Sashe 4
Anas Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Labarin irin ta'addancin da aka je ƙauyensu aka yi musu suka ba shi, har saka su a rumbu da Baffa yayi domin su tsira da rayuwarsu sai da suka ba shi.Da irin wahalar da suka sha a hanƴa kafin su iso nan duk sai da suka faɗa masa, ba su ɓoye masa kome ba har zuwa lokacin da wannan zakin ya ritsa su sai da suka faɗa masa.
"To a ina kuka samu wannan jaririn?" Safna ce ta faÉ—a masa yadda aka yi suka tsince shi yana ta kuka kuma babu uwarsa a kusa da alamu ita ma an kashe ta.
Hawaye maharbin ya shiga zubar wa, haƙiƙa ya tausayawa su Anas ba kaɗan ba, nan shi ma ya shiga ba su na shi labarin kamar haka.
Sunana Aisar ni haifaffen garin Katsina ne, na dawo nan yankin Taraba ne sakamakon Æ´anta'addan da suka addabi yankinmu.
Lokacin ina yaro mu na zaune, ni da iyayena mu ka ji ƙarar harbin bindigu, nan take mahaifina ya ɗauke ni, a kafaɗarsa ya ja hannun mahaifiyata mu ka fice daga ƙauyen namu ta ɓoyayyiyar hanƴa, ba tare da ɗaya daga cikin ƴanta'addan ya gan mu ba.
Sai da muka share awa uku muna tafiya, sannan muka iso wata mararrabar hanÆ´a. Sauke ni mahaifina yayi daga kafaÉ—arsa, yace mahaifiyata ta É—auke ni.
Sunkuyawa ta yi ta ɗauke ni, cikin nutsuwa mahaifina ya dubi mahaifiyata ya nuna mata wata hanƴa da ta yi yamma. Yace "ta bi hanƴar akwai garuruwa da ƙauyuka sosai akan hanƴar" duk garin da ta je kada ta tsaya, da ta samu ruwa da abinci ta sha to ta ƙara gaba, domin a kowanne lokaci ƴanta'addan za su iya riskar ɗaya daga cikin garuruwan.
Sannan yace wa mahaifiyata ta bani tarbiyya dai-dai gwargwado. Sannan ya sake cewa ta saka ni a makarantar boko da islamiyya, kada ta barni na zama mutumin banza.
Ya ciro wani zobe daga hannunsa, ya miƙawa mahaifiyata yace "idan na girma ta ba ni shi a matsayin gadon da mahaifina ya bar mini."
Juyawa yayi zai tafi, mahaifiyata ta yi wuf, ta riƙe rigarsa ta saki wani kuka mai tsuma zuciya tace "Abban Aisar don Allah kar ka tafi ka bar ni!"
Hawaye Abbana ya goge, sannan ya dubi mahaifiyata yace "Binta dole ne na koma wajen mutanen can, domin na É—auki fansar ran iyayena" kuma na kare rayukan mutanen garinmu.
Bai tsaya sauraron abinda Ummata za ta faÉ—a ba, ya juya ya fara tafiya domin ya koma garin ya tari Æ´anta'addan.
Kama hannuna Ummata ta yi, muka fara tafiya, sai faman kuka Ummata take yi tana waigen Abbana.
Har suka daina hango juna, Ummata ba ta daina hangen Abbana ba.
Da kyar Ummata take iya ɗaga ƙafarta, tana tafiya ita kaɗai cikin yashi.
Sai da muka shafe sama da awa uku muna tafiya, sannan Ummata ta tsaya a gindin wata bishiya, ta sauke ni ta ba ni nono nan take kuwa na riƙe na fara sha.
Barci mai nauyi ne ya ɗauke ni, Ummata ta shimfiɗa mayafinta a ƙasa ta kwantar da ni a kai.
Ita ma ta kishingiɗa, take kuwa barci ɓarawo yayi gaba da ita, mun daɗe a gindin bishiyar muna barci, sai wajen doshin faɗuwar rana Ummata ta farka daga barcin, bakinta ɗauke da salati duban ta takai inda nake kwance, gani na tayi har lokacin ban farka ba, ajiyar zuciya ta sauke ganin babu abinda ya same ni.
Ɗauka ta tayi ta goya ni a bayanta, sannan ta cigaba da tafiya, cikinta ban da ciwo babu abinda yake yi, ƙirjinta yana yi mata zafi, sakamakon tana ciwon ulcer kuma ga shi bata samu abinci ta ci ba tun safe.
Yayin da Ummata ta ga duhu yana ƙoƙarin mamaye sauran hasken ranar da ya rage, sai ta samu waje a gefen hanƴa ta zauna ba tare da ta kwance ni daga bayanta ba.
Jim kaÉ—an da zamanta, sai ta fara jiyo wani irin gurnani, marar daÉ—in sauraro, da sauri ta tashi ta shige cikin wani kogon dutse da yake gefen hanÆ´ar.
Hussaini Yusufâœï¸
Comment and share
[12/9, 4:33 PM] ~HUSSAIN YUSUF~: *ðŸ«ðŸ« ANAS MALEEKðŸ«ðŸ«*
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_
*Alk’alaminmu ‘yancinmu*
Labari/Rubutawa
HUSSAINI YUSUF
*______________________________*
*Page 11&12*
Lokacin da Ummata ta shiga cikin kogon, sai ta ga cikinsa duhune sosai, haka yasa ta tsaya daga wajen ƙofa.
Ta rakuye jikin wani ɗan ƙaramin dutse, jikinta ban da rawa babu abinda yake yi, sannu a hankali ta fara hango hasken wuta a can cikin kogon.
Tafiya ta fara yi a hankakli, cikin sanÉ—a tana nufar cikin kogon, domin ta ga wanda ya hura wannan wutar, addu'a take yi a cikin ranta Allah yasa kada na farka daga dogon barcin da na koma.
Daga inda take ta hango wani mutum, sanye da kaya irin na mafarauta, yana gasa nama da alama ci zai yi, domin sai faman jujjuya naman yake yi akan wutar yana barbaÉ—a wani abu a kai, ko ba'a faÉ—a maka ba ka san gishiri ne.
Hamdala Ummata tayi sannan ta nufi wajen mafaraucin, tun daga nesa ya hangota, mamaki ne ya cika mi shi rai har yake tantama a cikin ran shi anÆ´a kuwa wannan mutum ce? Amma bai razana ba kasancewarsa gwarzon jarumi, kuma ba haka kawai yake shiga irin wannan dajin ba.
Bai ɗauke idanunsa daga kanta ba, har ta ƙaraso inda yake, ta yi tsaye akansa tana muzurai, kallonta yayi yace baiwar Allah mutum ko Aljan?
Cikin sanÆ´in murya irin ta wanda ya sha wuya sosai Ummata tace "Ni mutum ce kamarka."
Miƙewa tsaye yayi yace "idan ke mutum ce ya aka yi kika zo nan?" Zaunawa Ummata tayi a ƙasa tace ka taimake ni da ruwa, idan na samu nutsuwa sai na ba ka labarina, miƙa mata wani ƙaramin ƙoƙo yayi cike da ruwa, karɓa Ummata ta yi ta kafa kai sai da ta ji ya ƙulle mata ciki sannan ta ajiye, tare da yin wata ƙatuwar gyatsa.
Bayan ta samu nutsuwa, sai ta kwance ni daga bayanta ta ajiye ni akan cinÆ´arta, har lokacin sharar barcina nake yi, ba abinda ya dame ni.
Kallon mafaraucin nan ta yi, tace ka shirya yanzu zan baka labarina, da na dalilin zuwana wannan dajin mai matuƙar ban tsoro.
Cikin ƙanƙanin lokaci ta ba shi labarin abinda ya barota da garinsu da gidansu har da mijinta da ya koma domin yaƙar ƴanta'addan bata ɓoye masa ba.
Har hawaye sai da mafaraucin ya zubar, saboda tausayin Ummata da ya cika mishi zuciya yace "kash! dama mijinki bai yi gangancin komawa garin ba, tunda har ya riga ya gudo ba tare da sun gan shi ba." Amma yayi namijin ƙoƙari, tunda har ya tseratar da rayuwar iyalinsa, ko ba komai ai ya bar baya.
Wuƙa ya ɗauko ya miƙawa Ummata yace "ta yanki naman zomon da yake gasawa ta ci iya cinta ta ƙoshi."
Yankar naman zomon Ummata ta rinƙa yi, tana ci har sai da ta ji ta ƙoshi. Sannan ta miƙa masa wuƙar shi ma ya fara yanka yana ci, har ya ƙoshi sannan ya sake miƙowa Ummata ruwa ta karɓa ta sha, sannan shi ma ya sha.
Miƙewa tsaye yayi yace Ummata ta biyo shi a baya, take kuwa ta bi shi, wata siririyar hanƴa ya bi da ita, nan take kuwa hanƴar ta kai su har wata bukka wacce aka yi ta da itatuwa.
Tsayawa yayi a ƙofar bukkan yace "Ummata ta shiga ciki ta kwanta washegari, shi zai kwanta a waje." Ummata ta kalle shi tace "Me zai hana nima na dawo wajen mu kwana tare?" Wani kallo ya watsawa Ummata har sai da ta firgita, yace "ke ba musulma ba ce?" Kinsan dai Addinin musulunci ya hana mutum ya keɓe da matar da ba muharramarsa ba ko? To gaskiya ni ina kiyaye addinina don haka ki shiga ciki ki kwanta ni zan kwanta anan.
Idan kuma ba zaki iya kwanciya a ciki ba, ki fito ki kama hanƴa ki tafi ya faɗa a fusace, ba yadda Ummata ta iya ta shiga cikin bukkar ta kwanta, tunowa ta yi da Sallolin da bata yi ba, don a yau iya Sallar Asuba ta yi. Bata samu damar aiwatar da sauran sallolin da suka wajaba akanta ba, firgigit ta tashi ta fito waje tambayar inda zata samu ruwa tayi zata yi Sallah, nuna mata wani tulu yayi da yake cike da ruwa, ta ɗauko wani ɗan ƙaramin ƙoƙo ta tsiyaya, bayan ta kamo ruwa ta zo ta ɗaura alwala ta koma cikin ɗakin ta tayar da Sallah.
Sai da ta rama duk sallolin da ake bin ta a ranar, sannan ta ɗora da Sallar nafila, a takaice dai sai misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare Ummata ta gama Sallar.
Lokacin ni kuma na farka daga dogon barcin da nake yi, zuwa tulun nan me ruwa ta yi ta tsiyayo ruwan ta zo ta bani, ba kaÉ—an ba na sha ruwan sannan ta bani nono na sha na koma barci.
Ita ma nan ta ɗare gadon karan da yake cikin ɗakin, tunani ne kala-kala ya cika mata rai, tunanin mijinta da iyayenta da sauran jama'ar garinsu ne, ya cika mata rai, hawaye ne ya rinƙa sintiri a kan fuskarta a haka har barci ɓarawo ya zo yayi gaba da ita.
Duk abin nan da Ummata take yi, yana kallonta ganin yadda ta zage tana ta Sallah ne ya burge shi sosai, bayan ta barci ya É—auke ta shi ma ya tashi ya É—aura alwalar ya tayar da Sallah. Bai idar da sallar ba har doshin asuba, sannan yayi sallama ya É—an kwanta ya runtsa kafin alfijir yayi.
Washe gari da safe ya É—auko gurasa da gasashshen nama, ya bai wa Ummata yace ta ci. Bayan ta gama ci, sai ya kalleta yace "yau zai koma garinsu don haka ta shirya sai su koma tare."
"To a ina kuka samu wannan jaririn?" Safna ce ta faÉ—a masa yadda aka yi suka tsince shi yana ta kuka kuma babu uwarsa a kusa da alamu ita ma an kashe ta.
Hawaye maharbin ya shiga zubar wa, haƙiƙa ya tausayawa su Anas ba kaɗan ba, nan shi ma ya shiga ba su na shi labarin kamar haka.
Sunana Aisar ni haifaffen garin Katsina ne, na dawo nan yankin Taraba ne sakamakon Æ´anta'addan da suka addabi yankinmu.
Lokacin ina yaro mu na zaune, ni da iyayena mu ka ji ƙarar harbin bindigu, nan take mahaifina ya ɗauke ni, a kafaɗarsa ya ja hannun mahaifiyata mu ka fice daga ƙauyen namu ta ɓoyayyiyar hanƴa, ba tare da ɗaya daga cikin ƴanta'addan ya gan mu ba.
Sai da muka share awa uku muna tafiya, sannan muka iso wata mararrabar hanÆ´a. Sauke ni mahaifina yayi daga kafaÉ—arsa, yace mahaifiyata ta É—auke ni.
Sunkuyawa ta yi ta ɗauke ni, cikin nutsuwa mahaifina ya dubi mahaifiyata ya nuna mata wata hanƴa da ta yi yamma. Yace "ta bi hanƴar akwai garuruwa da ƙauyuka sosai akan hanƴar" duk garin da ta je kada ta tsaya, da ta samu ruwa da abinci ta sha to ta ƙara gaba, domin a kowanne lokaci ƴanta'addan za su iya riskar ɗaya daga cikin garuruwan.
Sannan yace wa mahaifiyata ta bani tarbiyya dai-dai gwargwado. Sannan ya sake cewa ta saka ni a makarantar boko da islamiyya, kada ta barni na zama mutumin banza.
Ya ciro wani zobe daga hannunsa, ya miƙawa mahaifiyata yace "idan na girma ta ba ni shi a matsayin gadon da mahaifina ya bar mini."
Juyawa yayi zai tafi, mahaifiyata ta yi wuf, ta riƙe rigarsa ta saki wani kuka mai tsuma zuciya tace "Abban Aisar don Allah kar ka tafi ka bar ni!"
Hawaye Abbana ya goge, sannan ya dubi mahaifiyata yace "Binta dole ne na koma wajen mutanen can, domin na É—auki fansar ran iyayena" kuma na kare rayukan mutanen garinmu.
Bai tsaya sauraron abinda Ummata za ta faÉ—a ba, ya juya ya fara tafiya domin ya koma garin ya tari Æ´anta'addan.
Kama hannuna Ummata ta yi, muka fara tafiya, sai faman kuka Ummata take yi tana waigen Abbana.
Har suka daina hango juna, Ummata ba ta daina hangen Abbana ba.
Da kyar Ummata take iya ɗaga ƙafarta, tana tafiya ita kaɗai cikin yashi.
Sai da muka shafe sama da awa uku muna tafiya, sannan Ummata ta tsaya a gindin wata bishiya, ta sauke ni ta ba ni nono nan take kuwa na riƙe na fara sha.
Barci mai nauyi ne ya ɗauke ni, Ummata ta shimfiɗa mayafinta a ƙasa ta kwantar da ni a kai.
Ita ma ta kishingiɗa, take kuwa barci ɓarawo yayi gaba da ita, mun daɗe a gindin bishiyar muna barci, sai wajen doshin faɗuwar rana Ummata ta farka daga barcin, bakinta ɗauke da salati duban ta takai inda nake kwance, gani na tayi har lokacin ban farka ba, ajiyar zuciya ta sauke ganin babu abinda ya same ni.
Ɗauka ta tayi ta goya ni a bayanta, sannan ta cigaba da tafiya, cikinta ban da ciwo babu abinda yake yi, ƙirjinta yana yi mata zafi, sakamakon tana ciwon ulcer kuma ga shi bata samu abinci ta ci ba tun safe.
Yayin da Ummata ta ga duhu yana ƙoƙarin mamaye sauran hasken ranar da ya rage, sai ta samu waje a gefen hanƴa ta zauna ba tare da ta kwance ni daga bayanta ba.
Jim kaÉ—an da zamanta, sai ta fara jiyo wani irin gurnani, marar daÉ—in sauraro, da sauri ta tashi ta shige cikin wani kogon dutse da yake gefen hanÆ´ar.
Hussaini Yusufâœï¸
Comment and share
[12/9, 4:33 PM] ~HUSSAIN YUSUF~: *ðŸ«ðŸ« ANAS MALEEKðŸ«ðŸ«*
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_
*Alk’alaminmu ‘yancinmu*
Labari/Rubutawa
HUSSAINI YUSUF
*______________________________*
*Page 11&12*
Lokacin da Ummata ta shiga cikin kogon, sai ta ga cikinsa duhune sosai, haka yasa ta tsaya daga wajen ƙofa.
Ta rakuye jikin wani ɗan ƙaramin dutse, jikinta ban da rawa babu abinda yake yi, sannu a hankali ta fara hango hasken wuta a can cikin kogon.
Tafiya ta fara yi a hankakli, cikin sanÉ—a tana nufar cikin kogon, domin ta ga wanda ya hura wannan wutar, addu'a take yi a cikin ranta Allah yasa kada na farka daga dogon barcin da na koma.
Daga inda take ta hango wani mutum, sanye da kaya irin na mafarauta, yana gasa nama da alama ci zai yi, domin sai faman jujjuya naman yake yi akan wutar yana barbaÉ—a wani abu a kai, ko ba'a faÉ—a maka ba ka san gishiri ne.
Hamdala Ummata tayi sannan ta nufi wajen mafaraucin, tun daga nesa ya hangota, mamaki ne ya cika mi shi rai har yake tantama a cikin ran shi anÆ´a kuwa wannan mutum ce? Amma bai razana ba kasancewarsa gwarzon jarumi, kuma ba haka kawai yake shiga irin wannan dajin ba.
Bai ɗauke idanunsa daga kanta ba, har ta ƙaraso inda yake, ta yi tsaye akansa tana muzurai, kallonta yayi yace baiwar Allah mutum ko Aljan?
Cikin sanÆ´in murya irin ta wanda ya sha wuya sosai Ummata tace "Ni mutum ce kamarka."
Miƙewa tsaye yayi yace "idan ke mutum ce ya aka yi kika zo nan?" Zaunawa Ummata tayi a ƙasa tace ka taimake ni da ruwa, idan na samu nutsuwa sai na ba ka labarina, miƙa mata wani ƙaramin ƙoƙo yayi cike da ruwa, karɓa Ummata ta yi ta kafa kai sai da ta ji ya ƙulle mata ciki sannan ta ajiye, tare da yin wata ƙatuwar gyatsa.
Bayan ta samu nutsuwa, sai ta kwance ni daga bayanta ta ajiye ni akan cinÆ´arta, har lokacin sharar barcina nake yi, ba abinda ya dame ni.
Kallon mafaraucin nan ta yi, tace ka shirya yanzu zan baka labarina, da na dalilin zuwana wannan dajin mai matuƙar ban tsoro.
Cikin ƙanƙanin lokaci ta ba shi labarin abinda ya barota da garinsu da gidansu har da mijinta da ya koma domin yaƙar ƴanta'addan bata ɓoye masa ba.
Har hawaye sai da mafaraucin ya zubar, saboda tausayin Ummata da ya cika mishi zuciya yace "kash! dama mijinki bai yi gangancin komawa garin ba, tunda har ya riga ya gudo ba tare da sun gan shi ba." Amma yayi namijin ƙoƙari, tunda har ya tseratar da rayuwar iyalinsa, ko ba komai ai ya bar baya.
Wuƙa ya ɗauko ya miƙawa Ummata yace "ta yanki naman zomon da yake gasawa ta ci iya cinta ta ƙoshi."
Yankar naman zomon Ummata ta rinƙa yi, tana ci har sai da ta ji ta ƙoshi. Sannan ta miƙa masa wuƙar shi ma ya fara yanka yana ci, har ya ƙoshi sannan ya sake miƙowa Ummata ruwa ta karɓa ta sha, sannan shi ma ya sha.
Miƙewa tsaye yayi yace Ummata ta biyo shi a baya, take kuwa ta bi shi, wata siririyar hanƴa ya bi da ita, nan take kuwa hanƴar ta kai su har wata bukka wacce aka yi ta da itatuwa.
Tsayawa yayi a ƙofar bukkan yace "Ummata ta shiga ciki ta kwanta washegari, shi zai kwanta a waje." Ummata ta kalle shi tace "Me zai hana nima na dawo wajen mu kwana tare?" Wani kallo ya watsawa Ummata har sai da ta firgita, yace "ke ba musulma ba ce?" Kinsan dai Addinin musulunci ya hana mutum ya keɓe da matar da ba muharramarsa ba ko? To gaskiya ni ina kiyaye addinina don haka ki shiga ciki ki kwanta ni zan kwanta anan.
Idan kuma ba zaki iya kwanciya a ciki ba, ki fito ki kama hanƴa ki tafi ya faɗa a fusace, ba yadda Ummata ta iya ta shiga cikin bukkar ta kwanta, tunowa ta yi da Sallolin da bata yi ba, don a yau iya Sallar Asuba ta yi. Bata samu damar aiwatar da sauran sallolin da suka wajaba akanta ba, firgigit ta tashi ta fito waje tambayar inda zata samu ruwa tayi zata yi Sallah, nuna mata wani tulu yayi da yake cike da ruwa, ta ɗauko wani ɗan ƙaramin ƙoƙo ta tsiyaya, bayan ta kamo ruwa ta zo ta ɗaura alwala ta koma cikin ɗakin ta tayar da Sallah.
Sai da ta rama duk sallolin da ake bin ta a ranar, sannan ta ɗora da Sallar nafila, a takaice dai sai misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare Ummata ta gama Sallar.
Lokacin ni kuma na farka daga dogon barcin da nake yi, zuwa tulun nan me ruwa ta yi ta tsiyayo ruwan ta zo ta bani, ba kaÉ—an ba na sha ruwan sannan ta bani nono na sha na koma barci.
Ita ma nan ta ɗare gadon karan da yake cikin ɗakin, tunani ne kala-kala ya cika mata rai, tunanin mijinta da iyayenta da sauran jama'ar garinsu ne, ya cika mata rai, hawaye ne ya rinƙa sintiri a kan fuskarta a haka har barci ɓarawo ya zo yayi gaba da ita.
Duk abin nan da Ummata take yi, yana kallonta ganin yadda ta zage tana ta Sallah ne ya burge shi sosai, bayan ta barci ya É—auke ta shi ma ya tashi ya É—aura alwalar ya tayar da Sallah. Bai idar da sallar ba har doshin asuba, sannan yayi sallama ya É—an kwanta ya runtsa kafin alfijir yayi.
Washe gari da safe ya É—auko gurasa da gasashshen nama, ya bai wa Ummata yace ta ci. Bayan ta gama ci, sai ya kalleta yace "yau zai koma garinsu don haka ta shirya sai su koma tare."