← Book details Anas Maleek Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 25

Sashe 25

Anas Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Ba Ƙaramin daɗi Anas ya ji ba da hukumarsu ta sojoji ta amince ya tunkari Sa'eed, nan take kuwa ba tare da ɓata wani lokaci ba ya fara shiri cikin ƴan mintuna ƙalilan ya gama kimtsawa ya fito cikin shigarsa ta sojoji. A hankali ya rinƙa saukowa ƙasa har ya gama saukowa su Aisar ya gani a tsaitsaye suna jiranshi ya sauko, kallonsu yayi ɗaya bayan ɗaya sannan ya ce "Yanzun nan zan je domin dawo da ƴan'uwana ku taya ni da addu'a."
Yana gama faɗar haka ya juya zai fice daga falon, "ANAS" muryar Aisar ta daki dodon kunnensa, juyowa yayi a hankali fuskarsa tana zubar da hawaye ya dubi su Inna ya ce "Ku gafarce ni Inna idan na mutu ku yafe min don Allah domin ban sani ba ko ba zan dawo a raye ba. Inna na yarda ki auri Daddin Ammar ko da ba na raye, domin ina da yaƙinin zaki samu farinciki da walwala a wajensa."
Kowa a wajen zubar da hawaye yake yi, Aisar ne ya buÉ—i baki cikin raunin murya ya fara magana "Anas ta yaya kake zaton za mu barka ka tafi kai ma ka hallaka? So kake mu rasa ku gaba É—aya ne, me kake faÉ—a haka ka, tsaya a bi komai a sannu mana, ka sani gaggawa aikin shaiÉ—an ce."

Murmushi Anas ya saki duk da ba wai murmushin murna ba ne, kana ganin murmushin ka ga murmushin takaici gami da alhini amma haka bai hana fuskar Anas haskawa ba, domin Anas irin samarin nan ne da mata suke mafarkin samu a rayuwarsu, ga ilimi ga kyau ga kuɗi sannan kuma jarumta, sai kuma babban abin da yayi wa rayuwarsa ado shine tausayi, Anas yana matuƙar tausayawa mace a rayuwarsa ko kaɗan ba ya so ya ga abin da zai ɓata mata rai kome ƙanƙantarsa kuwa.

Share hawaye Anas yayi daga idonsa ya ce "Baffa ba su Safna suke buƙata ba, ni suke buƙata na kai musu kaina shi yasa suka yi garkuwa da ƴan'uwana domin su same ni cikin sauƙi kuma ga shi sun samu."
"Ka sani da zarar yanzu na kai kaina zasu dawo da su har nan gida a yadda suka yi alƙawari ba za su cutar da ko ɗaya ba, indai ban karya musu dokokinsu ba. Don haka yanzi ni na tafi ba insha Allahu idan su Nasreen ba su dawo yau ba to gobe za su dawo wannan alƙawari ne na yi muku."

Yana gama faɗar haka ya juya zai tafi, sake dakatar da shi Aisar yayi ya ce "Ungo wannan ka ɗaura shi a damtsen hannunka na dama insha Allahu babu abin da suka isa suyi maka" ya faɗa yana mai miƙa masa wani kambu wanda aka naɗe shi da fatar zaki.
Karɓa Anas yayi da sauri ya fice daga falon don kada su sake tsayar da shi, ya zo dai-dai ƙofar gidansu ya ga Ammar shi kuma ya zo gidan.
Da sauri Ammar ya fito daga motarsa yana tambayar Anas ko lafiya, shiru Anas yayi hawaye yana kwararowa akan kyakkyawar fuskarsa sai da ya daidaita nutsuwarsa sannan ya dubi Ammar cikin nutsuwa ya ce........................✍🏻

To be continue.............📝📝📝

HUSSAINI YUSUF✍️
Chapter 25 · 0% Book details