Sashe 23
Anas Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Amma game da maganar na sanar da Baffanka Aisar, ai tun kafin na sani ma shi ya rigani sani. Domin ta hannunsa saƙon ya iso gare ni, kuma shi ya rinƙa roƙona akan na amince da maganar auren, ni na ƙi amincewa na ce sai na yi shawara da kai na ji ta bakinka sannan na amince. Yanzu ka tashi ka je ka kwanta, idan Allah ya kai mu gobe zan sanar da su ce wa na amince da auren." Tashi Anas yayi ya ce "To Inna sai da safe" murmushi ta yi ta ce "Allah ya kai mu" sannan ya fice tare da jawo ƙyauren ɗakin.
Tun da ya je ya kwanta tunaninta ya sake faÉ—o masa a rai, Allah-Allah yake gari ya waye domin yayi tozali da kyakkyawar fuskarta, mai sanyaya masa zuciya, nan take kuma ya koma tunanin hanyar da zai bi domin sanar da ita muradin zuciyarsa, amma sam ya rasa da wannan tunanin barci yayi gaba da shi.
*WASHE GARI*
Misalin ƙarfe 8:30am kowa ya hallara a dining area, abincine kala-kala sai wanda mutum ya zaɓa sannan zai ci. Dubawa Aisar yayi bai ga Anas ba, nan ya tashi Basma ya ce ta je ta kira wo shi yayi break fast. Fuskarta a murtuƙe ta tashi ta nufi ɗakinsa, domin ko kaɗan Basma ba ta son abin da zai haɗa ta da Anas ko kaɗan, kwata-kwata ba ta son haɗa wata mu'amala da shi, amma yanzu wai a rasa wanda za'a tura kiranshi sai ni kaɗai?" A hankali ta tura ƙofar ɗakin, shi kuma Anas lokacin ya fito daga bathroom yana tsane jikinsa da wani ɗan ƙaramin tawul, ji yayi an shigo ɗakin ba tare da neman izini ba.
Da sauri ya waiga domin ya ga wanda ya shigo, numfashinsa ne ya nemi É—aukewa yayin da yayi tozali da kyakkyawar fuskarta, mai É—auke da wani haske mai sanyaya zuciya, dara-daran idanuwanta da dogon hancinta da kyawun dirin da Allah ya bata sune suka fi ruÉ—ar shi ya ji tamkar Basma ta kasance tauraruwar Æ´an'mata ko kuma kai tsaye za'a iya kiranta da autar mata, saboda irinsu kaÉ—an ne a cikin al'umarmu ta Hausawa.
Yayin da ta gama buɗe kyauren ɗakin sai ta koma da sauri saboda tun da take a rayuwarta bata taɓa ganin namiji a haka babu riga a jikinsa ba. Murtuƙe fuska yayi cikin dakakkiyar murya ya kira ta "Ke zo nan" kamar kar ta koma haka zuciyarta ta rinka raya mata, amma da ta tuno irin muguntar da yake yi musu tun kafin ya tafi soja, to yanzu da ya dawo muguntar ai sai ta ninka ta da, tana gama wannan tunanin ta kutsa kanta cikin ɗakin.
Kanta a sunkuye ta ƙarasa shiga ciki, tana ta faman wasa da ƴan yatsun hannunta, murtuƙe fuska yayi kamar ba shi ba ya ce "Me ya kawo ki ɗakina?" cikin harɗewar harshe ta fara magana "Dam....dam...dama me min tsaya kina wani Kame-kame" da sauri ta ce "Dama haka aka ce na kirawo ka ka zo ayi breakfast" tana gama faɗar haka ta juya da sauri ta bar cikin ɗakin tare da jawo murfin da ƙarfi, alamun ranta ya ɓaci.
Bayan ya gama shiryawa ya ɗauko wata dakakkiyar shadda fara ya sanya ta a jikinsa, ba ƙaramin kyau Anas yayi ba dama ga shi asalin bafulatanin Mambila. Ya ɗauko wani agogo mai tsadar gaske ya ɗaura shi a tsintsinyar hannunsa na dama, sannan ya ɗauko wasu zobuna masu ɗan karan kyau da tsada ya zura su a zara-zaran yatsunsa, buɗe wardrobe ɗin cikin ɗakin yayi ya ɗauko wata hula kalar milk, ya ɗorata akansa wow! ba ƙaramin kyau Anas yayi ba sai ma kun gan shi musamman mata sai kun ƙyasa wallahi lol.
A hankali ya buɗe ƙofar falon ya fito, ɗaya bayan ɗaya yake take stairs ɗin kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki, ko kuma kamar wanda tafiya take wahalarwa. Yana ƙarasowa cikin falon, sai ya hango su a wani keɓantaccen waje wanda iya wani dogon dining table ne a wajen a jera abinci kusan kala goma, kowa sai dai ya zaɓi abin da zai ci hankalinsu kwance kowa sai faman zura lomarsa yake abinsa.
Samun ɗaya daga cikin kujerun da suka zagaye table ɗin yayi ya zauna, bayan ya gaishe da kowa a wajen, sannan su Safna da Nasreen har da Basma ma suka gaishe shi, Safna ce tayi saving na shi zaunawa yayi ya fara cin abincin har sai da ya ƙoshi.
Aisar ne yayi gyaran murya ya ce su Safna su tashi su shiga da ciki, babu musu kuwa su duka ukun suka tashi suka shiga, bayan sun tafi Aisar ya juyo ya kalli Anas ya ce "Yanzu zan faɗa maka dalilin da yasa ka gan mu a wannan ƙerarren gidan. Gyara zama Anas yayi ya ce "To Baffa ina sauraronka" numfasawa Aisar yayi sannan ya cigaba da cewa. "Bayan tafiyarka neman aikin soja, mahaifin Ammar ya nuna yana son auren mahaifiyarka, ita kuma ta ƙi amincewa ta ce "Har sai ka dawo ta ji ra'ayinka sannan ta amince."
Amma duk da haka mutumin nan bai daina yi mana hidima, da na faɗa masa sana'ar da nake yi ta sayar da gwanjo sai ya haɗa ni da wani babban dealer, ya ara mini kuɗi masu yawan gaske. Sannu a hankali kasuwancina ya rinƙa haɓaka, da ni da ke bai wa sarin kaya na dawo ni ne mai bayarwa, har na zo duk faɗin kasuwar Wambai babu inda ba'a sanni ba" "Na gina manyan shaguna na gani na faɗa, wasu ina kasa kayana wasu kuma na bayar da su haya ana kawo min balance ko wacce shekara."
Wata rana na je na saro kaya da yawa, na zo shago ina ta duddubawa kwatsam na ga wata ƴar madaidaiciyar jaka a ciki, ban yi wani jinkiri ba, na ɗauko ta ina dubawa kawai sai na ga dalolin kuɗi a ciki, a zatona ko me bamu kayanne yayi mantuwa amma sai na ga wata ƴar ƙaramar takarda ce wa "Zakka ce duk wanda ya samu rabonsa ne kuma halak ɗinsa ne" ai kuwa da sauri na ɗauki jakar na nufo gida da ita, da na nunawa Sa'ad ya ce "Wannan ba ƙananan kuɗi bane, nan da nan muka ɗebi kaɗan daga ciki muka je wajen canji, nan muka ga an bamu kuɗi masu yawan gaske wajen 30 million naira, nan muka shiga murna, da mamaki don ni ban taɓa ganin dala ba sai a wannan lokacin.
Nan da nan kuwa kasuwanci ya bunƙasa, a hankali muka rinƙa canjar da kuɗin, har suka ƙare mun samu kimanin naira biliyan ɗaya a kuɗin Najeriya. Yanzu haka ina da manyan shaguna da nake sayar da atamfofi da kayan sakawa a kasuwar kantin kwari.
Kuma kai ma na gina maka ƙaton mall na mallaka maka shi halak malak, kuma akwai wasu kuɗi da na tanadar maka, idan ka gama zama sojan zan baka su ka rinƙa ɗan taɓa kasuwanci. Kuma wannan gidan da kake gani da ribar
da na samu a shekara É—aya na gina shi, amma insha Allahu zan gina wanda ya fishi nan gaba kaÉ—an.
Numfasawa Anas yayi ya ce "Baffa haka Allah yake yin lamarinshi, idan ya soka da arziƙi yanzu ne zaka fi kowa, haka idan ya soka da talauci babu wanda ya isa ya fitar da kai daga ciki idan ba shi ba" "Wannan gaskiya ne Anas" cigaba Anas yayi da cewa "Amma Baffa shi kuma Baffa Sa'ad me ka yi masa?" murmushi Aisar yayi ya ce "Ai na gina masa ƙaton gida, a can unguwar Ƴar akwa kuma na bashi naira miliyan ɗari yayi jari, yanzu haka ma ya samu labarin dawowarka yana hanya zai zo ku gaisa......
Hussain YusufâœðŸ»
[12/9, 4:38 PM] ~HUSSAIN YUSUF~: *ANAS MALEEK*
*NA*
*HUSSAINI YUSUF*
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_
*Alk’alaminmu 'yancinmu*
*Page 49/50*
Murmushi Anas yayi ya ce "Baffa da ka ce masa ma ya zauna sai na je har gidan nasa na gaida shi".
"Anas kenan ka san halin mutumin naka da gardama, wallahi sai da na faɗa masa haka amma furr ya ƙi amincewa lallai sai dai ya zo da kansa ya sameka, a cewarsa kada a wahalar da kai.
Kafin Anas ya furta wani abun suka ji sallamar Sa'ad ya shigo cikin falon, da gudu Aisar ya je ya tare shi yana ce wa "Baffana sannu da zuwa da ka bari ma ai sai na zo da kaina mu gaisa ba sai ka zo ba" murmushi Sa'ad yayi ya ce "Ai zuwan da nayi yanzu, don na matsu na ganka ne shi yasa, amma ai na san zaka zo inda nake Anas É—ina."
Dai-dai lokacin su Nasreen da Safna da kuma Basmah suka fito daga ɗakinsu, cikin shirin tafiya school. Basmah ce ta hango Abbanta da Momynta a zaune, da gudu ta ƙarasa wajensu ta rungume su tana tambayarsu yaushe suka zo.
Sa'ad ne ya daka mata tsawa ya ce "Ke har yanzu ba ki daina wannan rashin hankalin ba ko? Ko haka ki ka ga sauran Æ´an'uwanki sun yi?"
"Haba Sa'ad me kuma yarinyar nan ta yi fisabilillahi, murna fa take yi da ganinku amma sai ka hau ta da wannan faɗan kamar za ka dake ta?" Cewar Aisar yana mai jin haushin Sa'ad akan takurawa Basma da yake yi, shi yasa ma ta zaɓi ta zauna da su Safna don ta daina fuskantar faɗan da take sha a wajen mahaifinta. Kamar ba shine ya haifeta ba haka yake rufeta da faɗa kullum ita da gidansu bata da sukuni, wannan halayya ta Sa'ad tana matuƙar ɓatawa mahaifiyar Basma rai, musamman idan ta kalli yadda Aisar yake tarairaiyar su Safna da Nasreen sai ta ji ina ma a ce haka mijinta yake yi wa tilon ƴarsu Basma, da ta fi kowa farinciki da jin daɗi, kullum idan sun zauna ban da aikin faɗa masa illar da abin da yake yi wa Basma take yi amma ya ƙi fahimta kwata-kwata.
Tun da ya je ya kwanta tunaninta ya sake faÉ—o masa a rai, Allah-Allah yake gari ya waye domin yayi tozali da kyakkyawar fuskarta, mai sanyaya masa zuciya, nan take kuma ya koma tunanin hanyar da zai bi domin sanar da ita muradin zuciyarsa, amma sam ya rasa da wannan tunanin barci yayi gaba da shi.
*WASHE GARI*
Misalin ƙarfe 8:30am kowa ya hallara a dining area, abincine kala-kala sai wanda mutum ya zaɓa sannan zai ci. Dubawa Aisar yayi bai ga Anas ba, nan ya tashi Basma ya ce ta je ta kira wo shi yayi break fast. Fuskarta a murtuƙe ta tashi ta nufi ɗakinsa, domin ko kaɗan Basma ba ta son abin da zai haɗa ta da Anas ko kaɗan, kwata-kwata ba ta son haɗa wata mu'amala da shi, amma yanzu wai a rasa wanda za'a tura kiranshi sai ni kaɗai?" A hankali ta tura ƙofar ɗakin, shi kuma Anas lokacin ya fito daga bathroom yana tsane jikinsa da wani ɗan ƙaramin tawul, ji yayi an shigo ɗakin ba tare da neman izini ba.
Da sauri ya waiga domin ya ga wanda ya shigo, numfashinsa ne ya nemi É—aukewa yayin da yayi tozali da kyakkyawar fuskarta, mai É—auke da wani haske mai sanyaya zuciya, dara-daran idanuwanta da dogon hancinta da kyawun dirin da Allah ya bata sune suka fi ruÉ—ar shi ya ji tamkar Basma ta kasance tauraruwar Æ´an'mata ko kuma kai tsaye za'a iya kiranta da autar mata, saboda irinsu kaÉ—an ne a cikin al'umarmu ta Hausawa.
Yayin da ta gama buɗe kyauren ɗakin sai ta koma da sauri saboda tun da take a rayuwarta bata taɓa ganin namiji a haka babu riga a jikinsa ba. Murtuƙe fuska yayi cikin dakakkiyar murya ya kira ta "Ke zo nan" kamar kar ta koma haka zuciyarta ta rinka raya mata, amma da ta tuno irin muguntar da yake yi musu tun kafin ya tafi soja, to yanzu da ya dawo muguntar ai sai ta ninka ta da, tana gama wannan tunanin ta kutsa kanta cikin ɗakin.
Kanta a sunkuye ta ƙarasa shiga ciki, tana ta faman wasa da ƴan yatsun hannunta, murtuƙe fuska yayi kamar ba shi ba ya ce "Me ya kawo ki ɗakina?" cikin harɗewar harshe ta fara magana "Dam....dam...dama me min tsaya kina wani Kame-kame" da sauri ta ce "Dama haka aka ce na kirawo ka ka zo ayi breakfast" tana gama faɗar haka ta juya da sauri ta bar cikin ɗakin tare da jawo murfin da ƙarfi, alamun ranta ya ɓaci.
Bayan ya gama shiryawa ya ɗauko wata dakakkiyar shadda fara ya sanya ta a jikinsa, ba ƙaramin kyau Anas yayi ba dama ga shi asalin bafulatanin Mambila. Ya ɗauko wani agogo mai tsadar gaske ya ɗaura shi a tsintsinyar hannunsa na dama, sannan ya ɗauko wasu zobuna masu ɗan karan kyau da tsada ya zura su a zara-zaran yatsunsa, buɗe wardrobe ɗin cikin ɗakin yayi ya ɗauko wata hula kalar milk, ya ɗorata akansa wow! ba ƙaramin kyau Anas yayi ba sai ma kun gan shi musamman mata sai kun ƙyasa wallahi lol.
A hankali ya buɗe ƙofar falon ya fito, ɗaya bayan ɗaya yake take stairs ɗin kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki, ko kuma kamar wanda tafiya take wahalarwa. Yana ƙarasowa cikin falon, sai ya hango su a wani keɓantaccen waje wanda iya wani dogon dining table ne a wajen a jera abinci kusan kala goma, kowa sai dai ya zaɓi abin da zai ci hankalinsu kwance kowa sai faman zura lomarsa yake abinsa.
Samun ɗaya daga cikin kujerun da suka zagaye table ɗin yayi ya zauna, bayan ya gaishe da kowa a wajen, sannan su Safna da Nasreen har da Basma ma suka gaishe shi, Safna ce tayi saving na shi zaunawa yayi ya fara cin abincin har sai da ya ƙoshi.
Aisar ne yayi gyaran murya ya ce su Safna su tashi su shiga da ciki, babu musu kuwa su duka ukun suka tashi suka shiga, bayan sun tafi Aisar ya juyo ya kalli Anas ya ce "Yanzu zan faɗa maka dalilin da yasa ka gan mu a wannan ƙerarren gidan. Gyara zama Anas yayi ya ce "To Baffa ina sauraronka" numfasawa Aisar yayi sannan ya cigaba da cewa. "Bayan tafiyarka neman aikin soja, mahaifin Ammar ya nuna yana son auren mahaifiyarka, ita kuma ta ƙi amincewa ta ce "Har sai ka dawo ta ji ra'ayinka sannan ta amince."
Amma duk da haka mutumin nan bai daina yi mana hidima, da na faɗa masa sana'ar da nake yi ta sayar da gwanjo sai ya haɗa ni da wani babban dealer, ya ara mini kuɗi masu yawan gaske. Sannu a hankali kasuwancina ya rinƙa haɓaka, da ni da ke bai wa sarin kaya na dawo ni ne mai bayarwa, har na zo duk faɗin kasuwar Wambai babu inda ba'a sanni ba" "Na gina manyan shaguna na gani na faɗa, wasu ina kasa kayana wasu kuma na bayar da su haya ana kawo min balance ko wacce shekara."
Wata rana na je na saro kaya da yawa, na zo shago ina ta duddubawa kwatsam na ga wata ƴar madaidaiciyar jaka a ciki, ban yi wani jinkiri ba, na ɗauko ta ina dubawa kawai sai na ga dalolin kuɗi a ciki, a zatona ko me bamu kayanne yayi mantuwa amma sai na ga wata ƴar ƙaramar takarda ce wa "Zakka ce duk wanda ya samu rabonsa ne kuma halak ɗinsa ne" ai kuwa da sauri na ɗauki jakar na nufo gida da ita, da na nunawa Sa'ad ya ce "Wannan ba ƙananan kuɗi bane, nan da nan muka ɗebi kaɗan daga ciki muka je wajen canji, nan muka ga an bamu kuɗi masu yawan gaske wajen 30 million naira, nan muka shiga murna, da mamaki don ni ban taɓa ganin dala ba sai a wannan lokacin.
Nan da nan kuwa kasuwanci ya bunƙasa, a hankali muka rinƙa canjar da kuɗin, har suka ƙare mun samu kimanin naira biliyan ɗaya a kuɗin Najeriya. Yanzu haka ina da manyan shaguna da nake sayar da atamfofi da kayan sakawa a kasuwar kantin kwari.
Kuma kai ma na gina maka ƙaton mall na mallaka maka shi halak malak, kuma akwai wasu kuɗi da na tanadar maka, idan ka gama zama sojan zan baka su ka rinƙa ɗan taɓa kasuwanci. Kuma wannan gidan da kake gani da ribar
da na samu a shekara É—aya na gina shi, amma insha Allahu zan gina wanda ya fishi nan gaba kaÉ—an.
Numfasawa Anas yayi ya ce "Baffa haka Allah yake yin lamarinshi, idan ya soka da arziƙi yanzu ne zaka fi kowa, haka idan ya soka da talauci babu wanda ya isa ya fitar da kai daga ciki idan ba shi ba" "Wannan gaskiya ne Anas" cigaba Anas yayi da cewa "Amma Baffa shi kuma Baffa Sa'ad me ka yi masa?" murmushi Aisar yayi ya ce "Ai na gina masa ƙaton gida, a can unguwar Ƴar akwa kuma na bashi naira miliyan ɗari yayi jari, yanzu haka ma ya samu labarin dawowarka yana hanya zai zo ku gaisa......
Hussain YusufâœðŸ»
[12/9, 4:38 PM] ~HUSSAIN YUSUF~: *ANAS MALEEK*
*NA*
*HUSSAINI YUSUF*
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}
https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_
*Alk’alaminmu 'yancinmu*
*Page 49/50*
Murmushi Anas yayi ya ce "Baffa da ka ce masa ma ya zauna sai na je har gidan nasa na gaida shi".
"Anas kenan ka san halin mutumin naka da gardama, wallahi sai da na faɗa masa haka amma furr ya ƙi amincewa lallai sai dai ya zo da kansa ya sameka, a cewarsa kada a wahalar da kai.
Kafin Anas ya furta wani abun suka ji sallamar Sa'ad ya shigo cikin falon, da gudu Aisar ya je ya tare shi yana ce wa "Baffana sannu da zuwa da ka bari ma ai sai na zo da kaina mu gaisa ba sai ka zo ba" murmushi Sa'ad yayi ya ce "Ai zuwan da nayi yanzu, don na matsu na ganka ne shi yasa, amma ai na san zaka zo inda nake Anas É—ina."
Dai-dai lokacin su Nasreen da Safna da kuma Basmah suka fito daga ɗakinsu, cikin shirin tafiya school. Basmah ce ta hango Abbanta da Momynta a zaune, da gudu ta ƙarasa wajensu ta rungume su tana tambayarsu yaushe suka zo.
Sa'ad ne ya daka mata tsawa ya ce "Ke har yanzu ba ki daina wannan rashin hankalin ba ko? Ko haka ki ka ga sauran Æ´an'uwanki sun yi?"
"Haba Sa'ad me kuma yarinyar nan ta yi fisabilillahi, murna fa take yi da ganinku amma sai ka hau ta da wannan faɗan kamar za ka dake ta?" Cewar Aisar yana mai jin haushin Sa'ad akan takurawa Basma da yake yi, shi yasa ma ta zaɓi ta zauna da su Safna don ta daina fuskantar faɗan da take sha a wajen mahaifinta. Kamar ba shine ya haifeta ba haka yake rufeta da faɗa kullum ita da gidansu bata da sukuni, wannan halayya ta Sa'ad tana matuƙar ɓatawa mahaifiyar Basma rai, musamman idan ta kalli yadda Aisar yake tarairaiyar su Safna da Nasreen sai ta ji ina ma a ce haka mijinta yake yi wa tilon ƴarsu Basma, da ta fi kowa farinciki da jin daɗi, kullum idan sun zauna ban da aikin faɗa masa illar da abin da yake yi wa Basma take yi amma ya ƙi fahimta kwata-kwata.