yace "nagode k'warai".
Da Bismillah ya fara cin Abinci, Shafa'atu ta zuba mishi ido cike da so da kauna, tana ganin yanda ya lumshe ido ta san cewa yaji dadin Abincin ta fadada murmushinta.
Loman da Baba zai k'ara ya dan dakata, bude baki yayi yace "Ina Zaid?"
Da sauri tace "yana gurin Minyamanshi ko, yi sauri ka ci kar ya huce Alhaji"
Kamar zai mik'e tsaye yace "Kira min shi yazo muci Abinci".
Ranta a bace tace "be fa jin yunwa, na bashi, bari na k'ara mai wani, akwai saura a kitchen kai dai ci"
Fuska ya dan bata yace "kinsan dai bana iya cin Abinci ni kadai in ba da shi ba" ya mike tsaye ya nufo dakin Minyama.
Ina daga chan rakube ina zaune, ban saba zama haka ba in Babana na Gida, a ko da yaushe ina jikinshi in dai aka ce yana Gida.
Yana shigowa ya ganni zaune daga gefe, yace "yana ganka a nan? Bayan ga Abincinmu chan"
Na dan kalli Minyama ta min ido nace "na k'oshi" be tsaya wata-wata ba ya cicciboni.
Minyama ta dan ci gabanshu tace "Alhaji, da dai ka barshi, ba ya jin yunwa" Baba ya harareta yace "sai ki gaya min yaushe na fara cin Abinci a KT ba tare da Zaid ba, kai Matan Gidan nan ku fita idona fa" ya fita tare dani a jikinshi ya koma Parlo inda Mama ke zaune ranta a Jagule.
"Shafata kinga ga Zaid din, ashe Maryama ce ta hanashi fitowa, zauna kaji Farincikina mu ci Abinci" ko kallon mu Mama ba ta yi ba, illa hucin da take yi, shi ko Baba be lura ba, ni kuma abunki da kwadayyaye, na zauna da na sa a cokali daya a baki sai naji kamar ban taba cin Abinci mai dadin wannan ba, sai kuma na ga kamar Abincin ya min kadan.
"Baba In cinye?" da sauri Baba yace "Cinye tas Zaiduna".
A hasale Mama tace "Haba Alhaji, ba fa ka ci komai ba".
"Zaid ya nuna ya na so, a kawo min na Gandu in ci" ran Mama yayi kololuwa gun baci. Sanwan da ta dauki Awowi ta na yi, wanda tayi domin shi be ci ba, sai dan loma dayan da yayi, fuuu ta tashi ta bar wurin kamar zata tashi sama.
Shi ko Baba hankalinshi ya maido guna cewa yake "Yi Sauri ka cinye Zaiduna" ni ko na zage na cinye Shagalin nan tas.
Dan Makaho ya tsagaita yana dariyan takaici kafin ya dan sha mur tare da murza kanannen Idonshi. Labiba kuwa zuba mishi ido tayi tana sauraronshi tana son taji k'arshen Labarin, ta k'agu taji amsoshin tambayoyinta.
Ya cigaba da cewa "Shi fa Baba har ga Allah bai san Mama ta ji haushi ba, in Baba na tare da ni kowa yake mantawa, ba ya karantar damuwa a fuskan Mutum, haka ya rik'o hannuna muka shiga Dakin Mama, inda muka ganta zaune, da alama Kuka ta sha, ko bi ta kanta Baba beyi b ya fada toilet din Dakin, ya barni zaune tare da Mama.
"Ni ko na matsa gunta "Mama me ya faru kike kuka? Baba ya miki fada ne? Zance ya daina miki fada" tureni tayi daga jikinta, na sake tashi na nufota "Mama wai" kafin na gama maganar da zanyi, Zuciya ta ci Mama ta riko min kunne ta fitar dani daga dakinta ta wurgar dani a Parlo."
"Da yatsa ta nuna ni "Zaid ka fita idona, ina tausayinka duk ranar da na kama ka, dan Ubanka Abincin kai na dafa mawa? Da zaka zauna ka cinye? Maye ne kai da duk k'oshin da kayi in na dafa ma Babanka abinci sai kaci, kai baka k'oshi ne? Wallahi duk randa na sake dafa mai Abinci kaci sai na ci ubanka, shege Maye, na tsaneka Zaid, da na sani da na barar da cikinka tun kafin a haifeka" ta juya fuu tayi hanyar dakinta."
"Kalamanta kenan a gareni, ba zasu taba gushewa a k'walwata ba, ban manta su ba tsawon Shekarun nan, kinsan me nace mata?" da sauri Labiba ta gyada kai alamun "aa" ya dan murmusa yace "yarinta ma dai to, ce mata nayi nima ban sonta kuma zan sa Babana ya koreta".
"A hasale ta juyo, ta san zan aika, ji take kamar ta shak'eni na mutu, a gefenta ta wawuro wani Cokali mai yatsu, fork, daga inda take ta saito ni ta wurgo min cokalin nan cikin bacin rai tare da cewa "in ka fasa ka ci Ubanka, shegen yaro ka zame min alak'aik'ai, wallahi sai nayi maganinka".
"Cokalin nan be tsaya ko ina ba sai a cikin Idona na hagu, wani gigitacen k'ara na saki wanda ya tsorata Mama,
"Allah Sarki Babana ashe duk abunda ke faruwa yana kallonmu, a guje ya k'araso gareni inda na ke zube a k'asa, ya tariyo ni jikinshi yana jijjigani, ni ko ihu nake ina ambaton idona".
"Minyama ta fito a rude, ita kanta Mama ta mugun rudewa, Baba ya ciccibeni, yayi waje dani, Mama a rude ta bi bayanshi, Minyama ma binmu tayi a baya".
Baba be tsaya jiran Direba ba ya figi mukuli ya fada mota, itama Mama da Minyama Mota daya suka shiga, hankali a tashe suka bi bayanmu da mu kayi General Hospital.
"A Emergency a ka karbeni, a lokacin Jini ya taru a cikin Idon, likitoci suka karbeni. Suka hau aiki, Alhamdulilahi ba wani ciwo a can cikin Idon, dama kin san ido baya son bak'on abu nan dai suka diga min magani a idon, suka rufe da bandage bayan Minti Talatin zasu dawo na bude in na bude ba wani abu InshaAllahu".
"Bayani suka ma Baba da su Mama kan cewa ba wani abu, jini ya taru sakamakon wani abu da ya shiga, amma sun diga magani, a hankali zai washe" Godia Baba ya musu tare da zama, be kalli Minyama ba da ke kuka ballantana Mama da ranta ke cike da Fargaba, tsoro, dana sani, suna nan zaune har Minti 30 suka dawo don bude idon, a lokacin nima na farka daga dan baccin da na samu bayan kukan da na sha".
"Warware Bandage din Likita yayi tare da cewa Zaid Bude idonka, sai labari ya sha bambam, da nayi yunkurin budewa sai nayi sauri na rufe, na yi hakan fiye a k'irga amma na kasa budewa, ba wai don idon ya manne ba, sai don tsoro, tsoro ya hanani budewa, Likita yayi, yayi amma na k'i budewa, fita Likita yayi don ya kira su Baba, kila in Baban ya min magana zan bude, nan su Baba suka shigo har da Minyama da Mama."
"Rungumeni Baba yayi, kamar jira nake na fashe da kuka idona na mai radadi fiye da zato, Baba shima kukan yakeyi, rik'e dani sosai ya ke magana a hankali "Zaid ka bude idonka, ka ganni Baba ne, Girgiza kai kawai nakeyi, hawaye na zuba daga idona, Baba ba zan iya ba".
"Baba yana kuka Sosai yace Zaid kar kace ba zaka iya ba, ba ka so mu cigaba da zuwa Filin Polo kallon Wasan Polo? Zaid in baka bude idonka ba, ta ya zaka ga na sa riga a bai-bai? Wa zai ce Baba ka zubar da miya a rigarka? Wa zaice baba-- Baba be k'arasa ba ya fashe da wani irin Kuka, duk mai rauni sai da ya tayasu".
"Jarumina, ka bude idonka kaji? A hankalina na fara bude idon ko second 3 beyi ba nayi sauri na rufe don ji nake kamar ana barbada min barkono a ciki".
Hannu Baba ya daura a kai kamar dan yaro yace
"ta nakasa min shi, shikenan yaro na ya zama Makaho".
Likitoci dai sukayi bakin k'okarinsu don ganin na bude Ido amma na kasa, sun sake bincika idon sun tabbatar ba komai a ciki, tsoro ne kawai, sai suka yanke shawaran bari na na dan kwana biyu, k'ila kafin lokacin tsoron ya fita a raina.
"Ba inda Baba yaje a Asibiti yake kwana, ba ya cin Abinci, dangi sai tururuwan zuwa gani na suke duk da an hanasu shiga, Mama duk ta fita hayyacinta, tana tsoron abunda zai faru, har yanzu Baba bai ce mata komai ba, duk da itama da ita ake zaman Asibitin, rashin mata magana na damunta matuk'a".
Har a kwana biyun ba wani Cigaba, haka suka sallamoni, sukace da Baba a hankali zan bude Idon, Baba ya ji haushi sosai har ya kusa dukan daya daga cikin likitocin, be koma dani Gida ba, sai wucewa dani Abuja da yayi, ba wanda ya san inda muka nufa, hankalin kowa tashe yake.
Lokacin Duniya a kwance take, ya mana processing zuwa k'asar Italy don zuwa Asibiti, ba a jima ba mu ka tafi Italy daga ni sai Baba, ba wanda ya san inda muke a Gida, Minyama Kuka, Mama Kuka.
Satinmu 2 a k'asar Italy, wanda suma kamar a kasar mu Najeriya, ba su ga komai a idon ba, illa tsoron da suka gani a tattare da ni, pediatric vision therapist shine ya duk'ufa wurin ganin na bude idon ta hanyar exercising idon kuma Alhamdulilah tsoron ya ragu sosai don yanzu ina dan bude Idon hagun amma ba completely ba. sai ya zama ina kanne idon kamar wanda ke tsoron wani abu zai shiga.
Ba yanda zasuyi dani don hakan ya zame mini Habit (Dabi'a) sallamarmu sukayi muka dawo Nigeria Abuja muka dan huta. Daga kallon Baba ka san cewa bai ji dadin sakamakon da muka samu a K'asar italy ba to amma ya zaiyi? hakan yafi da ace danshi ya makance gabaki daya, da ya kalleni sai yace "Zaiduna kayi hakuri, an nakasa min kai" ni sai dai na kalleshi.
Haka muka dawo Katsina, kowa yayi farincikin ganinmu, barinma Minyama da ta kasa kawaicin sai da ta rungumeni tana hawaye, Mama kuwa tsoro ya hanata magana har yau bata san Matsayinta ba, nima ban saki jiki a gabanta ba. Baba ya rik'eni yayi dakinshi dani, mukulli ya a ma dakin, don bai yarda da kowa ba, toilet ya fada, don yin wank, su Minyama kuwa suka shiga kitchen tareda Mama don yin abincin bak'i. Minyama ta lura da dari-dari da Mama keyi, ita fa har yau bata san me ya faru da ni ba.
Dangi sai zuwa mana Barka suke, a lokacin da Baba ya fito daga wanka, ina nan zaune yace muje na ma wanka, tubeni yayi ya min wanka kafin ya shafa min mai, ina da kaya a dakinshi, ya ciro min riga da wando tazarce irin nashi, anko mukayi, sai da yayi rubutu a 'yar takarda kafin ya rik'o hanuna ya jani zuwa babban Parlo inda yake cike Mak'il da 'yanuwa da abokan arziki, harta hajiyansu Baba su Mama Asabe sun rik'ota sun kawota.
Sai da Baba ya je gabanta ya gaisheta kafin ya fara amsa gaisuwan mutane, har yanzu yana rik'e da hanuna idona daya bude daya a kanne.
Baba Sani yace "wai yaya Ali me ya samu Zaid a ido, daga asibiti ba mu kara ganinku ba?" Baba yayi murmushi mai zafi yace "Zaidu ka gaya musu meya sameka a ido ranar nan da na dawo daga lagos" idanuwa suka dawo gurina na dan sa hanuna na murza idon, na kalli Minyama da ta yi kasak'e don son jin me ya samu idon, nayi imani kuma gaban mama na ta faduwa ganin yanda tayi firifiri.
"ba Mama bace ta wurgo min cokali me yatsu a ido don wai naci abincin da ta ma Baba"
Daki ya kaure da Inallilahi wa ina ilaihir rajiun, Minyama ta bude baki cike da mamaki, ko da wasa Mama bata taba gaya mata abunda ya faru ba.
Ita ko Mama kamar kasa ta bude ta shige ciki, ta rasa mai zata yi, dangi sun samu abunda suke so, nan kowa ya samu abunda yake fada.
Gyara murya Baba yayi, yace "In Zaid yace Mama to kuwa kun san Shafa'atu yake nufi, auren Soyayya mukayi da Shafa'atu, na aureta ne saboda ta na So na, nima ina Sonta, amma meye amfanin Zamanmu in har bata son abunda na haifa?".
Wasu sukace ba amfani.
Baba yace "ba na tauye mata hak'k'inta, ina biya mata buk'atunta, laifina, na ba Zaid abincin da ta girka min, wai Abinci, ta kan abinci ta nakasa min shi.
Da kunne na na ji Shafa'atu na ce ma Zaid ta tsaneshi, da kunnena wallahi naji tace da ta san hbaka zai zame mata da ta markade cikinshi tun kafin ya zama gudan jini, wai yaro kamar Zaid ake ma wadannan maganganun".
Magana daya ce, ba zan iya zama da wacce bata son Gudan jini na ba, ba zan iya zama da wanda ta tsani farincikina ba, kin nakasa mishi ido nan gaba ban san me zaki nakasa mai ba, Shafa'atu na tsaneki kamar yanda kika tsani Zaid, a yanzu kuwa na Sakeki SAKI UKU ga takardarki.
Jikin kowa sai da yayi sanyi, Minyama na can rakube sai da gabanta ya fadi, ita ko Mama jikinta sai rawa, idanuwanta na ta ambaliyar hawaye, kana iya karanta tashin hankali daga fuskarta, bakinta har wani rawa yakeyi hak'oranta na bugun junansu da karfi, durkusawa tayi a gabanshi, tace "Alhaji, donAllah kayi hakuri, kar ka sakeni, kayi hakuri, wallahi ina son Zaid, dama sharrin shaidan ne ya sa nayi abinda nayi, kuma wallahi tsautsayi ne, ba ma da niyya nayi ba, amma tun lokacin Alhaji banda wani kwanciyar hankali, donAllah ka yarda dani, muje ciki na maka bayani, nidai kawai ka janye, ba zan iya rayuwa ba kai ba".
Mik'ewa Baba yayi yace "kin taba ganin inda aka janye Saki 3? To in baki sani ba, ba aure tsakaninmu, Aurenki ya gama a kaina.
Baba ya ja Hannuna ya yi ciki dani ya bar kowa zaune
Banda Mama da ta ke burgima a k'asa tana wasu surutai mai kama da Sambatu.
Ni Ali zaka wulakanta? Ni ke tare da kai tun kafin ka san kanka, yau ta kan yaronka ka wulakantani gaban matsiyatan k'anenka, ni Ali? Bayan son da nuna maka? Sai chan ta fashe da wani irin kuka mai karfi, da yawa sun tausaya mata, haka suka fara fita daya bayan daya.
Da k'yar Minyama da ke daskare wuri guda ta taso don lallasanta, amma cikin zafin nama Mama ta tureta wanda hakan yayi sanadin faduwar Minyama akan wani table dake kusa da kujera, Minyama ta sak'i yar k'ara, su Asabe da suka rage a parlon suka yo kanta.
Dukan Shafa'atu suka fara yi don har ga Allah ba sa sonta, Ladidi ce tayi dakin Yaya Ali don sanar dashi Minyama na fitar da jini ta goshi.
A sittin muka fito, Baba ya kamata ya rik'e don zuwa Asibiti, bayan ya kira Securities dinshi suka fitar mai da Shafa'atu daga gidan a wulakance.
A Asibiti a ka ma Minyama Dressing muka dawo Gida, ta birkice ma Baba tana kuka tace "Alhaji, ba ka kyauta ba, irin sakin da Manzo baya so, shi kayi haba Alhaji" ranshi bace "wai ke wace iri ce? Ba kiji abubuwan da tayi ta kuma ce game da Zaid ba? Kurma ce ke? Kika san tun yaushe take mai mugunta yanzu da Asirinta ya tonu ba sai ki gode ma Allah ba da a nan abun ya tsaya, Allah kadai ya san abunda take mishi, kwanaki da yake cewa tana rankwashinshi yar barikin ba karyatawa tayi ba harda kukan munafunci? Nifa da ba ke kika haifeshi ba da na ce ba kya sanshi.
Tace Alhaji wallahi Kishi ne, duk macen da zaka aura dole tayi kishi da Zaid ba laifinta bane yace Shiyasa ba zan sake Auren ba, ke kadai kin isheni, ta dan sausauto da murya tace "ko in ta sake aure zaka Maidota?" ke Hajia Maryama ki fita Idona, ke Hajia Maryama ki kiyayyeni, zan mugun bata maki rai, a duk randa kika sake min maganar Shafa'atu, na dai saketa ko? Na kuma wuce gurin, ke kuma in da Dan Cikinki zakiyi Kishi zaki sha Mamaki, zan manta da Usmanu abokina ne na miki Rashin Mutunci, haka Baba yake yi in har yana fada a kaina idonshi rufewa yakeyi, Son da Baba ke min ya wuce tunaninki Labiba, ba zaki iya gane adadin Son da yake min ba.
Minyama jikinta yayi sanyi, kar fa garin neman gira ta rasa ido, garin gyara auren wata ta bata nata, tun daga ranar bata sake maganar Mama ba,
Mu dai ba mu san ya take ba, ko ta zo Gidan ba ma sani don Already Baba ya sa matakan tsaro na kar ta sake zuwan mai Gida. Haka muka shafe Mama a rayuwanmu.
YanUnguwa, Abokanan wasana, Manya da yara suka koma ce min DANMAKAHO, don da Ido daya nake amfani, abun har ya zame min jiki, don ko da yaushe ido daya a bude daya a rufe, Baba ba ya son sunan amma ya ya iya? Niko yarinta a lokacin har kidi a ke min ana min Wakan Zaidu DanMakaho me rijiyan naira niko inta rawa na ba tare da wata damuwa ba.
Duk wanda ya kirani da DANMAKAHO amsawa nake bai dameni ba, da yawa kan ce ina da wautar 'yan fari, amma fa sosai nake da farinjini, in dai na fito, to ko ina na shiga zakiji ana DanMakaho, DanMakaho manya da yara.
Wai kin san abun mamaki?bayan sakin Mama da shekara 2 Minyama ta samu ciki har ta haifeshi bayan wata 9?
Labiba ta jinjina kai tace "ikonAllah your Sister?" kai Zaid ya daga mata yace "lokacin aka haifi Halimattu Saadiya taci sunan Hajiyar Baba, tsakanina da ita Shekaru 11, kuma wani ikonAllah daga nan Minyama bata sake ko da batan wata ba.
Darling kamar yanda Baba ke ce ma Sadiya, ta fini haske, ta na kuma da shiga rai kinsan yanda mu ke sonta kuwa?" Sosai ta samu Soyayyar mu 3, ni Baba, Minyama sai kuma dangi, wallahi ta tashi cikin So da K'aunar kowa.
Ta yi Girma da Wayau, ta shiga Makaranta lokacin nikuma nagama na shiga Secondary.
Zaid ya dan murza idonshi tare da yin wani guntun murmushin da ya burge Labiba da alama wani abu ya tuna, ta nutsu tana kallonshi ta ji muryarshi ya cigaba da cewa "wai kinsan In Baba yace mata Darling ita mai tsiwa sai tace ba Darling ba Dalo, nikuma sai ince Dalo wai kuma sai tayi ta kuka" Labiba ta murmusa itama, murmushin ya sake yace
"Ni dan Boko wai sai na ke cema Minyama Momcy"Dalo bata iya cewa Momcy ba amma da tsamin bakinta sai da ta sa mata sunan da har gobe ya bita, kinsan me take ce mata?" da sauri Labiba ta girgiza kanta tace "Momso?" dariya ta ba Zaid wanda yana yi yana murzan idonshi kuma hakoranshi sun bayyana".
Tace "Atoh, ai naji ance mata Darling tace Darlo, Mumcy kuma sai Momso ko?"
Kayyatacen murmushi yayi yace "Mancy, Mancy ta ke ce mata".
Sunan da Darlo ta sanya ma Momcy kenan, ni Mancy, Baba ma Mancy, kowa ma Mancy, rayuwarmu gwanin ban shaawa, muna da Gata, kudi, kwanciyar hankali, muna kyautata ma Makwafta da danginmu, muna taimakawa duk wanda yazo mana da kukanshi, muna sharewa ma wanda ya tunkare mu da matsalarsu hawayensu, kuma ko wani Gida a Anguwar na da kwanon Abinci rana da dare.
Labiba wallahi ba mu san akwai wani abu wai shi damuwa ba, Baba da Mancy na biya mana ko wace irin bukata.
Motoci na sunfi 3 wanda duk baba ya mallaka minsu, kudi a account dina kuwa sai na rasa me zanyi dashi.
Bamu san komai ba sai Jin Dadi, Farinciki Annashuwa.
Da lokaci yaja Baba ya sake fantamawa cikin Siyasa, Mancy ta zama Sister a General Hospital, ni kuma na tafi karatun Degree a London bayan an sha fama da Baba wanda da k'yar ya yarda na tafi karatun, amma kinsan duk hutu ina dawowa Gida, in ban zo ba su zasuje, duk a lokacin duniya na kwance.
Wani dawowa hutu da nayi na san Yayanki, Baba ya aikeni da dubu 10 Gidanku, yace ka shiga gidan da ke jikin gidan nan, ka kaima Muhammadu kace gashi ya siya Rago yayi hidimar Suna inji ni, da na tambayi Mancy waye shi sai ta ce min wani Matashi ne mai sanin ya kamata, Ba su dade da dawowa garin ba, matarshi ce ta haihu, nace "ayyah Allah sarki, barin kai mishi sakon Baba" Lokacin aka haifi Ameera diyarki.
Na koma Makaranta na hada Degree dina, mai makon na dawo gida kawai sai na Jona Masters dina bangaren abunda na karanta wato Engineering.
"Ke nagaji"
Ya fada ya na me fito da kwalin Sigari a gefen Wandonshi, kallon mamaki ta bishi dashi, a ranta tace "ba dai Sigari zai sha a gabanta ba, aa ba shi bane, ya zai sha Sigari a daki?" a sannan hancinta ya jiyo mata warin sigarin da ya dade a dakin wanda sai yanzu ta ankare da warin meye.
Ba ta lura ba sai ganin hayak'i tayi na tashi, zabura tayi ta kalleshi, ashe tuni ya kyasta sigarin nan yana bankama cikin shi hayak'i.
Baki sake Labiba ke kallonshi, DanMakaho ya wuce tunaninta, kasa daurewa tayi sai da ta tanka tace "yanzu a daki ka ke shan Taba?" banza yayi da ita, sai ma kara kunna wata da yayi.
Ba ta yi shiru ba tace "ina laifin ka fita daga waje, ni gashi hayak'i ya isheni, kasan ina da athma" tarin k'arya ta fara yi.
A tak'aice yace "Fita"
Da sauri ta tsaida tarin k'aryanta, ta na son jin karashen labarinshi, akwai tambayoyin da take son ya amsa mata tace "ai bance zan fita ba, gani nayi bai kamata ace kana shan Taba ba a daki ba".
"Dakinki ko nawa?" ya soko mata tambaya da sauri tace "aa nakane, Allah ya baka hakuri".
"Kinga bansan wannan san iyawan da kike min ko?" Murmushi tayi tace "kayi hakuri".
Jikinshi yayi sanyi "Ok, kina ji ba? Komai ya chanza ne a ranar da na dawo Naija, wani hutu mukayi na dawo Gida".
Ranar da ba zan taba Mantawa ba, muna zaune a Bukkar waje Ni,Mancy da Dalo muna shan Fruits, dama Daddy yayi tafiya kwananshi 8 ba ya gida yaje Abuja wani aiki.
Sai ko ga Motocin Daddy sun shigo harabar Gidan, gabaki daya muka tashi don murna, mu uku muka hau rigerigen karasawa ga Daddy.
Sai ya fito kanshi a dage, maimakon ya kula mu da muka zak'u da ganinshi, sai dauke kai yayi ya zagaya ta dayan side din motar, a lokacin muka fahimci cewa bayan Odilenshi akwai mutum a Motar.
Wata Mata muka ga ta fito daga bangaren da Daddy ya bude k'ofa, ta fito ta na mana kallon kaskanci, gabana ya fadi na kalli Mancy wanda itama na rantse gabanta ya fadi, duk tsawon shekarun nan, duk rashin wayau na a wannan lokacin fuskar nan bata taba gushe min ba".
A kagauce Labiba tace "Wacece?" Zaid yace "Wacce tayi sanadiyar da ake ce min DanMakaho" Labiba ta zaro Ido tace "Aunty Shafa'atu?" Zaid yace "Exactly" labiba tace "Ya akayi? How comes? Wai itace dama Aunty Shafa ta yanzu? Ba saki uku Babanku ya mata ba?".
Sigari Zaid yaja Sosai ya furzar cikin bacin rai ya cigaba da cewa
"Ni da Mancy muka tsaya kallon kallon, Dalo bata santa ba, da gudu ta karasa gun Daddy don ta rungumeshi, yanda kika san wanda Kashi ya taba, haka Daddy ya zabura da da Dalo ta nufoshi, Dalo bata fahimci yanayin Daddy, ta kara kusantoshi, da wani Zafin nama Daddy ya ture Dalo ta fadi k'asa"
Mamaki ya rufe mu, da sauri na k'arasa gun Dalo na dagata don ta fara kuka, da murmushi a fuskana mai dauke da mamaki nace "Daddy sannu da zuwa" wani irin muguwar hararar da ban taba ganin Irinta ba Daddy ya wurgeni dashi, gabana yayi mugun faduwa a lokacin da na hango tsana a idon Daddy, lokaci daya wallahi Allah na fita hayyacina".
Mancy na tsaye fa, mamaki ya gama kare mata, da k'yar ta iya daga k'afa ta karaso tace "Sannunku da zuwa, Hajia Shafa, Baban Zaid,Sannunku da zuwa".
Kamar jiranta Baba yake "Baban Zaid? Kar ki sake kirana da wannan sunan, ke ki ma fitar min a Gida Na Sakeki Saki Uku Maryama bana sonki bana son ganinki".
Wani tsalle nayi na rik'o Mancy da ke niuar zubewa,Hankalina a tashe, Mancy kuwa kasa motsi ta yi, Dalo kuwa ta fashe da kuka ta karasa gun Daddy tana jijjiga shi "Daddy me kake cewa? Me ya faru? Daddy wacece wannan?".
Turetan Daddy ya sake yi, yace "muje Hajia Shafata" Hamshakiyar sai yanzu tayi magana tace "yi gaba Alhajina gani nan zuwa" kamar jiran umurni yake yayi gaba, takowa tayi kusa da mu tana murmushi mai kama da na mugunta.
Idonta a kaina tace "Zaid, ko ince DanMakaho, ina fatan baka manta ni ba? In ka manta ni zan tuna maka, ba zan so ka manceni ba, yanda ban taba mantaka ba, kaima ba zaka taba mance ni ba, yanda na tozarta a sanadiyarka sai ka wulakanta a sanadiyata, sai ka zama abun kwatance a garin Katsina"
Ta kalli Mancy tace "Alkawari nayi, duk randa na shigo cikin gidan nan ke kuma zaki fita"
Ta kalli Sadiya tace "Dalo ko? Ba a taba baki labarina ba? Nice Aunty Shafa dinki,Matar daddy dinku, shekarunki sha biyar? Shekaruna 16 rabona da gidan nan, na kuma dawo ba fita".
Ta na kaiwa nan ta wuce ta barmu tsaye, kowannenmu hankali tashe yake, bamu da wani sauran farinciki daga ranar, galihun mu ya bace, komai ya watse mana, duniyarmu ta koma k'ankanuwa".
Labiba ta fashe da kuka tace "ni fa ban gane ba, Ina Mancy? Me ya faru bayan nan? Ni har yanzu banji me nake son ji ba, donAllah ka gaya min". Kuka take sosai.
Zaid ya tashi tsaye yace "kinsan Allah nagaji, yunwa nikeji, ya dade da nayi magana mai tsawon haka, kar ki damu wata rana zan idasa gaya miki labarin, kawai dai a gurguje Mancy na aure a Abuja ta na da diya daya".
Kina son sanin meyasa na tsinci kaina a yanayin nan? Its obvious amma na miki alkawarin ida baki labarin, but a takaice zan iya shan kwalin cigari biyar a rana shisa 'yan bencin Eskaley suke ce min MANKAS.
Hello Bibilicious fans, afuwan, komai ya daidaita nagode da adduoinku da fatan alherinku gareni.
#Ilove
#DM
#SonSoFWA
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Tara (ABUNDA YA FARU)
Labiba na ta girgiza kai tace "donAllah ka gaya min mai ya maidaka haka?".
Dan kallonta yayi lafij yace "are you not listening? Ba ki fahimci duk abunda na fada miki ba yanzu? Isnt it obvious? Matar Uba ta maidani haka, ke ko komai sai an gaya miki kafin ki fahimta?".
Sausauta murya Labiba tayi tace "naji, ina son sanin Meyasa ka fara shaye-shaye? Wacce rana ka fara shan Sigari? Meye dalilinka na shan Sigari?"
Kallonta kawai DanMakaho yayi, mai take so ya sanar da ita baya ga abunda ya gaya mata yanzu? Ya lura ta na da naci sosai, tsaki yayi ya yayi hanyar k'ofa yace;
"Nagaya miki yunwa nakeji, ina da buk'atar cin abinci".
Gunguni tayi tace "da kana jin yunwa da ba ka banka ma cikinka wuta da sassafe ba".
Waigowa yayi yace "me kikace?"
Baki ta zumburo tace "fa banyi magana ba".
Kai ya girgiza sosai yace "kina wasa dani Labiba, zan miki hankali"
Ya sa kai ya fice, da sauri ta mik'e tsaye ta figi jakkarta ta bi bayanshi.
"Tsaya, ya zaka barni a nan?" Be juyo ba yace "dama ni na kawo ki?" "To wai ta ina zan fita?" Bai fasa tafiyar ba yace "ta inda kika shigo".
"Seriously?" Bai amsata ba yayi gaba abunshi, ba ta da zabin da ya wuce ta tsallaka fasassun bulo ta ketara zuwa Gidansu.
**__**_**_**_**_**_**_
Wannan Sakin da Alhaji Ali ya mata, ya girgiza duk wani gabban jikinta, ta san dole ya dau hukunci, ta san shirun da ya mata yana neman hukuncin da ya dace da ita, amma Saki? Saki har uku? Ba ta tunanin ta canchanci Saki Uku, ita da ta soshi tsakaninta da Allah, tun bai kai haka ba, ta zauna dashi da dadi ba dadi, ta shanye bakincikin da danginshi suka ta k'unsa mata, wai ita ya saka saboda danshi? yanzu ya zata yi? Ita fa ba ta so ta yarda, don tunanin na barazanar fasa mata kwanyar kai.
Yunk'uri tayi daga inda take durk'ushe a tsakiyar unguwa ta nufa Gidan da niyar shiga, sai dai kash akwai masu tsaron Gidan, suka sa mata fullstop daga bakin gate, tayi magiyar ta yi haukan amma a banza, wani ma daga cikin securities din ya shaida mata in ta sake zuwa zai ya daureta.
Kuka Shafa'atu keyi sosai, kallo daya zakayi mata ka san tana cikin tashin hankali, da ta ga ba sarki sai Allah, sai ta ja kafarta ta nufa Unguwarsu Aminiyarta Er Rabi.
Hankali tashe ta isa Gidan, jikin kawarta ta fada ta fashe da kuka mai ban tausayi, hankalin Er Rabi ya tashi, ta shiga lallashinta da kyar ta samu ta bata labarin duk abunda ya faru.
Kirji Er Rabi ta dafe, Saki uku? Yau an shiga uku, a kan wani dalili zai sakeki? Shi be san tsautsayi ba? Hmm Shafa'atu, wallahi banga laifin kowa ba sai laifinki, tun yaushe nake binki kan ki barar da cikin Maryama? Tun yaushe nake ce miki a batar da Zaid, saboda ni wallahi na san yaron nan shi zaiyi Sillar barin gidan ashe Hassashe na ya tabbata, yau mun shiga uku, sai da Alh Ali ya fara mahaukacin Azziki zai sakeki?"
Kuka Shafa ta fashe dashi tace " nidai ki taimaka min in koma, magiya ta fara yi mata, Er Rabi ta lura kawarta na son zarewa, dawowa kusa da ita tayi, ta tariyota jikinta tana lallashinta tace "kinsan dai a yanzu ba aure tsakaninki da Ali, sai kin sake wani auren".
"Wallahi ina da wanda zai aureni ya sakoni a yau dinnan" Er Rabi tace "dakata Hajia, ina ke ina aure yau? Ko kin manta shari'ah ne? Akwai Idda a kanki, bayan nan ma dai ina so na farko ki kwantar da hankalinki, na biyu kuma ki yarda dani ki bar min komai".
Share hawayenta tayi tace "eh na bar miki komai, na yarda dake".
Washegari Er Rabi ta fita tun kan gari ya waye, Shafa'atu ba ta tashi ta ganta ba, kasa hakuri tayi tayi wanka ta fita zuwa Gidan Alhaji Ali, kamar jiya masu gadi suka ci mata mutunci, suka hanata shiga, wuri ta samu ta rakube a inda marok'a ke zama don jiran fitowan Alhaji Ali duk safiyya, ta san ya kusa fita Office, bayan 1hr sai ga Motocinshi sun fara fitowa, da sauri ta mik'e tsaye ta nufe Motar da take da tabbaci yana ciki don ya tsaya yana sallamar marok'a, yana hangota ya ciro kudadden da be san yawansu ba ya ba wani Yaronshi yace ka raba ma kowa, ya kallo driver yace mu tafi, kafin ta karaso tuni driver yayi gaba, sauri sauri gudu gudu ta bi bayan motar, daga bisani ta tsaida kekenapep tace ya kaita Office din Speaker, tana isa kuwa ta iske karnuka irin police dogs dinnan, securities suka sake mata su bisa umurnin Ogansu, a guje ta bar gurin da kyar ta tsira ta koma Gidan Er Rabi tana haki Rai a bace.
Daidai da dawowan ErRabi, rik'ota tayi ganin tana neman kifewa "Hajia Shafa'atu meya faru? Lafiya?" Tana haki tace "Karnuka Ali ya sa aka sakar min, da kyar na tsere".
Ran Er Rabi bace tace "yanzu wurin shi kikaje Shafa'atu? Gashi ya wulakantaki a banza".
Sai da nace ki bar min komai" ita dai Shafa'atu bata bar kuka da kumbure kumbure ba.
Er Rabi tace "saurareni da kyau, daga gurin mallamina nake, na kai mishi kukanki, amma yace na kaiki, don ya kalli kwayar idanunki ya karanto miki matsalolinki, kinsan shi baa mai katsalandan, shiyasa banje dake tun wuri ba, in ba shi yace azo da mutum ba, ba a mishi jaye-jaye, aikinshi kamar yankan wuka, kuma ba kya fadin damuwarki da ya kalleki ya san damuwarki ta mecece"
Shafa'atu da ta natsu tana sauraronta tace "Er Rabi, kina da tabbacin zai magance min masalata, shi da bai santa ba ta ina zai maganceta?"
Shafa'atu tace "La Ilah, ya kike magana? Wai baki yarda dani bane?".
Hawayenta ta share mata ta kwantar mata da hankali, sai da ta ga hankalinta ya dawo gareta kafin ta fara magana,
"Banda haufi kan Mallam, sai dai in ban kai mai kuka na ba, da naje yake magance minshi"
"Yace inje dake" wuf Shafa'atu tayi tace "to wai jiran me mukeyi ne? Danallah mu tafi"
Er Rabi ta mike, suka fita gabaki daya basu tsaya ko ina ba sai tashar da zai kaisu kauyen Marmara.
Babban Gidane don Gidan kadai ne gini bulo, maigadi bai tsaya musu iso ba don Er Rabi yar Gida ce.
Mallam na zaune a wani parlorn da yaji kayan alatu, rik'e yake da wani zungureriyar chasbaha a hannayennshi biyu.
Daga wani tuntun Er Rabi ta zauna, ganin haka yasa Shafa'atu zama kusa da k'afar ErRabi. Er Rabi tace "Mallam kaga nadawo ko? Mutuniyar ce ba ta da sany shiyasa muka taho yau ba gobe ba".
Mallam da tun da suka shigo yake bin Shafa'atu da wani kallo, cikin rashin sabo da irin kallon da ya ke mata ta gaisheshi, ya amsata da faraarsa.
Ya fara magana ba tare da ya daina jan Chazbaharsaba
"A gurguje Sunanki Shafa'atu, kin auri mai girma Speaker Alh Ali Zaki tun baida komai, kin so shi tsakani da Allah, ba ki taba haihuwa ba, kin shanye bakin cikin dangin Miji, kin zauna da kishiyarki lafiya ba wai don kina sonta ba, sai don Mijinku, ta haihu, son duniya Alhaji Ali ya daura ma dan nan, kika zo kika fara kishi da dan, kika nakasa mishi ido, Alhaji Ali ya miki Saki uku, yanzu kina sonshi, kina so ki dawo gidanki, kina so wannan karon in kin dawo ki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
Da mamaki yanda ya karanto mata labarin Rayuwarta take gyada kai "hakane wallahi, ka taimakeni, da na sake aure zan kashe auren in koma ya aureni, bana so na samu matsala, bana so wani ya bani matsala wurin komawa Gidana, bana son kowa ya sake daga kai ya kalleni a wulakance".
Mallam yace "kije ki gama Idda ki dawo" ba gardama ta tashi tayi gaba Er Rabi kuwa ta tsaya suka danyi magana da Mallam kafin ta fita.
Bayan ta gama Iddah
Er Rabi ta jadadda mata kan Rashin yi ma Mallam Gardama, da kuma bin duk wani abunda yace tayi, ka nan suka koma Gidan Mallam.
"Shafa'atu aikina ba kamar na saura bane, bana aikin Ammaja, ina da kudi, bana karyar aiki, bana aikin da zai warware bayan shekaru dubu, ko mai zai faru aikina nike warwareshi da hannuna, ki gaya min, zaki iya bin sharrudda na?"
Da sauri ta gyada kai, don ita ta matsu ta koma Gidan aurenta, a yan watanni hudu, ji take kamar an rura mata wutan son Alh Ali tace "Mallam na shirya, zanyi duk abunda kace"
"Aikina ba a hadashi da na kowa, ni na fara sa hannuna cikin Alamarinki, ni na bude aikin ki, in kika koma gun wani ya miki aiki daga yanzu, aikin da na riga na sanya hannu, to zaki biya da ranki, mutuwa zakiyi".
Baki na rawa tace "Ni wallahi ban san kowa ba"
Yace "kamar yanda na gaya miki a zuwanki na wanchan karon, in har na karanceki daidai, a yanzu kina so ki koma gidanki, kina so wannan karon in kin komaki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
"Eh haka ne, haka nake so"
A takaice yace "to hakan ba zai faru a yanzu ba".
Gwalalo ido tayi hankalinta tashe yace "na duba sosai, ba wani abun kirki da na hango, ba Alheri, ko kin koma ba zaki tarar da komai ba sai bakinciki da kunci, kyara, hantara da tsangwama, ke babu ma hanyar komawarki a yanzu don ba karamar tsana dangin suka miki ba, kuma akwai kariya sosai a Jikin Alhaji Ali da Iyalenshi, so a yanzu ba zai yiwu ba, shawara, ko kiyi hakuri har sai lokacin da zan dubo daidai, ko kuma shi Alhaji Alin ki hakura da shi baki daya".
Fashewa tayi da kuka tace "Bangane ba, wallahi ba zan iya hakuri da shi ba, zan jira har sai lokacin da ka gano Alheri, ko nan da shekara 50 ne".
Dariya mallam yayi yace "be ma kai shekara50 ba, shekara sha biyar(15) ne ba yawa".
Fargaba, tsoro suka dura a kirjinta a yayinda ta hango iyakar gaskiarshi, cikin rudu take cewa "bangane shekara 15 ba, Mallam donAllah bar wasa muyi maganar da ya kamata".
Dariya yayi yace "Kina ganin kamar wasa nake, kije ki gwada auren Alhaji Ali, ai ba ma zaiyiwu bane, in kina son burin ki ya cika, ki daure ki cika shekaru 15 dinnan zaki ga ribar hakuri, har ki dafa dutse ki sha romonta".
"Mallam wai wani irin Shekaru 15? In na mutu kafin nan fa? In shi ya mutu fa? Kai in akayi K'iyama kafin shekarun su zagayo fa?"
"Ke ki bar wannan tunanin bana so ki hango komai sai nasara, ki kallo nasara har kin sameshi, a lokacin Arziki ninkin ba ninkin, kuma sai yadda kikace, kuma a duk inda kike, in dai shekarun suka cika, sai ya nemoki, ko da kina kasar sin".
Shiru tayi tana wasu tunani, ta waiga ta kalli ErRabi wacce take daga mata kai alamun amincewa, basirarta ta dode, zuciyarta ta bushe, hangen dogon buri take, take zuciyarta ta dinga hasko mata abubuwan jin dadi da ke jiranta nan da shekara Sha biyar.
"Na fahimta Mallam, shekara wata rana kwana ce, kamar gobe ne, Allah ya kaimu".
Mallam ya murmusa "to akwai wasu maganin da zan dinga rubuta miki a, ke da kanki zaki dinga wanke shi"
Ido ta gwalalo, tsoro ya rufeta.
"Kwantar da hankalinki, ni zan aureki, kinga kawai da nagana aiki a kanki, da na sakeki, kawai sai ki aure tsohon mijinki".
Da yake zuciyarta ta dakushe, ba ta da mafadi, ta amince da bukatar Mallam, Mallam ya aureta, ya cigaba da aiki a kanta a cewarshi, sakinta yayi bayan Sati 1.
Abun mamaki wai don auren da sukayi na kwanan 7. Shafaatu ta samu ciki, murna Shafaatu tayi harda kuka, gani take aikin Mallam ya fara ci, bata son Mallam ko kadan, amma inta tuna nan da shekaru sha hudu da rabi zata auri masoyinta na asali sai ta ji dadi.
Ba yanda Mallam beyi kan ta zubda cikinta ba ta ki, son cikinta take sosai, kuma ita da ba ta taba ko da bari ba akan me zata zubar da cikinta, aiko ta na son abunta".
Mallam yace "shi ko ba ruwanshi"
tace "ta yarda".
Yace "Kiyi tafiyarki, ki cigaba da rayuwarki kamar kowa, 18/10/2008 Alhaji Ali zai zo wurinki a duk inda kike,ki rubuta ki ajiye, ki fara irga kwana daga yau".
Da Murna ta bar Gidan Mallam ta koma Gidan Er Rabi, ta hade kayanta da yan kudadden da take dasu ta koma Gidansu da ke Jos.
Uwarta ta shiga tashin hankali da ta gaya mata sakinta a kayi, amma ta kwantar da hankalinta ganin hankalin diyarta a kwnace yake. Zaune suke da dadi ba dadi, lokacin haihuwarta ta yayi ta haifi diya Mace suka sa mata suna Amina suna ce ata Annah.
Bata damu ta gaya ma mallam ba don ya riga da yace ba ruwanshi da diyar, don shi mallam bai san iya adadin yaranshi ba.
Haka Shafa'atu tayi rayuwar Jos da dadi ba dadi,duk da son Ali Zaki beta bacewa ba.
Shafa'atu na da Labarin Gidan Alhaji Zaki kaf dinshi, duk abunda suke ciki Er Rabi na gaya mata.
Tare take da Mahaifiyarta, da diyarta da k'aninta Hudu da ba zai wuce tsaran Zaid ba, ko ya girmeshi ba da yawa bane.
A shekararsu ta 5 ne Mamarta ta fara wani irin ciwo, sosai rashin Lafiyarta ya kwantar da ita a babban Asibitin Jos, bincike ya nuna Hantarta ce ta kumbura, kuma tana buk'arta a mata open surgery.
Hankalin Shafa'atu ya tashi, ta rasa inda zata neman kudi, gashi ba kudin nan, damar duk buga buga ce.
Duk inda zata aron kudi sai ace babu. Ta kira Er Rabi a waya tace ta ara mata dubu dari3, Er Rabi tace "wallahi bata dashi babu" hankalinta ya tashi, ErRabin ce hope dinta, yanzu ya zatayi? Katsina zuciyarta ke kira mata, kawai taje gurin Alhaji Ali.
Ba doguwar Shawara washegari ta shirya Annah, suka bi Motar haya zuwa Garin Katsina, shi kuma Hudu zai zauna wurin Mama kafin su dawo.
Suna isa duk a gajiye, Annah ta fita hayyacinta, ga yunwa ga gajiyar Mota, direct ta nufa Offishinshi duk da Marece yayi.
Wurin Secretary dinshi ta buk'aci ganinshi, Secretary tace "ba ki da appointment, kuma 4 ya wuce, baya ganin visitors, kuma he is about to leave, ki bari sai gobe" magiya ta fara yi mata, Annah ta fara kuka.
"Meke faruwa a nan?" Muryarshi ta doki kunnuwanta, da sauri ta waiga inda yake tsaye, ya fito daga office ga wasu mutane masu bakin suit da bakin Gilashi suna gefenshi.
Idonshi ya sauka kanta, nan da nan fuskarshi ta hade, kafin ta yi magana yace a kausashe "me kikeyi a nan? Bana ce kar ki kara fitowa gaban idona ba? Bance miki bana son sake ganinki ba? Bance miki na tsani ko da kalonki ba? At this instant, bace min daga gani kafin na sa a Wulak'antaki".
Dama tuni take zube gabanshi, kuka take tana girgiza kai "Alhajina, ka taimakeni, Mama na chan kwance bata da lafia"
Bai saurareta ba yayi umurni da a fitar da ita.
A wulakance a ka fitar da ita, tana kuka ta karasa Gidan Er Rabi, ErRabi ta basu Abinci, ta tausheta da cewa nan da shekara 10 zata dawo Gidanshi sai ta fanshi bakincikin da ya kunsamata na shekaru, a haka ta dinga lallabata.
"DonAllah muje ki rakani wurin Mallam, kila zai taimaka min, ga Annah ma, be ma san ya take ba, kuma diyarshi ce"
Er Rabi tayi saurin katseta, "aa Shafa'atu ba haka kukayi ba, sai da yace zai baki magani ki zubar da cikin Annah kikace aa, kikace ya bar miki cikinki, harda kuka, yace kar ki taba zuwa gabanshi da diyrki, kar ki taba ambatonshi a matsayin uban diyarki, kikace kin amince, yanzu kuma kice muje gurinshi? Karki manta yace ya gama aikinshi kanki rana kawai zaki jira, yace duk randa kika zo mishi da maganar diyarki zai kwance komai da ya kulla kinga kinyi jiran banza, Shekara 5 ta tafi a banza, komai ya tashi a banza, ke dai kiyi hakuri yanzu, gobe ki koma Jos a fara ma Mama maganin hausa zaa dace".
Kuka Shafa'atu kawai take, Washegari da Asuba tayi Sakkon komawa garin Jos ranta 6ace, ta na dawowa da kwana daya Mamarta tace ga Garinku nan, ta girgiza da mutuwar Mahaifiyarta ta sha kuka son ranta tana tausayin kanta da na kaninta Hudu, basu da kowa, basu da komai.
Rayuwa ya mata zafi, dole ta rayu kafin Burinta ya cika, dole ta zama karfin Annah da Hudu, dole duk su rayu, mikewa tayi tsaye ta fara Abincin Saidawa kamar yanda sukeyi a da, kasancewar ta iya Girki, kuma akwai Tsafta ya sa take samun Customers. Kuddirinta na nan, ranta chunkushe, Ganinta Ali zaki ne yayi sanadiyar mutuwar Mahaifiyarta, da ya taimaka mata, da amma Uwar ta aiki da ta warke, Ta k'agara Shekaru 10 su cika ta fanshe Bakincikinta.
Bayan Shekara Goma
18/10/2008
Yau take Sallah a gurin Hajiya Shafa'atu, kwalliya ta ci ta sa tsaddaden leshin da Allah kadai ya san inda aka samu kudin dinkawa, harta lalle sai da aka K'unsa mata, yanda ka san Sabuwar Amarya.
Da karfe 1 na rana Annah ta shigo dakinsu, tace "wai ni Mummy ina Baban nawa? Har yanzu bai iso ba?"
Shafa'atu ta fara girgiza kafarta, ita fa a ganinta ko garin yau be idasa wayewa ba zata ga Alinta, gashi har an fara kiraye kirayen Sallah.
Ba ta so ta sa shakku a Aikin Mallam, Shekaru 15 tayi tana jiran Ranar nan, ga ranar tazo, gashi ranan ya mata kama da sauran ranakun da suka shude, ba wani abu special game da ranar yau, ko dai tayi wauta da sakaci da ta yarda da maganganun Mallam? Ko Annah bata amsa ba ta ciro wayarta ta latso Er Rabi, Er Rabi na dauka ta fashe da kuka.
Yau waya kala kusan 10 sukayi, Er Rabi tace "Yaya ne? Ya iso ne?"
Shafaatu ta fashe da kuka tace "wani isowa? Har yanzu shiru, sai da nace miki zanzo Katsina kila gidan ya mai wahalar ganewa, er Rabi ya zanyi? Ko dai mallam ya wanke mu ne?"
Er Rabi tace "ke dai baki da hakuri, ki bari ranar yau ta kare mana kafin kiyi korafi, kinsake hakuri, kar ki sake kirana sai yazo" dif Er Rabi ta kashe waya, ran Shafaatu a bace.
ABUJA
Zuciyarshi ke mishi Zafi tun bayan Sallahr Asuba, Ji yake kamar a na yankar Naman jikinshi. Meeting sukayi , amma be fahimci komai ba.
Meke damunshi? Ya tambayi Zuciyarshi.
"SHAFA'ATU"
A takaice zuciyar ta amsa mai.
Yana son ganinta, ta na ina? Tayi aure? Akwai auren wani a kanta? Ta mutu? Da sauri ya girgiza kanshi da ke barazanar tarwatsewa, tunanin Mutuwarta na neman dauke mishi numfashi, in ta mutu sai ya bita, in kuma tana da aure ko zaiyi yawo tsirara sai ya raba auren nan ya dawo kanshi, zai biya Mijin da duk wani k'addara tashi.
"Ina zan fara nemanta?" Ya tambayi zuciyarshi.
JOS ta amsa mai, kamar ana karanto mishi abunda zaiyi haka yake ji, kurum ya kira PA dinshi yace a siya mishi ticket din Jirgi zuwa Jos, haka ko a kayi, a gurguje suka isa Airport, suka nufa Jos bayan Mintuna da basu kai 50 ba suka isa Jos.
Akwai Convoy din da suka zo tarbenshi, be manta Unguwarsu ba, ya gaya ma driver cikin 30mins suka iso Unguwarsu Shafa'atu.
Kamar ana ingizashi ya fada Gidan, ko Sallama babu, abunka da me jira, ta na zaune tsakar Gida, tana ganinshi ta mik'e tsaye, murna ya sa ta fashewa da kuka, da niyarta in yazo ta dan gasa mai gyada a hannu ta ja aji, amma ganin yanda ya shigo, ta manta da duk wani bacim rai da ya taba kunsa mata a rayuwa, Son shi ya goge mata komai, daga inda yake ya choge tsaye, hankalinshi ya dan tashi ganin ta na zubda hawaye kai ya girgiza mata tare da ware hanayenshi Biyu, da gudu ta fada jikinshi ya rungumeta gam yana samun wani irin natsuwa.
Murya a dishe yace "Shafata, ina kikaje kika barni cikin kewanki, Shafata me na miki kika barni?" Kiyi hakuri kizo mu cigaba da Zamanmu, Ina sonki, kece wacce na fara so a rayuwata" ganin yanda yake sake rungumeta ya sata cewa "Yarinya na kallonmu,Alhajina ai Sakina kayi, Saki Uku ma" da sauri ya tureta yace "Inji Ubanwa yace Sakin ki nayi? Nifa ban sakeki ba, ta ya zan rabu da rayuwata? Baki da labarin kece Rayuwata".
Dan tabe baki tayi tace "Ya kayi da Shekaru 15 da suka wuce?" Yana son yin dogon tunani amma ya kasa cewa yayi "Ni bansani ba, kar ma ki tambayeni, abunda na sani shine, san karashe rayuwata dake, ba zan taba bari kiyi man Nisa ba".
Wani Farinciki ya ziyarceta, dadi kamar tayi tsalle, "Shafata, Katsina zan tafi dake, ba zan iya kwana ba da ke ba, yau dare yayi, gobe zamu dau hanyar KT kinji?"
"To wa ya ce maka zan bika? Ina da Auren wani a kaina" ganin yana neman haukacewa tayi saurin cewa "Wallahi wasa nake maka hahaha" kamar yayi kuka yace "kina son wahalar dani ne? Ki zo mu tafi Masaukina" Cike da shagwaba tace "Auren fa? Ba zaa maida ba?"
Yace "Yanzu kuwa zaa maida, Da anyi sallahn maghrib sai a daura" Dadi kasheta, nan ta mishi introducing Annah a matsayin diyarta da Babanta ya mutu, Hudu kuma kaninta.
Yace "duk baki da damuwa, Annah Diyata ce, Hudu kuma kanena, dukkansu na dauki nauyinsu na tsaya musu, tare zamu tafi dasu".
Godia tayi mai sosai, bayan Sallahn Maghrib aka daura Aurensu sadaki dubu dari 5, a ranar duk basuyi kwanan Gidansu ba, sai a kayattacen Hotel dake Jos.
Washegari da Sassafe suka hau Jirgi suka nufi Kano, daga Kano suka hau Mota zuwa Katsina.
Suna isa KT ya bada Umurni a kai Annah da Hudu Shopping Mall suyi siyayyan Kaya.
Shikuma suka nufi Gida tare da Amaryarshi.
^^^^^^^
Kiraye kirayen Sallahr Azahar akeyi, ashe ta dade a wurin Dan Makaho, ita ina ta lura lokaci ya ja? Wuri ta samu ta buga tagumi, tana ta nazarin Labarin danMakaho, wayarta tayi k'ara Jay ta gani a gaban screen.
Numfashi ta ja ta saki ta dauka wayar da Sallama "Labeenah, ina kika shigane? Nayi missing dinki sosai" In Ina ta fara "Eh wallahi lecture mukeyi, nima nayi missing dinka"
"Yaushe zaki ban lokaci na zo Katsina?" Murmushi tayi tace "duk lokacin da kazo, ina maraba da kai"
Hangoshi tayi daga inda take, ya dawo dauke da wani abu a hannu, mancewa tayi da Wayar da take ta mike zuruf ta kuka tsallaka fasasssun Blocks din ta bishi daki har ta kusa bashi tsoro.
"Ke wai meyasa baki da hankali ne? Ta ya zaki ta shigo min daki ne? Wato ba kiji warning din da na miki ba ko?"
Baki ta tabe ta kalli ledar hannunshi, Bread ne sai Sardines, tace "ni karashen labarina nazo ji"
"To ba zaa bada ba"
Wuri ta samu ta zauna harda daura kafa daya kan daya tace "gama ci dai".
Tsaki yayi, gardama da ita aikin banza ne ya bude Kifin gwangwaninshi, ya na dangwala mai din da bread yana ci, be kulata ba, ita kuma latsar wayarta kawai take.
Daga waje kuwa Blocks aka kawo da Cement da Yashi zaa fara aiki.
"Kina ji ba?" Da ya gama kenan, da sauri ta ajiye wayar tace "eh ina jinka.
"Jikin Mancy Rawa kawai yake, rik'ota nayi na mata garkuwa da kafada na" ban bi ta kan Dalo da ke kuka ba, Mancy ta zare jikinta daga gareni tayi hanyar cikin gida duk sai muka bita.
A parlo muka tsaya inda muka ga Baba da Anty Shafa'atu suna magana, ce mishi take ita ba zata iya zama a dakunan nan ba, bata san surkullen da ke ciki ba, kafin ya bata amsa ya hngo mu, Baba na ganinmu kamar an aiko mai da mutuwa, dif annurin fuskarshi ya dauke, ya ja hannunta ya fita, muma muka bishi riiiiiii,
Mancy ta dan Matsa kusa dashi tace "ka riga da ka furta, ba aure tsakaninmu, aure ya k'are, ina so na san me na maka da na chanchaci Saki Uku gaban Yarana?" Kamar jira yake ya hau kan Mancy da duka, hankalina ya tashi na shiga tsakaninsu, na janye Mancy ina ma Baba Kallon Mamaki.
"Ki fitar min A Gida Maryama, ki kwashi yaranki ki bar min Gida bana son ganinku ku duka, na tsaneku"
Mancy ta share hawayenta, nikuma ina tsaye kamar gunki, Dalo kuwa na zaune dirshen a k'asa.
Mancy ta matsa kusa da Dalo ta tallafota gabaki daya.
Yanayin da ban taba ganin Mancy a ciki ba, ta bude murya tace "Zaid, Sadiya, zamana ya k'are a gidan nan, rabonku ne dama ya kawoni gidan nan, ku sani Nan Gidan Ubanku ne, ba ku da inda ya fi nan, ko ma mai zai faru, i mean no matter what will happen, this is Your Father's house, kar ku taba mantawa, kar ku manta da kalar Soyayyar da ke tsakaninku, kar ku bari kowa ya shiga tsakaninku"
Hannayenta ta daga Sama "Ya Allah, ga Bayinka nan, Allah ga Zaid, Allah ga Sadiya, Allah kaine gatansu,Allah ka sakama duk wanda aka zalunta"
Shafa'atu ta fashe da Ihu "Ni Alhaji sai dai ka Sakeni, Matarka so take ta kafurtani".
Aiko ya yunkuro zai bige Mancy nayi saurin tareshi ina girgiza kai don ban ma da k'arfin magana.
Ki tafi da yaranki" Baba ya sake jaddada mata, tace "ba inda zani dasu, nan ne gidansu, gidan ubansu, Ba inda zani dasu, kamar Zaid? Yana Masters? Ina zani dashi? Dalo da ba nono take sha ba ina zani da ita? Ai suna gidan ubansu, su ba Mata bane balle a sake su, 'Ya'yane su".
Nan suka fara hayaniya, da karfi, ban taba sanin Mancy ta iya fada, don ko an kure hakurinta ne.
Kinsan mai hakuri in an taboshi.
Shafa'atu tace "kinga Maryama rufin Asirinki ki tafi dasu, kika san me zan musu in suka zauna? Ba kya tsorona ne? Ki tafi dasu, wannan Gidan daga ni sai yaran da zan haifa ma Alhajina Magada Babansu".
"Huh tsoro? Bana Shafa'atu, bana tsoron makircinki, ko da ba tsoronki nake ba, kawai na fi so a zauna lafia, kuma yarane gasu nan, ki sa kansu gabas ki yanke, suna Gidan Ubansu, haihuwa kuma Allah ya kawo miki 100, duk dai yaran da zaki haifa ba zaki taba haihuwan Yayan Zaid ba, koma Sadiya, dole sai Kannensu zaki haifa".
Sosai kalaman Maryama suka bata haushi, me zata mata ta bak'anta mata rai? Alhaji wai tsayawa zakayi tana gaya min magana? Wallahi sai dai ka sakeni".
Yana jin haka ya rufe Mancy da duka a karo na biyu, na shiga tsakani ya hada dani, Dalo ma ta shiga tsakani aka hada da ita, ya dinga dukanmu ko ta ina yana halbemu, mu ko muna rungume da junanmu, Dalo sai kuka mai sauti take.
:::::
Zaune yake da 'yar Matarshi, da jaririnsu, wani abu yake ji daga Makwaftanshi kamar hayaniya, kasa kunne yayi sosai,
Gabanshi ya yanke ya fadi, Gidan da ya sani a matsayin Gida da suka kansu a kan Soyayya, Aminci da juna, abunda be taba ji ba, hayaniya, ya ji kamar ana maganar Saki, ya ji kamar maganar Barin Gida ake, wacece Matar nan da ta shigo tsakanin Gidan nan da basu son komai ba sai SO?.
Matarshi ya kalla yace "Aseena, akwai matsala". A tsorace tace "Wai Sakin Mancy aka yi? Inallilahi" kafin ya bata amsa sukaji kamar kuka, da suka kasa kunnensu sai sukaji ashe dukansu yakeyi, da sauri suka tashi a sittin sukayi Gidan Alh Ali Zaki.
Kamar an tara Mutane don wurin cike yake, kowa mamakin Alh Ali yake, yau shine yake dukan Farincikinshi? Da girman Zaid yake dukanshi, yake dukan Sadiya diyar da yake gani itace Yar Gwal, ga matar da yake so kamar ranshi, yau itace yake duka da hannu duk ya galabaitar da ita, rigarta har ya yage har kana iya hango abunda ke ciki, da Zaid ya tashi taimaka mata sai ya sa security su rik'eshi.
Manyan Unguwan sai magana suke mishi suna rokonshi da ya barsu haka, amma be tanka kowa ba.
Muhammad ya shigo da Matarshi Asee, kutsawa sukayi tayi, gidan kamar ana shooting film, kutsawa yayi ya shiga, matarshi ta bi bayanshi, daidai nan Alhaji Zaki ya daga wani katako zai kwala ma Mancy kenan ya karasa da gudu.
"Haba Alhaji, Haba, menene haka? Meya sameka Alhaji? Wallahi ba Girmanka bane? Inalillahi wa ina ilaihir rajiun"
Hajiya Shafa'atu ta dago ta kalli Muhammad da tsana, shi ko Alhaji samun kanshi yayi da maimaita Inalillahi wa ina ilaihir rajiun" waigawa yayi yana kallon su yashe a k'asa, abun alfaharinshi, dukkansu yashe a k'asa.
Hajia Shafa'atu tace "nifa su tafi, ina son na huta" kamar an ingiza shi yace "duk ku fitar min daga Gida, yan iska shegu, duk na tsaneku".
"Alhaji ina kake so suje? Basu fa da inda ya wuce nan" ni wallahi sai sun fitar min a Gida, Muhammadu, ba na k'aunar ganinsu"
DanMakaho ya kalli Labiba sosai yace "Kinsan Unguwar nan kaf, ba wanda nake ganin mutuncinshi irin Yayanki?" Labiba ta murmusa tace "Yayana na da kwarjini" yace "ya min abunda ba zan taba mantawa ba, zuwa yayi ya dago ni ya rungumeni, ya lallasheni ya rada min a kunne, ka zama k'arfin Mahaifiyarka da kanwarka, tashi ka rik'o Dalo, muje gidana muyi magana".
Umurninshi na bi, na tashi na mik'ar da Dalo da ke kwance magashiyan a k'asa. Yayanki ya matsa kusa da Matarshi, ya karbi jaririn hannunta yace ki taimaka ma Mancy, bin umurninshi tayi, ta daga ta ta riko hannunta, ta ja ta, ba gardama Mancy ta bi bayanta.
Sosai mutane suka tausaya mana, ina jiyo muryar wani yana cewa "Me ya samu Gidan nan? Me ya samu jin dadi da walwalar Gidan nan" wani yace "ko nayi rantsuwa ba kaffara, wanchan ce, itace Ummul Abais" Wallahi DanMakaho Allah ya saka muku, Allah ya bi muku hakkinku".
Ba mu ce komai ba muka fita zuwa Gidan Yayanki, kan tabarman da suke zaune na kwantar da Dalo, na yi hanyar fita Mancy tace ma Yayanki donAllah kamo min shi, a wahalce take magana.
Mallam Muhammad yace ina zaka?" Zuwa zanyi ya gaya min dalili? Me muka mishi ya tsane mu, Mallam Muhammad Babanmu ya wulakanta mu gaban mutane, Babanmu ya daga hannu ya dake mu gaban mutane, me muka mishi? Me ya chanzashi".
"Zaid"
Mancy tayi kirana.
Na dan choge na tsaya tace "kazo ka zauna, donAllah, kana da Uwa, and i promise you, ba za ku bar Gidan Ubanku ba"
"Mancy, zaman me zamuyi ba kya ciki? Ta ya zamu fara rayuwa a Gidan nan ba da ke ba, Mancy kafarki kafarmu Allah".
Mancy ta girgiza kai, ta kawar da maganar "Maman Amira DonAllah kina da Panadol a ba Sadiya?".
Eh barin dauko mata, ta shiga Ciki, baban Amira ya bi bayan Matarshi.
Mancy ta matso kusa dani ta rik'oni tace "Stay Strong, kaine Gatan Dalo in bana nan".
"Mancy".
Ta katseni "Zaid, kayi min Alakawari, no matter what happens, ba zaka taba barin Gida ba, aure kawai zai rabaka da Gida, zaka kula da Sadiya, zaka kula min da kanku"
"Mancy"
"Zaid, DonAllah".
"Mancy, ba ki ga kallon da Baba ke mana ba? Ya tsanemu fa"
"Still Zaiduna, you wont leave home".
Kai na gyada mata nace "I wont leave home".
Dalo ta sha panadol, amma masassara ta rufeta, kinga yanda muka damu, lokacin Maghrib Yayanki ya sani Alwala don zuwa masallaci, na bar Mancy da Dalo tare da Antynki.
A waje sai kallona ake tayi, wai kinsan me nagani kofar Gidanmu? Labiba ta girgiza kai yace "Katuwar Mota nagani, tana kwashe kayayyaki wanda kallo daya na musu na san kayan dakin Mancy ne da nawa" nufansu nayi, amma yayanki ya rikoni tare da girgiza min kai, yace mu tafi Masallaci kaji?" Jikina rawa yake, idona ya ciko da hawaye, lallai baba yana son Wulakanta mu.
A gidan Yayanki muka kwana, daki daya ya bamu, Mancy tayi ta mishi godia, yace "haba Mancy, ai kowa ya san ke Uwa ce a Anguwar nan, duk me zamu miki ba zamu taba biyanki Alheranki ba".
Washegari Mancy tace "Zaid, Sadiya, yau zan koma Kano gidan Yaya"
Nace Mancy Dalo bata da karfin jikinta Masassara takeyi, ina zaki tafi ki barta? Ni ya zanyi? Mancy karki tafi? Kar ki juya mana baya donAllah, kar ki barmu, atleast not now, kina ganin korar da ya mana, na gya miki an fitar da kayayyakinmu tas".
Mancy tace "Zaid ya zanyi? Wa ke gareni duk dunia in ba Yayana ba? Ina zanje? Sakina yayi fa, saki 3, ina na nufa? Nan gidan zan ta zama? Ai ba zaiyiwu ba, kuna da Mahaifi, da ranshi, yanzu ba anjima ba zan raku Gida, nikuma na wuce, ina so kuyi hakuri da duk yanda rayuwa ta zo muku, donAllah kuyi hakuri, ina sonku sosai, fiye da rayuwa da kanta".
"Mancy"
Ta katseni tace "Zaid mun riga da mun gama maganar nan, dole ku koma Gidan ubanku, whatever happens he is still your Father, ku tashi mu tafi, so nake kafin karfe 11 in isa Kano".
Labiba banson ma Mancy gardama don wallahi a daren ranan bata runtsa ba, a kan idona tayi ta kuka, zuciyata ta karye amma sai nayi kamar bacci nake, banson ta sha wahalata shiyasa kawai na share, na rike dalo sosai ta ma Yayanki Godia, muka fita muka nufa Gida, dukkanmu gabanmu na faduwa.
Karfe 8 saura muka shiga Gida.
Da sallama Mancy ce me k'arfin halin Rafka Sallama.
Wata Yarinya da bata wuce saar Dalo ba ta fito daga kitchen tana mana kallon wulakanci, sai ga wani shikuma ya fito daga daki wanda nawa ne.
Hannayenmu Mancy ta ja, har cikin parlo, ta zaunar damu, Nasiha ta cigaba da yi mana.
Sallama aka sake yi muka amsa Yan Gidansu Babanmu ne, su Aunty Asabe da Baba Sani, Maza da Matansu, sun kai su 15. Wurin mu suka nufa, Mancy ta tashi ta taryesu da faraa, suko kallon tausayi suke mata.
Ina kwananku muka gaishesu, suka amsa Baba Sani yace "Maryama ashe abunda ya faru kenan? Wallahi sai yau da asuba wani abokina ke gaya min" tace "Ya muka iya da k'addara Baba Sani, zama ne ya k'are" duk su Aunty Asabe suka ma Mancy Jaje don sosai suke sonta.
Wannan yarinyar tayi hanyar Dakin Baba da gudu ta na kiran Mummy, Mummy zo kiga wasu sun shigo mana Gida.
Da ido duk muka bita, ba da jimawa ba sai ga shi sun fito Mama da Anty Shafa'atu.
Da Mamaki kowa yace "Shafa'atu"
Ita ko ta shigo ta na yatsuna Baba na binta a baya kamar Rakumi da Akala.
"Su waye suka shigo mana Gida da farar safiya kamar masu bin bashi?"
Kamar kare baba ya fara haushi "Eh.. su waye suke mana Sauko da sassafen nan?"
Asabe tace "Yaya mune, mai Shafa'atu takeyi a gidan nan?"
"Shafa'atu Matata ce, Jiya aka daura mana Aure a Jos, dama chan kune munafukan da kuka sani Sakinta"
Nan aka fara kallonkallo.
Mancy ta mik'e da alamu ba su ma lura da mu ba tace "Alhaji ka sa an firda min kaya ina aka kaisu?" Kamar wuta ya taso, Gidan da na daukoki chan nace a kai maki, don maita ashe baku tafi ba?".
Tace "Nagode da ka sa a kaimin kayyayakina, tafiya kuma yanzu zan wuce Kano, ga dai Yaranka nan".
Shafa'atu tace "Alhaji nan zata bar maka su" nan ya hayayyak'o "Kai ku fitar min a Gida, Wallahi ba zasu zauna min a Gida ba".
Baba Sani yace "Ahh Yaya, ina zata kaisu? Tunda ka saketa, ai yara nakane, Ina zata da Zaid dan Shekara 25 Sadiya yar shekara 15?".
Wani abu kamar Hauka Baba ya fara "Sani ka fita Idona, ina ruwanka da Sabgar Gidana? In yaran kake so ka dauke su ka tafi dasu, nidai ku fita harkana, banda 'ya'ya in ba Annah ba ita kadai ce diyata".
"Wacece Annah?" Injisu. Aunty Shafa'atu tace "Our Only Daughter ga ta tsaye" kowa ya bi Annah da ido, sai faman harare harare take.
Su Asabe suka fashe da kuka, Waiyo Yayanmu me aka maidaka? Zaka dauki diyar da ba taka ba kace itace kadai diyarka? Yayanmu ka manta yaranka mafi soyuwa gareka Zaid da Sadiya?".
Shafa'atu ta fashe da kuka cike da kissa "Yanzu haka Alhaji yanuwanka zasu dinga min gori?ni gaskia ka sakeni ba zan iya ba, dama chan yanuwanka sun tsaneni".
Hargagi ya fara "Kai Buhun Uban da ya k'ara cewa Zaid da Sadiya ne mafi soyuwa a gareni, kai zan fa kulleku, ku fitar min a gida dukkanku, wallahi duk ku fice min, na sake ganin kafar dayanku a cikin Gidana sai na sa a kulle ku a Cell, yan iska, Matsiyata".
Ya juya garemu yace "Ku kuma na sake bude ido na ganku a gidan nan wallahi zan iya kasheku, don baku san yanda nakeji game daku ba na tsaneku sosai".
Wuf Mancy tayi ta mik'e tsaye "Alhaji Sai ka Kashe su fa kace?" Kina waswasi ne? To ki bari na k'ara ganinsu a cikin Gida kika ga mai zan musu.
"Alhaji ban san mai sihiri ya maidaka ba, Yaya Asabe sai kun tashi tsaye kan Danuwanku, a baiyane kunga dai ba yin kanshi bane, sai kuna sanya shi a addua, nima zan taya ku da Addua a matsayinshi na Uban 'ya'yana amma a yanzu zan dauki mataki, duk abunda ya sami yarana a cikin Gidan nan to shine".
Shafaatu tace "to ki tafi dasu mana in ba kya son komai ya samesu, ai rufin Asirinsu su biki kawai, don ko be kashesu ba, zaman gidan nan sai ya gagaresu, ba Ubanda zai tsaya musu duk fadin Kt, so kinga da su biki daga baya gwara kin tasa keyarsu kun wuce yanzu".
Mancy tace "Abunda ba ki gane ba Hajia Shafa'atu shine, Zaid da Sadiya ba inda zasu, ba wanda zai rabasu da Gidan Ubansu, ko da Uban nasu ne kam, kuma in kinga dama duk ranar Allah ki dinga sa wuk'a kina yankar namansu kuna miya, sai kuma wanda zai tsaya musu? Allah, shi zai tsaya musu, ki ja dashi in kina iyawa".
Ta juya ta kalli Yanuwan Baba tace "DonAllah wa zai kaini Gidan Sarki? Ai in ba wanda ya isa da kai Alhaji, ai baka fi k'arfin hukuma ba" Baba Sani da ranshi ya gama 6aci yace "Muje hajia Maryam, muje ni zan kaiki".
Baba Aminu yace "nima zanje, don wallahi wannan Makirar Matar ba zamu barta haka ba" Su Aunty Asabe sukace muma zamu.
"Wai ni zaku kai k'ara? Ni zaku hade ma kai? Ni zaku tona ma Asiri?".
Hajia Shafa'atu tace "Dallah, duk burga ce, suje muga zasu iya Ja da kai" kamar sakarai yace "to ku tafi din, matsiyata, bani ba ku, kar shegen da ya sake zuwa min Gida".
Ba wanda ya kulashi, sukayi gaba,
Dama Motoci kusan 4 suka zo, kowannensu ya samu Wuri ya zauna, suka nufi Gidan Sarki suna sake yi wa Juna Jaje.
Da suka iso Gidan mai Girma Sarkin Katsina, ba su sha wahalan shiga ba don Amaryar Sarki kawar Mancy ce, tun zuwansu makka suke zumunci.
Sasshenta ta shiga, ita kadai, duk sauran na Mota, bayan su gaisa ta gaya ma kawarta tazo ganin Sarki ne.
Gimbiya tace "kin ko ci saa yau kwanana ne, ya kusa shiga Fada, barin ga in yana iya ganinki yanzu".
Mancy tace "ba ni kadai bane, sauran na Mota".
Gimbiya tace "toufa, bari naje naga"
Bayan kusan minti 40 sai ga ta ta dawo "Afuwan Kawata, ashe yana Karamin Fada, yana ganin wasu baki ne, duk da haka kuna iya shiga" Mancy ta mik'e tace "barin je na kira sauran".
Sun samu shiga Fadar, da biyayya suka gaida Sarki.
Wasu tsofi Mata guda biyu na zaune, sai kusa da Sarki wani mutum ne, sai dogarai 4 sai magatakarda.
Mancy ta zauna kusa da k'afar daya daga cikin tsofin ta gaishesu, su Aunty Asabe duk a ka gaigaisa.
Gimbiya tace "Mai Martaba, wannan k'awata ce, ta buk'aci ganinka, duk da na san yau ba ranar ganinka bane na nemi a mana alfarma aji da me tazo" cike da izza ya gyada kai".
Daya daga cikin dogarawa yace "Gyara Kintsi, matso gaba ki fadi damuwarki".
Ko dar Mancy bata ji ba ta matsa kusa da Kafar Sarki, wanda gefenshi wani mutumi ne sanye da Babbar Riga.
"Sunana Maryam, wanchan babban da na ne sunanshi Zaid, waccan itace auta ta sunanta Sadiya, wadannan k'annen Mijina ne na da".
Sarki ya gyada kai alamun yana ji "Muna zaman lafiya da Uban yarana, tafiya yayi, yana dawowa ya min Saki Uku, yace kuma dole da yarana zan tafi, ina zani dasu Mai Martaba? Nace mishi da yara kanannene sai na tafi dasu amma ni ba zan tafi da baligai ko ina ba, banda kowa sai Yayana, ina yake so naje dasu? Wannan shekararta 15, wannan shekarunshi 25 masters ma yakeyi, ina zan kaisu? In ya sakeni me zai sa ya koresu, har yana ikirarin ya bude ido ya sake ganinsu zai iya kashesu?".
Sarki yace "Wanene Mijinki? Yana gari? In yana gari a kirawo manshi yanzu, in be gari na bashi kwana biyu yazo ina kiranshi".
Wani bafade yace "Kiran Sarki Doka".
Mancy tace "Yana Gida, Alhaji Ali Zaki".
Mutumin kusa da Sarki yace "Speaker?" Sai a sannan ta kalli mutumin, daga kai tayi tace "eh shine".
Sarki yace "A aika ma Ali Zaki Sammaci, ace ina kiranshi yanzu".
Baba Sani yace "Harda Matarshi wacce itace ummulabaisi, ita ce ta sa ya saketa, muma yanuwanshi ya wulakantamu, sihiri ta mishi"
Sarki yace "A zo da matarshi".
Suna nan zaune jugumjugum magatakarda ya fita da wani zuwa aiken Sarki.
Da Sak'o ya je musu, Shafa'atu taso ya bijire ya k'i zuwa, amma kiran Sarki ba wasa ba, lallashinta yayi ta hanyar nuna mata illan rashin zuwan, rashin zuwan na iya kawo mishi cikas a Siyasar shi, kuma shi Sarki Uban kowa ne.
Da k'yar ta zura wani minnirin mayafi suka bi bayan dogarai bayan tace Hudu ya kula da Annah.
Bayan Zuwansu ne Alhaji Ali kunya duk ta rufeshi ganinshi gaban Sarki, ga kuma Alhaji Ibrahim Iroro, ita uwar gayyan sai da ta ji shakkun Sarki duk da tsagerancinta.
Sarki ya bada umurni, a ka buk'aci Mancy da ta sake fadan abunda ta fada, kamar yanda ta fada dazun haka ta sake fada.
Sarki ya tambayeshi "meye dalilinka na cewa ba zaka rik'e yaranka ba?".
Alhaji Ali ya keta zufa, gaban Shafa'atu na faduwa Allah ya sa kar yace ita ce bata so.
"Allah ya kara ma Imani, wallahi bana kaunar bude idona na zuba kansu, wallahi banson ganinsu, na tsanesu".
Sarki yace "Aiko ba ka isa ba, wani yace ka haifesu? To ba tare da bata lokaci ba, wannan abun mai sauki ne, a Addinance, tunda Yara Baligai ne, kai ke da hakkin daukarsu, da ace yaran k'anana ne sai ta daukesu, amma wadannan yara gurinka zasu zauna Alhaji Ali".
Da sauri yace "donAllah aa, zan bata ko nawa ne na kula dasu, zan dauki nauyinsu, nidai kawai su bar min gidana".
Sarki yace "to ke kinji, yace zai dauki nauyinsu, amma su tafi da ke".
Mancy tace "Aa Allah ya kara maka Imani, Saki Uku ya min, shari'ah ta bashi damar rik'e Baligai, Shari'ah ta hutar dani da gajaniyarsu tunda ba yara kanana ne dani ba, Allah ya ja nisan kwana, in na samu Miji aure zanyi, ya zanyi in be amince da na zauna da Yarana ba? Ya zanyi in yace na zaba ko aurenshi ko yarana? Ya zanyi in ya fasa aurena saboda Ina da Yara Baligai? Ban k'i su dinga zuwa min ziyara ba, Allah ya ja nisan takawa, ban amince ba, hankalina zaifi kwanciya in Yarana na gidan Ubansu".
Sarki ya jinjina kai yace "Alhaji Ali, Yara zasu zauna a gurinka, zaka dauki nauyinsu kamar yanda duk wani Uba zaiyi, cin su, shan su, suturarsu, iliminsu, tarbiyarsu, komai, duka, kayi maganar zaka iya kashesu, zan sanya ido a kanka, in ka karya doka, doka zata taka ka, kasan kai sananne ne, kayi tunanin mai zai faru a rayuwarka ta siyasa in nace zan tona asirinka, Yara naka ne, amma Girma ya bani Iko a kanka da yaranka da duk wani rai da ke cikin garin katsina da kewaye, ina fatar ka fahimceni".
Kan Alhaji Ali a k'asa ya kasa magana, sai da wani dogari ya daka mai tsawa kafin ya amsa baki na rawa "to to rankai dade".
Mancy ta murmusa tace "Allah ya kara ma Girma da daukaka da daraja, nagode kwarai, ka gama min komai, Allah ya ja da rai ya kera lafiya, Ina neman alfarma a bani kudin motar zuwa Kano".
Duk suka bita da ido, Asabe tace "Maryama yo ai baki gama ba, ko kin manta da Shafa'atu ce silar sakinki, ba kiyi maganar cin kashin da ta sa Yaya ya mana ba".
Mancy tace "Yaya Asabe, damuwata sune 'ya'yana tunda na kwatar musu 'yancinsu banda sauran damuwa, kuma Saki dai ya riga da yayi har uku ba kome, sauran kuma nakune, Allah ya sa a dace".
Mamakinta suke gabaki daya, rana daya ta rikide musu, kamar ba Maryama mai hakuri da kawaici ba.
Sarki yace "a bata kudin Mota zuwa Kano" na kusa da shi yace "ai kano din mukayi, ni da su Hajia sai mu sauketa".
Hajiya da kawarta sukace "aiko dai sai muyi ta tafiya".
Sarki yace "to barka".
Mancy ta tako har gaban Zaid da Dalo inda fuskokinsu sunyi ja saboda kuka, ta dago su gabaki daya tace
"Ina Sonku, kar ku taba mantawa"
Dalo na kuka tace "Mancy karki tafi ba dani ba"
Mancy a girgiza kai tace "mun gama magana Sadiya, ki kula da kanki, Allah ya miki Albarka".
Ta rik'e hannun Zaid da yake ta faman murzan idon Hagunshi tace "sai Idon ya kara kankancewa Zaidu? Kabar murzan idon nan, bana so"
Gyada kai yayi alamun to, bubbuga kumatunshi tayi a hankali tace "Stay Strong".
Zan kiraku kunji?. Ta rungumesu sosai kafin tace ku zauna. Umurninta suka bi suna kuka ita kuma ta fita daga Fadar da sauri, Zaid ya dago kannennen idonshi ya bita da kallo har ta bace ma ganinshi.
Abokan tafiya suka tashi suka ma Sarki sallama suka bi bayan Mancy.
Zaid ya runtse idonshi ya kalli Labiba da ta ke ta sharan hawaye yace "ki tafi Marece yayi" karfe 5 da ta duba agogonta.
Majina ta ja tace "Oh Allah, ban san lokaci ya ja haka ba, zan dawo gobe, zan idasa jin labarin kaji Yayana?"
Banza yayi da ita ya dauko sigari ya sa a baki ya kyasya lighter ya fara zuk'a.
Jakarta ta dauka ta bude kofar sai dai me? Gani tayi har an gama Shafe, an gyara passage dinta, duk an gama gyran bulo din, suna ina har aka gyara wurin? Duk suna aikinme basu san a gyara ba, lallai ta shagala da yawa. Kofar ta bude sosai yanda Zaid zai hango Bangon gidan.
Jinjina kai yayi yace "Wow, har an gyara".
"Yanzu ni ta ina zan bi?" Yace "ta Gate mana ko zaki fasa bangon ne ki fita sai a sake gyarawa?".
Tace "muje donAllah ka rakani" "saboda ni na shigo dake?" Ya tambayeta cike da tsageranci.
"DonAllah nace Yayana"
Banza yayi ya kyaleta, ganin tana k'ara bata lokaci ne ya sa ta sakin kofar ta fita tana mai tafiya sadaf sadaf kamar mai shirin Sata.
Gabaki dayansu suna zaune a Bukka, nan suke zaune duk yammaci su sha Fruits, ganin wata sukayi ta wuce sutana tafiya kamar barauniya tana tafiya tana waigen baya, a tare suka mike tsaye.
Hudu ne ya daka mata tsawa yace "Keeee"
Sai da hanjin Labiba suka kada, chak ta tsaya ta kasa juyowa, jikinta sai rawa yake. Duk suka nufota.
"Uwar wacece ke? Daga ina, barin zo in ga fuskarki" cewar Anty Shafa'atu.
Labiba a tsorace ta fara juyowa taji muryanshi na cewa;
"Beebs, donot turn".
Fasa juyowan tayi ta tsaya tana mai kallon gate, su kuma hudun suka juya suna kallon DanMakahon dake nufosu sauri-sauri gudu-gudu".
Yana zuwa daidai Labiba ya finciko hannunta ya yi gaba ita ko ta bishi a baya hannunsu rike da juna.
Muryan Aunty Shafa'atu sukaji tana cewa "Yau Mun Shiga Uku Alhaji, Karuwa har cikin Gida".
Hello Lovers, Vote and Comment line by line please.
#1love
#DM
#FWASonSo
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: BABI NA GOMA1⃣0⃣
Kalmar Karuwa shine sanadiyar tsayawarta cak, duk wani lakka na jikinta ji tayi kamar an zaresu, a lokaci daya kuma jikinta ya fara rawa.
Baki na rawa tace
"ka tsaya, ni ba karuwa bace, wallahi ni ba ita bace"
K'ara damk'e hannunta yayi ya jata har sai da suka yi daf da fita Gidan.
Muryar Alhaji Zaki sukaji na cewa "Shege, Tsinanne, karuwa kake kawo man Gida ko? Kanwartaka bata isheka ba? Sai ka kawo na waje Gida?".
"Ya Rabb" ta furta da k'arfi, be sake hannunta ba ya cigaba da janta, togewa tayi, ta k'i gaba ta k'i baya, gabanta ya tsaya, ya rik'o kafadunta da duka hanayenshi,
Kai ya girgiza mata, da dan karfi tace
"Tsine maka fa yakeyi, Shegantaka yakeyi, ko baka ki bane? mu koma in mishi bayani, mu koma na gaya mishi ni ba karuwa bace".
Hannunta ya rik'e ya cigaba da janta har suka fita daga gidan baki daya, ko da suka fita Gate be sakar mata hannu ba, haushinshi taji karo na farko a rayuwarta, da kyar ta samu ta fincike hannunta daga nashi.
Ta waiga ta kalli Unguwarsu da ke busy asaboda marece yayi, ta sa hannu ta shafi goshinta ta da ya danyi zufa.
"Baba ba karuwa bace, abunda ya kamata kace kenan, amma ka kasa, har sai yaushe zaka cigaba da karban laifin da ba naka ba? Shiru na nufin fa ka amince da kayi abunda ba kayi ba".
Hannu ya sa ya murji idonshi "Ba zaki gane ba, yin maganata bata da wani amfani".
Ta katseshi ta hanyar cewa "sai kayi, kayi magana ko bata da amfani, yafi ace ka yarda da abunda bakayi ba, maganarka yafi ace ka na neman k'anwarka da lalata, ya fi ace kana kawo karuwa Gidanku".
Gashin kanshi ya dan shafa kafin ya murje idanun duka biyu, sannan ya koma kallonta yana karantarta, ya fada a ranshi "ta na da gardama kuma bata ganewa".
A fili yace "nayi rantsuwa na daina cewa banyi abu ba, duk wani abu da zai fito daga bakinsu, hakan ne, banda k'arfin jayayya, yau ko kisa sukace nayi, kawai hakan ne, they are right".
Takaici ya sa Labiba yin gaba, da sauri bata ma da abunda zata ce mishi, tafiyarta kawai tayi, don tana ganin Zaid be ma da hankali.
Bin bayanta yayi yana kwala sunan "Beebs" amma tayi burus dashi, ta ci sa'ar samun Keke Napep ta hau ta fadi sunan Anguwarsu Aunty Asee.
Tsayawa yayi ya bi Keke Napep din da ido, ya juya ya kalli Gidansu, kurum yaji Garin Katsina ya mai zafi duk da ni'imtaccen iskar da ke bosowa, garin da alamun hadari.
Ya buga tsaki da ya ciro sigari ya kyasta ya koma Gida, suna nan tsaye kamar yanda ya barsu, maganganu suke wanda yake da tabbacin La'antarshi sukeyi, straight hanyar BQ yayi, yana jin Baba na faman kwala mai kira amma yayi burus da shi ya wuce dakinshi.
Yana shiga Daki ya sa mukulli ya rufe ya fada kan Gado yana mai tunanin Labiba.
Labiba ma da tunanin Zaidu ta isa Gidansu Aunty Aseey, jikinta duk a mace,ta shiga Gidan da Sallama su Ameera su ka taso don yi mata oyoyo, da yak'e ta taryesu, ta karasa ciki ta gaida Hajiar Aunty Aseey da 'yan Gidan.
Aunty Aseey tace "Labiba ya makaranta?" Dan jim tayi, yau ko hanyar Makaranta bata bi ba,amma sai tayi karya tace "Alhamdulilah"
Hajiyar su Aunty Aseey tace "ya mukaji da wannan abu? Bango ya Fadi" Labiba tace "eh wallahi Mama, an ma gyara".
Aunty Aseey tace "Kin biya Gidan ne?" Da sauri tace "Aa, nasan dai angama saboda marece yayi, yaya kuwa yace aikin be da wuya".
Aunty Aseey tace "haka ne, tashi ki ci Abinci".
Mik'ewa Labiba tayi tana mai jin haushin kanta, wai itace yau da k'arya har so 2, Allah ka yafe min".
Gab da Maghrib suka koma Gida a Keke Napep, sun tarar da an gama gyaran Bangon, Labiba ta share tsakar Gidan ta shiga kitchen don daura musu taliya, bayan sunyi Sallahr Maghrib, suka ci Abincin, gabaki dayan su suke zaune kan tabarma kasancewar ba Wuta.
Hadari ya taso, iska mai karfi ya taso, da sauri suka nade shimfidarsu, suka shige dakunansu.
Baban Amira yace "Oh Allah ka ci da ginin bangon nan kar ya rushe" Anty Aseeyah tace "ai sai yanda ta yiwuwu dai kawai"
Jugum-jugum suka zauna suna sauraron ruwan Sama, sai ga ruwa kam da bakin kwarya, suna jin ginin ya sake faduwa wurin da aka gyara, ta window sukayi ta lek'e suna jimami.
K'arfe har k'arfe 10 saura ruwa bai tsaya ba, duk sunyi bacci banda Labiba da ke daki tana waya da AbuSideeq inda yake tambayanta dalilin rashin zuwanta makaranta.
Karya tayi Kamar yanda ta gaya ma Aisha da sukayi waya dazun haka ta gaya mishi, bata lafiya. Sannu ya mata ya mata sallama da fatan samun sauk'i.
Ruwan saman nan na kawo ma duk wani bawa mai rai nutsuwa, saboda yanda yake sauka cikin wani yanayi mai sa Nishadi. Jugum tayi zaune tana latsar wayarta kadan ne babu cikin karfe 10.
Me ya keyi? Bacci? Ya koyi Sallahn Isha'i? Ko ma ya ci abinci? Ko ya suka k'are dazun da Babanshi? "Ya Rabb" ta fada da ta tuna yanda sukayi dazun, shaf ta manta da wani fushin da tayi dashi.
Haka kurum Zuciyarta ke k'yank'yasa mata Zaid cikin daren nan, Son ganinshi take son yi, son sanin halin da yake ciki takeyi, kawai tana son ganinshi da daren nan, har ya kai ga ta na ji kamar ba zata iya bacci ba in har bata saka shi a Idanuwanta ba.
Juyi ta koma yi kan Katifarta, da duk numfashin da ke sauka daga kirjinta tana mai hasassho halin da Zaid yake ciki a wannan Dak'ikan.
Wuf ta tashi kamar an tsikareta, ta yanke hukuncin da bata san ko ya kamata tayi abunda take shirin yi ba.
Dakin DANMAKAHO zata.
Hijabinta ta dauko ta daura kan Rigar baccinta ta fita sadaf sadaf tayi hanyar bangon da zai sadata da Gidansu DanMakaho kamar barauniya. Chogewa tayi ta tsaya kuma tana wani tunani.
Bai ka mata ba ko kadan ace taje Dakinshi a wannan daren, ba ta san halin da yake ciki ba, ba ta san mai zai mata ba, it is wrong, so wrong, daya daga cikin zuciyarta na cewa "Dont Labiba, Dont". Dayar ko Ingizata takeyi.
Zai rantse be taba jin wannan yanayin ba, zai rantse bai taba zama yayi tunanin wata haka ba, tunanin wata bai taba lik'ewa a k'wak'walshi ba, tun dazun ya ke tunaninta, yanda ranta ya baci ne ya dameshi, duk abubuwan da yake gaya mata ko yake yi mata bata taba fushi dashi ba, ba ya so ya chanzata, ba ya son ya k'ure hakurinta, tunda har ta shiga rayuwarshi, gobe InshaAllah zai bata hakuri.
Ji yayi kamar ana taba k'ofarshi, duk da bai sanya sakata ba amma kofar datse take,ba wanda ya damu da dakinshi, wa zai zo yanzu? ko dai iskan ruwan da akeyi ne yake hurowa? To ai Kofar datse take, kuma kofar irin ta manyan wood din nan ne, iska ba zata budeshi ba, da sauri ya tashi ya bude k'ofar.
A kallo na farko ya zata Dalo ce, sai da ya kalleta sosai ya gano Labiba ce, a cikin sakwan kadan ya finciko hannunta ya jawota cikin dakin ya rufe kofar kamar mai tsoron kar wani ya gansu.
Hannu ya sa ya murji idonshi, tana tsaye tana farfar da ido tana rawan sanyi, Hijab dinta duk ya jik'e.
"Bibbs ba kya jin magana meyasa ba kya ji? Me kika zo yi nan?".
Murmushi tayi tace "Bango ya sake faduwa".
Ba wannan yake sonji ba "how could you be so reckless? Don me zaki dinga zuwa min daki? Ba kya tsorona? Ba kya tsoron ina iya danneki cikin daren nan? Baki ga tsinuwan mahaifi a kaina ba? Ba ki san mutuncin mutum na zubewa ba idan aka ganshi da ni ba? Ba ki san dazun da sun ganki ba sai sun bata miki suna ba? Don me zaki dinga zuwa inda nake? Da daddare, wai ke baki san ni Namiji bane of 28years? Baki san me ke faruwa ba in Namiji da Mace suka kebe? Are you not worried about yourself? About your Family? About Mami? Kin manta Gidanku baa karatun boko amma mahaifinki ya yarda ya turo ki karatu saboda ya yarda dake? Ya yarda zaki kama mutuncin kanki, ki kare martaban gidanku, amma zuwa dakin Namiji mutunci ne? In yayanki ya kamaki ya zaiji?".
Kyafta idanuwa tayi, tace "Ya Zaid, na yarda dakai, ba zaka cutar dani ba" ba tare da ya tanka YaZaid din da ta kirashi dashi ba yace "baki sani ba Bibbs, baki san ko zan iya cutar dake ba ko ba zan iya ba, World fa nake sha...Uhm Wiwi".
"Dagaske na san ba zaka cutar dani ba, ba zaka min abunda zakaji haushi ba in anyi ma Dalo". DanMakaho ya tsura mata ido kafin yace "DonAllah DonAnnabi me kike so, its late, ki koma Gida, gobe zamuyi magana".
Kai ta girgiza tare da zama kan kujerar dakin tace "ni bana jin bacci, ba kuma abinda zanyi, so yafi ka idasa bani labarin".
Idonshi ya murza sosai kafin ya zauna yana harararta, ita ko sai murmushi take sakar mai.
Sarki ya mana Nasiha kuma yace in muna da wata damuwa da Babanmu ko Matarshi muzo mu gaya mai, sarki ya sallame mu.
Baba da Aunty Shafa suka fita daga fada ransu a bace, Baba Sani ya dauke mu ya maidamu Gida nida Dalo bayan ya mana nasiha sosai ya bamu hakuri.
Daga wannan rana komai ya chanza mana Beebs. Da muka Shiga Gida mun tarar da Baba, Aunty Shafa, Hudu da Annah zaune a Parlo, jikinmu yayi sanyi yanda mukaga suna kallonmu, jan hannun Dalo nayi zan sadata da Dakinta amma na jiyo Ihun Baba.
Danubanku kuzo nan. Beebs, bamu saba ba, Babanmu baya zaginmu,Babanmu ba ya daga mana murya, k'ara matse hannunta nayi muka shiga Parlon sosai.
A gefe muka dan rakube, ran Baba bace yace "yanzu ni Maryama ta tona ma asiri ko DanMakaho? Kuna ganin uwarku ta kaini k'ara Gidan Sarki, bayan duk abubuwan da na mata, duk hallacin da na mata ta rasa da me zata saka man sai ta kaini Kara a Fadar Sarki? Ni Alhaji Ali Zaki?".
Mu dai ba muce komai ba Baba ya cigaba da cewa "to tunda Maita ta hanaku bin Uwarku, ku zauna, amma ba ruwanka Zaid da cikin Gidana, Boysquarter zaka koma, ban yarda da kai ba, ina da Diya Mace, kar kazo ka keta mata haddi, wani irin yammmm naji a jikina, na dago kai na kalli Babana, wanda banda tabbacin ko shine ko ba shi bane,anya Baba na ne Mahaifi? Me ji dani? Me yin duk wani abunda nakeso?".
Ya cigaba "Ke Sadiya, Annah tace dakinki take so, so ki koma BQ tare da Yayanki, ko ki koma gunsu Raliya masu dafa Abinci". Dalo ta dago baki zatayi magana sai kawai ta fashe da kuka.
Ni ko na fara girgiza kai alamun rashin yarda nace Baba ta ya Dalo zata koma Boysquaters? Dakuna nawane a cikin Gidan nan da har sai ta koma BQ? Haba Baba kar ka juya mana baya".
Hayyayakowa yayi "DanUbanka DanMakaho ina fada kana fada? Rashin da'a zaka min? Danubanka nace ba ku zama min cikin Gida, ku koma BQ, bana son ganinku, ina laifi ma da na barku a BQ din".
Zaid ya tashi inda yake rak'ube yace "Baba, wallahi ba zata yi zaman BQ ba, in ka matsa yanzu sai naje Gidan Sarki na gaya mishi "
Baba ya tunzura, danubanka ni zaka tona ma Asiri? Kaje ka gaya mishi to, tsinanne watsattse, da sauri na tashi hankalina a tashe ban ma ganin gabana na dinga jefa kafata kasa na fita daga Parlon.
Aunty Shafa tace "barshi Alhaji, kaga dai abunda Sarki yace, kar a kama mu da saba ma Umurnin sarki, Baba ya amince, Anty Shafa tace ke Sadiya ki koma dakin kusa da naki, naki Annah ke so, Sadiya bata da rigima duk da ta san Dakin da ake so ta zauna ba komai ciki daga Gado sai toilet amma na ta har Tv akwai bayan decoration din dakin da akayi da pink and purple color. Kai ta gyada alamun ta amince, Anty Shafa ta koreta cewar zasuyi magana ta zauna musu, sumsum ta mik'e ta wuce dakin da aka ce ta koma.
Ni kinsan abun bai dameni ba zaman boysquaters don na san in 2days zan koma makaranta so Dalo ma ne nake jiye ma zaman bakincikin da zatayi.
Duk ranar wayar Mancy a kashe yake, na kirata yafi so dari naji ya take, me take ciki, karamin hauka na kusa yi. A waje na zauna bayan Sallahr Maghrib, ga yunwa ina ji bana ma son shiga Gida balle naga kayan bacin rai, kawai na wuce gunsu Raliya masu dafa Abincin Unguwa, aiko na samu Jollof din Shinkafa a wurinta, ta na tausata da bani baki kan mu jure duk wani abun da zamu gani daga yanzu.
Washegari da safe na tashi na tafi cikin Gida don ganin yanda Dalo ta tashi, kallo daya na mata na lura da tsantsar ramar da tayi na kwana daya, tausayinta ya kamani, na karasa gunta ta dago da murmushi mai kama da yak'e.
"Ya Zaid, har yanzu ba ka samu Mancy din ba? Wayarta a kashe" ta fada cike da karaya, ka sa amsata nayi, na durkusa daidai tsawonta nace "ba kiyi breakfast ba, tashi mu shiga kitchen na hada mana kalaci".
A Gidanmu kowa ke hada breakfast dinshi da kanshi, saboda rarrabuwan raayi, in kuma k'osai da koko din Raliya kake son ci sai kaje baya kaci.
Na rik'o hannunta muka shiga Kitchen, muka kalli juna cike da mamaki, ba wai ba komai cikin kitchen din ba, aa sai ganin babu abubuwa da yawa, trolley din kayan tea, ba komai, ba kwai ba komai cikin fridge dana duba, yanda na lura duk wani abunda zaa sarrafa a sa a baki babu, da mamaki muka kalli juna, yaushe akayi wannan kayekayen? Dalo tace "maybe suna a Store" da sauri na karasa store na jishi a gark'ame.
Da karfi na kwada ma Raliya kira, sai ko gata nan da saurinta, tnace wai ina kayan Abincin gidan nan? Ta duba kitchen din da idonta tace "toufa, kamar an kwashe komai, na jinjina kai na san aikin matar chan ce, nace Raliya Yunwa mukeji, tace ai DanMakaho akwai Kalaci a kitchen din baya, bari na kawo muku. Parlo muka zauna muka jira Raliya ta kawo mana Breakfast.
Dadi kosai da koko dinta, sosai mukaci don jiya rabonmu da abinci tun rana. Muna cikin breakfast sai ga Aunty Shafa'atu ta shigo da nightgown jikinta. Da mamaki ta kallemu tace "ina kuka samu Abincin nan?" Daga kai nayi na kalleta nace "meye amfanin kwashe kayan abincin kitchen da kikayi? So kikayi kiyi starving dinmu da yunwa? Ko so kikayi ulcer ma ta kama mu? A gidan ubanmu? To ba zai yiwu ba, wallahi baki isa ki horar damu yunwa ba a Gidan Ubanmu".
Fuuu ta wuce ta banka dakin da Baba ke ciki, ko bacci yake ko zaune yake oho, amma da karfi naji tana cewa "ni yanzu a sallami su Raliya masu Abincin Gandu". Baba yayi dan jim kafin yace"Shafata, Abinci sukeyi wanda ake rabama yan Unguwa, da yawa da nan gidan sukayi relying, in aka Sallamesu wa zai dafa Abinci har a ba Makwafta? Kicinkicin tayi da fuskarta tace "nidai Alhajina kana shagwaba talakawa, in ka dinga basu abinci kullum ta ina zasu samu zuciyan neman na kansu? Zuciyarsu bushe take, su a ganinsu sun samu bati ni dai kawai ka sallame su Raliya, daga yau an gama Abincin Badawa".
Da sauri Baba yace "kuma fa? Hakane mutane son banza garesu, daga yau ba zaa k'ara Abincin badawa ba, ko wani shege ya tashi ya nemi na kanshi, ai maza a kira man su Raliyan".
Well ina gaya miki Beebs, baba ya ma su Raliya da masu taimaka mata wurin dafa Abinci, Sallaman Wulakanci Aunty Shafa na tunzurashi kamar wani robot take control dinshi, ni kuma da na ga haka, nace su jirani naje Bank, da sauri na dauki Motata na nufi Bank, na zaro dubu 200 na basu nace su ja jari, godia suka dinga min kamar zasu min sujadda, suka dinga min addua suna mana fatan Allah ya karemu daga sharrin Matar Uba, Raliya da yake zata girma Mancy, ta dinga min Nasiha da kuma na kula da Kanwata, suka min Sallama suka kwashe kayayyakinsu.
Ashe Hudu ya ga lokacin da na mik'a ma Raliya Kudi, ashe ya je ya barar ma Yayarshi, yayarshi ta tada ma Baba rigima da haka yake barina ina kashe kudi? Be san kudi na bata yaro ba? Ita gaskia ba zata yarda ba?.
Hahaha Labiba Babana ya kira Manager ya sashi freezing account dina, bayan ya kwace makulan Motanshi, da wayar hannuna a cewarshi da kudinshi na siya, God, to ban ma dai yi mamaki ba sai da bayan kwana biyu na samu Baba game da son komawa Makaranta.
Nan ne Baba ya min Wulakanci gaban Matarshi da Diyarta da k'anenta.
Da farko banza yayi dani ya k'yale sai da na sake magana nace "Baba lokacin da ya kamata na koma Makaranta yayi, jarabawa zaa fara da sati 2, zan koma na fara shiri".
Baba ya dan kallo Anty Shafa, da ido ta mishi magana, haba sai baba ya fara Spark, wani irin Makaranta, Kai dan iska ina sane da duk wata burobar da kake a k'asar Ingila ba, Shekarar 6 a chan amma ka kasa hado degree, sai dai kaje ka shek'e ayarka da yanmata, ka dawo Nigeria ka kuma koma London san da kaga dama, to ba zaiyiwu ba wallahi, ba zai taba yiwuwa ba".
Nan ne ya kasheni da Mamaki, baki na nauyi nace "Baba, wani Degree kake magana? Ina Degree din da na amsa ranar da kukaje London kai da Mancy da Dalo? Baba har fa Graduation Dinner sai da kukaje, ko kuma ka manta na riga da nayi joining Masters, befi min Wata daya nagama ba? Yanzu da na koma nayi Exams fa na gama".
Baba ya dinga zare ido "kai ni ban san wannan ba, ni sisi na ba zan k'ara kashewa a kanka ba DanMakaho" hankalina ya tashi amma na daure nace "kayi hakuri babana, ka bude min account dina, akwai kudi na, ni zan dauki nauyin kaina, i need to go back Baba".
Tsawa ya daka min yace "Bazan ba, nace bazan ba, na cire kudadden Account dinka tas, London kuma ba zaka kara zuwa ba". Guiwowina na dire a kasa ina kuka "Baba ka min rai donAllah, kar ka hanani komawa, Baba in wannan shine abu na karshe da zaka min a duniya donAllah ka maidani London, don Girman Allah baba".
Kafa ya sa ya shure ni sai da na k'ume, a kausashe yace "bazan kai ka ba, naira daya ta gama kuka a kanku".
Shafa'atu tace "kaima Alhaji ka rabu dashi, tunda shi ya fi so a yi ta magana daya".
Raina ya baci ban san sanda nayi wani kukan kura ba na chakumo wuyanta, na mak'ureta kamar zan kasheta, Hudu da Baba suka yo kaina, suka rufe ni da duka amma ko gezau banyi ba, na cigaba da matse hannuna a wuyanta ita ko sai k'akarin mutuwa take.
Dalo ta fito daga daki da gudu da ta ga hayaniya tayi yawa, ni ko wani karfi ya zo min na ingiza Baba da Hudu, na hau dukkan Aunty Shafa'atu, Dalo na kuka tana Yaya donAllah ka rabu da ita, ina sam ban ji ta ba, ita ko a galabaice take kukan wahala, Hudu ya rikoni ta baya, Baba ya dunkula hannunshi ya dinga kai min naushi ko ta ina kamar zararre, itama Aunty Shafar ta mik'e ta nufoni tana dukana Dalo ta rike mata hannu ta wurgar da ita.
Kamar daga Sama mukaji ana Sallami, muryar tsohuwa ce ke cewa "Ki kori Mahaifiyarsu ki juya kan ubansu yanzu ku mishi rubdugu? To wallahi baki isa ba, sai na ci uwarki, yau sai na ga Bokanki, daga nan har Pilatu sai na ga Uban da ya tsaya miki a Najeria".
Dalo ta dago kai ta kalli Tsohuwar da ta ke niyar cin danmara, a wahalce tace ;
NENE..
Ai Nene ba ta bi kan dalo ba ta shiga cikin fadar nan ta finciko Shafaatu ta kaita k'asa, ta dinga kilarta kamar Allah ya aikota, Baba yazo shiga tsakani ta sa hannu ta tsokale mishi ido, ganin haka na maida hankalina kan Hudu, ni da Nene muka kaisu k'asa ina kilar kani Nene na kilar Yayar, baba hankali tashe ya wawuro wayarshi ya latso kiran Police Station.
Wai tsohuwa Nenen nan sai da ta ma Shafa habo kafin ta tureta, ta rik'o hannuna da na Dalo tayi gaba, tana maida numfashi, tana haki tana cewa "ni ai ko bokon Saude sai da ya tantance Aminene Mamman, zaki zo ki shiga tsakanin da Da Mahaifi, shegia K'abilar banza".
Muna jin Aunty Shafa'atu na cewa "wacece wannan Alhaji?" Kafin Baba ya bata amsa Nene tayi karaf tace "Uwarki ce, kaii a'a ni ban haifi Azzaluma ba, Sunana Aminene Mamman kije kiyi tambaya kaina".
A tsakar Gida muka tsaya ta kalleni rai bace tace "kai danubanka sai kayi tsaye suyi maka taron dangi?" Ta kalli Dalo tace "ke kuma sakara kin tsaya kin bare baki kamar famfo kina ta kuka ana dukan Yayanki, baki dauko wuka ki watsa taron?"
Baki bude nake kallonta na san Matar kamar zararra take amma me take nufi? Nace Nene fa harda Baba fa, kai dallah arr, ni sai na bugeshi tunda ni ba ubana bane, sai na mushi mugun bugu tunda shi sakarai ne shanyayye".
Kai ni ina Gida Raliya ta kawo min zance abunda ya faru, to wai danuban Maryaama tana da wadda ta fini ne duk garin Katsina, ashe cin kashin da Ali ya mata kenan? Bayan ya wulakantata harda bugu? Ni ina me baa zo an sanar dani ba? Wato ni hoto ce, banda wata amfani".
Zaid ya dafe kai, matar nan tana son saka mishi pressure da yamman nan, ni yanzu kiyi hakuri Nene, wallahi ban ma cikin hayyacina cikin yan kwanankin nan".
Kai dallah ar raggon maza, ba ka biyo masu Sunan ba, Zaidu Bawan Allah jarumi ne".
Labiba ta share hawayenta amma yanzu murmushi na dauke a fuskarta tace "Wacece wannan? Kakarku ce?".
DanMakaho ya murmusa shima yace "Ba dangin Iya bara ne Uba, wai kawar Mancy ce, amma fa tsohuwa ce kuma a haife ta haifi Mancy".
Labiba da mamaki tace "Kawa kuma?"
Yace "Eh kinsan Mancy na yawan zuwa Hajj da Umrah, to a chan suka hadu, dakinsu daya a cewarta Mancy ta taimaketa sosai da hidima a Makka shiyasa suke kawance, to tunda suka dawo suke zumunci ko muje ko tazo, tsohuwa ce amma bata da hakuri, karfinta kamar na garada Goma". Sosai Labiba ke daria.
Ya cigaba
Kafin wani yayi magana sai jin siren din Motan yansanda mukayi. Baba ya fito Shafa'atu na biye dashi a baya, ke wai Baba ya shigo da YanSandan nan yace a tafi damu a rufe mu bayan karta harda Nenen.
Nene kuwa tayi kukan kura tace "duk uban da ya tabani sai naci kutumar ubanshi, yara ba ku sanni ba" ta zaro wayarta a purse ta mik'o min tace "latso min Zaidu Bawan Allah, kai ba ma shi zaka kira ba, latso min Habibu Lema, in na tuna da kyau harda shi yayi silarka ka zama abin da ka zama a yau".
"Yo ku kadai kuka san manya? Nima dana Habibu ai suke da gwamnati, kuma shi ba tsaranka bane, kai soko maza kira man shi" ko mai Baba yayi tuna oho sai cewa yayi "ku bar tsohuwan, ku tafi dashi ku kulle, ku lallasa min shi".
Haka yan Sandan nan suka kamani kamar barawo, Dalo ta fashe da kuka.
Nene tace "oho, nidai ba uban da ya isa ya kulleni, shi da ka isa dashi ka sa su tafi dashi, ke kuma ki ma mutane shiru komai kuka, kai kuma Danka ne, ka barshi a chan bayan karta kar Allah ya sa ka firdoshi, ka barshi chan ya mutu Sakarai shanyayye, ke kuma a juri zuwa rafi".
Ta fizgo wayarta daga hannuna ta wuce fuuu kamar zata tashi sama.
Ba su jira wata ba suka tusa k'eyata suka sakani a bayan motarsu suka tafi dani, hankalina tashe, yau nine haka a wulakance, ba wani wata wata a ka wurgani bayan karta.
Wani zauri ya bugi hancina, ga k'uda, ga k'azanta daga wani bangare, hawayen bakinciki suka soma kwaranyo min, yau ni ni ne a Cell? Yau ni ne a wulakance, meyasa na ma dawo hutu? Meyasa nake da rabon ganin wanan rana? Kuka nake sosai ban damu da kallon da yan bayan kartan ke bina dashi ba, ban damu ba.
A sannu na yi ta hasasso rayuwarmu a da, da rayuwarmu a yanzu, komai ya chanza Alkalamin k'addararmu tayi zanen da ba zata kankaru ba, sosai nake kuka, na dade kuma ina kukan, bansan minti ko awan da dauka ba ina kuka.
"DanMakaho" naji an fada
Da sauri na dago kai don ganin me min kiran nan wanda tabbas ya sanni tunda ya kirani da sunan da yan Unguwa kadai ke ce min.
Na sanshi, ina ganinshi a Unguwa, Dan shaye-shayene, ya sha rokona kudin da zai ci abinci duk da na san karya ne shaye-shaye zaiyi dadu ban taba hanashi ba, da shi da yan bencin Eskaley na sha raba musu naira dubu dubu.
Da kyar na ambaci sunashi "Haruna, me kakeyi a nan?" Haruna ya danyi daria yace ai ni nan bana sati 2 k'warara banzo nan ba, kai ne dai zan tambaya me kake anan. Ban iya ce mishi komai ba na duk'ar da kaina.
Gaskia DanMakaho Babanku ya kwafsa, ji yanda ake ganin mutuncinshi amma wa shine zai yi wannan kwafsin? Harda dukan Hajia Mancy gaban kowa, Kai ya mugun kwafsawa.
Kamar jira nake na fashe da wani sabon kukan, be lallasheni ba, bai hanani ba, bai kuma tafi ya barni ba".
Sai da na tsagaita kuka na kafin na dago kai na ga hannunshi a mik'e alamun wani abu yake so na karba daga hannun.
World kenan, ka sha shi, wallahi ka sha shi damuwar da kake ciki zai bace bat, ka dan ta6a world ba ka da wata matsala.
Kallo daya na ma kullin garin na kauda kai. Zama yayi kusa dani
Kagane ko ka sha taimaka min, ka sha fiddo ni cikin damuwa da yanayi, in ka bani kudi, kaga abunda nake siya nan, dagaske in na sha shi wallahi bana da wata sauran damuwa, wallahi World duniya ne, duk yanda kake cikin damuwa, bakinciki, kuncin rayuwa, da ka zuk'a so daya damuwar zata kwaranye, zuk'a ta biyu kuma zakaji kanka a kan gajimare, ka gwada zuk'a daya, da kanka zaka nemi k'ari, in kuma ka zuk'a damuwarka bata gushe ba kayi kan duk abunda kake so".
Runtse Ido na nayi, na yarda gajeran tunani gareni, shaidan ya buga min ganga, a cikin Cell dinnan na zubdar da duk wani tarbiyan da Mancy ta min shekara 25, Wallahi Beebs da na bude World na fara zuk'a ta hanci, sai da na zukeshi tass, Haruna ya so ya kwace amma na hanashi, burina damuwa na ta kau".
Ido na a runtse na ji ni a wani irin yanayin da ban taba shiga ba, wani yanayi mai wuyar fasali, wani yanayin da ban taba saninshi ba. Wanda suka dade a harkar da wuya su ja World fiye da biyar, ni ko na ja shi ya fi so 20, mamaki na Haruna keyi yanda ya ga nayi bagas a k'asa ido na a runtse in rausaya da kaina hagu in rausaya da shi dama.
Haruna na tsoron kar na haukace, don in yayi yawa yana sawa a zare, sunana ya fara kira
DanMakaho
DanMakaho shiru ba amsa ido na runste
A kira na uku ne na bude ido tare da sakin wani irin murmushi.
Cikin jin dadi haruna yayi wani juyi, tare da jinjina hanayenshi guda biyu alamun ya sara min gami da cewa;
MAANNNKAAAASSSSS.......
Yes Guys your one and Only Nene is here
Who's happy?
Vote and comment line by line please
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Sha Daya1⃣1⃣
(MANKAS II)
(Note: wannan Events din ya faru ne Bayan dawowan Nene daga London lokacin da Nasiban Rafeeq ta Haihu. Fahimt?)
A kan idonta a ka wuce dashi cikin motar yan sanda, ranta a bace, sai dai ya ta iya? Fuuu ta shige bayan motar da aka kawota, ko magana bata iya mishi ba ta wuce Gidan Lema.
"Banda Sakarai shanyayye, wa ke tura yaronshi police station?" Haka tayi ta fadi har ta shiga cikin Gidan Lema, Mami ta mata sannu da zuwa, Nene tace "ke yau ni naga k'awar Saude".
Sai da Mami ta dafe k'irji tace "a ina Nene?".
"Wannan Kishiyar Maryaman"
"Nene dagaske an Saki Hajia Maryam?"
"Ke ina baki kina k'in karba, Makira ce Matar nan, wai ke in gaya miki Yaro na samu bakin gate ya bani labarin duk abunda aka ma Maryama, ke fa da naje samu nayi sun ma Takwaran Zaidu Bawan Allah Rubdugu, aiko na shigar mai, na tsokale wa Uban Ido, ita kuma na lallasata".
Mami tace "yanzu Nene fitanki har kinyi Dambe?" Nene tace "aa fa ni fa ba dambe nayi ba, bugun tsiya na mata, ke dallah ina kaiki.
Ke shaida ce irin So din da Alhaji Zaki yake ma Matarshi Maryama da Yaranshi, kina zuwa Gidan Kema, kinga kyakyawar Alak'a tsakaninsu, ke kawai sai rana daya, ya auri tsohuwar Matarshi, ya zabure ya ma Matarshi duka gaban 'yan anguwa, ya cika mata saki 3 ya sa aka kwashe mata kaya, ya zo ya tsani yaranshi, ya shigo da Agola su biyu, ya fifita su fiye da yaran cikinshi, me zakice? Me kike ganin ya faru?"
Mami ta danyi jim kafin tace "ta na iya yiwuwa Chanji ne kawai, ko dokin sabon auren da yayi ne".
Hannu Nene ta sa a kai dauke da takaici tace "ke wai bakiji me nace ba, don yana dokin aure sainya juya ma Yaran cikinsa ba? Ya kike magana ne kamar ba ki san aikin asiri ba, ke da Saude ta rafka muku asiri ke da Mijinki aka rabaku tsawon shekaru?.
Mami tace "kawai banson zargin Asirin ne, tunda bamu da hujjah".
Nene tace "wai ya kike magana? In ba asiri ba meye? Hujja ya wuce wanda na karanto maki, ke wai don uwar yaron nan da ni zai sa a kulle a pirisin?".
Mami ta zaro Ido, tace ya akayi? "Aa wai mun bugar mishi Mata, ya kira YanSanda wai su tafi dani da Zaidu Bawan Allah, nace mishi ya kira min Habibu, da yaga uwar bari, sai cewa yayi a barni amma a tafi da Dan, yanzu dan na chan kulle, ki latso min Mijinki".
Sai ko gasu shigo tare da Uncle Zaid.
Nene ko ta tarbesu "Oyoyo Sannu da zuwanku" Uncle Zaid ya murmusa yace "Nenemu ni da Seebi".
Jawo hannunshi tayi ta zaunar dashi tace "wai Zaidu Bawan Allah, ina kawata Hajia Maryama da ke Tudun Matawalle wanda ka taba kaini Gidanta?" Cikin fahimtarta yace "Matar Speaker Ali Zaki?".
Tafi tayi cikin jin dadi tace "itafa"
Uncle Zaid da neman k'arin bayani yace "me ya sameta?".
Nene tace "to asiri kishiyarta ta ma Mijinta ya saketa saki 3 bayan ya lakada mata na jaki, ya kuma juya ma yaran Baya, kai wai jiya suka kori su Raliya masu abincin da na kai ma Maryama, aiko Raliya tazo ta gaya min duk abunda ke faruwa, ni ko na wanke kafa na sa Sabitu ya kaini Gidan.
Kai wai daga isa na naga sun saka takwaranka Zaidu a tsakiya suba ta jibgarshi, ni ko naci dammarata nayi kansu".
Kai wai sai ga 'yan Sanda sunzo wai tafiya da mu, wai zasu samu bayan Karta, wai mun bigi Matarshi, niko nace wallahi bai isa ba, sai dai a tafi da danshi ba dai ni ba, kuma nace a latso min Habibu ai ba su kadai bane Manya".
Daddyn Rafeeq ya jinjina kai yace "Gaskia da Ali Zaki yayi Babban kuskusre da yayi gigin Kulleki" Nene ta yi darian jin dadi tace "yo shiyasa na bashi tsoro wallahi, shegen ya tsorata, ai gaba da gabanta".
Uncle Zaid ya girgiza kai yace "wai Nenenmu ni da Seebi yanzu dambe kikayi? wai ba ma na hanaki Shiga abunda bai shafeki ba?".
Gimtsa baki tayi tace "yi hakuri Mamman".
Mami tayi daria tace "yau Zaidu Bawan Allahn zaa watse?".
"Yo ai naga Zaidu Bawan Allah ko meye nama Hajia Maryama ban fadi ba, matar da ta soni kamar Uwarta, ke Aisha da muke Makka wani ciwo da nayi, wallahi ita ke hidima dani, duk nisan Samanmu sai ta sauki ta siya min abinci da magani, ta rirrikeni in zan fadi, ni ko gani da raki da fada, yanda kika san diyata haka nake watseta , duk tsarabar da na maku ita ke zabar maku kuma so dayawa ita ke biyan kudin, karamcin Maryama mara misaltuwa ne, to yanzu don na taimaka ma yaranta sai ace nayi shiga sharo ba shanu?".
Duk suka jinjina kai, tace "Alhaji Habibu DonAllah kayi man taimako, kaje polis station ka sa a firdo Takwaran Zaidu Bawan Allah, kuje kuyi belinshi, wallahi dan gata ne, be saba irin rayuwar nan ba".
Daddyn Feeq yace "InshaAllah Nene, bari inyi waya inji yana a wani Police Station ne".
Ba jimawa yace "yana Police Station din Tudun Matawalle, barin je inji". Nene tayi wuf tace "muje". Gardama da ita bata lokacine, fits sukayi su Uku, Nene da Alhaji Habibu da kuma Zaid BawanAllah.
Ko da suka isa Police Station din tuni DPO ya fito ya tarbesu, ba bata Lokaci Alhaji Habib ya buk'aci a saki dan Gidan Alhaji Ali Zaki da aka kawo dazun". Jim DPO yayi kafin yace "anya kuwa Alhaji? Alhaji Zaki yace mu rik'eshi kar mu sake mu ba kowa Bail dinshi, kayi hakuri Sir yaron kangararre ne, Mahaifinshi ke da rights akan shi kuma yace a hukuntashi".
Nan Nene ta fara surfa musu ruwan Bala'i wanda Su Haruna da ke bayan Karta sun ji banda Zaid da ya dade a duniyar da World ta kaishi. Da k'yar Uncle Zaid ya firda Nene daga police station din don da har ta fara maganar dukan DPO.
Daga Station basu wuce ko ina ba sai Gidan Alhaji Zaki, iso aka musu har parlo, tare da hamshak'iyar suka fito, suna ganin Nene Shafaatu ta sha mur, riko hannunta Alhaji Zaki yayi suka karasa cikinParlon, hannu ya ba Zaid da Daddyn Feeq sukayi Musabaha".
Alhaji Habibu yace "Alhaji Ali, Nene ta zo mana da wata magana wai ka sanya an kulle Zaid, munje muyi bailing dinshi sunje ba bail, Alhaji komai yayi zafi maganinshi Allah, kayi hakuri ka firdoshi".
Kallon Hajia Shafa yayi ta banka mishi harara, lokaci daya ya fara bala'i "Haba Alhaji Lema, wai ni ina ruwanku dani da iyalina? Shin Zaid din ba yaro na bane? Ina ruwanku ko yanka shi zanyi? DonAllah ina ganin Girmanka, ka tsaya a nan, ba zan dauki shiga sharo ba shanu ba".
Nene ta katseshi ta hanyar cewa "Kai dallah sakarai rufa ma wa mutane baki, ka na zaune sai juya ka ake kamar Masa, kai Asirin ma sai fa sakarai take ma tasiri, shiyasa da ta kamaka tayi maka mugun kamu, to wallahi ka natsu kayi wa kanka kanka fada".
Ta matsa kusa da Shafa'atu ta sake mata wani zazzafan Rankwashi wanda ya sanyata ihu, a tare Alhaji Zaki da Zaid Lema suka tashi, Zaid yayi kan Nene, Zaid ya janyeta yana "Haba Nene".
"Ni Zaidu wallahi ban san harka da Stupid, nidai a Sako min Amanar da Allah ya bani".
Shafa'atu wanda rankwashin ya shigeta ta fara kuka "wallahi Alhajina sai ka sakeni, ba zan iya ba, ace har Gidana wata tsohuwa zata dinga bina tana duka na? Kamar yar yarinya? Ni wallahi ba zan iya ba".
Hankalin Ali Zaki ya tashi da sauri yace "Alhaji Habib Lema, ba gaya ma ina mugun jin kunyarka, ku fitar min daga Gida, ku fita daga harkan Gidana, wallahi in Mamarka ta sake taba Matata wallahi ba zamu kwashe da kyau ba".
Aiko ya tunsura Nene tace "Allah ya tsine maka in har ka bari muka kwashe da kyau, Shege, mara hankali".
Zaid ya ja hannunta tayi ta fizgewa, da k'yar ya iya fitar da Nene daga Parlon, ga Nene da karfi.
"Alhaji Habib Lema, ka ja mata kunne, ta fita daga harkan Gidana, ko kuma hukuma ta shiga tsakaninmu, ai mata Iyaka da Gidana".
Daddyn Feeq be iya magana ba sai dai fitan da yayi a zucciye.
A Mota yace "Don Girman Allah Nene ki fita daga harkan Gidan Zaki, Nene ta ya zan iya dauka in wani ya miki rashin kunya, Nene ki sa mishi ido, duk daren dadewa gaskia zata bayyana, Dan shi ne, chan cikin ranshi akwai sonshi a cikin shi, donAllah kar ki sake zuwa Gidan".
Zaid ma ya shiga lallashinta da tausassun lafazi, yana cewa ta bisu da addua, Allah ne zai kare ma Maryama Yaranta.
Takaici ya hana Nene cewa komai sai Girgiza k'afar da takeyi tana tunanin yanda zata shigo Gidan Alhaji Zaki karfe ukun dare ta ci ubansu daga shi har Matar.
***
Kwana na 2 a Cell, banda wata damuwa, saboda me? Saboda World, sosai yake batar min da duk wata damuwata. Baba bai zo ba, bai kuma ce a sakeni ba, so ba ranar fita daga wannan wurin.
A kwana na ukun ne Ina zaune kawai naga wani kurtu ya lek'o yace "kai Dan Gidan Zaki fito" mamaki ya cikani, to Baba ya hakura kenan, ya sa an firdoni, tashi nayi na fita sai ganin Dogarawa fiye da uku tsaye da dorinarsu.
Dogarawan nan suka tisa k'eyata bayan sun sanar dani cewa mai Martaba Sarkin Katsina ke nema na. Motar Emirates muka Shiga Har Fadar Sarki dake K'ofar Soro, wani dogaribya fara shiga bayan Mintuna Goma sai gashi ya dawo yace mu shiga.
Ina Shiga Fadar gabana ya fadi, ganin Dalo durk'use gaban Fada, daga gefe kuma Baba ne da Aunty Shafa, sai Hudu da Annah, sai wata da ke Durk'ushe tana ta bayani ta bawa Fada baya".
Muryarta kawai ya ankarar dani ko wacece.
"Nene ce".
Kwakwalwata ta fahimci cewa Nene ce dai ta kawo Baba k'ara.
****
Tun bayan dawowar su Nene daga Gidan Zaki ta rasa sukuni, bata da wani madafa ga shi Zaidu kamar yayi kuka wurin rokonta a kan kar ta sake zuwa Gidan Alhaji Zaki. Bata san ya zatayi ba har kwana 2 suka shide bata da wani dabara, duk tayi sukuku, bari ta kira Seebinta ko zataji sanyi.
Zuwa yanzu Nene ta iya kiran Mutanen London a waya da taimakon hotunan su wanda Zaidu Bawan Allah ya sa a jikin ko wani Contact, Hoton Seebi ta lalubo cikin contacts din ta danna kira don tana da kudi fiye da Dubu 10 cikin wayar duk don kiran Mutanen London wanda Zaidu BawanAllah ne ke sawa".
"Hellooo Neh-Neh" taji muryarshi
Da sauri tace "Dunkum. Kai na kira?" Ta na mai dauke wayan daga kunnenta tana sake duba screen din don ganin wa ta kira kuma dai hoton Nasibar ne.
Mur ta sha kamar yana gabanta tace "kai dallah ba mai wayar wayarta". Dan daria yayi yace "Neh-Neh kinyi missing dina ne? Baki nemeni kwana biyu ba".
Yau bata da lokacinshi cewa tayi "kai Arr, ina Nasibar?" Dan daria ya sakeyi yace "Sunje wani Birthday Party ita da Yarona".
Tsaki Nene tayi tace "Wani yace ba yaronka bane? Rasa kunya beran kitchen, kace ta kirani in ta dawo".
"Wai ya Neh-Neh yau sai gwasuleni akeyi? Wai ba mun shirya ba? Ai mun bar fada ko? Ko yau kin tuna kanki a Airport ne wurin masu Red din Kunne" ya karashe yana daria.
"Wallahi Dunkum ubanka zanci"
Guntun tsaki yayi yace "kinga Matsalarki ko Zagi? Wai ba Uncle Zaidu ya hanaki Zagi ba? Barin kirashi in gaya mai".
Da sauri ta katseshi "kai dallah tsaya kaji, ka tuna Hajia Maryama Mamarsu Takwaran Zaidu BawanAllah da Dalo?".
Rafeeq yace "Eh na tuna kawarki da kike bamu labarinta, me miki Wanki a Makka".
Cike da jin dadi tace "Good, good Dunkum, to wallahi Mijinta ya mata Saki Uku, ya mata dukkan tsiya gaban Mutane" nan ta shiga bashi labari kamar a gabanta akayi, har zuwa zuwanta na farko da dukan da ta ma shafa, da kulle Danmakaho da akayi da zuwan su karban bailing dinshi".
Ran Rafeeq ya baci, wai yaushe mutane zasu bar zama Victim din Matar Uba? Karon shi da Saude ya tuno, abubuwan da tayi da yanda ta shiga tsakaninshi da Mahaifiyarshi ya tuno, guntun tsaki yayi yace
"Neh-neh Wai are Women Selfish?".
Nene tace "Uwar me? Hausa zakai man dallah".
Tsaki yayi yace "Neh-neh tunda Baban bai dubi Girman Daddy ba ya ci muku mutunci, ai yana da magabata, in ya fi karfin Magabata ai bai fi karfin Hukuma ba, in ko yafi karfinsu bai isa ya fi Karfin Baban Kowa na Katsina ba".
Nene tace "Sarkin Katsina".
Rafeeq yace "Shine Magana kawai, Neh-neh ba tare Kukaje Makka da Amaryar Sarki ba?".
Nene cikin Jin dadi tace "ehmana dakin mu daya da matar sarki da Maryama".
Rafeeq yace "ki samu ganinta ta miki hanya kawai".
Allah Dunkum? Yace "wallahi kuwa"
Tace "Zaidu Bawan Allah ya rokeni kan na fita daga harkarsu wallahi".
Rafeeq yace "Nene sharesu wallahi, ki taimaka musu, ni na san sharrin Matar Uba, DonAllah kar ki karaya".
Cikin Samun Karfin Guiwa tace "tankiyu Dunkum, i lobiyu, i miss you Dunkum".
Yace "Yeah Right i miss you too My Amazing Granny".
Ji yayi tace "Uwarka ka zaga"
Tsaki yayi yace "kina da damuwa wallahi, ke fa kika fara turancin, kuma in an miki sai ya zama laifi?"
"Oho dai kace ma Matarka in ta ga dama ta kirani" dif ta kashe wayar.
Ta yanke Hukunci, Washegari karfe 8 na safe tafita, bata gaya ma kowa ba balle a hanata, ko driver bata bi ta kanshi ba ta samu A daidaita Sahu ta hau sai Gidan Sarki, Part din Gimbiya, aka ma Nene iso, bayan wasu mintuna Gimbiya ta fito, aiko ta rungumo Nene, suka gaisa cike da mutunta Juna.
Nene tace "mai Martaba na nan? Shi nazo gani? Ko yana da bak'i?" Gimbiya tace "ko da bak'i ai zai ga Nenenmu ina fatan Lafiya?"
Nene tace "k'aran Sakaran Mijin Maryama na kawo".
Gimbiya tace "wani abun ya sakeyi? Ko sati biyu baayi ba da Maryama ta zo nan maganar rik'on yaya wai don ya saketa sai dai su bita".
Nene tace "kinji Gilu ko? Ashe kun ma san da maganar, to shekaran jiya wacchan naje Gidan, naga matar da kanenta da uban sun mishi taron dangi sai bugunsh suke wai bayan nan kuma ya kulleshi a Police station, ke cin kashi kala kala ake musu a gidan nan, nace aiko suna da Gata, shine na garzayo don Ganin Mai Martaba". Gimbiya ta mik'e tace barinje in mai bayani.
Bayan Sarki ya saurari Nene ya aika a Kira Mishi Alhaji Ali Zaki da Iyalanshi Gabaki daya, sannan ya tura Police Station a sako Zaid.
Wannan Kenan
*****
"Aa Allah ya kara ma Imani, Matata suka tarar mawa, Nene kuwa harni ta tsokale wa ido" Nene tayi karaf tace "ba gaskia bane, kaine dai kuka taran mashi, ni ina ni ina dambe? Ina neman shekara Saba'in da dori? Ta ya tsohuwa kamata zata iya Dambe da kai da wanchan matashin da kuma Matarka? DonAllah Mai Martaba duk wanda yaji wannan ai ya san karya ne".
Duk da ina cikin tashin hankali sai da na murmusa da jin zanttutukan Nene. Bayan Sarki ya ji bayanan Nene da kuma na Baba da na Shafa'atu, aka min tambayoyi aka ma Dalo tambayoyi Sarki ya yanke hukunci.
"Alhaji Ali Zaki, wannan ya zama karo na karshe da zamuyi zama kanka da yaranka, na saurari komai, na fahimci komai, ba ruwan Matarka da Yaranka, ba ruwanta da su, ke shafaatu ba ruwanki da duk abunda zai ma yaranshi, ba ruwanki da hanashi, ba ruwanki da sa shi, na miki iyaka da su, yauwa ba kuma da k'ayyade musu abincin cinsu, gidan ubansu ne, yana iya sakin ki, amma bai iya sakinsu, kina jina?".
Shiru tayi bata amsa ba, bata ankara ba sai jin Dorina tayi a bayanta, wani irin bank'arewa tayi tare da sakin ihu, haka wannan dogarin ya sake shada mata a baya yace "kinji ko ba kiji ba?" Da sauri tace "naji wallahi, wallahi naji".
Hankalin Alhaji Ali ya tashi amma ba abunda zai iyayi da ya wuce sanya ido, Sarki ya ja ma Baba kunne sosai, kafin ya tambaye in akwai mai magana.
Nace ina da magana "Masters nakeyi, saura kwanakin da ba su wuce 3 na fara jarabawa, Baba yayi freezing accounts dina, ya kwace duk wani abun da ya bani, ya hanani komawa don kammala karatuna".
Sarki yace "Alhaji Zaki hakane?" Baba ya fara in ina yace "Wallahi Mai martaba, ba kudi ne, amma inshaAllah da komai ya daidaita zan maidashi".
Sarki yace "to madallah, duk da zaiyi wuya ace kai baka da halin maidashi karatu ba damuwa bane wannan, indai be rasa ci da sha ba to komai mai sauki ne, wannan tsakaninku ne, ku tashi ku tafi, ku kuma in akwai wani abu kuna iya zuwa Fada ku sanar dani, akwai mai magana?".
Baba yace "eh ni, mai Martaba, donAllah ace ma wanchan Tsohuwar kar ta sake zuwa man gida, tayi nesa da iyalina donAllah, ayi mata iyaka da Gidana". Nene ta murmusa tace "indai Gidanka ne ba zan kara zuwa ba".
Murmushin da takeyi ne ya fadar ma Baba da Aunty Saude Gaba, ba su yarda ba, wannan tsohuwa akwai bariki".
Sarki yace "to Madallah"
A haka ya sallame mu, ko ba komai Nene ta kwatar mana yanci ta siya mana mutunci, ta nuna mana muna da sauran gata.
Nene ta rik'e hannuna da na Dalo ta ja mu waje tace "ku je Gida, da kunga abunda bai muku ba ku kirani, ka kula da kanwarka" sosai hankalinmu ya kwanta.Nene ta tsaida abun hawa tayi tafiyarta Gida abunta.
Mu kuma da Motar Emirate a ka maidamu Gida, ba wanda yace ma kowa komai sai ni da Dalo da ke fira jefi jefi.
A ranar Baba yaje Gidan Alhaji Lema don kara ja mishi kunne kan Uwarshi, lokacin sun fito daga Masallaci shi da Abbii(baban Nasiba) a nan ne ma ya san Mamarshi na wani Case, shi kuma Alhaji Lema a nan ne ya san cewa Nene taje Gidan Sarki, hakuri Abbi ya ba Baba. Nan suka shiga tattaunawa tsakaninsu.
Abbi yace "wallahi ko me zaa ma Nene ba zata fita daga harkansu ba, oh Allah Nene ita bata damuwa taje ta siya fada da kudinta".
Alhaji Habib yace "kawai Zaidu gobe ya wuce da ita Kaduna kawai, ta dan kwana biyu chan".
Abii yace "anya zata yarda ta bishi?
Alhaji Habib yace "wannan kuma aikin Zaidu bawan Allah ne". Dariya sukayi baki daya.
Da kissa da kissina zasu bar Gidan ba tare da sun sake waiwayan gidan sarki ba, ki kulla makirci da duk wani sharrin da zaki iya musu, fadan ba naki bane, ya zama na Uba da yaranshi, ke kawai ki zama 'yar kallo. Hudubar yar rabi kenan da tazo Gidanta, haka kawai zatayi dole tayi taka tsantsan bata son duk abunda zai sake hadata da gidan Sarki don ta ji Dorunar nan, ta san me zatayi. Da kansu zasu bar Gidan baki alekum.
SAI DAI ME?
Rayuwa ta cigaba mana, ba dadi, ba mu taba waya da Mancy ba tunda ta bar katsina, tunda na dawo ni ke shiga kitchen in dafa Abincina, ban yarda na ci abincinsu ba, wani community school Baba ya maido Dalo wai be da kudin biyan makarantar da take a da, amma kin san me? Chan ya maida Annah, ga hudu da ke fantamawa cikin Motocin Gida ni ko nawa kallo.
In naji Bakinciki kamar ya kasheni, na kanje dakin Haruna na shak'a World, a hankali na dinga taba Sigari har ya zame min jiki, a rana sai in sha kara fiye da biyar, komai ya cigana da wakana Babanmu na fiffita Bare kanmu, kashi ya fimu daraja, banda Abinci da wurin kwana ba komai na Babanmu a wurinmu, ke sai yazo ma na daina damuwa da komai, na daina shakkun Baba, na fetsare, na koma abota da su haruna na zama wani dan jagaliya, na koma Taraiyya da yan Bencin Eskaley. World din na batar min da duk wata damuwa, sai likafa ta cigaba sai in zuqi World na bi da kwalin Sigari guda, to fa Sigar Zuk'i daya nake mishi ya kare na cillar na kunna wata, shiyasa suke ce min Mankasssss...
Ke kwatsam wata rana ina daki Dalo ta shigo dakina Hankalinta tashe, tana kuka wai ance mata ina shaye-shaye, ni abokinsu Eskaley ne. Hankalina ya tashi bana so ta taba ganin wannan side din nawa, nima kukan na sa nace mata "wallahi zan bari, ba zan karaba". Da kyar na samu tayi shiru na lallasheta. Rakata nayi har dakinta a cikin Gida, tausayinta ke kamani, duk ta fige ta lallace ta kuma yi duhun bak'i".
Nazo wucewa daidai dakina na da na ji muryar Hudu na cewa "eh na saka mai a karkashin katifar shi" sai na ji Aunty Shafa tace "Yauwa kawai ai shi ya dauke su" sai kuma suka sa darian shewa.
Kafadu na na daga, ba su dameni ba, na wuce dakina da ke baya, na dauko ragowar World na zuk'e, na zauna ina recieving current din da World ke bani a lokaci daya ina busar sigari, ina jina a gajimare naji an banko kofar Daki.
Baba, da Anty Shafa ne, a dage na kallesu na watsar na cigaba da bankan Abuna".
Cike da hargowa Baba yace "Kai DanMakaho, ina Sarka da yan kunnen Zinarin Matata da ka shiga ka sace a dakinta?" Duk da Maganar ta buga zuciyana ban dago na kallesu ba na cigaba da busar Sigarina".
Aunty Shafa ta fara kukan munahinci tace "wallahi da idona naga ya fito dashi daga dakina, na mishi magana kan ya bani abuna ya min zagi ta uwa ta uba, shime nace ni ba zanyi komai ba balle ace ban kyauta ba, bari kai ka dawo tunda kai ka haifeshi sai ya baka".
Wani murmushin bakinciki nayi wanda ya sa na zuk'e ragowar Sigarin, ido na ya kada yayi jazir, amma dai tak bance musu ba.
Cin kwalar rigata Baba yayi "Danubanka yana ina? Hudu duba min dakin nan".
Don rainin Wayau Hudu ya daga Katifata kawai sai ga sarka da yan kunne? Kutumar.
Wai sai suka shiga rafka Salati.
"Wallahi kai ba dana bane ba, ni ban haifi Barawo ba, Maryama ta dade tana haintata, cikin shege tayi ta lakafa min Da, ashe Barawo ne, Allah ya isa tsakanina da Maryama, ta sa na raini Barawo, shege dan shegia, Allah ya isa na, Allah ya tsine ma Maryama".
Da sauri na kwace kaina nayi hanyar Fita.
Muryar Makirar naji tana cewa "dama Alhaji baka san DanMakaho Shege bane? Be da Uba, kai a ka dauka sakarai a ka lakafa maka shi, kai kuma ka raineshi tsakaninka da Allah".
Wani kukan Kura nayi na finciko hannun Baba na tillashi waje, kafin su ankara na sa mukulli na kulle Dakin, kafin ta farga da me nake niyyan yi na ciro Charger Laptop dina na dinga laftarta ta da shi, ihu takeyi na sa k'afa na tande kafafuwan ta, shi ko Baba daga waje Hankalinshi a tashe yana ta kokarin budewa, ya rasa yanda zaiyi.
Sai da nagaji da kaina na kyaleta, duk tayi laasar, fuskarta tayi suntum, wannan shine ba a rabu da bukar ba, ita zaman shekara 15 din da tayi ba wai don ta zo dan Miji na dukanta bane, ita bata ma ga wani chanji ba, bata ga ribar shekarun da ta dauka ba, zuwa zatayi ta samu Er Rabi dole a sake sabon Zama.
Ni ko na kyasta Sigarina na hau busawa, bude k'ofa nayi na bi ta inda Baba ke tsaye cike da tashin hankali, ya na ko ganina ya hau la'anta ta.
"Allah ya tsine maka DanMakaho, Allah ya watse maka Karama, Allah ya kwashe maka Albarka, Allah ya laance ka" ya dinga tsina na.
•••••
Kalar kukan da Labiba keyi ne ya sa shi tsaida labarin, murmushi mai cike da tarin takaici da bakinciki yake yace "Kefa kika dameni da na baki labarina, kuma da na fara sai kuka?".
"INA SONKA"
Ta tsaida duk wata na'urar da ke jikinshi daga aiki.
Da kyar ya iya lallubo kalmar "Sha biyu Saura, dare yayi sosai, tashi muje na rakaki Gida".
"DAGASKE, Ina Sonka".
Cikin ido ya kalleta ya hango tsantsar Gaskiarta tsakani da Allah, wannan wace iri ce? Wace kala ce cikin Mata? Ya san ba da dabi'ar 'yan arewa, don babu wata 'yar arewa da zatayi abubuwan da Labiba keyi, ba 'yar arewa mai ajin da zata kalli Namiji gatsau haka ta gaya mishi kalmomi masu tsada, dauke kanshi yayi sakamakon binshi da wani kallo da takeyi.
Ba tare da ya kalleta ba yace "Its Late, ki tashi na rakaki Gida".
Hawayenta ta goge ta mik'e tsaye yayi gaba ta bishi a baya, da hasken Torchlight ya haska Fasassun Blocks ya tsallakesu, ya haska mata itama ta tsallake. Har tsakar Gidansu Labiba ya shiga.
Da taimakon Hasken Farin Wata suke kallon juna cikin Ido.
"So na kikeyi? Ko tausayina kikeyi?" Ya tambayeta kwayar idonshi kan nata.
"In tausayina kike ji, nagode, ki bari, ni bana bukatar tausayin kowa"
"In kuma sona kikeyi, shima ki bari, bana bukatar a So ni".
So biyu ta kyafta idanuwanta kafin ta tsaidasu a kanshi tace Dagaske Sonka Nikeyi.
Bata ganewa ya fada a ranshi, ya juya ya barta a tsaye, tafiyanshi yayi, ya sake tsallaka Fassassun blocks ya shige Gidansu, kan idonta ya bude kofar dakinshi ya shiga ya maida ya rufe.
Zubewa tayi a kan guiwowinta biyu a k'asa a hankali ta furta YA RABB.....
INTERMISSION.
Vote and comment line by line please..
#1love
#DM
#anatare
#SonSoFWA
#staytuned
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉
('YAN ZAMAN KASHE WANDO)
3/05/2013
Kamar kullum, zaune suke kan Benchi daidai shagon Eskaley dake farkon layi, zaman banzan da suke yi ke nan duk bayan Sallar La'asar, daga gefenshi Haruna ne ke shan Sigari.
Haruna ya mik'o mishi Sigarin da ke dab da k'arewa, ya karba ya sa a baki zai zuk'a ke nan suka hada idanuwa da halitta daya da yake jin kunya duk duniya, da sauri ya tura karan sigarin cikin doguwar hannun rigarshi ya kawar da kai kamar ba wani abu.
K'arasowa ya yi bakin shagon ya musu sallama. Haruna kadai ya amsa tare da gaishe shi sai Eskaley, shi dai gudan kawar da kansa ya yi.
Naira Dari ya fiddo daga Aljihun gaban rigarshi ya ce da Eskaley "Barka dai! Maggi za ka bani Mai Star da Farin Maggi" karban kudin Eskaley yayi, ya hada mishi kayan daya bukata ya ba shi chanjin Naira Goma Sha Biya(15) bai amsa ba sai cewa ya yi a bashi Ashana da sauran. Sallama ya sake yi musu ya wuce cikin layin don tafiya gidan shi.
Haruna ne ya lura da Zufar da abokinshi ke yi, d'an zungurar shi ya yi da hannu yace "Ya dai Mankas?" Da sauri wanda aka kira da Mankas ya zura hannun shi cikin doguwar hannun rigarshi ya zaro karan Sigari, ya jefar kasa tare da sa kafa ya murjeshi. kafin kuma ya hau nannade hannun rigar. Haruna da mamaki yace "Mankas? Kana da hankali kuwa? Sigari mai wuta ka tura cikin rigarka? Mtss! gashi nan har ya taba fatarka".
Mankas ya kauda kai daga kallon fatar hannunshi da ya yi bororo lokaci guda saboda wutan da ya taba fatar, abunka da farin fata, tuni wurin ya yi Ja.
Garin wata hoda Eskaley ya wurgo ma Haruna ya ce "jik'a ka shafa mai a wurin" Haruna ya bude 'yar takardar, ya dauki fasasshen ruwan ledan da ke gefenshi ya dan jik'a ya kamo hannun Mankas zai shafa, Mankas ya janye hannunshi, da k'yar ya iya cewa "Ka barshi, ba damuwa".
Haruna cike da damuwa ya ce "kai fa Mankas gardama gare ka, ka tsaya don Allah."
Bai ce komai ba, sai ya mik'a masa hannun. Hakan ya ba Haruna daman Shafa masa Powdern a wurin da ya fara tashi.
Suna fira jefi-jefi sauran Abokan zaman kashe wandon suka karaso, nan unguwar ya kaure da hayaniyan yan benchin Eskaley , rabi da kwata duk gardama ce.
Da Sallama ya shiga Gidanshi, Ameera da Sabit suka rugo wurin Mahaifinsu dan taren shi "Baba Sannu da dawowa" kansu ya shafa ya ce "Yauwa sannu, ya makaranta?" suka amsa mi shi, "Barka da Dawowa Yaya" ya kalleta da fara'a ya ce "Barka dai Labeeba, ya Makaranta?" murmushi ta mishi tace "Alhamdulilah" shiga ciki tayi ta dauko Tabarma ta shimfida mi shi, ya cire takalminshi ya hau kai, Sabit ya zauna kan kafar Babanshi Amira kuma ta jingina da jikinshi yana musu tambayoyi suna amsawa.
Aunty Asiya ta fito daga Toilet da Buta a hannu, ta ce "Barka da dawowa Baban Amira" wani murmushi me k'ayatarwa suka ma junansu, da ba dan idon yara ba da sun rungume juna, da kallon kauna ya ce "Asee, ya Gida ya Yaran?" ta ce "lafiya lau, ya Kasuwan?" ya ce "Kasuwa Alhamdulilah, kin san sai da na bar kasuwa na ga message dinki? Sai da na shigo Unguwa na tsaya shagon Eskaley dinnan na siyo Magunan" ya k'arashe tare da mik'a mata ledar Maggin.
Murmushi tayi ta ce "Maggin ke nan nayi amfani dashi a Abincin rana, shi ya sa na ce bari na maka text ka taho mana da shi" ta karba tare da isa kitchen inda ta iske Labeeba na jera Cooler din Abincin Baban Amira a Tray, karban Tray din tayi ta ce "Fasa k'ankarar nan cikin Sobon" Labeeba ta amsa mata da "To" ta bude dan firij din da ke kitchen din ta dauko kankarar ta fasa ta juye a Jug.
Duk da su Sabit sunci Abinci sai da suka taya Babansu cin na shi. Ya ce "Wai ya ba a je Islamiya ba yau?" Ameera ta ce "Baba yau fa Alhamis" yace "Afuwan na shafa'a, to ina Homework dinku, na tabbata an baku" Amira ta ce "Sai da daddare zanyi nawa" Baban Amira ya ce "Aa, kuyi yanzu tun ido na ganin ido, ba sai dare ya yi ba, ba wuta a rasa yadda za'ayi" Aunty Asiya ta ce "tashi ku dauko Aunty Labeeba ta koya muku" Rige-rigen tashi suka yi suka shiga dakinsu.
Baban Ameera ya ce "Labeeba to ya Makarantar?" ta ce "Wallahi Yaya Ranar tsiya, kaji zafi, ga nisan tsiya" Aunty Asiya tace "nan ta shigo min kamar zata kife" dariya ya yi yace "Haha, yarinya yanzu kika fara, baki ga komai ba" tace "Wai Allah!" duk suka yi daria.
Ta danyi kewar Gida, tana kewar Mamarta, da yanuwanta, sosai take kewan mahaifarta inda ta girma, amma tana jin dadin zaman Gidan Yayanta sosai, tana sha'awar yadda Yayanta ke tafiyar da Gidanshi, bata da damuwar komai, to damuwar me za ta yi tana gidan Ɗan'uwanta Shak'iki, ga kuma Matarshi da ko kusa ba ta da matsala, ga Yaran Yayanta masu matuk'ar kaunarta, zama da su kan dauke mata duk wata kewa. Haka yanzu ta zauna ta ci gaba da koya ma Amira Homework dinta, sai da ta gama kafin ta ma Sabit da yake shi Tracing ne.
***
6:35pm
Baban Amira ya tashi ya shiga bandaki ya fito tare da daura Alwala, ya kalli Sabit ya ce "Mallam Sabit muje Masallaci ko?" Sabit ya mik'e da murna ya yi alwalarshi duk da ba daidai bane, ya rik'o hannun babanshi. Aunty Asiya da ke kitchen tana tuk'a tuwon dare Baban Amira ya lek'a ya ce "Asee, mun tafi Masallaci, sai bayan Isha'i in Allah ya kaimu" fatan dawowa lafiya ta musu, Labeeba ma haka suka fita daga gidan rik'e da hannuwan Juna.
Suna nan zaune har aka kira Sallar Maghrib, cikinsu babu wanda ya yi yunkurin tashi zuwa Sallah duk da Massalacin na gefensu.
Har Baban Amira ya ketara su ya dawo baya ya ce "Dan Makaho, kuna ji ana kiran Sallah, kuna nan zaune, haba kuji tsoron Allah mana" Tero yace "kai Mallam kaga an Sallame Sallar ba muyi ba ne?" Baban Amira ya ce "ai gani nayi baku da niyya shi ya sa na ce bari na muku tuni" Haruna yace "Zamu yi anjima" Baban Amira yace "Haba, da hankalinku? Anjima? Yanzu me kukeyi? Kun san hukuncin masu Tarrikus Salat? Jinkiri wurin yin Sallah? Kunsan fallalar Jam'i" Master yace "Kaga ba ruwanka da mu, in kai ke karban Sallahn kar ka karbi namu".
Dan Makaho ya mik'e yana kallonshi da mak'allelen idonsa da k'yar yace "Yanzu za mu tafi".
Baban Amira ya kalli Master yace "Aa bani ke karban Sallar ba, tuni ne nawa, Allah ya shirya" ya ja hannun Sabit suka wuce tare da k'etara Titi suka wuce Masallaci.
Cikin muryan yan shaye-shaye Master yace "Kai Mankas naga sai wani lallaba Gayen nan kake, daka barshi dan uwattai, kallon kafirai yake mana" Dan Makaho yayi tsaki yace "Eskaley bani Ruwa leda biyu" Eskaley ya mik'o mai Ledar Pure water dan gefe ya matsa ya fara Alwala.
Haruna yace "kai ma dai Master, bak'ar magana ka gaya mishi, ni ban ga laifinshi ba" Tero yace "Yan Unguwanan Gulma buroba ne dasu, Master ka min daidai" Haruna ya mik'e shima ya karbi ruwan ya matsa inda Dan Makaho yake shima yayi Alwalarsa. Master kuwa da Tero zamansu sukayi, suna kuna Sigari. Har Eskaley ya fito ya kulle Shagonsa, Master da Tero suna nan zaune.
Su uku suka nufi Masallacin Unguwansu da ake ma lak'abi da Sharp-Sharp.
Vote and Comment line by line
#1love
#DM
#anatare
#FWA
#nagode
Biebee Isa.
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Biyu 2⃣
(SHARRI)
4/05/2013
Kan'nannen Idonshi ya dago ya kalli Sady da ta ke zaune a gaban dakinshi, da alama shi take jira, ya dan k'araso da sauri yace "Ya akayi ne Sadiya" ya tambaya fuska cike da damuwa, kamar ba zata amsa ba tace "Barin Gidan nan zanyi" ido ya dan ware kafin ya murza Idonshi yace "me ya faru?" bata amsa shi ba, ta sake jadadda mai da "Gidan nan zan Bari" dan mur ya sha kafin yace "ba inda zaki, ba ki da inda yafi nan, ni a matsayina na miji ban bar gidan nan ba, kema ba zaki bar gidan nan ba" kuka ta fashe dashi ya matso gareta ya janyota jikinshi ya rungume yana shafa bayanta alamun lallashi, ya sama magana a hankali "Sady, komai zi wuce--" Be karashe maganar da ya so mata ba sukaji ana rafka sallati a bayansu "Inallillahi wa ina ilaihir rajiun, DanMakaho kanwarka kake runguma haka? Kana shafa mazaunanta?" cike da tashin hankali suka sake juna suna kallon Aunty Shafa'atu Matar Babansu. Bambamin da ta hau yi ne ya sa mutanen Gidan suka firfito, Aunty Shafa bata bar tafa hanaye tana jefansu da mugayen kalamai ba.
Jikin Sady na bari ta karasa gunta tace "Aunty Shafaatu donAllah kiyi shiru, wallahi ba wani abu bane, kin manta Yaya Zaid Yayana ne Muharramina Shakikina?" hannu Aunty Shafa'atu ta sa ta buge bakin Sady tace "yi min shiru Munafuka, yau kuka fara shafar juna kuna iskanci? Shegia Yar Shegia Karuwar Yayanta.".
Ran Mankas ya baci ainun, be san lokacin da yayi wani tsalle ba ya shak'o wuyan Aunty Shafa'atu ba ya danganata da bango, k'aninta Hudu ya yo kanshi, be saketa ba, k'ak'arin mutuwa take tana jin azaba tace "DanMakaho kasheni zakayi? Hudu ci man ubanshi" kamar umurninta yake jira, nan ya fara dukkanshi yana kai mai naushi ko ta ina, ko motsi beyi ba illa kara matse hannunsa da yayi a wuyanta.
Fati da Annah suka rufe Sadiya da duka durkusawa tayi tana kuka ba su bar dukanta ba, kukanta yaji ya tsananta, ar yanzu su Hudu ba su bar dukkanshi ba kuma be saketa ba, kukan da Sadiya keyi ne ya sa shi sakin Anty Shafaatu ya karasa gun su Fati ya finciko su yana kai musu duka ko ta ina,.
Sarkin yawa ya fi sarkin karfi, nan suka hadu gabaki daya suka ma Sadiya da Mankas dukkan tsiya.
****
Bangon Kantangarsu daya, ko meke faruwa a cikin Gidan Alhaji Zaki musamman ta wurin BQ suna ji kamar a cikin Gidan akeyi, suna zaune baki daya kan darduma sukaji muryar Hajia Shafa'atu na cewa "Inallillahi wa ina ilaihir rajuun, DanMakaho kanwarka kake runguma haka? Kana shafa mazaunanta?" zumbur suka mik'e tare da matsawa kusa da bangon Gidan.
Suna nan tsaye jigum-jigum, sunji komai kamar gabansu ake, jikinta sai bari yake, baki na rawa tace "Aunty Asee kar su kashesu, muje mu rabasu DonAllah" Aunty Asee tace "hmm, Labiba ina mu ina shiga fadan Gidan Alhaji Ali Zaki? Haka suke, ai sun dade ma basuyi ba, haka suke wallahi".
Muryar Alhaji Ali sukaji yana fadin "Me ke faruwa a gidan nan ne? Da alamu yanzu ya shigo Gidan, da sauri suka tashi daga jikinsu Mankas. Anty Shafaatu ta fashe da kuka ta matsa kusa dashi cike da kissa "Nagaji Alhajina, nidai ka sakeni, ba zan iya ba, har sai yaushe Dan Miji zai bar dukana? " Hankali tashe yake tambayarta me ya faru, ta ja majina tace "Zuwa nayi baya naga DanMakaho na ta latsar Sadiya yana mata wasu abubuwan da na kasa hakuri sai da na mishi magana na nusar dashi Kanwarshi ce Muharamma, in kuma aure yakeso ya fada sai a mai, bansan ya akayi ba sai dai kawai naga ya kaini k'asa yana dukana Sadiya na tayashi da kyar su Hudu suka zo suka karbeni daga hannunshi".
Labiba ta bude baki tana kallon Aunty Aseeyah tace "Laah Aunty Karya takeyi, wallahi karya take musu, ba abunda ya faru ba kenan, karya ne" Aunty Aseeyah ta tabe baki ta koma kan dardumanta ta zauna tace "Labiba, meye naki? Sharri ai ba yau ta saba k'ala musu ba, In Allah ya tashi saka ma DANMAKAHO da k'anwarsa wallahi sai Hajia Shafa'atu ta wulakanta ta shiga hakkinsu sosai, wata irin Mata ce da muke neman tsarin Allah daga garesu".
Jin muryar Alhaji sukayi yana cewa "Allah ya tsine maka Zaid, matar tawa ka buga? Allah ya tsine ma ban yafe ba, watsatsse kawai" Labiba ta fashe da wani irin kuka, kamar ita a ka tsinemawa Aunty Aseeyah ta kallota tace "Labiba" cikin kuka tace "Aunty Asee Mahaifinshi ya tsine mai, Mahaifinshi ya laanceshi, be san gaskiar abunda ya faru ba, ya hau kan maganar matarshi, zanje in gaya mai gaskia, wallahi zan gaya mishi matarshi k'arya takeyi" ta zabura Aunty Asee ta taso don kamota, amma bata ci nasara ba, har ta kusa k'ofar Gidan Baban Sabit ya shigo, hakan ya sa tayi turus.
"Ina zakije?" kamar bata cikin hayyacinta tace "K'arya Auntynshi take mishi, wallahi ba haka akayi ba, ina bakin katanga, naji komai, yaya Babanshi tsine mishi yake" Baban Ameera ya kalli Aunty Aseeya, girgiza mai kai, ya sa hannu ya rik'o Labeeba ya jawota har tsakar gida ya zaunar kan tabarma yace "me ya faru" a hankali Aunty Aseeya ta bashi labarin abunda suka ji, jinjina kai yayi yace "to ke me zai dameki?" Majina ta ja kafin tace "Yaya, wallahi Allah sharri suka mishi, k'arya suke" ganin tana magana kamar me shirin fita hayyaci, ya ma matarshi alamu da ta shiga da ita ciki.
Aunty Aseeya ta kamo hannunta ta ja ta zuwa daki, bakin Gado ta zauna ta rafka uban tagumi, Aunty Aseeyah ta fita gun Mijinta, Kubra ta rasa me ke mata dadi, bata da kuzari, ko da suka zo bacci, hakan tayi ta juyejuye, haka Labeeba ta k'arashe darenta.
Washegari da safe idanunta sunyi luhuluhu saboda kukan da taci, bata san shi ba, amma abunda aka mishi ya tsaya a ranta, to shi wani iri ne da ba zai iya kare kanshi ba? Meyasa ba zai iya furta k'arya ake mishi ba? Shi sakarai ne? Haka ta tashi tayi shirin Makaranta, ta shiga ta gaida Aunty Aseeyah, Baban Ameerah ya kai yara Makaranta, Aunty Aseeya tace mata ta tsaya ta yi kalaci amma tace sauri take ta makara, adduan samun nasara ta mata, ta rakota har bakin k'ofar gidan, Adduan fita daga Gida Labiba tayi ta fice ta bi dogon hanyar unguwarsu ta Tudun Matawalle inda zata neman abun hawan da zai kaita National inda zata hau Motar Makaranta (School Bus).
Kasancewar Safiya ce, Unguwar bata cika sosai ba kamar yanda take cika wurin k'arfe 11 na rana, tafiya take cikin dan sauri, unguwar sai an fito bakin Titi ake samun abun hawa.
Daga chan nesa ta ke hango wani zaune na busar sigari, da sauri ta zaro wayarta don ganin lokaci, 8;17am, mamaki ya cikata, wanene ke banka ma cikinshi hayak'i da sassafe haka, da ta k'araso gurin sai ta ga matashin saurayine, daidai nan ya murje guntun da k'afa ya sake kyasta wani da ya zaro daga aljihun gaban rigarshi ya fara zuk'a.
Labiba ta dan yi jim tana kallon bawanAllahn nan, Zuciyarta na tunzurata kan taje ta mishi magana. Har tazo ta gabanshi ko kallonta beyi ba, haka ta tsallaka titi tana waigenshi har ta samu kekenapep da zai kaita National don tafia Hassan Usman Polythecnic.
#1love
#DM
#SonSo
#anatare
#Fikrawriters
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Uku3⃣
('YAN MAKARANTA)
Har lectures din ya k'are Labeeba bata fahimci komai ba, a hanyarsu na zuwa Masallaci yin Sallahr Azahar, Aisha Usman K'awarta take tambayarta lafiya yau ta ganta wani sukuku da ita, jim tayi kafin tace "Kaina ne yake dan ciwo amma ya bari yanzu" Aisha tace "haba ni dai ince, yau na ganki ga ki nan, Allah ya sauwak'e" murmushi Labiba tayi tana kara k'allon k'awarta.
Kafin su k'arasa Masallaci suka ji ana k'wala musu kira ta baya, dakatawa suka yi tare da dan waigawa, cikin hanzari ya k'araso yana me sakin su da k'ayattacen murmushi.
"Aisha, Labeeba, ya kuke?" a tare suka amsa masa da Ina wuni Captain Abu Sideeq? Ya amsa tare da cewa "kun gama lectures din yau ai?" Aisha ta gyada kai, Labeeba tace "eh mun gama" yace "Good, to kuje kuyi Sallahr, ku sameni a Ajinmu, sai mu duba karatun yau ko na 1hr ne" amsawa suka yi tare da wuce shi don nufar Masallacin.
Aisha tace "Son ki yake" Murmushi Labiba tayi, tace "na sani" da doki Aisha tace "I knew it, kema kina sonshi?" Labeeba ta sake wani murmushin kafin tace "ina dai ganin mutuncinshi, yana kuma burgeni, ina son naga mutum me k'wazo da basira" Aisha ta dan tafa hannuwanta tace "a sannu kema zaki fara son shi, ai ya hadune ya hada komai, ga bokon, ga addinin, ga kuma Kyaun".
Labiba tace "ba k'arya".
Daidai nan suka iso Masallaci, ko waccen su ta d'auki buta ta nufi Fampo.
Sun idar da Sallah suka nufi ND2 inda AbuSideeq yake, yana ganinsu ya k'araso yana jefan Labiba da wani irin kallon da shi kawai ya san ma'anarsa.
Murmushi kawai Labiba tayi, yace "muje daga k'arshen Ajin, yana gaba suna bin shi a baya, daga can suka samo Bench suka zauna, shi ne a tsakiyarsu, ba bata lokaci suka hado masa Jotting din Lectures Biyu da suka yi yau, dubawa ya yi kafin ya shiga yi musu bayani cike da k'warewa.
K'arfe 2:30 ya ce su dakata haka. Godiya suka masa me tarin yawa, ganin yadda AbuSideeq ke bin Labiba da wani irin kallo ya sa Aisha ta dan mik'e ta ce "bari na dan amsa waya".
Ganin haka yasa AbuSideeq fara magana "Labiba..." sai kuma ya yi shiru, ya sake fadin "Labiba ina... ina..." sai ya sake yin shiru, sai da, mintuna kusan 4 suka wuce kafin ya ce "bansan ya zaki dauki maganar nan ba, amma ina so in fada miki wani abu, amma kuma dai na kasa, k'ila rashin faden shi ne Alheri, bari kawai in bar shi, tashi muje na rakaku ku samu abun hawa".
Dago idanuwanta tayi ta kalle shi, kafin ta saukar da kai ta fara magana cikin sanyinta ta ce "So na kake yi, kana jin nauyi na, kana tsoron yadda za ka gaya mini, kana gudun kar hakan ya zaman silar bacewar kyakyawar Alak'ar da ke tsakaninmu?" da sauri ya kalleta.
Kai ya fara gyadawa kamar k'adangare. "Haka ne, wallahi haka ne Labiba, tun farkon haduwarmu a office din HOD, lokacin da Yayanki ya rakoki Registeration na kamu da sonki" Labiba ta danyi murmushi ta ce; "Ban yi mamaki ba, its obvious ai".
K'arfin guiwa ya samu, ya ce "Ina fatan zaki amince mini?" murmushi tayi ta ce "wallahi ban sani ba, bansan me nake ji a kanka ba, bansan me zanji nan gaba a kanka ba, amma nasan cewa ina matuk'ar ganin girmanka, sosai kake burgeni Captain, bansan ko nan gaba wata alak'a da ta wuce wannan zata shiga tsakaninmu ba, amma ko me ke nan, Allah ya zaba mana abin da yafi Alheri a rayuwarmu".
Kallonta kawai ya tsaya yi, sosai ta burgeshi, sonta na k'ara ruruwa a zuciyarshi, bai taba ganin irinta ba, bai taba sanin Matan Katsina na iya kallon Namiji haka su gaya masa gaskaya ba tare da wani 6oye-6oye ba, ba ta rufe mishi komai ba, ta gaya mishi iyakar gaskiyarta, hakan da tayi ta matukar burge shi, yana da tabbacin da wata ce, yaudarar shi za ta yi, ko ta ce mishi eh itama tana sonshi ko don wani abu, ko kuma ta bata mishi lokaci, ko kuma ta ja mishi aji, haka yake so Mata su kasance Straightforward, in ana haka, da ba a samu Yaudara da cin amana a cikin Soyayya ba.
Mik'ewa yayi yace "tashi muje na nema muka abun hawa" murmushi tayi tare da sa6ar jakkarta, ta bi bayanshi, a bakin kofa suka ga Aisha, tace "muje ko?" Labiba ta gyada kai, a haka har suka fita bakin makaranta ya tsaida musu keke Napep, fadin inda zasu sukayi, mai Keke Napep yace "ke ta tudun Matawalle ciki zaa shiga?" Labiba tace "eh ciki ne ta wurin Makarantar Hope" yace "150 ne kudinki, ke kuma ta k'ofar k'aura layout ki bada 250" da yake hakan suke badawa ba su tsaya ciniki ba.
Aisha ta fara shiga kafin Labiba, Labiba na ganin AbuSideeq ya sa hannu cikin Aljihu tace ma Adaidaita sahu, mu tafi kaji" ba tare da bata lokaci ba ya ja Kekenshi, ta dan juyo ta daga ma Captain hannu, shi ko yatsarshi ya nuna mata alamun "ke ko" kafin suka sakar ma juna murmushi.
Aisha tace "Bawan Allah, be gajia" Labiba ta gyara zamanta tace "kullum cikin Hidima yake".
**
Abu Sadeeq Abu, dan Department of Engineering HUK Poly, wani irin Yaro ne me matuk'ar k'okari, HND2 yake, a nan ya gama ND ya jona HND dinsa, a Dept din kowa na sonshi sabida kyakyawar Alak'ar da yake dashi da Malamai da Dalibai, k'okarinshi be daura mai Girman kai ba.
So da yawa in ana darasi, kace ma Mallami ba ka gane darasin yau ba, zai ce "ka sa min AbuSideeq a HND2 ya ma bayani zaka fi ganewa" hakan ne ya faru da Labiba a ranar da suka samu Mallama Amina bayan darasi, tace "ta sake mata bayanin wani fannin da bata fahimta ba" mallamar tace "Wallahi sauri nake, amma kije HND, ki samu a AbuSadeeq a HND2, kice ni na aiko ki, ya miki bayanin topic din". Labiba ta mata godia ta ja Aisha suka tafi inda Mallama ta mata kwatance.
Ko da sukaje sukayi tambaya, nuna musu shi akayi, yana tsakiyar maza biyu da mata 3 daga gani 'yan ND2, yan gaba da ajinsu Labiba, yana ta faman musu bayani. Aisha tace "mu jira ya gama, ko muje mu dawo" Labiba ta girgiza kai ta musu Sallama" suka amsa tace "ina wuninku? DonAllah Abu Sadeeq muke nema" kallonta yake yi sosai, yarinyar nan ce da Yayanta ya kawota office din HOD ranar da yake ciki, murmushi ya mata yace "Ga wani Abu Sadeeq nan"
Murmushi tayi sosai, ta ganeshi, shine HOD yace mata in tana da matsalar karatu ta zo gurinshi zai mata bayani".
"Sannu da Aiki, Mallama Amina ce tace na sameka, wani abu ne ya shige min duhu a course dinta, shine nakeso in kana da lokaci ka dan min bayani" Agogo ya kalla, kafin yace "Alright ba damuwa, amma ga yayyinki nan muna karatu, saidai in mun gama" tace "lahh dama ai sai kun gama" yace "to nam da 30mins InshaAllahu" murmushi ta sakar masu duka, sosai ta burge duk na wurin, tace "bari mu dawo" ta ja hannun Aisha da ba tace ma kowa komai ba.
Ya musu bayani yanda ya kamata, Labiba da Aisha sun fahimta, suka mishi godia sosai, yace musu daga yau duk bayan ko wane lectures suzo ya sake musu bayani, hakan zaisa su fi fahimta. Godia suka sake mishi, tare da exchanging numbers.
Tun zuwansu Poly Aisha ke tare da ita, tana son Labeeba sosai, duk da a Ajin Maza sunfi Mata yawa, matan basu wuce sha biyar (15) amma Aisha bata da k'awar da ta wuce Labiba, ko wata daya basu rufe a Makarantar ba, amma Aisha na jin Labiba har ranta.
Labeeba za ta iya rantsuwa Aisha na sonta matuk'a, kodayake ita dai haka take, indai ta zauna a wuri, to tana da farin jinin mutane, kowa na sonta, ba za a ce don Kyau ba, don ba fara ba ce, a'a, don kyauwun zuciyarta ake sonta, ta iya zama da jama'a, kowa nata ne, bata da zabin mutane da take mu'amala dasu.
Wannan kenan.
Labari suke da Aisha kafin a shiga layin Unguwarsu Labiba, Aisha ke hada ta da Allah tazo gidansu don Mamarta na son ganinta, har k'arya ta mata cewa Mamar ta ce in ita Labiban bata je ba to ita za ta zo gidansu Labiban da kanta, duk dai don taje Aishar ta ce mata haka.
Dariya Labiba ta yi tace "Insha Allahu zanzo wannan Satin, ki ce Mama tayi hakuri.
"Allah ya sa kana da chanjin dubu daya" cewar Labiba, mai Adaidaita ya buga tsako yace "Hajia sai kiyi magana tun wuri ni banda chanji" Aisha tace "nima wallahi dubun ne" mai A daidaita ya fara mita da ya san Chanji ne da be dauko su ba, gashi har ya kusa shiga Tudun Matawalle, Labiba tace "Afuwan, akwai shago a ta wurin zasu samu Chanji" mai Napep yace "ga unguwanku ba dadin shiga, balle jiya anyi ruwa" Labiba dai hakuri ta sake bashi, Aisha dai tsaki tayi tace "ya cika mita".
Daidai Shagon Eskaley ya ci burki, Aisha ta mik'a mishi dubu daya tace "gashi ka samo chanji ka cire duka" ko waigowa beyi ba yace "Yo Anguwarmu ne? ko sani na sukayi da zasu bani chanji?" Labiba ta lura Mai Keke Napep dinnan dan tijara ne, ta sauka tace "bari na samo" Aisha ta bude baki tace "ya za'ayi kije gurin 'yan Shaye-shayen chan? Haba Labiba ba mutuncinki bane a ga kinje chan shagon, ki bari ya samo" Labeeba ba ta tsaya ba, illa ta karasa bencin Eskaley da Sallama.
*
Zaune yake kan plastic chair, cikin wata longsleeve shirt da 3 quartern Sojoji, face cap dinshi wanda ya rufe kanshi har wurin idonshi ruf ma irin wandon ne, kayanshi kenan duk dunia, ya dora k'afa d'aya kan d'aya, Idonshi lumshe. Yana shak'ar k'amshi, yana jin dadin yanayin da World ke sashi,
World shine sunan da 'yan bencin Eskaley ke kiran Tabar Wiwi, a cewarsu, Ita Wiwin Duniya ce, ma'ana komai, in suka zuk'eta, jin kansu suke daidai da Saraki, Sarauta Wiwin ke sasu. In ka zuk'i World, kafi kowa, wannan ma ya sa Zaid zama shi kadai tare da ba su Master baya, wanda suke fama buga Whot ko na Sigari basu dashi.
Duk k'ullin Worlda naira dari biyu Eskaley ke saidawa, yana bada bashin Sigari, amma be yarda ya bada bashin World ba.
Tunda suka ga ta nufosu suka k'ura mata ido, Eskaley ya amsa yana washe hak'oranshi jajjaye, da murmushi ta kallesu tace "Ina wuninku, DonAllah chanji naira dubu nake son ka taimaka min dashi" ta maida hankalinta gun na cikin shagon, Eskaley yace "Ahhh, chanjin dubu da sauk'i, basu kai ba wallahi" Labiba tace "akwai Credit? Mtn?" "Aa wallahi ya k'are" dubu dayan ta mik'a mishi tace "to DonAllah ka dan ara min #350 na ba me keke Napep" Eskaley yayi daria yace "Hajia yau wallahi da sauk'i, yau ba ciniki"
"Oh Allah!" ta fada a gajiye, ta musu Godia ta juya.
"Ga 350" taji an fada murya a dakushe, ta juyo ta ga wa ke magana, bata samu kallon fuskarshi ba sai gani tayi wani ya fincike kudin da aka mik'a mata.
"Shege Mankas, kana da kudi a aljihunka kasa Eskaley ya hana ni World, kai mik'o min World dinnan" ran mankas 6ace yace "donuwarka bata kudin" master ya kalleshi yace "mankas ni zaka ma wulakanci don nace ka siya min World, don ni ba mace ba ce, banda kayan dadi ko? to ranta min uku da hamsin dinnan, zan baka" daidai nan mai Napep ya sake buga horn, Labiba dai ikonAllah take kallo.
K'yallararen idonshi ya dago ya kalli Master bece komai ba, Master ya buga tsaki ya matsa kusa da Labiba yana cewa "Danmakaho ya ga Chikala" da sauri Labiba ta kalli mazauna gurin don ganin dan Makaho, amma bata samu nasarar ganinshi ba don ya juya mata baya, dubu dayan ta mik'a ma Master, tace "ka bashi, na biyo shi chanji, zan zo na amsa" master ya yashe jajayen hak'oranshi yace "Yayata, donAllah ki bar min chanjin mana" tace "aa gaskia ni ba zan baka kudina ka k'ona su ba" da sauri Master yace "wallahi ba Sigari zan sha ba, abinci zanci Yunwa nakeji". Labiba tace "ban yarda ba, nidai ka ba DanMakaho chanjina".
"Haba Babbar yaya kin fi k'arfin dari bakwai da hamsin, nidai Godia nake" Horn mai Napep ya sake buga mata har yana mata masifa, da k'arfi master yace "dallah ware Mallam, zaka ishemu da Oda, ka bita a hankali ko na ci uwarka, Yayarmu Allah ya kiyayeki" Mai Adaidaita tuni ya shiga taitayinshi, kar ya sha duka a banza, Labiba na shiga ya ja Napep dinshi suka shiga cikin Unguwa.
"Master, bani" cewar DanMakaho, "me zan baka?" master yayi kamar be san me yake nufi ba, Haruna yayi wuf yace "kai Master, muna gani fa ta baka 1k, kuma muna ji tace ka ba DanMakaho chnajinta, kawai kawo kowa a bashi world daidaiya" DanMakaho ya dago k'yallararen idonshi yace "ku bani nan" Master yace "haba Mankas, yawa kakeyi wallahi, kai ma fa World dinnan ka taba, kuma ka hanani, ka bari mana Eskaley ya bamu daidaya".
"DonAllah Mankas ka bar mana kudin nan, haba mana yawa kake" mik'ewa yayi ya fizge kudin, tare da cewa "In tazo k'arbar chanji ta uwar me kuke so na ce mata?" Master yayi wuf yace "ta fa bani" DanMakaho ya zira kudin Aljihun gaba inda Kwalin Sigari ke ciki, tare da fadin, "in na bata ta baku".
Barin gurin yayi, ya shiga cikin unguwa, su Master suka bishi da Ashar kala-kala ransu bace.
**
5:20pm
Baccin Awa 2:30 yayi, yana farkawa World ta sakeshi, ko da yake be shak'eta duka ba, Kewaye ya shiga ya dauro alwala, yazo ya hada Azahar da La'asar, rigarshi ya shinshina yaji tana warin zufa da rana ga kuma k'aurin hayak'i, guntun tsaki yayi, be yarda ya zauna da dauda ko k'azanta ba, duk da wadan nan sune suturunsa, sai wata bak'ar jallabiya da yake sawa a duk lokacin da zai wanke riga da wandonshi yana iya k'okarinshi wurin tsaftace su, be son shiga cikin Gida amma dole ya shiga ya dauko sabulu, ya ga dan Shegiar da zai hanashi.
Straight ciki ya shiga, da Hudu ya ci karo ya fito kamar mara gaskia, yana zare ido, da sauri ya wuce boysquaters, da dan mamaki DanMakaho ya kallesh yana mamakin saurin da yakeyi kamar wanda yayi k'arya, amma da yake ba damuwarshi bane sai yayi gaba ya shige Store ya dauko Klin.
Ya na fitowa daga Store yaji Aunty Shafa na cewa "Uban wa ya dauke min Naira Dubun da na aje kan Center Table" Annah ta fito daga daki tace "nidai Wallahi Aunty bani bace, tun dazun ina daki" Fati tace "ni kuma wallahi ban ma san kin aje kudi ba" "duk dauke dauken da ake min bana magana, yau abun ya isheni, daga in aje kudi in shiga in fito sai na nema kudi na rasa? ina Sadiya?" Fati tace "tana cikin dakinta ko?" Aunty shafa tace "na san itace, ya zaayi dama ku dauka, aiko ko ta bani kudina ko na mata mugun bugu, kuma Ubanta yazo ya biyani kudina"
Mankas be gama jin sauran zancen ba ya banko labulen Parlo ya shigo, ya na bude idonshi ganin ina Sadiya, ganin bata cikinsu ya kutsa cikin dakin ya ganta chan gefen gado me kama da na 'yan boarding durk'ushe tana karkarwa, ga dukkan alamu ta ji zantuttukan su Aunty Shafa, kuma ta tsorata, be tsaya kwantar mata da hankali ba ya finciko hannunta ya ja ta har Parlo gaban Aunty Shafa ya tsaya.
"Uwar da ta fasa taba ta, ta raina Uwar da ta haifeta" duk suka yi cirko-cirko ba me motsi, ya juya ga Annah da Fati, yace "duk randa kuka sake daga mata hannu, sai na sassareku" Aunty Shafa tace "Dubu daya ta ta dauka, kuma sai an biyani, DanMakaho ka fita idona, ni ba sa'arka bace, Uwarka ma bata fara yi dani ba, wallahi ku firdo min Kudina kafin Daddynku ya dawo, kaga duk inda yake yana daf da Gida, ku bani kudina, ba zai ji komai ba".
Baki na rawa Sadiya tace "Wallahi Aunty bamu dauka ba" Mankas ya daka mata tsawa yace "dallah kyaleta, munje mun dauka, ba za kuma a bayar ba, in ya dawo me zaiyi? Tsine min? Wani irin tsinuwa ne zai min wanda be min ba? Mtswww" ya buga tsoki kafin ya ja hannun kanwarshi suka fita daga Parlorn.
Daidai nan Hudu ya shigo yana zare ido, "Wai meye ke fariwa nake jin Hayaniya Hajia?" Kwafa Aunty Shafaa tayi tace "dani Dan Makaho yake cikin Gidan nan, wallahi zaman Gidan nan sai ya gagareshi fiye da yanzu, bari Alhaji ya dawo".
*
Zaunar da Sadiya yayi gaban k'ofar dakinshi ya dan bata baki, tare da kwantar mata da hankali ta hanyar gaya mata zai rok'i Babansu kan ya barta taje Gidan Mamansu hutu, sai da ya ga ta saki ranta kafin ya koma daki ya dauko Bak'ar jallabiyarshi ya zura, ya kwaso Riga da Wandon da zai wanke tare da bucket a toilet, cire abubuwan gaban Aljihunshi yayi, da Mukulli, da kwalin Sigari, da Naira dubu daya ya ajiye k'asa, Klin ya Jik'a ya fara tsoma rigar ya fara cudawa.
Be gama wanke Rigar nan ba yaji muryan Daddynshi yana fadin "Ina Dan Makahon yake?" dago idonshi yayi ya kalli Daddynshi da ya nufosu kamar Zakin da ya kwana 7 be ci abinci ba, duk 'yan Gidan sun rufa mai baya, kafin ya ankara Daddynshi ya sakar mai nushi kala biyu a gefen baki, ko motsawa beyi ba, Sadiya ta fashe da kuka.
" Sata? A gidana DanMakaho? Dama duk sace-sacen da akeyi kai ne? Yau dubun ka ya cika, yau wallahi sai ka kwana bayan Kanta" wayarshi ya dauko ya latso DPO, Sadiya ta zube gabanshi tare da rikon kafarshi, tace "Daddy Wallahi ba shi ya daukar mata Dubu dayanta ba, wallahi bashi bane, Daddy, Klin kawai ya shigo ya dauka, Daddy ka yarda damu" Haurinta yayi dai da ta matsa gefe, da sauri Mankas ya karasa gunta ya durkusa tare da dagota yana watsa ma 'yan Gidan mugun kallo, ya tsaida kallonshi ga Mahaifinshi ido cikin ido yake kallonshi.
"Zaid Mahaifinka ne, Zaid kar ka manta Soyayyar da ya wanzu tsakaninku, Zaid kar ka sake ka yi ma Mahaifinka ba daidai ba, duk yanda zuciya ke tunzuraka kan ka mishi wani abu, Zaid ba zan yafe ma ba, kar ka ga tsinuwan Mahaifinka kamar baya tasiri a kanka, Zaid a ranar da zan juya ma baya, Zaid ka rasa Lahirarka wanwar, Zaid Mahaifinka ne, ba komai tsakaninku sai k'auna da kyautatawa" muryar Mahaifiyarshi yaji na mai kuwa kamar a lokacin take magana.
Runtse ido yayi sosai, muryar Hudu ta katseshi inda yake cewa "Lahhh, ga Dubu daya chan" da sauri ya bude idonshi, ya ga Hudu har ya durkusa ya dauka, da azama ya karasa shima ya rik'o kudin, idonshi duk biyun ya bude su yace "Sake min kudi".
Aunty Shafaa ta karade da "Wallahi dubu daya tace, ashe dama kai ka dauka, in kace kana so ai DanMakaho dubu daya ba komai bace, zan baka, amma meyasa zaka daukar man kudi?".
Daddy yace "Zaka sake kudin nan ko sai ranka ya baci?" sai da Daddy ya sake maimaitawa kafin ya sakar, ran Daddy a bace yace "Shege Barawon Banza, kaji haushi" halbi Zaid yayi da Bokitin Wanki, ya shige daki rai a dagule.
***
Zaune suke gaba ki daya , Fira sukeyi har Yara suna dariya, daga bisani sukaji an fara iface iface, sosai su ke jin abunda ke faruwa daga kan tabarmar da suke zaune,
Labiba ta mik'e da sauri ta k'arasa jikin Bangon Gidan, nan taji komai,
Girgiza ka ta farai kamar k'adangaruwa, "Wallahi ba sata yayi ba, Aunty Aseeyah wallahi dubu daya ta ce, kudina ne, ni na bashi, Aunty DanMakaho ba Barawo bane, Ya Illahi".
°°°°°°°
Kindly Vote and Comment Line by Line
#1love
#DM
#anatare
#™SonSo
#FWA
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DANMAKAHO 😉
4⃣
Rikota tayi da hannu biyu, "Labiba, ki yi min magana". Naunayar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta bata labarin abun da ya faru dazun.
Aunty Aseeyah tace "Labiba, akwai abubuwa da yawa dake faruwa gidan Alhaji Ali Zaki, tun kafin zuwanmu Unguwar nan, ba zaki gane ba, amma akwai 6oyayyen alamari tsakanin duk wani rai da ke cikin gidan, wanda ba hurumin mu bane, ba mu da wata alak'a dasu da ta wuce makwafataka".
Labiba ga kalli Matar Yayanta " Aunty, Hakkin Makwaftaka fa? wannan babban hak'k'i ne, ya kamata a yi wani abu a kai, so biyu ina jin Makirar Matar nan na hada makircinta, ba zata tsaya a nan ba, ba za kuma ta bari ba, ya kamata Aunty a tari Alhaji Zakin".
"Hmm, Labiba, fadan da ya fi k'arfinka sai ka maida shi wasa, ba abunda za mu iya yi. Hajia Shafa, ta zarce tunaninki, bana son matsala da Hajia Shafa, yanda ba abunda ya taba hada mu, bana son komai ya hadamu, amma tabbas Dan Makaho da k'anwarshi na buk'atar Addu'a, shi kawai zamu taya su".
Hannu ta sa ta ja dankwalinta baya, murya k'asa k'asa tace " Sakarai! Kamar ba namiji ba, ba ya iya kare kanshi? Meyasa be iya k'aryatasu in sun mishi sharri? Mts"
Aunty Aseeyah tace "Magana kike?" girgiza kai tayi tare da mik'ewa ta shige daki
5/5/2013
1:30pm
Tunda garin Allah ya waye zuciyarta ke mata kitse-kitse, DANMAKAHO k'wak'walwarta ke kwada ma kira, baza ta iya shaidashi a hanya ba don ba saninshi tayi ba, dalili take so ya sa ta ga DanMakaho, kamar shekaran jiya, da tunaninshi ta tashi, ta damu da lamarinshi, abu kamar a film ko a littafan hausa, so take ta shiga rayuwarshi, so take taji damuwanshi, abun da kamar wuya, amma sosai take so ta hadu dashi, haduwarsu ta farko in brief ne, ko ganin fuskarshi ba ta samu tayi ba, gashi yau ba ta zuwa Makaranta balle ta sa ran ganinshi a Waje, haka kurum ta tsiri zuwa Gidansu Aisha.
Yara na Tahfiz, Parlo ta iske Yayanta da Matarshi, a gefen Kujera ta zauna tana musu murmushi "Yaya, ina neman izinin zuwa Gidansu Aisha Usman, Mamarsu ke son ganina, har cewa tayi in ban zo ba, ita zata zo".
Dan dariya sukayi kafin Yayan yace "Kinsan Gidan ne?" Girgiza kai tayi alamun aa kafin tace "kwatance ta min" yace "to bari naci Abinci na saukeki" tace "to shikenan nagode".
*
Da kwatance suka gano Gidansu Aisha, dari biyu ya bata yace " ki hau Adaidaita sahu, kuma kar ki kai Maghrib"
Godia ta mishi, Aisha ta gaisheshi sannan suka shiga Gida.
Ina za'a saka Labiba don murna, tunda ta tako cikin gidansu Aisha ta ke cin karo da Soyyayar mutanen gidan, har Mai aikinsu ta san Labeeba, da kaunar da ke tsakaninsu.
Ya Illahi, haka suke sonta? Barin ma Mamar Aisha da take ji kamar ta goyata, kayan mak'ulashe a ka cika gabanta, daga bisani a ka kawo mata Abinci mai rai da lafia, ita dai Labiba daria take tayi, tana cikin cin Samosa Aisha ta k'atseta da cewa "Zo muje ki gaida Daddy".
Kunya ya kama Labiba, "DonAllah ki bari sai anjima" Aisha bata saurareta ba, sai jan hannunta tayi don ta mik'e tsaye tare da janta ta na gaba Labiba na bin ta a baya.
Har k'asa ta durkusa ta gaida Daddy, Daddy ya amsa cikin kulawa ya dauko dubu biyu ya bata, bata iya amsa ba sai dai Aisha ta amsar mata sukayi Godia suka koma dakinsu Aishan. Sai da Laasar yayi suka yi Alwala don yin Sallah.
Labiba na adduointa ta ji kamar ihu daga waje, sai da ta kasa kunnuwanta sai taji ashe Ihun murna ne da alamun bak'i sukayi, tashi tayi ta ninke Darduma, ta zauna gami da tsiyayo kunun Aya a Cup. Aisha ce ta shigo fuskarta dauke da murna. "Besty kinsan me? Cousins dinmu ne sukazo daga Abuja wallahi dadi kamar ya kasheni".
Labiba tace "Inye, fatan sunzo Lafiya" "Lafiya lau wallahi, taso muje ku gaisa" hararar wasa ta jefeta dashi, ta dan muskuta tace "tafiya zanyi ni, banason marace yayia ina waje, kuma dai zaun daura Sanwar dare" Aisha ta san ta mata tunda tun bayan Azahar tazo, don tace zata tafi yanzu ba wani abu ne. Mikewa tayi tace to "barin sanar da Mama".
Labeeba tace "ke dai jira mu tafi tare, katon gyalenta Khashka me kauri ta yafa, Aisha kuma ta janyo wata yar gyale bayan ta mata packaging su Samosa da Springrolls tace a kai ma su Ameera.
Ba ta Parlor inda ta barsu, ba dai har sun tashi ba? Da sauri ta ja hannun Labeeba sukayi tsakar Gida, inda ta gansu tsaitsaye, kallo ta bisu dashi kafin tace "Yaya Hafeez ba dai kun fito ba". "wallahi kuwa A'i, gwara muje mu gaida Hajia Kaka kafin ta kira Abba tace Munfi Awa 8 a katsina bamuje mun gaisheta ba".
Dariya sukayi gabaki daya, Mama tace za kuci Gidanku, Sirrikar tawa kuke ma iyashege?" daria suka sakeyi. Mama tace "Af! Labeeba ba dai kin fito ba" ta dan k'araso garesu cikin takunta tace "Wallahi Mama gwara na tafi, Marece yayi" Mama tace "eh Gaskia ne".
Dukkansu Maza Ukun idanuwansu suka zuba ma Labeeba, idanuwa taji a kanta, ta dan dago ta kallesu su ukun a lokaci daya tace "Ina wuninku? Kunzo lafiya?" amsawa sukayi a tare suna kallonta sosai, Aisha tace "Besty, wadannan sune yanuwana rabin Jikina, kika tsaga tsokata Jininsu kawai zaki gani".
Dariya Labeeba keyi wanda ke k'ara ma fuskarta kyau, ta cigaba da sauraron Aisha, "ga Yaya AbdulHafiz ga Yaya Abdulmajeed kuma ga Yaya Jawad, yau yau dinnan suka zo daga Abuja don Sada zumunci" wani murmushin ta sakeyi, tace "Barkanku da zuwa Katsina ta dikko Ya Abdulhafiz Ya Abdulmajeed da Yaya Abdul-" ta dan yi shiru tana son tuno sunan gudan, wanda suka kurawa junansu ido shi da ita, murmshi ya mata ya girgiza kai yayi yace "ba Yaya Abdul bane, Yaya Jawad ne" kamar bitar karatu ta maimaita "Yaya Jawad".
Aisha ta katsesu tace "Brothers, ga Besty ta, Labiba Ahmad" a tare sukace "Labiba" Mama ta dan murmusa tace "cikinku wa zan ba Diyata?" ta fada tana dafa Labibar da tayi saurin sadda kai k'asa".
Yaya Abdulmajeed yayi karaf yace "Ni zaki ba Antisco, Yaya Hafiz na da Mata, dama nine online, kinga sai in hada da Aminiyarta na aure, kinga no kishi".
Aisha ta harareshi, tace "sai me don na hada Miji da Besty ai ba wani abu bane, ba dai kai bane Mijin"
Dariya Ya Majeed yayi yace "to ni nace ke na ke nufi ne? Nidai Antisco ina so" Mama ta yi Daria, ta maida dubanta ga wanda take ma Labiba kwadayi tace "Jawad fa?" murmushi kawai yayi da ya sake kallon Labiba.
Ya Hafiz yace "nifa bangane ina da Mata ba, don ina da Mata sai aka ce ba zan iya sake ta biyu ba?".
Antisco tayi daria tace "to zan raba gardama, kuzo ayi tseren gudu, wanda ya riga zuwa bakin Gate, shi zan ba damar daidaitawa da Diyata Labiba".
Kafin ta rufe baki tuni Jawad ya ruga a guje ya isa bakin gate daria suka sa baki dayansu, Abdulmajeed yace "Cheating! Ni fa Mancy ban shirya ba, gaskia a sake" Mama tace "Wani ya hanaka shiri da wuri? Ni Jawad na ba dama" Ya Majeed ya cubune fuska yace "dama Antisco na lura kin fi san Jawad" Daria suka sa baki daya.
Labiba tayi saurin katsetsu da cewa "barin tafi, yamma na k'arayi" Mama tace "ki tsaya su Jawad su sauke ki sai Aisha ta raka ki" Labiba tace "Baban Amira Zaiyi fada, bari dai in samu Keke Napep" duk sai ta burgesu duka.
Mama tace "Gaskia ne, to besty mungode, mungode Allah saka da Alheri, ki gaida Aunty Aseeyar da yaranta" Labiba tayi murmushi jin sunan da Mama ta kirata dashi wai 'Besty' tace "sai anjimanku" tayi Gaba Aisha ta bita a baya.
"Nidai Antisco wallahi tayi min ina so" Jawad ke fadin maganar nan, Antisco tace "dagaske Jawad?" "wallahi Antisco" Mama tace "maza je ka karbo numberta, gwara ta baka da hanunta" da dan gudugudu ya bi bayansu, har sun fita bakin gate, k'arasawa yayi gunsu yana dan haki, Aisha tace "Ya Jawad ya akayi ne kake gudu?" wani kallo me wuyar fassaruwa yabi Labiba dashi tare da cewa, "Zuciyata na biyo, zuciyata, ta tafi dashi" tafi Aisha tasa, ita kuma Labiba ta rufe fuskarta da hannu biyu.
Dan gefe Aisha ta tsaya don basu wuri su dan tautana.
Kallonta yake cikin ido, duk jarumta irin tata sai da ta kasa jure kallon, sadda kanta tayi k'asa, cike da shauk'i Jawad yace "Labee" da sauri ta dago ta kalleshi, jin sunan da ya kirata dashi, murmushi mai nuna jin dadi ta mishi.
"Ba zan tsayar da ke ba, Yamma nayi, ki bani numbernki DonAllah" "ka karba gurin Aisha" girgiza kai yayi da sauri yace "Haram, ke zaki bani da hannunki, in kuma hanani zakiyi shikenan" yayi fuskan tausayi kamar mai shirin kuka.
Dan daria tayi me k'ayatarwa tace "be maka kyau ba" ya dan kallota yace "mene?" tace "shagwabar mana" dan bubbuga k'afa ya fara yi kamar dan yaro, da sauri tace "Ya hakuri Baby kar ka tara min jama'a kawo wayar na sa ma".
"Baby,Wow, sunan da aka bani yayi dadi" da sauri ta girgiza kanta da hannuwanta bibbiyu kamar mai yin bye bye tace "ni fa ba wannan Babyn nake nufi ba, naga kana abun yara ne shiyasa na kiraka da Baby". Kafadunshi ya daga " Oho, nidai zan dauka a matsayin Dayan, yanzu dai gashi ki samin number" karba tayi ta sa Numberta.
Tsaida mata Keke Napep sukayi, Jawad ya bude mata k'ofa yace "kin k'i yarda na kaiki Gida ko?" murmushi tayi tace "Bye Ya Jawad" lumshe ido yayi ya bude "Good bye Labee" Aisha ta bude baki ganin yanda Bestynta da danuwanta suka shagala da aika wa junansu sak'onni, "Hello! An manta dani ko? To ina wurin besty?" Kunya ya sa Labeeba rufe fuska tana daria, ta umarta mai Keke Napep da su wuce.
***
5:45pm
Tuk'i Yaya Hafiz keyi cike da nutsuwa, sun fito daga Unguwar Alk'ali Gidan Kakarsu, zasu tafi su aje Sak'o kafin su wuce Masauki don Gobe zasu wuce Abuja.
Yaya Hafiz yace "Yauwa Majeed, kira Yaron Mancy mu biya mu kai mai sak'on nan don ni gaskia nagaji ni da fita sai gobe".
AbdulMajid ya ciro wayarshi daga Aljihu ya latso numbern da Mancy ta bashi, har wayar ta katse ba a dauka ba, sake dialing yayi nan ma ba answer.
"Ba ya dauka fa" cewar Majeed, Hafiz yace "Kira Mancy ka gaya mata" dialing Numbern Mancy din yayi ringing na biyu ta dauka.
"Assalam Majeed" ta fada cike da Murna, "Hello Mancy ina wuni, dama mun ta kiranshi dan mu bashi sak'on be dauka ba" "Oh Allah, sorry na wahalar daku, ko ku barshi" Majeed yace "haba Mancy, har muzo gari kuma mu juyo da sak'o? Ba wani abu bari na sake kira InshaAllah zamu sameshi".
"Nagode sosai, bari nima in kira k'anwarshi in ba ya nan sai ta amsa" nan suka katse wayar.
Tudun Matawallen suka nufa kamar yanda Mancy ta gaya musu.
Majeed be fasa trying numbern shi ba, Jawad har ya k'ulu, shi fa be son bacin lokaci, tsaki ya sake yi, shi ba Fan din Mancy bane, be kuma k'inta, kawai dai bata cikin 'yan kayanshi kamar yanda yayyunshi biyu ke yinta.
Sun fi minti 10 a cikin Tudun Matawalle basu san inda zasu ba, sake kiran Mancy Majeed yayi tace "kuyi hakuri, wallahi wayar k'anwar tashi kashe take, na kuma ta kiranshi be dauka ba wallahi, kuyi tafiarku kawai Majeed".
"To Mancy ya sunan Maigidan sai muyi sallama mu bada a ajiye musu" dan jim tayi na wasu sakwanni kafin tace "kawai Majeed ku dawo ba wani abu" ba ya so ya matsa sai cewa yayi "to Mancy, amma banji dadi ba" ya kashe wayar ya ce masu "tace a bari kawai, amma banji dadi ba wallahi".
A k'ufule Jawad yace " to ya zamuyi, nan zamu lallace? Ya Hafiz mu tafi please" ta Mirror Hafiz ya kalli k'aninshi da harara yace "Jawad!!!" kawar da kai yayi, Hafiz yace "Majeed sake kira" Majeed yace "for the 14th time, Allah ka sa ya dauka".
Bencin Eskaley
World DanMakaho ya zuk'a, sarauta ta sa mai, k'afa daya kan daya ya daura, yana kallon kowa a dage, me tsautsayi kawai zai shiga harkanshi yau, yanda yake jin kanshi tsaf zai kakarya mutum.
Master da su Haruna ke buga Whot, suna yi suna busar sigari, yau ma basu da arzikin siyan World,sunyi ma Eskaley Magiya amma fir ya k'i basu".
"Wai Mankas ba wayarka ke k'ara ba tun dazun, kusan so 10?" Haruna yace "yo ina zai iya dauka, World fa ya ta6a" Master yace "yo in baka dauka ka kashe shegia mana, ni nan ta cikan kunne"
Tsaki Eskaley ya buga ya mik'e ya nufa Mankas hannu ya sa a Aljihun gaba inda Wayar ke k'ara, dauka yayi kafin ya amsa da "Hello?".
"Eh Hello, Zaid?" daga bangaren Eskaley yace "Eh to ba Zaid din bane" daga dayan bangaren a ka ce "DonAllah gamu a Tudun Matawalle, sak'o aka bamu daga Abuja mu kawo ma Zaid, don Allah ina zamu sameshi?" Eskaley yace "kuna ta ina?" "mun dan shiga cikin Anguwar" "Ayya, ku dawo farkon Anguwar, akwai wani kiosk nan Yellow".
Eskaley ya kalli su Master yace "Daga Abuja aka aiko wasu gun Mankas, gashi Mankas na birnin Sin ya zaayi?" Master yace "to ya fa? Uban kowa ya san Mankas na eh ya ne".
Horn sukaji na wani mota bak'a k'irar 507, duk suka tashi don yau kakarsu ta yanke sak'a.
Wayar Mankas ta sake ringingin Eskaleh ya dauka " Hello? Kaine a bakar Mota? Eh nan ne, barin zo" Eskaley yayi gaba, su Master na binshi a baya.
Ta Window suke kallon masu tunakaro su, "'Yan Shaye-Shaye ne" cewar Jawad "Mai ya hada yaron Mancy da Shaye-Shaye?" inji Hafiz, ba su da wannan amsar illa fitowa da sukayi gabaki dayansu.
Musabaha sukayi da dukkansu harda Jawad da ya mik'a musu hannu a kyamace, su ko 'yan bencin Eskaley kamar su musu Sujjada don biyayya, Hafiz ya kallesu daya bayan daya, ya lura duk ba na kirki cikinsu, duk warin Sigari suke, daurewa dai yayi magana yace "Ina Zaid?" Master da Haruna suka kalli juna suna tunanin waye Zaid? Shaf sun manta da wani Zaid".
Kafin Master yace "au Mankas? Gashi chan baya, in sak'o ne ku kawo a bashi" Majeed yace "Aa, hannu da hannu zamu bashi" Haruna yace "Ai Mankas ya hau network, ba zai gane bayanin da zaku mishi ba, mune Aminnanshi".
" DanUwarku Mahaukaci ne ni da ba zan gane bayani ba?" gabaki dayansu suka juya, Mankas ne ke tunkaro su, tuni Master da Haruna suka matsa mai ya k'araso yana k'are musu kallo duk a dage, ya tsaya kan Jawad mai kallonshi a k'yamace, Mankas ya wurga mishi mugun kallo shima kafin ya kalli su Master yace Duk ku ware?".
Hafiz ya mik'a mishi hannu, k'in amsa yayi, ran Jawad ya mugun baci, Majeed yace "Zaid, Mancy ce ta bamu sak'o mu baka".
Runtse ido yayi da k'arfi ya bude, tuni ya dawo hayyacinsa, Hafiz ya nufa da sauri ya dan durkusa " DonAllaj kayi hak'uri babban Yaya kuyi hakuri, wallahi akasi aka samu" daga yanda yake magana sun san a buge yake, yana dai k'okari ya dawo hayyacinsa ne.
Hafiz ya girgiza kai yace "Zaid, Mancy Mutuniyar kirki ce, donAllah ka bar Shaye-Shaye" da sauri Zaid yace "Wallahi na bari, ba zan k'ara dama yau na fara" sun san ba gaskia ya fada ba amma dai suka share" Majeed ya bude Booth ya dauko Ghana MustGo dan k'arami ya mik'a mishi.
Karba yayi, yace "nagode, Allah tsareku, ko uban wa ya tabaku ku gayan naci uwar mutum, duk garin Katsina, ko da kuwa Sarkin Katsina ne".
Takaici ya sa Jawad saurin fadawa Mota, Majeed ya girgiza kai yana mai fatan shiriya, shiko Hafiz da yake Ustazu ne sai da ya sake masu Mankas da abokanshi nasiha kan su bar Shaye-Shaye.
Nan suka fara mishi rantsuwar kaffara kan sun daina ba za su sake ba. Master har yana k'arawa da cewa dama don rashin abun yi ne ya sa suke Shaye-Shaye. Hafiz kudi ya ciro kusan 10k ya basu.
Master yayi wuf ya amshe tare da zuba Godia kamar zasu goyasu. Addua suka dinga zuba musu har Hafiz ya shige Mota ya ja suna mishi byebye.
Mankas be tsaya bin ta kudin da aka basu ba ya dauki ghanar nan ya danna a guje yayi Gida kamar wani zararre.
Su ko su Master yau take Sallah, World suka siya kowa qulli biyar biyar.
Washegari
5/05/2013
Tashi sukayi yau ba ruwa a Gidan, Drums dinsu empty, dama da k'yar suka samu Ruwan Alwala da Asuba, ko ruwan da zasu dafa suyi kalaci basu dashi.
"Oh ni Labiba ya zamuyi? Gashi Baban Amira bacci yake yi balle yaje nemo mai ruwa, bansan tadashi wallahi" Labiba tace "to Aunty Aseeyah ko in fita inga in zan samu mai Ruwan?" dan shiru tayi tace "Oh, ko zaki dan lek'a Gidan Alhaji Zaki ki samo mana a Kettle? Naga su borehole garesu".
Ba tare da wani tunani ba tace "eh wallahi barin shiga, ina zuwa" da sauri ta fita.
Aunty Asee mamakin Labiba take kawai ta ga fuskarta da walwalwa daga cewa taje Gidan Alhaji Zaki debo ruwa.
Maimakon Kettle wani Plastic Bucket na fenti taga ta dauko.
"Aa Labiba, ina zaki iya daukan wannan Bokitin, ki dibo a Kettle din zai isa kafin Yayanki ya tashi, ya nemo mai ruwa". Da murmushi tace "Anty Aseeyah kar ki damu, zan debo daidai ni" bata tsaya jin me zatace ba, tafita da sauri tana jin wani annashuwa a tattare da ita burinta daya, Allah ya sa ta Hadu da DanMakaho.
**
Tun jiya da ya kwanta bayan Maghrib be farka ba sai yanzu, fitowa yayi don ruwa be zuwa a toilet dinshi, Alwala zaiyi ya hade sallah tun Maghrib din jiya zuwa Asubar yau.
Fitowa yayi zuwa Babban Tankin Gida.
"Hajia masu Gidan bacci suke, nikuma banda hurumin barin ki diban ruwa, aikina Gadi kawai".
"Yauwa ga DanMakaho nan" karasowa yayi gunshi yace ya akayi ne Manu?" yauwa wannan yarinyar Gidan Baban Amira take, ruwa suke so a tsammasu" juyawa yayi ga Labiba da ta shagala tana kallonshi, da kannennen idonshi ya kallota yace "ki shigo ki diba, Manu barta ta diba".
Kamar sakara ta bi bayan dan Makaho har bakin Tank din gidan, karban Bucket din Labiba yayi ya tara a Fampo ya bude fampon, hankalin Labiba na gun karantarshi,
fari ne, amma wahalar rayuwa ta maida Fuskarshi bak'i, bayan hannunshi da dan haske amma tafin hannun da duhu, bakinshi ma yayi duhu, ganin kallon k'urillan da Labiba ke mishi ya sashi cewa " Chanjinki na nan, in na chanza zan kawo miki".
Wani irin kallon da be san na meye ba take binshi dashi, ji yayu ta fara magana tace "Meyasa?" dan kallonta yayi da kannenen ido me kama da bacci yace "Meyasa sai nayi chanji zan baki chanjinki?".
Da sauri ta girgiza kai tace "Meyasa baka iya kare kanka? Meyasa kake tsayawa ana daura maka laifin da ba naka ba? Meyasa kake daukan laifin wasu? Duk a zatona DanMakaho nakasasshene da ba zai iya tabuka ma kanshi komai ba, a zatona Dan Makaho bai da karfi da ikon kare kanshi, ashe ba haka bane, ashe kawai Dan Makaho Matsoraci ne, ashe dan Makaho ba zai iya tsayawa garkuwa ma k'anwarshi ba" baki bude yake kallonta cike da dumbin mamaki.
"Yanzu ba lokacin bude baki bane ka kalleni kamar Photo, ina jinka jiya da aka ce ka dauka naira dubu dayan da na baka, ba sai ka min k'arya ba, na san baka da ko sisi, ina kuma ji ranar da akace kana iskanci da k'anwarka, ina son sanin dalilin da ya sa baka iya kare kanka".
Da k'yar yace "Wacece ke?"
••••••
Yay!!! Late night post
Afuwan
Dont forget to vote and comment line by line
#1love
#DM
#anatare
#FWA
#SonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Biyar (RUWAN SAMA)
Barka da Sallah Bibilicious freaking fans, da fatan anyi Sallah Lafia? Allahu ya maimaita mana na badin badada.
Okay, please, before you start reading Vote first, number of Votes na decreasing, ku bani barka da Sallah ta hanyar voting kafin karatu Nagode.
"Dan Makaho ba tambayar da zaka min ba kenan, ka gaya min mene dalilin da ya sa ba ka iya kare kanka?" shiru yayi be da niyyar amsata.
"ba fa shiru zaka min ba, amsa nake so ka bani, meyasa kake daukar laifin da ba naka ba?"
Hannu ya sa ya shafi sumar kanshi "first of all ki daina min magana kamar wata uwata, secondly ba zaki ta6a ganewa ba, everything is beyond your expectations (komai ya zarce zatonki)" wani kallon mamaki take bin shi da shi, turancinshi mai kyau ne kalar na turawa.
Mamaki ya gani a fuskarta "Oh wow! kallon jakki, dak'ik'i kike min. I'm a Graduate Miss, thank you very much for asking, in kinaso zo in daura miki ruwan a kai, in ba kya so kuma sauri nake Sallah zanyi".
Bata gama mamakin da yace shi Graduate ba ne kuma taji wai Sallah zaiyi da mamaki tace "Asuba?" ba tare da jin komai ba yace "da Maghrib da Isha'i ba".
"Auzubillahi, haba Dan Makaho, me kake yi haka da ya hanaka Sallah? Me kakeyi da ka tara Sallah haka? Kai banji dadi ba wallahi, ka bari bana so" fada ta fara mishi sosai.
Cike da Mamaki ya dubeta kafin yace "To Hajia Maryam, zaa bari". Kallonshi ta danyi tace "wacece Hajia Maryam? Ni sunana Labiba?".
"To ai naga kin tasani gaba kina ta min fada, in ba uwata ba, ba uwar da ta isa ta tasani gaba tana min fada, kuma ni bandamu da sanin sunanki ba, kuma ki daina labe kina jin gulma, duk randa kika sake tsareni kika titsitseyeni da tambaya sai naci Uwarki".
Ya dauki Bokitinshi yayi gaba ya barta tsaye cike da mamakinshi, dan bude murya tayi yanda zai jiyota tace "ai dai ban tsoronka, zamu sake haduwa kuma" ba tare da ya juyo ba yace "aiko zakici Uwarki".
Da sanyayyar guiwanta ta dauki handle din bokitinta ta fita guiwa a sage.
Tana shiga Gida ta diba ruwan a tukunya ta kunna Risho.
Aunty Asee na lura da ita, yanayinta ya chanza, ba kamar da ta fita ba "Labiba? Wulakanci suka miki halan?" da k'yar ta girgiza kanta, tace "kai na ke dan ciwo" "ki shiga ki dan kwanta zai bari" kamar jira take ta fada daki, ta zube kan Gado kafin ta mik'e zumbur ta zauna.
K'wak'walwarta ta shiga tana sak'a da warwara.
Gidan Alhaji Ali Zaki Babban Gida ne, duk Anguwar ba Gidan da ya kai Gidanshi Girma da kyau.
Zaid na da k'anwa Sadiya? To ina Mamarsu? Ko ta rabu da Alhaji Ali ko kuma ta rasu.
Tabbas Hajia Shafa Matar Ubansu ce? Sauran muryoyin da take ji kuma na yaranta ne, ta san 'yan uba da matar uba, don ta na dasu, Gidansu gidan yawa ne, amma tsakani ga Allah ba sa irin zaman Gidan Alh Zaki.
To shi DanMakaho tunda Iliminshi meyasa ba zai nemi aiki ba? Meyasa yake shaye-shaye? Meyasa ya bata rayuwarshi haka?.
A baiyane tace "Ya Rabb! Ina son sani, nasan ba hurumina bane, amma ina son sani" Wayarta ne ya katse mata tunanin da takeyi.
Jawad ne, murmushi ya dan su6uce mata kafin ta dauka da Sallama.
"Labee nah, ina son ganinki kafin na koma Abuja" abunda ya fara ce mata kenan.
Murmushi ta saki mai laushi kamar tana gabanshi, kafin tace "Ina kwana? Ka tashi lafiya?".
Da sauri ya katseta "Wallahi ba Lafia ba, ina ta tunaninki, let me see you please".
Sausauta murya tayi tace "kayi hakuri, ni bansan me zance ma Baban Ameerah ba, amma nan gaba zan mishi maganarka, sai kazo Gida ko?".
Jim ya danyi kafin yace "Alright, Zamu biya ta Gidansu k'awarki kafin mu dau hanya, i will call you later, Ina Sonki Labiba".
Bata taba sanin ana shiga irin wannan yanayin ba, ba ta taba saurayi ba, da yawa nace mata suna Sonta, ba ta taba samun kalaman da sukayi tasiri a zuciyarta ba kamar na Jawad, Ina Sonki Labiba.
Maganar ta sake dawo mata katseta yayi "kinyi Shiru" tace "to me zan ce?" "kice kema kina So na" murmushi tayi tace "ka cika shagwaba, kai dan Auta ne?" yace "Ehmana, ashe ana ganewa, OK gotta go, zan kiraki in na isa Abuja".
"Allah ya tsare ya kaiku lafiya" ya amsa mata da Ameen.
Gab da zasu katse wayar.
Yace "Labiba, a hankali zan koya miki So na, I love you".
Kaste wayar sukayi, Ruf da ciki ta kwanta, wani irin yanayi ta shiga, wannan ne yanayin da ma'abota soyayya ke shiga? Wannan ne yanayin da ke ta6a zuciya. Pillow ta janyo ta rungume a k'irjinta tare da lumshe ido,
Mantawa tayi da duk wani abu, ta manta da komai, har DanMakaho, ba abunda zuciyarta ke aiyana mata sai JAWAD.
Shin Son so ne?.
Jawad da Yayyinsa sai da suka biya Gidan Kakarsu, kafin sukaje Gidan k'anin Babansu suka musu sallama. Jawad ya sake jadadda ma Aisha son da yake ma Labiba don ta kafa mishi Fada a wurin kawarta, yayi alk'awarin dawowa ba da dadewa ba, daga Gidansu Aisha ba su tsaya ko ina ba sai a Shagalinku Restaurant dake Zaria sukaci Abinci sukayi Sallah kafin suka sake daukan hanyar Abuja.
ABUJA
Da Marece suka iso Garin Abuja, Gidansu da ke Garki suka nufa, a tare suka fito daga Motar, Autarsu Mimi ta hangosu, da gudu ta kwasa ta na musu Oyoyo, AbdulMajeed ya dagata sama yana chafewa, Jawad shafa kanta yayi kawai ya shige ciki ya barsu, yarinya ce 'yar shekara uku, amma akwai surutu da shiga rai, cikin muryarta tace "Yaya Ina kukaje? Mancy tace kunje Katsina, ni meyasa bakuje dani ba?" Abdulhafiz yace "Sorry Mimi, da mu ka fita bacci kikeyi next time OK?" gyada kai kawai tayi.
A jikin AbdulMajeed suka k'arasa cikin gidan. A main Parlor duka zube, sai ga Jawad ya fito daga wani Daki, Mahaifiyarsu na biye dasu, bakinta har kunne saboda murmushi. "Sannunku da zuwa Boys" a tare suka gaisheta da "mun same ku lafiya Hajia? Ya gidan" da murmushi ta amsa musu da "Lafiya lau, ya mutanen KT?" suka amsa mata, tayin abinci ta musu.
AbdulHafiz ya mik'e yace "bari dai na k'arasa Gida Hajiya, Ummita ta min Waina" Hajia tace "to ba matsala ka gaidasu, muje na rakaka ma" ta k'arasa gunshi tana dan turashi kamar mai gudun kar yaga wani abu ko kuma kar ya tsaya yin wani abu, ranta ne ya dan sosu da taji yace "bari na Gaisheda Mancy" AbdulMajeed ma yace "Mimi sauka muje mu gaida Mancy" yarinya ta k'i sauka, haka ya dauketa a jikinshi, ya bi bayan yayanshi suka wuce Hajiyarsu da Jawad da je tsaye suka nufa hanyar dakin Mancy.
Abunda bata so kenan, abunda take gudu kenan, bata so yaranta suna ba Kishiyarta muhimmanci, suna nan tsaye sai ganin fitowarsu sukayi su duka har bakunansu na motsi da alamu wani abun ta basu, ranta ya baci, don me suka maida zuwa gaishe da kishiyarta Wajibi, itace Uwarsu ba Mancy ba, amma don me zasu dinga raba musu matsayi? Har suna cin abun hannunta?.
Muryan Mancy sukaji "Jawad, ashe an dawo, ya hanyan?" ba yabo ba fallasa yace "lafiya lau" tace 'Abdulhafiz, Allah ya huta gajia, a gaida Ummita, ke kuma zo nan ki bar Yaya Majeed yaje ya huta" Mimi ta mak'e kafada. Abdulhafiz ya musu sallama ya fita don tafiya Gidanshi, AbdulMajeed ya ba Mancy Mimi da k'yar shima ya wuce daki, Jawad ya ja Hajiyarshi suka shige daki, ita kuma Mancy ta ja hannun diyarta suka wuce daki.
Jawad ya zauna kusa da cinyar Mamanshi, ya na mai bata labarin Labiba, da irin son da yake mata, da kuma gaskia shi aurenta yake sonyi, Hajia Luba tayi mamaki matuk'a, ita ta san yaronta Miskili ne a wani fanni, ta san halinshi da kyale mutane, so da yawa kawayenta ke so su hadashi da 'yaransu amma fir yake nuna ba ya da raayi, tayi mamakin yanda ya furta da bakinshi kan cewa ya samu Mata.
Hajiya tace "to zan kira Antisco din na tambayi hallayar yarinyar" Jawad yace "to Hajia, bari ma na kira miki ita ku gaisa" Hajia tayi murmushi ganin zumudin Jawad.
KATSINA
Labiba ta lek'a dakin Yayanta inda matarshi ke kishingide tace "Aunty Asee barin je in siyo kati, duk yau bamuyi waya da su Mami ba" mik'ewa tayi "tace yauwa nima siyo min na dari" Labiba tace "to" fita tayi tana gyara zaman mayafinta.
Daidai da fitowarshi daga Gida, karaf suka hada idanuwa, dauke kai ya fara yi, ya fara tafiya, da sauri ta bi bayanshi tana fadin "DanMakaho Chanjina, zanyi amfani dasu" chak ya tsaya ya dan juyo, kafin yace "wai ba kince kin san Kudin be wurina ba? Ban dasu yanzu ban da dalilin samun su, na san inda kike, da na samu zan kawo miki har Gida"
Yana kai wa nan ya juya ya cigaba da tafiyarshi, dan jim tayi kafin tayi saurin binshi tana cewa "Dan Makaho, tsaya tsaya DonAllah" dan dakatawa yayi "ka rakani wurin siyan Kati, kaga dai shagon Oga kulle yake, dole sai chan Bencin Eskaley, kuma 'yan shayeshaye ke wurin, nikuma ban san zuwa, ka sansu ban so su ci mutunci na, ko su min magana bana son magana da su wallahi, ni tsoron su ma nakeji, donAllah ka rakani" ta k'arashe kamar me niyyan kuka.
Ya harzuk'a yace "wai ke don Uwarki me kika daukeni? Zan fa ci uwarki, zan babbala ki, ki fita harkana" fuskarta ya dan chanza amma murmushin be gushe da ga kan fuskarta ba tace "dazun da safe ka zagi Uwata so biyu, yanzu ka sake Zaginta, shin me ta maka? Ba ma fa ta sanka ba? Amma kake ta zaginta, don nace ka raka ni?".
jikinshi yayi dan sanyi, shafa kai yayi da hannu kafin yace "to ai duk cikin 'yan bencin Eskaley na fisu shaye-shayen don me zakice na rakaki, ba kya tunanin na miki wani mugun abun yanda kike shishige min haka?". Kallonshi tayi ta ga yanda yake kallonta da kannennen idonshi tace "I'm safe with you, na sani, in zaka rakani muje". Gaba tayi da sauri ya cin mata suna tafiya kafada-kafada ba mai ce ma wani komai har suka iso shagon Eskaley.
Tuni su Master da Haruna suka fara shewa "Shege Mankas, wo kai Mankas" Master yace "Yayar mu ina wuni, ya kwana biyu? A dan dari biyu inci abinci donAllah" Tero yace "amma wallahi kin hadu fa, kina da kyau, Labiba ta kawar da kanta kawai tana mai da na sanin zuwa shagon nan, ina ma yaro ta samu ta aikoshi nan, kamar tayi kuka, jin irin maganganun da suke mata.
"Zan ci uwarku ku ka sake mata magana, danuwarku kalarku ce? To danuwarku waninku ya sake cewa wani abu game da ita, zai kwana Asibiti billahilazi" Tero yace "Kai ji Mankas, yo kai ka shiga wurin sai ka hanamu shiga, indai ba kalarmu bace kaima ba kalarka bace, ai tunda muka ganta tare da kai, ai mun san 'yar hannu ce, Eskaley bata World, dan na san shi tazo saye, ba sai an tsaya mana wani kwane kwane ba, mun san kina Eh-Yaneh Malama".
Kafin Labiba ta gama gano inda Zancen Tero ya nufa, tuni DanMakaho ya kai Tero k'asa ya na kai mai nushi ko ta ina, ba wanda yayi yunk'urin rabasu don sun san halin Mankas, Labiba da tashin hankalin yayi yawa sai ta rasa me zatayi, tana waigawa inda zata ga jama'a don a samu mai rabasu, kowa harkan gabanshi yake , sai da Mankas ya ma Terro Ha6o kafin ya barshi, ya tashi ya nuna su da yatsa yace "duk daniskan da ya sake mata magana sai na ci uwarshi" fizge kudin hannun Labiba yayi yace "Eskaley bamu Kati" Tero ya mik'e a wahalce yace "Wallahi Mankas sai na rama, ko ba yau ba" Mankas yace "zo rama dan uwarka" ya nufoshi da gudu Tero ya bar gurin.
Be ko kalleta ba ya amshi Katin daga wurin Eskaley, gaba yayi ganin haka ya sa ta bishi a baya, sai da suka zo har k'ifar Gidajensu kafin ya mik'a mata katin, amsa tayi tace "Nagode, meyasa kayi Fada?" kallonta yayi ya kawar da kai, tace "Fada be kamace ka ba, be maka kyau ba, komai be maka kyau, ka bari donAllah " a fusace tace "Danuwarki bana ce ki bar shiga harkata ba" shiru tayi ta sadda kanta kasa, sai daga baya yayi laakari da zaginta da ya sakeyi.
Hannu ya sa ya murza idonshi na hagu, yace "kinga ke ke sa ina zaginki, kiyi hakuri, ki kyaleni, ki fita harkata" kallonshi take sosai kafin ta daura hannunta saitin k'irjinta tace "bansan menene ba, Zuciyana daidai nan, na min Zafi, bansan meyasa nake son saninka ba, ba son meyasa na damu da lamuranka ba, dagaske banson meyasa ba, amma dagaske Zuciyana na min Zafi, yana azazzala min, yana tafasa, zakayi mamakin don me ko? Nima mamakin nake, don me, so ka taimakeni, ka gaya min, ko zan samu sausauci".
Kafin yayi maganar Wayarta ta fara ruri, dubawa tayi taga Jawad ne, har ya katse bata dauka ba, ya sake kira DanMakaho yace "ki dau ka wayanki, zan sake ganinki, za kuma ki san ko Ni Waye, ban taba maganar nan da kowa ba, amma zanyi dake, ki shiga ciki, zamu sake Haduwa".
Da duk wata kalmar da ta fito bakinshi suka samu zama a Zuciyarta, samun kanta tayi da bun umurninshi, ba tare da ta ce mishi komai ba ta shige Gida tare da amsar Wayar Jawad.
"Haba Labee nah, ina kika aje waya ina ta kira?" dan guntun murmushi tayi "sorry na fita siyo Kati ne" "God, laifina ne, by the way, Hajiyata zaki gaisar" Dakinta ta fada, tace "Haba Jay, is too early" wani darian farinciki taji yayi, yace "Zamuyi maganan sunan da kika bani Anjima, amma ga Hajiar" kafin tace wani abu ya sadata da Hajiarshi.
Da Sallama ta amsa "Hello Assalam Alaikum" Labiba ta saki murmushi kamar tana gabanta "Ummanmu ina wuni?" dama a handsfree wayar take dadi ya kama Jawad, "Lafiya lau Labiba, ya kike ya su mamanku?" Labiba ta amsa mata, Umma ta tambayeta ya Makaranta, kafin ta mata addua sukayi Sallama.
"Ameen Ummanmu, Nagode Allah ya k'ara Girma ya kuma ja Kwana".
Labiba mai Farinjini tuni Umman Jawad taji ta na sonta sosai, tace "Jawad, Labiba wayayya ce, ba ruwanta" Jawad yace "sai ma kin ganta a fili" Umma ta kai mai dukan wasa tana cewa "wuce ka zubo abinci Ja'iri".
ALHAJI ABU SHAMSU
Asalinshi dan Garin Katsina ne, Alhaji Abu Shamsu na da k'ani daya rayyaye, sauran duk sun Rasu, Alhaji Abu Shamsu fitattacen dan Kasuwa ne mai zaman kanshi wanda ake damawa dashi a k'asa, Hajiya Lubabatu itace Uwargidanshi tun auren saurayi da budurwa, itama 'yar Katsinar ce, tun Abu Shamsu na 'yan buga-buganshi sukayi Aure har Allah ya mishi budi.
Alhaji Abu Shamsu da Hajiya Luba na da yara Uku, duk Maza, Abdulhafiz shine babba, sai AbdulMajeed sai auta a cikinsu Jawad.
Amaryar Alhaji Abu Shamsu wacce basu rufe Shekara 4 da aure ba Sunanta Hajia Maryam, diyarta daya Aminatu ana ce mata Mimi.
Wannan kenan
Ruwan Sama akeyi ba k'ak'autawa, tun k'arfe 10 dare, har wayewar Gari, da Asuba Baban Amira ya fito don yin Alwala don tafiya masallaci yin Sallahr Asuba, gabanshi ne ya fadi ganin bangon da ke tsakanin gidanshi da Alhaji Ali Zaki ya rushe, "Subhanallah, Inallillahi wa ina ilaihir rajiun" ya furta, da kyar ya daure ya shiga kewaye ya dan zagaya tare da yin alwala ya fita masallaci.
Bayan Sallahr Asuba suka hadu da Alhaji Ali Zaki, Baban Amira ya karasa wurinshi sukayi musabaha cikin mutuntawa.
Alhaji Ali yace "Mallam ya Iyali?" Baban Amira yace "Alhamdulilah, sai ga tsautsayi kuma" Alh Ali yace "Subhanallah, me ya auku?" be yi mamakin rashin sanin da yayi ba saboda bangon ta baya ne, ta inda Boysquaters yake, Baban Amira yace "jiya Ruwa yayi Gyara, Bangon da ke hade dade da Gidanka ne ya fadi".
Alhaji Ali yace "Subhanallah, IkonAllah, wallahi ban gani ba, ko don ban lek'a bayan ba, ta wurin DanMakaho ne kenan, InshaAllahu zaa gyara, bari gari ya waye" Baban Amira yayi Godia suka taho Gida tare, "ai Alhamdulilah tunda bangon be fado ma wani ba" "Ai don dare ne, amma wurin Iyalina suke shimfida don wurin akwai inuwa" Alhaji Ali yace "IkonAllah, Allah ya k'ara tsarewa"
A haka suka iso Gida, Baban Amira ya shigar dashi ta Gidanshi ya gani, suka sake jajantawa juna Alhaji Ali kuma ya tabbatar mishi da cewa da Safe zaiyi waya a siyo Bulo da k'asa da Siminti sai a gyara. Godia ya sakeyi kafin ya bi ta dan hanyar ya shige Gida.
Aunty Aseeyah haka ta tashi ta ga Ikon Allah, da mamaki, Baban Ameera ya mata bayani, ya kuma gaya mata yanda sukayi da Alhaji Ali, jinjina lamarin tayi kafin ta k'ara da Allah ya tsayar nan, dan tautaunawa sukayi, Baban Amiran ya yanke Shawaran su fita gabaki daya, sai ita Asiyar ta tafi Gidansu, in Yara sun tashi daga Makaranta sai a kaisu gidansu Aseeyar, Labiba
Sallah tayi ta shiga dakin Labiba da Yara, Labiba na fashin Sallah. Aunty Aseeya ta fara tada yaran don suyi shirin Makaranta yau Monday.
Labiba ta farka ta gaida Aunty Aseeyah, ta amsa tace "sai kika ga Bango ya fadi ko?" Wuf Labiba ta mik'e zaune tace " "Bango? Na ina? Inallillahi, ya akayi?" Aunty Aseeyah ta mata bayani, Labiba ta jajanta abun, Aunty Asiya tace "to yanzu dai k'ofar k'aura zamu yini, zuwa anjima InshaAllahu anyi gyaran. In kin tashi daga Makaranta ki wuce chan, yayanki yace zai gaya ma Mai Adaidaita sahun su Ameera da ya kaisu chan in sun tashi" Labiba tace "to shikenan Allah shi kyauta ya tsare".
Yara suka fara tafiya Makaranta, kafin Baban Amira ya fita Kasuwa, Aunty Aseeyah tace "karfe nawa kike da lectures?" Labiba tace "9 ne" "Ohh, na zata yanzu ne, bari na jiraki sai mu fita tare" Labiba tace "ki tafi kawai Aunty, in na gama sai na kulle Gidan ko?" sai da suka danyi mahawara kafin Aunty Aseeyah ta amince.
Itama 8 daidai ta shiga wanka, ta fito ta shirya cikin riga doguwar Riga Bak'a, Jan gyale medium ta sa ta yane kanta, ta kulle kofar Dakin, dama Aunty Asiya ta rufe Dakinta da Parlo da kitchen. K'ara saba jakkarta tayi ta yi hanyar fita, bata san dalilin juyawa ba, sai juyawa tayi ta hada Ido da k'ofar dakin da ke kallonta na Gidan Alhaji Zaki, kuma tana da tabbacin daya daga Ciki na DanMakaho ne,
Kila ko Sallahr Asuba beyi ba cewar zuciyarta, har tayi gaba, zuciyarta ta tunzurata da ta je ta kwankwasa mai, ya tashi yayi Sallah, samun kanta tayi da bin umurnin Zuciyarta, tsallake rusassun bulo din ta dinga yi har sai da ta dangana da Gidan Alh Ali Zaki, amsa kuwar zuciyarta take yi , duk da faduwan gaban da take jin zuciyarta nayi, bata fasa tafiya ba
har ta k'arasa gaban k'ofar dakin.
K'wank'wasawa tayi amma ba amsa, Zuciyarta na harbi da sauri sauri, gabanta na tsananta faduwa, ta lek'a ta window, kwance ta ganshi ruf da ciki.
Sake k'wankwasawa tayi, tare da murda handle din k'ofar.
"A bude take, k'ofar a bude take, ki shiga ki tadashi yayi Sallah" cewar Zuciyarta
Girgiza kai tayi tare da runste ido, amma zuciyarta na sake tunzurata.
Ki kiyaye mutuncinki Labiba, ki tsare mutuncinki, a kullum maganar Maminta kenan a duk lokacin da sukayi waya.
Ta san abunda take shirin yi is wrong, babu Macen arzik'in da zatayi hakan, ba Macen da zata shiga dakin Namiji Baligi ba Muharamminta ba, duk abunda ya faru da ita, ita ta jawa kanta, ita ta kai kanta, ko dakin Yayyinta Mahaifinta ya masu iyaka da shiga sashensu, balle wannan da ba zatayi shaidarshi a kan komai ba, bata san menene ke sa tana biyewa zuciyarta a 'yan kwanakin nan, ba halinta bane, amma bata san yanda zata tsayar da abun ba,
Bude k'ofar tayi tare da sa Kanta, tattaro Natsuwarta tayi kafin ta bubbuga kan Katifar da yake kwance tace "DAN MAKAHO"
Firgigit ya tashi, k'anannen idonshi ya dago ya kalleta da mamaki, kafin ya mik'e tsaye kyam yana binta da wani irin kallo, cikin Labiba ya bada k'ulululu, ta zabure zata ruga a guje, da sauri ya sha gabanta fuska daure yace "Ina kuma Zaki?".
Yayyyyyy people, Labiba ta kawo kanta fa.. Ba shi ya kirata ba, ita ta kawo kanta
Yau Mankas zai Angwance Rengyem
Me kuke tunanin zai faru?
Drop your thoughts here
Biko Vote Vote and Vote.
#1love
#DM
#SonSoFWA
#anatare
#nagode
Biebee Isa.
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Shidda (WACECE KE?)
Vote before reading please don ku kai karshe kun manta da wani zancen voting, just vote now. Thanks
"Saurin me kikeyi? Ina zaki ba wurina kika zo ba? To ina kuma Zaki? Ba so kike ki san ko ni waye ba, to yau ko zaki sanni, ba ke 'yar iska ba, kin san yanda ake zuwa dakin Namiji ko? Aiko zaki gaya musu, kwanta dan ubanki, yau sai na miki lagalaga" ya fada yana me yunk'urin tu6e riga don ya tsorata ta.
Runtse ido tayi cike da kidima, hawayenta su ka soma kwaranyowa, tana girgiza kai da k'yar ta lalubo kalmomin nan "ni Sallah na zo tadaka kayi, kuma wallahi ni ba 'yar iska bace".
Hanayenshi ya rungume a k'irjinshi, yana kallon yanda take rantsuwan ita ba 'yariska bace, iyakar gaskiyarta ya gano, daurewa yayi yace "yanzu in zagi uwarki kiji haushi, ni yaro ne da zakizo tadani yin Sallah? Bude ido tayi a tsorace, bata son ganinshi ba riga, amma da rigarshi.
Baki na rawa tace jiya fa naga sai daga garin Allah ya waye ka hada Salloli har Maghrib da Isha'i, shine nayi zaton ko bakayi ba, shine nace barin zo na tadaka ,ko zan samu lada, in ba haka ba, ba abunda zai kawo ni nan, saboda na damu da kai, ina so mu tsira tare ranar gobe k'iyama".
Kallonta sosai yake yana nazarinta, daga bisani yace " kin damu dani? Ni k'anin uwarki ne ko na ubanki?".
Kai ta girgiza tace "Aa, kai ba daya daga cikinsu bane, k'annen Mahaifana ba haka suke ba, kuma na lura Zagi kamar a jininka yake, na san na maka shishigi, ina kan maka shishigi a rayuwarka, amma ina rok'onka, wannan ya zama karo na k'arshe da zaka Zageni, kar ka k'ara zagina DanMakaho, babu mai ganin Mutuncinka a duk Unguwar nan, ni kam Ina ganin mutuncinka, inshort ni kadai ke ganin mutuncinka, so be kamata ace kana danno min Ashar ba" ta fada cike da sanyi, murmushi be kauce daga fuskarta ba.
DanMakaho ya kalleta sosai, yana mamaki, be taba sanin a Arewacin Nigeria akwai Mata masu Confidence irinta ba, be taba sanin akwai Matan da zasu iya expressing kansu kamarta ba a Katsina ba, yana mamakinta sosai.
Kallo ya bita dashi a hankali yace "WACECE KE"
Ta amsa mai da "Labiba Ahmad".
Ya Girgiza kai yace " Aa, wacece ke, kamar yanda kike son sanin Ni wanene haka nake so ki sanar dani ke wacece, sai na san ko ke wacece kafin zan iya sanar da ke ko ni waye".
Murmushi tayi tace "Makaranta zanje, nidai kaje kayi Sallahr Asuba".
Jim ya danyi, yace "Nayi" ta kalleshi da alamun rashin yarda, yace "ke ni fa bana k'arya, ba Bango ya fadi ba?nagani da Asuba". Murmushi ta sakar mai tace " tabbas kayi Sallah, to ni na tafi School".
Bai ce da ita komai ba, ta raba shi ta wuce, har ta kai bakin k'ofan ta dakata, zuciyarta na kitsa mata da ta tsaya suyi magana, opportunity ne ta samu, k'ila daga yau ba zata sake samun irin damar nan ba.
Dakata wa tayi ta juyo gareshi tace "lets talk Dan Makaho".
Ya dan waigo yana mamakin rashin tafiyarta yace " lectures din fa?".
Wuri ta samu daga gefe ta zauna, ta dago ta kalleshi, ta sakar mishi da murmushi tace "We are going to have our lectures here".
Bata jira yace komai ba ta fara magana;
Alhaji Ahmad Dakata
Alhaji Ahmad Dakata dan asalin k'asar Nijar ne, Maraya ne, baya da kowa, ya zo ya fara 'yan bugabuganshi a Garin Katsina, da yake yana kaifin basira da fasaha, nan ya fara shigeshige yana samun k'anannun kwangiloli.
Baiwa gareshi, yana da Ilimin Hak'a Rijiya da gina mugudanun ruwa, da ilimin Quantity surveyor amma be taba shiga Aji ba ma'ana beyi karatu ba, a shekaru da yawa a baya saboda kwarewarshi ya sa ake daukan shi gari gari don yin Aiki,
Da ya dan samu kudi yake zuwa Maradi gurin Tsohon da ya tashi a gidansa, a nan ne aka aura mishi Wata buzuwa Zaharau, marainiya ce itama, ya taho da ita Katsina.
Da Likafa ta cigaba mai, a ka dinga fita dashi garuruwa don yin kwangilar Tituna da Hak'on rijiyoyi, da janyo ruwa daga wani kauye zuwa babban Birni.
Babban kwangila ta sameshi inda zaiyi aikin kusan Shekara a Garin Edo Benin City da Zara'u ya tafi, lokacin tana da jaririn ciki, nan ya dan kama musu dan karamin Gida, ya hau aikinshi. Ganin aikinshi ba ha'inci, ya sa shi kafin ya gama wannan aikin ya samu wani aikin, haka zaman Edo ya kamashi, sai ya zama ya fara jin dadin Edo fiye da duk wani garin da yake zuwa, a nan ya kafa Iyalinshi.
Alhaji Ahmad Dakata Yana da Mata Biyu, Hajia Zahara'u, da Hajiya Jamila wacce ya aura bayan dawowanshi Edo kwatakwata, ko wacce da iya adaddin yaranta don Haihuwa suke MashaAllah.
Hajiya Zaharau itace UwarGida ta haifi yara Sha daya amma Uku ke da rai Mata 2 namiji daya , Yaya Muhammadu, Yaya Hajara, sai Auta Labiba daga kanta Mami kamar yanda suke ce ma Mahaifiyarsu bata sake haihuwa ba.
Hajiya Jamila itace Amaryar Alhaji Ahmad, Yaranta 7, 3Maza Yaya Aminu, Yaya Muntari, Mata Yaya Salisu, Yaya Fadime, Yaya Zaliha itace tsarar Yaya Hajara, sai Samira tsarar Labiba duk da ta girmi Labiba da 'yan watanni sai Auta Halisa.
Gidan Alhaji Ahmad kamar yawancin Gidaje ne Masu mata biyu maana mai Kishiyoyi, akwai kishi tsakaninsu, sa'anan akwai 'yanubancin.
Alhaji Ahmad yana tsayawa tsayin daka akan hade kawunan iyalanshi, amma abun da kamar wuya, a cikin kaso Dari, suna zaman lafiya kashi Tamannin, amma dai ana iya cewa na ciki na ciki, akwai ganin k'yashi da hassada musamman wanda 'yan wannan dakin ke ma wanchan.
Muhammad da Aminu suna da Shekaru 18 aka haifi Samira ba da dadewa ba aka haifi Labiba.
Sun taso kamar 'yan biyu, amma Labiba ta faye wayau, ganin tana da Wayau sosai, ga Shegen tambaya Muhammadu yayanta ya kwadaitu da son autar mamanshi ta shiga boko, don ba zai bari Babansu ya ma yarinya mai saurin daukan abu kamar Labiba abunda ya musu ba.
Alhaji Ahmad Dakata be damu da sanya yara a Makarantar Boko ba yana dai sanya su a Islamiya, in Namiji ne in ya kai shekara 10 yake fita dashi wurin aiki ya koya musu Aikinshi, in kuma Mace ce, da kin samu Miji zai maki aure, .
Daga Samira sai Labiba da Auta Halisa ne kawai basuyi aure ba, yawanci ba Hausawa suke aure ba, amma Maza kuwa daga Yaya Muhammad da Yaya Aminu wanda ke zaune cikin Gidan Alhaji Ahmad Dakata da matarshi.
%%%%%%
Da yaje wurin Baban da bukatar sanya kanannun yaran Makaranta, Baban fir yak'i, bayan Muhammadu ya kwantar da kai ya ma Baban bayani sosai kan Muhimmancin Karatu musamman ga 'ya Mace, sai suka tafka muhawara, daga k'arshe Baban ya amince. Aka sanye Labiba da Samira wani Private school.
Samira bata da passion din karatu, Labiba kuwa tana son k'aratu sosai, har suka gama Primary School. A lokacin ne Zamani ya fara dakushe tauraron Alhaji Ahmad Dakata, sai ya rage samun Kwangiloli, a nan ya Umurci yaranshi da su fita su samu Aikin hannun da zai ma kowannensu, ko wanne ya kama gabanshi, Muhammadu ne yayi Arewa a garin Katsina, yanemi izinin Babanshi da ya bashi hayar Gidan da yake Katsina zai zauna Baban yace yaje dai ya zauna in ya mutu a sa Gidan a Gado. hakan kuwa akayi amma hakan ya taba zuciyar yan uba. Muhammad ya tafi katsina da ya fara 'yan bugabuga, ko shekara baayi ba da zamanshi Katsina, ya samu mata ya aura a Katsina, har Allah ya sa mishi Albarka a kasuwancinshi ya bude dan madaidaicin Provision store a Kasuwa.
Samira ta tsani karatu, daga JSCE tayi ta zillewa bata son karatun, Mamanta ta biye mata, shi kuma Alhaji Dakata tunda be da damuwa kan Karatun boko, be matsa mata ba.
Amma Labiba ta dage da bada himma a karatunta ta shiga Senior Secondary School. Labiba ta ke kutsawa cikin 'Yayan kudun nan ta dau ilimi, bata fiye k'awaye Mata ba saboda gulma da fada, yawancin abokanta Maza ne kuma Kiristoci, don Musulmai basu fiye yawa ba, a nan ne ta koyi tambaya akan komai, ta iya mu'amala da kowa, tun tana primary ake fita Debate da ita, bata jin komai Magana gaban dubannin mutane, ba kuma ta kunyar tambaya.
Labiba tafi so ta sanya dogon Wando budadde, da rigar da ta wuce mazaunanta, tana da burin zaman Injiniya saboda duk abokanta Maza da tunanin zama Engineer suka tashi, duk tunanint irin na Maza ne amma ko so daya bata taba tunanin kwace hanyarta ba, tana da ilimin addini, bata wuce gona da iri ta fanin nan, ko hannu namiji ya bata sai ta galla mishi harara.
Wayon Labiba ya girmi shekarunta, shiyasa take samun laifi da Mama kamar yanda suke cema Mamansu Samira, Mama tana son lak'afa mata sharri, ita kuma in ta san batayi abu ba, ba zata taba amincewa ba, ko me zaa mata.
A lokacin da ta gama Secondary School Samari suka mata chaaa, ba sa gabanta, in sun zo zata fita ta sha hira dasu, amma kar take gaya musu ba wanda zata aura cikinsu, burinta dai tayi karatu ta zama Injiniya, in har suna sonta su jirata in ta zama Injiniya zata dawo, sai ko wannensu ya gwada bajintarshi, a hakan ta samu suke shafa mata lafia .
Result sun fito, duk sunyi kyau, ta kira yayanta Muhammad ta na kuka sosai kamar ranta zai fita, ta nuna mai tana son cigabawa da Makaranta amma tasan Babansu ba zai taba bari ba. Yayan ya kwantar mata da hankali ya shaida mata zaizo k'arshen Wata..
Bata gaya ma kowa ba burin son cigabawa da karatu, harta Maminta bata sani ba, sai da Yaya Muhammad yazo da Iyalanshi, Aunty Asiya da Ameera da Sabit, murna wurin su baa magana don sai sufi shekara 3 ba suzo Edo ba sai dai waya,
Aunty Asiya na san Mami don bata surukkuta da ita, tana son k'annen Mijinta, Labiban ma na sonta, da ta shiga gaida Mama, a dage ta amsa, gani take kamae Muhammad yafi yaranta kudi da arziki.
A lokacin da Muhammad ya shiga da bukatar son Labiba ta cigaba da karatu, ran Baban ya baci, yace shi aure zai musu karatun da tayi a baya Allah ya amfana. A nan ma wata Muhawarar suka sake tafkawa amma Baban yace shi sam Diyarshi ba zatayi Jami'ar Edo ba, ba zatayi karatun gaba da Secondary cikin Arna ba, muma shi tsakani ga Allah aure yake son musu, ya lura kan Labiba na rawa, wai rannan nan har tistitsiyeshi tayi da tambaya don me be sa sauran yaranshi Makaranta ba.
Muhammad dariya yayi, yace in zai yarda zai tafi da ita Katsina ya sanyata a Polytechnic, kuma ya mishi Alkawari da ta samu Miji, zai dawo da ita a mata Aure da k'yar Baban ya yarda, tara su yayi gabaki daya ya shaida musu hukuncin da ya yanke, nan Mama ta fara jin zafi, tace "Haba Alhaji, anya kuwa? Duk cikin 'ya'yanka, Maza da Mata, ba wanda ya taba karatu sai Labiba yanzu kuma kace zaka kaita wani gari tayi karatun Jami'ah? Ina guje maka dana sani Alhaji, Wallahi AbdulFatah ya nuna ya na sonta, gwara ka mata aure".
Labiba tace "Allah ya sauwak'e in auri mai shan taba, ki aura mishi Samira" Mami ta wurgeta da harara, Samira tace "Kinga Labiba Mama na ba tsaranki bane, wallahi ki daina maida mata magana in tayi" Alhaji Dakata yace "to nidai na amince Muhammad ka tafi da Labiba, amma idan Labiba ta kwaso abun kunya, ko tayi wani abun da zai kunyatani a idanun jama'a, to ba ruwana da kai da ita da Mahaifiyarku" Mami ta kalleshi cikin tashin hankali, Labiba kuwa ko a jikinta dom ta san ba zata taba basu kunya ba, dadi ya rufeta tace "Niko wallahi sai na baka Mamaki Abbah, zan zama abun alfaharinku, da Allah, ba zakayi dana sani ba, Mami karki damu, wallahi karatu kawai zani Katsina, sai na kula muku da jikokinku" wasu sukayi dariya wasu ko sukayi fuska.
Hakan kuwa akayi, Muhammad ya koma Katsina ya mata Appying HUK poly, don bin sharrudan uban, tunda Diploma Shekara 2ce, kuma akwai sharadin in ta samu Miji za tayi aure. Labiba na daga cikin wanda aka dauka da farko, saboda ko Jamb dinta Mark din yan jami'ah ne, ya gama mata preparation nan da wata biyu zata zo katsina fara lectures.
Abbansu ya kirata daki, ya mata nasiha sosai, ya bata kudi Naira dubu ashirin yace kuma InshaAllahu zai dinga turo mata ko da dubu uku ne duk wata, godia tayi sosai, ta rungume Abbanta.
Maminta ta ki rata daki tace "Na zauna a Katsina shekaru da yawa, na san yanda suke, yanda suke ma'amala da mutane ya sha bamban da yanda mukeyi a nan, baki taba barin Edo ba, Arewa zaki Labiba, dole ki koma halaiyar 'yan Arewa, kije kasuwa ki dinko atamfa da ankara, ki dinga shigan Hausawan usul, ba zasu miki uzurin ba a chan kika taso ba, zasu miki fassara in kikayi wani dabi'ar da ba tasu ba, ke ke son Karatu, dole ki zama irinsu ba zan so ki fito da wani penti duk kankantashi ba, kingane? Labiba ta gyada kai, Mahaifiyarta ta dade ta na mata nasiha kan kare Mutuncinta.
Tana son karatu, tana son fidda mahaifiyarta kunya, zatayi komai don ganin ta cimma burinta, ta shiga kasuwa ta siyo manyan gyaluluwa da atamfofi, ta dinka su. Lokacin zuwa Katsina Yaya Muhammad ya zo da kanshi don tafiya da ita, kowa na alhinin tafiyar Labiba, don tana da shiga rai, harta Samira da ba sa shiri tayi kukan rabuwa da ita, haka suka ma Edo Sallam suka taho Katsina ta dikko dakin Kara.
Gidan Yaya Muhammad dakuna biyu ne sai Parlo, da kitchen da toilet a waje, k'aramin Gida ne, Dakinta Aunty Asiya ta bar mata da Amira babban diyan Yaya Muhammad, ita kuma Aunty Asiya da Sabit suka koma dakin Yaya Muhammad.
Yaya Muhammad ya raka Labiba Registeration ba wai don ya san yanda ake ba, Sati guda ya kashe yana kaita Makaranta, ta hanyar bin School Bus, ya kuma koma ya daukota, ce mishi tayi ya bari hakan nan, ta gane hanya, zata iya zuwa ta dawo da kanta, a sati na biyu ne ta fara zuwa da kanta a lokacin har tayi k'awa Aisha Usman.
Wannan kenan.
Zaid ya gama jinta lokacin da ta gama bashi tak'aiceccen labarinta da murmushi dauke a fuskanta, kallon da yake binta da shi ne ya sa tace "ya akayi ne?" mur Zaid ya sha "are you stupid?" kallon mamaki ta mai tace "me ya faru?".
Hannu ya sa ya murza idonshi "wai ke lafiyar ki lau? Alk'awarin da kika daukar ma Maminki kenan? Don me zaki shigo dakina? Kare mutuncin kenan? Kinsanni ne? Yanzu in na danne ki, na miki abunda ba kya zato, me zakice mata? Kin san me kikayi risking? Farincikin ki, na Yayanki, na Mahaifiyarki wanda barazana ne ga aurenta, to kinyi risking kin shigo dakina, for what? Is it worth it?".
Labiba tayi shiru "nasan ban yi daidai ba, but kamar yanda nace ma, wallahi kamar ana controlling dina, bansan meyasa when it comes to you, nake yin abubuwa da yawa, i am just curious, Ya Rabb, amma kasan me? Wallahi banyi dana sanin shigowa dakinka ba, bansanka ba, bansan what you are capable of ba, amma na san ka san abunda kayi, shi za'ayi ma, na san kana da k'anwa Sadiya, na san in ka shiga gonan da ba taka ba, itama zaa shiga tata, nasan ba zaka min abunda ka san ba zaka ji dadi ba in an mata ba, na san fandarewarka a busa ma ciki hayak'i ne, kuma ina da tabbacin kai ba mazinaci bane".
Idon ya sake murzawa ya kwantar da murya, kamar zaiyi kuka, damuwa taji a muryarshi yace"Labibaah, you cant be so sure, ba a gane daniska a fuska, baki san abun da wani zai miki ba, ba kowa ke da irin zuciyar da kike tunani ba, wasu suna da abun ban mamaki, baki gane bak'in halinsu, nidai please kar ki kara shiga dakin kowanne namiji, ina tsoron abunda wani zai miki".
Ido ta lumshe ta bude ta sakar mai murmushi, tana me jin dadin muryar nan, tace "ka damu dani?" hannu ya sa a cikin gashi kafin ya daure yace "ke dallah, tashi ki tafi School" raurau tayi kamar me shirin kuka, nifa ba inda zani, already an fito 1st lecture, kawai na baka labarina sai kuma kace zaka koreni, ai ba haka mukayi ba?".
Tsaye yayi yana kallonta, itama kallonshi takeyi, sun dau mintuna fiye da uku suna kallon kallo, ko wannensu fa da abinda yake sak'awa, Wayarta ne ya katse su.
Aisha ce, dauka tayi "Hello Aisha? Ya kike, eh wallahi Ruwan Jiya ya mana gyara. Bangon Gidanmu ya fadi, shiyasa banzo ba, Ayyah Allah sarki, ya lectures? Ok to".
Ashe Aisha na tare da Abu Sadeeq, bashi wayar Aisha yayi suka gaisa ya mata jaje, ya shaida maya da yana missing Dimta, murmushi ta mishi kawai ta kashe wayar.
Har yanzu be fasa kallonta ba, wani kiran ya sake shigowa, kallon screen din wayar tayi taga Jay mamaki ta ba kanta da ta kasa daga wayar har wayar ta tsinke, don me zata k'i daukar wayar? ta tambayi kanta, kafin ta ba kanta amsa wayar ya sake ringing, sai ta daga ido a hankali ta kalli DanMakaho da sauri ta ajiye idonta k'asa tana wasa da hanayenta, wayar na kan Katifa tana ruri.
Wayar ta katse ta sake ruri, DanMakaho ya cire idonshi daga kanta, ya ga Jay a screen din, da kyar yace "Saurayinki na kira".
Da sauri ta daga kai ta kalleshi da kuma sauri ta sauke kanta kasa ta kawar da kai gefe, "Oh baki iya dauka a gabana?bari na fita" ta san in ya fita nan zai barta, ganinshi aiki ne tayi saurin cewa "aa, donAllah ka tsaya zan iya dauka".
Da sauri ta dauka "Hello Jay, zan kiraka, ina lectures ne" tayi saurin katse kiran, DanMakaho ya kalleta da mamaki.
Da murmushin mugunta yace "Lectures? Seriously? Wow, ashe kin iya k'arya" itama tayi mamakin k'aryan da ta sharara amma sai ta dake ta daure fuska tace "Ina Jinka, ka gaya min wanene kai?"
Wuri ya samu ya zauna daga gefe a sanyaye yace "Labarina bai da dadin ji" gyara zama tayi tace "zan iya saurarenka" yace "Labarina akwai tsawo" ta gyara zama tace "i have the whole day. (Ina da dukkan rana).
Murmushin takaici yayi
Yace "Sunana Zaid, Zaid Aliyu Zaki"
Da sauri tace "Meyasa ake ce maka DanMakaho? Meyasa ake kiranka da Mankas?"
A fusace yace "Zaki man shiru ko kuwa? in azarbabi zaki min tashi ki fita".
Hannu ta sa ta kama bakinta "Afuwan, nayi shiru".
A hankali ya soma Magana.
°°°°°°°
Wa zai iya mana hasashen Labarin Zaid?
Vote Vote Vote please.
#1love
#DM
#SonsoFWa
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Bakwai (ASALIN SU)
Alhaji Aliyu Umar Zaki tsohon dan Siyasa ne da yayi tashe a Da.
Yana da Shekaru 28 ya auri Shafa'atu 'yar mutanen Jos. Ya hadu da Shafa'atu ne lokacin da yaje Gaisuwar Mamar wani Abokinshi.
A GURGUJE
A lokacin, Mamar Shafa'atu na da Gidan Abinci, kafin Ali yaje Gidan Rasuwan ya fara zuwa Shagonsu Shafa'atu dake bakin hanya don cin Abinci.
Shafa'atu ce ta zo ta same shi, a natse ta gaishe shi ta tambayeshi abunda za'a kawo mishi, kallonta yayi yace "ki kawo min Shinkafa da Miya da Wake, sai kan Kifi" Shafa'atu ta dago ta kalleshi da mamaki tace "babu kan Kifi, saidai gangar Jiki da Bindi".
Ya dan tuburne fuska yace "ni kuma Kan Kifin nakeso" ta dan sa yatsar ta a baki tana nazari, su ba sa ba Customers kan kifi, amma wannan ya buk'aci da a bashi, tace "ka dan bani mintuna na soya maka" murmushi yayi don sosai 'yar budurwar ta burgeshi.
Bayan wasu 'yan mintuna ta dawo da abunda ya buk'ata, sosai ya ci Abincin nan, don ya sha tafiya, rabonshi da abinci tun kafin ya baro Katsina, sai ruwan da ya sha a Tasha, tambayar kudin Abincin yayi, tace mishi "kudinka naira dari da hamsin ne" cirowa yayi ya bata.
Ali sai ya manta da abunda ya kawo shi garin Jos, ya ja Shafa'atu da fira, haka ta biye mishi, da yaga Maghrib na neman yi baije yayi abunda ya kawo shi ba, ya ciro takardan da aka rubuta Adireshin Gidan Rasuwan, ya gwada mata "ko kin san Anguwar nan?" tace "eh ba nisa" nan ta sake mai kwatance.
Sallama sukayi tare da shaida mata zai dawo Gobe, murmushi suka sakar ma junansu, Ali ya tafi kwatancen da ta mishi da taimakon wani mai a kori kura ya gane Gidan. Sosai Abokinshi yaji dadin ganinshi, ya mishi godia sosai.
Washegari Ali ya koma Shagon su Shafa'atu, tun wurin k'arfe 10 na safe, dama da tunaninshi Shafa'atu ta kwana, taji dadin ganinshi yau, nan suka zauna suna ta fira, ba abunda ke tadata sai in Customers sunzo da ta basu abincinsu take dawo gurin Ali, Mamarta bata damu ba in dai kudi na shigo musu bata da matsala.
Maimakon kwana 1 da Ali yayi niyyan yi, sai gashi har kwana Uku be koma Katsina ba, duk da yayi Sallama da Abokinshi.
A cikin 'yan kwanakin nan Shak'uwa mai k'arfi ya shiga tsakanin Ali da Shafa'atu don Soyayya har ta shiga tsakaninsu kamar Almara.
Ranar da yace zai koma kar hankalin 'yan Gida ya tashi, Shafa'atu ta sha kuka sosai, a cewarta in ya tafi ba zai dawo ba, shi kuwa ya mata Alkawarin dawowa nan bada jimawa ba don zuciyarshi na wajenta a k'arshe ma ya tabbatar mata da cewa da labarin Aure zai dawo Mata.
Da wannan batu suka rabu Ali ya dawo Gida Katsina.
Ali ne Babba a Gidansu, yana da k'anne Maza da Mata.
Yayi karatun Arabi da Boko a Kano, be da wani aiki takamaime, amma yana da shige-shige da kutse-kutse, in yaje wuri sai ya tabbatar da an san shi a wajen kafin ya bar gurin, shiyasa abokan shi ke mai Inkiya da Ali Zaki ko suce Zaki kawai.
Tunda ya dawo Katsina yake ta tunanin Shafa'atu, hankalinshi dungurugum na gurinta, zuciyarshi na gaya mai ya koma Jos, nan ya bi zuciyarshi, ya sanar da Mahaifiyarshi zai koma Jos don ya samu Mata a chan, Mamarshi tayi mamaki sosai, amma sai tace "yanzu Ali duk Matan da ke garin nan da k'auyen garin nan basuyi maka ba sai ka dangana da Jos? Da dai ka bar maganar ta Jos ka zo ka bincika cikin Dangi, kasan Babanku dai" nan ya hau mata Magiyan donAllah ta goya mishi baya, zai samu amincewar Baban in har ta goya mishi baya, bayan ya dan sha wahala ya ci nasarar convicing dinta daga k'arshe.
Bayan 'yan kwanaki ya Koma Jos da Babanshi da k'anenshi sukaje ma Maman Shafa'atu da maganar Aure. Ta amince da hannu bibbiyu, Baban Shafaatu be da ta cewa don sai abun da Mamar tace, abu dai kamar wasa aka daura Auren Shafa'atu da Aliyu Zaki.
Bisa Alada aka rakota nan Gidansu Ali da ke Katsina inda a ka kaita dakin Ali.
Sosai Ali ke Son Shafa'atu, itama haka take sonshi, tana kyautata ma Mahaifiyanshi da k'anenshi, zaman lafiya sukeyi sosai.
Ali na dan fita yayi 'yan buga buganshi ya samu na cefane, ya kawo Gida a dafa kowa ya ci, zama suke na tsakani da Allah.
Bayan wasu yan Shekaru
Har Shafa'atu tayi shekara 3 a gidan bata taba ko da bari ba, wannan ya ja hankalin Dangin Mijinta gareta, abun ya soma damunta. Alin ne ke kwantar mata da hankali yana sake tunatar da ita kan Haihuwa ta Allah ce, yana ba wanda ya so a duk lokacin da ya so.
A lokacin ne Ali ya fara Shiga Siyasa, da yake yana da baki, ya iya magana sai hakan ke jawo mai Alheri daga Manyan 'yan siyasa, nan ya siya fili dan madaidaici ya fara gini, don su koma tare Matarsa duk don ya kwantar mata da hankali don ya lura rashin haihuwar nan, na damunta sosai.
Har wasu Shekarun suka k'ara shudewa, Shafa'atu bata yi ko da batan wata ba, abubuwa da yawa sun faru, Baban Ali ya rasu, duk nauyin Gidansu ya dawo kan Ali.
A Lokacin Ali ya shiga Siyasa tsundum don a yanzu ya wuce dan kwarako, a nan ta buk'aci da ya kaita Jos don a ganinta bata da Lafiya, ya kan ce mata "ta bar irin maganganun nan, don Haihuwa ta Allah ce, k'ila lokacin Haihuwar beyi ba" bata saurarenshi sai tayi ta kuka don danginshi sun sanga mata udo, habaibaici sukeyi mata, don Matan k'anenshi daga mai yara daya sai biyu, ita dai ya taimaka ya kaita ta samu magani".
Ba don ya so ba, ya kaita Jos da Motarshi, ya barota chan, nan Mamarta ta shiga dirka mata magungunan samun ciki.
Watanta daya a Jos Ali ya dawo daukarta don yayi kewar Matarshi sosai.
K'ulle mata magungunan akayi, har da na hayak'i, a ka kuma hadota da k'aninta Hudu dan shekara 4, Ali bai damu ba, don zai iya yin komai don Matarsa..
Shiru-Shiru bayan Watanni babu wata alama, hankalinta yayi mugun tashi da taga ba sarki sai Allah, sai ta bar yin maganin ta zubawa sarautar Allah ido.
BAYAN WASU 'YAN WATANNI
Alhaji Ali yayi suna, ya lula cikin siyasa tsundum, a lokacin shine Dan Majalissar dake wakiltar Katsina a Birnin tarayyah Abuja. Tunda Allah ya buda mishi yake kai danginshi aikin Hajj.Ya hada da Mahaifan Shafa'atu.
Wata rana, Alhaji Ali na hanyar zuwa Katsina daga Abuja shi da Drivernshi, suka tsaya a Masallacin Matafiya da ke Zaria. a gidan mai Masallacin yake. Bayan sun idar da Sallah ya hadu da wani Abokinshi Alhaji Usman Shehu da suka yi Karatu a Kano tare.
Da Murna suka rungume juna, bayan sunyi gaisuwa, Alhaji Ali yace "Haba Abokina ka boye" Alhaji Usman yayi dariya yace "Ina talaka zai ganka kana dan majalissa, ai ka zarce ni" Dariya sosai Alh Ali yayi yace "kai har yau baka bar iskanci ba" sukayi dariya baki daya. "Daga ina zuwa ina?" Alh Usman yace "daga zariya zamu koma Kano , chan nake zaune da wallahi iyalaina" Alhaji Ali yace "yaranka nawa?" "su 3 ne muje ku gaisa na san sun idar da sallah suna Mota" Tare suka je inda yayi parking Motar shi, ya bude yace ma matarshi ta fito su gaisa da abokinshi, fitowa tayi daga mota yaran suka fito su ma suka gaisheshi, daya bayan daya ya daukesu yana tambayan sunayensu yana mai sha'awarsu, sosai yake son yara, barin ma na k'annenshi, so yake ya dauki wasu daga cikin yaran k'annen nashi, amma da yake suna da yawa be son daukan dan wani ya bar na wani, kar ace ya nuna bambanci ko fifiko ga wani da kuma be so Shafa'atu taji an mata ba daidai ba don ita bata haihu ba, shiyasa be taba bijirowa da son rike 'ya'yan kanenshi ba.
"Kaifa yaranka nawa?" dan murmushi yayi yace "tukunna dai Allah bai kawo ba" Alhaji Usman sai yayi nadamar tambayarshi don kar yaga kamar yana son ci mai fuska ne, Alhaji Ali ya lura da yanayin da abokinshi ya shiga yace "kai daniska, kar ka damu, haihuwa ai ta Allah ce, idan da rabona zan samu D'an cikina ko ba dade ko ba jima zan samu, kawai ka tayani da Addu'a" InshaAllah Abokina inji Alh Usman.
Alhaji Usman ya kalli matarshi yace "wai ina Maryama ne?" dan murmushi tayi tace "ta na cikin masallacin mata muka barota bata idar ba" da mamaki Alhaji Usman yace "k'assarun?" tayi dariya tace "shi fa, ka santa da dadewa gun sallah" yace "danAllah je kirata muna kan hanya kar muyi marece" kafin waninsu ya sake magana hankalin Alhaji ya kai bakin Masallaci da wata halitta fara ta fito daga ciki tana gyara zaninta wanda shine matsayin mayafi.
Yauwa gata nan ta fito cewar matar, bude baki yayi yace "sallatu yi sauri ko?" da murmushi ta k'araso, ta kalli Alh Usman da ya shagala wurin kallonta tace "ina wuni" kasa amsa mata yayi sai da abokinshi ya lura dashi ya sa hannu ya zunguro shi kafin ya amsa mata. Oya a shiga mota, ya umurce su.
Alhaji Ali yace "Abokina wacece wannan?" yace "Maryama ce kanwata ko" dan shiru yayi kafin yace "indai har baku yi mata miji ba ina so, zan aureta".
#############
Dariya Alhaji Usman yayi "kai wallahi Ali ba ka rabuwa da shiririta" tamk'e fuska Alhaji Ali yayi yace " kai ni wallahi dagaske nake, in dai wallahi ba kuyi mata Miji ba, ina so".
Kallonshi Alhaji Usman yayi sosai yaga iyakar gaskiarshi kenan, yace "in har dagaske kake, to wallahi ka samu Maryam, kai dai kawai ka zo Gida, sai mu sake tautaunawa".
Hannunshi ya rike yace "Wallahi zanzo, kawai ka bani full address dinka." Alhaji Usman yace "ba damuwa".
Paper ya fallo a cikin Motarshi ya rubuta mishi Adireshin Gidanshi a Kano, shi ko Alhaji Ali hannu ya sa a Aljihu ya ma yara Alheri suna ta Godia, a nan ne kowanensu ya shiga Mota suka ma juna Oda kafin suka wuce.
Tunda ya zauna yake lumshe ido yana sake hasaso ma kanshi Maryama, haka Driver ya ta shatata gudu Alhaji Ali na ta begen Marayama a zuciyarshi.
Ya iso Katsina lafiya, sai da ya fara zuwa Gidansu ya gaida Mahaifiyarshi, kafin ya sauke mata tsarabar da yayi mata, ya ma Matasan Gidan Alheri kafin ya wuce Gidansi.
Shafa'atu ta tarbeshi kamar yanda ta saba, cikin shiga ta alfarma, suka rungume juna don sunyi kewan juna, sai da ta kaishi yayi wanka, kafin ta zubo mishi Abinci suka ci tare.
WasheGari, ya dauki hanyar Kano.
Alhaji Usman Aminin Alhaji Ali ne tun suna Makaranta, Maryama k'anwarshi ce, kasancewar Mahaifansu sun Rasu, Alhaji Usman ne ke rik'on Maryama tun bayan Rasuwar Mahaifiyarsu, yana kula da ita sosai don har makarantar Unguwanzomanci ya sakata(Midwifery).
Da Azahar suka karbi bak'uncin Alhaji Ali, Alhaji Usman yayi mamakin ganinshi, don beyi zaton zai zo nan kusa ba, lallai ya nuna mai dagaske yake. Abinci Matar A. Usman ta gabatar mai da shi, ya ci sannan ya gabatar mai da buk'atarshi,
Alhaji Usman yace "ba damuwa, shi dai ya bashi ita, kuma ya san yarinya ba zata bashi kunya ba, don Matsayin Uba yake a gunta" ya mik'e tare da cewa "bari ya turo mishi ita".
A daki ya isketa tana zaune kan wata kujera tana duba wani littafi, zama yayi a dan nesa da ita, tana ganinshi ta gyara zamanta tare da kulle littafin da ke hannunta.
"Maryama, ina so ki Saurareni, a Parlo, akwai abokina Alhaji Ali, wanda muka hadu jiya a Zariya a Masallaci! Na san kin ganeshi, to shine ya zo neman aurenki gurina, ni kuma na bashi ke, saboda na san kyawawan halaiyanshi, na san ba zaki watsa min k'asa a ido ba".
Shiru tayi batayi magana ba, yace "Maryama, ba dai bijiremin zakiyi ba ko?" da sauri ta girgiza kai tace "Yaya, kai ne Uwana kai ne Ubana duniya banda sama da kai, na san ba zaka zaba min abinda zai cutar dani ba, Nagode da zabinka gareni, Allah ya shige mana gaba". Da fara'a ya amsa da "Ameen, ni na san ba zaki bani kunya ba, ina Alfahari da ke Maryama, maza tashi, ki sanya Mayafi kije gareshi yana jiranki". Kanta a k'asa ta ciro Zaninta ta yafa ta fita waje.
Da Sallama ta shiga Parlorn kanta a k'asa, zama tayi a kan kujera daga farko, kafin ta dan rusuna ta gaisheshi, shi ko da kallon So da Kauna ya bita, ya amsa gaisuwarta cikin shaukin soyayya, a hankali a hankali ya ke tambayarta tana bashi amsa, sun dau lokaci suna zantawa, daga bisani yace "ta shiga ciki ta turo Yayanta".
Alh Ali ya gaya ma Alh Usman shifa ya samu Mata, ba bata lokaci yace "suje ya gabatar dashi wurin Kawun su".
Alhaji Ali be bar Kano ba sai da ya tabbatar an bashi Maryama.
Da farinciki ya koma Katsina, ya je ya sanar da Mahaifiyarshi yana neman Aure, ta sa mishi Albarka, Danginshi ko sunfi kowa Murna don su na son su ga gudan jininshi, k'ila Auren Rabo ne ke zuwa, nan fa aka fara shirin Biki.
Ba wanda ya sanar da Shafa'atu game da Auren.
Kudade ya biya masu dimbin yawa aka fara gina Mishi Katafaren Gida a wani Anguwa da kusan shi kadai ya fara Gini a wurin wato Tudun Matawalle,
Shafa'atu kuwa tausayinta yake sosai, yana shakkar gaya mata maganar Aurenshi, be so taji kamar zai kara aure ne saboda haihuwa, baya so ta ga kamar ya gaji da ita ne, baya son bata mata sam, karshe dai ya biya mata kudin Umra ta tafi Makka, kuma ya siya mata 190, a lokacin da wuya kaga Mace na tuk'a mota, amma ita ya mallaka mata Motar kanta, Bayan tafiyarta Makka ya samu ya fara shirin bikinshi a tsanake.
Ana saura Sati 3 Biki
Shafa'atu taje Gidan Surikanta da Akushi dauke da Tuwo Miyan Kubewa busassa dominos uwar Mijinta, tunda ta shiga ta ji gabanta ya fadi, da Sallama ta shiga k'urya, zaune k'annen Alhaji Ali suke su 9 suna diba kaya, da alamu lefe ne, akwati 2 manya, da fara'arta ta gaishesu, da Hajiyarsu, Hajiya ta amsa tana dan jin nauyinta, basu san zata zo ba.
Shafa'atu ta kallesu tace "to, lefe ne ake kallo? Karime wa aka kawo wa lefe bamu sani ba?" Karime ta dan kawar da kai gefe tana yak'e ta rasa me zata ce mata, Shafa'atu ta sa hannu tana daga kayayyakin tana gani tana yabawa "wai Kayan waye? Wa aka kawo mawa?" Ladidi tace "wa dai zaa kai ma wa ko?"
Karime ta zungurota da hannu, da yake Ladidi ta fi ki jinin Shafa'atu tace "har sai yaushe zaa boye mata? Ke Shafa'atu lefen Yayanmu ne, za'a kai Kano Gobe in Allah ya kaimu" Shafa'atu da dan yak'e a fuskarta tace "Ahh, Yaya Shehu Aure zai sake? Waiyo Allah shi kaimu, ashe muna da biki".
Ladidi tace "Iyeeee, wato Shehu kadai ne yayanmu? To babban Yayanmu nake nufi" Hajia tace "Ladidi kiyi shiru" Shafa'atu da bata fahimci komai ba tace "bangane ba, Babban yayanku? Wanne kenan?" Ladidi tace "baki gane ba? To Yaya Ali nake nufi" tsalle Shafa'atu tayi ta dire tace "Ba ku da hankali, kun ga dai bana san irin wasan nan" Asabe tace "wake miki wasa? Tunda kin kasa haihuwa, zaa auro me haihuwa".
Karamin bori Shafa'atu ta hau, ta hau facali da kayan cikin Akwatunan, kafin ta wawuri Akushin Miya ta bude Miyan ta juye a jikin kayayakin, nan suka yo kanta, ta dire ta yi kan Hajiyarsu. "munafuka, ke kikace yayi aure ko?" aiko su Ladidi sukayo kanta, suka hau dukanta wai ta zagar musu mahaifya da k'yar Hajia ta hanasu dukanta, har tace "zata tsine musu in suka sake bugunta"
Ina bakin shafa bai mutu ba, ta dinga surfa musu Zagi, tana laantarsu, tana cewa itace Ajalinsu, shegu k'azamai, talakawan banza, duk kyautata muku da nakeyi? Ni zakuyi wa butulci, biye nake da ku kamar na muku sujadda shine zaku saka min da wannan? Aiko zaku sha mamaki, ayi auren mu gani, ta fita fuuu, ko zaninta bata dauka ba, ta ci karo da Ali a hanya ko kallonshi bata yi ba ta fada motarta ta danna a guje, Ali ya ji gabanshi ya fadi. Ya shiga Gidan da sauri
Hajia ce tace "ta ga kayan lefen ne, ka bita ka lallasheta" kallon kayan yayi yace "meye wannan kamar miya?" Ladidi ta chafe tace "Wai baka ga ruwan wulakanci da tayi a gidan nan ba, har ta na zagin Hajia, kanta farau kishiya?" ran Ali ya baci yace "Ta zageki Hajia?" Hajia ta girgiza kai tace "aa ba fa ta zageni ba ladidi" tana wurgar Ladidin da harara, kai dai ka je ka san me za ka ce mata kasan mata ba sa son Kishiya.
Tashi yayi jiki a sabule ya nufi Gida, ya jima a bakin gate kafin ya shiga, zaune ya ganta har ta bashi tsoro don ta ci kuka har ta gaji, k'arasawa yayi a tsorace, be san ta inda zai fara ba, yana karasowa ta ci kwalarshi, tana jijigashi tana dukanshi ko ta ina, ni zaka yaudara Ali don kayi kudi, ni da nake zaune da kai tun baka da komai, ni zaka ci amanata Ali? Kasa magana yayi, ya kasa motsi, ta cigaba da dukanshi kafin ta fashe da wani irin kuka, rungumeta yayi tsam tun tana motsi har tayi lamo a jikinshi tana mayar da ajiyar zuciya, sai da ta daina motsi kafin ya soma magana.
"Shafa'atu na san ban kyauta miki ba da na boye miki maganar Auren nan, amma ki san cewa ina sonki fiye da zatonki, duk wata Macen da zan aura a bayanki take, kar ki manta irin Son da nake maki, ki dauka wannan Auren k'addara ce, ki bani goyon baya nayi auren nan, wallahi ba zan taba wulakantaki ba, wallahi Shafata kin fi karfin wulakanci a wurina, Shafa'atu ba ayi macen da take karshena da zata wulakantaki ba, in naga ba zata girmamin ke ba, wallahi ina iya rabuwa da ita, ki taimaka min" abun mamaki hawaye ta gani kwance a idanuwanshi tana son Mijinta sosai, kalamanshi sun darsu a zuciyarta, bata da wani zabi illa ta danne zuciyarta.
Bayan ta gama kumburinta ta sauko, hakan ya bashi kwarin guiwa ya cigaba da sabgarshi, amma walwalarta sam bata dawo ba, da tsanar danginshi da ya darsu a ranta, danne zuciyarta kawai take.
***.
Ba wai don tsoronta yake ba kawai don a zauna lafiya ya sakar mata ragamar bikin gaba ki daya, sai yadda tace ake yi, harta dakin da Amarya zata zauna ita ta za bar mata, ya so ta ba Amarya daki biyu, amma tace nata ne kawara daya ne na amarya, be damu ba don ya san da ya gama gininshi zasu koma sabon Gida kowa da Dakinshi da Parlornshi, shiyasa be ce mata komai ba.
A ka zo jere, da katifa da kujera da kayan kitchen duk aka jera a daki daya kasancewar dakin k'ato ne.
Tun daga jere dangin Maryama suka gano matsala daga gun Abokiyar zaman Maryama, amma basu ce komai ba gudun sa mata tsoro da fargaban kishiya, kuma sun lura Dangin Ali na son Abun.
"Kinsan Shafa'atu, ki bi a sannu, kinsan Mijinki yana daidai gwargwado gurin kyautata miki, to in kika faye zak'ewa kika kureshi, zai bar bi takanki, ke dai kawai ki bi ta bayan fage ki kori amaryar nan, ki mata zagon k'asa, kishin mimik'e zakiyi, kar ki yarda a gane ba kya sonta kin gane?" ta jinjina kai tana kwasan karatu gurin Aminiyarta Hajiya Er Rabi,
Nan ta kwantar da kai ta bi har Gidansu Hajiar Ali ta basu hakuri, kan haukan da tayi sharrin shaidan ne, Hajia tace ba komai ya wuce dama an san mata da kishi, balle ita da aka boye mawa.
Jumu'ah na zuwa aka daura Auren Alhaji Ali Zaki da Maryama Adamu a garin Kano ta dabo, an kawo Amarya dakinta.
Uwar Dakinta Matar Yayanta ta dade tana jadadda mata nasihan da yayanta ya mata, kafin suka bar Katsina, Maryama ta sha kuka kamar idanuwanta zasu fadi.
Murmushi ya mata yace "nagode Allah ya miki Albarka Maryama"
Shafa'atu kamar ta fashe amma sai ta hau yak'e tace "bari ta dauko musu Abinci".
Da sauri ta mik'e ta fice hanyar kitchen, Ali ya dinga bin Maryama da kallo ita ko kunya ma yake bata.
Tare sukaci abinci kafin suka gama, Shafa'atu tace bari ta shiga ciki ta musu sai da safe.
Shiga daki tayi ta dinga gwala kanta a bango, tana kukan bakinciki, anya hanyar nan mai bullewa ce? Anya zata cigaba da nuna komai lafiya lau ne alhalin ba haka bane? Gaskia da sake.
Su ko maaurata tuni suka shige dakinsu.
A GURGUJE
Bayan wasu 'yan Satittika
Zaman lafiya suke kadaran kadahan, Maryama dama sanyi gareta, biye take da Shafaatu, sun raba kwana bibbiyu, ko wacce burinta ta zama tauraruwa wurin Mijinta, sosai Shafa'atu ta danne zuciyarta don su zauna lafiya da Maryam, barin ma da ta ga bata da matsala.
****
Ta gane tana da ciki, saboda sauyin da ta ji jikinta nayi, bata ce ma kowa komai ba ta cigaba da harkokinta.
Sosai Mijinta ke nuna mata k'auna, a gaban Shafa'atu ya kan nuna kawaici, amma in suka kebe kamar ya hadiyeta.
Sannu a tashi alamun Ciki ya fara bayyana a jikin Maryam, tara miyau a baki, da amai in taji tashin zuciya, daga Shafa'atun har Alin ba su dago cikin bane don ba sani sukayi ba.
Ita dai Maryam ta san ciki ne da ita, in ta fara kwarara Amai kamar ta amayo hanjin cikinta.
Wata Rana Hajia Er Rabi, k'awar Hajia Shafa'atu tazo gidan, Maryam ta fito don gaisheta, kallo daya ta mata ta san cewa tana da shigar ciki, da ta shiga ciki, tace "kawata, ashe mutuniyar har ta dau ciki" Shafa'atu ta mata kallon rashin fahimta. Er Rabi tace "kar ki ce baki san tana da ciki ba?" ta dan zamo daga kujera tace "kar ki ce man ciki gareta, wallahi ban sani ba, shima Alin bai sani ba" Er Rabi tace "lallai kam, ban yi mamaki ba don ko bari baki ta ba yi ba, ba ki san yanda ake gane ciki ba, to Kishiyarki Ciki ne da ita".
Dam gabanta ya fadi "yanzu Maryam ciki ne da ita? Bata gaya mani ba?" Er Rabi tace "ke ya ma fi haka, kinga yanzu da kika sani, sai mu 6arar da cikin ba tare da kowa ya sani ba, balle mu shiga zargi" ido ta zaro tace "a barar da shi fa kika ce?" ta girgiza kai da sauri, tana da kishi sosai amma rashin imaninta bai kai nan ba, ta san Mijinta ya dade yana neman haihuwa, kuma amfanin Maryaman kenan ta haihu, bata ji dadin cewa ba ita zata haifa ma Ali 'ya'ya masu kama dashi ba, amma ba za ta taba halaka dan Cikin Maryama ba.
Ta kalli k'awarta tace "ba wannan maganar, duk da bana so ta haihu, ba abunda zan mata gaskia, Cikin Mijina ne, farincikinshi nake so, don gaskia be rageni da komai ba" baki sake take kallon Shafa'atu tace "lallai Shafa'atu, kina tafka wauta, wayace miki Dan Miji Da ne? Kinga zaki tafka kuskure, a duk ranar da Maryama ta haihu musamman Namiji ti kashin ki ya bushe, ba mai kara kallonki da daraja, ke ce Uwargida, amma gida zai koma nata. Dangin Mijinki kuwa dama sun tsaneki da ta haihu sunanki abar tausayi".
Hajiya Shafa'atu tace "nidai gaskia a bar maganar zubda cikin" Er Rabi tace "an bari, amma zakiyi kuka da kanki, ni kinga tafiyata" ta mik'e ranta a bace "haba kawata ina zaki?" tace "yo zaman me zanyi? Ana gwada maki annabi kina runtse ido".
Hajiya Er Rabi ta fita, Shafa'atu ta bi bayanta tana magiyar ta tsaya amma tak'i.
Da daddare wurin cin Abinci, suna zaune su uku kamar yanda suka saba, Shafa'atu tace "Alhaji, Albishir ne dani me zan samu" ya tsaya da cin tuwo ya kalleta yace "Shafata duk abunda kike so zan baki, gaya min" Maryama ta zuba mata ido, tana tunanin abunda Shafa'atu ke tafe dashi, murmushi tayi tace "Maryama Ciki gareta, akwai danka a Mahaifarta" mamakin ya sa Maryama kallonta, shi ko Gogan wani Yammm yaji a kunnenshi, ba zai iya fasalta abunda yakeji a tattare da shi ba a cikin wannan lokacin, duk suka zuba ido don ganin halin da zai shiga.
Mamaki ya basu duka, da k'yar yayi murmushi yace "Allah Sarki, to Allah ya raba lafiya" ya mik'e tare da cewa bari ya wanko hannunshi, Shafa'atu ta bishi da ido, a matsayinshi na wanda baa taba mishi irin wannan Albishir din ba, tayi mamakin yanda ya karbi zancen, to ko baya son Haihuwan ne shiyasa bai taba mata k'orafi kan rashin Haihuwar ta ba, tunaninka da yawa suka darsu a zuciyarta.
Ita ko Maryam ba ta ji dadin yanda Mijinta ya karbi Zancan ba, ko da ace ya saba haihuwa aka ce tana da ciki ya kamata a nuna farincikinshi, ita da take da burin haihuwa duk shekara don ta cika mishi Gida da 'ya'ya, amma ba komai, ta tashi ta kwashi kwanonin ta kai kitchen ta dauraye kafin ta koma daki.
Alh Ali Zaki na shiga dakinshi ya fada kan Kujera tare da fashewa da wani irin kuka, kuka ne mai dauke da ma'anoni da dama, shi ne Zai haihu? Shi Allah ya azurta matarshi da ciki? Shekara fiye da bakwai da aure? Yau shi matarshi ke da ciki? Farincikinshi ba mai fassaruwa bane. Alwala yayi ya jera nafilfili don nuna farinciki ga Allah SWT.
Watanni sun shude
Tun Safe ta ke jin nak'uda, amma sai ta daure, ganin ciwon na k'aruwa yana sake yawa ya sa ta fitowa ta kwankwasa dakin Shafa'atu tana cije baki.
"Yaya Cikina kamar zai balle, mutuwa zanyi" da sauri Shafa'atu ta kamota tace "gashi Alhajin be nan, ko zaki sake daurewa har ya dawo?". Maryam ta riko hannunta tace "ki taimakeni, wallahi mutuwa zanyi, nidai ki kira Unguwanzoma".
Kamar daga sama sukaji Sallamarsu Ladidi da Asabe, Shafa'atu ta manta rashin jituwarsu ta karasa gunsu tace "yauwa ina jin Maryama nak'uda takeyi" Ladidi tace "to da me zaki mata? Ke zaki karbi haihuwar ki danna kan yaro ya koma?" ran Shafaatu ya baci "ai da banson a haihun da tun lokacin da take da ciki na barar da shi" Ladidi tace "ai ko ba ki fada ba na san bakincikin cikin nan kikeyi, to ta Allah ba taki ba, sai an haifeshi munci moriyar Magajin Yaya Ali da yardan Allah". Asabe tace "kinga muje mu taimaka mata, tana cikin mawuyacin hali".
A daddafe suka kaita dakinta, haihuwar ce dama, bayan yan mintuna ta santalo danta jazur dashi, bayan Ladidi ta gyara Da da Uwan ta aiki Asabe zuwa chan GidanGandunsu taje ta fadi haihuwar.
Shafa'atu na nan tsaye gefe tana jin kukan jariri tsoro ya mamayeta, kasa shiga dakin tayi sai ta wuce dakinta ta fashe da wani kukan da bata san ko na meye ba, fargaba ne fal ranta.
Kamar daga Sama sai ga Alhaji Ali da Kanenshi, yana Gidansu Asabe ta je ta fado haihuwar, Shafa'atu na jin muryan Mijinta ta fito waje,
"Alhaji sannu da dawowa" be ko kalleta ba ya wuce ya barta tsaye, gabanta ya fadi, me kenan? Ta tambayi zuciyarta, bayanshi ta bi da ido, kafin ta rufa mai baya.
Yana shiga ya amsa Jaririn daga hannun Ladidi ya rungumeshi tsam a k'irjinshi, tsigar jikinshi suka mimike, wani yanayin da be taba shiga irinshi ba ya shiga, hawaye suka soma kwaranyowa daga idanuwanshi, hamdala yake yi yana godewa Allah, addua ya ma yaronshi, kafin ya karasa gun Maryama yana ta jero mata sannu yana sanya mata Albarka.
Duk a kan Idon Shafa'atu, hawayen bakinciki ta fara ta fita daga dakin da sauri.
Labarin Haihuwa ya Zagaye Gari, sai zuwa barka akeyi, ana taya Alhaji Ali murna, kullum Gidan ceike yake da Danginshi da yan barka.
Shafa'atu ta zama kamar bakuwa, don da ta zo wuri ake mata habaici, ita Maryama bata da ta cewa sai yanda dangin Miji sukayi da ita don ma suna sonta, kowa so yake ya burgeta, daga masu dafa mata abinci, sai masu ina zaa saka da ita.
Alhaji Usman da Iyalanshi da Dangin Maryama sunzo barka, da yawa sun tsaya Suna.
An san Alhaji Ali da kyauta, amma tunda akayi haihuwar nan, ya Soma kyauta kamar baya son kudadenshi, kyautata ma Makwaftanshi yake.
Ranar Suna aka radawa yaro Suna ZAID ALI ZAKI.
Zaid ya sha kyaututuka daga manyan 'yan siyasa.
Anyi babban liyafan Sunan da baa taba yin irinshi ba a Anguwar.
Wani sabon kulawa Alh Ali ke ba Zaid da Mahaifiyarshi, dan kawaicin da yake ma Shafa'atu a da yanzu babu shi, gabanta yake nuna tsantsar soyayarshi ga danshi, in yana tare da Zaid ba ya da lokacin kowa da komai, Abujan da yake yawan zuwa yanzu ya bari, in ko Zaid na kuka da kanshi yake zaro Nono daga Jikin Maryama ya ba Zaid ko gaban waye.
Ba ya kawaici ko shariya wai don Zaid ne dan fari, mutane na mai uzuri ganin be taba haihuwa ba.
Shafa'atu ta fara jin ba daidai ba, Alhaji Ali ya rage damuwa da ita, kacokam hankalinshi ya koma kan Zaid, tun tana daurewa har ta tare shi wata rana da maganar a parlo.
Yana rike da Zaid a k'irjinshi "Alhaji, magana nake so muyi" ya dan kallota amma be fasa ma Zaid wasa ba, hakan da yayi ya nuna mata yana sauraronta tace "Alhaji, wai kai baka da lokacin kowa da komai sai na Zaid? Kai ko dan kawaicin Dan fari bakayi? Alhaji, ba ka gudun bakin mutane? Komai Zaid komai Zaid?" baki sake yake kallonta yace "Shafa'atu wace irin magana ce wannan kike? To in banyi lokacin Zaid ba lokacin wa zanyi? Don mutane kar suce banda kunya, ko kuma kar suce banda kawaici sai na k'i nuna ma yarona So, Kauna da kulawa? To mutane sun dade ba suyi magana ba, aj dade baa zageni ba, banda kamar Zaid wallahi, kuma zan iya rabuwa da kowa ta kan Zaid ko da Mahaifiyarshi ce balle ke".
A tsorace ta kalleshi, mamakinshi take, tace "Alhaji Ni? Sai ka rabu dani ta kan Zaid? Me na mishi?" yace "Yo sai na rabu da ke nana Shafa'atu, haka kurum kinzo min da wani soki burutsu, ni da Dana? Duk mai son ganin bacin raina to ya kawo kushe ga Zaid, kika cire Mahaifiyata, Wallahi na fi sonshi fiye da kowa a Duniyar Yanzu, to ki bi a hankali".
Hankalinta ya tashi sosai, sum sum ta tashi ta shige dakinta tana fashewa da kuka Sosai.
Haka ta kwanta zuciyarta na k'una, tunaninka kalakala, washegari ta ma Gidan Hajia Er Rabi diran Mikiya,
Matsalarta ta karanto mata.
Er Rabi tayi dariya, "ba ke dadi Miji ba? Ba yanda banyi dake kan a barar da cikin nan ba ki ka ki, gashi ya zame miki ciwon Ido, mai makon ace kinyi Kishi da Kishiyarki, kin kare da kishi da Dan Mijinki, ai wallahi kuka yanzu kika far yinshi, ba zaki san tsakanin Mahaifa da Gudan jininsu ba tunda ba haihuwa kika taba yi ba".
Bata rai tayi tace "abun 'yar gori ce?" tace "aa, ina dai gaya miki ne, kashin ki zai k'ara bushewa a duk lokacin da Maryama ta sake haihuwa, in ko ta cika mishi Gida da yara to wallahi zaki zama Almajira a cikin gidan aurenki, kar ki yarda ta sake haihuwa, ki tashi tsaye Shafa'atu, ki kwatar ma kanki 'yanci".
Jin saukar maganganun Er Rabi take kamar Darma mai zafi, dole ta tashi tsaye, da ta bisu ta arziki ba abunda ya kare ta dashi, zata bisu ta tsiya, duk sai ta ci uwarsu, nan Hajia Er Rabi tayi ta zugata tana gaya mata abubuwan da ya kamata tayi.
Tun daga ranar Hajia Shafa'atu ta chanza ma Maryama, a gaban Mijinsu kamar ta goya su ita da Zaid, amma a bayan idonshi Kashi ya fisu daraja.
Zaid na da Wata 5 Maryama ta sake daukan Ciki, hankalin Shafa'atu ya tashi ya a ka k'are da Zaid balle an yi mishi kanwa, kila Alhaji Ali ba zai samu lokacin yi mata magana ba.
Samun Er Rabi tayi, ta gaya mata ai Maryama na da ciki, wani magani ta bata tace ta zuba mata a cikin Abinci.
Ta ko ci saa cikin ya zube, bayan Maryama ta sha bak'ar wahala. Tun daga lokacin nan, ciki ya bar Zama a jikin Maryama, da tayi da cikin ya zube, kusan bari 9 tayi a shekara 4.
A cikin Shekarun nan Hudu da suka shude, Alhaji Ali yayi wani irin kudi mai ban tsoro, ya koma Sabon Gidanshi da ke Tudun Matawalle, Gidan Sama ne, a Sama akwai Dakuna 3 daya na Maryama daya na Alhaji Ali, daya na Shafa'atu, sai a k'asa Akwai K'aton Parlo da dakuna biyu, sai k'aton Kitchen din da duk mai sanwa take shiga.
Sai kuma ya na da masu dafa Abinci a baya inda Boysquaters suke, Gidajen da ke kusa dashi kullum suna da kwanon Abinci a Gidanshi, tunda ya dawo Anguwar kullum yana da 'yan maula masu jiranshi a k'ofar Gida, bai taba gajia ko kosawa da su ba, yana musu ihsani.
Kullum hannunshi rik'e da na Zaid, duk inda ya sa k'afa to Zaid na biye dashi, mutane kuwa sai su dinga wasa Zaid da kirari ko don ya musu Alheri, Zaid na da matuk'ar wayau, baya da k'uiwa, duk yan Unguwa na sanshi, yana da son mutane kamar Mahaifinshi, yana da shekara 4 yayi wani irin wayau.
Shafa'atu tsanar ta ga Maryama da yaronya karuwa yake.ta yi ruwa tayi tsaki dai gun hanata sake haihuwa, duniya ba abunda ta k'i jini irin Zaid, abunda ke bak'anta ranta, sai ta dage tayi abinci domin Mijinta, sai Alh Ali ya kira Zaid wai tare zasuci, ko kuma ya kwashe mishi namomin yace "maza cinye Zaiduna" abun nan na ci mata tuwo a kwarya, ji take ta na iya harbeshu da bindiga.
In ko ranar Girkin Maryama ne sai tayi sanadin bata mata sanwa, ko ta k'ara mata gishiri, ko yaji, don dai suyi fada da Alhaji, amma bata taba jin kansu ba.
Yaran Yayan Maryama na zuwa mata hutu sosai, in har Alhaji Ali baya nan, to Abinci a cikin Samira take ba Maryama wai da ita da bak'inta, ta kuma kulle kitchen din CIkin Gida don kar Maryama ta dafa komai a cewarta ai ana abincin gandu, zai zama albazaranci ayi ta dafuwa kalakala. Maryam bata taba kaima Mijinsu k'orafi ba.
Da ta hadu da Zaid to sai fa ta hada shi da wani Rankwashi, ko tsunguli, in ko yana bacci har razor ta ke sawa ta fasa mishi jiki dan k'eta.
Ran da ya ba kowa mamaki, randa suke zaune gabaki daya su hudu suna cin Abinci, Zaid na kan cinyan Babanshi yana sa mishi doya a baki kamar an tsunguleshi yace "Yauwa Baba, kaga kullum mama sai ta tsunguleni ta min haka akai" ya Rankwashi baban a kanshi a hankali yace "amma ni mai zafi takeyi min, me na mata baba?".
Mama kamar yanda yake ce ma Shafa'atu, kowa ya san ita kadai ce Mama don Maryama Minyama ya ke ce mata.
Alhaji Ali ya kalli Shafa'atu, Maryama kuwa kau da kanta tayi, yace "Shafa'atu? Ke kin Rankwashi shi da tsungulinshi? A kan mene?" Shafa'atu da tayi zaune kamar gawa ta kasa motsi, mamaki ta hanata motsawa.
Sai da ya daka mata tsawa kafin ta fara borin kunya, haba Alhaji, kai ka san yanda na dauki Zaidu kamar dan cikina, don me yaro dan shekara hudu zai ma magana ka hau kai? In tsunguleshi inji me? Daga jin maganar nan an san kitsa mai a kayi, kuma ban yafe ba, Zaid ni na san ba kayi wayon hada maganganun nan ba, na san gaya maka akayi, ba wani abu, don ban taba haihuwa ba shine ake ta min abubuwa a gidan nan".
Jikin Alhaji Ali yayi sanyi, shi ya san Yaronshi beyi wayon yin karya ba, amma kuma maganganun da Shafa'atu tayi sun shiga ranshi. Sai dai ya share ya cigaba da cin Abincinshi, amma ya kudurta a ranshi duk wanda ya matsa ma Zaid shima zai matsa mishi.
Wannan kenan
Vote and Comment line by line pls
#1love
#DM
#anatare
#SonSoFWA
#nagode..
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Takwas (WANENE SHI?)
Bibilicious freaking fans, Vote before reading please, thank you.
Ya kalli Labiba yace "A zaman Gidan Kishiyoyi, ko a auro Amarya tazo ta takura ma Uwargida, ko kuma Uwargida ta takura ma Amarya, a gidanmu ba haka bane, Matar Ubana , ni ta takura mawa, da yaron Gidan take kishi, ni ta sanya wa Ido".
Idan har ta bude idonta ta ganni, ji takeyi kamar ta kasheni.
Ba zan manta ba wata rana Baba ya tafi Lagos wani Taro, a lokacin ina da shekara 5, na shiga Makarantar Boko, ranar da Baba zai dawo Mama ke Kitchen, ta dade tana hada Abincicika kala 2 masu dadi, da farko tuwo miya taushe, sai na biyu Shinkafa da ya ji kaza ko ta ina, kuma don rowa sai tayi don cikinshi kadai.
Kamshin Abincin ya cika Gidan gabaki daya, har na kasa hakuri na bita har kitchen nace "Mama zanci Abinci" kora na tayi har da dan biyoni da gudu.
Fadawa nayi daki kan Minyama, ta kasance ta na jina da Mama a kitchen, rik'oni tayi tace "Zaid, ba fa yunwa kakeji ba" nace "Ni Abincin Mama nake son ci, kuma ta hanani, bakomai, ai da Baba ya dawo tare zamuci"
Minyama ta kalleni sosai kafin ta rik'o hannayena duka tace "Zaid, kana ja min matsala, DonAllah in Babanka ya dawo kar kaje wurin ci Abincinshi, zan maka irinshi ranar Girkina kaji DanAlbarka?" sai da Minyama ta dade tana lallashina kafin na amince ba zanje gun Babana ba in yana cin Abinci.
Da Baba ya dawo, kamar ko da yaushe da tsarabata ya shigo, ya dauke ni ya tillani sama ya chafe "Farincikina" kamar yanda ya saba ce min, ni ko na mak'alk'aleshi ina dariya, yace "Kayi Kewana?" nace "Sosai ma".
Ina kallon Mama ta galla min harara, da yake ita ce ta biyoshi daki, tuni na shiga taitayina na dan zame na bar musu dakin.
Nan suka sake gaisawa, sai da yayi wanka kafin suka fito Parlo tare, ta gabatar mishi da shagalin da tayi dominshi, ta zuzzuba mishi a Plate.
Baba ya lumshe ido yace "wai kin san yanda nayi kewan Girkinki Shafata?" Murmushi tayi tace "ai gaka ga shi, sai kaci ka k'oshi, nayi dominka kai kadai" Baba yayi murmushi yace "nagode k'warai".
Da Bismillah ya fara cin Abinci, Shafa'atu ta zuba mishi ido cike da so da kauna, tana ganin yanda ya lumshe ido ta san cewa yaji dadin Abincin ta fadada murmushinta.
Loman da Baba zai k'ara ya dan dakata, bude baki yayi yace "Ina Zaid?"
Da sauri tace "yana gurin Minyamanshi ko, yi sauri ka ci kar ya huce Alhaji"
Kamar zai mik'e tsaye yace "Kira min shi yazo muci Abinci".
Ranta a bace tace "be fa jin yunwa, na bashi, bari na k'ara mai wani, akwai saura a kitchen kai dai ci"
Fuska ya dan bata yace "kinsan dai bana iya cin Abinci ni kadai in ba da shi ba" ya mike tsaye ya nufo dakin Minyama.
Ina daga chan rakube ina zaune, ban saba zama haka ba in Babana na Gida, a ko da yaushe ina jikinshi in dai aka ce yana Gida.
Yana shigowa ya ganni zaune daga gefe, yace "yana ganka a nan? Bayan ga Abincinmu chan"
Na dan kalli Minyama ta min ido nace "na k'oshi" be tsaya wata-wata ba ya cicciboni.
Minyama ta dan ci gabanshu tace "Alhaji, da dai ka barshi, ba ya jin yunwa" Baba ya harareta yace "sai ki gaya min yaushe na fara cin Abinci a KT ba tare da Zaid ba, kai Matan Gidan nan ku fita idona fa" ya fita tare dani a jikinshi ya koma Parlo inda Mama ke zaune ranta a Jagule.
"Shafata kinga ga Zaid din, ashe Maryama ce ta hanashi fitowa, zauna kaji Farincikina mu ci Abinci" ko kallon mu Mama ba ta yi ba, illa hucin da take yi, shi ko Baba be lura ba, ni kuma abunki da kwadayyaye, na zauna da na sa a cokali daya a baki sai naji kamar ban taba cin Abinci mai dadin wannan ba, sai kuma na ga kamar Abincin ya min kadan.
"Baba In cinye?" da sauri Baba yace "Cinye tas Zaiduna".
A hasale Mama tace "Haba Alhaji, ba fa ka ci komai ba".
"Zaid ya nuna ya na so, a kawo min na Gandu in ci" ran Mama yayi kololuwa gun baci. Sanwan da ta dauki Awowi ta na yi, wanda tayi domin shi be ci ba, sai dan loma dayan da yayi, fuuu ta tashi ta bar wurin kamar zata tashi sama.
Shi ko Baba hankalinshi ya maido guna cewa yake "Yi Sauri ka cinye Zaiduna" ni ko na zage na cinye Shagalin nan tas.
Dan Makaho ya tsagaita yana dariyan takaici kafin ya dan sha mur tare da murza kanannen Idonshi. Labiba kuwa zuba mishi ido tayi tana sauraronshi tana son taji k'arshen Labarin, ta k'agu taji amsoshin tambayoyinta.
Ya cigaba da cewa "Shi fa Baba har ga Allah bai san Mama ta ji haushi ba, in Baba na tare da ni kowa yake mantawa, ba ya karantar damuwa a fuskan Mutum, haka ya rik'o hannuna muka shiga Dakin Mama, inda muka ganta zaune, da alama Kuka ta sha, ko bi ta kanta Baba beyi b ya fada toilet din Dakin, ya barni zaune tare da Mama.
"Ni ko na matsa gunta "Mama me ya faru kike kuka? Baba ya miki fada ne? Zance ya daina miki fada" tureni tayi daga jikinta, na sake tashi na nufota "Mama wai" kafin na gama maganar da zanyi, Zuciya ta ci Mama ta riko min kunne ta fitar dani daga dakinta ta wurgar dani a Parlo."
"Da yatsa ta nuna ni "Zaid ka fita idona, ina tausayinka duk ranar da na kama ka, dan Ubanka Abincin kai na dafa mawa? Da zaka zauna ka cinye? Maye ne kai da duk k'oshin da kayi in na dafa ma Babanka abinci sai kaci, kai baka k'oshi ne? Wallahi duk randa na sake dafa mai Abinci kaci sai na ci ubanka, shege Maye, na tsaneka Zaid, da na sani da na barar da cikinka tun kafin a haifeka" ta juya fuu tayi hanyar dakinta."
"Kalamanta kenan a gareni, ba zasu taba gushewa a k'walwata ba, ban manta su ba tsawon Shekarun nan, kinsan me nace mata?" da sauri Labiba ta gyada kai alamun "aa" ya dan murmusa yace "yarinta ma dai to, ce mata nayi nima ban sonta kuma zan sa Babana ya koreta".
"A hasale ta juyo, ta san zan aika, ji take kamar ta shak'eni na mutu, a gefenta ta wawuro wani Cokali mai yatsu, fork, daga inda take ta saito ni ta wurgo min cokalin nan cikin bacin rai tare da cewa "in ka fasa ka ci Ubanka, shegen yaro ka zame min alak'aik'ai, wallahi sai nayi maganinka".
"Cokalin nan be tsaya ko ina ba sai a cikin Idona na hagu, wani gigitacen k'ara na saki wanda ya tsorata Mama,
"Allah Sarki Babana ashe duk abunda ke faruwa yana kallonmu, a guje ya k'araso gareni inda na ke zube a k'asa, ya tariyo ni jikinshi yana jijjigani, ni ko ihu nake ina ambaton idona".
"Minyama ta fito a rude, ita kanta Mama ta mugun rudewa, Baba ya ciccibeni, yayi waje dani, Mama a rude ta bi bayanshi, Minyama ma binmu tayi a baya".
Baba be tsaya jiran Direba ba ya figi mukuli ya fada mota, itama Mama da Minyama Mota daya suka shiga, hankali a tashe suka bi bayanmu da mu kayi General Hospital.
"A Emergency a ka karbeni, a lokacin Jini ya taru a cikin Idon, likitoci suka karbeni. Suka hau aiki, Alhamdulilahi ba wani ciwo a can cikin Idon, dama kin san ido baya son bak'on abu nan dai suka diga min magani a idon, suka rufe da bandage bayan Minti Talatin zasu dawo na bude in na bude ba wani abu InshaAllahu".
"Bayani suka ma Baba da su Mama kan cewa ba wani abu, jini ya taru sakamakon wani abu da ya shiga, amma sun diga magani, a hankali zai washe" Godia Baba ya musu tare da zama, be kalli Minyama ba da ke kuka ballantana Mama da ranta ke cike da Fargaba, tsoro, dana sani, suna nan zaune har Minti 30 suka dawo don bude idon, a lokacin nima na farka daga dan baccin da na samu bayan kukan da na sha".
"Warware Bandage din Likita yayi tare da cewa Zaid Bude idonka, sai labari ya sha bambam, da nayi yunkurin budewa sai nayi sauri na rufe, na yi hakan fiye a k'irga amma na kasa budewa, ba wai don idon ya manne ba, sai don tsoro, tsoro ya hanani budewa, Likita yayi, yayi amma na k'i budewa, fita Likita yayi don ya kira su Baba, kila in Baban ya min magana zan bude, nan su Baba suka shigo har da Minyama da Mama."
"Rungumeni Baba yayi, kamar jira nake na fashe da kuka idona na mai radadi fiye da zato, Baba shima kukan yakeyi, rik'e dani sosai ya ke magana a hankali "Zaid ka bude idonka, ka ganni Baba ne, Girgiza kai kawai nakeyi, hawaye na zuba daga idona, Baba ba zan iya ba".
"Baba yana kuka Sosai yace Zaid kar kace ba zaka iya ba, ba ka so mu cigaba da zuwa Filin Polo kallon Wasan Polo? Zaid in baka bude idonka ba, ta ya zaka ga na sa riga a bai-bai? Wa zai ce Baba ka zubar da miya a rigarka? Wa zaice baba-- Baba be k'arasa ba ya fashe da wani irin Kuka, duk mai rauni sai da ya tayasu".
"Jarumina, ka bude idonka kaji? A hankalina na fara bude idon ko second 3 beyi ba nayi sauri na rufe don ji nake kamar ana barbada min barkono a ciki".
Hannu Baba ya daura a kai kamar dan yaro yace
"ta nakasa min shi, shikenan yaro na ya zama Makaho".
Likitoci dai sukayi bakin k'okarinsu don ganin na bude Ido amma na kasa, sun sake bincika idon sun tabbatar ba komai a ciki, tsoro ne kawai, sai suka yanke shawaran bari na na dan kwana biyu, k'ila kafin lokacin tsoron ya fita a raina.
"Ba inda Baba yaje a Asibiti yake kwana, ba ya cin Abinci, dangi sai tururuwan zuwa gani na suke duk da an hanasu shiga, Mama duk ta fita hayyacinta, tana tsoron abunda zai faru, har yanzu Baba bai ce mata komai ba, duk da itama da ita ake zaman Asibitin, rashin mata magana na damunta matuk'a".
Har a kwana biyun ba wani Cigaba, haka suka sallamoni, sukace da Baba a hankali zan bude Idon, Baba ya ji haushi sosai har ya kusa dukan daya daga cikin likitocin, be koma dani Gida ba, sai wucewa dani Abuja da yayi, ba wanda ya san inda muka nufa, hankalin kowa tashe yake.
Lokacin Duniya a kwance take, ya mana processing zuwa k'asar Italy don zuwa Asibiti, ba a jima ba mu ka tafi Italy daga ni sai Baba, ba wanda ya san inda muke a Gida, Minyama Kuka, Mama Kuka.
Satinmu 2 a k'asar Italy, wanda suma kamar a kasar mu Najeriya, ba su ga komai a idon ba, illa tsoron da suka gani a tattare da ni, pediatric vision therapist shine ya duk'ufa wurin ganin na bude idon ta hanyar exercising idon kuma Alhamdulilah tsoron ya ragu sosai don yanzu ina dan bude Idon hagun amma ba completely ba. sai ya zama ina kanne idon kamar wanda ke tsoron wani abu zai shiga.
Ba yanda zasuyi dani don hakan ya zame mini Habit (Dabi'a) sallamarmu sukayi muka dawo Nigeria Abuja muka dan huta. Daga kallon Baba ka san cewa bai ji dadin sakamakon da muka samu a K'asar italy ba to amma ya zaiyi? hakan yafi da ace danshi ya makance gabaki daya, da ya kalleni sai yace "Zaiduna kayi hakuri, an nakasa min kai" ni sai dai na kalleshi.
Haka muka dawo Katsina, kowa yayi farincikin ganinmu, barinma Minyama da ta kasa kawaicin sai da ta rungumeni tana hawaye, Mama kuwa tsoro ya hanata magana har yau bata san Matsayinta ba, nima ban saki jiki a gabanta ba. Baba ya rik'eni yayi dakinshi dani, mukulli ya a ma dakin, don bai yarda da kowa ba, toilet ya fada, don yin wank, su Minyama kuwa suka shiga kitchen tareda Mama don yin abincin bak'i. Minyama ta lura da dari-dari da Mama keyi, ita fa har yau bata san me ya faru da ni ba.
Dangi sai zuwa mana Barka suke, a lokacin da Baba ya fito daga wanka, ina nan zaune yace muje na ma wanka, tubeni yayi ya min wanka kafin ya shafa min mai, ina da kaya a dakinshi, ya ciro min riga da wando tazarce irin nashi, anko mukayi, sai da yayi rubutu a 'yar takarda kafin ya rik'o hanuna ya jani zuwa babban Parlo inda yake cike Mak'il da 'yanuwa da abokan arziki, harta hajiyansu Baba su Mama Asabe sun rik'ota sun kawota.
Sai da Baba ya je gabanta ya gaisheta kafin ya fara amsa gaisuwan mutane, har yanzu yana rik'e da hanuna idona daya bude daya a kanne.
Baba Sani yace "wai yaya Ali me ya samu Zaid a ido, daga asibiti ba mu kara ganinku ba?" Baba yayi murmushi mai zafi yace "Zaidu ka gaya musu meya sameka a ido ranar nan da na dawo daga lagos" idanuwa suka dawo gurina na dan sa hanuna na murza idon, na kalli Minyama da ta yi kasak'e don son jin me ya samu idon, nayi imani kuma gaban mama na ta faduwa ganin yanda tayi firifiri.
"ba Mama bace ta wurgo min cokali me yatsu a ido don wai naci abincin da ta ma Baba"
Daki ya kaure da Inallilahi wa ina ilaihir rajiun, Minyama ta bude baki cike da mamaki, ko da wasa Mama bata taba gaya mata abunda ya faru ba.
Ita ko Mama kamar kasa ta bude ta shige ciki, ta rasa mai zata yi, dangi sun samu abunda suke so, nan kowa ya samu abunda yake fada.
Gyara murya Baba yayi, yace "In Zaid yace Mama to kuwa kun san Shafa'atu yake nufi, auren Soyayya mukayi da Shafa'atu, na aureta ne saboda ta na So na, nima ina Sonta, amma meye amfanin Zamanmu in har bata son abunda na haifa?".
Wasu sukace ba amfani.
Baba yace "ba na tauye mata hak'k'inta, ina biya mata buk'atunta, laifina, na ba Zaid abincin da ta girka min, wai Abinci, ta kan abinci ta nakasa min shi.
Da kunne na na ji Shafa'atu na ce ma Zaid ta tsaneshi, da kunnena wallahi naji tace da ta san hbaka zai zame mata da ta markade cikinshi tun kafin ya zama gudan jini, wai yaro kamar Zaid ake ma wadannan maganganun".
Magana daya ce, ba zan iya zama da wacce bata son Gudan jini na ba, ba zan iya zama da wanda ta tsani farincikina ba, kin nakasa mishi ido nan gaba ban san me zaki nakasa mai ba, Shafa'atu na tsaneki kamar yanda kika tsani Zaid, a yanzu kuwa na Sakeki SAKI UKU ga takardarki.
Jikin kowa sai da yayi sanyi, Minyama na can rakube sai da gabanta ya fadi, ita ko Mama jikinta sai rawa, idanuwanta na ta ambaliyar hawaye, kana iya karanta tashin hankali daga fuskarta, bakinta har wani rawa yakeyi hak'oranta na bugun junansu da karfi, durkusawa tayi a gabanshi, tace "Alhaji, donAllah kayi hakuri, kar ka sakeni, kayi hakuri, wallahi ina son Zaid, dama sharrin shaidan ne ya sa nayi abinda nayi, kuma wallahi tsautsayi ne, ba ma da niyya nayi ba, amma tun lokacin Alhaji banda wani kwanciyar hankali, donAllah ka yarda dani, muje ciki na maka bayani, nidai kawai ka janye, ba zan iya rayuwa ba kai ba".
Mik'ewa Baba yayi yace "kin taba ganin inda aka janye Saki 3? To in baki sani ba, ba aure tsakaninmu, Aurenki ya gama a kaina.
Baba ya ja Hannuna ya yi ciki dani ya bar kowa zaune
Banda Mama da ta ke burgima a k'asa tana wasu surutai mai kama da Sambatu.
Ni Ali zaka wulakanta? Ni ke tare da kai tun kafin ka san kanka, yau ta kan yaronka ka wulakantani gaban matsiyatan k'anenka, ni Ali? Bayan son da nuna maka? Sai chan ta fashe da wani irin kuka mai karfi, da yawa sun tausaya mata, haka suka fara fita daya bayan daya.
Da k'yar Minyama da ke daskare wuri guda ta taso don lallasanta, amma cikin zafin nama Mama ta tureta wanda hakan yayi sanadin faduwar Minyama akan wani table dake kusa da kujera, Minyama ta sak'i yar k'ara, su Asabe da suka rage a parlon suka yo kanta.
Dukan Shafa'atu suka fara yi don har ga Allah ba sa sonta, Ladidi ce tayi dakin Yaya Ali don sanar dashi Minyama na fitar da jini ta goshi.
A sittin muka fito, Baba ya kamata ya rik'e don zuwa Asibiti, bayan ya kira Securities dinshi suka fitar mai da Shafa'atu daga gidan a wulakance.
A Asibiti a ka ma Minyama Dressing muka dawo Gida, ta birkice ma Baba tana kuka tace "Alhaji, ba ka kyauta ba, irin sakin da Manzo baya so, shi kayi haba Alhaji" ranshi bace "wai ke wace iri ce? Ba kiji abubuwan da tayi ta kuma ce game da Zaid ba? Kurma ce ke? Kika san tun yaushe take mai mugunta yanzu da Asirinta ya tonu ba sai ki gode ma Allah ba da a nan abun ya tsaya, Allah kadai ya san abunda take mishi, kwanaki da yake cewa tana rankwashinshi yar barikin ba karyatawa tayi ba harda kukan munafunci? Nifa da ba ke kika haifeshi ba da na ce ba kya sanshi.
Tace Alhaji wallahi Kishi ne, duk macen da zaka aura dole tayi kishi da Zaid ba laifinta bane yace Shiyasa ba zan sake Auren ba, ke kadai kin isheni, ta dan sausauto da murya tace "ko in ta sake aure zaka Maidota?" ke Hajia Maryama ki fita Idona, ke Hajia Maryama ki kiyayyeni, zan mugun bata maki rai, a duk randa kika sake min maganar Shafa'atu, na dai saketa ko? Na kuma wuce gurin, ke kuma in da Dan Cikinki zakiyi Kishi zaki sha Mamaki, zan manta da Usmanu abokina ne na miki Rashin Mutunci, haka Baba yake yi in har yana fada a kaina idonshi rufewa yakeyi, Son da Baba ke min ya wuce tunaninki Labiba, ba zaki iya gane adadin Son da yake min ba.
Minyama jikinta yayi sanyi, kar fa garin neman gira ta rasa ido, garin gyara auren wata ta bata nata, tun daga ranar bata sake maganar Mama ba,
Mu dai ba mu san ya take ba, ko ta zo Gidan ba ma sani don Already Baba ya sa matakan tsaro na kar ta sake zuwan mai Gida. Haka muka shafe Mama a rayuwanmu.
YanUnguwa, Abokanan wasana, Manya da yara suka koma ce min DANMAKAHO, don da Ido daya nake amfani, abun har ya zame min jiki, don ko da yaushe ido daya a bude daya a rufe, Baba ba ya son sunan amma ya ya iya? Niko yarinta a lokacin har kidi a ke min ana min Wakan Zaidu DanMakaho me rijiyan naira niko inta rawa na ba tare da wata damuwa ba.
Duk wanda ya kirani da DANMAKAHO amsawa nake bai dameni ba, da yawa kan ce ina da wautar 'yan fari, amma fa sosai nake da farinjini, in dai na fito, to ko ina na shiga zakiji ana DanMakaho, DanMakaho manya da yara.
Wai kin san abun mamaki?bayan sakin Mama da shekara 2 Minyama ta samu ciki har ta haifeshi bayan wata 9?
Labiba ta jinjina kai tace "ikonAllah your Sister?" kai Zaid ya daga mata yace "lokacin aka haifi Halimattu Saadiya taci sunan Hajiyar Baba, tsakanina da ita Shekaru 11, kuma wani ikonAllah daga nan Minyama bata sake ko da batan wata ba.
Darling kamar yanda Baba ke ce ma Sadiya, ta fini haske, ta na kuma da shiga rai kinsan yanda mu ke sonta kuwa?" Sosai ta samu Soyayyar mu 3, ni Baba, Minyama sai kuma dangi, wallahi ta tashi cikin So da K'aunar kowa.
Ta yi Girma da Wayau, ta shiga Makaranta lokacin nikuma nagama na shiga Secondary.
Zaid ya dan murza idonshi tare da yin wani guntun murmushin da ya burge Labiba da alama wani abu ya tuna, ta nutsu tana kallonshi ta ji muryarshi ya cigaba da cewa "wai kinsan In Baba yace mata Darling ita mai tsiwa sai tace ba Darling ba Dalo, nikuma sai ince Dalo wai kuma sai tayi ta kuka" Labiba ta murmusa itama, murmushin ya sake yace
"Ni dan Boko wai sai na ke cema Minyama Momcy"Dalo bata iya cewa Momcy ba amma da tsamin bakinta sai da ta sa mata sunan da har gobe ya bita, kinsan me take ce mata?" da sauri Labiba ta girgiza kanta tace "Momso?" dariya ta ba Zaid wanda yana yi yana murzan idonshi kuma hakoranshi sun bayyana".
Tace "Atoh, ai naji ance mata Darling tace Darlo, Mumcy kuma sai Momso ko?"
Kayyatacen murmushi yayi yace "Mancy, Mancy ta ke ce mata".
Sunan da Darlo ta sanya ma Momcy kenan, ni Mancy, Baba ma Mancy, kowa ma Mancy, rayuwarmu gwanin ban shaawa, muna da Gata, kudi, kwanciyar hankali, muna kyautata ma Makwafta da danginmu, muna taimakawa duk wanda yazo mana da kukanshi, muna sharewa ma wanda ya tunkare mu da matsalarsu hawayensu, kuma ko wani Gida a Anguwar na da kwanon Abinci rana da dare.
Labiba wallahi ba mu san akwai wani abu wai shi damuwa ba, Baba da Mancy na biya mana ko wace irin bukata.
Motoci na sunfi 3 wanda duk baba ya mallaka minsu, kudi a account dina kuwa sai na rasa me zanyi dashi.
Bamu san komai ba sai Jin Dadi, Farinciki Annashuwa.
Da lokaci yaja Baba ya sake fantamawa cikin Siyasa, Mancy ta zama Sister a General Hospital, ni kuma na tafi karatun Degree a London bayan an sha fama da Baba wanda da k'yar ya yarda na tafi karatun, amma kinsan duk hutu ina dawowa Gida, in ban zo ba su zasuje, duk a lokacin duniya na kwance.
Wani dawowa hutu da nayi na san Yayanki, Baba ya aikeni da dubu 10 Gidanku, yace ka shiga gidan da ke jikin gidan nan, ka kaima Muhammadu kace gashi ya siya Rago yayi hidimar Suna inji ni, da na tambayi Mancy waye shi sai ta ce min wani Matashi ne mai sanin ya kamata, Ba su dade da dawowa garin ba, matarshi ce ta haihu, nace "ayyah Allah sarki, barin kai mishi sakon Baba" Lokacin aka haifi Ameera diyarki.
Na koma Makaranta na hada Degree dina, mai makon na dawo gida kawai sai na Jona Masters dina bangaren abunda na karanta wato Engineering.
"Ke nagaji"
Ya fada ya na me fito da kwalin Sigari a gefen Wandonshi, kallon mamaki ta bishi dashi, a ranta tace "ba dai Sigari zai sha a gabanta ba, aa ba shi bane, ya zai sha Sigari a daki?" a sannan hancinta ya jiyo mata warin sigarin da ya dade a dakin wanda sai yanzu ta ankare da warin meye.
Ba ta lura ba sai ganin hayak'i tayi na tashi, zabura tayi ta kalleshi, ashe tuni ya kyasta sigarin nan yana bankama cikin shi hayak'i.
Baki sake Labiba ke kallonshi, DanMakaho ya wuce tunaninta, kasa daurewa tayi sai da ta tanka tace "yanzu a daki ka ke shan Taba?" banza yayi da ita, sai ma kara kunna wata da yayi.
Ba ta yi shiru ba tace "ina laifin ka fita daga waje, ni gashi hayak'i ya isheni, kasan ina da athma" tarin k'arya ta fara yi.
A tak'aice yace "Fita"
Da sauri ta tsaida tarin k'aryanta, ta na son jin karashen labarinshi, akwai tambayoyin da take son ya amsa mata tace "ai bance zan fita ba, gani nayi bai kamata ace kana shan Taba ba a daki ba".
"Dakinki ko nawa?" ya soko mata tambaya da sauri tace "aa nakane, Allah ya baka hakuri".
"Kinga bansan wannan san iyawan da kike min ko?" Murmushi tayi tace "kayi hakuri".
Jikinshi yayi sanyi "Ok, kina ji ba? Komai ya chanza ne a ranar da na dawo Naija, wani hutu mukayi na dawo Gida".
Ranar da ba zan taba Mantawa ba, muna zaune a Bukkar waje Ni,Mancy da Dalo muna shan Fruits, dama Daddy yayi tafiya kwananshi 8 ba ya gida yaje Abuja wani aiki.
Sai ko ga Motocin Daddy sun shigo harabar Gidan, gabaki daya muka tashi don murna, mu uku muka hau rigerigen karasawa ga Daddy.
Sai ya fito kanshi a dage, maimakon ya kula mu da muka zak'u da ganinshi, sai dauke kai yayi ya zagaya ta dayan side din motar, a lokacin muka fahimci cewa bayan Odilenshi akwai mutum a Motar.
Wata Mata muka ga ta fito daga bangaren da Daddy ya bude k'ofa, ta fito ta na mana kallon kaskanci, gabana ya fadi na kalli Mancy wanda itama na rantse gabanta ya fadi, duk tsawon shekarun nan, duk rashin wayau na a wannan lokacin fuskar nan bata taba gushe min ba".
A kagauce Labiba tace "Wacece?" Zaid yace "Wacce tayi sanadiyar da ake ce min DanMakaho" Labiba ta zaro Ido tace "Aunty Shafa'atu?" Zaid yace "Exactly" labiba tace "Ya akayi? How comes? Wai itace dama Aunty Shafa ta yanzu? Ba saki uku Babanku ya mata ba?".
Sigari Zaid yaja Sosai ya furzar cikin bacin rai ya cigaba da cewa
"Ni da Mancy muka tsaya kallon kallon, Dalo bata santa ba, da gudu ta karasa gun Daddy don ta rungumeshi, yanda kika san wanda Kashi ya taba, haka Daddy ya zabura da da Dalo ta nufoshi, Dalo bata fahimci yanayin Daddy, ta kara kusantoshi, da wani Zafin nama Daddy ya ture Dalo ta fadi k'asa"
Mamaki ya rufe mu, da sauri na k'arasa gun Dalo na dagata don ta fara kuka, da murmushi a fuskana mai dauke da mamaki nace "Daddy sannu da zuwa" wani irin muguwar hararar da ban taba ganin Irinta ba Daddy ya wurgeni dashi, gabana yayi mugun faduwa a lokacin da na hango tsana a idon Daddy, lokaci daya wallahi Allah na fita hayyacina".
Mancy na tsaye fa, mamaki ya gama kare mata, da k'yar ta iya daga k'afa ta karaso tace "Sannunku da zuwa, Hajia Shafa, Baban Zaid,Sannunku da zuwa".
Kamar jiranta Baba yake "Baban Zaid? Kar ki sake kirana da wannan sunan, ke ki ma fitar min a Gida Na Sakeki Saki Uku Maryama bana sonki bana son ganinki".
Wani tsalle nayi na rik'o Mancy da ke niuar zubewa,Hankalina a tashe, Mancy kuwa kasa motsi ta yi, Dalo kuwa ta fashe da kuka ta karasa gun Daddy tana jijjiga shi "Daddy me kake cewa? Me ya faru? Daddy wacece wannan?".
Turetan Daddy ya sake yi, yace "muje Hajia Shafata" Hamshakiyar sai yanzu tayi magana tace "yi gaba Alhajina gani nan zuwa" kamar jiran umurni yake yayi gaba, takowa tayi kusa da mu tana murmushi mai kama da na mugunta.
Idonta a kaina tace "Zaid, ko ince DanMakaho, ina fatan baka manta ni ba? In ka manta ni zan tuna maka, ba zan so ka manceni ba, yanda ban taba mantaka ba, kaima ba zaka taba mance ni ba, yanda na tozarta a sanadiyarka sai ka wulakanta a sanadiyata, sai ka zama abun kwatance a garin Katsina"
Ta kalli Mancy tace "Alkawari nayi, duk randa na shigo cikin gidan nan ke kuma zaki fita"
Ta kalli Sadiya tace "Dalo ko? Ba a taba baki labarina ba? Nice Aunty Shafa dinki,Matar daddy dinku, shekarunki sha biyar? Shekaruna 16 rabona da gidan nan, na kuma dawo ba fita".
Ta na kaiwa nan ta wuce ta barmu tsaye, kowannenmu hankali tashe yake, bamu da wani sauran farinciki daga ranar, galihun mu ya bace, komai ya watse mana, duniyarmu ta koma k'ankanuwa".
Labiba ta fashe da kuka tace "ni fa ban gane ba, Ina Mancy? Me ya faru bayan nan? Ni har yanzu banji me nake son ji ba, donAllah ka gaya min". Kuka take sosai.
Zaid ya tashi tsaye yace "kinsan Allah nagaji, yunwa nikeji, ya dade da nayi magana mai tsawon haka, kar ki damu wata rana zan idasa gaya miki labarin, kawai dai a gurguje Mancy na aure a Abuja ta na da diya daya".
Kina son sanin meyasa na tsinci kaina a yanayin nan? Its obvious amma na miki alkawarin ida baki labarin, but a takaice zan iya shan kwalin cigari biyar a rana shisa 'yan bencin Eskaley suke ce min MANKAS.
Hello Bibilicious fans, afuwan, komai ya daidaita nagode da adduoinku da fatan alherinku gareni.
#Ilove
#DM
#SonSoFWA
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Tara (ABUNDA YA FARU)
Labiba na ta girgiza kai tace "donAllah ka gaya min mai ya maidaka haka?".
Dan kallonta yayi lafij yace "are you not listening? Ba ki fahimci duk abunda na fada miki ba yanzu? Isnt it obvious? Matar Uba ta maidani haka, ke ko komai sai an gaya miki kafin ki fahimta?".
Sausauta murya Labiba tayi tace "naji, ina son sanin Meyasa ka fara shaye-shaye? Wacce rana ka fara shan Sigari? Meye dalilinka na shan Sigari?"
Kallonta kawai DanMakaho yayi, mai take so ya sanar da ita baya ga abunda ya gaya mata yanzu? Ya lura ta na da naci sosai, tsaki yayi ya yayi hanyar k'ofa yace;
"Nagaya miki yunwa nakeji, ina da buk'atar cin abinci".
Gunguni tayi tace "da kana jin yunwa da ba ka banka ma cikinka wuta da sassafe ba".
Waigowa yayi yace "me kikace?"
Baki ta zumburo tace "fa banyi magana ba".
Kai ya girgiza sosai yace "kina wasa dani Labiba, zan miki hankali"
Ya sa kai ya fice, da sauri ta mik'e tsaye ta figi jakkarta ta bi bayanshi.
"Tsaya, ya zaka barni a nan?" Be juyo ba yace "dama ni na kawo ki?" "To wai ta ina zan fita?" Bai fasa tafiyar ba yace "ta inda kika shigo".
"Seriously?" Bai amsata ba yayi gaba abunshi, ba ta da zabin da ya wuce ta tsallaka fasassun bulo ta ketara zuwa Gidansu.
**__**_**_**_**_**_**_
Wannan Sakin da Alhaji Ali ya mata, ya girgiza duk wani gabban jikinta, ta san dole ya dau hukunci, ta san shirun da ya mata yana neman hukuncin da ya dace da ita, amma Saki? Saki har uku? Ba ta tunanin ta canchanci Saki Uku, ita da ta soshi tsakaninta da Allah, tun bai kai haka ba, ta zauna dashi da dadi ba dadi, ta shanye bakincikin da danginshi suka ta k'unsa mata, wai ita ya saka saboda danshi? yanzu ya zata yi? Ita fa ba ta so ta yarda, don tunanin na barazanar fasa mata kwanyar kai.
Yunk'uri tayi daga inda take durk'ushe a tsakiyar unguwa ta nufa Gidan da niyar shiga, sai dai kash akwai masu tsaron Gidan, suka sa mata fullstop daga bakin gate, tayi magiyar ta yi haukan amma a banza, wani ma daga cikin securities din ya shaida mata in ta sake zuwa zai ya daureta.
Kuka Shafa'atu keyi sosai, kallo daya zakayi mata ka san tana cikin tashin hankali, da ta ga ba sarki sai Allah, sai ta ja kafarta ta nufa Unguwarsu Aminiyarta Er Rabi.
Hankali tashe ta isa Gidan, jikin kawarta ta fada ta fashe da kuka mai ban tausayi, hankalin Er Rabi ya tashi, ta shiga lallashinta da kyar ta samu ta bata labarin duk abunda ya faru.
Kirji Er Rabi ta dafe, Saki uku? Yau an shiga uku, a kan wani dalili zai sakeki? Shi be san tsautsayi ba? Hmm Shafa'atu, wallahi banga laifin kowa ba sai laifinki, tun yaushe nake binki kan ki barar da cikin Maryama? Tun yaushe nake ce miki a batar da Zaid, saboda ni wallahi na san yaron nan shi zaiyi Sillar barin gidan ashe Hassashe na ya tabbata, yau mun shiga uku, sai da Alh Ali ya fara mahaukacin Azziki zai sakeki?"
Kuka Shafa ta fashe dashi tace " nidai ki taimaka min in koma, magiya ta fara yi mata, Er Rabi ta lura kawarta na son zarewa, dawowa kusa da ita tayi, ta tariyota jikinta tana lallashinta tace "kinsan dai a yanzu ba aure tsakaninki da Ali, sai kin sake wani auren".
"Wallahi ina da wanda zai aureni ya sakoni a yau dinnan" Er Rabi tace "dakata Hajia, ina ke ina aure yau? Ko kin manta shari'ah ne? Akwai Idda a kanki, bayan nan ma dai ina so na farko ki kwantar da hankalinki, na biyu kuma ki yarda dani ki bar min komai".
Share hawayenta tayi tace "eh na bar miki komai, na yarda dake".
Washegari Er Rabi ta fita tun kan gari ya waye, Shafa'atu ba ta tashi ta ganta ba, kasa hakuri tayi tayi wanka ta fita zuwa Gidan Alhaji Ali, kamar jiya masu gadi suka ci mata mutunci, suka hanata shiga, wuri ta samu ta rakube a inda marok'a ke zama don jiran fitowan Alhaji Ali duk safiyya, ta san ya kusa fita Office, bayan 1hr sai ga Motocinshi sun fara fitowa, da sauri ta mik'e tsaye ta nufe Motar da take da tabbaci yana ciki don ya tsaya yana sallamar marok'a, yana hangota ya ciro kudadden da be san yawansu ba ya ba wani Yaronshi yace ka raba ma kowa, ya kallo driver yace mu tafi, kafin ta karaso tuni driver yayi gaba, sauri sauri gudu gudu ta bi bayan motar, daga bisani ta tsaida kekenapep tace ya kaita Office din Speaker, tana isa kuwa ta iske karnuka irin police dogs dinnan, securities suka sake mata su bisa umurnin Ogansu, a guje ta bar gurin da kyar ta tsira ta koma Gidan Er Rabi tana haki Rai a bace.
Daidai da dawowan ErRabi, rik'ota tayi ganin tana neman kifewa "Hajia Shafa'atu meya faru? Lafiya?" Tana haki tace "Karnuka Ali ya sa aka sakar min, da kyar na tsere".
Ran Er Rabi bace tace "yanzu wurin shi kikaje Shafa'atu? Gashi ya wulakantaki a banza".
Sai da nace ki bar min komai" ita dai Shafa'atu bata bar kuka da kumbure kumbure ba.
Er Rabi tace "saurareni da kyau, daga gurin mallamina nake, na kai mishi kukanki, amma yace na kaiki, don ya kalli kwayar idanunki ya karanto miki matsalolinki, kinsan shi baa mai katsalandan, shiyasa banje dake tun wuri ba, in ba shi yace azo da mutum ba, ba a mishi jaye-jaye, aikinshi kamar yankan wuka, kuma ba kya fadin damuwarki da ya kalleki ya san damuwarki ta mecece"
Shafa'atu da ta natsu tana sauraronta tace "Er Rabi, kina da tabbacin zai magance min masalata, shi da bai santa ba ta ina zai maganceta?"
Shafa'atu tace "La Ilah, ya kike magana? Wai baki yarda dani bane?".
Hawayenta ta share mata ta kwantar mata da hankali, sai da ta ga hankalinta ya dawo gareta kafin ta fara magana,
"Banda haufi kan Mallam, sai dai in ban kai mai kuka na ba, da naje yake magance minshi"
"Yace inje dake" wuf Shafa'atu tayi tace "to wai jiran me mukeyi ne? Danallah mu tafi"
Er Rabi ta mike, suka fita gabaki daya basu tsaya ko ina ba sai tashar da zai kaisu kauyen Marmara.
Babban Gidane don Gidan kadai ne gini bulo, maigadi bai tsaya musu iso ba don Er Rabi yar Gida ce.
Mallam na zaune a wani parlorn da yaji kayan alatu, rik'e yake da wani zungureriyar chasbaha a hannayennshi biyu.
Daga wani tuntun Er Rabi ta zauna, ganin haka yasa Shafa'atu zama kusa da k'afar ErRabi. Er Rabi tace "Mallam kaga nadawo ko? Mutuniyar ce ba ta da sany shiyasa muka taho yau ba gobe ba".
Mallam da tun da suka shigo yake bin Shafa'atu da wani kallo, cikin rashin sabo da irin kallon da ya ke mata ta gaisheshi, ya amsata da faraarsa.
Ya fara magana ba tare da ya daina jan Chazbaharsaba
"A gurguje Sunanki Shafa'atu, kin auri mai girma Speaker Alh Ali Zaki tun baida komai, kin so shi tsakani da Allah, ba ki taba haihuwa ba, kin shanye bakin cikin dangin Miji, kin zauna da kishiyarki lafiya ba wai don kina sonta ba, sai don Mijinku, ta haihu, son duniya Alhaji Ali ya daura ma dan nan, kika zo kika fara kishi da dan, kika nakasa mishi ido, Alhaji Ali ya miki Saki uku, yanzu kina sonshi, kina so ki dawo gidanki, kina so wannan karon in kin dawo ki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
Da mamaki yanda ya karanto mata labarin Rayuwarta take gyada kai "hakane wallahi, ka taimakeni, da na sake aure zan kashe auren in koma ya aureni, bana so na samu matsala, bana so wani ya bani matsala wurin komawa Gidana, bana son kowa ya sake daga kai ya kalleni a wulakance".
Mallam yace "kije ki gama Idda ki dawo" ba gardama ta tashi tayi gaba Er Rabi kuwa ta tsaya suka danyi magana da Mallam kafin ta fita.
Bayan ta gama Iddah
Er Rabi ta jadadda mata kan Rashin yi ma Mallam Gardama, da kuma bin duk wani abunda yace tayi, ka nan suka koma Gidan Mallam.
"Shafa'atu aikina ba kamar na saura bane, bana aikin Ammaja, ina da kudi, bana karyar aiki, bana aikin da zai warware bayan shekaru dubu, ko mai zai faru aikina nike warwareshi da hannuna, ki gaya min, zaki iya bin sharrudda na?"
Da sauri ta gyada kai, don ita ta matsu ta koma Gidan aurenta, a yan watanni hudu, ji take kamar an rura mata wutan son Alh Ali tace "Mallam na shirya, zanyi duk abunda kace"
"Aikina ba a hadashi da na kowa, ni na fara sa hannuna cikin Alamarinki, ni na bude aikin ki, in kika koma gun wani ya miki aiki daga yanzu, aikin da na riga na sanya hannu, to zaki biya da ranki, mutuwa zakiyi".
Baki na rawa tace "Ni wallahi ban san kowa ba"
Yace "kamar yanda na gaya miki a zuwanki na wanchan karon, in har na karanceki daidai, a yanzu kina so ki koma gidanki, kina so wannan karon in kin komaki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
"Eh haka ne, haka nake so"
A takaice yace "to hakan ba zai faru a yanzu ba".
Gwalalo ido tayi hankalinta tashe yace "na duba sosai, ba wani abun kirki da na hango, ba Alheri, ko kin koma ba zaki tarar da komai ba sai bakinciki da kunci, kyara, hantara da tsangwama, ke babu ma hanyar komawarki a yanzu don ba karamar tsana dangin suka miki ba, kuma akwai kariya sosai a Jikin Alhaji Ali da Iyalenshi, so a yanzu ba zai yiwu ba, shawara, ko kiyi hakuri har sai lokacin da zan dubo daidai, ko kuma shi Alhaji Alin ki hakura da shi baki daya".
Fashewa tayi da kuka tace "Bangane ba, wallahi ba zan iya hakuri da shi ba, zan jira har sai lokacin da ka gano Alheri, ko nan da shekara 50 ne".
Dariya mallam yayi yace "be ma kai shekara50 ba, shekara sha biyar(15) ne ba yawa".
Fargaba, tsoro suka dura a kirjinta a yayinda ta hango iyakar gaskiarshi, cikin rudu take cewa "bangane shekara 15 ba, Mallam donAllah bar wasa muyi maganar da ya kamata".
Dariya yayi yace "Kina ganin kamar wasa nake, kije ki gwada auren Alhaji Ali, ai ba ma zaiyiwu bane, in kina son burin ki ya cika, ki daure ki cika shekaru 15 dinnan zaki ga ribar hakuri, har ki dafa dutse ki sha romonta".
"Mallam wai wani irin Shekaru 15? In na mutu kafin nan fa? In shi ya mutu fa? Kai in akayi K'iyama kafin shekarun su zagayo fa?"
"Ke ki bar wannan tunanin bana so ki hango komai sai nasara, ki kallo nasara har kin sameshi, a lokacin Arziki ninkin ba ninkin, kuma sai yadda kikace, kuma a duk inda kike, in dai shekarun suka cika, sai ya nemoki, ko da kina kasar sin".
Shiru tayi tana wasu tunani, ta waiga ta kalli ErRabi wacce take daga mata kai alamun amincewa, basirarta ta dode, zuciyarta ta bushe, hangen dogon buri take, take zuciyarta ta dinga hasko mata abubuwan jin dadi da ke jiranta nan da shekara Sha biyar.
"Na fahimta Mallam, shekara wata rana kwana ce, kamar gobe ne, Allah ya kaimu".
Mallam ya murmusa "to akwai wasu maganin da zan dinga rubuta miki a, ke da kanki zaki dinga wanke shi"
Ido ta gwalalo, tsoro ya rufeta.
"Kwantar da hankalinki, ni zan aureki, kinga kawai da nagana aiki a kanki, da na sakeki, kawai sai ki aure tsohon mijinki".
Da yake zuciyarta ta dakushe, ba ta da mafadi, ta amince da bukatar Mallam, Mallam ya aureta, ya cigaba da aiki a kanta a cewarshi, sakinta yayi bayan Sati 1.
Abun mamaki wai don auren da sukayi na kwanan 7. Shafaatu ta samu ciki, murna Shafaatu tayi harda kuka, gani take aikin Mallam ya fara ci, bata son Mallam ko kadan, amma inta tuna nan da shekaru sha hudu da rabi zata auri masoyinta na asali sai ta ji dadi.
Ba yanda Mallam beyi kan ta zubda cikinta ba ta ki, son cikinta take sosai, kuma ita da ba ta taba ko da bari ba akan me zata zubar da cikinta, aiko ta na son abunta".
Mallam yace "shi ko ba ruwanshi"
tace "ta yarda".
Yace "Kiyi tafiyarki, ki cigaba da rayuwarki kamar kowa, 18/10/2008 Alhaji Ali zai zo wurinki a duk inda kike,ki rubuta ki ajiye, ki fara irga kwana daga yau".
Da Murna ta bar Gidan Mallam ta koma Gidan Er Rabi, ta hade kayanta da yan kudadden da take dasu ta koma Gidansu da ke Jos.
Uwarta ta shiga tashin hankali da ta gaya mata sakinta a kayi, amma ta kwantar da hankalinta ganin hankalin diyarta a kwnace yake. Zaune suke da dadi ba dadi, lokacin haihuwarta ta yayi ta haifi diya Mace suka sa mata suna Amina suna ce ata Annah.
Bata damu ta gaya ma mallam ba don ya riga da yace ba ruwanshi da diyar, don shi mallam bai san iya adadin yaranshi ba.
Haka Shafa'atu tayi rayuwar Jos da dadi ba dadi,duk da son Ali Zaki beta bacewa ba.
Shafa'atu na da Labarin Gidan Alhaji Zaki kaf dinshi, duk abunda suke ciki Er Rabi na gaya mata.
Tare take da Mahaifiyarta, da diyarta da k'aninta Hudu da ba zai wuce tsaran Zaid ba, ko ya girmeshi ba da yawa bane.
A shekararsu ta 5 ne Mamarta ta fara wani irin ciwo, sosai rashin Lafiyarta ya kwantar da ita a babban Asibitin Jos, bincike ya nuna Hantarta ce ta kumbura, kuma tana buk'arta a mata open surgery.
Hankalin Shafa'atu ya tashi, ta rasa inda zata neman kudi, gashi ba kudin nan, damar duk buga buga ce.
Duk inda zata aron kudi sai ace babu. Ta kira Er Rabi a waya tace ta ara mata dubu dari3, Er Rabi tace "wallahi bata dashi babu" hankalinta ya tashi, ErRabin ce hope dinta, yanzu ya zatayi? Katsina zuciyarta ke kira mata, kawai taje gurin Alhaji Ali.
Ba doguwar Shawara washegari ta shirya Annah, suka bi Motar haya zuwa Garin Katsina, shi kuma Hudu zai zauna wurin Mama kafin su dawo.
Suna isa duk a gajiye, Annah ta fita hayyacinta, ga yunwa ga gajiyar Mota, direct ta nufa Offishinshi duk da Marece yayi.
Wurin Secretary dinshi ta buk'aci ganinshi, Secretary tace "ba ki da appointment, kuma 4 ya wuce, baya ganin visitors, kuma he is about to leave, ki bari sai gobe" magiya ta fara yi mata, Annah ta fara kuka.
"Meke faruwa a nan?" Muryarshi ta doki kunnuwanta, da sauri ta waiga inda yake tsaye, ya fito daga office ga wasu mutane masu bakin suit da bakin Gilashi suna gefenshi.
Idonshi ya sauka kanta, nan da nan fuskarshi ta hade, kafin ta yi magana yace a kausashe "me kikeyi a nan? Bana ce kar ki kara fitowa gaban idona ba? Bance miki bana son sake ganinki ba? Bance miki na tsani ko da kalonki ba? At this instant, bace min daga gani kafin na sa a Wulak'antaki".
Dama tuni take zube gabanshi, kuka take tana girgiza kai "Alhajina, ka taimakeni, Mama na chan kwance bata da lafia"
Bai saurareta ba yayi umurni da a fitar da ita.
A wulakance a ka fitar da ita, tana kuka ta karasa Gidan Er Rabi, ErRabi ta basu Abinci, ta tausheta da cewa nan da shekara 10 zata dawo Gidanshi sai ta fanshi bakincikin da ya kunsamata na shekaru, a haka ta dinga lallabata.
"DonAllah muje ki rakani wurin Mallam, kila zai taimaka min, ga Annah ma, be ma san ya take ba, kuma diyarshi ce"
Er Rabi tayi saurin katseta, "aa Shafa'atu ba haka kukayi ba, sai da yace zai baki magani ki zubar da cikin Annah kikace aa, kikace ya bar miki cikinki, harda kuka, yace kar ki taba zuwa gabanshi da diyrki, kar ki taba ambatonshi a matsayin uban diyarki, kikace kin amince, yanzu kuma kice muje gurinshi? Karki manta yace ya gama aikinshi kanki rana kawai zaki jira, yace duk randa kika zo mishi da maganar diyarki zai kwance komai da ya kulla kinga kinyi jiran banza, Shekara 5 ta tafi a banza, komai ya tashi a banza, ke dai kiyi hakuri yanzu, gobe ki koma Jos a fara ma Mama maganin hausa zaa dace".
Kuka Shafa'atu kawai take, Washegari da Asuba tayi Sakkon komawa garin Jos ranta 6ace, ta na dawowa da kwana daya Mamarta tace ga Garinku nan, ta girgiza da mutuwar Mahaifiyarta ta sha kuka son ranta tana tausayin kanta da na kaninta Hudu, basu da kowa, basu da komai.
Rayuwa ya mata zafi, dole ta rayu kafin Burinta ya cika, dole ta zama karfin Annah da Hudu, dole duk su rayu, mikewa tayi tsaye ta fara Abincin Saidawa kamar yanda sukeyi a da, kasancewar ta iya Girki, kuma akwai Tsafta ya sa take samun Customers. Kuddirinta na nan, ranta chunkushe, Ganinta Ali zaki ne yayi sanadiyar mutuwar Mahaifiyarta, da ya taimaka mata, da amma Uwar ta aiki da ta warke, Ta k'agara Shekaru 10 su cika ta fanshe Bakincikinta.
Bayan Shekara Goma
18/10/2008
Yau take Sallah a gurin Hajiya Shafa'atu, kwalliya ta ci ta sa tsaddaden leshin da Allah kadai ya san inda aka samu kudin dinkawa, harta lalle sai da aka K'unsa mata, yanda ka san Sabuwar Amarya.
Da karfe 1 na rana Annah ta shigo dakinsu, tace "wai ni Mummy ina Baban nawa? Har yanzu bai iso ba?"
Shafa'atu ta fara girgiza kafarta, ita fa a ganinta ko garin yau be idasa wayewa ba zata ga Alinta, gashi har an fara kiraye kirayen Sallah.
Ba ta so ta sa shakku a Aikin Mallam, Shekaru 15 tayi tana jiran Ranar nan, ga ranar tazo, gashi ranan ya mata kama da sauran ranakun da suka shude, ba wani abu special game da ranar yau, ko dai tayi wauta da sakaci da ta yarda da maganganun Mallam? Ko Annah bata amsa ba ta ciro wayarta ta latso Er Rabi, Er Rabi na dauka ta fashe da kuka.
Yau waya kala kusan 10 sukayi, Er Rabi tace "Yaya ne? Ya iso ne?"
Shafaatu ta fashe da kuka tace "wani isowa? Har yanzu shiru, sai da nace miki zanzo Katsina kila gidan ya mai wahalar ganewa, er Rabi ya zanyi? Ko dai mallam ya wanke mu ne?"
Er Rabi tace "ke dai baki da hakuri, ki bari ranar yau ta kare mana kafin kiyi korafi, kinsake hakuri, kar ki sake kirana sai yazo" dif Er Rabi ta kashe waya, ran Shafaatu a bace.
ABUJA
Zuciyarshi ke mishi Zafi tun bayan Sallahr Asuba, Ji yake kamar a na yankar Naman jikinshi. Meeting sukayi , amma be fahimci komai ba.
Meke damunshi? Ya tambayi Zuciyarshi.
"SHAFA'ATU"
A takaice zuciyar ta amsa mai.
Yana son ganinta, ta na ina? Tayi aure? Akwai auren wani a kanta? Ta mutu? Da sauri ya girgiza kanshi da ke barazanar tarwatsewa, tunanin Mutuwarta na neman dauke mishi numfashi, in ta mutu sai ya bita, in kuma tana da aure ko zaiyi yawo tsirara sai ya raba auren nan ya dawo kanshi, zai biya Mijin da duk wani k'addara tashi.
"Ina zan fara nemanta?" Ya tambayi zuciyarshi.
JOS ta amsa mai, kamar ana karanto mishi abunda zaiyi haka yake ji, kurum ya kira PA dinshi yace a siya mishi ticket din Jirgi zuwa Jos, haka ko a kayi, a gurguje suka isa Airport, suka nufa Jos bayan Mintuna da basu kai 50 ba suka isa Jos.
Akwai Convoy din da suka zo tarbenshi, be manta Unguwarsu ba, ya gaya ma driver cikin 30mins suka iso Unguwarsu Shafa'atu.
Kamar ana ingizashi ya fada Gidan, ko Sallama babu, abunka da me jira, ta na zaune tsakar Gida, tana ganinshi ta mik'e tsaye, murna ya sa ta fashewa da kuka, da niyarta in yazo ta dan gasa mai gyada a hannu ta ja aji, amma ganin yanda ya shigo, ta manta da duk wani bacim rai da ya taba kunsa mata a rayuwa, Son shi ya goge mata komai, daga inda yake ya choge tsaye, hankalinshi ya dan tashi ganin ta na zubda hawaye kai ya girgiza mata tare da ware hanayenshi Biyu, da gudu ta fada jikinshi ya rungumeta gam yana samun wani irin natsuwa.
Murya a dishe yace "Shafata, ina kikaje kika barni cikin kewanki, Shafata me na miki kika barni?" Kiyi hakuri kizo mu cigaba da Zamanmu, Ina sonki, kece wacce na fara so a rayuwata" ganin yanda yake sake rungumeta ya sata cewa "Yarinya na kallonmu,Alhajina ai Sakina kayi, Saki Uku ma" da sauri ya tureta yace "Inji Ubanwa yace Sakin ki nayi? Nifa ban sakeki ba, ta ya zan rabu da rayuwata? Baki da labarin kece Rayuwata".
Dan tabe baki tayi tace "Ya kayi da Shekaru 15 da suka wuce?" Yana son yin dogon tunani amma ya kasa cewa yayi "Ni bansani ba, kar ma ki tambayeni, abunda na sani shine, san karashe rayuwata dake, ba zan taba bari kiyi man Nisa ba".
Wani Farinciki ya ziyarceta, dadi kamar tayi tsalle, "Shafata, Katsina zan tafi dake, ba zan iya kwana ba da ke ba, yau dare yayi, gobe zamu dau hanyar KT kinji?"
"To wa ya ce maka zan bika? Ina da Auren wani a kaina" ganin yana neman haukacewa tayi saurin cewa "Wallahi wasa nake maka hahaha" kamar yayi kuka yace "kina son wahalar dani ne? Ki zo mu tafi Masaukina" Cike da shagwaba tace "Auren fa? Ba zaa maida ba?"
Yace "Yanzu kuwa zaa maida, Da anyi sallahn maghrib sai a daura" Dadi kasheta, nan ta mishi introducing Annah a matsayin diyarta da Babanta ya mutu, Hudu kuma kaninta.
Yace "duk baki da damuwa, Annah Diyata ce, Hudu kuma kanena, dukkansu na dauki nauyinsu na tsaya musu, tare zamu tafi dasu".
Godia tayi mai sosai, bayan Sallahn Maghrib aka daura Aurensu sadaki dubu dari 5, a ranar duk basuyi kwanan Gidansu ba, sai a kayattacen Hotel dake Jos.
Washegari da Sassafe suka hau Jirgi suka nufi Kano, daga Kano suka hau Mota zuwa Katsina.
Suna isa KT ya bada Umurni a kai Annah da Hudu Shopping Mall suyi siyayyan Kaya.
Shikuma suka nufi Gida tare da Amaryarshi.
^^^^^^^
Kiraye kirayen Sallahr Azahar akeyi, ashe ta dade a wurin Dan Makaho, ita ina ta lura lokaci ya ja? Wuri ta samu ta buga tagumi, tana ta nazarin Labarin danMakaho, wayarta tayi k'ara Jay ta gani a gaban screen.
Numfashi ta ja ta saki ta dauka wayar da Sallama "Labeenah, ina kika shigane? Nayi missing dinki sosai" In Ina ta fara "Eh wallahi lecture mukeyi, nima nayi missing dinka"
"Yaushe zaki ban lokaci na zo Katsina?" Murmushi tayi tace "duk lokacin da kazo, ina maraba da kai"
Hangoshi tayi daga inda take, ya dawo dauke da wani abu a hannu, mancewa tayi da Wayar da take ta mike zuruf ta kuka tsallaka fasasssun Blocks din ta bishi daki har ta kusa bashi tsoro.
"Ke wai meyasa baki da hankali ne? Ta ya zaki ta shigo min daki ne? Wato ba kiji warning din da na miki ba ko?"
Baki ta tabe ta kalli ledar hannunshi, Bread ne sai Sardines, tace "ni karashen labarina nazo ji"
"To ba zaa bada ba"
Wuri ta samu ta zauna harda daura kafa daya kan daya tace "gama ci dai".
Tsaki yayi, gardama da ita aikin banza ne ya bude Kifin gwangwaninshi, ya na dangwala mai din da bread yana ci, be kulata ba, ita kuma latsar wayarta kawai take.
Daga waje kuwa Blocks aka kawo da Cement da Yashi zaa fara aiki.
"Kina ji ba?" Da ya gama kenan, da sauri ta ajiye wayar tace "eh ina jinka.
"Jikin Mancy Rawa kawai yake, rik'ota nayi na mata garkuwa da kafada na" ban bi ta kan Dalo da ke kuka ba, Mancy ta zare jikinta daga gareni tayi hanyar cikin gida duk sai muka bita.
A parlo muka tsaya inda muka ga Baba da Anty Shafa'atu suna magana, ce mishi take ita ba zata iya zama a dakunan nan ba, bata san surkullen da ke ciki ba, kafin ya bata amsa ya hngo mu, Baba na ganinmu kamar an aiko mai da mutuwa, dif annurin fuskarshi ya dauke, ya ja hannunta ya fita, muma muka bishi riiiiiii,
Mancy ta dan Matsa kusa dashi tace "ka riga da ka furta, ba aure tsakaninmu, aure ya k'are, ina so na san me na maka da na chanchaci Saki Uku gaban Yarana?" Kamar jira yake ya hau kan Mancy da duka, hankalina ya tashi na shiga tsakaninsu, na janye Mancy ina ma Baba Kallon Mamaki.
"Ki fitar min A Gida Maryama, ki kwashi yaranki ki bar min Gida bana son ganinku ku duka, na tsaneku"
Mancy ta share hawayenta, nikuma ina tsaye kamar gunki, Dalo kuwa na zaune dirshen a k'asa.
Mancy ta matsa kusa da Dalo ta tallafota gabaki daya.
Yanayin da ban taba ganin Mancy a ciki ba, ta bude murya tace "Zaid, Sadiya, zamana ya k'are a gidan nan, rabonku ne dama ya kawoni gidan nan, ku sani Nan Gidan Ubanku ne, ba ku da inda ya fi nan, ko ma mai zai faru, i mean no matter what will happen, this is Your Father's house, kar ku taba mantawa, kar ku manta da kalar Soyayyar da ke tsakaninku, kar ku bari kowa ya shiga tsakaninku"
Hannayenta ta daga Sama "Ya Allah, ga Bayinka nan, Allah ga Zaid, Allah ga Sadiya, Allah kaine gatansu,Allah ka sakama duk wanda aka zalunta"
Shafa'atu ta fashe da Ihu "Ni Alhaji sai dai ka Sakeni, Matarka so take ta kafurtani".
Aiko ya yunkuro zai bige Mancy nayi saurin tareshi ina girgiza kai don ban ma da k'arfin magana.
Ki tafi da yaranki" Baba ya sake jaddada mata, tace "ba inda zani dasu, nan ne gidansu, gidan ubansu, Ba inda zani dasu, kamar Zaid? Yana Masters? Ina zani dashi? Dalo da ba nono take sha ba ina zani da ita? Ai suna gidan ubansu, su ba Mata bane balle a sake su, 'Ya'yane su".
Nan suka fara hayaniya, da karfi, ban taba sanin Mancy ta iya fada, don ko an kure hakurinta ne.
Kinsan mai hakuri in an taboshi.
Shafa'atu tace "kinga Maryama rufin Asirinki ki tafi dasu, kika san me zan musu in suka zauna? Ba kya tsorona ne? Ki tafi dasu, wannan Gidan daga ni sai yaran da zan haifa ma Alhajina Magada Babansu".
"Huh tsoro? Bana Shafa'atu, bana tsoron makircinki, ko da ba tsoronki nake ba, kawai na fi so a zauna lafia, kuma yarane gasu nan, ki sa kansu gabas ki yanke, suna Gidan Ubansu, haihuwa kuma Allah ya kawo miki 100, duk dai yaran da zaki haifa ba zaki taba haihuwan Yayan Zaid ba, koma Sadiya, dole sai Kannensu zaki haifa".
Sosai kalaman Maryama suka bata haushi, me zata mata ta bak'anta mata rai? Alhaji wai tsayawa zakayi tana gaya min magana? Wallahi sai dai ka sakeni".
Yana jin haka ya rufe Mancy da duka a karo na biyu, na shiga tsakani ya hada dani, Dalo ma ta shiga tsakani aka hada da ita, ya dinga dukanmu ko ta ina yana halbemu, mu ko muna rungume da junanmu, Dalo sai kuka mai sauti take.
:::::
Zaune yake da 'yar Matarshi, da jaririnsu, wani abu yake ji daga Makwaftanshi kamar hayaniya, kasa kunne yayi sosai,
Gabanshi ya yanke ya fadi, Gidan da ya sani a matsayin Gida da suka kansu a kan Soyayya, Aminci da juna, abunda be taba ji ba, hayaniya, ya ji kamar ana maganar Saki, ya ji kamar maganar Barin Gida ake, wacece Matar nan da ta shigo tsakanin Gidan nan da basu son komai ba sai SO?.
Matarshi ya kalla yace "Aseena, akwai matsala". A tsorace tace "Wai Sakin Mancy aka yi? Inallilahi" kafin ya bata amsa sukaji kamar kuka, da suka kasa kunnensu sai sukaji ashe dukansu yakeyi, da sauri suka tashi a sittin sukayi Gidan Alh Ali Zaki.
Kamar an tara Mutane don wurin cike yake, kowa mamakin Alh Ali yake, yau shine yake dukan Farincikinshi? Da girman Zaid yake dukanshi, yake dukan Sadiya diyar da yake gani itace Yar Gwal, ga matar da yake so kamar ranshi, yau itace yake duka da hannu duk ya galabaitar da ita, rigarta har ya yage har kana iya hango abunda ke ciki, da Zaid ya tashi taimaka mata sai ya sa security su rik'eshi.
Manyan Unguwan sai magana suke mishi suna rokonshi da ya barsu haka, amma be tanka kowa ba.
Muhammad ya shigo da Matarshi Asee, kutsawa sukayi tayi, gidan kamar ana shooting film, kutsawa yayi ya shiga, matarshi ta bi bayanshi, daidai nan Alhaji Zaki ya daga wani katako zai kwala ma Mancy kenan ya karasa da gudu.
"Haba Alhaji, Haba, menene haka? Meya sameka Alhaji? Wallahi ba Girmanka bane? Inalillahi wa ina ilaihir rajiun"
Hajiya Shafa'atu ta dago ta kalli Muhammad da tsana, shi ko Alhaji samun kanshi yayi da maimaita Inalillahi wa ina ilaihir rajiun" waigawa yayi yana kallon su yashe a k'asa, abun alfaharinshi, dukkansu yashe a k'asa.
Hajia Shafa'atu tace "nifa su tafi, ina son na huta" kamar an ingiza shi yace "duk ku fitar min daga Gida, yan iska shegu, duk na tsaneku".
"Alhaji ina kake so suje? Basu fa da inda ya wuce nan" ni wallahi sai sun fitar min a Gida, Muhammadu, ba na k'aunar ganinsu"
DanMakaho ya kalli Labiba sosai yace "Kinsan Unguwar nan kaf, ba wanda nake ganin mutuncinshi irin Yayanki?" Labiba ta murmusa tace "Yayana na da kwarjini" yace "ya min abunda ba zan taba mantawa ba, zuwa yayi ya dago ni ya rungumeni, ya lallasheni ya rada min a kunne, ka zama k'arfin Mahaifiyarka da kanwarka, tashi ka rik'o Dalo, muje gidana muyi magana".
Umurninshi na bi, na tashi na mik'ar da Dalo da ke kwance magashiyan a k'asa. Yayanki ya matsa kusa da Matarshi, ya karbi jaririn hannunta yace ki taimaka ma Mancy, bin umurninshi tayi, ta daga ta ta riko hannunta, ta ja ta, ba gardama Mancy ta bi bayanta.
Sosai mutane suka tausaya mana, ina jiyo muryar wani yana cewa "Me ya samu Gidan nan? Me ya samu jin dadi da walwalar Gidan nan" wani yace "ko nayi rantsuwa ba kaffara, wanchan ce, itace Ummul Abais" Wallahi DanMakaho Allah ya saka muku, Allah ya bi muku hakkinku".
Ba mu ce komai ba muka fita zuwa Gidan Yayanki, kan tabarman da suke zaune na kwantar da Dalo, na yi hanyar fita Mancy tace ma Yayanki donAllah kamo min shi, a wahalce take magana.
Mallam Muhammad yace ina zaka?" Zuwa zanyi ya gaya min dalili? Me muka mishi ya tsane mu, Mallam Muhammad Babanmu ya wulakanta mu gaban mutane, Babanmu ya daga hannu ya dake mu gaban mutane, me muka mishi? Me ya chanzashi".
"Zaid"
Mancy tayi kirana.
Na dan choge na tsaya tace "kazo ka zauna, donAllah, kana da Uwa, and i promise you, ba za ku bar Gidan Ubanku ba"
"Mancy, zaman me zamuyi ba kya ciki? Ta ya zamu fara rayuwa a Gidan nan ba da ke ba, Mancy kafarki kafarmu Allah".
Mancy ta girgiza kai, ta kawar da maganar "Maman Amira DonAllah kina da Panadol a ba Sadiya?".
Eh barin dauko mata, ta shiga Ciki, baban Amira ya bi bayan Matarshi.
Mancy ta matso kusa dani ta rik'oni tace "Stay Strong, kaine Gatan Dalo in bana nan".
"Mancy".
Ta katseni "Zaid, kayi min Alakawari, no matter what happens, ba zaka taba barin Gida ba, aure kawai zai rabaka da Gida, zaka kula da Sadiya, zaka kula min da kanku"
"Mancy"
"Zaid, DonAllah".
"Mancy, ba ki ga kallon da Baba ke mana ba? Ya tsanemu fa"
"Still Zaiduna, you wont leave home".
Kai na gyada mata nace "I wont leave home".
Dalo ta sha panadol, amma masassara ta rufeta, kinga yanda muka damu, lokacin Maghrib Yayanki ya sani Alwala don zuwa masallaci, na bar Mancy da Dalo tare da Antynki.
A waje sai kallona ake tayi, wai kinsan me nagani kofar Gidanmu? Labiba ta girgiza kai yace "Katuwar Mota nagani, tana kwashe kayayyaki wanda kallo daya na musu na san kayan dakin Mancy ne da nawa" nufansu nayi, amma yayanki ya rikoni tare da girgiza min kai, yace mu tafi Masallaci kaji?" Jikina rawa yake, idona ya ciko da hawaye, lallai baba yana son Wulakanta mu.
A gidan Yayanki muka kwana, daki daya ya bamu, Mancy tayi ta mishi godia, yace "haba Mancy, ai kowa ya san ke Uwa ce a Anguwar nan, duk me zamu miki ba zamu taba biyanki Alheranki ba".
Washegari Mancy tace "Zaid, Sadiya, yau zan koma Kano gidan Yaya"
Nace Mancy Dalo bata da karfin jikinta Masassara takeyi, ina zaki tafi ki barta? Ni ya zanyi? Mancy karki tafi? Kar ki juya mana baya donAllah, kar ki barmu, atleast not now, kina ganin korar da ya mana, na gya miki an fitar da kayayyakinmu tas".
Mancy tace "Zaid ya zanyi? Wa ke gareni duk dunia in ba Yayana ba? Ina zanje? Sakina yayi fa, saki 3, ina na nufa? Nan gidan zan ta zama? Ai ba zaiyiwu ba, kuna da Mahaifi, da ranshi, yanzu ba anjima ba zan raku Gida, nikuma na wuce, ina so kuyi hakuri da duk yanda rayuwa ta zo muku, donAllah kuyi hakuri, ina sonku sosai, fiye da rayuwa da kanta".
"Mancy"
Ta katseni tace "Zaid mun riga da mun gama maganar nan, dole ku koma Gidan ubanku, whatever happens he is still your Father, ku tashi mu tafi, so nake kafin karfe 11 in isa Kano".
Labiba banson ma Mancy gardama don wallahi a daren ranan bata runtsa ba, a kan idona tayi ta kuka, zuciyata ta karye amma sai nayi kamar bacci nake, banson ta sha wahalata shiyasa kawai na share, na rike dalo sosai ta ma Yayanki Godia, muka fita muka nufa Gida, dukkanmu gabanmu na faduwa.
Karfe 8 saura muka shiga Gida.
Da sallama Mancy ce me k'arfin halin Rafka Sallama.
Wata Yarinya da bata wuce saar Dalo ba ta fito daga kitchen tana mana kallon wulakanci, sai ga wani shikuma ya fito daga daki wanda nawa ne.
Hannayenmu Mancy ta ja, har cikin parlo, ta zaunar damu, Nasiha ta cigaba da yi mana.
Sallama aka sake yi muka amsa Yan Gidansu Babanmu ne, su Aunty Asabe da Baba Sani, Maza da Matansu, sun kai su 15. Wurin mu suka nufa, Mancy ta tashi ta taryesu da faraa, suko kallon tausayi suke mata.
Ina kwananku muka gaishesu, suka amsa Baba Sani yace "Maryama ashe abunda ya faru kenan? Wallahi sai yau da asuba wani abokina ke gaya min" tace "Ya muka iya da k'addara Baba Sani, zama ne ya k'are" duk su Aunty Asabe suka ma Mancy Jaje don sosai suke sonta.
Wannan yarinyar tayi hanyar Dakin Baba da gudu ta na kiran Mummy, Mummy zo kiga wasu sun shigo mana Gida.
Da ido duk muka bita, ba da jimawa ba sai ga shi sun fito Mama da Anty Shafa'atu.
Da Mamaki kowa yace "Shafa'atu"
Ita ko ta shigo ta na yatsuna Baba na binta a baya kamar Rakumi da Akala.
"Su waye suka shigo mana Gida da farar safiya kamar masu bin bashi?"
Kamar kare baba ya fara haushi "Eh.. su waye suke mana Sauko da sassafen nan?"
Asabe tace "Yaya mune, mai Shafa'atu takeyi a gidan nan?"
"Shafa'atu Matata ce, Jiya aka daura mana Aure a Jos, dama chan kune munafukan da kuka sani Sakinta"
Nan aka fara kallonkallo.
Mancy ta mik'e da alamu ba su ma lura da mu ba tace "Alhaji ka sa an firda min kaya ina aka kaisu?" Kamar wuta ya taso, Gidan da na daukoki chan nace a kai maki, don maita ashe baku tafi ba?".
Tace "Nagode da ka sa a kaimin kayyayakina, tafiya kuma yanzu zan wuce Kano, ga dai Yaranka nan".
Shafa'atu tace "Alhaji nan zata bar maka su" nan ya hayayyak'o "Kai ku fitar min a Gida, Wallahi ba zasu zauna min a Gida ba".
Baba Sani yace "Ahh Yaya, ina zata kaisu? Tunda ka saketa, ai yara nakane, Ina zata da Zaid dan Shekara 25 Sadiya yar shekara 15?".
Wani abu kamar Hauka Baba ya fara "Sani ka fita Idona, ina ruwanka da Sabgar Gidana? In yaran kake so ka dauke su ka tafi dasu, nidai ku fita harkana, banda 'ya'ya in ba Annah ba ita kadai ce diyata".
"Wacece Annah?" Injisu. Aunty Shafa'atu tace "Our Only Daughter ga ta tsaye" kowa ya bi Annah da ido, sai faman harare harare take.
Su Asabe suka fashe da kuka, Waiyo Yayanmu me aka maidaka? Zaka dauki diyar da ba taka ba kace itace kadai diyarka? Yayanmu ka manta yaranka mafi soyuwa gareka Zaid da Sadiya?".
Shafa'atu ta fashe da kuka cike da kissa "Yanzu haka Alhaji yanuwanka zasu dinga min gori?ni gaskia ka sakeni ba zan iya ba, dama chan yanuwanka sun tsaneni".
Hargagi ya fara "Kai Buhun Uban da ya k'ara cewa Zaid da Sadiya ne mafi soyuwa a gareni, kai zan fa kulleku, ku fitar min a gida dukkanku, wallahi duk ku fice min, na sake ganin kafar dayanku a cikin Gidana sai na sa a kulle ku a Cell, yan iska, Matsiyata".
Ya juya garemu yace "Ku kuma na sake bude ido na ganku a gidan nan wallahi zan iya kasheku, don baku san yanda nakeji game daku ba na tsaneku sosai".
Wuf Mancy tayi ta mik'e tsaye "Alhaji Sai ka Kashe su fa kace?" Kina waswasi ne? To ki bari na k'ara ganinsu a cikin Gida kika ga mai zan musu.
"Alhaji ban san mai sihiri ya maidaka ba, Yaya Asabe sai kun tashi tsaye kan Danuwanku, a baiyane kunga dai ba yin kanshi bane, sai kuna sanya shi a addua, nima zan taya ku da Addua a matsayinshi na Uban 'ya'yana amma a yanzu zan dauki mataki, duk abunda ya sami yarana a cikin Gidan nan to shine".
Shafaatu tace "to ki tafi dasu mana in ba kya son komai ya samesu, ai rufin Asirinsu su biki kawai, don ko be kashesu ba, zaman gidan nan sai ya gagaresu, ba Ubanda zai tsaya musu duk fadin Kt, so kinga da su biki daga baya gwara kin tasa keyarsu kun wuce yanzu".
Mancy tace "Abunda ba ki gane ba Hajia Shafa'atu shine, Zaid da Sadiya ba inda zasu, ba wanda zai rabasu da Gidan Ubansu, ko da Uban nasu ne kam, kuma in kinga dama duk ranar Allah ki dinga sa wuk'a kina yankar namansu kuna miya, sai kuma wanda zai tsaya musu? Allah, shi zai tsaya musu, ki ja dashi in kina iyawa".
Ta juya ta kalli Yanuwan Baba tace "DonAllah wa zai kaini Gidan Sarki? Ai in ba wanda ya isa da kai Alhaji, ai baka fi k'arfin hukuma ba" Baba Sani da ranshi ya gama 6aci yace "Muje hajia Maryam, muje ni zan kaiki".
Baba Aminu yace "nima zanje, don wallahi wannan Makirar Matar ba zamu barta haka ba" Su Aunty Asabe sukace muma zamu.
"Wai ni zaku kai k'ara? Ni zaku hade ma kai? Ni zaku tona ma Asiri?".
Hajia Shafa'atu tace "Dallah, duk burga ce, suje muga zasu iya Ja da kai" kamar sakarai yace "to ku tafi din, matsiyata, bani ba ku, kar shegen da ya sake zuwa min Gida".
Ba wanda ya kulashi, sukayi gaba,
Dama Motoci kusan 4 suka zo, kowannensu ya samu Wuri ya zauna, suka nufi Gidan Sarki suna sake yi wa Juna Jaje.
Da suka iso Gidan mai Girma Sarkin Katsina, ba su sha wahalan shiga ba don Amaryar Sarki kawar Mancy ce, tun zuwansu makka suke zumunci.
Sasshenta ta shiga, ita kadai, duk sauran na Mota, bayan su gaisa ta gaya ma kawarta tazo ganin Sarki ne.
Gimbiya tace "kin ko ci saa yau kwanana ne, ya kusa shiga Fada, barin ga in yana iya ganinki yanzu".
Mancy tace "ba ni kadai bane, sauran na Mota".
Gimbiya tace "toufa, bari naje naga"
Bayan kusan minti 40 sai ga ta ta dawo "Afuwan Kawata, ashe yana Karamin Fada, yana ganin wasu baki ne, duk da haka kuna iya shiga" Mancy ta mik'e tace "barin je na kira sauran".
Sun samu shiga Fadar, da biyayya suka gaida Sarki.
Wasu tsofi Mata guda biyu na zaune, sai kusa da Sarki wani mutum ne, sai dogarai 4 sai magatakarda.
Mancy ta zauna kusa da k'afar daya daga cikin tsofin ta gaishesu, su Aunty Asabe duk a ka gaigaisa.
Gimbiya tace "Mai Martaba, wannan k'awata ce, ta buk'aci ganinka, duk da na san yau ba ranar ganinka bane na nemi a mana alfarma aji da me tazo" cike da izza ya gyada kai".
Daya daga cikin dogarawa yace "Gyara Kintsi, matso gaba ki fadi damuwarki".
Ko dar Mancy bata ji ba ta matsa kusa da Kafar Sarki, wanda gefenshi wani mutumi ne sanye da Babbar Riga.
"Sunana Maryam, wanchan babban da na ne sunanshi Zaid, waccan itace auta ta sunanta Sadiya, wadannan k'annen Mijina ne na da".
Sarki ya gyada kai alamun yana ji "Muna zaman lafiya da Uban yarana, tafiya yayi, yana dawowa ya min Saki Uku, yace kuma dole da yarana zan tafi, ina zani dasu Mai Martaba? Nace mishi da yara kanannene sai na tafi dasu amma ni ba zan tafi da baligai ko ina ba, banda kowa sai Yayana, ina yake so naje dasu? Wannan shekararta 15, wannan shekarunshi 25 masters ma yakeyi, ina zan kaisu? In ya sakeni me zai sa ya koresu, har yana ikirarin ya bude ido ya sake ganinsu zai iya kashesu?".
Sarki yace "Wanene Mijinki? Yana gari? In yana gari a kirawo manshi yanzu, in be gari na bashi kwana biyu yazo ina kiranshi".
Wani bafade yace "Kiran Sarki Doka".
Mancy tace "Yana Gida, Alhaji Ali Zaki".
Mutumin kusa da Sarki yace "Speaker?" Sai a sannan ta kalli mutumin, daga kai tayi tace "eh shine".
Sarki yace "A aika ma Ali Zaki Sammaci, ace ina kiranshi yanzu".
Baba Sani yace "Harda Matarshi wacce itace ummulabaisi, ita ce ta sa ya saketa, muma yanuwanshi ya wulakantamu, sihiri ta mishi"
Sarki yace "A zo da matarshi".
Suna nan zaune jugumjugum magatakarda ya fita da wani zuwa aiken Sarki.
Da Sak'o ya je musu, Shafa'atu taso ya bijire ya k'i zuwa, amma kiran Sarki ba wasa ba, lallashinta yayi ta hanyar nuna mata illan rashin zuwan, rashin zuwan na iya kawo mishi cikas a Siyasar shi, kuma shi Sarki Uban kowa ne.
Da k'yar ta zura wani minnirin mayafi suka bi bayan dogarai bayan tace Hudu ya kula da Annah.
Bayan Zuwansu ne Alhaji Ali kunya duk ta rufeshi ganinshi gaban Sarki, ga kuma Alhaji Ibrahim Iroro, ita uwar gayyan sai da ta ji shakkun Sarki duk da tsagerancinta.
Sarki ya bada umurni, a ka buk'aci Mancy da ta sake fadan abunda ta fada, kamar yanda ta fada dazun haka ta sake fada.
Sarki ya tambayeshi "meye dalilinka na cewa ba zaka rik'e yaranka ba?".
Alhaji Ali ya keta zufa, gaban Shafa'atu na faduwa Allah ya sa kar yace ita ce bata so.
"Allah ya kara ma Imani, wallahi bana kaunar bude idona na zuba kansu, wallahi banson ganinsu, na tsanesu".
Sarki yace "Aiko ba ka isa ba, wani yace ka haifesu? To ba tare da bata lokaci ba, wannan abun mai sauki ne, a Addinance, tunda Yara Baligai ne, kai ke da hakkin daukarsu, da ace yaran k'anana ne sai ta daukesu, amma wadannan yara gurinka zasu zauna Alhaji Ali".
Da sauri yace "donAllah aa, zan bata ko nawa ne na kula dasu, zan dauki nauyinsu, nidai kawai su bar min gidana".
Sarki yace "to ke kinji, yace zai dauki nauyinsu, amma su tafi da ke".
Mancy tace "Aa Allah ya kara maka Imani, Saki Uku ya min, shari'ah ta bashi damar rik'e Baligai, Shari'ah ta hutar dani da gajaniyarsu tunda ba yara kanana ne dani ba, Allah ya ja nisan kwana, in na samu Miji aure zanyi, ya zanyi in be amince da na zauna da Yarana ba? Ya zanyi in yace na zaba ko aurenshi ko yarana? Ya zanyi in ya fasa aurena saboda Ina da Yara Baligai? Ban k'i su dinga zuwa min ziyara ba, Allah ya ja nisan takawa, ban amince ba, hankalina zaifi kwanciya in Yarana na gidan Ubansu".
Sarki ya jinjina kai yace "Alhaji Ali, Yara zasu zauna a gurinka, zaka dauki nauyinsu kamar yanda duk wani Uba zaiyi, cin su, shan su, suturarsu, iliminsu, tarbiyarsu, komai, duka, kayi maganar zaka iya kashesu, zan sanya ido a kanka, in ka karya doka, doka zata taka ka, kasan kai sananne ne, kayi tunanin mai zai faru a rayuwarka ta siyasa in nace zan tona asirinka, Yara naka ne, amma Girma ya bani Iko a kanka da yaranka da duk wani rai da ke cikin garin katsina da kewaye, ina fatar ka fahimceni".
Kan Alhaji Ali a k'asa ya kasa magana, sai da wani dogari ya daka mai tsawa kafin ya amsa baki na rawa "to to rankai dade".
Mancy ta murmusa tace "Allah ya kara ma Girma da daukaka da daraja, nagode kwarai, ka gama min komai, Allah ya ja da rai ya kera lafiya, Ina neman alfarma a bani kudin motar zuwa Kano".
Duk suka bita da ido, Asabe tace "Maryama yo ai baki gama ba, ko kin manta da Shafa'atu ce silar sakinki, ba kiyi maganar cin kashin da ta sa Yaya ya mana ba".
Mancy tace "Yaya Asabe, damuwata sune 'ya'yana tunda na kwatar musu 'yancinsu banda sauran damuwa, kuma Saki dai ya riga da yayi har uku ba kome, sauran kuma nakune, Allah ya sa a dace".
Mamakinta suke gabaki daya, rana daya ta rikide musu, kamar ba Maryama mai hakuri da kawaici ba.
Sarki yace "a bata kudin Mota zuwa Kano" na kusa da shi yace "ai kano din mukayi, ni da su Hajia sai mu sauketa".
Hajiya da kawarta sukace "aiko dai sai muyi ta tafiya".
Sarki yace "to barka".
Mancy ta tako har gaban Zaid da Dalo inda fuskokinsu sunyi ja saboda kuka, ta dago su gabaki daya tace
"Ina Sonku, kar ku taba mantawa"
Dalo na kuka tace "Mancy karki tafi ba dani ba"
Mancy a girgiza kai tace "mun gama magana Sadiya, ki kula da kanki, Allah ya miki Albarka".
Ta rik'e hannun Zaid da yake ta faman murzan idon Hagunshi tace "sai Idon ya kara kankancewa Zaidu? Kabar murzan idon nan, bana so"
Gyada kai yayi alamun to, bubbuga kumatunshi tayi a hankali tace "Stay Strong".
Zan kiraku kunji?. Ta rungumesu sosai kafin tace ku zauna. Umurninta suka bi suna kuka ita kuma ta fita daga Fadar da sauri, Zaid ya dago kannennen idonshi ya bita da kallo har ta bace ma ganinshi.
Abokan tafiya suka tashi suka ma Sarki sallama suka bi bayan Mancy.
Zaid ya runtse idonshi ya kalli Labiba da ta ke ta sharan hawaye yace "ki tafi Marece yayi" karfe 5 da ta duba agogonta.
Majina ta ja tace "Oh Allah, ban san lokaci ya ja haka ba, zan dawo gobe, zan idasa jin labarin kaji Yayana?"
Banza yayi da ita ya dauko sigari ya sa a baki ya kyasya lighter ya fara zuk'a.
Jakarta ta dauka ta bude kofar sai dai me? Gani tayi har an gama Shafe, an gyara passage dinta, duk an gama gyran bulo din, suna ina har aka gyara wurin? Duk suna aikinme basu san a gyara ba, lallai ta shagala da yawa. Kofar ta bude sosai yanda Zaid zai hango Bangon gidan.
Jinjina kai yayi yace "Wow, har an gyara".
"Yanzu ni ta ina zan bi?" Yace "ta Gate mana ko zaki fasa bangon ne ki fita sai a sake gyarawa?".
Tace "muje donAllah ka rakani" "saboda ni na shigo dake?" Ya tambayeta cike da tsageranci.
"DonAllah nace Yayana"
Banza yayi ya kyaleta, ganin tana k'ara bata lokaci ne ya sa ta sakin kofar ta fita tana mai tafiya sadaf sadaf kamar mai shirin Sata.
Gabaki dayansu suna zaune a Bukka, nan suke zaune duk yammaci su sha Fruits, ganin wata sukayi ta wuce sutana tafiya kamar barauniya tana tafiya tana waigen baya, a tare suka mike tsaye.
Hudu ne ya daka mata tsawa yace "Keeee"
Sai da hanjin Labiba suka kada, chak ta tsaya ta kasa juyowa, jikinta sai rawa yake. Duk suka nufota.
"Uwar wacece ke? Daga ina, barin zo in ga fuskarki" cewar Anty Shafa'atu.
Labiba a tsorace ta fara juyowa taji muryanshi na cewa;
"Beebs, donot turn".
Fasa juyowan tayi ta tsaya tana mai kallon gate, su kuma hudun suka juya suna kallon DanMakahon dake nufosu sauri-sauri gudu-gudu".
Yana zuwa daidai Labiba ya finciko hannunta ya yi gaba ita ko ta bishi a baya hannunsu rike da juna.
Muryan Aunty Shafa'atu sukaji tana cewa "Yau Mun Shiga Uku Alhaji, Karuwa har cikin Gida".
Hello Lovers, Vote and Comment line by line please.
#1love
#DM
#FWASonSo
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: BABI NA GOMA1⃣0⃣
Kalmar Karuwa shine sanadiyar tsayawarta cak, duk wani lakka na jikinta ji tayi kamar an zaresu, a lokaci daya kuma jikinta ya fara rawa.
Baki na rawa tace
"ka tsaya, ni ba karuwa bace, wallahi ni ba ita bace"
K'ara damk'e hannunta yayi ya jata har sai da suka yi daf da fita Gidan.
Muryar Alhaji Zaki sukaji na cewa "Shege, Tsinanne, karuwa kake kawo man Gida ko? Kanwartaka bata isheka ba? Sai ka kawo na waje Gida?".
"Ya Rabb" ta furta da k'arfi, be sake hannunta ba ya cigaba da janta, togewa tayi, ta k'i gaba ta k'i baya, gabanta ya tsaya, ya rik'o kafadunta da duka hanayenshi,
Kai ya girgiza mata, da dan karfi tace
"Tsine maka fa yakeyi, Shegantaka yakeyi, ko baka ki bane? mu koma in mishi bayani, mu koma na gaya mishi ni ba karuwa bace".
Hannunta ya rik'e ya cigaba da janta har suka fita daga gidan baki daya, ko da suka fita Gate be sakar mata hannu ba, haushinshi taji karo na farko a rayuwarta, da kyar ta samu ta fincike hannunta daga nashi.
Ta waiga ta kalli Unguwarsu da ke busy asaboda marece yayi, ta sa hannu ta shafi goshinta ta da ya danyi zufa.
"Baba ba karuwa bace, abunda ya kamata kace kenan, amma ka kasa, har sai yaushe zaka cigaba da karban laifin da ba naka ba? Shiru na nufin fa ka amince da kayi abunda ba kayi ba".
Hannu ya sa ya murji idonshi "Ba zaki gane ba, yin maganata bata da wani amfani".
Ta katseshi ta hanyar cewa "sai kayi, kayi magana ko bata da amfani, yafi ace ka yarda da abunda bakayi ba, maganarka yafi ace ka na neman k'anwarka da lalata, ya fi ace kana kawo karuwa Gidanku".
Gashin kanshi ya dan shafa kafin ya murje idanun duka biyu, sannan ya koma kallonta yana karantarta, ya fada a ranshi "ta na da gardama kuma bata ganewa".
A fili yace "nayi rantsuwa na daina cewa banyi abu ba, duk wani abu da zai fito daga bakinsu, hakan ne, banda k'arfin jayayya, yau ko kisa sukace nayi, kawai hakan ne, they are right".
Takaici ya sa Labiba yin gaba, da sauri bata ma da abunda zata ce mishi, tafiyarta kawai tayi, don tana ganin Zaid be ma da hankali.
Bin bayanta yayi yana kwala sunan "Beebs" amma tayi burus dashi, ta ci sa'ar samun Keke Napep ta hau ta fadi sunan Anguwarsu Aunty Asee.
Tsayawa yayi ya bi Keke Napep din da ido, ya juya ya kalli Gidansu, kurum yaji Garin Katsina ya mai zafi duk da ni'imtaccen iskar da ke bosowa, garin da alamun hadari.
Ya buga tsaki da ya ciro sigari ya kyasta ya koma Gida, suna nan tsaye kamar yanda ya barsu, maganganu suke wanda yake da tabbacin La'antarshi sukeyi, straight hanyar BQ yayi, yana jin Baba na faman kwala mai kira amma yayi burus da shi ya wuce dakinshi.
Yana shiga Daki ya sa mukulli ya rufe ya fada kan Gado yana mai tunanin Labiba.
Labiba ma da tunanin Zaidu ta isa Gidansu Aunty Aseey, jikinta duk a mace,ta shiga Gidan da Sallama su Ameera su ka taso don yi mata oyoyo, da yak'e ta taryesu, ta karasa ciki ta gaida Hajiar Aunty Aseey da 'yan Gidan.
Aunty Aseey tace "Labiba ya makaranta?" Dan jim tayi, yau ko hanyar Makaranta bata bi ba,amma sai tayi karya tace "Alhamdulilah"
Hajiyar su Aunty Aseey tace "ya mukaji da wannan abu? Bango ya Fadi" Labiba tace "eh wallahi Mama, an ma gyara".
Aunty Aseey tace "Kin biya Gidan ne?" Da sauri tace "Aa, nasan dai angama saboda marece yayi, yaya kuwa yace aikin be da wuya".
Aunty Aseey tace "haka ne, tashi ki ci Abinci".
Mik'ewa Labiba tayi tana mai jin haushin kanta, wai itace yau da k'arya har so 2, Allah ka yafe min".
Gab da Maghrib suka koma Gida a Keke Napep, sun tarar da an gama gyaran Bangon, Labiba ta share tsakar Gidan ta shiga kitchen don daura musu taliya, bayan sunyi Sallahr Maghrib, suka ci Abincin, gabaki dayan su suke zaune kan tabarma kasancewar ba Wuta.
Hadari ya taso, iska mai karfi ya taso, da sauri suka nade shimfidarsu, suka shige dakunansu.
Baban Amira yace "Oh Allah ka ci da ginin bangon nan kar ya rushe" Anty Aseeyah tace "ai sai yanda ta yiwuwu dai kawai"
Jugum-jugum suka zauna suna sauraron ruwan Sama, sai ga ruwa kam da bakin kwarya, suna jin ginin ya sake faduwa wurin da aka gyara, ta window sukayi ta lek'e suna jimami.
K'arfe har k'arfe 10 saura ruwa bai tsaya ba, duk sunyi bacci banda Labiba da ke daki tana waya da AbuSideeq inda yake tambayanta dalilin rashin zuwanta makaranta.
Karya tayi Kamar yanda ta gaya ma Aisha da sukayi waya dazun haka ta gaya mishi, bata lafiya. Sannu ya mata ya mata sallama da fatan samun sauk'i.
Ruwan saman nan na kawo ma duk wani bawa mai rai nutsuwa, saboda yanda yake sauka cikin wani yanayi mai sa Nishadi. Jugum tayi zaune tana latsar wayarta kadan ne babu cikin karfe 10.
Me ya keyi? Bacci? Ya koyi Sallahn Isha'i? Ko ma ya ci abinci? Ko ya suka k'are dazun da Babanshi? "Ya Rabb" ta fada da ta tuna yanda sukayi dazun, shaf ta manta da wani fushin da tayi dashi.
Haka kurum Zuciyarta ke k'yank'yasa mata Zaid cikin daren nan, Son ganinshi take son yi, son sanin halin da yake ciki takeyi, kawai tana son ganinshi da daren nan, har ya kai ga ta na ji kamar ba zata iya bacci ba in har bata saka shi a Idanuwanta ba.
Juyi ta koma yi kan Katifarta, da duk numfashin da ke sauka daga kirjinta tana mai hasassho halin da Zaid yake ciki a wannan Dak'ikan.
Wuf ta tashi kamar an tsikareta, ta yanke hukuncin da bata san ko ya kamata tayi abunda take shirin yi ba.
Dakin DANMAKAHO zata.
Hijabinta ta dauko ta daura kan Rigar baccinta ta fita sadaf sadaf tayi hanyar bangon da zai sadata da Gidansu DanMakaho kamar barauniya. Chogewa tayi ta tsaya kuma tana wani tunani.
Bai ka mata ba ko kadan ace taje Dakinshi a wannan daren, ba ta san halin da yake ciki ba, ba ta san mai zai mata ba, it is wrong, so wrong, daya daga cikin zuciyarta na cewa "Dont Labiba, Dont". Dayar ko Ingizata takeyi.
Zai rantse be taba jin wannan yanayin ba, zai rantse bai taba zama yayi tunanin wata haka ba, tunanin wata bai taba lik'ewa a k'wak'walshi ba, tun dazun ya ke tunaninta, yanda ranta ya baci ne ya dameshi, duk abubuwan da yake gaya mata ko yake yi mata bata taba fushi dashi ba, ba ya so ya chanzata, ba ya son ya k'ure hakurinta, tunda har ta shiga rayuwarshi, gobe InshaAllah zai bata hakuri.
Ji yayi kamar ana taba k'ofarshi, duk da bai sanya sakata ba amma kofar datse take,ba wanda ya damu da dakinshi, wa zai zo yanzu? ko dai iskan ruwan da akeyi ne yake hurowa? To ai Kofar datse take, kuma kofar irin ta manyan wood din nan ne, iska ba zata budeshi ba, da sauri ya tashi ya bude k'ofar.
A kallo na farko ya zata Dalo ce, sai da ya kalleta sosai ya gano Labiba ce, a cikin sakwan kadan ya finciko hannunta ya jawota cikin dakin ya rufe kofar kamar mai tsoron kar wani ya gansu.
Hannu ya sa ya murji idonshi, tana tsaye tana farfar da ido tana rawan sanyi, Hijab dinta duk ya jik'e.
"Bibbs ba kya jin magana meyasa ba kya ji? Me kika zo yi nan?".
Murmushi tayi tace "Bango ya sake faduwa".
Ba wannan yake sonji ba "how could you be so reckless? Don me zaki dinga zuwa min daki? Ba kya tsorona? Ba kya tsoron ina iya danneki cikin daren nan? Baki ga tsinuwan mahaifi a kaina ba? Ba ki san mutuncin mutum na zubewa ba idan aka ganshi da ni ba? Ba ki san dazun da sun ganki ba sai sun bata miki suna ba? Don me zaki dinga zuwa inda nake? Da daddare, wai ke baki san ni Namiji bane of 28years? Baki san me ke faruwa ba in Namiji da Mace suka kebe? Are you not worried about yourself? About your Family? About Mami? Kin manta Gidanku baa karatun boko amma mahaifinki ya yarda ya turo ki karatu saboda ya yarda dake? Ya yarda zaki kama mutuncin kanki, ki kare martaban gidanku, amma zuwa dakin Namiji mutunci ne? In yayanki ya kamaki ya zaiji?".
Kyafta idanuwa tayi, tace "Ya Zaid, na yarda dakai, ba zaka cutar dani ba" ba tare da ya tanka YaZaid din da ta kirashi dashi ba yace "baki sani ba Bibbs, baki san ko zan iya cutar dake ba ko ba zan iya ba, World fa nake sha...Uhm Wiwi".
"Dagaske na san ba zaka cutar dani ba, ba zaka min abunda zakaji haushi ba in anyi ma Dalo". DanMakaho ya tsura mata ido kafin yace "DonAllah DonAnnabi me kike so, its late, ki koma Gida, gobe zamuyi magana".
Kai ta girgiza tare da zama kan kujerar dakin tace "ni bana jin bacci, ba kuma abinda zanyi, so yafi ka idasa bani labarin".
Idonshi ya murza sosai kafin ya zauna yana harararta, ita ko sai murmushi take sakar mai.
Sarki ya mana Nasiha kuma yace in muna da wata damuwa da Babanmu ko Matarshi muzo mu gaya mai, sarki ya sallame mu.
Baba da Aunty Shafa suka fita daga fada ransu a bace, Baba Sani ya dauke mu ya maidamu Gida nida Dalo bayan ya mana nasiha sosai ya bamu hakuri.
Daga wannan rana komai ya chanza mana Beebs. Da muka Shiga Gida mun tarar da Baba, Aunty Shafa, Hudu da Annah zaune a Parlo, jikinmu yayi sanyi yanda mukaga suna kallonmu, jan hannun Dalo nayi zan sadata da Dakinta amma na jiyo Ihun Baba.
Danubanku kuzo nan. Beebs, bamu saba ba, Babanmu baya zaginmu,Babanmu ba ya daga mana murya, k'ara matse hannunta nayi muka shiga Parlon sosai.
A gefe muka dan rakube, ran Baba bace yace "yanzu ni Maryama ta tona ma asiri ko DanMakaho? Kuna ganin uwarku ta kaini k'ara Gidan Sarki, bayan duk abubuwan da na mata, duk hallacin da na mata ta rasa da me zata saka man sai ta kaini Kara a Fadar Sarki? Ni Alhaji Ali Zaki?".
Mu dai ba muce komai ba Baba ya cigaba da cewa "to tunda Maita ta hanaku bin Uwarku, ku zauna, amma ba ruwanka Zaid da cikin Gidana, Boysquarter zaka koma, ban yarda da kai ba, ina da Diya Mace, kar kazo ka keta mata haddi, wani irin yammmm naji a jikina, na dago kai na kalli Babana, wanda banda tabbacin ko shine ko ba shi bane,anya Baba na ne Mahaifi? Me ji dani? Me yin duk wani abunda nakeso?".
Ya cigaba "Ke Sadiya, Annah tace dakinki take so, so ki koma BQ tare da Yayanki, ko ki koma gunsu Raliya masu dafa Abinci". Dalo ta dago baki zatayi magana sai kawai ta fashe da kuka.
Ni ko na fara girgiza kai alamun rashin yarda nace Baba ta ya Dalo zata koma Boysquaters? Dakuna nawane a cikin Gidan nan da har sai ta koma BQ? Haba Baba kar ka juya mana baya".
Hayyayakowa yayi "DanUbanka DanMakaho ina fada kana fada? Rashin da'a zaka min? Danubanka nace ba ku zama min cikin Gida, ku koma BQ, bana son ganinku, ina laifi ma da na barku a BQ din".
Zaid ya tashi inda yake rak'ube yace "Baba, wallahi ba zata yi zaman BQ ba, in ka matsa yanzu sai naje Gidan Sarki na gaya mishi "
Baba ya tunzura, danubanka ni zaka tona ma Asiri? Kaje ka gaya mishi to, tsinanne watsattse, da sauri na tashi hankalina a tashe ban ma ganin gabana na dinga jefa kafata kasa na fita daga Parlon.
Aunty Shafa tace "barshi Alhaji, kaga dai abunda Sarki yace, kar a kama mu da saba ma Umurnin sarki, Baba ya amince, Anty Shafa tace ke Sadiya ki koma dakin kusa da naki, naki Annah ke so, Sadiya bata da rigima duk da ta san Dakin da ake so ta zauna ba komai ciki daga Gado sai toilet amma na ta har Tv akwai bayan decoration din dakin da akayi da pink and purple color. Kai ta gyada alamun ta amince, Anty Shafa ta koreta cewar zasuyi magana ta zauna musu, sumsum ta mik'e ta wuce dakin da aka ce ta koma.
Ni kinsan abun bai dameni ba zaman boysquaters don na san in 2days zan koma makaranta so Dalo ma ne nake jiye ma zaman bakincikin da zatayi.
Duk ranar wayar Mancy a kashe yake, na kirata yafi so dari naji ya take, me take ciki, karamin hauka na kusa yi. A waje na zauna bayan Sallahr Maghrib, ga yunwa ina ji bana ma son shiga Gida balle naga kayan bacin rai, kawai na wuce gunsu Raliya masu dafa Abincin Unguwa, aiko na samu Jollof din Shinkafa a wurinta, ta na tausata da bani baki kan mu jure duk wani abun da zamu gani daga yanzu.
Washegari da safe na tashi na tafi cikin Gida don ganin yanda Dalo ta tashi, kallo daya na mata na lura da tsantsar ramar da tayi na kwana daya, tausayinta ya kamani, na karasa gunta ta dago da murmushi mai kama da yak'e.
"Ya Zaid, har yanzu ba ka samu Mancy din ba? Wayarta a kashe" ta fada cike da karaya, ka sa amsata nayi, na durkusa daidai tsawonta nace "ba kiyi breakfast ba, tashi mu shiga kitchen na hada mana kalaci".
A Gidanmu kowa ke hada breakfast dinshi da kanshi, saboda rarrabuwan raayi, in kuma k'osai da koko din Raliya kake son ci sai kaje baya kaci.
Na rik'o hannunta muka shiga Kitchen, muka kalli juna cike da mamaki, ba wai ba komai cikin kitchen din ba, aa sai ganin babu abubuwa da yawa, trolley din kayan tea, ba komai, ba kwai ba komai cikin fridge dana duba, yanda na lura duk wani abunda zaa sarrafa a sa a baki babu, da mamaki muka kalli juna, yaushe akayi wannan kayekayen? Dalo tace "maybe suna a Store" da sauri na karasa store na jishi a gark'ame.
Da karfi na kwada ma Raliya kira, sai ko gata nan da saurinta, tnace wai ina kayan Abincin gidan nan? Ta duba kitchen din da idonta tace "toufa, kamar an kwashe komai, na jinjina kai na san aikin matar chan ce, nace Raliya Yunwa mukeji, tace ai DanMakaho akwai Kalaci a kitchen din baya, bari na kawo muku. Parlo muka zauna muka jira Raliya ta kawo mana Breakfast.
Dadi kosai da koko dinta, sosai mukaci don jiya rabonmu da abinci tun rana. Muna cikin breakfast sai ga Aunty Shafa'atu ta shigo da nightgown jikinta. Da mamaki ta kallemu tace "ina kuka samu Abincin nan?" Daga kai nayi na kalleta nace "meye amfanin kwashe kayan abincin kitchen da kikayi? So kikayi kiyi starving dinmu da yunwa? Ko so kikayi ulcer ma ta kama mu? A gidan ubanmu? To ba zai yiwu ba, wallahi baki isa ki horar damu yunwa ba a Gidan Ubanmu".
Fuuu ta wuce ta banka dakin da Baba ke ciki, ko bacci yake ko zaune yake oho, amma da karfi naji tana cewa "ni yanzu a sallami su Raliya masu Abincin Gandu". Baba yayi dan jim kafin yace"Shafata, Abinci sukeyi wanda ake rabama yan Unguwa, da yawa da nan gidan sukayi relying, in aka Sallamesu wa zai dafa Abinci har a ba Makwafta? Kicinkicin tayi da fuskarta tace "nidai Alhajina kana shagwaba talakawa, in ka dinga basu abinci kullum ta ina zasu samu zuciyan neman na kansu? Zuciyarsu bushe take, su a ganinsu sun samu bati ni dai kawai ka sallame su Raliya, daga yau an gama Abincin Badawa".
Da sauri Baba yace "kuma fa? Hakane mutane son banza garesu, daga yau ba zaa k'ara Abincin badawa ba, ko wani shege ya tashi ya nemi na kanshi, ai maza a kira man su Raliyan".
Well ina gaya miki Beebs, baba ya ma su Raliya da masu taimaka mata wurin dafa Abinci, Sallaman Wulakanci Aunty Shafa na tunzurashi kamar wani robot take control dinshi, ni kuma da na ga haka, nace su jirani naje Bank, da sauri na dauki Motata na nufi Bank, na zaro dubu 200 na basu nace su ja jari, godia suka dinga min kamar zasu min sujadda, suka dinga min addua suna mana fatan Allah ya karemu daga sharrin Matar Uba, Raliya da yake zata girma Mancy, ta dinga min Nasiha da kuma na kula da Kanwata, suka min Sallama suka kwashe kayayyakinsu.
Ashe Hudu ya ga lokacin da na mik'a ma Raliya Kudi, ashe ya je ya barar ma Yayarshi, yayarshi ta tada ma Baba rigima da haka yake barina ina kashe kudi? Be san kudi na bata yaro ba? Ita gaskia ba zata yarda ba?.
Hahaha Labiba Babana ya kira Manager ya sashi freezing account dina, bayan ya kwace makulan Motanshi, da wayar hannuna a cewarshi da kudinshi na siya, God, to ban ma dai yi mamaki ba sai da bayan kwana biyu na samu Baba game da son komawa Makaranta.
Nan ne Baba ya min Wulakanci gaban Matarshi da Diyarta da k'anenta.
Da farko banza yayi dani ya k'yale sai da na sake magana nace "Baba lokacin da ya kamata na koma Makaranta yayi, jarabawa zaa fara da sati 2, zan koma na fara shiri".
Baba ya dan kallo Anty Shafa, da ido ta mishi magana, haba sai baba ya fara Spark, wani irin Makaranta, Kai dan iska ina sane da duk wata burobar da kake a k'asar Ingila ba, Shekarar 6 a chan amma ka kasa hado degree, sai dai kaje ka shek'e ayarka da yanmata, ka dawo Nigeria ka kuma koma London san da kaga dama, to ba zaiyiwu ba wallahi, ba zai taba yiwuwa ba".
Nan ne ya kasheni da Mamaki, baki na nauyi nace "Baba, wani Degree kake magana? Ina Degree din da na amsa ranar da kukaje London kai da Mancy da Dalo? Baba har fa Graduation Dinner sai da kukaje, ko kuma ka manta na riga da nayi joining Masters, befi min Wata daya nagama ba? Yanzu da na koma nayi Exams fa na gama".
Baba ya dinga zare ido "kai ni ban san wannan ba, ni sisi na ba zan k'ara kashewa a kanka ba DanMakaho" hankalina ya tashi amma na daure nace "kayi hakuri babana, ka bude min account dina, akwai kudi na, ni zan dauki nauyin kaina, i need to go back Baba".
Tsawa ya daka min yace "Bazan ba, nace bazan ba, na cire kudadden Account dinka tas, London kuma ba zaka kara zuwa ba". Guiwowina na dire a kasa ina kuka "Baba ka min rai donAllah, kar ka hanani komawa, Baba in wannan shine abu na karshe da zaka min a duniya donAllah ka maidani London, don Girman Allah baba".
Kafa ya sa ya shure ni sai da na k'ume, a kausashe yace "bazan kai ka ba, naira daya ta gama kuka a kanku".
Shafa'atu tace "kaima Alhaji ka rabu dashi, tunda shi ya fi so a yi ta magana daya".
Raina ya baci ban san sanda nayi wani kukan kura ba na chakumo wuyanta, na mak'ureta kamar zan kasheta, Hudu da Baba suka yo kaina, suka rufe ni da duka amma ko gezau banyi ba, na cigaba da matse hannuna a wuyanta ita ko sai k'akarin mutuwa take.
Dalo ta fito daga daki da gudu da ta ga hayaniya tayi yawa, ni ko wani karfi ya zo min na ingiza Baba da Hudu, na hau dukkan Aunty Shafa'atu, Dalo na kuka tana Yaya donAllah ka rabu da ita, ina sam ban ji ta ba, ita ko a galabaice take kukan wahala, Hudu ya rikoni ta baya, Baba ya dunkula hannunshi ya dinga kai min naushi ko ta ina kamar zararre, itama Aunty Shafar ta mik'e ta nufoni tana dukana Dalo ta rike mata hannu ta wurgar da ita.
Kamar daga Sama mukaji ana Sallami, muryar tsohuwa ce ke cewa "Ki kori Mahaifiyarsu ki juya kan ubansu yanzu ku mishi rubdugu? To wallahi baki isa ba, sai na ci uwarki, yau sai na ga Bokanki, daga nan har Pilatu sai na ga Uban da ya tsaya miki a Najeria".
Dalo ta dago kai ta kalli Tsohuwar da ta ke niyar cin danmara, a wahalce tace ;
NENE..
Ai Nene ba ta bi kan dalo ba ta shiga cikin fadar nan ta finciko Shafaatu ta kaita k'asa, ta dinga kilarta kamar Allah ya aikota, Baba yazo shiga tsakani ta sa hannu ta tsokale mishi ido, ganin haka na maida hankalina kan Hudu, ni da Nene muka kaisu k'asa ina kilar kani Nene na kilar Yayar, baba hankali tashe ya wawuro wayarshi ya latso kiran Police Station.
Wai tsohuwa Nenen nan sai da ta ma Shafa habo kafin ta tureta, ta rik'o hannuna da na Dalo tayi gaba, tana maida numfashi, tana haki tana cewa "ni ai ko bokon Saude sai da ya tantance Aminene Mamman, zaki zo ki shiga tsakanin da Da Mahaifi, shegia K'abilar banza".
Muna jin Aunty Shafa'atu na cewa "wacece wannan Alhaji?" Kafin Baba ya bata amsa Nene tayi karaf tace "Uwarki ce, kaii a'a ni ban haifi Azzaluma ba, Sunana Aminene Mamman kije kiyi tambaya kaina".
A tsakar Gida muka tsaya ta kalleni rai bace tace "kai danubanka sai kayi tsaye suyi maka taron dangi?" Ta kalli Dalo tace "ke kuma sakara kin tsaya kin bare baki kamar famfo kina ta kuka ana dukan Yayanki, baki dauko wuka ki watsa taron?"
Baki bude nake kallonta na san Matar kamar zararra take amma me take nufi? Nace Nene fa harda Baba fa, kai dallah arr, ni sai na bugeshi tunda ni ba ubana bane, sai na mushi mugun bugu tunda shi sakarai ne shanyayye".
Kai ni ina Gida Raliya ta kawo min zance abunda ya faru, to wai danuban Maryaama tana da wadda ta fini ne duk garin Katsina, ashe cin kashin da Ali ya mata kenan? Bayan ya wulakantata harda bugu? Ni ina me baa zo an sanar dani ba? Wato ni hoto ce, banda wata amfani".
Zaid ya dafe kai, matar nan tana son saka mishi pressure da yamman nan, ni yanzu kiyi hakuri Nene, wallahi ban ma cikin hayyacina cikin yan kwanankin nan".
Kai dallah ar raggon maza, ba ka biyo masu Sunan ba, Zaidu Bawan Allah jarumi ne".
Labiba ta share hawayenta amma yanzu murmushi na dauke a fuskarta tace "Wacece wannan? Kakarku ce?".
DanMakaho ya murmusa shima yace "Ba dangin Iya bara ne Uba, wai kawar Mancy ce, amma fa tsohuwa ce kuma a haife ta haifi Mancy".
Labiba da mamaki tace "Kawa kuma?"
Yace "Eh kinsan Mancy na yawan zuwa Hajj da Umrah, to a chan suka hadu, dakinsu daya a cewarta Mancy ta taimaketa sosai da hidima a Makka shiyasa suke kawance, to tunda suka dawo suke zumunci ko muje ko tazo, tsohuwa ce amma bata da hakuri, karfinta kamar na garada Goma". Sosai Labiba ke daria.
Ya cigaba
Kafin wani yayi magana sai jin siren din Motan yansanda mukayi. Baba ya fito Shafa'atu na biye dashi a baya, ke wai Baba ya shigo da YanSandan nan yace a tafi damu a rufe mu bayan karta harda Nenen.
Nene kuwa tayi kukan kura tace "duk uban da ya tabani sai naci kutumar ubanshi, yara ba ku sanni ba" ta zaro wayarta a purse ta mik'o min tace "latso min Zaidu Bawan Allah, kai ba ma shi zaka kira ba, latso min Habibu Lema, in na tuna da kyau harda shi yayi silarka ka zama abin da ka zama a yau".
"Yo ku kadai kuka san manya? Nima dana Habibu ai suke da gwamnati, kuma shi ba tsaranka bane, kai soko maza kira man shi" ko mai Baba yayi tuna oho sai cewa yayi "ku bar tsohuwan, ku tafi dashi ku kulle, ku lallasa min shi".
Haka yan Sandan nan suka kamani kamar barawo, Dalo ta fashe da kuka.
Nene tace "oho, nidai ba uban da ya isa ya kulleni, shi da ka isa dashi ka sa su tafi dashi, ke kuma ki ma mutane shiru komai kuka, kai kuma Danka ne, ka barshi a chan bayan karta kar Allah ya sa ka firdoshi, ka barshi chan ya mutu Sakarai shanyayye, ke kuma a juri zuwa rafi".
Ta fizgo wayarta daga hannuna ta wuce fuuu kamar zata tashi sama.
Ba su jira wata ba suka tusa k'eyata suka sakani a bayan motarsu suka tafi dani, hankalina tashe, yau nine haka a wulakance, ba wani wata wata a ka wurgani bayan karta.
Wani zauri ya bugi hancina, ga k'uda, ga k'azanta daga wani bangare, hawayen bakinciki suka soma kwaranyo min, yau ni ni ne a Cell? Yau ni ne a wulakance, meyasa na ma dawo hutu? Meyasa nake da rabon ganin wanan rana? Kuka nake sosai ban damu da kallon da yan bayan kartan ke bina dashi ba, ban damu ba.
A sannu na yi ta hasasso rayuwarmu a da, da rayuwarmu a yanzu, komai ya chanza Alkalamin k'addararmu tayi zanen da ba zata kankaru ba, sosai nake kuka, na dade kuma ina kukan, bansan minti ko awan da dauka ba ina kuka.
"DanMakaho" naji an fada
Da sauri na dago kai don ganin me min kiran nan wanda tabbas ya sanni tunda ya kirani da sunan da yan Unguwa kadai ke ce min.
Na sanshi, ina ganinshi a Unguwa, Dan shaye-shayene, ya sha rokona kudin da zai ci abinci duk da na san karya ne shaye-shaye zaiyi dadu ban taba hanashi ba, da shi da yan bencin Eskaley na sha raba musu naira dubu dubu.
Da kyar na ambaci sunashi "Haruna, me kakeyi a nan?" Haruna ya danyi daria yace ai ni nan bana sati 2 k'warara banzo nan ba, kai ne dai zan tambaya me kake anan. Ban iya ce mishi komai ba na duk'ar da kaina.
Gaskia DanMakaho Babanku ya kwafsa, ji yanda ake ganin mutuncinshi amma wa shine zai yi wannan kwafsin? Harda dukan Hajia Mancy gaban kowa, Kai ya mugun kwafsawa.
Kamar jira nake na fashe da wani sabon kukan, be lallasheni ba, bai hanani ba, bai kuma tafi ya barni ba".
Sai da na tsagaita kuka na kafin na dago kai na ga hannunshi a mik'e alamun wani abu yake so na karba daga hannun.
World kenan, ka sha shi, wallahi ka sha shi damuwar da kake ciki zai bace bat, ka dan ta6a world ba ka da wata matsala.
Kallo daya na ma kullin garin na kauda kai. Zama yayi kusa dani
Kagane ko ka sha taimaka min, ka sha fiddo ni cikin damuwa da yanayi, in ka bani kudi, kaga abunda nake siya nan, dagaske in na sha shi wallahi bana da wata sauran damuwa, wallahi World duniya ne, duk yanda kake cikin damuwa, bakinciki, kuncin rayuwa, da ka zuk'a so daya damuwar zata kwaranye, zuk'a ta biyu kuma zakaji kanka a kan gajimare, ka gwada zuk'a daya, da kanka zaka nemi k'ari, in kuma ka zuk'a damuwarka bata gushe ba kayi kan duk abunda kake so".
Runtse Ido na nayi, na yarda gajeran tunani gareni, shaidan ya buga min ganga, a cikin Cell dinnan na zubdar da duk wani tarbiyan da Mancy ta min shekara 25, Wallahi Beebs da na bude World na fara zuk'a ta hanci, sai da na zukeshi tass, Haruna ya so ya kwace amma na hanashi, burina damuwa na ta kau".
Ido na a runtse na ji ni a wani irin yanayin da ban taba shiga ba, wani yanayi mai wuyar fasali, wani yanayin da ban taba saninshi ba. Wanda suka dade a harkar da wuya su ja World fiye da biyar, ni ko na ja shi ya fi so 20, mamaki na Haruna keyi yanda ya ga nayi bagas a k'asa ido na a runtse in rausaya da kaina hagu in rausaya da shi dama.
Haruna na tsoron kar na haukace, don in yayi yawa yana sawa a zare, sunana ya fara kira
DanMakaho
DanMakaho shiru ba amsa ido na runste
A kira na uku ne na bude ido tare da sakin wani irin murmushi.
Cikin jin dadi haruna yayi wani juyi, tare da jinjina hanayenshi guda biyu alamun ya sara min gami da cewa;
MAANNNKAAAASSSSS.......
Yes Guys your one and Only Nene is here
Who's happy?
Vote and comment line by line please
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Sha Daya1⃣1⃣
(MANKAS II)
(Note: wannan Events din ya faru ne Bayan dawowan Nene daga London lokacin da Nasiban Rafeeq ta Haihu. Fahimt?)
A kan idonta a ka wuce dashi cikin motar yan sanda, ranta a bace, sai dai ya ta iya? Fuuu ta shige bayan motar da aka kawota, ko magana bata iya mishi ba ta wuce Gidan Lema.
"Banda Sakarai shanyayye, wa ke tura yaronshi police station?" Haka tayi ta fadi har ta shiga cikin Gidan Lema, Mami ta mata sannu da zuwa, Nene tace "ke yau ni naga k'awar Saude".
Sai da Mami ta dafe k'irji tace "a ina Nene?".
"Wannan Kishiyar Maryaman"
"Nene dagaske an Saki Hajia Maryam?"
"Ke ina baki kina k'in karba, Makira ce Matar nan, wai ke in gaya miki Yaro na samu bakin gate ya bani labarin duk abunda aka ma Maryama, ke fa da naje samu nayi sun ma Takwaran Zaidu Bawan Allah Rubdugu, aiko na shigar mai, na tsokale wa Uban Ido, ita kuma na lallasata".
Mami tace "yanzu Nene fitanki har kinyi Dambe?" Nene tace "aa fa ni fa ba dambe nayi ba, bugun tsiya na mata, ke dallah ina kaiki.
Ke shaida ce irin So din da Alhaji Zaki yake ma Matarshi Maryama da Yaranshi, kina zuwa Gidan Kema, kinga kyakyawar Alak'a tsakaninsu, ke kawai sai rana daya, ya auri tsohuwar Matarshi, ya zabure ya ma Matarshi duka gaban 'yan anguwa, ya cika mata saki 3 ya sa aka kwashe mata kaya, ya zo ya tsani yaranshi, ya shigo da Agola su biyu, ya fifita su fiye da yaran cikinshi, me zakice? Me kike ganin ya faru?"
Mami ta danyi jim kafin tace "ta na iya yiwuwa Chanji ne kawai, ko dokin sabon auren da yayi ne".
Hannu Nene ta sa a kai dauke da takaici tace "ke wai bakiji me nace ba, don yana dokin aure sainya juya ma Yaran cikinsa ba? Ya kike magana ne kamar ba ki san aikin asiri ba, ke da Saude ta rafka muku asiri ke da Mijinki aka rabaku tsawon shekaru?.
Mami tace "kawai banson zargin Asirin ne, tunda bamu da hujjah".
Nene tace "wai ya kike magana? In ba asiri ba meye? Hujja ya wuce wanda na karanto maki, ke wai don uwar yaron nan da ni zai sa a kulle a pirisin?".
Mami ta zaro Ido, tace ya akayi? "Aa wai mun bugar mishi Mata, ya kira YanSanda wai su tafi dani da Zaidu Bawan Allah, nace mishi ya kira min Habibu, da yaga uwar bari, sai cewa yayi a barni amma a tafi da Dan, yanzu dan na chan kulle, ki latso min Mijinki".
Sai ko gasu shigo tare da Uncle Zaid.
Nene ko ta tarbesu "Oyoyo Sannu da zuwanku" Uncle Zaid ya murmusa yace "Nenemu ni da Seebi".
Jawo hannunshi tayi ta zaunar dashi tace "wai Zaidu Bawan Allah, ina kawata Hajia Maryama da ke Tudun Matawalle wanda ka taba kaini Gidanta?" Cikin fahimtarta yace "Matar Speaker Ali Zaki?".
Tafi tayi cikin jin dadi tace "itafa"
Uncle Zaid da neman k'arin bayani yace "me ya sameta?".
Nene tace "to asiri kishiyarta ta ma Mijinta ya saketa saki 3 bayan ya lakada mata na jaki, ya kuma juya ma yaran Baya, kai wai jiya suka kori su Raliya masu abincin da na kai ma Maryama, aiko Raliya tazo ta gaya min duk abunda ke faruwa, ni ko na wanke kafa na sa Sabitu ya kaini Gidan.
Kai wai daga isa na naga sun saka takwaranka Zaidu a tsakiya suba ta jibgarshi, ni ko naci dammarata nayi kansu".
Kai wai sai ga 'yan Sanda sunzo wai tafiya da mu, wai zasu samu bayan Karta, wai mun bigi Matarshi, niko nace wallahi bai isa ba, sai dai a tafi da danshi ba dai ni ba, kuma nace a latso min Habibu ai ba su kadai bane Manya".
Daddyn Rafeeq ya jinjina kai yace "Gaskia da Ali Zaki yayi Babban kuskusre da yayi gigin Kulleki" Nene ta yi darian jin dadi tace "yo shiyasa na bashi tsoro wallahi, shegen ya tsorata, ai gaba da gabanta".
Uncle Zaid ya girgiza kai yace "wai Nenenmu ni da Seebi yanzu dambe kikayi? wai ba ma na hanaki Shiga abunda bai shafeki ba?".
Gimtsa baki tayi tace "yi hakuri Mamman".
Mami tayi daria tace "yau Zaidu Bawan Allahn zaa watse?".
"Yo ai naga Zaidu Bawan Allah ko meye nama Hajia Maryama ban fadi ba, matar da ta soni kamar Uwarta, ke Aisha da muke Makka wani ciwo da nayi, wallahi ita ke hidima dani, duk nisan Samanmu sai ta sauki ta siya min abinci da magani, ta rirrikeni in zan fadi, ni ko gani da raki da fada, yanda kika san diyata haka nake watseta , duk tsarabar da na maku ita ke zabar maku kuma so dayawa ita ke biyan kudin, karamcin Maryama mara misaltuwa ne, to yanzu don na taimaka ma yaranta sai ace nayi shiga sharo ba shanu?".
Duk suka jinjina kai, tace "Alhaji Habibu DonAllah kayi man taimako, kaje polis station ka sa a firdo Takwaran Zaidu Bawan Allah, kuje kuyi belinshi, wallahi dan gata ne, be saba irin rayuwar nan ba".
Daddyn Feeq yace "InshaAllah Nene, bari inyi waya inji yana a wani Police Station ne".
Ba jimawa yace "yana Police Station din Tudun Matawalle, barin je inji". Nene tayi wuf tace "muje". Gardama da ita bata lokacine, fits sukayi su Uku, Nene da Alhaji Habibu da kuma Zaid BawanAllah.
Ko da suka isa Police Station din tuni DPO ya fito ya tarbesu, ba bata Lokaci Alhaji Habib ya buk'aci a saki dan Gidan Alhaji Ali Zaki da aka kawo dazun". Jim DPO yayi kafin yace "anya kuwa Alhaji? Alhaji Zaki yace mu rik'eshi kar mu sake mu ba kowa Bail dinshi, kayi hakuri Sir yaron kangararre ne, Mahaifinshi ke da rights akan shi kuma yace a hukuntashi".
Nan Nene ta fara surfa musu ruwan Bala'i wanda Su Haruna da ke bayan Karta sun ji banda Zaid da ya dade a duniyar da World ta kaishi. Da k'yar Uncle Zaid ya firda Nene daga police station din don da har ta fara maganar dukan DPO.
Daga Station basu wuce ko ina ba sai Gidan Alhaji Zaki, iso aka musu har parlo, tare da hamshak'iyar suka fito, suna ganin Nene Shafaatu ta sha mur, riko hannunta Alhaji Zaki yayi suka karasa cikinParlon, hannu ya ba Zaid da Daddyn Feeq sukayi Musabaha".
Alhaji Habibu yace "Alhaji Ali, Nene ta zo mana da wata magana wai ka sanya an kulle Zaid, munje muyi bailing dinshi sunje ba bail, Alhaji komai yayi zafi maganinshi Allah, kayi hakuri ka firdoshi".
Kallon Hajia Shafa yayi ta banka mishi harara, lokaci daya ya fara bala'i "Haba Alhaji Lema, wai ni ina ruwanku dani da iyalina? Shin Zaid din ba yaro na bane? Ina ruwanku ko yanka shi zanyi? DonAllah ina ganin Girmanka, ka tsaya a nan, ba zan dauki shiga sharo ba shanu ba".
Nene ta katseshi ta hanyar cewa "Kai dallah sakarai rufa ma wa mutane baki, ka na zaune sai juya ka ake kamar Masa, kai Asirin ma sai fa sakarai take ma tasiri, shiyasa da ta kamaka tayi maka mugun kamu, to wallahi ka natsu kayi wa kanka kanka fada".
Ta matsa kusa da Shafa'atu ta sake mata wani zazzafan Rankwashi wanda ya sanyata ihu, a tare Alhaji Zaki da Zaid Lema suka tashi, Zaid yayi kan Nene, Zaid ya janyeta yana "Haba Nene".
"Ni Zaidu wallahi ban san harka da Stupid, nidai a Sako min Amanar da Allah ya bani".
Shafa'atu wanda rankwashin ya shigeta ta fara kuka "wallahi Alhajina sai ka sakeni, ba zan iya ba, ace har Gidana wata tsohuwa zata dinga bina tana duka na? Kamar yar yarinya? Ni wallahi ba zan iya ba".
Hankalin Ali Zaki ya tashi da sauri yace "Alhaji Habib Lema, ba gaya ma ina mugun jin kunyarka, ku fitar min daga Gida, ku fita daga harkan Gidana, wallahi in Mamarka ta sake taba Matata wallahi ba zamu kwashe da kyau ba".
Aiko ya tunsura Nene tace "Allah ya tsine maka in har ka bari muka kwashe da kyau, Shege, mara hankali".
Zaid ya ja hannunta tayi ta fizgewa, da k'yar ya iya fitar da Nene daga Parlon, ga Nene da karfi.
"Alhaji Habib Lema, ka ja mata kunne, ta fita daga harkan Gidana, ko kuma hukuma ta shiga tsakaninmu, ai mata Iyaka da Gidana".
Daddyn Feeq be iya magana ba sai dai fitan da yayi a zucciye.
A Mota yace "Don Girman Allah Nene ki fita daga harkan Gidan Zaki, Nene ta ya zan iya dauka in wani ya miki rashin kunya, Nene ki sa mishi ido, duk daren dadewa gaskia zata bayyana, Dan shi ne, chan cikin ranshi akwai sonshi a cikin shi, donAllah kar ki sake zuwa Gidan".
Zaid ma ya shiga lallashinta da tausassun lafazi, yana cewa ta bisu da addua, Allah ne zai kare ma Maryama Yaranta.
Takaici ya hana Nene cewa komai sai Girgiza k'afar da takeyi tana tunanin yanda zata shigo Gidan Alhaji Zaki karfe ukun dare ta ci ubansu daga shi har Matar.
***
Kwana na 2 a Cell, banda wata damuwa, saboda me? Saboda World, sosai yake batar min da duk wata damuwata. Baba bai zo ba, bai kuma ce a sakeni ba, so ba ranar fita daga wannan wurin.
A kwana na ukun ne Ina zaune kawai naga wani kurtu ya lek'o yace "kai Dan Gidan Zaki fito" mamaki ya cikani, to Baba ya hakura kenan, ya sa an firdoni, tashi nayi na fita sai ganin Dogarawa fiye da uku tsaye da dorinarsu.
Dogarawan nan suka tisa k'eyata bayan sun sanar dani cewa mai Martaba Sarkin Katsina ke nema na. Motar Emirates muka Shiga Har Fadar Sarki dake K'ofar Soro, wani dogaribya fara shiga bayan Mintuna Goma sai gashi ya dawo yace mu shiga.
Ina Shiga Fadar gabana ya fadi, ganin Dalo durk'use gaban Fada, daga gefe kuma Baba ne da Aunty Shafa, sai Hudu da Annah, sai wata da ke Durk'ushe tana ta bayani ta bawa Fada baya".
Muryarta kawai ya ankarar dani ko wacece.
"Nene ce".
Kwakwalwata ta fahimci cewa Nene ce dai ta kawo Baba k'ara.
****
Tun bayan dawowar su Nene daga Gidan Zaki ta rasa sukuni, bata da wani madafa ga shi Zaidu kamar yayi kuka wurin rokonta a kan kar ta sake zuwa Gidan Alhaji Zaki. Bata san ya zatayi ba har kwana 2 suka shide bata da wani dabara, duk tayi sukuku, bari ta kira Seebinta ko zataji sanyi.
Zuwa yanzu Nene ta iya kiran Mutanen London a waya da taimakon hotunan su wanda Zaidu Bawan Allah ya sa a jikin ko wani Contact, Hoton Seebi ta lalubo cikin contacts din ta danna kira don tana da kudi fiye da Dubu 10 cikin wayar duk don kiran Mutanen London wanda Zaidu BawanAllah ne ke sawa".
"Hellooo Neh-Neh" taji muryarshi
Da sauri tace "Dunkum. Kai na kira?" Ta na mai dauke wayan daga kunnenta tana sake duba screen din don ganin wa ta kira kuma dai hoton Nasibar ne.
Mur ta sha kamar yana gabanta tace "kai dallah ba mai wayar wayarta". Dan daria yayi yace "Neh-Neh kinyi missing dina ne? Baki nemeni kwana biyu ba".
Yau bata da lokacinshi cewa tayi "kai Arr, ina Nasibar?" Dan daria ya sakeyi yace "Sunje wani Birthday Party ita da Yarona".
Tsaki Nene tayi tace "Wani yace ba yaronka bane? Rasa kunya beran kitchen, kace ta kirani in ta dawo".
"Wai ya Neh-Neh yau sai gwasuleni akeyi? Wai ba mun shirya ba? Ai mun bar fada ko? Ko yau kin tuna kanki a Airport ne wurin masu Red din Kunne" ya karashe yana daria.
"Wallahi Dunkum ubanka zanci"
Guntun tsaki yayi yace "kinga Matsalarki ko Zagi? Wai ba Uncle Zaidu ya hanaki Zagi ba? Barin kirashi in gaya mai".
Da sauri ta katseshi "kai dallah tsaya kaji, ka tuna Hajia Maryama Mamarsu Takwaran Zaidu BawanAllah da Dalo?".
Rafeeq yace "Eh na tuna kawarki da kike bamu labarinta, me miki Wanki a Makka".
Cike da jin dadi tace "Good, good Dunkum, to wallahi Mijinta ya mata Saki Uku, ya mata dukkan tsiya gaban Mutane" nan ta shiga bashi labari kamar a gabanta akayi, har zuwa zuwanta na farko da dukan da ta ma shafa, da kulle Danmakaho da akayi da zuwan su karban bailing dinshi".
Ran Rafeeq ya baci, wai yaushe mutane zasu bar zama Victim din Matar Uba? Karon shi da Saude ya tuno, abubuwan da tayi da yanda ta shiga tsakaninshi da Mahaifiyarshi ya tuno, guntun tsaki yayi yace
"Neh-neh Wai are Women Selfish?".
Nene tace "Uwar me? Hausa zakai man dallah".
Tsaki yayi yace "Neh-neh tunda Baban bai dubi Girman Daddy ba ya ci muku mutunci, ai yana da magabata, in ya fi karfin Magabata ai bai fi karfin Hukuma ba, in ko yafi karfinsu bai isa ya fi Karfin Baban Kowa na Katsina ba".
Nene tace "Sarkin Katsina".
Rafeeq yace "Shine Magana kawai, Neh-neh ba tare Kukaje Makka da Amaryar Sarki ba?".
Nene cikin Jin dadi tace "ehmana dakin mu daya da matar sarki da Maryama".
Rafeeq yace "ki samu ganinta ta miki hanya kawai".
Allah Dunkum? Yace "wallahi kuwa"
Tace "Zaidu Bawan Allah ya rokeni kan na fita daga harkarsu wallahi".
Rafeeq yace "Nene sharesu wallahi, ki taimaka musu, ni na san sharrin Matar Uba, DonAllah kar ki karaya".
Cikin Samun Karfin Guiwa tace "tankiyu Dunkum, i lobiyu, i miss you Dunkum".
Yace "Yeah Right i miss you too My Amazing Granny".
Ji yayi tace "Uwarka ka zaga"
Tsaki yayi yace "kina da damuwa wallahi, ke fa kika fara turancin, kuma in an miki sai ya zama laifi?"
"Oho dai kace ma Matarka in ta ga dama ta kirani" dif ta kashe wayar.
Ta yanke Hukunci, Washegari karfe 8 na safe tafita, bata gaya ma kowa ba balle a hanata, ko driver bata bi ta kanshi ba ta samu A daidaita Sahu ta hau sai Gidan Sarki, Part din Gimbiya, aka ma Nene iso, bayan wasu mintuna Gimbiya ta fito, aiko ta rungumo Nene, suka gaisa cike da mutunta Juna.
Nene tace "mai Martaba na nan? Shi nazo gani? Ko yana da bak'i?" Gimbiya tace "ko da bak'i ai zai ga Nenenmu ina fatan Lafiya?"
Nene tace "k'aran Sakaran Mijin Maryama na kawo".
Gimbiya tace "wani abun ya sakeyi? Ko sati biyu baayi ba da Maryama ta zo nan maganar rik'on yaya wai don ya saketa sai dai su bita".
Nene tace "kinji Gilu ko? Ashe kun ma san da maganar, to shekaran jiya wacchan naje Gidan, naga matar da kanenta da uban sun mishi taron dangi sai bugunsh suke wai bayan nan kuma ya kulleshi a Police station, ke cin kashi kala kala ake musu a gidan nan, nace aiko suna da Gata, shine na garzayo don Ganin Mai Martaba". Gimbiya ta mik'e tace barinje in mai bayani.
Bayan Sarki ya saurari Nene ya aika a Kira Mishi Alhaji Ali Zaki da Iyalanshi Gabaki daya, sannan ya tura Police Station a sako Zaid.
Wannan Kenan
*****
"Aa Allah ya kara ma Imani, Matata suka tarar mawa, Nene kuwa harni ta tsokale wa ido" Nene tayi karaf tace "ba gaskia bane, kaine dai kuka taran mashi, ni ina ni ina dambe? Ina neman shekara Saba'in da dori? Ta ya tsohuwa kamata zata iya Dambe da kai da wanchan matashin da kuma Matarka? DonAllah Mai Martaba duk wanda yaji wannan ai ya san karya ne".
Duk da ina cikin tashin hankali sai da na murmusa da jin zanttutukan Nene. Bayan Sarki ya ji bayanan Nene da kuma na Baba da na Shafa'atu, aka min tambayoyi aka ma Dalo tambayoyi Sarki ya yanke hukunci.
"Alhaji Ali Zaki, wannan ya zama karo na karshe da zamuyi zama kanka da yaranka, na saurari komai, na fahimci komai, ba ruwan Matarka da Yaranka, ba ruwanta da su, ke shafaatu ba ruwanki da duk abunda zai ma yaranshi, ba ruwanki da hanashi, ba ruwanki da sa shi, na miki iyaka da su, yauwa ba kuma da k'ayyade musu abincin cinsu, gidan ubansu ne, yana iya sakin ki, amma bai iya sakinsu, kina jina?".
Shiru tayi bata amsa ba, bata ankara ba sai jin Dorina tayi a bayanta, wani irin bank'arewa tayi tare da sakin ihu, haka wannan dogarin ya sake shada mata a baya yace "kinji ko ba kiji ba?" Da sauri tace "naji wallahi, wallahi naji".
Hankalin Alhaji Ali ya tashi amma ba abunda zai iyayi da ya wuce sanya ido, Sarki ya ja ma Baba kunne sosai, kafin ya tambaye in akwai mai magana.
Nace ina da magana "Masters nakeyi, saura kwanakin da ba su wuce 3 na fara jarabawa, Baba yayi freezing accounts dina, ya kwace duk wani abun da ya bani, ya hanani komawa don kammala karatuna".
Sarki yace "Alhaji Zaki hakane?" Baba ya fara in ina yace "Wallahi Mai martaba, ba kudi ne, amma inshaAllah da komai ya daidaita zan maidashi".
Sarki yace "to madallah, duk da zaiyi wuya ace kai baka da halin maidashi karatu ba damuwa bane wannan, indai be rasa ci da sha ba to komai mai sauki ne, wannan tsakaninku ne, ku tashi ku tafi, ku kuma in akwai wani abu kuna iya zuwa Fada ku sanar dani, akwai mai magana?".
Baba yace "eh ni, mai Martaba, donAllah ace ma wanchan Tsohuwar kar ta sake zuwa man gida, tayi nesa da iyalina donAllah, ayi mata iyaka da Gidana". Nene ta murmusa tace "indai Gidanka ne ba zan kara zuwa ba".
Murmushin da takeyi ne ya fadar ma Baba da Aunty Saude Gaba, ba su yarda ba, wannan tsohuwa akwai bariki".
Sarki yace "to Madallah"
A haka ya sallame mu, ko ba komai Nene ta kwatar mana yanci ta siya mana mutunci, ta nuna mana muna da sauran gata.
Nene ta rik'e hannuna da na Dalo ta ja mu waje tace "ku je Gida, da kunga abunda bai muku ba ku kirani, ka kula da kanwarka" sosai hankalinmu ya kwanta.Nene ta tsaida abun hawa tayi tafiyarta Gida abunta.
Mu kuma da Motar Emirate a ka maidamu Gida, ba wanda yace ma kowa komai sai ni da Dalo da ke fira jefi jefi.
A ranar Baba yaje Gidan Alhaji Lema don kara ja mishi kunne kan Uwarshi, lokacin sun fito daga Masallaci shi da Abbii(baban Nasiba) a nan ne ma ya san Mamarshi na wani Case, shi kuma Alhaji Lema a nan ne ya san cewa Nene taje Gidan Sarki, hakuri Abbi ya ba Baba. Nan suka shiga tattaunawa tsakaninsu.
Abbi yace "wallahi ko me zaa ma Nene ba zata fita daga harkansu ba, oh Allah Nene ita bata damuwa taje ta siya fada da kudinta".
Alhaji Habib yace "kawai Zaidu gobe ya wuce da ita Kaduna kawai, ta dan kwana biyu chan".
Abii yace "anya zata yarda ta bishi?
Alhaji Habib yace "wannan kuma aikin Zaidu bawan Allah ne". Dariya sukayi baki daya.
Da kissa da kissina zasu bar Gidan ba tare da sun sake waiwayan gidan sarki ba, ki kulla makirci da duk wani sharrin da zaki iya musu, fadan ba naki bane, ya zama na Uba da yaranshi, ke kawai ki zama 'yar kallo. Hudubar yar rabi kenan da tazo Gidanta, haka kawai zatayi dole tayi taka tsantsan bata son duk abunda zai sake hadata da gidan Sarki don ta ji Dorunar nan, ta san me zatayi. Da kansu zasu bar Gidan baki alekum.
SAI DAI ME?
Rayuwa ta cigaba mana, ba dadi, ba mu taba waya da Mancy ba tunda ta bar katsina, tunda na dawo ni ke shiga kitchen in dafa Abincina, ban yarda na ci abincinsu ba, wani community school Baba ya maido Dalo wai be da kudin biyan makarantar da take a da, amma kin san me? Chan ya maida Annah, ga hudu da ke fantamawa cikin Motocin Gida ni ko nawa kallo.
In naji Bakinciki kamar ya kasheni, na kanje dakin Haruna na shak'a World, a hankali na dinga taba Sigari har ya zame min jiki, a rana sai in sha kara fiye da biyar, komai ya cigana da wakana Babanmu na fiffita Bare kanmu, kashi ya fimu daraja, banda Abinci da wurin kwana ba komai na Babanmu a wurinmu, ke sai yazo ma na daina damuwa da komai, na daina shakkun Baba, na fetsare, na koma abota da su haruna na zama wani dan jagaliya, na koma Taraiyya da yan Bencin Eskaley. World din na batar min da duk wata damuwa, sai likafa ta cigaba sai in zuqi World na bi da kwalin Sigari guda, to fa Sigar Zuk'i daya nake mishi ya kare na cillar na kunna wata, shiyasa suke ce min Mankasssss...
Ke kwatsam wata rana ina daki Dalo ta shigo dakina Hankalinta tashe, tana kuka wai ance mata ina shaye-shaye, ni abokinsu Eskaley ne. Hankalina ya tashi bana so ta taba ganin wannan side din nawa, nima kukan na sa nace mata "wallahi zan bari, ba zan karaba". Da kyar na samu tayi shiru na lallasheta. Rakata nayi har dakinta a cikin Gida, tausayinta ke kamani, duk ta fige ta lallace ta kuma yi duhun bak'i".
Nazo wucewa daidai dakina na da na ji muryar Hudu na cewa "eh na saka mai a karkashin katifar shi" sai na ji Aunty Shafa tace "Yauwa kawai ai shi ya dauke su" sai kuma suka sa darian shewa.
Kafadu na na daga, ba su dameni ba, na wuce dakina da ke baya, na dauko ragowar World na zuk'e, na zauna ina recieving current din da World ke bani a lokaci daya ina busar sigari, ina jina a gajimare naji an banko kofar Daki.
Baba, da Anty Shafa ne, a dage na kallesu na watsar na cigaba da bankan Abuna".
Cike da hargowa Baba yace "Kai DanMakaho, ina Sarka da yan kunnen Zinarin Matata da ka shiga ka sace a dakinta?" Duk da Maganar ta buga zuciyana ban dago na kallesu ba na cigaba da busar Sigarina".
Aunty Shafa ta fara kukan munahinci tace "wallahi da idona naga ya fito dashi daga dakina, na mishi magana kan ya bani abuna ya min zagi ta uwa ta uba, shime nace ni ba zanyi komai ba balle ace ban kyauta ba, bari kai ka dawo tunda kai ka haifeshi sai ya baka".
Wani murmushin bakinciki nayi wanda ya sa na zuk'e ragowar Sigarin, ido na ya kada yayi jazir, amma dai tak bance musu ba.
Cin kwalar rigata Baba yayi "Danubanka yana ina? Hudu duba min dakin nan".
Don rainin Wayau Hudu ya daga Katifata kawai sai ga sarka da yan kunne? Kutumar.
Wai sai suka shiga rafka Salati.
"Wallahi kai ba dana bane ba, ni ban haifi Barawo ba, Maryama ta dade tana haintata, cikin shege tayi ta lakafa min Da, ashe Barawo ne, Allah ya isa tsakanina da Maryama, ta sa na raini Barawo, shege dan shegia, Allah ya isa na, Allah ya tsine ma Maryama".
Da sauri na kwace kaina nayi hanyar Fita.
Muryar Makirar naji tana cewa "dama Alhaji baka san DanMakaho Shege bane? Be da Uba, kai a ka dauka sakarai a ka lakafa maka shi, kai kuma ka raineshi tsakaninka da Allah".
Wani kukan Kura nayi na finciko hannun Baba na tillashi waje, kafin su ankara na sa mukulli na kulle Dakin, kafin ta farga da me nake niyyan yi na ciro Charger Laptop dina na dinga laftarta ta da shi, ihu takeyi na sa k'afa na tande kafafuwan ta, shi ko Baba daga waje Hankalinshi a tashe yana ta kokarin budewa, ya rasa yanda zaiyi.
Sai da nagaji da kaina na kyaleta, duk tayi laasar, fuskarta tayi suntum, wannan shine ba a rabu da bukar ba, ita zaman shekara 15 din da tayi ba wai don ta zo dan Miji na dukanta bane, ita bata ma ga wani chanji ba, bata ga ribar shekarun da ta dauka ba, zuwa zatayi ta samu Er Rabi dole a sake sabon Zama.
Ni ko na kyasta Sigarina na hau busawa, bude k'ofa nayi na bi ta inda Baba ke tsaye cike da tashin hankali, ya na ko ganina ya hau la'anta ta.
"Allah ya tsine maka DanMakaho, Allah ya watse maka Karama, Allah ya kwashe maka Albarka, Allah ya laance ka" ya dinga tsina na.
•••••
Kalar kukan da Labiba keyi ne ya sa shi tsaida labarin, murmushi mai cike da tarin takaici da bakinciki yake yace "Kefa kika dameni da na baki labarina, kuma da na fara sai kuka?".
"INA SONKA"
Ta tsaida duk wata na'urar da ke jikinshi daga aiki.
Da kyar ya iya lallubo kalmar "Sha biyu Saura, dare yayi sosai, tashi muje na rakaki Gida".
"DAGASKE, Ina Sonka".
Cikin ido ya kalleta ya hango tsantsar Gaskiarta tsakani da Allah, wannan wace iri ce? Wace kala ce cikin Mata? Ya san ba da dabi'ar 'yan arewa, don babu wata 'yar arewa da zatayi abubuwan da Labiba keyi, ba 'yar arewa mai ajin da zata kalli Namiji gatsau haka ta gaya mishi kalmomi masu tsada, dauke kanshi yayi sakamakon binshi da wani kallo da takeyi.
Ba tare da ya kalleta ba yace "Its Late, ki tashi na rakaki Gida".
Hawayenta ta goge ta mik'e tsaye yayi gaba ta bishi a baya, da hasken Torchlight ya haska Fasassun Blocks ya tsallakesu, ya haska mata itama ta tsallake. Har tsakar Gidansu Labiba ya shiga.
Da taimakon Hasken Farin Wata suke kallon juna cikin Ido.
"So na kikeyi? Ko tausayina kikeyi?" Ya tambayeta kwayar idonshi kan nata.
"In tausayina kike ji, nagode, ki bari, ni bana bukatar tausayin kowa"
"In kuma sona kikeyi, shima ki bari, bana bukatar a So ni".
So biyu ta kyafta idanuwanta kafin ta tsaidasu a kanshi tace Dagaske Sonka Nikeyi.
Bata ganewa ya fada a ranshi, ya juya ya barta a tsaye, tafiyanshi yayi, ya sake tsallaka Fassassun blocks ya shige Gidansu, kan idonta ya bude kofar dakinshi ya shiga ya maida ya rufe.
Zubewa tayi a kan guiwowinta biyu a k'asa a hankali ta furta YA RABB.....
INTERMISSION.
Vote and comment line by line please..
#1love
#DM
#anatare
#SonSoFWA
#staytuned
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉