Gabatarwa
Abu Cikin Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 414 min read
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
BISSIMILLAHI RAHAMSNIN RAHIM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI INA GODIYA GA ALLAH DAYA BAN DAMAN FARA WANAN LITTAFIN, UBAGIJI INA ROKON KA YADDA MUKA FARA A SA,A MU KARASA SHI CIKIN FARIN CIKI DA JIN DADIN JUNAN MU.
YAN UWA MASOYANA HAR KULLUN INA MAI KARA BAKU HAKKURI DA KUYI HAKKURI DA ZAMAN TARE ZOMU ZAUNA ZOMU SABA DA FATAN ZAMU FAHINCI JUNA DAKU DON SAI KUN KARA HAKKURI DANI SAMA DA FARKO A YANZU KASANCEWA ZAN HADA TAURA BIYU A BAKI LOKACI GUDA.
BADON KOWA BA NAI HAKA DON KUNE MASOYA NA MASU KAUNATA A KULLUN FARIN CIKIN KU SHINE NAMU DON DA BAZAN KU MUKE RAWA A KODA YAUSHE.
FADA KARWAN DAKE CIKIN LABARIN NAN UBANGIJI YASA MU AN FANA DASHI AKAN MU DA YAYAYEN MU ALLAHUMA AMIN.
DARI UKUNE HAR YANZU BAN KARA BA IDAN KINA SO SAI KU TUNTUBENI A LAYINA DON HAR YANZU DASHI NAKE AMFANI BUT ONLY TEXT DON DA WUYA KIRA YA SHIGO MIN A NAN YANZU.
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MTN KO EIRTEL NAGODE ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMIN SHI AMIN.
A hankali take saukowa daga matakalan jirgin jirgin mai tambarin Nigeria Air way daya sauka a filin jirgin malam Aminu kano.
Fuskanta yana saye da bakin glass din ido sai takunkumin dake saye a fuskan nata bayan ta yan samari biyu ne masu tsanin kama suna mara mata baya.
Doguwar rigace baka a jikin ta sai gyalen shi data yafe har zuwa kanta takalman dake kafanta flat ne basu da wani tudu sosai .
Sai handback din hannun ta data riko wanda ba wani babba bane sosai dan madaidaici dashi.
Kallo daya zakai mata ka gane hamshakiyace ita din don siffan shigar da tayi kawai ya isa ya nunama hakan.
Hjy Iyami ke nan matar tsohon Ambasardor din kasar America wanda ya wakilci Nigeria a 1986 zuwa 93 .
A hankali ta runtse idanuwan ta kafin ta bude su ta kara kallon yanayin kasan nata na haihuwa wanda a yanzu ya zama mata abin kallo.
Duk da dadewan da tayi bata a cikin kasan hakan bai hanata ganin wasu abubuwan da ta bari ba a tsawon shekarun data kwashe bata kasan.
Da mamaki irin halin gwauntin kasan ta Nigeria a ranta taci gaba da saukowa a matakalan jirgin sannu a hankali duk da yanayin kasan nata hakan bai hanata son ganin ta dawo kasan ta na gado ta zauna tare da iyalan ta ba.
Easy hajjajo daya daga cikin samarin dake bayan ta ya fada don ganin irin yadda take bin ko ina da kallon mamaki don rashin ganin wani cigaba da da kasan tayi sosai a zuwa nan lokacin data dawo.
Don tun bayan barin mijin ta aiki sai take can da iyalinta dake kararu inda itama take aiki da wani company a can hakan ne ya dauke mata hankali da gida sosai.
Sai yanzu take ganin dacewan dawowa gidan a cikin yan uwa da abokan arzikin su da suka bari badon komai ba sai don tarbiyan yaran ta da jikokin ta dake tasowa yanzu.
Saboda yawan haramtatacen al,adan da yanzu ya mamaye duniya sai take ganin namu tarbiyan na malam bahaushen kamar daban yake da sauran tarbiyan wasu al,umman na duniya a yanzu .
Don shi malam bahaushe yana mayar da al,ada ya zama addini sosai a gareshi balle kuma abinda addini din ya koyar damu.
Duk da lalacewan duniya a yanzu malam bahaushe yayi kokari wurin ingata wasu tarbiyan da su koma kamar addini a garshi wanda yake taimakon al,umma a yanzu.
Hakan yasa ta yanke shawara ba tare da zaunawa ta shawarci kowa daga cikin a halin nata ba a yanzu da take shugaba a gidan ga baki daya.
Ba karamin tashin hankali ta fuskanta ba a gurin yaya da jikokin ta don jin zancen komawa sun gida Nigeria da sukayi.
Wanda hakan yasa ta rufe ido taciwa kowa daga cikin su mutumci kan umurni ta bayar ba rokon su takeyi ba.
Hajiya Iyami bata fada ma kowa ba saida komai ya gama kammala daga banhareta a yadda take son komai yazo mata daidai idan sun dawo.
Gama daga gyaran gida zuwa company da sauran abubuwan rayuwa ta rigada ta kammala komai yadda zai tafi mata idan sun zo ba tare da sun sha wahalan komai ba tunda akwai kudin su ta fitar aka aiwatar masu da komai yadda take bukatan shi.
Har zuwa yanzu da Allah ya nufa sun tataro sun dawo Nigerian da zama inda duk tawagan nata suke ransu a bace don suna ganin ta rabosu da rayuwan inda suka saba dashi yanzu ta kwasosu zuwa kasan da duhun kai da jahilci yayi katutu a ko ina.
Alhamdullahi a bangaren hjy don ta isa da kowa na ahalin nata daga mazan su har matan su babu mai iya musa mata ga bukatan nata idan ta fada.
Haka yasa abin ya kara zuwa mata da sauki sosai don bata samu tangarada a kowan su ba sai gun babban danta koshi ta daga mai kafa saboda irin aikin shi ne a can don shi tun gama karatun shi yake zaune a kasan chaina inda yake aiki tare dasu.
Ta yarda da imanin shi dari bisa dari don ta auna shi taga yana da riko da addinin shi yana kan tarbiyan da suka bashi tun farko.
Wanan dalilin yasa ta yarda ta barshi a can inda yake aikin wanda a yanzu zamuce shine dauke da nauyin komai da kowa na ahalin don iya sarrafa na,uran computer daya iya da wasu fasahana zamani kasan na chaina ta dauke shi yake aiki tare dasu dama wasu company na kere keren zamani.
Motocine a jere a da suka zo daukan su wanda duk gaba daya nasu ne da aka saye da sunanyen kowa a gidan.
Baya bo ba fallasa fuskan hjy iyami a dan sake tana farin cikin ganin yan uwanta dana mijin ta da sukazo filin jirgin don tarbon su.
Aka dan gagaisa a gurguje inda kowa ke son nuna kulawan shi a garesu kamar dai yadda akeyi ga kowani mai hali a cikin zuria,
Bayan shigar su motane inda sai a lokacin ta fata samun natsuwa a hankali ta runtse idanuwanta tana mai tuno da mijin ta marigayi Alh ma,azu ambasado.
Wanda shine dalilin gatansu a yanzu har suka kai hakan ga Allah ya azurta yaran su da ma wasu dake zaune a karkashin inuwan su ta sanadiyar shi.
Saidai ubangiji bai nufi yaga wanan baiwan ta yayan nasa ba a duniya don yanzu shekara kusan goma ke nan da Allah ya karbi rayuwan mijin nata.
Duk da hakan suna zaune a can waje kamar yadda suke zaune tun farko da yake raye rasuwan shi bai sa sun dawo gida ba tun wanan lokacin saboda aikin ta dana yayan ta da sukeyi a can.
Dan tafiya sukayi kasancew nisan kano da kaduna ba wani tazara mai tsawo bane sosai yasa basu kara wani wahala ba sosai.
Duk hjy na cikin halin tunanen irin rayuwan da zasuyi a nan din yanzu cikin yan uwa da abokan arziki a haka suka shigo garin kadunan don ita bata ga wani nisan tafiyan da yaran nata keta faman jan tsukin nisan sa ba .
A nan ma sun samu dandazom yan uwa na kusa da suka cika gidan suna murna da zuwan wanan family din.
Anci ansha an gagaisa tare da tambayan bayan rabo inda yaran nata da duk mazane sai autar ta da matar danta dayayi aure saidai bata yarda ya auri yar can ba yar nan cikin dagi ta aura mashi aka kai mata ita can suke zaune lafiya da ita don iya zama da sarakuwar nata da ta iya.
Tun wanan ranan rayuwa ta koma masu sabo a gidan ga yan uwa na nisa da kusa dasuke zuwa taron su da murnan dawowan su gida lafiya.
Dawowan ta kasan yasa ta dauko diyan yan uwa mijin ta mata biyu ta hada da yarta suke zaune a tare.
Saidai asali ba itace ta dauko su ba sudin ne dai sukaga wurin zama suka zauna a gidan tare dasu.
Hajiya bata nuna komai ba illa kara jan su a jikin da tayi suka zauna a tare da sai yar sister daya suka cike su hudu yan mata a gidan.
Rayuwa na jin dadi da sakewa sukeyi don hjy iyami na tsaye da saka ido ga motsin kowa a gidan.
Saidai ta fanin karatu da jin dadin rayuwa a cikin gida duk abinda suke so a ransu tana ganin ta kawar masu da shi don kawai kada su gani ga wani har su saka rai sukai ga dauko mata magana.
Ta farko itace salma yar gurin kanin mijin nata dake kula da duk wani al,amarin su daya shafi gida don shi suke sakawa a gaba tankar maigidan nata yana raye don mutumin yana da fahinta dakuma biyayya daya dace.
Sai Rufaida diyar autar su maigidan nata dake aure a jos a can suke zaune da mijin ta da yaranta Rufaidace yarta ta biyu itama dawowan hjy nan kasan .
Daga zuwa da sunan hutu tun lokacin bata koma ba take zaune tare dasu don jin dadin irin rayuwan da ake a gidan.
Sai ta uku jamila ke nan diyar autan su hjy da ita kanta hjy ta dauko ta don ta sahalewa yar uwan nata nauyin yaran da suke a gaban ta zata debe mata wani kewan itama a matsayinta na yar yar, uwan haihuta.
Tankar yar cikin ta take ganin ta a wurin ta don hakan ta daukesu gaba dayan su tankar diyan data haifa a cikin ta suma ba laifi a nasu bangaren hakan suke kokarin nuna mata kamar yadda itama din take kokarin nuna masu duk daya suke a wurin ta.
ANCAU
Tun a soron gidan nasu take jiyo muryan Asabe kakar su data haifi mahaufisun tana faman zazzaga bala,i.
Dukda bata shiga gidan ba tasan bada kowa Asabe ke wanan fadan ba haka illa da mahaifiyar su.
Don inda sabo aita saba da wanan hali na Asaben don tun bata da wayo da wanan hali ta bude idanuwanta a gidan.
Kusan kullun fitinan Asabe ne ke tayar dasu daga barci na yau daban na gobe daban.
Yau ma daga inda take take jiyo muryan Asaben tana fada akan iccen girki da innar tasu.
A haka ta karasa ciki rai bace duk da gajiyan ranan data kwaso ga yunwa ga kishin ruwa don tun safe da ta fita bata karya ba .
Hakan kuma ta juyo gida da kafa duk da nisan dake akwai daga makaranta zuwa gidan su.
Shigowan Abu gidan bai hana Asabe fadin abinda take fadawa mahaifiyar tasu ba a lokacin.
A daidai lokacin inna ke fadin adan maraice umma dama ba wani icce mai yawa bane dashi nayi koko da safe yanzu kuma na danyi muna danbun tsakin da akwai don yaran nan idan sun dawo su samu abinci.
Duka bakin wutan baifi guda hudu da guntu indon ruwan dumine barin hada gawayin nan sai ruwan yayi dumi ki samu ki watsa din.
Salman Abune yasa su juyowa gaba dayan su sai dai inna ce tayi karfin halin anwa a lokacin duk da tana cikin rudu da rikecewan bala,in Asaben.
Asabe na fadin to sannu issasa mai diya ke kika san zafin diyan su kin iya kokarin nema masu abinda zasuci.
Niko nawa dan dabai damu dani ba ai haka yasa kafa ya fita bai damu yasan da damuwata ba.
Saukin abindai kema yaya matane a gaban ki, kinkin zuciya duk da gorin da kike sha a gari ki haifa mashi ko da naji dayane da zai taimaka mai idan karfin shi ya kare yasan yana da magaji.
Ke kenan kullun dauksn ciki kina zuba mai diya mata a gida yau ace kitso gobe kumshi sai ko na omo.
Ta yaya zai samu ya aje kullun laluran su yana kara yawa gareshi kullun yana fita nema ba matai maki sai Allah.
Da maza kika haifa ai zai sa ran zasu taimaka mai a wani gurin ga wanan data saka kanta wani karatun boko da baida amfani a gurin ya mace.
Abu dake kallon ta da mamaki tana cire takalmin makarantar dake kafanta wanda duk ya sude a titi saboda rana da yawan bin hanya ga ba kudi balle a saya mata sabo dole haka take maneji dashi.
Saukin abin ma yanzu duk da karancin shekarun ta amma haka ta samu don kokarin ta ba,a taba mayar da ita baya ba har takai aji shida tana neman fitane yanzu.
Duk irin matsin da Asabe kewa mahaifi su akan karatun nasu baida wani rana garesu kasancewar su na yaya mata gareshi.
Don a cewar ta aure zata masu da zaran Abu ta cika shekara goma sha biyar da haihuwa a duniya don ko yanzu wasu daga cikin sa,annin ta sun riga da sunyi aure suna gidajen mazan su zaune daram.
Muryan Asabene ya dawo da ita ciki tunanen da takeyi tana fadin ke kuma munafuka ki kura mi ido kuru kuru kina kallona dasu.
Don rashin kunya rashin tarbiyan da baku samu ba tun farko ga uwar ku babba na magana yara suna kashe shi da ido don rashin kunyan da kuka gada a wurin uwar ku.
Karya nake fada ba gaskiya na fada ba komai ya samo yana gurin ku keda yan uwan ki da makiran uwar ku ku gaku ga bawa na haifar maku ko ?
Ice ma da mutum zai saka ruwan dumi ace an kona shi a gidan nan gaba daya wanan wani irin masifane yaron nan ya haifar min a gidan nan.
Baki na turo gaba don jin irin cin zarafin da kullun Asabe ke muna muda mahaifiyar mu har wata rana takan tsaya sai baba ya saki inna ko kuma ya kara auren macen da zata zo ta dinga haifa mai diya maza a gidan mu.
Da kyat Abba da wasu makwabta sukan iya shawo kan Asabe idan ta fara wanan bambamin nata lokacin.
Inna dai tana duke a bakin murhu tana kokarin hura wuta da gawayi ne data dan kashe dazun sai faman fifita wutan take don ya kama.
Daki na shiga na kwabe tufafin makaranta dake jikina don sanin bamu da clean din da zamu wanke a yau don gobe haka yasa na kwabe su na baza a dan gambun langa langan kwanon dake kofan dakin namu nafito.
Wurin madafin namu na hara ina fadin inna kawo in hura kije ki huta hakana da ranan nasan tun safe baki huta ba.
Barshi inna ta fada tana kokarin boye fuskanta gare ni don kada inga hawayen dake zubo mata a idanun ta a lokacin.
Wanda nasan ba komai inna kewa hawaye ba sai gorin diya matan da Asabe ke mata don indan don fadan barana da Asabe ke fadin tanayi ne ta saba da wanan sai dai wana gorin ne inna bata iya shayewa a ranta sai ta nuna gazawan ta anan.
Da kyar inna ta yarda ta bani maficin tana fadin kije ki huta yar mairo dan inna bata kiran sunana kasancewata yar fari a garesu.
Ina tsugune bakin murhun Abba ya shigo gidan da kayan aikin shi idannun shi ya sauka a kaina yake fadin yar mairo kece har kika shiga girki daga dawowan ki haka?
Dagowa nayi daga inda nake ina fadin Abba sannu da zuwa na nufo shi don amsar ledan dake hannun shi.
Bayan na karba na juya don zuwa dakin su in aje Asabe ta fito tana fadin to to mai zaki tura daki daga kawowa yar nema data gaji kilibibi a gurin uwarta.
Kai haba umma ba komai bane a ciki sai dan garin tuwo da kubewa ko za a samu a dan tuka da dare a samu naci .
Don na fita dazun ban samu bada ko sisi ba a samu ko abin karyawa a gidan nan ina can na damu da tunane tun safe ina faman babu kwasta duk masu zuwa sai cewa suke ai masu bashi idan sun samu zasu kawo kudi.
Kai Amma mutane sun lalace yanzu da son bashi facin ma shi kanshi bashi za ai masu shi kai Allah ya rabamu da fititinun duniyan nan .
Sai lokacin Abba yakai kasa yana fadin barka da wuni umma mun wuni lafiya ya gidan kuma.
Mun wuni lafiya ba lau ba dai tunda ko ruwan da zan dan samu in watsa a gidan nan ban kaiga samu ba har yanzu.
Don kawai nace bazan iya wanka da farar safiya ba sai kawai a hana min ruwan ina kallo wanan matar taka ta hura wuta a gidan nan har ta gama abinda take saida taga icen ya kone ga baki daya .
Amma yarinyar nan ta kasa saka min ruwan dumi in watsa don bakin ciki da rashin sanin muhinmancina a gidan nan.
Daga inda Abba yake tsaye yana jin Asabe takai ayah yace kiyi hakkuri umma .
Kin sa halin da nake ciki yanzu aikin ne nawa babu kasuwa ko ina ya rufe yau kwana uku sai ita saudatune ke dan dabara a cikin aljihun ta muna samu muna dan tabawa.
Asabe tace da mamaki karara a fuskan ta take fadin haka ka koma ban sani ba dan nan ?
Kai bakaji kunyar fadin wai ashe mace ke ciyar damu duk kwanakin nan a gidan nan ba.
Mafarin abin gari ana yadamu da fadin talaucin mu yakai haka har mace ce take ciyar damu a gidan nan kai ka kasa.
Kaga amfanin haihuwan da namijin da nake fadama ke nan da yanzu yarinyar nan namiji ne aida ta fara taimaka maka ta wani gurin.
Inna ta fito dakin ta nufi wurin madafin danbun tsakin masaran data hadane ta shiga rabawa yayin da tsakar gidan namu yayi shiru kowa ya zuba idanu yana kallon inna.
Na Asabe ta fara zubawa ta mike ta nufo ta tana fadin umma akai dakine ko a kawo maki nan aje anan in gani Asabe ta fada a hasale.
Saida Inna ta kai kasa don girmamawa ta aje kwano a gaban ta inda take zaune saman kujera dan tsugunno.
Bude kwanon samiran tayi tare da juya dan danbun dake cikin kwanon a yatsune tana tabe baki kafinta dago kai tana fadin.
Saudatu wanan abincin fa kamar za,aba dan goye shi ta juya wurin Abba tana fadin ka duba dai ka gani da idanuwan ka yanzu dan abinda aka zubamin.
Don kawai kace itace ke ciyar damu a gidan yanzu ai dole wullakanci ya shigo a bani abinda akaga dama don kawai rainin da kaja muna don kasawan ka yanzu da gidan.
Umma ba hakana bane kiyi hakkuri tsakin ne baida yawa iyakarshi ke nan dan gyara don yaran nan dake.
Nasan nida malam ba samu zamuyi bama a karshe tace duk da haka a kara min don wanan dai ba isane zaiyi ba ehhe.
Kallin Asabe nayi lokacin da naji ta fadi hakan ina mamaki hali rashin tausayi irin nata duk da jin zancen inna din da tayi.
Dakuwa ta jefo min da hannun tana hagu tana fadin daina kallo na yan nema mai kama da yanyawa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL TA BANK KO KATIN WAYA DON TURAWA A BANK ZAKI IYA TURAWA A WANAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK ALLAH YA BADA IKON BIYA A CIKIN DAUKI AMIN
Ki daure ki guji shiga hakkin wani abinda ka raina shike zama babba gareka don Allah yar uwa mu guji daukan hakkin a kan mu ki daure ki biya ki karanta don Allah.
Hjy ce zaune a falon ta hannun ta rike da waya kaya take oder da za, a turo masu dan yanzu ba sai ka fita zuwa waje ba idan kasa hutar da kanka waya ya wadatar da komai ga kowa.
Sallaman da akayi daga kofane ya dawo da ita cikin hankalinta ta dago kai tana kallon kofan shigowa falon nasu.
Da fara,a a fuskanta tana aje wayan daga gefen kujera take fadin kune tafe sannun ku da zuwa a cikin fara,a kamaf yadda ta saba tarbon duk wani dan uwa da zaizo gidan musanman daga bangareta kona mijin ta .
Yanzu ma yan uwan mijin tane su biyu sula shigo gidan barin abinda takeyi tayi ta tari bakin nata.
Yau kan mun taki sa,a kina waje don zuwan mu biyu ana fada muna kina ciki bazamu ganki ba.
A daidai lokacin ta sauke glass din dake idon ta tana fadin abako fada min zuwan ku ba gidan nan ko sau daya.
Dayan tace yau dai aimun taka sa,a mun samu kina wajen dan dariya hjy iyami ta sakeyi tana fadin mun dade bamu haduba.
Safiya ya bayan rabo wace ta kira da safiya tace wallahi haka al,amari yakan kasance ai rayuwa ke nan idan na tuna baya sai nakanji kamar abubuwan da su dawo sabo.
Dariya sosai hjy iyami ta sake tare da fadin kin tuna zamanin kurciya ke nan dai ga wanan zancen naki.
Safiya ta lumshe ido tana bin lafiyan kujera sanyin AC yana ratsa jikin ta a hankali tare da fadin bari matar yaya ai kowa tuna bara baiji dadin bana bane.
Jin hakan hjy ta fahinci mai take nufi yasa tayi saurin kawar da zancen tana fadin bari a kawo muna abinci muci nima yanzu na dawo gidan .
Yau na fita ziyarane har gidan su Ado da salihu nake don tun zuwa na garin ban leka kowa ba bako dadi mutum yana kulaka kai baka mayar da kara akace.
Tana fadin hakan ta mayar da hankali kan wayanta dake gefe dauka tayi ta kira mai aiki tare da umartan a kawo masu abinci tana da baki a falo.
Kai matar yaya wai wasu baki har yanzu dai wanan halin naki yana nan ashe ance idan kasan mutum ko shekara nawa ne kada ka tambayi halin sa.
Murmushi hjy tayi tana fadin meye duniya sa,ade wanan duniyan har nawa yake ga bawan sa.
Idan badon muzo mun gani da idanun mu bazamu taba yarda da kina nan a yadda kike ba a yanzu.
Wai sa,ade ina da wa yanda sukafi min kune a rayuwa duk mace mai hankali da tasan ya kamata ai baki nata ba ko yaya yake kuwa.
Don samun duniya sai idon ka ya rufe ka mata da goben ka ko makomar yayan ka yau fa in mune gobe bamu bane.
Wani lokacin koda kana raye sai kaga anayi ba tare da kai haka abubuwan suke zuwa ai kinga gara mutum ya gyara tun duniya bata kisa ba.
Mai aikin data kirane ta shigo dakin dauke da katon ture da manyan kuloli abinci saman shi dining ta nufa da zuman jerawa yadda ta saba.
Sai hjy iyami take fadin ki kawo muna nan yau a kasa zamu zauna muci dan dariya suka kwasa tare da fadin za a tuna da baya ke nan dai.
Lokacin da yaya yake aiki lagos muna gida tare dake ake zuba abinci a cikin katon ture mu taru munaci ana hiran arziki.
Ai wanan abin duk shigowan sadiya ya kawar muna dashi tana fadin wai muna taruwa ana gulmanta bazan manta da zuwan wanan yar uwan hjyn mu datazo daga kauye take fadin kema ai saiki fito ayi gulman dake.
Budan bakin sadiya sai cewa tayi ni ba zan shiga cikin su rainani ba ko ita wanan don diyan tallakawane ita bata san kanta ba.
Dan murmushi hjy iyami ta sake don tuna wanan labarin da safiya ke fadi yanzu sa,ade tace yau ina arzikin nata dana gidan su datake tun kaho dashi din.
Duniya ke nan alokacin tana dauka tafi kowa da komai bata san me gobe zai iya haifa ba a gare ta.
Hjy ce ke fadin bissimilah ku muci abinci ko juyowa sukayi a lokaci guda suna kallo abincin da mai aiki ta hada masu gwanin ban sha,awa kai kace wani dinner aka hada hakan .
Haka kamshin shi abin sone ga mutum balle ya kai ga baki yaji dandanon shi.
Daidai hjy na zama a kasan take fadin ance yanzu koyarwa kikeyi safiya ke kuma sa,ade nursece asibiti ?
Ashe kina da labarin mu ke nan har yanzu tana daukan cokali take fadin haba aiba zan taba mantawa da kuba a rayuwana .
Adaidai lokacin data fara bude kulan tana mika masu plate a gaban su da spoon da fork ga kofuna da lemoka don sha aka tabardar masu.
Nan kowa ya shiga dirkawa cikin sa abinci suna danci suna taba hira yayin da sanyin AC ya fara ratsa jikin su.
Sai da anty safiya ta hadiye naman da take tauna a bakin ta na kaza take fadin a gaskiya mun gode daz bamu lokacin ki da nuna rashin kyama ko babbanci a garemu yadda ake nuna muna har yanzu a gidan mu.
An mayar damu bare a cikin dangi duk kokarin da baba yayi yaga ya hada kan zurian shi kafin ya bar duniyan nan .
Zan iya cewa daga ke sai mijin kine baku nuna muna wani bambanci a tsakanin sabanin sauran dake yawan nuna mu barene a cikin su ko yaushe wani abu idan ya taso na family din mu.
Din kawai mu uwarmu kadai ta haifa a cikin su lokacin da yaya ke raye yana iya kokarin shi damu amma tun bayan rasuwan yaya din abubuwa suka kara lalace muna ga baki daya.
Wani abin saidai mu tsunci labarin faruwan shi a gare bamuci arzikin da za,a fada muna ba mu.
A hsnkali ta lumshe idanuwan ta tana maijin zafin yadda ake yawan nuna masu a cikin yan uwan su din.
Tace ku dauka har yanzu ma yayan ku yana a raye ne safiya don ya barni ya bar zurian shi komai ke damun ku kofa a bude yake dakuzo da bukatan ku nan mudin dai abin baifi karfina ba agidan nan.
Sallama yan matan hjy ne da suka dawo daga school saida su ukune kawai don farida yar wurin hjy ba a kaduna take karatun taba tun dawowan su suka sama bata gurbin karatu Abuja can take zaune tana karatun ta.
Sai hutu take dawowa gidan haka yasa idan ba hutu akeyi ba zaka gansu su uku ne kawai a gidan.
Kansu a sama suka gaidasu kamar basu sheda ko suwaye su din ba garesu don kawai raina masu arziki da sukeyi.
Safiyace take fadin wai ba Rufaida bace da salma nan dan juyowa salma tana fadin nice daga haka tasa kai tana kokarin shigewa daki.
Rufaida salma kuzo nan hjy ta fada a kausashe saiga su sun dawo da sauri suna fadin gamu mommy ta nuna su safiya da hannu tana fadin baku san wa yan nan bane halan ?
Mun sansu mama gwaggo safiyace da gwaggo sa,a salma ta fada a dan yatsune kafin hjy tace duk da kun san su saidai kamar baku san yaya suke da mahaifan ku bako ?
Nan kan shiru sukayi suna kokarin dukar da kawunan su kasa don sun fahinci mai hjy take nufi da fadan hakan.
Karna kara ganin kunyiwa wani babba wanan gaisuwan koda basu din bane wai salma sai yaushe zaku gyara halin kune don Allah ta fada a dan hasale .
We sorry mommy gajiyace dama ya hana mu tsaya dan Allah ku ban guri marasa ta ido kawai ta fada a dan hasale.
Bayan shigewar su dakunan sune anty safiya ta sauke ajiyan zuciya tana fadin kindai gani yanzu ke nan ai.
Wanan ba akidar kwarai bane ka nunawa yaro ga yadda kake da dan uwanka har abin yazo ya shafi naku yayan nan gaba.
Mikewa sa,ade tayi tana fadin antyce ma dai ta damu da wa yan nan mutane, nina dade da zubar da duk wani wanda ya nuna baison wata alaka zumunci dani ai.
Zancen ta baiwa hjy dadi ba ta fahinci akwai bacin rai a cikin halaiyan da yan uwa ke nuna masu kasancewar su su biyun yan uba ga yan uwan haihuwan nasu.
Sallama sukaiwa hjy tare da mata godiya da nuna jin dadin su irin taron data nuna masu din bata nuna masu halin da yan uwa suke nuna masu a cikin su.
Ita kanta bata samu mahaifiyar su a gidan raye ba saidai ga yadda take jin labari zamane akayi bana dadi ba a cikin gidan lokacin da mahaifan su suke a raye wanda itama ta dan ga wani abu a rayuwan datayi dasu gidan kafin Allah ya azurta mata mijin ta harsu bar gidan zuwa lagos karshe ma suka bar kasan ga baki daya.
Lokacin ita kanta sarakuwanta tana yawan nuna mata tayi hankali da yaran don su din ba jinin taz bane diyane kawai na maigidan ta da aka haifa mai auren baya daya kara na karamar yarinya daya auro.
Ga yadda take ji sarakuwar ta itace mata ta farko a guri mijin su saida sukai kusan shekara hamsim a tare ya auro mahaifiyar su safiya din.
A cewar hjy ita ba a hadawa diyan ta yan uba don haka ta hana mijin nata kara wani aure daga baya .
Surukin nasu yana sana,a a kauye har ya shigo birni ya fara sayar da kayan mata irin su dan kune da sarka da jakkuna.
Daga baya kuma daya bun kasa ne ya fara sayar da gwala gwale wanan ne ya kawo mai tarin arziki mai yawa har ya tamfasawa iyalan shi katon gida da suke zaune a ciki.
Bawai bokaye kawai ko asiri taga sarakuwar nata nbi ba saidai iri matan nan ne masu ji da izza da isa da gadara wanda take ganin yanzu diyan nata da jikoki suna koyi da wanan halin.
Saidai daga bayane kariyan arziki ya afkawa mijin nasu bayan siyasan shehu shagari da mazajen arewa da dama suka samu wanan koma bayan a sanadiyar canji da gwaunatin soja mai a lokacin ta kawowa mutane yayi sanidiyar karewa wasu bayin Allah da dama a cikin su har da surukin nata ya samu wanan iftila,in tare dashi.
ANCAU KADUNA STATE
Kamar yadda Asabe ta sha alwashi akan Abban mu dole sai ya kara aure hakan ne ya faru don Asabe taje nema mashi auren yar wata mata da ta dade tana zawarci batai aure ba a kauyen mu.
Tun innan mu bata san wanan zancen ba har yakai ta sani saboda bakin Asabe dake sake suratai barkatai na rashin ilimi da jahilci tare da kiyayya ga inna damu diyan ta.
Da yake Allah yayi inna mu mace ce mai hakkuri da kawar da ido ga komai koda tasan kaine ke cuta mata din.
Sai ma bata nuna tasan Asabe nayi ba a gidan don bata nuna damuwata ga abinda Asabe ke yawan fadi ba ko yaushe.
Mu kan mu bamu tsira ba gurin Asabe don tana nuna muna tsana karara kamar ba jinta muke ba mudin .
Daga zagi sai dungura dan abu kadan yanzu zata sauke muna bala,i a kanu komai mukayi bamuyi daidai ba.
Ainihi Asabece mahaifiyar data haifi mahaifin mu ta hayayyafa da dama basa tsayawa da sun dan tasa an yayesu sai zazabi ya kama su su mutu.
Sai ya kasance ga mahaifin mu ta samu ya fara tsayawa sai mace da muke kira da gwaggon birni don a birni take yanzu da mijin ta daya samu wani ubangida a can ya daukesu bayan aure ya mayar dasu a birnin.
Sai ya kasance mahaifin mu yanzu kawai a gaban ta sai yan jikoki da take dashi ta tsatson shi wanda kiyayyan fitowan mu diya mata a duniya yasa bata kaunar mu har cikin ranta.
Ni dana dan kawo wayau a cikin mu nasan halin da muke gidan na zaman Asabe da innar mu don su sauran yan uwana gorin inna bai taba tayar masu da hankali ba sai ma kawai ja baya da sukayi da al,amarin ta.
Don yawan fada da zagi da take muna a gidan duk da Abba ya dan kewayewa Asabe gefen ta ma,ana ya dan raba tsakanin mu da ita sai dai hakan bai hana Asabe fitowa zaman sa ido ga inna damu.
Wajen karfe dayan rana kasancewar yau asabar muna gida bamu zuwa boko mun dawo islamiya tun sha daya muna gida.
Ina daki ln mu na yara don shigata ke nan na gama wanke tufafin mu da suka dan taru nayi wanka ina shafa mai.
Naji muryan innar mu tana kwala min kira da yar mairo na amsa da Na,am inna daga dakin tare da saka hijjab a jikina na fito da sauri.
Ina fadin gani inna tace yi maza ki dauku abincin nan ki kaiwa umma kada yayi sanyi nace tau inna tare da dukawa na dauki kwanon samiran abincin Asabe.
Munace mata Asabe ne don dukka gari haka ake kiranta dashi in ka debe Abban mu da innar mu koshi Abba sai zuwan inna ne gidan ya canza mata suna dama da Asaben yake kiranta.
Na isa kofan Asabe ina ta sallama bata karba min ba haka yass na kunna kai dakin na aje mata abincin a gefen kofan ta kadan ko waige banyi ba na fito daga dakin.
Dawowa nayi na karasa shirina kafin mu zauna cin abinci tare da yan uwana don a tare mu hudu ake hada muna abinci don yana kawo dankon zumuci inji manya sukace.
Muna gab da gamawa sai ga Asabe tun kan ta karaso wurin mu take kwalawa inna kira cikin tashin hankali.
Gaba dayan mu hankalin mu ya koma gare ta muna duban hanyar kofanta tana zuwa take tambaya wa yakai min abinci a dakina ?
Cikin sanyi murya irin na innar mu da kusan kowan mu ya gado hakan take tambayan Asabe wani abin ne inna ?
A hasale asabe ke fadin tambaya nakeyi wa kika aika yakai min abincin don yanzu na aje dankali na fito bangani ba .
Haka yasa nasan duk wanda yakai min abinci shine ya daukan min shi dama an dade ana min sata a daki ina hakkuri banda dama in aje yan kwabbaina sai in nema in rasa.
Da sauri na furta Allah ya tsareni da daukan abin wani nina kai abinci kuma ko kallon dakin ki banyi ba na fito.
Ke rufa min baki kwadayayya satan naku har yakai haka ban sani ba dole in kira mai gyara ya saka min kuba a kofana don watarana kada kuyi min wanda yafi wanan.
Wani irin bakin cikine ya rufe ni a lokaci daya ina jin idona kamar zai rufemin a wurin don satan dankalin da Asabe ta laka min.
Da ba don nasan itace ta haifi mahaifin mu da naja mata Allah ya isa a gurin duk da hakkurin inna saida tayi magana wanan karon.
Haba umma a gabana yarinyar nan ta shiga takai maki abinci ta fito kuma ban ganta da komai ba a hannun ta.
Ai dada goyon bayan ta zakiyi ta fara mugun abu tun a gida idan yayi karfi sai ta zauna maki a gida ai don babu mai kwasan barauniya yakai gidan shi.
Abbane yayi sallama ya shigo ganin mu cirko cirko a tsaye bai hannashi fadin yanzu dankaline har yai yawa haka a gidan aka barwa Akuyan umma tana ci haka?
Gaba dayan mu kallon Asabe mukayi don jin abinda baba ya fada nan kuma ta fara kame kame tana fadin .
Hannu na dora akai na fasa wani uban ihu ina fadin Asabe mai nayi maki kika dafa min sata a gaban kowa.
Ashe akuyan kice ta daukar maki dankalin ki kazo kina fadin nice na satar maki harda kudi nake shiga dakin ki in sata.
Abba ya daka min tsawa tare da fadin ke ke meye haka kike fada da sauri kanwata Fatima dake bi mun take fadin Abba yanzu fa Asabe ta gama fadin wai Abuce ta sace mata dankalin ta a daki daga kawai takai mata abincin ta da innarmu taba takai mata.
A wani irin yanayi na bacin rai da mamaki lokaci guda Abba ya juyo yana fadin sata kuma umma ?
Ina yaran ne jinin kine umma koda itace ta daukar maki ai ba zaki kira hakan da sunan sata ba.
Ta daka mashi tsawa tana fadin yi min shiru wanda baisan abinda yakeyi ba.
Yau aka fara sata min abu a gidan nan bana magana don gudun irin haka in magana ku karyatani a gaban diyan ka da matan ka.
Waya sani ko itace ma ta dauko din ganin za,a ganeta ta jefawa Akuyan nawa.
Allah ya sauwaka Abba yace ya nufi hanyar dakin su bai shiga ba ya duka ya dauki buta zuwa ban daki.
Asabe ma ta juya zuwa sashenta tana fada inda take shiga ba nan take fita ba wai Abba da innar mun suna lalatamu da gurbatacen tarbiyan da suke bamu.
Inna kan daki ta shige tana kuka hankan yasa dole na tsayar da nawa hawayen don komai ya wuce a ran inna.
Tun faruwan wanan abin na ja baya da lamarin Asabe ba ruwa na da tsabganta iya kana da ita gaisuwa ban yarda in shiga ko lungunta.
Muna kallo idan jikokin ta na birni sukazo yadda take ji dasu take nuna kamar su kadaine ta haifi uwarsu sam mu bamu isa mu rabe ta ba.
Shi yasa ake fadin kakanni sun fison jika na wurin diya mace don ni na tabbatar da wanan maganan gun kakantamu.
Sannu sannu har lokacin Auren data nema wa Abban mu ya karaso buki ya tashi sosai Asabe ita tayi uwa tai makarbiya don Abba yace shi baida zarahin kara aure a yanzu.
Ta saka aka tayar damu daga dakin da muke kwana munaji muna gani aka gyarashi tsab wace kullun take kukan bata da kudi sai gata ta fitar da kudi don kawai taga ta kuntatawa innar mu rai .
Sai fadi take Allah dai ya kawo amaryan Abba tazo ta haifa masu magaji a gidan ko suma zasu shiga fagen zurian dake tun kaho da diya maza a gari.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL DON SAMUN SHI ZAKIYI TEXT A WANAN LAMBAN DON LAYIN BAYA KASAN A YANZU KO KI TURO KATI WAYA KO KI TURA BANK DA WANAN LAYIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK NAGODE DA KULAWAN KU GAREMU, , , ,
Ta dade zaune tana son mikewa zuwa daki don ta dauko takardan da take son turawa saidai jikin daya fara manyanta tana jin kiuya da nauyin tashi daga falon ta zuwa daki a lokacin.
Wani wawan tsuki taja a ranta take raya ya kamata dai ta samu wanda zai dinga taimaka mata wanan dawainiyar yayi yawa a yanzu gareta.
Wayan ta dake gefen tane ya dauki kira ta dauko tana kara jan tsuki sai dai ganin bakon lamba dake kiranta ne kuma ga layin special nomba ne ya bata mamaki.
Taso share kiran don bata san mai layin wayan dake kiran nata ba a lokacin wayan yana gap da tsukewane ta samu ta daga.
Muryan namijine yake mata sallama ta amsa da mamaki don har lokacin bata gane mai kiran nata ba dai.
Bayan sun gama gaisawa ne mai magana ke fadin hjy nasan ba zaki sheda mai kiranki ba a yanzu don an dade bamu hadu ba tun muna US rabon damu gaisa.
Sai mamaki hjy keyi a ranta tana fadin waye wanan kuma wanda ban gane ba dan tunane tayi kafin tace isma,il soba ko ?
Dan dariya ya sake tare da fadin abin mamaki gaskiya kinyi kokarin sheda muryana is about 20 years yanzu da bamu hadu ba.
Ai ba zan manta da muryan ka ba a duk inda naji shi ta fada tana daure fuska kamar wanda take wayan yana kusa a lokacin.
Yace hjy sai naji kina kasan har kusan shekara daya da rabi abin ya ban mamaki matuka har ki shigo kasan nan muna jaha daya ban san da hakan ba.
Yanzu ka sani ai wakila don bai zama dole irin ku su sanda dawowan nawa bane nan ta bashi amsa.
Watau halin na nan a yadda nasan shi hjy baki barin ko ta kwana har yanzu ashe ?
Jin tayi shiru ba amsa yace hjy dama naso muyi wani magana dake ne wanda ya shafi rayuwan ki sai dai naga kamar baki maraba da wayana a yanzu.
Kai isma,il kafi kowa sanin halina don haka babu abinda ya shafi rayuwan ka dani a yanzu dama nasan don ka bata min rai ka nemi layina don haka ina maka warning da kada ka sake kirana.
Dan murmushi taji ya sauke dama yasan za a rina idan hjy iyami ce don bata daukan maganin raini ko kadan.
Shidin yasanta ta dalilin yin karatu a tare ne duk da ya girme mata sosai ga haihuwa amma haka suke shan fama da ita don akwaita da kwazo da basira a lokacin da sukai karatun tana goyon danta na uku ne .
Kawar da zancen yayi ta hanyar tambayan ta yaran don sunayen su bai bace mai ba har wanan lokacin.
Wanan tambayan yaran daya jefo mata yasa ta dan sasauta mashi tare da amsa mai da suna lafiya .
Ance in kana son kama uwa rike yaranta yanzu zaka zama masoyi a gurin ta hakan ko ya faru da hjy har ta manta da fadan ta dashi take fada mai rayuwan yaran ta a yanzu.
Karshe dai yace sai sun zo don bashi kadai ne zaizo ba akwai magana mai muhinmanci da zasu so suzo yi da ita.
Nan ma saida hjy tayi korafi akai kafin ta kashe wayan tana kara jadda mai cewa idan yasan shirmene zai kawo shi kadama su zo din .
Shi dai dariya yayi yana fadin sai idan sunzo din zataji sukai sallama ya kashe wayan.
Kai hjy ta girgiza tana fadin mutane akwai tsegumi har suna daukan zancen abinda bai shafesu ba suna dangantawa da lamarin su.
Mikewa tayi don dauko takardan datake so daki har lokacin tana maijin zafi a ranta na ba gaira ba dalili wata kila kuma har yanzu haushin wayan da abokin karatun ta yayi matane oho ?
Kiuyan fitowa dakin tayi zuwa falon ta har akai kiran sallah ta samu ta mike don zuwa sallah.
Yanzu idan akwai abinda hjy ta tsana shine rashin son motsa jikin ta don hutu yariga da ya gama ratsa ko ina nata ga yaran da take zaune dasu baka more ne gaba dayan su son jikin su yama so yafi na hjyn yanzu don gatan da ake nuna masu.
Sai dai duk da hakan tana dan kokartawa tana sakasu wani abin can ba,a rasa ba sai dai zata sha mita da jini duk tana hakkuri da wanan.
Wani lokaci kuma zata zage tayi masu fada sosai akan rashin son motsa jikin da basa yi dan abu kadan zasuce sun gaji.
KAUYEN ANCAU
An kawo amaryan Abba wata bakace gajera bata da tsayi saidai akwai mazauna irin na mata gareta.
Ni dai banga abinda nagani gareta ba sai halin kiyayya kawai da Asabe ta dagwarawa mahaifiyar mu in bashi ba babu ta inda ta kama kafan innan mu.
Zaman su ba yabo ba fallasa don inna bata shiga tsabganta ko yaushe tana kofanta ita kuma amarya tana lungun Asabe.
Idan muna gida mune abokan hiran innar mu sai kuwa ranan da akace itace da girki ranan zan fara labe labe don ban yarda da tsarin Asabe ba .
Na cewa mu dinga kwana dakin ta haka yasa na share dan karamin dakin da ake tara tarkace a gidan mu dakin ba wani girma ke gareshi ba asalima madafane Abba yayiwa innan mu don da dama tana wahalan girki a ruwan sama.
Abba yayi fada har ya gaji don ko naje lungun Asabe da sunan kwana bana shiga dakin ta saidai in tsaya daga waje.
Idan na faki idon Abba ya shige zan dawo wanan dan dakin in kwanta dama mu uku ne masu dan wayau da muke zuwa kwana dakin Asaben.
Zakaji tunda asuba Asabe na fada wai an jawo mata kwanan wahala a daki yara sunzo sun hanata shakat daki suna damun ta da tusan dare ko tace wai an mata fitsari a daki.
Ranan da tace fitsari kanwata dake bi mun tace itama daga ranan a inda nake kwana zata dinga kwana don sherin Asabe ya isheta.
Sai lokacin Abba yasan ban kwana dakin dole yakawo ido yasa mun hakana muka mayar da dan dakin wurin zaman mu koda da rana ne a nan zamu zauna muyi tsabgogin mu.
Wanan baiwa Asabe ba don ganin yadda mukan saka innan mu a cikin nishadi wani lokacin har mu zauna ana hira da dariya .
Sai kuma hakan ya fara basu haushi suka kulla wani sherin a kaina wanda ya girgiza mu ga baki daya yan dakin mu.
Ranan monday da safe muna ta shirin makaranta tunda naga Asabe ta fito daga lungunta zuciyana ke bani akwai wani abu da zai faru a gidan don daga dakin da muke ina jin muryan ta a tsakar gida tare da Lantana Amaryan Abba suna dan zance kasa kasa.
Don ranan inna muce da girki a dan dakin mu muka kwana inna tunda ta fito ta dama kokon safe da zamu karya dashi kafin mu fita ta koma daki don ta shirya kananun da basu iya shirya kansu sai an taimaka masu.
Na fito da sauri kada in makara kofan innar mu na isa ina fadin inna ni zan tafi kada in makara.
Na juyo inda su Asabe suke da zuman in sallame su lokacin Abba daga daki yake fadin kin karyane Abu ?
Na karya na bashi amsa daga waje don ban shiga dakin ba tunda na girma innan mu ta koya muna hakan idan Abba yana ckin dakin namu.
Zoki karbi murtala ki rike ko fanke kya saya a hanya Abba ya fada daga dakin.
Tsiyan banza dama nasan kai ke koya masu kashin kudi don baka gudun Abin kunya kai kan wa yan nan yaya matan naka.
Karatun bokon dole duk yan uwanka wa kaga ya dage kan sai diya mace tayi boko haka ?
Badani za, ayi wanan abin kunyan ba kuke nan ko yaushe ku dorawa ubanku wahala don kawai baisan ciwon kanshi ba.
Gani kunan haihuwan yuyuyu da aka tara mai agida ace har mace bakwai ko daya ba kawar ba a cikin ku.
Daku da uwarku kunki ku barshi ya ji da abinda zai ciyar daku da wanda zai tara yai maku aure nan gaba.
Amma kullun in sata in maita sai ya lalube aljihun shi ya baku dan abinda ya kwana dashi ko kuma in bakuje makarantar ba uwar ku ta lalabe shi a daki.
To hakan ba zai yuyu ba don baku da uwar ku kadai na haifarwa shi ba don haka daga yau na kashe wanan bokon naki.
Aure zan maki shekara goma sha hudu ai kin isa aure har kina batun wuce munzali.
Gwanda ki tafi dakin mijin ki yaji da sauran yan uwan ki da suka rage kafin suma a fitar dasu sai gidan ya koma hondaku .
Bansan lokacin da Abba ya fito daga dakin inna ba don tunda ta fara magana na zuba mata ido ina kallon ta cikin al,ajabi da mamakinta.
Muryan Abba naji yana fadin haba dai umma aure fa yanzu ga Abu haba wani irin aure kuma kamar yadda taken nan.
Hae guda nawa Abu take da za ace za,ai mata aure a yanzu akaita gidan miji ?
Wani tsawa ta dakawa Abba tana fadin yi min shiru shanyaye kawai wanda baisan ciwon kanshi ba.
Dame su hansai da Adawiya suka fita ga shekaru da akai masu aure kuma suna zaune kalau a dakin mazan su har yanzu.
Abba yace Allah ya huci zuciyar ki umma ni gani nayi har guda nawa Abun take ne da za a ce aure yanzu.
To ai gaskiya umma ta fada inji lantana amaryan Abba ta fada aure ga ya mace shine wajibi.
Ba wani karatun boko ba can da yanzu shike kara lalata yara yanzu haka idan ance ma yarinyar mnan tasan komai game da aure kada kayi musu.
Ke lantana ahir dinki ga bata min diya da wanan kalamin naki sai Asabe tace kaji sauna yo ai gaskiya ta fada ko karya nakeyi Asabe ta tsatsareni da idanuwan ta na tsufa.
Bansan lokacin da kuka yazo min ba na juya zuwa cikin dakin da na fito don jin sherin da ake kokarin lakaka min da farar safiya haka a gidan mu.
Sauran magana ban jisu ba saboda kukan da nakeyi makarantar da ban tafi ba ke nan ranan don maganan Asabe tankar umurni ne ga Abba gama kowa a gidan.
A karshe dai na fito yin alwala nake jin lantana na fadin toke umma tunda kowa yasan kyauta na dan maciciji ne babu masunsuni gareta.
Ai baki kyale haka a zuba mata ido ba dadai kin nemi wani a cikin kauyen nan ki hadata dashi zaifi sai aji da sauran .
Don muddin tana gaban ku haka ba wanda zai kula sauran duk sai ai masu daukan daya kinsan halin garin nan sarai.
Duk wanan zance da sukeyi inna tana jin su bata ko nuna tasan ana zancen ba ta kawo ido ta sakawa kowa don nuna ka waici ga wasu mata na karkara.
Har kwana hudu sati na batun shigewa ban shiga school ba na gaji da zama daki mu don ko tsakar gidan mu na daina fita idan ba wani abu zanyi wajen ba.
Daki innar mu na shiga na saneta tana nade kayan data wanke na yara gaida ita nayi ta juyo tana amsawa fara nade kayan nayi sai inna tabar min nadin ta juya tana fadi.
Saliha tazo tambayan kitso nace ta tafi ta dawo don nasan halin ki sarai dan ajiyan zuciya na sauke ina fadin.
Ni inna banwa kowa kitso a barni inji da abinda yake damuna sai naga inna tayi murmushi tana kaiwa zaune gefen gadon famekan ta.
Tace ai dama haka ake son a ganki cikin kuntatawa da damuwa sai bukatan lantana da umma ya biya idan sunga kina wanan takura dama abinda ake so ke nan damu.
Shiru nayi ina nazarin maganan inna da bata kara dora wani lafazi ba bayan wanan data fada hawaye ne yadan biyo fuskana na share da sauri.
Don nasan ran innan mu ba zaiyi dadi ba itama don ban taba jin ta furta komai cikin zancen hanani zuwa makarantar ba sai yau da tayi mi hannun ka mai sanda.
Dan hira muke jefi jefi mukaji muryan saliha ta dawo tana tambayan kitson ina jin tana kwada sallama lantana na fadin wai waye haka ke damun mu da sallama ne.
Fitowa nayi daga dakin inna ina amsawa tare da fadin saliha shigo dama yanzu inna ke gaya min kin zo ai ina barci.
Saliha race wallahi nazo ko zan samu ki kwashe min kai zamu birni wurin bukin dan uwan maigidan mu ne.
Nace bissimilah shigo bari na dauko tabarma na juya zuwa dakin innan mu na dauko mata tabarma muka zauna zaman kitson.
Na koyi kitsone akan yan kanne na don yawan yawon neman kitso da kashin kudin da inna takeyi kan kitson mu.
Wanan yasa har na koyi kitso ina zama in masu har na hannu na iya ba wevean ba kawai don ina dake son kitson hannu wanan kuma a kanta na koya.
Yanzu kuma in muna makaranta nakan koyi kumshi a pepper har na fara zanawa kannena sai dai ba sosai na iya ba.
Wasa wasa tun daga ranan da naiwa saliha kitso mutanen unguwan namu ke shigowa wurina yin kitso ko su turo yaran su in masu.
Sai ya kasance har na fara mantawa da zancen hanani karatun da umma tayi yanzu.
Ga kudi baya katse muna dan abinda zamu kashe a kauye baya buwayan inna yanzu.
Don a wuni akalla muna dan rike dari biyu ko dari uku tundai idan akave weekend ne don ba wani kudi bane mai yawa kudin kitson kauye talati hamsim ne wani a kyauta zan mai ya tashi.
Ga Abba abin kara lalacewa yayi mai tun shigowan Lantana gidan shi abinda zamuci ma yana batun gagaran mu a gidan.
Don haka muke dan dora karamin tukunya mu dafa dan cimar da zamuci iyamu damu don Asabe ta fara a gaban mu zata dan dafa abu.
Saidai muji tana kwalawa Lantana kira tazo ta karba idan lantana ta karbo a gaban mu zasu zauna suci har tana santi don muji haushi.
Wani lokacin yan kannen mu sai su sa ido suna son ci sai inna ta doke su ko Asabe ta dinga fada ita ba zata iya ciyar da taron yan mata ba uwar mu data haifo mu ta nema ta bamu muci.
Da ku mazane ai da bamu kai haka ba a gidan nan da yanzu kuna wurin nema kuna taimakawa mahaifin ku.
IIrin wanan maganganun na kakar mu yasa muka dan fara dafa tukunyar gefe don kada kannen mu su koyi daukan ido ta wanan dalili.
Ranan inawa wata makwaciyar mu kitso kanwa saratu tana dafa fate don shi zamu gyara muci don Abba bai kawo komai a gidan ba tun safe.
Girkim ya dauko kamshi duk ya dume gidan da kamshi saratu na bakin murhu tana faman fita wuta don iccen baya ci sosai.
Sai ga lantana ta fito lungun Asabe gurin kwata inda muke wanke wanke kakarin amai ta fara da karfe da yaji.
Sai duk mukayi tsaye cirko cirko muna kallon ta da mamaki don bamu dade da jin dariyan su ba da asabe kamar ba sarakuwar ta bace lantana.
Sai ga Asabe da sauri ta fito tana salati tare da fadin yau may zangani haka Lantana lafiya meya same ki ?
Asabe ke tambayan ta a rude sai ga inna ta ma tafito daga dakin ta tana fadin Lantana meya faru.
Ganin Lantana na nuna gurin da saratu ke girki da hannun ta alama dai warin girkin namu wai ya jawo mata aman a yanzu.
Ja inna tayi baya don ta fahinci makircin da Lantana ke shiryawa a kan girkin da mukeyi din don muci tun safe bamu karya ba.
Wani guda mukaji Asabe ta sake wanda bamu fahinci ko na menene ba sai da tace .
Ahhaye nanaye Allah nagodema yau magaji ya bayana a gidana da yardan Allah.
Ta juya wurin saratu tana fadin ke kashe wutan nan ki bar girkin nan kada kija min hasara a gida don ku ba damuwan ku bane tunda bata son kamshin dahuwan naku.
Saratu ta mike tsaye ta fara buga kafa tana yaya zan kashe wuta kina ganin tun safe bamu karya ba.
Kada ki kawo min diban albarka nace a kashe wutan ku mutu idan bakuci ba mana waya damu daku wanan matsalan uwarku ce.
Wallahi bazan kashe ba tunda bai dahu ba saratu ta bata amsa saiga inna ta laiko daga daki tana fadin saratu jaye itace don Allah banson gardama da manya.
Tamayi gardaman dani Asabe ta fada tana nufar wurin randan ruwan mu ta debo ruwa a roba tana zuwa ta lemawa itacen da garwashin wuta lokaci guda wutan ya mutu.
Aiko saratu ta sake wani uban ihu tana fadin wallahi ban yarda Asabe tunda ba bamu abinda zamuci zakiyi ba tana magana ta nufi wurin murhun tana hawaye.
Muryan innace ke fadin karkiyi barshi hakana kuci ko bai dahu ba idan zai ciyu.
Wallahi inna bandade da zubawa ba tazo ta kashe wutan matar makwabtan mu da nakewa kitsone tace dauki dahuwan ki shiga gidan mu ki karasa girkin naki don Allah ku bar wanan magana.
Saratu tana sharan hawaye take fadin wallahi Asabe saina rama don ba yarda zanyi ba kun dafa naku kunci zaki hanamu dafawa yanzu.
Ranan dai sai gidan makwabciyan mu saratu ta karasa dafa abincin da zamuci ga Abba bai dawo ba har dare don haka da bafon faten ba haka zamu kwana da yunwa a ciki mu.
Saida safe ne nake jin muryan Abba cikin jin dadi yana fadin masha Allah abu yayi kyau Allah ya raba lafiya.
Ma,ana dai watau lantana ta samu ciki a gidan mu ke nan ni banji komai a raina ba a lokacin .
Don ban gama mallakan hankalin kaina ba da zan gane may hakan ke nufi damu sai can naji muryan Abba nawa saratu fada don me tayiwa Asabe rashin kunya kamar Abba zai doki saratu din.
Ban san ina Asabe ta tafi ba wai ashe ta fitane zuwa gidan wata mata mai bada magani ta ansowa lantana maganin baki kada innan mu ta zubar mata da cikin jikin ta.
A daidai wanan lokacin saratu ta shige lungun Asabe ta fasa mata babban randan ruwanta ba wanda yasan da shigan ta har ta fito daga sashen.
ZAINAB IDRI MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL GA MAI BUKATA TARE DA IMANI DA SANIN AKWAI HISABI GOBE KIYAMA.
DON ALLAH YAN UWA MUJI TSORON ALLAH GA DAUKA HAKKI A KAN MU TA WANAN HANYAN SAYAR DA LITTAFI A ONLINE MUKE SAMUN CIGABA DA RUBUTUN DA MUKE MAKU KADA KIJI HASARAN BAMU HAKKIN MU KODA KADAN NE .
Sai salatin Asabe mukaji a tsakar gida tana ta faman rabka salati da fada tare da zagi ga duk wanda yai mata wanan aikin.
Babu wanda ya tanka a cikin mu har innan mu saiga Lantana ta fito tana fadin meya farune umma ?
Meye ma bai faru ba randar ruwana tun tele tele na samu a fashe yau sai nasan wanda yai min wanan ta,asan a gidan nan ta fada tana zare ido.
Lantana tace kema umma da wani zance kike ai wa zaiyi wanan banda yaran gidan nan ko Akuyar ki ta fada mata.
Badai Akuya ba su din daine zasu aikata min haka saboda bakin ciki da mugun hali yau dai ai za,a yita ta kare ko a biyani randan ruwana ko kuma yasan inda zaiyi dasu nagaji wallahi .
Ta karasa tare da juyawa wurin randan ta nufa tana hada guntayen sakainan da suke wurin a warwatse a kasa.
Ranan wuni jininin wanan abin tayi babu wanda ya fito yace shi ya aikata hakan sai lantanane ke taya ta fadan.
Abba na dawowa da wanan zancen aka tare shi kira ya kwalawa innan mu dake daki ta fito.
Cikin yaran nan wayaiwa umma wanan barnan ya tambaya yana kallon fuskan ta.
Malam ina zan sani tunda ba yawo nake dasu ba balle duk cikin su babu wanda ke yawan shiga wajen umma ko tana nan balle bata gidan yau tun safe.
Asabe tayi caraf tana fadin waya sani ko ita dince tayi wanan abin don kawai tsaban bakin ciki dake cinnta.
Aure daine na karawa dana ga kuma abin arziki har an samu saidai bakin ciki ya kashe mutum din sai anyi ma yayan ki dan uba a gidan nan.
Wanan bai taba damuna ba umma kin sani in ma za a karo mai biyune rana guda su shigo su haihu a rana daya bai taba damun rayuwana.
Kana dai jin wuyan matar ka yayi kauri har tana fada min bakar magana haka a gaban ka.
To kisha kurmin ki wanan din ce dai guda na aura mai kuma baki so hakan ba dake da diya matan naki da suke tayaki kishin.
Allah ya baku hakkuri umma randan ruwa ne dai ban san wanda ya kashe maki shiba .
Makirci daine kiyi tayi aiga diya mata nan maki zube a gida har yau babu wanda ya sallama da sunan kiran su.
Shiga dakin inna yayi daidai da soma fadan Abba Asabe na fadin in fito da miji cikin samarina Abba yace kwarai kuwa da gara dai in fara rage su nima zaifi min sauki tunda har sunyi wayau yin hakan yanzu.
Idan ma bata da tsayayyene akwai wanda zan hada ta dashi ai shi a shirye yake ko yanzu idan har na bashi.
Abba yace a, a umma gara dai a bari ta kawo din da kanta zaifi tunda kin ga yadda yar gidan muddi suka kare kan hakan yanzu.
Gashi kullun maigari maganan shi ke nan a bar yara su zaba da kansu da ai masu dole.
Ai ba dole bane tunda shidin wanda zan hadasu din yana son ta ai itama zata so shi tunda bata kaishi gata ba.
Koma dai menene umma don Allah kada a soma hakan banda zarahin zuwa birni sharia tunda kinga can ake kai mutun kai tsaye.
Jin hakan yasa Asabe tabe baki tana juyawa zuwa wurin ta tare da fadin ni banga ranan haihuwan diya mata ba a rayuwana ko kadan.
Inna dake daki kuka take darza a hankali batare da fitar da sauti ba balle wani ya jita.
Alwala nayi na nufi dakin ta sanin Abba ba dakin yake ba na samu inna zaune tayi tagumi a wurin data idar da nata sallah.
Inna kada zancen su Asabe ya tayar maki da hankali har ki shiga damuwa tunda bake kika ba kanki diya mata ba ai.
Meye laifina a cikin wanan zance yar mairo don kawai na haife a mata yasa umma ta dauko tsangwama ta dora min ni meye nawa a ciki.
Su suke raina diya mata ina saboda in kin kula Asabe ba da bukatan ilimin addini ko kadan ne matar da ko alwala bata tsaya ta koya ba .
Idan kuma za a gyara mata tace ina mutum ya fito ta kashe shi ai kinga fadin hakan daga bakinta ba abin mamaki bane jahilcine ke damunta daga ita har yar koran nata.
Bashi yafi damuna ba yar mairo yadda yanzu mahaifin ku yake kokarin juya min baya tun lokacin zancen cikin matanshi da umma tayi.
Ina kallo zai sayo mata abu a gaba zai bata idan nayi magana yace min tana da lalura dole a lalabata ai.
Inna kema idan kina son abin ai sai ki fitar da kudi ki saya idan baifi karfin ki ba kiyi hakkuri ki saka masu ido Allah ba azzalumin kowa bane ai.
Sallah nayi har na idar tana zaune tana faman tunane kafin ince niko inna sai nake ganin kamar saratu ne tayi wa randan ruwan Asabe ta,asa don abinda tai muna ranan .
Don dazun naga sanda ta fita zuwa lungun Asabe bata dade ba ta dawo daki tana dariyan kyata.
Amma idan itace ta aikata hakan sai na bata mata rai yau inna ta fada a hasale.
Da sauri na tare inna ina fadin a, a inna idan kin doke ta zasu gane kiyi mata fada kawai don Allah idan ta shigo.
Kwafa innayi ba tare da kara furta komai ba ta mike tsaye ta tada sallah don isha,i da ake kira lokacin.
A daidai lokacin saratu ta shigo gida tana wakan ta mai kama da habaici a fakaice .
Gamu munzo taron dangi, bama tsoro kugafar bama tsoro har zuwa karshen wanka tanayi tana rawa kafin sallama ta shigo dakin inna kai tsaye.
Ganin muna sallah yasa itama ta juta ta suri buta ta shiga bandaki ta dade a ciki kafin ta fito tayi alwala lokacin har sauran sun shigo dakin ko suna sallah.
Nice na fara idarwa don Inna ta tsaya dogon adduan da takeyi bayan sallah.
Fatima ki tashi kuci abinci kada kiyi barci bakuci abinci ba cewa da yar karaman kanwar mu data kwanta tana shirin barci.
Mikewa nayi don in raba muna abincin da mukayi tunda rana tuwo ina tayi muna da miyar ganye da gyada shine mukaci da rana sai koko da take cika roba ta aje don mai yara bata yarda ta rabu da koko a dakinta a kauye.
Saratu na shigowa take fadin yanzu ma tuwon ne zamu kara ci nace idan kin tanadar muna wani abin ba sai kici ba.
Sallah ta tayar har ta idar daga inda take fadin Abu bani abinci na zanci in kwanta ne yau barci nake ji.
Ba zaki biya karatun ki ba ke nan yau barci zakiyi tace na gaji ne yau sosai na dibar muna abincin sai da muka faraci dakin hayi tsit a lokacin.
Don inna ta horemu da hakan tun muna yara har muka gama kowa yaje ya wanke hannu muka dawo tana gyara wurin kwanciya inna tace.
Saratu may yakaiki wurin inna har kika fasa mata randar ruwanta yau don kawai ki jawo min sabon masifa cikin gidan nan ina fama da kaina.
Juyowa tayi inda nake ta dan kalleni kafin tace wani inna wallah, , , , bata karasa ba don tsawan da inna ta daka mata da rufe min baki tun kan na mareki wurin nan.
Shiru tayi har inna ta kare mata fada bata sake magana ba don fada sosai inna tayi mata tana shiru har inna din ta gama.
Ina jin tayi shiru nace ni inna gaskiya gobe zanyiwa Abba maganan karatuna gashi har zamu fara exam din shiga wani zango ban tafi ba.
Idan kinga zaki iya ai gaki gashi nidai babu ruwa na tunda kikaji umma tace kin daina boko to ki barwan nan zacen a hakan.
Har muka kwanta ba kara magana ba sai faman tunane nake a raina don ba abindake damu kamar rashin karatu da ban fita yanzu na riga da na kwallafa rai ga boko nace ni nurse zan zama idan na girma.
Washe gari baba bai fito dakin lantana da wuri ba har kowa ya gama shiri ya fita don sauran suna zuwa makaranta basu fada kangin Asabe.
Hankalina yana wurin fitowan baba daga daki lantana sai wuran goma ya fito tare da ita tana mai rakiya don kawai kada yace zai biya wurin innar mu su gaisa.
Har yasha dan kwanan fita daga ciki gida na fito da sauri na same shi ina fadi Abba ina kwana.
Ya tsaya tare da juyowa yana fafin yar mairo kun tashi lafiya ina kannen naki sun fita ko ke nan ?
Nace a sanyayaye sun tafi baba sai na fara hawaye daga inda nake tsungune ina dan gogewa da gefen hijabi na.
Me ya sameki kike kuka haka da safe Abba ya tambayeni cikin kullawa kasa bashi amsa nayi sai sharan hawayen da nakeyi a lokacin.
Lantana dake tsaye gefen shi kamar bodyguard din shi ta tabe baki tana fadin ya wuce dai zancen auren ta da umma ke fadi.
Kai haba lantana wani zancen aure kuma yanzu gun yar mairo adaiyi hakkuri ta karasa karatun nan datasa a gaba har kwana nawa yarage ta karasa idan muna raye.
To ai naga kai umma take tausayawa a cikin zancen nan kamar rage maka nauyine umma ke kokarin yi ga hakan.
Ya juyo wurina yana fadin kinga yar mairo kije kiyi hakkuri har in zauna da umma in fahintar da ita ko Allah zai bamu sa,a a kanta.
Lantana dake jin mu ta karyar da kanta gefe tana fadin gamu gani ai indai umma ce a gidan nan.
Na bude baki da kyar ina fadin don Allah Abba ka taimaka min na karasa karatuna ko iya secondary din ne in tsaya.
Taysayinane ya kama Abba lokaci guda sanin yadda gun ina kankanuwa nake son boko har irin dagewan da nakeyi kan karatun a yanzu.
Yayi karfin halin fadin kada ki damu yar mairo insha Allahu zaki karasa karatun ki har ki more a rayuwan ki, duk da lantana na fadin malam kasan fa ka makara kada kwastama su dinga mitan hakan.
Haka yasa Abba ya wuce badon yaso ba don tausayina da yaji a lokaci guda ya rufe mashi zuciya.
Bayan fitan baba lantana ta juyo ta dubeni a lalace tana fadin iska na wahal da mai kayan kara.
Lantana wurin Asabe ta nufa ta fesa mata yadda mukayi da Abba tunda naga ta nufi can zuciyana ya raya min hakan.
KADUNA GARIN GWAUNA
Wanka tayi ta shiya a gurguje cikin shigar manyan mata da boko ya gama ratsa su.
Fuskanta babu wani kwaliyan zama a tare da ita sai dan maikon mai data shafa sai man lebe data murza don yanayin garin.
Gurin takalma ta nufa ta saka wanda yai shige da kayan jikinta da sauri ta fito daga dakin duk da sauri takeyi amma idan ka ganta sai ka dauka takon isa da iza takeyi saboda wayewa.
Makullin mota ta dauka don bata bukatan driver a inda zata tafi yau don gidan safiya take son kaiwa ziyara da sa,a.
Tana bude falo sukayi kicibis da bakin ta dake hawo steps din da zai sada mutum da kofan shiga gidan.
Tsayawa sukayi suna kallon kallo a tsakanin su kafin hjy iyami ta fara fadin kune tafe banda labarin hakan.
Sai lokacin Alh isma,il yayi dan murmushi yana kawar da abin kunyan dayaso yi lokaci guda don ganin hjy dayayi a yau bayan tsawon shekarun daya dauka basu hadu ba.
Shima ya wayence da fadin af na manta da gidan bakar baturiya zamu ziyarta dole saida notice.
Kai ta girgiza tare da kallon wanda suke tare tana fadin sannu da zuwa kaidai shi wanan har kullun baya tsufa halin shi na kurciya yana nan a yadda yake da zolaya.
Ke kuma zolayan ne bakya so ba bissimillah ku mana ku shigo kasa na tsaya mun bar bako a waje.
Bako ko baki don nima bokon ne tunda ban taba zuwa gidan ba ai kinga na zama bako.
Hjy iyami tace kaidai ka sani tana ja dan gefe guda tare da nuna masu hanyar shiga don bata yarda su sakata gaba ba kasancewar su maza.
Falon suke bi da kallon yadda ake tsara komai zakace a kasan turai gidan yake don tun a waje suke bin ginan gidan da kallon sha,awa.
Zama sukayi saman kujerun alfarman dake falon kafin aka fara gaisawa tare da tambayan iyali.
Alh isma,il yana tambayan samarin hajiya daya sani take fadin kai ai yanzu sun zama magidanta in ka debe shi na biyun da har yanzu baiyi aure ba yana chaina yana aiki dasu a yanzu.
Kai masha Allahu Alh yace sai kuma yayi mata gausuwan rashin mijin ta don tun lokacin basu hadu ba dashi yace koda suka zo gaisuwa mata sunyi yawa basu shigo ba.
A lokacin yanayin hjy yadan canza take fadin hakane saidai bamu dade ba muka koma don yara dake karatu a can.
Bayan sun dan sha abin shanda aka cika masu gaba dashi yake fadin hjy dama kamar yadda nace dake magana ce tafe damu sai fuska da fuska zamuyi maganan .
Hjy tace kwarai hakan kace yanzu ku nake saurare ai dayan mutumin ne ya karbe zancen da fadin hjy nasan baki sanni ba ni.
To ni sunana Aliyu zaki kubau dan majalissan dake wakiltan nahiyar uku dake makwabtaka damu.
Munzo nan ne da wani bukata ko shawara na duba a gareki wansn ba wani zance bane sai sunan ki da muke son mu bayar don zaman ki macen data cancanci wani mukami da muke son a samu a tamu nahiyar a cikjn gwaunatin nan.
Ni kuma Alh har yaushe na dawo kasan nan da zan iya shiga wanan harkan na siyasan kasan nan yanzu.
Bayan haka kuma ni yanzu duk wani mukami na gwaunati ko wani aiki ban ra, layin shi saboda hutu nake so a yanzu a cikin iyalina.
Me nake nema a yanzu wanda Allah bai ban ba sai hamdala da shukura ga ubangijina ga yara sun kawo karfi suma Allah yana duba mana duk a yanzu.
Mun san da hakan hjy sanin hakan ma yasa mukaga cancantan ki ga wanan matsayin don kece zaki tsaya muna badon kudi ba sai don tausayawa jama,an mu.
Kada kace haka Alhaji don shi mukami da kake gani ba haka yake ba na rike na kuma san meke cikin sa sarau.
Balle mukamin irin gwaunatin kasan nan sai a hankali don mutane ba gaskiya suke so ba a yanzu niko kasan a bisa tubalin mijina nake komai shine gaskiya.
Don haka tun zancen baiyi nisa ba ina rokon ku da ku janye wanan magana a duba wata da ake ganin ta cancanci hakan a bata don Allah.
May na fadama Alh isma,il ya fada yana kallon abokin nasa cikin dan murmushi nasan wanan matar ba zata canza ba ai a yadda na santa tun farko.
Kaji ke nan ina nan a yadda nake har yanzu hjy iyami ta fada sai dayan mutumin yace hjy zamu baki lokaci kiyi shawara yadda ya dace don bamu son wanan daman ya kubbuce muna a yanzu.
Don dama ne da hujja da muke dashi akan ki na mace mai ilimi da matsayi irin wanda ake nema a wanan nahiyar tamu a yanzu.
Shiya sanni yasan ko wacece ni banda ra,ayin irin wanan mukamin ko a majalissan dunkin duniya danayi aiki dasu acan da ka fadi sunana sun san dani a wurin.
Hjy ki dai kara shawara a duba abin kamar yadda nake fada maki a yanzu don wani abin ansan badon kudi mutum ke rike sa ba sai don al,umman nahiyan ka.
Zatayi shara yanzu dai mun fada maki bukatan mu don Allah muna son kiyi duba ga wanan abin kafin mu sake dawowa muji shawarab da kika yanke akai.
Hakana dai sukai sallama ba tare da sunga alaman yarda daga gurin hjy iyami ba shi dayan mutumin daya kira kanshi da Ali zaki kubau yana cike da mamakin hjy iyami din don bai dauka akwai irin matan nan a jaharsu ba haka.
Unguwar da hjy bata fita ba ke nan a ranan don bayan tafiyan bakin ta sai taji kasalan fita ya kamata lokaci guda don tunanen maganan bakin nata da sukazo mata dashi.
Tsuki taja tana gyara kafan ta saman kujera data dagwara don taji dadin zama da kyau tana fadin ina zaman zamana kuja min sabon zagi da tonon asiri da tsufana.
Nikan dariya nayiwa hjy ina fadin hjy ina tsufan yake a nan saidai inda babu tsofin ko za a kiraki da tsohuwa ko dadtijuwa din.
Don babu mai ganin ta a yanzu yace itace mahaifiyar wa yan nan yaran nata a yanzu.
Sai data dan dade zaune ta tuna da zancen unguwar da zata tafi do yau taso ta ba su safiya mamaki ta ziyarci gidajen su su sanda suma yan uwane kamar kowa.
Don kawai sun fito ba ciki daya da yan uwan su ba bai kamata ana ware su haka ba a cikin dangi don tasha alwashin ida nufin marigayin mijin ta duk akan yan uwanta idan tana raye a duniyan nan .
Saidai muce Allah ubangiji ya ida nufi na alheri hjy da haka mata suke duka wurin raya zumucin da zumunci a yanzu bai tabarbare ba a duniyan nan.
Shigowan yaran ta dake gida suna hutu ne ya dawo da hankalinta garesu gurinta suka nufo kamar yara kanana muhsin ya zauna a gefen ta tare da rankwafo kanshi saman wuyan ta yana fadin wallahi mami na gaji sosai.
Kafin dayan ya zauna a makari kujera dayan gefeb yana fadin hajjaju zaman garin nan fa ya fara isata wallahi.
Gashi ko a nan zaku zauna don ba zan yarda wani cikin ku ya kara niss dani ba kamar yadda kewan dan uwanku ke wahal dani a yanzu.
Wai mami idan an tashi magana sai ki kawo zancen yaya jackson shifa ina jima yanzu ya manta da Nageria a ranshi.
Dan duka takai mai ga kai tana fadin daga min ya daga da sauri yana fafin wassh Allah na yana shafan wurinda ta dukeshi din.
Tana fadin har daku cikin batawa dan uwanku sunan shi na musulunci da kiranshi wai wani jackson cen ba dadin ji.
Allah hajjaju idan ba kince haka ba a turai babu mai gane shi ake afadi don jackson din ko jack ya rufe sunan nasa a yanzu.
Bai rufe ba ta fada a hayayyake shima idan yazo zan mashi magana kan hakan idan baso yake yaje lahira ana tayar dashi da wanan sunan kafiran ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAN UWA MASOYA ANNABI ALLAH YA KARAWA ANNABI DARAJA YABA MU IMANIN A MAI ANFANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , ,
DON SAMUN LITTAFI BA TARE DA DAUKAN HAKKI DA NAUYI A KANKI BA SAI KI TURA DARI UKU A BANK DINA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA TA WANAN LAYIN 08036959257 KO 09036
Tun bayan fitan Abban mu ban koma daki ba wankin dana tara na farayi muna kafin yan kitso su fara shigo min su hanani aikin komai.
Ina shanya kayan ne nake jiyo zagin da Asabe ke durawa wanda ba sosai nake jiyo su ba daga inda nake har na samu na gama ruwa na diba naje nayi wanka.
Ban kai ga karasawa aikai sallama ko ban leka ba nasan masi kitsonane suka fara shigowa lokacin .
Makwabciyar mu hassana ce da yaranta yan mata biyu da zan wa kitso suka shigo fitowa nayi na dauko tabarman da innan mu ta bani don yan kitso din na shifinda tare da gaida ita.
Dakin inna na shiga tana zaune tana gyaran sarkan kanwarmu daya katse nake fadin inna ko zan dora abinci ne kafin in zauna.
Jekiyi tsabgan gaban ki gunda ga mata sun fara shigowa barni in gama in dafa muna fate da guntun tsakin daya saura muna shekaran jiya.
Ko zai kaimu har dare tunda ba abinda zamu dafa da daren inna Allah zai bamu da yardan ubangiji tunda ga yan kitso nan sun fara shigo min yanzu sai a sayo ko taliyan hausa a dafa da daren.
To kije ku zauna kada matar mutane ta dade a zaune inna ta fada na juya na fita raina babu dadi a lokacin don a yanzu kan ina iya fahintar halin da mahaifiyar namu ke ciki na mijinta da sauran mutanen gidan mu din.
Daga kofan innan mu kadan nake zama muyi kitso don Asabe tace bata yarda ana sake masu gashin mata barkatai a gida ba kada azo a barbada masu tsiya a gida.
Ina kitson ina tunanen halin da innar namu take ciki na bakin cikin rayuwa duk saboda kasancewan mu mata a gareta don kila badon mun fito a yaya mata ba da bata fuskanci duk wanan nakin cikin haka ba.
Muryan lantanane ya dawo dani ga dogon tunanen dana lula ina rike da kan yar karamar yarinyar dana farawa kitson lokacin.
Wai har an zauna wanan bakar sana,an da babu karuwa a kullun a cika muna gida da yan gulma da sunan kitso nikan malam ya dawo ya tare min wurina don wanan abin ya isheni hakana.
Kai ke nan duk abinda kakeyi idon mace na kanka a zubama ido a fita dakai waje ana baradawa a cikin gari.
Dagani har matan da nakewa kitso ba wanda ya tanka a cikin mu don idan da sabo sun saba da wanan halin na habaici idan sun zo kitson don kiri kiri ake nuna min hassada ga yin kitson kuma.
Maimakon ta shiga dakin datayi niyar shiga da farko sai kuma ta juya ta koma lungun Asabe ta dade kafin ta fito.
Lokacin har na gamawa yaran duka biyu na farayiwa uwar saura kadan mu karasa kitson namu tana yan wake waken ta na hausa mai kama da habaici.
Naji matar da nakewa kitson tace uhumm wanan matar baban naki da jan magana take naga dai kullun nazo kitso gidan nan sai ta samu abindata fada a kanmu.
Ina jin dadin yadda baki kulata kike aikin gaban ki ba tare dakin damu da ita ba don irin su saboda bakin ciki suke haka don tayi sanadin da zata saka a hanaki kitson ga baki daya tunda sun san kina samu a nan.
Ba komai ai wata ran sai labari na fada mun gama ta dauko dari biyar sabuwa ta mika min na girgiza kai tare da fadin a, a wallahi ki ban dari ko dari da hamsin .
Haba Abu kullun na turo yara a kyauta kike min kitson nan ki karba baban sune ya bamu mu kawo maki da nake fada mai alherin da kikewa yaran shi kullun.
Dole na karbi kudin badon naso ba damun wanan kudin ya zama kamar buduwar hanyar alherina ranan don duk wa yanda sukazo kitso mun samu alheri sosai a wurin su.
Bansan yaya Asabe sukayi da mahaifin mu ba ya dai bani hakkuri kan in hakkura da karatun nan kawai a yanxu.
Ranan nayi kuka sosai kamar ba gobe tun innan mu na ban hakkuri har ta gaji ta kyaleni ta saka min ido.
Saratu ne abinka da dan uwa data dawo innan muke fada mata wuni nayi ina kuka a daki yau don Abba yace ba zancen komawa makaranta a wurina.
Tashi tayi ta sameni a dakin tana ban hakkuri tare da ban shawaran da muke ganin zai fitar dani daga kuncin da Asabe ds lantana ke shirin jefani s ciki.
Fitowa nayi don taya innan aiki gitkin dare haka ma su sararu da sauran yan uwan mu suna debo ruwa daga rijiyan uguwar mu suna cika duk kayan dake gidan na ruwa.
Har sun kusa cika na kofan lantana don sheri kawai lantana tace wai habiba ta saka hannu a ruwan don haka bata so sai dai su zubar su debo mata wani.
Wanan ya kawo rikici a gidan mu sosai ranan don har inna takai ga tanka masu Abba kuma ya dawo ya hau innan mu da fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Wai inna ke goya muna baya muna iya shegen da mukaga dama a gidan ai lantana ma kamar uwa take a gurin su tunda tana auren shi.
Saratu dai taki komawa diban ruwa kuma ta hana yan uwa zuwa su debo suka kada guga a riya karshe dai ruwan da ba,a deboba ke nan har Abba ya dawo hake wanan fadan .
Kwala min kira yayi wai na kwashe ruwan randan innan mu guda in zubawa lantana a nata randan in yaso mu mu zauna ba ruwan tunda saratu ta zama abinda ta zama a yanzu duk gaba daya zai hadamu yai muna aure lokaci guda tunda ba finta nayi da wani girma ba.
Inna kan bata da aiki sai kuka don hakane kowa ke kokarin takata yadda yaso a gidan don rashin maganan da bata yi idan suna mata abinda sukaga dama, mu a namu ganin ke nan.
Hjy iyami abin duniya y isheta ga matsin da gwaunati da yan siyasa ke mata dole ta zauna da yaranta da yan uwanta kan maganan.
Inda suka bata shawaran karban mukamin don taimakawa rayuwan tallakawa da sauran al,umman nahiyar su din.
Haka yasa ta shedawa Alh Aliyu zaki kubau amincewan ta wanda ba karamin farin ciki yayi da jin hakan ba daga bakinta ,.
Duk da yana hangen da wuya su iya tafiya a yadda suke so da ita don ra,ayin daya hango a tare da matar duk da ba laifi ko yaya ne ai wayau maza yafi na mata ya fada.
Tawaga guda sukayo zuwa gidan sun dade suna tataunawa da ita kafin suyi mata godiya su tafi.
Hakan yasa taji duk ta gaji ga ranan don yan aikin ta kawai bazasu iya mata abinda take so ba daidai a hakane safiya suka zo gidan suka same ta cikin gajiya.
Bayan sun gaisane tare da mata murnan abin arzikin dake shirin faruwa da ita take fadin anya safiya zan iya wanan abin yanzu.
Yau kawai duk nabi na gaji dan dawainiyar dana wuni inayi da jama,a agidan nan .
Shiyasa nake son a samo min yarinya yar maidaidaciya da take da rikon Amana in zauna da ita don wa yan nan kinga su ba zama sukeyi ba ko ba school sai sun kirkuro fita sam basu zama a tare dani.
Na rasa inda zan samu irin yarinyar da nake bukata na kusa wace zata dinga min hidima ko yaushe.
Dan shiru safiya tayi kafin tace za a duba a gani indaya dace sai a samo maki yarinyar kamar yadda kika bukata.
Zanje kauye in duba maki mai dama mu gani idan zata iya idan kuma ta gaza sai a mayar da ita a sake duba wata.
Dakin mun hakan dana gode kuwa safiya shiyasa nake kara jin dadin ki wallahi na dade ina tunanen ta ina zan fara duba yarinyar data dace yadda nake so nan gari.
Da wanan maganan suka rabu ranan inda safiyan ta koma gida da tunanen inda zata duba yarinyar data dace takawowa hjy a yanzu gashi tayi alkawarin hakan gare.
Kafin gari ya waye ta yanke shawara a ranta zata duba ta gefen mahaifiyarsu ta gani idan hakan zai samu garesu.
Don koma meye zata iyayiwa hjy iyami indai zata iya baifi karfinta ba don ko meye hjy ta cancin hakan garesu .
Don ta nuna a duniya su yan uwan mijintane a yanzu don ko wani wuri zata tafi na alfarma suna daga cikin masu mata rakiya.
Wanan abin yana ba mutane da dama haushi har suka fara fadin asiri sukai mata suka shiga zuciyan hjyn a lokaci guda.
Daga hjy harsu suna jin ire iren wanan magana saidai ba abin mamaki bane hakan da mutane suke fadi don yanzu mutane basu dogara ga Allah sun manta da ba duga aka zama daya ba.
ANCAU
Tunda safe na samu masu kitso don haka na zauna muna kitson ga innan mu tana aikin girkin gida don yau Abba yayo cefane ana dafawa aci duka gida.
Ditin mota mukaji a kofan gidan mu sai dai bamu dauki hakan wani abu ba don ba wanda zaizo gidan mu da mota ai.
Haka yasa muke zaton ko makwabtan mu motar tazo yin wani abu sai can mukaji sallaman mata na shigowa gidan namu lokaci guda.
Amsa masu sallama mukayi dani da matan da nakewa kitso sai inna ta dago dan ganin masu shigowa gidan lokacin.
Tarbon su tayi tana fadin wa nake gani yau kamarsu hjy safiya garin namu ?
Ba kama bane mune dai din kike gani don kasancewar su kamar tobasai tunda tana auren yaya a garsu.
Dakinta ta kaisu don Asabe bata gidan lokacin ba laifi don dakin inna duk da yawan mu koda yaushe tsab yake don tsabtan ina yara basu hanata gyaran daki da tsakar gida har din muka koyi hakan.
Don ko a kauye akwai masu hali irin na yan birni da zaka samu a talauci amma komai nasu yana tsab.
Tabarma ta shimfida masu saman sumintin dakin dake sheki sai dan kamshin turaren wutan dake tashi ba wani mai kamshi ba amma duk da hakan ba laifi dai dakin don ba zakace dakin mai yara bane.
Ruwa ta kawo masu a kofin silver tana fadin ga dai ruwan namu babu sanyi don har yanzu yayan naku baija wuta ba gidan nan.
Ikon Allah duk wutan nan daya kewaye garin nan ba a ja maku wuta ba har yanzu inna dai bata ce komai ba kada zancen yayi nisa a hakan.
Safiya ta dauka ta dan kurba kadan ta mikawa anty Sa, a kaita girgiza alaman ba zata sha ba ta aje kofin a gefen ta.
Lokacin na sakewa matar kai nazo don in gaidasu da zuwa a dakin innar mu din .
Saida nakai har kasa na fara gaida su da zuwa anty safiya na fadin wai kada dai ince wanan ce nan wa take da sunama don mantawa da sunana da tayi a ranta.
Inna tace ki dai tuna don kinsan niba fada maki zanyi ba dai ta fada tana mikewa don barin dakin.
A hankali nace Abu sunana gwaggo tace naji dayan da ake kira da anty sa, a tace min haba wani irin Abu kuma keda kanki kike batawa kanki suna haka?
Zainab din ne kike kira da Abu wai kamar sunan wani abu can daban wanan ai suna tsofine nagani.
Nidai na fita ina dan murmushi don jin may suke fada a gatin nan kan wa zai tsaya kirana da wani zainab can.
Nakai kofa naji tana tambayana ina yan uwan ki suke nake fadin suna makaranta na fita daga dakin kai tsaye na koma inda nake kitso .
Yaro inna ta nema ta tura a kira mata Asabe datace zata shiga makwabta tana jin lokacin da take fadawa Lantana hakan.
Ba, a jima ba sai ga Asabe da dan saurin ta ta shigo tana fadin bakin daga birni su waye umma yayan kine su safiya inna tace.
Sai lokacin na tuna dasu da suna yawan zuwa gidan muna kanana amma daga baya suka daina zuwa ban san dalilin hakan ba garesu.
Suna ina Asabe ta tambaya inna ta nuna mata dakinta sai ta dan tabe baki ta nufi dakin inna din .
Muryan lantana ne ya dakatar da ita shiga dakin lokacin lantana na fadin umma kin dawo ashe ?
Na dawo yar nan yanzu yaro ya sameni wai nayi baki daga birni sai lantana tace au baki akayi ashe mu dake gidan ma bakin ciki ya hana a sanar damu.
Dago kai nayi na kalli lantana da take maganan don nasan da innan mu take wanan maganan haka.
Asabe ta shiga basu dade ba suka fito zuwa sashen ta tare da bakin sai lokacin lantana ta tafi gaida su.
Don a nata nufin bazata shiga dakin innan mu ta gaida bakin da zuwa ba don innan mu bata kai mata can ba .
Inna tana gama abinci ta zuba masu a kwano mai kyau ta dauka takai masu ta dawo ta debi ruwa ta sake kai masu a can.
Abba ya shigo gidan yana fadin yanzu ake fadamin anga munyi baki a gidan yasa na garzayo in ga su waye suka zo.
Can ya samesu a aurin Asabe suka zauna sun dan dade a tare kafin su fito suce zasu tafi sai da suka sake shiga dakin innan mu sukai mata alheri kafin su fito su tafi din.
Bayan kwana biyu naji lantana na fadin duk kyau da bokon wasu ga aikatau zasu kare rayuwan su karshe ma su kare ga auren maigadin gida.
Dagani har innan mu kallon juna mukayi lokaci guda don ba wanda ya fahinci may zancen ta ke nufi a lokacin.
Share ta kowa yayi abu kadan yan kwanajkin nan zata ce kyau wasu ya kare ga banza tunda zasu tafiyin bauta a gidan wasu.
Banga wanda ya isa ya tura min dana yawon bauta ba a gidan kamar banda kowa a duniya har dai ranan da dare muna zaune muna hira a dakin inna gaba dayan mu inna ke fadin.
Nikan wanan zancen bautan da amaryan baban ke fadi na rasa gane inda maganan ta ya dosa da fadin haka ko yaushe .
Wanan inna ai ita ko ba dalili kirkiro magana take ta yabawa mutane don kawai ayi fitina tunda bata son a zauna lafiya ita na fada.
To dan wataga za,a tura yin bauta da take fadin haka inna karma magananta ya dameki don Allah saratu ta fada tana jan tsuki.
Shiru mukayi kowa na nazari a cikin ranshi kan zancen don innan mu tafimu fahintan da akwai wani abinda zai faru da diyan ta don haka kawai bai saka lantana tayi ta gorin haka a tsakar gida.
Aiko ranan da safe baba yai kiran mu nida innan mu yana lungun Asabe muka tafi don amsa kiran Abba din.
A zaune muka same su a dakin kowa yai shiru saidai yanayin su ya nuna kowa na cikin bacin rai a lokacin.
Wuri muka samu muka zauna nikan ina daga kofan dakin don ban shiga ba a lokacin inna tace gamu malam.
Zuwan lantana yasa yayi shiru ya kasa maganan da zaiyi sai Asabe take fadin kayi magana ka tsaya kana wani kimbiya kumbiya kamar kana tsoron matar taka da yarka.
Ke yahanasu bawani abu bane yake son fada maku ke da yarki sai zancen tafiyan yar ki birni da nace a turrata aikatau.
Koba komai zai dan samu abinda zai rage saya mata kayan daki a nan tunda kunki bari ya aje komai gashi sun cika muna gida zagada zagada dasu.
Aikatau kuma umma ina ta fada da mamaki karara a fuskan ta sai naji asabe tacd eh aikatau ko yar taki tafi karfin yin sikatau din ne.
Ina ko tafi umma wanda yake nema ya samu duk wata za,a lalo mashi yaji dumus ai yafi zaman wanan kitson da takeyi kullun tana tara muna munafukai a gida lantana ta fada daga inda take.
Koba zaki bari ta tafi bane Asabe ta fada a hasale tana duban inda inna take zaune.
Abba yayi karfin halin fadin a barta suyi shawara da yarta umma don kinga daga sama sukaji wanan maganan yanzu.
Shawaran me zasuyi wanda yafi wanda na fada yanzu a gaban ta kuma ko kuma sai abinda tace zamubi tunda itace ta ajemu bamu ba.
Ai shike nan tunda kace haka dama ni kai nakejiwa nake tausaya maka tunda hakan ne kawai zatayi ma a matsayinta na ya mace ta taimakawa rayuwan ku na dan lokaci.
Umma ai Allah daya bamu su yasan yadda zai iya mana dasu basai mun kaisu inda bamu san kowa ba don neman abin duniya.
To mara kunya akan yar fadin ki kike kokarin musayan magana dani to kiji ki karaji zuwa birni babu fashi ga Abu.
Idan ta samo kudin bakuso ku bani wani ya hana ki haifota a namiji halan birni daine kamar taje tagama yanzu haka na fada babu fashi ga zancena kuma.
Inyaso idan ta tafi ta shiga duniya karewan rashin sanin kowa inds zata ke nan aikatau daine sai ta tafi.
Wani kuka ne na fashe dashi lokaci guda don jin hukuncin da asabe ta yanke min yau a gidan mu.
Ta hanani karatu don wani manufanta yanzu kuma zata turani birni yin aikatau do kawai a musgunawa innan mu.
Daki inna ta sameni ina rusa kuka itama kukan ta shigo dashi a dakin muka taru muka rasa wanda zai ba wani hakkuri a cikin mu lokaci guda.
Sai nice nayi karfin halin fadin inna kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zan tafi yin aikatau ba a birni.
Yar mairo me nayiwa umma take min haka a raguwana ko yaushe take kokarin sai taga bakin cikina a rayuwan ta.
Ita ya mace ba diya bace da za ai alfahari da ita cikkn zuria da wasu basu gane hakan.
Ban taba bakin ciki da nadaman samun ku a diya matan da kukazo min ba don ban san kyautan da Allah yai min ba don haka bazan butulcewa Allah na ba.
Amma umma kulun magana ya tashi a gidan maganan ta daya ne shine na cika masu gida da diya mata bafa san yadda zatayi da diya matan da nake haifo masu ba.
Innan mu kiyi shiru ki barsu nasan munafuncine aka kula a turani yin bauta a gidan wasu.
Koda Allah ya nufa zan tafi inna nayi maki alkawarin kula da kaina a duk inda na samu kaina din.
Balld ba zaki tafi ba yar mairo muddin nina haifeki ba zaki tafi wanan bautan da umma ke nufin kije ba don kawai ta musgunawa rayuwan mu a gidan nan.
Innan mu don Allah kada kice zakiyi wani abinda auren ki zai tamu gun Abba tunda shima ya nuna baison hakan a gaban mu amma asabe tace sai na tafi.
Kiyi hakkuri ki bini da addua a duk inda zasu kaini ya zama kariya a gareni ko yaushe.
Sai naji ta kara rushewa da wani kukan nima kukan na fara lokaci guds mun dauki lokaci a haka a dakin.
Ranan da wanan bakin cikin gaba dayan mu muka kwana tare da tunanen ina za,a turani shine abinda ke damuna a raina .
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
6️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA LITTAFINA NA KUDINE DON DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA KI DAUKI HAKKIN HAKAN A KANKI SAI WACE TA BIYA TAKE DA ALHAKIN KARANTAWA A SAUWAKE NA FITAR DA HAKKIN KI NA FADA MAKI GASKIYA.
Don Allah ki guji daukan alhaki akanki don gujewa fita ko yaushe abinda ka raina shike zama babba gareka wata rana.
Ban gaskanta zancen tafiyana ba sai ranan da anty safiya ta dawo garin wanan karon ita kadai tazo ba tare da yar uwarta ba.
Ina wa wata mata kitso kamar yadda na saba yiwa mata kitso a kullun aka tare ta cikin mutunci ta samu Asabe na gida a lokacin.
Bata wani jima ba a dakin naji asabe ta kwalawa innan mu kira daga lungunta inna ta amsa taje sai Asaben ke fadi Abun ta shirya don anzo tafiya da itane yanzu kamar yadda na fada maku za a kaita birni aikatau.
Cikin karfin hali inna tace basan da wanan zance ba tunda tun ranan na fada karatunta nake so ta karasa ai.
Yahanasu ni kike fadawa hakan ko kinyatani kike son yi a bainar jama, a yanzu ki nuna min kina da iko kan yarki ko ?
Tama nuna in bashi ba umma zaki bada umurni har ta tsaya tana gardama a kanshi don kawai ta nuna ta isa lantana ta fada.
Eh ai naga alaman hakan kedai yar nan don kawai tana ganin an zuba mata ido dasu a gidan ko ?
A,a umma anty safiya ta fada kin san fa irin wanan abin natsuwa yake so tun farko idan har baku sharwace ta bane ta hanyar daya dace gskiya ba,a kyauta wa matar yaya ba Anty safiya ke fadin hakan.
Wani irin a fada mata ko yau kika zo daukan yarinyar nan nace na yarda ga abindana tsara ai in ita mai tunane ba zata tsaya jayaya dani ko ?
Umma ni ba jayyaya nake dake ba gaskiya ta na fada don yatinyar ban diya mace ce kowa ko bs zaiso hakan ga nasa ba a dauki yarinya akai inda ban sani ba kamar bata ds gata.
Eh lalai magana kike son daukowa kanki yahanasu umma tace tana kumfar baki ga innar mu wanda hakan yasa nayi shiru ina sauraren shiru na sauraren su daga inda nake zaune zaman kitso.
Hawaye ne ya fara zubo min sannu a hankali don na fahinci akan me suke magana naga Abba ya shigo gidan da kyat na iya budan baki na fara gaidashi.
Bai tsaya amsa min yadda ya saba ba ya nufi shiyan Asaben inda yake jin muryan Asabe yana tashi a can.
Wai yaya ne meke faruwa kuma ya fada lokacin da yake shiga wurin Asabe din yana mai binsu da kallo gaba dayan su wurin.
Wanan matar takace ke son ta raina min wayau yanzu wai bata sanda wanan zancen ba ita ba mai tafiya da yarta do ita keda abinta.
Anty safiya tace a, a umma bata fadi hakana ba ta dai nuna bata san da zancen ba sai kuma ra,ayinta na son yarta taci gaba da karatun ta tace.
Abba ya juya wurin inna yana fadin idan mugun wuri za a kai yarunyar nan ai ba za,a hada baki da safiya ko muba a kaita.
Tunda umma tace a kaita din ke meye naki a ciki yanzu banda yiwa yarinya fatan alheri kawai.
Amma dai malam kasan ba ai muna adalci ba idan akai muna haka ke nan bamu da inci daga har yaran sai yadda akayi damu ke nan.
Gunma dai kaji da kunnuwan ka yanzu abinda take nufi ke nan tun dazun ita yar nan bata fahinci hakan ba da cewa anty safiya.
Kinga ki kwantar da hankalin ki kada ki tayarwa yarinyar nan da nata hankalin taje can ta kasa tsayar da hankalin ta wuri daya.
Inna batacewa anty safiya komai ba illa mikewa da tayi ta bar dakin muna jin Asabe na fadin in ba wanan ba wani taimakone ya mace zatayi a gidan nan dayafi wanan na dan lokaci.
Dagani har matan da nakewa kitso a gurguje don inyi in gama mata ta tafi kada taji me gidan mu ke ciki batu yabi gari.
Matar ke fadi wai rikicin me ake hakane nace maganar sune ta manyan gida kawai .
Ina gama mata ta tafi na wanke hannu na na nufi dakin inna kuka na samu inna nayi wiwi zaune a dakin haka yasa nima na samu wuri na fara rera kukan kamar yadda innan mu takeyi.
Muryan Abban mune ya leko falon yake fadin wai ina yar mairon takene ta fito su kama hanya kada a yi yamma a hanya.
Kin tashi nayi sai gashi dakin ya shigo yana fadin bakiji me nace ba tashi ki shirya ku tafi Allah ya tsare hanya.
Wani kuka mai karfi na sake tare da ambatan sunan Abba din ina fadin don Allah Abba kada ku kaini birni bauta.
Har zai fita ya dawo ya tsaya yana fadin kinga kin saka yarinyar nan hankalin ta ya tashi ga tafiyan nan.
Na rasa me kike nufi da hakan gaba daya yanzu kin canza a gidan nan kin dauko rayuwan banza kin sakawa kanki saboda bakin kishi dake cin ki.
Ji Abba fa wai duk haklurin da inna keyi a yanzu Abban mu bai gani har yake fadin haka kai tsaye.
Wani tsawa ya daka min tare da fadin zaki tashi a nan ko sai na makeki wurin nan maza ki tashi ku kama hanya.
Ai gaskiyan umma data kawo sharan turaki birni aiki idan kin zauna nan uban me zaki tsinanawa mutane a nan in bada kullun ku saka uwarku a daki tana koya maku kilibibin baza.
Mikewa nayi ba shiri na shiga daukan kayana a dakin inna ya juya ya fita ganin na fara tsuntar kayana.
A cikin muryan kuka inna ke fadin yar mairo kiyi hakkuri da halin da muka riski kanmu a ciki ki tsare mutuncin ki ibadan ki da kima.
Kije har kullun Allah yana tare da mai gaskiya komai wuya komai dadi ki kula da yin addua kinji sai kuma ta kasa karasa sauran zancen saboda kukan da yazo mata lokaci guda.
Anty safiya ce tashigo dakin inna da kanta tana fadin na fahinci halin da kike ji yahanasu.
Babu dadi ace ba,a fitar maki da hakkin ki ba su sanar dake ku sasanta kanku sai dai nayi maki alkawari insha Allahu wanan tafiyan nata zai zama alheri a gareku baki daya.
Yanzu na kara fahintar rayuwan dake gudana a gidan nan naku na fahinci komai yan mintinan danayi daku a nan .
Murmushin karfin hali inna tayi cikin kukan da takeyi take fadin na yarda dake safiya Allah ya iya muna ya tsare min ita aduk inda take .
Ba komai kitafi da ita din tunda haka suka zabar mata insha Allahu tafiyan nan nata zai zama maku alheri tunda bada zuciya daya suka tura maki itaba.
Ta bude jakka ta ciro kudi masu yawa tana fadin hjyn da zan kaitane ta bada wanan kudin aba iyayyen ta.
Nayi niyar baiwa umma su sai na fahinci akwai kulli cikin harkan nan don haka ki karba kiyi maza ki boye albashin tama idan an bayar nasan yadda zan dinga maku dashi insha Allahu.
Don sam ban dauka ita za a bamu ba nadai zowa umma da zancen muna son yarinya a garin nan idan da akwai yadda za a samu.
Sai yau danazone naga ashe itace zamu tafi da ita ki dauka kamar tana gaban kine insha Allahu.
Jin hakan da anty safiya ke fadi ya kara kwantarwa umma da hankali sosai muryan Asabe ne ke fadin .
Wai ina safiyan take ne in kin soma ki bar bata bakin ki wurin lalashin ta ko ta yarda ko kada ta yarda tafiyan nan ba fashi .
Muna ji muna gani haka muka kama hanya da yan kayana cikin ledan bacco don banda jakkana tafiya da zan saka kayan a ciki.
Inama na taba zuwa hana rantsu daga makaranta mukazo zaria kuma ba a bari an kwana ranan muka koma gida wurin iyayyen mu.
Har kofan gida wurin mota asabe ta biyo mu da lantana tana fadin atafi can a dandadi duniya aji yadda take.
Kina nan zaune gida ba wanda ya taya balle a sallama muna da sunan kiranki zance.
Umma wa zaiso ta a haka tana zama ko yaushe kamar kucaka gari kamar a kansu talauci ya kare a duniya.
Allah yasa dai ta iya abinda taje yi din kar taje ta jawowa mutane abin kunya a can don dai sanin hakin kam.
Kallon Abba nayi don jin abinda lantana ta fada sai naga Abba ya kawar da kanshi gefe daya na mayar da kallona kofan cikin gida namu ko Allah zaisa inga inna ta leko sai dai har motar ta daga banga inna din ba.
KADUNA
Hjy iyami zaune a dining din gidan bata da hutu a yanzu tun soma wanan zancen aikin data samu din koda yaushe tana makale da waya a kunnen ta.
Yanzu ma wayan ta kare da wani lauyanta kan kammala mata duk wani takarda da take bukatan samu wanda za a tura abuja a tura zauren majalissa.
Abincin dake gaban ta ta kalla tana dan jan tsuki kafin ta kai hannu ta sama warmer din abincin dake gaban ta.
Budewa tayi sai ga tururin abincin dake cikin kulan yana tashi kamshi ya daki hancin ta tabe baki tadab yi don tasan ba lalai ne yayi dan danonon da take so ba.
Plate ta jawo zuwa gaban ta ta fara diban abincin kadan ta tsakura don ba gwana bace wurin loda abinci a cikin taba.
Lemo ta tsiya ta fara kaiwa a bakinta tana lumshe ido do sanyi da dandanon shi dake shiga cikin ta lokaci guda.
Sallama akeyi a kofa ta amsa tana ba maishi umurnin ya shigo tafiya yake a cikin isa da izza har ya karaso inda take zaune.
Daga tsayen da yake suka fara gaisawa dashi idon shi ya sauke kan abincin dake gaban ta kafin ya amsa mata gaisuwan nata.
Bissimillah ka zauna take nuna mashi kujeran zama dake wurin yace ba zama nazo yi ba nazone in kara jin abinda kika yanke ga maganan mu.
Alh Adamu ina dai yanzu kasan ba,a karskshin ku nake ba don mai rabawa ya raba tsakani da yayan ku ko.
So banga wani abinda zaisa ka jefa kanka a cikin lamarin rayuwana ba kuma.
Yara daine babu taulali a cikim su gaba dayan su sun kawo girma don haka ka barmu muyi rayuwan mu a cikin sallama don Allah.
Jin abinda ta fada yasa ya dan sakd murmushi a fuskan shi yana jawo kujeran yakai zaune tare da fadin zaki iya fadin haka tunda baki so gaskiya.
Kin sani sarai wanan abinda nake neman ki dashi ba haramttacen abu bane sunnan ma aiki zamu raya ta hakan.
Wani kallo ta watso mai tare da fadin Alh Adamu na fada ma ka fita hanya da maganan banzan ne shin wai yin aure dolene ?
Ya dan kara sake murmushi yana fadin amma kinsan aikin ladane ko na rasa meke damun ki kan hakan idan don ta matatace kinsan dai a yanzu kinfi karfin ta ta ko ina.
Mikewa tayi a fusace tana nuna mai kofa tare da fadin fita min daga gida tunda kai bakasan abin arziki ba.
Kai ko kunya bakaji kazo ka kalli idona kace wai aurena kake son yi don kawai kunga kasa ya fufewa mijjna ido.
Yace shi kansh miijin maki ai da zai tasone a yanzu zaiyi alfari da abinda nake shirin aikatawa a yanzu.
Eh na yarda lalai namiji baida kunya yau Adamu kaine da kanka wai kazo neman yardana akan in aureka don kasa ya gama rufe minin idon miji ko ?
Har kamanta da irin tsana da kiyayyan da matarka ta saka min a gida lokacin da kuke ganin kowa a banza a idon ku shine yanzu don baka da kunya zaka dawo da wani zance a kaina.
Matsalan ku ku mata ke nan dawo da abinda ya wuce baya kada ki hada wancan lokacin kurciya da yanzu garemu.
Ni niyana na alheri ne gareki nasan ko yaran ki zasu farinciki da zaben dan uwan mahaifin su a matsayin mijin ki a yanzu.
Ka fice min gida kafin in saka a fitar min dakai ta tsiya ya ce bazan gaji da tunkaran ki da wanan zancen ba har lokacin da zaki sauko don kanki.
Yana fadab haka ya juya ya bar gidan bishi tayi da kallon takaici da kunan rai wanan yana daya daga cikin abinda ya hanata dawowa kasan tun rasuwan mijinta.
Yana fita gidan wuri motar shi ya nufa kai tsaye yashiga ya dade a zaune yana karewa gidan kallo yata da motar ya tafi.
Mun kawo lokacin yamma baiyi ba sosai don la, asar ya wuce a lokacin kai tsaye gidan anty safiya muka nufa.
Gidane tsarare mai ban sha,awa gaskiya ba laifi gidan ya hadu ni dai a ganina ciki muka shiga yayin da muka zauna a falo.
Tau zainab kinga gida yau dai don har umma bata san inda muke zaune ba duk zumuntan mu da ita yau sai gashi ke Allah ya kawo ki gidana.
Mikewa tayi zuwa wurin fridge ta dauko min ruwa mai sanyi a fridge ta aje min tare da fadin sha ruwa kafin ki shiga ki watsa ruwa kiyi sallah sai ki fito muci abinci.
Daukan ruwan nayi da zuman sha sai naji sanyin shi yayi min yawa a bakina ta yadda bazan iya sha ba.
Mayar da kofin nayi na aje saman dan table din ta dawo tana fadin taso in nuna maki dakin da zaki zauna kafin in kai gidan da zaki aikin.
Dakine da gado sai mirrow ta nufi wani kofa tana fadin nan bandakine ki shiga kiyi wanka da alwala ki fito.
Tana fadin hakan ta juya ta fita daga dakin kayana na fara cire na nufi bandakin kamar wace za,a cewa na sheka na sheka da gudu.
Ina shiga naja na tsaya wuri daya ina karewa wurin kallo da mamakin ban dakine haka a gyare tsab.
Saida na gama karewa wurin kallo na nufi bakin famfon dake ciki badon na taba amfani dashi ba a fili amma dai nasan yadda ake kunnawa ruwa yazo.
Don an koyamu a makaranta nagani wanka nayi a tsanake zuciyana fam da tunanen inna mu da yan uwana.
Sai kuma tunanen Abban mu dasu Asabe irin maganganun batanci da sukeyi lokacin da zan baro gida don wai kawai ina ya mace suke min hakan.
Sallah na tayar saman kafet din dakin ban tsaya neman sallaya ba don wurin tsab yake ni a ganina ina zaune a gurin bayan na idar da sallah.
Sai ga anty safiya ta shigo dakin tana ganina kasa take fadin subbahanallahi zainab badai a kasa kiyi sallah ba sam na manta da na kawo maki abin sallah a dakin taso muje kici abinci ko ?
Mikewa nayi na biyo ta zuwa falon na samu yaranta da sukaje islamiya sun dawo gida a lokacin.
Ku gaida anty tace wa yaran da suke kallona da mamaki a fuskokin su suka fara gaidani din kamar yadda mahaifiyar nasu ta umurce su.
Wuri ta nuna min na zauna tana fadin ki saki jiki ki nan kamar gidane a gare ki zainab.
Nakai zaune ina murmushi abincin ta debo ta kawo min a gabana tana fadin ci abinci nasan rabon ki da abinci tun safe.
Kallon abincin nayi dan shikafane da miya sai taliya da ganye da nama tsoka uku a sama.
Dan tsakura nayi duk da ya zamo min bakon abincin daya dace inyi dsukin cin shi a lokacin tunda ban saba cin abinci haka ba.
Sai gashi halin da zuciyana yake ciki ya hanani cin abincin sai tunanen yan uwana da innarmu nakeyi a raina.
Gashi yan uwa basu gida aka wuto dani balle ko sallama in samu inyi dasu tunda bansan tsawon lokacin da zan dauka a wurin wanan bautan ba dabazo yi garin kaduna kamar yarda umma tace.
Bansan mijin anty yana gidan ba saida naji yana magana da yaran shi na dago da sauri ina kallon shi.
Gaidashi nayi hakan yasa ya dago yana kallona tare da amsa min gaisuwan da nayi mai yake cewa.
Itace kuka zo din tare eh yar dan uwanane sukai min karamci suka ban ita kaga abin yazo min da sauki ke nan.
To Allah yasa a dace sai ki ja mata kunne sosai don kin san zama a irin gidajen nan ba kowane zai iya rawayu dasu ba.
Daki na mike zan koma anty ke fadin zaki shiga cikin ne kuma kifa sake jiki nan gidane na fada maki.
Nace zan kwantane ina shiga naji mijin na anty na fadin wanan yar yarinyar suka turo ban san me yasa mutanen kauye suke da wanan akidar ba kan yaya mata.
Yadda wanan rayuwa take a yanzu kosu masu dauko yarab dasun gane su dogara da shiga fadawa wani rikici sam duniyan nan cike yake da rudani daban daban.
Sai dai daman ita wanan din da kika dauko ansan gidan su da kuma inda zaki kaita din in don haka ba gaskiya da zan baki shawara ki mayar masu da yarsu inda kika dauko ta.
Nima kaina saida naje naji banji dadin ganin wanan yarince zasu ban ba don uwarta ba karamin rikici akayi da ita ba kafin ta yarda muzo nan din.
Yace ke nan uwar tasan kanta da abinda take yi ga yarinya kallo daya zaikai mata kasan tana cikin wani yanayi.
Zaka iya sani tunda aikin kune hakan ai don nuna fin karfi kawai aikai masu daga ita har mahaifiyar ta aka ban ita.
Shine kuma kika dauko masu ya safiya baki tsoro abinda kaje ya dawo nan gaba kada faki lalata maku zumunci .
Wallahi don dai hjy iyami ce kuma na riga da nayi mata alkawarin hakan kaga idan na saba mata ba zataji dadin hakan ba.
Yace Allah ya sauwa ka saidai kija mata kunne sosai kafin ki kaita na fada maki zama irin gidan nan akwai kalubalin masu yawa ga wanda bai saba hakan ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
RAYUWA KE NAN YAN UWA MU FADI ALHERI KO MUYI SHIRU SHINE KOYI DA SUNNAN ANNABI SAW , , , ,
DON ALLAH YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON ALLAH KI GUJEWA KAYAN ALLAH YA ISA A KANKI
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 300 NE KACAL ZAKI TURA SABODA ALLAH SHINE HAKKINA GAREKU.
Na dade kwance a dakin badon nayi barci ba tun ina jin karan tv da muryoyin su a falon har nazo na daina jin komai ina jin anty ta shigo tana ja min abin rufa sai naji sonta na yan uwan taka ya kara shiga raina sabanin dazun da nake jin haushinta ina ganin da hadin bakin ta wurin rabani da yan uwana da innan mu.
Tambayan kaina na karayi karo na batkatai mai Asabe da lantana suke nufine a kaina.
Mau ye lafin innar mu da bata ganin laifin Abba shi tunda ba inna kadai ta haifomu a mata ba.
Meye laifin kasancewar yaya mata da asabe ke gani ga innan mu damu wanan halin shi a kowani gida da yaya mata sukafi biyu zuwa ukku kamar mu.
Ba addinine yace a kyamaci diya mace ba wanan hain rayuwane na wasu mutane da hakan ya zama masu al,ada.
A ganina duk da da aka haifa ta sunna walau mace ko namiji albarkan rayuwa ya kamata iyayye su newa yaro.
Ni dai ba zan iya cewa nayi wayau naga inna da Asabe a cikin dadin raiba a gidan mu duk ko da irin biyayyan da ina ke mata sau da kafa.
Ba zan manta a da can baya har talla asabe ta fara dora min idan na dawo boko zan dauki tallan goro ko gyada in fita dashi duk da ina kankanuwa a lokacin.
Da kyat Abba ya samu ya hana wanan tallan ranan kan yasha fitina wurin Asabe ba Abba kawai ba har innan mu ba,a barta ba don cewa Asabe tayi inna ce ta zuga Abban mu don tana bakin ciki ina fita mata talle.
Haka muke abu kamar marayu a gidan mu bawai don mun rasa uwa da uba a raye ba sai don kawai zama da fitinaniyar uwar miji da Allah ya hada inna da ita.
Yanzu kuma tsanar yakai har Asabe ta turoni yin aikatau a birni ba tare da kowa ba gidan mu yasan inda za a kaini ba.
A haka naci gaba da sake saken abinda zan tafi in taras gidan da Anty safiya zata kaini din.
Juyawa nayi ina lumshe idanu tare da fadin Allah yasa hakan shine alherin mu gaba daya kamar yadda anty safiya ta fadawa inna da zamu zo.
Har barci ya daukeni ban sani ba ga dai gadon laushi ga fanka a dakin na samu amma haka bai hanani barci a cikin damuwa ba.
Karfe biyar da wani abu na falka kamar yadda inna ke tayar damu don sallah asuba idona bude nabi daki da kallo .
Sai a lokacin na tuna da inda nake a yanzu da sauri na sauko saman gadon na fada bandakin dake dakin da nake ciki .
Alwala nayi a gurguje na fito na tayar da sallah ina idarwa na dan zauna nayi addua kafin in mike na bude kofan a hankali na fito dakin.
Duk da sauran duhun dare gari bai gama haskawa ba a lokacin amma na gane hanyan kitchen din anty safiya da jiya naga tana shiga tana fitowa da abinci.
Wanke wanke na sama tare a kitchen din ban tsaya jiran komai ba na shiga wanke su a hankali don kada in tayar da mutanen gidan don har lokacin banji motsin kowa a gidan ba.
Na gama na share kitchen din na fito zuwa falo na fara shara da kakabe kujeru da suka kewaye falon can naji motsi alaman wani na fitowa daga dayan dakunan su na kwana.
A, a naji muryan anty safiya na fadi zainab kece a nan kuma har kin tashi ashe ban sani ba yau na gajine sosai dan tafiyan nan da mukayi jiya duk jikina ciwo yake min wallahi.
Ban bata amsa ba sai kaiwa da nayi kasa ina gaida ita da kwana ta amsa min a gurguje tana shiga kitchen din ta.
Sai kuma gata ta fito tana fadin ke yaushe kika tashi halan da kikayi wanan uban aikin haka zainab kin koyi barci da dare ko kin kasa barcine kina tunanen gida.
Nace nayi barci dana tashi nayi sallahne na fito na wanke su tace ikon Allah toh sannu da kokari ashe tafiya zatayi kyau tunda baki da son jiki haka ?
Abinci ta hadawa yaranta yayin da ni kuma na share ko ina na gidan sai gaidani da aiki takeyi tana fadin kinga idan har zakici gaba da hakan ina mai tabbatar maki zaki ji dadi sosai a wurin hjy.
A raina nace watau ma wurin hjyce za a kaine kenan matar mai kudine tunda naji harda hjy anty ta kirata matar yanzu.
Ni tace in shiga in shirya yaranta a wani daki nayi ta bin dakin da kallon mamaki a raina tana min bayanin abinda zan masu.
Ta fita ta barni da yaran a dakin ina shirya su bayan nayi masu wanka da broshe tsab suka fito a tare muka fito daga dakin tace dani kinga koma ki gyaro min dakin nasu in karasa shirya su a nan.
Dakin na koma na fara tattara kayan da suka watsar kafin in hau gadon dakin da gyara kafin wani lokaci sai ga dakin tsab dashi kamar bashi bane suka bata dazun da tarkace ko ina.
Nan anty safiya ta yaba min sosai tana kara min bayanin kinga tun da safe idan kin tashi kinyi sallah.
Kada ki tsaya sanyin jiki ki yi duk wani aikin da kika san naki ne a gidan tunda kina da kwazom tashi haka da safe.
Don Allah zainab kada ki yarda ki bani kunya don inda zan kaiki nima gidan kunyanane can tayi bugun gaba ne dani tasa in samo mata yarinya natsatsiya mai kwazo da tsabta da amana.
Idan kinga abu ba a baki ba kada ki yarda ki taba shi komai son da kikewa wanan abin a ranki.
Na amsa da to anty tace zaki ga kudi kamar a banza mai yuyuwa zata gwada ki na dan lokaci taga idan kina da amanan hakan kafin ta yarda dake bandai sani ba.
Zan fada mata gaskiya ke din yar uwatace ta jini don ba zan lamunci suyi maki wullakanci irin wanda akewa yan aiki ba ke kuma sai ki rike min amana sosai don Allah wanan abin taimakon kai da kai zamuyi tsakani nidake zainab.
Insha Allahu anty na fada don idan ta kirani da zainab din nan yanzu sai inji kamar badani take magana ba.
Wasa wasa na share sati daya gidan anty safiya banji zancen tafiya gidan da za a kaini din ba, nima kuma ban tambaya ba.
Ashe hikimar ta na barina a gidan ta don dai in koyi wani abinda ta fahinci ban sani ba kada ta kaini a sha wuya a can .
Gashi kullun cikin yi min bayani take da fahintar dani komai na rayuwa a birni wanda mu can kauye bama yin su.
Har na dan fara sabawa da yaranta yanzu sosai ranan da dare muna zaune falo muna kallon wani shiri na yara naji anty ta ambaci sunana .
Hakan yasa na juyo ina kallon ta cikin ladabi take fadin ina ganin gobe zan kaiki wajen hjy dazun muyi waya da ita take tambayana ke .
Wani irin ba dadi naji a raina lokaci guda damuwa da fargaba ya dira min a zuciyana lokaci daya.
Ganin canjin yanayina take fadin ki kwantar ds hankalin ki can ma nafada maki gidane a garemu ai tunda gidan babban yayan mu ne saidai shi a yanzu bai raye matarce kawai da yaran su a gidan kuma yaran ba yara kana bane sun girma kananan ma zaku zo yan sa,a daya dasu.
Sai dai daga mazan har mata kada ki shiga tsabangan kowa duk abinda suka saki indai baya kaucewa idini bane wanda kuma ya shafi gaban kowa a cikjn gida kiyi.
Na fahinci may anty ke nufi a nan ma, ana na kama mutuncina da kimata ga kowa a gidan dai.
Haka na kwanta da tunane mai yawa sai kewan gida ya dawo min sabo sosai a raina don haka ban samu barci sosai a ranan saboda tunane.
Karfe goma na safe muka bar unguwan su anty safiya wanda nake jin ana kira da barnawa muka doshi inda zasu kaini a motar mijin anty safiya din.
Anty ta ban wani jakka nata na saka yan kayana wanda ta sai min kala hudu dana zo don tace nawa ba zasu tafi ko ina ba a haka.
Sai bin garin nake da kallo yayin da anty suke gaba da mijinta zaune suna dan hiran su da ban san ko a kan wa suke zancen su ba.
Kafin mu bar gidan anty safiya sai da sukai min nasiha sosai mjin anty safiya yace in kiyaye ibadana inyi hakkuri da duk yanayin da zangani a gidaba, ainyi biyayya ga wa yanda na sama a gidan.
Shiga nan bullo nan har muka kawo unguwar mai kama da kasan waje muka fita ba jahata na kaduna ba.
Uguwar kanshi abin kallo ne ba mutane sai motoci jefi jefi da suke wulgawa saman shimfudeden kwaltan da aka zuba a titin.
Idan kaga wanan ginan sai kace shiyafi kyau sai kuma idan kaga wani kallo ya koma sabo.
Wani katon gida daya tafi da imanina tundaga nisa mijin anty ya tsayar da motan shi yana danna horn.
Kafin wani mutum daba tsoho ba ya fito yana dan lekowa naji anty na fadin bude get mune da mijina.
Ya amsa yana washe baki tare da saurin komawa sai naga kofan na budewa kamar injin.
Ya danna kan motar zuwa cikin gidan naji mutumin gidan yanayi masu sannu da zuwa da alama dai yasan anty din sosai .
Saida mijinta ya tsayar da motar shi ne take fadin amma dai kasa yau zaka shiga ku gaisa da hjy ko ?
Yace zan shiga kodon ta san yarinyar nan tana da muhinmaci sosai a garemu ai don ni dai da kinbi tanawa da ba, , ,
Please dear ina mun gama wanan zancen tun a gida sai kuma ta juya da harshen turanci tana magana.
Ko ta dauka bokona baikai indanji abinda take fada bane oho do maganan da sukeyi da alama mijin nata yace a mayar danine kota rikeni tunda yar uwarta nake.
Allah sarki nace a raina wanda ma suka haifeni suka san zafina sun kasa barina a gaban su balle anty da daga sama ta ganni haka.
Don ina jin tana fada mai taso hakan amma kawo ni nan din shine mafita a gareta naji yace to shike nan Allah ya tsaya mata da hausa.
Su suka fara fita daga motar kafin anty din ta zagayo ta bude min gefen da nake tana fadin in fito.
Na fito sai bin gidan nake ko ina da kallon mamaki ina rayawa a raina wai yanzu mutane ne sukai wanan ginan haka da hannun su ?.
Nidai ina bisu a baya ina karewa gidan kallo ta danna wani abu a bango ba, a dauki lokaci ba sai ga wata yar dattijuwa farace tafito tana fadin waye sai sukayi arba da anty dake tsaye a kofa.
Hjy kece take cewa anty safiya nice kande ko hjyn tana ciki ta tambaye ta ?
Tana nan yanzu ko tashiga daga cika ta fadi tana matsawa daga kofan da take tsaye.
Shiga mukayi kai tsaye saida naja baya don abindana fara takawa ko ina na falon sai kyali yake da daukan ido.
Zama sukayi a kujerun dake katon falon yayin da nakai kasa daga gefen anty din mijinta ya kalleni tare da fadin ki zauna saman kujera mana.
Naji anty tace kasan ta ai da halin su na yan kauye barta kawai zata zo ta saba wata rana ai.
Matar da naji anty ta kira da kande ne ta dawo falon dauke da tire da abin sha a ciki.
Ga kan shin girki yana tashi a wani bangare na gidan duk da kamshi da falin keyi bai hana na girkin ziyaran hancina ba.
Ga abin sha hjy kafin hjy ta fito, ta fada tana ajewa a gaban su bin abinda ta aje din nayi da kallo.
Saida suka dan taba hira da mijin ta muna zaune ni dai sai bin hotunan dake tsaye a falon manya manya dasu kamar mutun ne tsaye a wurin nakeyi da kallo.
Sai ga matar gidan ta fito da fara,a a fuskanta tana fadin ashe kuna tafe yanzun nan na shiga ciki.
Tun safe yaran nan suka tayar dani da rigimar su na fito tarba na mutunci naga tana masu tana saki fuska da jiki dasu.
Ta kalli mijin anty tana fadin yau baka fita aiki ba ke nan ta fada tana kallon shi.
Ban fita daga nan zan wuce ya bata amsa da kara fadin yarinyar nan muka kawo dama.
Ta juyo tana kallona tare da dan kuramin ido na dan lokaci tace masha Allah.
Yarinya kamar kin shiga zuciyana kinga irin age din da nake so ta kasance min gashi ko kin samu ai anty safiya ta bata amsa.
Menene sunan ki ta juyo tana tambayana kafin ince Abu naji anty safiya tace zainab ce sunanta.
Kai zainab kice uwata ce ashe yarinya kin samu suna mai kyau kuwa tana kallona da kulawa.
Aikuwa na manta sunan mama na unguwar rimi ke nan fa dacewa kanwar mahaifiyar hjyn .
Mijin anty ne yake fadin ni zan tafi hjy don Allah sai a hada da hakkuri don kin san yarinyar akwai kurciya da kauyanci a tare da ita yanzu.
No no no kada kuji komai wallahi muma ai kauyene asilin mu a da ko kowa ka gani daga kauye yake ai.
Shigowa wasu yara kanana su biyu mace dana miji falon yasa zancena ya tsaya a nan suka juya magana kan yaran.
Anty ke fadi a a ashe mutanena suna nan sai hjy tace wai yau hutu sukeyi basu je school ba sun shiga meet time break ne.
Hannu anty safiya ta mika masu suki tare da make kafadun su suka nufi sirin kakan su kai tsaye.
Tafiya ya fara yi tare da fadin to zainab a kulla kinji banda rashin ji anty safiya tace in tayi rashin ji ai zata gamu da nine sosai.
Karfe nawa zaka dawo yace na fada maki sai yamma don haka idan kin gama ki koma gida don yara kada su dawo school bakya nan.
Wai har yanzu motar bai tashi bane hjy ke tambayan anty motar ta kafin anty tace wanan motar ai sai wata yanzu gashi yaki ya saya min wata ina ta faman bin shi yana ja mi rai.
Ki bar kanina ya huta safiya indon motace zan sa a duba maki idan ba zaki raina ba dai kai kai kai kice wanan zuwan takice ashe mijjn ta ya fada .
Kasan ai safiya ta hannun damana ce sosai tafi danan a gurina in dai tana so.
Ya tafi tare da ma hjy sallama nabishi da dan kallo kamar ince don Allah kada ya tafi ya barni.
Anty ta mike tabi bayan shi bayan tafiyan tane falon ya danyi shiru tana ta danne danne a wayan ta sai ga anty safiya din ta dawo falon.
Zama tayi sukaci gaba da hira a cikin hiran nasu ne take fada mata yadda muke da ita .
A hiran na kara fahintar irin zumuntar dake tsakanin mu da ita din wai ashe mahaifiyar su da Asabe ce ya da kanwa.
Asabece ya mahaifiyar su kanwarta tace kai kice min ita din ta gidace ashe eh ta gidace gaskiya sai dai gaskiya kin san yadda zumuncin zamanin nan yake ai.
Koma dai yaya ne ai takice ita zan duba inga yadda zamu zauna sai ta kira wanan matar ta dazun data kawo ruwa tana fadin.
Kande ga bakuwa ki bata daki wanan na kusa dani zaki bata don ni tazo gidan nan don kula da harkokina.
Don haka zaku zauna tare sai dai kowa da aikin shi daban ke naki kula da kitchen ne da sauran ayukan da kika sa kinayi.
Ita din dai ki barta dani sai zuwa gaba idan ta saba zan fara nuna mata aiyukan ta yadda ya dace.
Sannu da zuwa kande tace min tana kokarin daukan jakkar kayana da anty ta shigo dashi ta aje a kuss dani.
Kagin anty tace na karbs ni har na mike ina karba matar na fadin ai da ki barta bakuwace fa nace a a mama kawo in dauka.
Jeki ta kaiki daki da zaki zauna kafin in shigo hjy ta fada tana dora kafanta saman dan table din dake kusa da ita.
Muka nufi cikin gidan wanda bai isata da kallo matar na gaba ina binta har zuwa cikin dakin da akace ta kaini din.
Dakin ta bude tana fadin bissimila shigo daga ciki nabi bayanta muka shiga.
Wanan shine dakin ki sai ki zauna ki huta kafin girki ya sauka a wuta muci ni nawa dakin yana can daga waje kadan ta hanyar kitchen idan kina nemana.
Daga haka ta juya ta barmin dakin ina tsaye sai bin dakin nakeyi d kallo nida ke santin gidan anty safiya sai gani a wanan dakin da fadin tsaruwan shi bata lokaci ne.
Anty safiya bata bar gidan ba sai karfe dayan rana bata tafi ba saida ta shigo dakin ta kara min nasiha kan nayi biyayya ga kowa a gidan .
Ta tafi ta barni cikkn kadaici da damuwa a gidan da ban san kowa a cikinsa ba ban ma san a inda nake ba dai.
Wani irin kuka ne na rushe dashi ganin ta tafi ta barni daga ni sai halina sai wa yanda a yanzu zan zauna dasu din.
Ganin kuka ba zai min bane yasa ni tashi na shiga bandaki dukda ba a nuna min ba dan zaman da nayi gidan anty na dan fahinci ya ginan birni yake yanzu.
Alwala na dauro nazo na tayar da sallah ban daga ba na dade a wurin ina addua kafin na dan kai kwance sai ga barci ya daukeni a haka ba tade dana sani ba a wurin.
Babu komai a raina sai tunanen halin da mahaifiyata take ciki a yanzu tare ds yan uwana a raina.
Nasan innan mu zata kara shiga wani hali a yanzu don barina kusa da ita dan taimakon su daya ne wanan kudin da ban san ko nawa bane da anty ta bata da zamu zo.
Irin wanan tunanen nakeyi sai hawaye yazo mi lokaci guda don tunanen hakin da inna zata shiga yanzu da ban kusa dasu dama da dan kudin kitson da nake muke tallafawa ake samun abinda akaci.
Gashi yanzu lantana da Asabe sunyi makarkashiyan da aka raba tsakanina da mahaifiyata da yan uwa anya zan iya mantawa da wayan nan mutanen a raina kuwa , ?
.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ALLAH KA SADA MU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN RANAN TA JUMMA,AT ALLAHUMA AMIN , , , , , ,
DOMIN SAYA SAI KI TURA KUDI TA WANAN ACCOUNT DON KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , , ,
Ni Abu ban taba tunanen zan gani a cikin irin wanan dakin ba ko a mafalki ban taba hango wanan irin gidan a malkina ba.
Yau sai gani nayi barci na falka na ganin cikin wanan gidan ga sanyin AC da kande ta kunna kafin ta fita ya hade dana ties din dakin yana ratsa balgon jikina a hankali.
Duk da sanyin yana damuna ban tashi a yadda nake kwance ba a kasan na dunkule a wuri daya sai faman tunane nakeyi na rayuwa.
Muryan hjyn ce yasani dagawa daga inda nake kwance wanan karon ta sauya kayan dake jikin ta zuwa dogon riga mai laushi da daukan ido jikin shi wani dabbara dabbara ne kamar jikin zabra.
Taci gaba da fadin ke zainab bakya gudun sanyin kasan nan ya ja maki illa kiyi ciwo fa.
Da sauri na dago ina gaida ita dakin take bibda kallo ta sauke idon ta ga jakkan kayana tana fadin ga wardrobe nan ki saka kayan ki a ciki .
Taci gaba da fadin ki dunga kula da kani ki kula da tsafta sai muyi zaman mu lafiya.
Mu gaimaki juns tsakanin mu don kingani nan bana shiri da wanda baida tsafta sam.
Iyakar sikin ki a gidan nan yanzu shine kula da sashina da komai wanda ya shafi rayuwana a cikin gidan nan.
Yarana duka manya ne kuma duk zasu girme maki kinga kenan suna matsayin yayyin ki ne.
Ni a yanzu yar kasuwace kuma mai rike da mukamin gwanatin kasan nan .
Kinga ina da manyan hidimomi a tare dani wanda hakan yasa banda lokacin kaina shine dalilin da yasa nace a samo min yarinya da zata dinga taimakamin.
Sai gashi ke Allah ya nufa a sama min na kuma yaba da irin yanayin dana ganki dashi na natsuwa .
Ina fatan zaki zauna damu gaba daya gidan nan da zuciya daya cikin amana da yarda.
A hankali na dago kai tare da fadin insha Allahu hjy nayi alkawarin hakan.
Ban iddasa rufe bakina ba tace ba hjy nake a gurin ki ba mami nake don ni uwarkice a yanzu ki dauke ni yadda sauran yaran gidan nan suke daukana.
Da fatan kin fahince ni tace ta fara tafiya don fita dakin tare da fadar ki fito kici abinci a falo yanzu idan kin gama saka kayan a ciki.
Na amsa da to hjy da sauri nace mami tayi murmushi ta fita yayin da baki na yake dafe don katobaran dana farayi.
A gurguje na jera kayan kamar yadda tace saidai saida nasha wahala wurin gane yadda zan bude wardrobe din.
Falon na fito na dauka ita kadai ce kamar dazun sai dai naga sabanin hakan don sun kai su gama zaune wurin a ganina.
Ja nayi na tsaya dan nisa kadan dasu ban karasa wurin da suke ba hjy ce ta dago tana fadin.
Zainab zo ki zauna mana kici abincin tana kallon inda naja na tsaya dan nisa dasu kadan.
Firgigit nayi daga sana,ata dana fara watau tunane don yanzu ya zama min abin yi ko yaushe.
Sai lokacin sauran dake zaune suka farga da fitowana falon gaba dayan su juyowa sukayi suna kallona lokaci guda.
Karaso mana kizo nan ga abinci nan ki diba ta kara fada sai naji sun kwashe da wani dariya.
Wai mami sabuwar mai aikice kika dauko kuma take tambayan hjy tare da juyawa taji amsan da zata bayar.
Haba dai mai aiki a haka kuma sai a rasa wace za a dauko aiki sai wanan yar kauyen haka irin yan kauyen nan fa wahalan sha,ani garesu kafin kansu ya waye don basu iya komai ba sai shirme da kauyanci wata yar farafara ta fada.
Dayan ta yamutsa fuska tana fadin but she is dirty mami don Allah kada ta karaso nan inda muke.
Ai kin san halin hajjajo da son mutane yanzu haka wani wurin ta kwasota itama ya fada yana mayar da kai ga abincin da yake ci.
Yar uwan gwaggon Safiya ce kuga kenan kuma ta zama yar uwarku ai .
Yanzu a nan gidan zata zauna damu ke nan ko dai tazo yin wani abune Rufaida ta tambaya a yatsune ?
A haka mami zata zauna damu Nazifa ta fada tana kyabe baki tare da fadin ashe zamu sha kauyanci a gidan nan kuwa.
Hjy tayi murmushi tana fadin in dai wanan da kuke ganine cikin kwana biyu zata goge ta zama yar birni tayi fes kamar kowa.
Dariya suka sa gaba dayan su a lokaci guda nidai ina tsaye a inda nake ina kallon su kasa kasa ina jin cin mutuncin da suke min.
Zainab kinja kinyi tsaye karaso mana ki dibi abinci kici hjy ta fada tana yafutoni da hannu.
A, a mami don Allah dai karta matso nan ta bari idan mun gama sai ta zo ta diba amma ai haka raina mu zatayi ta dauka daya muke da ita.
Tsawa hjy ta dakawa mai maganan tana fadin karna sake jin haka daga gareki ita din ba mutum bace kamar kowa nima a haka mahaifin ku ya daukoni ai.
Shiru sukayi suna cigaba da cin abincin su yayin dana karaso inda hjy take na dan labe ina kaiwa kasa na fara gaida su.
Ku duba yadda ta baku girma yanzu a cikin mutunci amma ku kuna kokarin zubar da darajan ku a idanunta, baku san cin fuska baida dadi ba.
Shiru sukayi kowa na kai abinci ga bakin shi tashi ki dibi abinci hjy ta sake fada karo na barkatai.
Plate wace batai magana ba ta jawo ta fara zuba min salma ke nan ta juyo tana fadin may za, a zuba maki ?
Na nuna wanda ke cikin plate din dayan namijin dashima baiyi magana ba sai kallon banza da yake min.
Dariya suka kwashe dashi ya dago kai yana tambayan menen suke cewa choice din ku daya da yarinyar nan abincin ka ta nunafa.
Ware idanuwa yayi waje tare da fadin ke ni sa,arkice bakiga kowa ba a wurin nan saini halan.
Yana fadin haka yai kwafa ya ture abincin ya tashi daga wurin sai suka kara fashe mai da dariya.
Miko min abincin tayi na karba tare da dan rusunawa ina fadin nagode na juya zan bar wurin naji hjy na fadin ina kuma zaki tafi kici abincin ?
Dan marairaicewa nayi ina fadin dakina hj, , mami ba zaki sake jikin ki ba har yanzu kina kewan gidane ko nidai na danyi murmushi na juya na tafi.
Ina kallon abincin wai duka wanan naman da aka zuba a ciki nawane ni kadai kai yan birni kan suji dadin su.
Wanan ai shine zamuci duka gidan mu da sallah idan yazo don sallah kadai muke cin nama sai ko idan rabo ya ratsa Abba ya sayo muna a ci.
Gaba daya na cinye abincin tas na dauko plate din zuwa kitchen don na fahinci a nan kitchen din yake dazun da mama kande ta fito da abinci.
Na canka daidai na samu baba larai tare da wata mata tana juya miyan da zasuci da dare miyan kaine saidai ban san ko kan me bane na daiga ya ciko tukunya sosai tana motsawa.
Gaida su da aiki nayi kande ke fadi kin kamala ci yar nan ina jin marasa ta idon gidan nan dazun sunayi maki shakiyanci da suka iya.
Ki fita batun su dan haka halin su yake da rainin wayau tsiya tundai in sun raina da kuran mutum sai suso su raina shi.
Don ma hjy tana taka masu burki aida abin nasu yafi nan wallahi dayan matar ta fada.
Inda wanke wanke suke na nufa na shiga hadawa da sauri kande tace yar nan me zakiyi nace wankewa zanyi mama.
Rufa min asiri kada hjy tazo tagane ki tace na baki aikin da yafi karfin ki ko dazun saida ta kara jaddamin zance a kanki.
Zan iya ai basu da yawa na fada ina kokarin hada kayan wa yanda sukaci abinci dasu da yamma.
A gurguje na wanke kayan tas dayan matar da ake kira larai tana saka min albarka na kare tare da fadin aikwai wani aikin da zanyi kuma mama na tambaya ?
Babu yar nan sai dai kizo muje dakin hjy na fara gwada maki aiyukan datace a nuna maki na bangaren ta.
Hannu ta dauraye tana gaba ina binta baya muka nufi inda sashen hjy yake don gyarawa a kofa muka tsaya.
Tana kwankwasawa kafin a bamu izinin shiga daga ciki hjy tana kwance kishingide saman wani kujera mai kaman gado a dakin.
Ga wani abu babba kamar waya a gaban ta tana latsawa ta dago tana fadin kande baki bar yar nan ta huta ba yau yau da kawota.
Ai sai taga aibun kan hakan to hjy nayi laifi wai gani nayi dai ta fara sani tun yanzu ai ba aikin zatayi ba a yanzu gani kawai zatayi ta koya.
To shi ke nan hjy ta fada tana mayar da hankalin ta wurin abinda takeyi a lokacin.
KAUYEN ANCAU
Iska na wahal da mai kayan kara a gidan nan yarinyace dai ta tafi ba dawowa zatayi ba balle mutum ya shige daki yaki fitowa.
Lantanace ke magana ita kadai a tsakar gida inna na daki tun bayan tafiyan mu har yara suka dawo boko suka tafi islamiya taki fitowa waje.
Gashi sai tambayana suke inna ina yayar mu bamu ganta ba tun dazun tace dasu ta fita kawai daga haka kowa ya shiga harkan gaban shi.
Sun tafi islamiya sun dawo sun samu inna a yarda suka barta haka yasa saratu mai dan wayau a cikin su sake tambayan inna.
Inna wai lafiya kike yau kuwa ina yayan mu tajene tun dazun bata dawo ba kuma ban santa da zuwa unguwa haka ba ai.
Hawayene ya fara zubawa inna da sauri saratu ta juya wurin jakkan kayana tana dubawa tare da fadin inna sun dauke yayan mu sun turata aikatau ke nan ?
Wani irin kuka inna ta kara fashewa dashi lokaci guda saratu ma kukan ne yazo mata sai hakan ya jawo hankalin sauran yan uwan mu dake wasa kofan inna.
Saratu ke fadin wayo yayan mu ki dawo kada kije aikatau don Allah an ce ana lalacewa wurin aikatau din nan.
Haba dakin inna ya koma dandalin kuka da tashin hankali don kuka sosai yaran keyiwa inna.
Da gudu lantana taje ta kira Asabe tana mayar mata da karya wai ga inna can ta tasa yara a gaba sai kuka sukeyi don tafiyana.
Asabe ta fito babu ko dan kwali a kanta sai a hannu ta rike tana fadin bamu cikin abin kuka da yamman nan .
Kuyi muna shiru masu mugun manufa da sheri don tafiyar yar uwarku zaki zauna ki dasa muna kuka ke da yara haka kamar anyi mutuwa a gidan.
Asabe wallahi sai kin dawo muna da yayan mu ko zaman gidan nan ya gagareki keda munafukanki da cewa lantana.
Mara kunyar banza da wofi koke can kika nufa idan naji dadin yar uwanki ana turo min kudi irin haka marasa hankali kawai.
Da kuna zaune a gida kara zube ina zamu samu irin kudin da muka samu yau a gidan ba gashi har kun dawo kun samu anyi abinci ba yau.
Kowan nan sai ya dandani wanan hanyar aini yanzu gaba haihuwan ku ya kaini tunda na samu mafita daku.
Ana cikin hakane Abba ya shigo yana fadin yaya yayane tun a kofa nake jin muryan ki umma.
Asabe tace barni da mutanen kawai din nan wai tafiyar yarinyar nan yahanasu ta saka yaran nan a gaba suka mayar muna da gida gidan makoki.
Yahanasu kina da hankali kuwa ke yanzu idan kina da tunane ai wani nauyi aka rage maki Abba ya fada.
Fada mata dai ko zata gane hakan ina nan gashi dan kudin da hajiya ta fara bayarwa kowa ya fara amfana dashi gidan nan ba gashi kunci shinkafa da wake ba yau a gidan.
Umma kyale ta barin ganta ni yahanasu har mamaki take bani yanzu kan yarunyar nan babu nuna kawaici a kanta ko kadan.
Idan ma bata nuna ba ita ta sani nidai na nuna mata nike da iko da abina daga diyan ko har kai a gidan nan ko wa yan nan na samu mai daukan su bayar dasu zanyi zuwa birni.
Ba saki bada muba tunda ke kika haife mu cewan Saratu sai inna takai mata duga daidai Abba na shigowa dakin inna din.
Bar dukan ta rabuwa da dan uwa nada zafi tundai irin wanan na yarsu nima dai ba haka naso tafiyan nataba kai tsaye so nayi muje tare inga wurin.
Koma dai menene yanzu aikun nuna min kukeda yarku saidai ina son ku sani naji umma na fadin har wa yan nan za a tura min can birni aikatau.
To wallahi hakan ba zai yuyuba wanan ya isa haka idan da hali dawo da yata zanyi gabana yafi mun kwanciyar hankali idan kasa mukeci mu kwaba muci tare.
Toto to ya isa haka yana sa hannu ga aljihun shi ya ciro yan dubu guda biyu yana fadin ga wanan kya samu ko sabulun wanki ku saya.
Da da nake saya kai kake ban kudi katafi da kudin Allah ya isan ka can kuci ku kadai ku gani.
Kwadan ku ya fada kun raba ni da yata kun rabata da gatan ta da Allah yai mata don kawai tana diya mace.
Shiru Abba yayi don inna bata taba tsayawa ta fada mai magana ba haka kai tsaye irun ranan.
Kwafa yayi ya fita bayan ya mikawa saratu kudin yana fafin karbi ki aje mata idan ta sauko zata karba a wurinki.
Yana fadin haka ya fita daga dakin don kada yayi laifi a gurin lantana dake tsaye ta rike kugunta tun shigan Abba dakin inna.
Yana fitowa fuskanta ya fara kallo ta watsa mai wani harara ta juya zuwa dakin ta shima abba yasan sauran zancen ranan a guri lantana don haka wani dabara ya fado mai.
Yana shiga dakin ta juyo zata fara fada yace me zakiwa fitina kin san dai ba zama nayi a can ba rufe mata baki nayi da dubu biyu ke kuma ga naki dubu biyar ki rike.
Sai lokacin lantana ta dan saki murmushi tana fadin wallahi yau Allah yaso ka da kakoma can ka kwana surin tsohuwar matar ka
Nina fara hakan gani da dalleliya kamar ki inje dakin da warin fitsari da kwamatse ya ciki.
NEW G R A KADUNA
A hankali mama kande take koyar dani komai duk wani abinda ya shafi mami da zirga zirgan ta na cikin gida nice mai mata hidinar shi..
Da na zauna zaki ta kirani da zeey zan amsa da na,am mami in zo da sauri don biya mata bukatun ta wanda ba wani aiki bane.
Sai dauko min kaza jiki mayar da wanan a cikin wardrobe ko dauko min ruwa shine aikin nawa kawai dawai mami bata iyawa sai an dauko mai mata wanan hidimar da ban daukeshi a aikin komai ni.
Sai gashi cikin sati daya kacal na gane komai na mami nasan lokacin tashin ta daga barci .
Zan shiga dakin in gyara gado in wanko mata ban daki zan koma in hada mata ruwan wanka tana zaune tana lazumi don mami akwaita da yawan ibada sosai.
Zan dawo dakina in jirata tana tashi zata kirani in dawo in share dakin duk da ba wani datti ke ga dakin ba amma kullun sai nayi gyaran shi sau biyu a wuni.
Kafin ta fito wanka nagama hada komai sai in koma dakina can kuma idan ta fito zata kirani da zeey zan zo in je dining in hada mata tea wanda wani ruwa ne baki kawai sai dan sugar kadan bata shan madara da suga ita.
Idan na gama zan koma dakina inyi wanka in shirya in dan huta kafin ai mi wani kiran kuma inzo.
Kai masu kudi suna shagalin su banda abin aikin kudi wai wanan dinne aikin da aka raboni da gida do shi aikin da mutum zaiwa kansa ba sai ya nemi mataimaki ba.
Amma hjy gashi tana ganin ina aiki sosai sai fadi take yarinyar akwai kwazo da sanin ya kamata.
Do ita gani take yanzu komai na zuwa mata da sauki a nata bangare har zata samu tayi barci ta huta na dan lokaci.
A bangaren yaran gidan hjy kuwa ba ruwab su da shiga tsabgata nima hakan ne dasu.
Saidai su wani lokacin zasu sakani wani aiki a gidan wanda ya shafi rayuwan su suma ga tsana karara da ko wace ke nuna min.
Dan gara salma da har yanzu ba zance tsanane ko tausayina ba a ranta don na kasa fahintar inda ta dosa dani a ranta.
Wani lokaci inji sanyi a wurin ta wani lokaci kuma idan ta daka min tsawa sai na gigice don tsoro.
Ita irin mutanen nan ne shiru shiru da mugun ta don surutu bai dameta ba ko kadan za a zauna wuri ba zakaji bakin ta ba sai wani lokaci ta furta idan ta furta daya kuma shike nan.
Duk wanan abinda suke min bai damuna naka ma raya a raina idan naga sun dau wanka zasu tafi school nakan ce inama a ce nice a matsayin su haka.
Nasan da ko Asabe ba zatayi gigin takani ba balle lantana dana tsana fiye da kowa a gidan mu yanzu.
Ni dai na rasa dalilin da yasa yaran gidan hjy suka tsaneni a baki dayan su in ka debe hjy da mama kande da suke nuna min kulawa a gareni.
Tun dai ace yan matan don a fili suke nuna min kin jini da kyama duk da yanzu nasan nima ina tsabta fiye dacan da nake Ancau din mu.
Na kanyi tunane indon dun kauyancine da kazanta yazu duk na daina wanan a ganina do na canza nayi fes na kara zama shar kamar bani ba.
Ga mai da turare na yan gagu da hjy taban tace in dinga shafawa idan nayi wanka gun kashe gari dana zo.
Komai ina yi shi a taka tsamtsam a gidan ban yarda in ketare iya inda aka ajeni ga aikina dan dama wani lokaci idan zama ya isheni nakan shiga kitchen in taya su mama kande aiki do su basu da hutu kamarni.
Ko yaushe a cikk girki suke dan hutun su kadan ne tundai idan yaran gidan suna gida wancan yace kaza yake so wana yace baya cin kaza yau.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
9️⃣
YAR UWA NOVEL DINA NA KUDINE KIJI TSORON ALLAH KI BAN HAKKINA KAFIN KI KARANTA DON GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , ,
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI TURO KATIN WAYA DARI UKU NE KACAL BA YAWA, , , ,
Ina daki naji muryan hjy tana kwalla min kira daga dakin ta nima na amsa da karfi da Na,am mami.
Fitowana daga wanka ke nan lokacin don haka na dauki riga a gurguje na saka a jikina don zuwa amsa kira hjy din.
Na sameta zaune tana waya saman gadon da yasha gyara a wurina tunda safe nake gyaran dakin mami din don duk wani aiki da zata kai ga bude baki tace inyi kafin ma tace nayi din tunda yanzu nasan aikina a gidan.
Bana jin kiuya ko kasala tunda na saba aikin daya fi wanan a kauye don hakane hjy bata samun matsala dani koda an samu din ma saidai gyaran dan abinda ba,a rasa ba kawai.
Ganin tana waya yasa naja na tsaya daga nesa kadan ina jiran ta gama waya ta bani umurnin abinda zan mata lokacin.
Wasu kaya data fitar ta nuna min da hannu alaman in dauko mata su ban tsaya ba na juya zuwa wurin kayan na fara dauko su ina ajewa a gaban ta.
Sai waya take ta faman yi mai kama da fada da alama dai da danta ne ko wani kanin ta take waya yadda nake jin tana fitar da kalamai gareshi.
Bayan na gama kwaso kayan ne naje gefe na tsaya don bata ban umurnin in tafi ba.
Hango tawul din data fito wanka ta goge jiki nayi gefen gadon ta na juya zuwa wurin na dauke tare da nufar kofan ban daki na shiga na baza shi a dan karfen da ake bazawa.
Unders din da suka taru a duk da na ranan dana daren jiya datai amfani dasu ne kamar rigan nono da buje da handkacin amfanin ta.
Sai na tsaya na wanke tun ina jin muryan mami tana waya har nazo na daina ji da alaman ta dai gama wayan ne a lokacin.
Nafito ta bini da kallo tana fadin wai dama kina cikin dakin nan zeey ?
Ina ciki ina wanke under din da ke ajene tace min kai zee bakya hutu ko yaushe kina cikin aiki ai kiranki nayi kawai don ki miko min kayan nan in gani don jiya aka turo min su daga Dubai.
Daga min su daya bayan daya nagani na duka na fara dauko kayan ina dagawa daya bayan daya tana daga kai idan na nuna mata.
Amma sai naga kamar wanan yafisu tsaruwa zeey tana tambayana ta hanyar dago kanta taji me zan fada.
Mami duk suna da kyau sai dai wanan din zai fi maki kyau gaskiya don kallan jikin ki.
Ido ta kura min kamar tana nazarina kafin tace ashe kin iya zaben abu mai kyau kema ni dai murmushi nayi kawai ina kawar da kaina gefe.
Sai dai ke har yanzu dadina dake kinki sake jiki a gidan nan ki nuna nina haifeki kamar kowa .
Kullun kina abu kamar bakuwa a gidan nina rasa wanan halin naki kodai bakijin dadin zama da mune zainab ?
Da sauri na dago kai ina fadin mami ina ji haka dai yanahina yake ko a gida nan ma aina sake ke nan .
Sai tayi dan murmushi tare da fadin a hakan da kikeyi sai na dinga tunane ko bamu kyauta makine wani sa, an.
Shigowan Rufaida dakin ne a daidai lokacin da nake kwashe kayan zuwa wardrobe din mami kamar yadda ta umurceni inyi.
Rufaida tayi sallama ta shigo ina jin suna gaisawa da mami din take fadin kunga dama kun tashi ke nan yau weekend kun samu wuri kun kwanta kuna ta barci ina sauran mashiriritan suke basu tashi bako har yanzu ?
Ban dubasu ba ta bata amsa gefen hjyn naga ta zauna ysyin da nazo wurin da niyar incewa hjy din akwai wani abinda zan matane ko in wuce.
Kafin in furta Rufaida ta daka min wani uban tsawa malama may kikeyi kuma a nan bakin gama aikin ki ba ki fita magana nake son yiwa mami yanzu.
No no no Rufaida na fada maku bana son wanan hattaran da kukewa yarinyar nan bari ganin tazo tana aiki a karkshin mu.
Ku dauka hakan gazawa ne ko wani abu ni da kaina na rokota hannun iyayyen ta kuma aikaimin karamci aka ban ita don haka duk daya na dauke ku gareni don jinta nake kamar diyar cikina itama.
Bana son wanan halin da kuke nuna mata a gidan nan to ai mami biyan ta akeyi bata daya damu ai.
Na fada maku ban son hakan da kukeyi nan aikin ta yake tare dani dole kuma ta shigo dakin nan tunda abinda tazo yi ke nan a gidan nan.
Baki Rufaida ta zunburo wai ita an mata fada ni dai ina tsaye ina sauraren su can nace mami da wani abinda zan maki yanzu ne wanka na fito dama ?
Yamm yamm yamm don Allah fita kiba mutane wuri inda aikin ma zan karasa mata shi amebo kawai.
Nidai na juya na fice daga dakin raina bai min dadin hakan ba ko kadan yadda yan matan nan suke min a gidan gashi naga duk da mami na tsawata masu sai dai bata son ransu ya baci ko kadan.
Yanzun na gama waya da yayan ku yana son ya raina min wayau wai ba zai samu zuwa rantsar damu ba da za ayi.
Abinda naji mami tana fada ke nan lokacin da zan fita daga dakin bayan korar da Rufaida tayi min.
Dakina na koma na karasa shirina duk da ba wani shiri bane dan dongon rigar da anty safiya ta sai min sune nake sakawa yanzu saidai naji hjy tana wakan tana son a samu lokaci aje a sai min kaya don tana kunyar wanan kayan da nake sakawa haka.
Ban sa raina ba sai na gani balle zumudin hakan ya hana zuciyana shakat da damuwa na fito na nufi kitchen don samawa cikina abin karyawa.
Ruwan shayi da soyayyen dankalin turawa nagani a cikin kula shina diba na hada tea na dawo inda Larai ke gyara kayan miya na zauna kusa da ita na fara sha ke nan naji muryan Rufaida na kwala min kira da yar aikin hjy don sunan da suke kirana dashi ke nan dashi a gidan in ka debe hjy dake ce min zeey sai su mama kande da suke kirana da zainab.
Amsawa nayi da na,am tana karyawa Larai ta fada yadda zata iya jiyo ta tana karyawa shine ba zata zo ba Rufaida ta fada.
Dole na mike zuwa amsa mata kiran a tsakiyan falo na sameta tsaye ta rike kugu tana jirana a hasale.
Ina zuwa take fadin ke don uban ki zan kiraki kice kina karyawa haba Rufaida wanan zagin fa haka ?
Muryan Anty salma ce dake zaune wurun dinning tana karyawa lokacin ba dole in zage ta ba don daukan kanta take daya damu wanan yarinyar.
Kin san dan kauye bai iya samun wuri ba dama idan yaga ya waye sai yake gani yafi kowa waye wa ki shige dakina kaya na nan na tara a bayi na ki wanke min ta fada tana juyowa inda nake tsaye ina kallon ta da idanuwa da suka ciko da hawaye don zagin da tayi min.
Bazaki tafi yin abinda nasaki bane ta fada cikin tsawa da sauri na juya na nufi hanyar dakin nata don kwaso kayan datace din.
Saurara ta fada naja na tsaya cak wuri guda ina saurarenta kada ki fara ki satar min wani abu a dakin nan don ranki zai baci sosai idan kinyi hakan.
Haba haba hakan baida kyau fa Rufaida and kuma kinsan mami ba zataji dadi ba idan tasan da hakan anty salma tace.
Mami kina nufin banda right din sakata aiki ko warning dinta akan kayana tana yar aiki gidan nan.
Nidai na juya na wuce ina shara hawaye don abu biyu ga zagin dana samu ga kuma zargin sata yanzu.
Dakin na shiga na same shi a ya mutse kamar ba mace ke kwana a cikin sa ba don daki babu gyara ko kadan yadda na ganshi.
Bai da banbanci da dakin da nake bambancin su dai wanan mirrow shi cike yake tab da kayan shefe shafe sai manyan akwatuna dake gefe ajiya ga kuma tv bango babba.
Duk a fakaice na kalli dakin nasan da hakan don wanan ne shigana na farko wani daki daya shifi gidan in kin debe na mami da kullun ina cikin sa.
Mami bata taba ce min wani abu game da dakinta da zanga kudi ko agogo ko sarka da sauran su sai dai in dauka in mayar inda take aje sarka ko agogo kudi kuma zan daga filo in aje mata shi yadda suke.
Ina shiga ban dakin idona ya fara arba da pant din ta saman kayan su rigan nono da bujen ciki kai kaya daine na unders da mace ke sakawa a jikin ta ta tara gudan masu yawa a wurin.
Tattarawa nayi na a bucket din dana gani a bayin nafito tana tsaye tana kokarin cire rigan dake jikinta take fadin ki tsaya ki gyara min daki kafin kije wankin.
Dole ba yadda na iya tunda nazo cin arziki ne gidan su na fara gyaran dakin ita kuma ta shige bayi don yin wanka kafin ma ta fito na gama na bar dakin.
Can baya naje inda ake wanki da sauran aiyuka na wanke na shanya mata tunda wanan ba aiki bane a wurina.
Na gama na dawo na samu ruwan tea di dana aje har yayi sanyi haka na dauka nakarasa shan shi da sanyi.
Fitowa nayi da niyar komawa dakina na samu yan matan gidan zaune da kawayen su a falo zaune.
Zuwa nayi zan wuce ba tare da nayi masu magana ba nakai tsakiyan naji muryan Nazifa na fadin amma wanan yarinyar bata kunya.
Sai duk suka dawo da kallon su wurina wanan wacece yaushe tazo gidan nan cewar wata daga cikin bakin.
Rufaida dake cin chewing gun ta tabe baki tana fadin a kauye mami ta dauko ta .
A hakan mami ta dauko yar aiki wanan wani aiki zata iya kazama da ita haka ga ruwan kauyanci ko ina tare da ita.
Gaba daya suka sa dariya lokaci guda ke zoki gaidasu ki shige salma ta fada a dake ba tare da tayi dariya ba ita.
Nazo gaban su na tsuguna ina gaidasu basu amsa ba sai dayan ke fadin kina gani ta nan idan ta waye sai duk kun girgiza a gidan nan.
Amma dai kin gama damu Laila wanan din ne zamu girgiza don tayi clean .
Oh kina raina irin kauye ke nan ai barsu yadda kika gansu ba wani zancen clean gareta don tana clran aurin nan ba karamin taksici zakuci ba duk wanda ya zo kanta zai tsaya rabu da mutum ka barshi a ranan da yake kawai don idan kace zaka kaishi innuwa shiko yana turaka rana .
Salma ta kalleni cikin takaici tace ba kingaida su ba me kike jira kuma a nan yanzu ?
Sai ta gama jin abinda muke fada mana Rufaida tace tana watsa min harara na mike ba bar wurin ina jin bakin na fadin ke wanan ai idan tayi clean ko yaran gidan nan ba zasu barta ba tana hakama yaya aka kare da suranta duk mai hankali yasan anyi halitta a nan ai.
Ire iren haka yasa nakan shige daki in zaune in dai ba mami ke gida ba dole ina falon don aike ko wani aiki da zan mata.
Yan matan basu bar gidan ba har mami ta dawo daga unguwar data tafi tana shigowa ta samesu a falon gaisawa suka farayi bata ko amsa masu ba ta fara fadin ina wanan yarinyar zeey take ne ?
Sai kawai ta shiga kwala min kira ina cikin daki na kulle kaina naci kuka har na gaji naji an bankado min kofan dakina da karfi .
Haka yasa na dago kai ina kallon mai shigowa dakin lokacin ba kowa bane sai Nazifa ke kina nan zaune to mami tana kiran ki.
Mikewa nayi da sauri ban ko tsaya share fuskana daya gama dan hawa ba saboda kukan da nasha.
Mun iso falin daidai mami ta dauki ruwa zata kurba nake fadin sannu da dawowa mami ta dago kai ta kalleni sai ta furzo da ruwan lokaci guda daga bakin ta.
Gaba daya hankalin kowa ya koma kanta don ganin me ya faru tana fadin zainab mamana kuka kikayi ne ?
Kaina na girgiza mata kafin in ce a a ahankali ina wasa da yatsun hannuna haba bana son inganki cikin damuwa ko kadan.
Shiru ta danyi ta mayar da hankalin ta ga wayan ta kafin tace kwashe kayan nab ki kai min daki.
Na duka na dauki kayan zuwa dakinta kallo ta bini dashi tana fadin na rasa me yake samun wanan yarinyar taki ta sake jiki damu har yanzu.
Cikin ko in kula salma tace mami tambayi yaran ki don su suka bata mata rai suka kirata da yar kauye a gaban ta dazu nasan shi takema kuka dai.
Salma haka take bata shiga harkan kowa kuma bata boye gaskiya fadin shi takeyi komai dacin sa a cikin su.
Amma na fada maku tun randa yarinyar nan tazo kan ku kiyayyeta a gidan nan ko ban fada ba ranan kan mami tayi masu tas a kaina a gaban kowa don sauran ma ashe ba baki bane duk yan gidane suma.
Wanan fadan ne ya kara jawo mi bakin jini a gurin su sosai suka saka kafan wando daya dani dole idan mami bata gidan ina daki ko wurin kande.
Haka kuma bai hanasu sakani aikin wahala da suke gani suna ban ba gashi mami bata zama gida yanzu don shirye shiryen da ake na zuwa rantsar dasu Abuja.
Wanan ya dauke mata hankali daga komai dake faruwa a gidan ba wankin unders ba har tufafin su yanzu suke bani in wanke wai nafi mai wankin gidan iya wankin kaya sufita a cewar su don mugunta kawai.
Ranan ina dakina kwance mami ta kirani kande aka aiko ta kirani nazo da sauri tare da wani na samesu ina zuwa ta nuna mashini tana fadin ka ganta nan duk ita zaka dinkawa kayan .
Kallona tellan yayi yana fadin bari a aunata ke nan da sauri hjy tace tana daga mai hannu ina warning din ka da wanan awon da kukewa mata yana daga cikin aikata alfashan zama koda kuwa namijine dan uwanka ko mace yar uwar mace haramun ne yin hakan.
Hjy za,a kiyaye ya fada yana dan sosa kai tare da dan jin kunyan abinda hjy ta fada mai sai kuma ta dago yana fadin kayab zasu matse ne ko a danyi mata su free ne.
Kafin mami ta bashi amsa na karbe da fadin free nake so kada ya matseni don Allah.
Ji mun yarinya kin san abinda yake nufi ke nan ko ni dai nayi dan murmushi kawai ina dukar da kaina kasa cikin kunya.
Kudi masu yawa taba tella ya tafi yana mata sallama tare da godiya gareta wuri na samu sama kafet din dake tsakiya a daidai inda mami ta dora kafanta tana zauna cikin limtsetsen dogon kujeran falon.
Hjy ta kalleni tayi murmushi kafin tace min wai zee yaushe zaki daina wanan hali naki ga kuja zaki wani zauna a kasa kamar marainiya.
Dama ina son jin wani abu a dangane da rayuwan ki mahaifiyar ki tana da rai ?
A bazata tambayan yazo min da sauri na dago kai na kalli hjy kafin ince tana da rai sai kuma tace mahaifin ki fa ?
Shima yana nan na bata amsa kai tsaye kuma suna tare da babar ki kai na gyada mata wanan karon idanuna yana kawo hawaye.
Yaya akayi suka barki zuwa inda basu sani ba kina matsayin kina ya mace zeey basu gudun ki fada mugun hannu ne ?
Hawaye bakeyi sosai tare da fadin Asabe ne tace sai nazo birni suka hada kai da lantana aka turoni don innan mu na haihuwan yaya mata wai.
Tace idan ba aikatau ba bamu da wani moriya nan gaba tunda aure zamuyi mu barsu gida.
Tauuu ita Asaben ta fadi haka diya mace bata da amfani sai aikatau ta tambaya tana kallona.
Kaina gyada mata alaman eh sai naga tayi wani dan murmushi iya fuska kawai.
Wacece Asabe ta tambaye ni nace kakar mu ce wacce ta haifi Abban mu tare muke zaune gida daya .
Mami tace kuma ita ta haifi Abban naki itace ta haifeshi shida gwaggon habiba subiyu ne yaranta kawai.
Ina ita gwaggon naki take yanzu nace ance tana aure a zaria ne tace ikon Allah zarian nan dai tamu kaina gyada nan ma..
Bata san an kawoki gidan nan bane aiki daga garin ku nace nima ban sani ba mami don tana dadewa bata zo garin mu ba.
Amma ai bata rasa samun labarin an kawo ki kaduna in har yar uwan haihuwan mahaifin kice ta hakika ya kamata acs suzo suga inda kike nawane kaduna da zaria .
Sai ga hawaye nabin idona nace itama yanzu tunda Abba ya auri lantana ba ruwanta da innan mu kuma.
Ikon Allah ita innan taku ina yan uwanta suke nace cikin ancau suke da zama saidai it inna iyayyen ta duk sun rasu kafin mu girma bamu sansu ba.
Tace mahaifin ki kika kwaso da kama ko babar ki nace Asabe kullun in tana fada sai tace wai zubin innan mu kwaso sak.
Kenan ita kika biyo da dirin jikin kin ga ai wata rana nasan zamu hadu da innar take idan ta kawo maki ziyara nan ko ?
Yana da wuya inna tazo nan don Asabe ba zasu bari inna din tazo nan ba don ko zuwa za ayi sai dai Abba yazo kila.
Kina da kanne da kuka fito ciki daya dasu nace mu bakwaine mata innar mu ta haifa shine Asabe ke mata gorin hakan.
Ta auro lantana yanzu na barta da ciki wai za a haifawa Abban mu magajin gida tunda inna ta kasa haifa mai namiji.
Innalillahi hjy ta fada tare da rike baki tana fadin har yanzu akwai irin jahilcin nan ashe ?
Zata kara magana waya ta yai kara ta dauko haka yasa na mayar da hankalina ga tv dake aiki ga falon .
Saiga yan jikokin ta su shigo do basu faye shigowa wurin kakar tasu ba uwarsu ma baifi sau uku na ganta a part din hjy ba.
Daga bayane ma nasan a gida daya suke zaune da ita saidai ita tana nasu bangaren ne daban.
Tunda nazo ban taba taka ko wurin get din gidan ba kullun ina cikin gida idan ma na fito iyakata backyard din gidan inda su mama kande kan zauna da yamma su sha iska.
ZAINAB IDRIS MAKAWA*_
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
🔟
RAYUWA YANA FARUWA WUCEWA YAKE KAMAR BA, AYI BA ALLAH KABAMU IKON AIKATA ALHERI A KWANAKIN DA SUKA RAGEWA MUSULMI BAKI DAYA AMIN, , , , ,
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU KACAL NE HAKKINA KAFIN KI KARANTA NAGODE, , , ,
Kamar yadda mami ke yawan jana a jiki yanzu na fara sake jiki a gidan mami saidai bada yan matan ta ba dan gara samarin ko a gaban mami zasu sakani wani aiki mami na fada tana komai zan masu shi.
Hakama yau ya kasance kowa na gidan yana falo zaune ana hira ban dade da fitowa falon ba mami ta kirani in dauko mata wani takarda sunan shi kawai ta fada min nace nagane shi na juya da sauri zuwa dauko takardun.
Rufaida ta kalleni tana fadin wanan akwai iya yin tsiya ko ina ta iya karatu balle ta san shi wai ta gane bari ta dauko shirme yau sai na mata tsiya a gidan nan kuwa.
Yo aini tafi min ku kodai bata gane ba ai zata dauko din da kwatace ballema tunda tace ta gane ta gane din ne.
Wani lokaci yarinyar tana bani mamaki sai in manta in mata magana cikin turanci sai kuma ta gane me na fada mata din.
Hajjaju ko dai tayi karatu ne watakila ta danyi boko a can garin su fa yaya jalal ya fada yana dakilan wayar shi.
Sai jamal yace boko for ware kana ganin yarinya yar tipical yar kauye da ita na maganan wani education nan.
Sai gani da saurina nazo har gaban mami ina mika mata takardan mami ta karba tana fadin tau Rufaida dake da ita duk kun kuru yau a gidan nan .
Lah mami ashe kin hakeni kimin tsiya idan na taba maki yar ki ke nan Rufaida ta fada tana dariya kafin ta juyo ta watsa min wani harara.
Oh wellcome my boy jalal ke fada don shigowan jikokin hjy falon rike da takardun makarantar su yaron na zuwa ya fada jikin kanin mahaifin shi da sauri.
Saiga uwarsu a bayan su itama ta shigo falon ashe tare suke tafe har yaran sun fara zuba mami tace oya great us cikin daure fuska.
Take yaran suka fara bin kowa a falon suna gaida su har zasu gaidani Nazifa tayi saurin fadin she is not your aunt .
Nazifa ki fice min a idona akan yarinyar nan kafin rayukan mu yakai ga baci a gidan nan don ba zan lamuci hakan ba.
Jamal ya mike yana fadin ke stop interrupt your self akan wanan yar mami din a gaban ta don yanzu itace da mami baku ba.
Ashe ka gane gaskiya bana son ana raina dan Adam a rayuwana idan ka sanni a da ban kokai zeey wayewa ba kuma a haka mahaifin ku yace sai ni.
Duk aka kwashe da dariya falon wurin Rufaida yarinyar karama ta nufa tana fadin anty ki koya min assigment dina mommy tace bata iya ba.
Karban littafin tayi tana dubawa kafin da namijin ya juyo zuwa gareta shima ta karba tana duba kafin tace wanan sai Nazifa kila don ban gane me ake nufi ba gaskiya.
Wani subject ne Nazifa ta tambaya tace mathematics ne fa wanan ai sai ku Nazifa wace nazifan ta fada tana fadin su dai kaiwa salma ta duba.
Salma dake zaune tana duban wayan ta tace kada ma su haroni don ban iyawa zanyi ba indai maths ne.
Fuska yaran suka bata mami na fadin amma ko kunji kunya ta mika hannu yaran su kawo ta gani .
Ban san lokacin da nace mami barin duba masu ko zan iya ba mami ba kowa dake falon dago kai yayi yana kallona da mamaki.
Ke wanan fa ba tallan goro bane karatune na boko ake fada don kinji mami tace kina daidai da kowa zaki kawo muna rigima.
Ban damu da abunda Nazifa ke fadi na karbi littafin tare da jawo yarinyar a jikina.
Tsayawa nayi tare da nazarin abinda aka basu kafin in fara rubutu duk idanuwan su a kaina yake.
Tiryan tiryan nakewa yarinyar bayani yadda zata gane har muka gama da nata na dago kai ina fadin namijin ya kawo nasa.
Sai lokacin naga kallon mamakin da kowa ke min a falon lokaci guda mami tace dani kinyi boko ne mamana ?
Nayi na bata amsa a hankali duk yan matan mami suka zaro ido waje kinyi boko kike haka kuma a aikatau ?
Ban kulasu ba naci gaba da koyawa yaron assigment bamu dauki lokaci ba na karasa yaron ya dago yana murmushi.
Mami ta mika hannu ta karba da wanda nayi mai musali ya kwashe ciki tana bin rubutu na da kallon mamaki.
Wani maki kika tsaya a karatu ne zeey ta tambaya cikin kureni da idanu tana son jin amsa daga bakina.
Ina ss3 Asabe ta fitar dani da banan nan zan gama karatu tace wai bata ga amfanin boko gun ya mace ba tunda ba namiji nake ba shine karshe ta turo ni nan.
Kowa a falon shiru yayi yana kallon yadda hawaye ke zuba min a idanuna lokaci guda don maganan da nakeyi.
Yanzu kina son karasa karatun ki ko aure zasuyi maki kauye kina da tsayayye acan .
Kai na girgiza tare da fadin banda kowa sai Asabene tace wai zata sama min miji ta hadani dashi.
Kai waiko wanan Asaben ita ta haifi mahaifin ku da cikin ta wanan abinda take gwada maku yayi yawa gaskiya.
Karatun ma da zakiyi ki samu madogara a rayuwan ki saida ta hana kiyin shi gaskiya na tsani wanan matar damai irin halin ta.
Muryan Nuriya matar yaya mubarak ke fadin mami ashe kuma an daga tafiyan ?
Mami ta juyo tana ce mata sun daga kedai kin san abin gwaunatin kasan nan baida tabbas ai yanzu kuma sai dai sun kiramu kuma.
Ai wa yan nan sun kwafsa muna wallahi don kila yaya Jafar ya fasa shigowa kasan nan ke nan sai wani jikon .
Yasan an daga ne mami ta tambaya tana kallon jamal dayayi magana sai jamal din ya juya yana kallon jalal yana dariya.
Kudai kuka sani da tsegumi kamar mata haba mami don mun fada mai an daga ranan shine tsegumi shifa ya tambaye mu muka fada mai gaskiya.
Waya aike ku fada mai da ku barshi sai idan yazo yaji ai ba shike nan ba zai kirani ai zamu gamu dashi ta fada a hasale tana mayar da hankali kan sytem din ta data bude a gaban ta.
Nice ta farkon mikewa a falin bayan Nuriya matar yaya mubarak data ja yaran ta suka koma part din su ba don yaran sun so haka ba don ko shigowan nan nasu don assigment din yaran tashigo har dasu.
Dakina na shiga nabi gadona mai laushi na kwanta ga sanyin A C dana sake ya game dakin sai barci.
Bada masaniya ba mami ta sama min makaranta don inci gaba da karatuna a wani college dake gaba da unguwaelr kadan.
Ranan da dare take fadamin zancen ci gaba da karatun nawa lokacin nema kowa a gidan yasan da zancen cigaban karatuna yanzu.
Wanan yasa yan matan nata kara jin haushina sosai banda daman bin motar su kamar yadda mami tace mu rika tafiya tare da safe idan zan tafi.
Ganin haka ban fadawa mami ba nake takawa da kafa ina zuwa makaranta don nisan shi ai bai kai na kauyen mu dana baro.
Zan tashi da asuba inyiwa mami duk wani abinda nasan nice mai mata shi kafin gari ya haska na karasa zan karya in taka da kafa inje school.
Sam mami bata san da zancen tafiyana da kafa zuwa school ba sai wata rana zata unguwa da safe hakan yasa ta fito da wuri daga dakin ta.
Yan matan ta samu zaune suna karyawa take tambayan ina nake nan suka fara kallon kallo a tsakanin sai salmace take fadin mami wayen garin nan banganta ba ai.
Tafa tafi school Nazifa ta bada amsa sai mami tace usman ne ya kaita ya dawo ya dauke ku sai sukayi shiru don sun san da kafa nake tafiya school duk dadewan nan.
Bana son irin haka sai kuyi kwanciyar ku a daki kuna sharan barci sai lokacin da yai maku dadi zaku fito .
Alhalin kunsan da cewa ita nasu school din ana duka idan an makara ko shi malam usman din yayi ta zaman jiran fitowan ku.
Fada sosai mami tayi masu kafin ta fita can ta hadu dani na kusan shiga school din mu ta tsaya tana tambayana yaya akayi na tako da kafa ?
Nace mami bana sin in makara ana duka idan mun makarane maza shige mota in karasa dake ke baki tsoron wanan titin namu gashi shiru babu kowa a wanan lokacin.
Har ta saukeni fada take min ta bude jakka ta zaro five hundred tana miko min tare da fadin karbi wanan kiyi break dashi don nasan baki tsaya karyawa ba kika fito.
Lah mami wallahi na karya kafjn in fito ki bar kudin don mami bata ban kudi sai dai tace na karya kona dauki abinci inje dashi school din.
Ina kallo ta wuce karfe biyu da yan mintoci na shigo gida har lokacin mami bata dawo daga unguwar da ta tafi ba.
Haka yasa na samu daman samun dan barci rana bayan nayi sallah azahar ban sake fitowa ba duk da yunwan da nake ji don kudin da mami ta ban na kasa kashe su don ban saba da kashin kudi ba.
Ban farka ba sai bayan la,asar wanka nayi lokacin ne naga fashin sallah yazo min don haka nayi wanka kawai na fito na dauki always na kimtsa jikina dashi.
Abinci ya fito dani naga ashe yamma yayi sosai a lokacin haka yasa na gane na dade ina barcin rana yau.
Don na samu har yan university sun dawo suna cin abinci mam kande ne ta dauko kuloli take fadin yau kan yar gidan hjy kin sha barcin rana.
Ba dole tayi barci ba tunda taga arzikin banza wanan irun kune idan kun samu wuri kuke mayar da yan gida daga kofa.
A a saidai tasan wanda zata mayar Nazifa tace tana amsawa Rufaida sai naji salma tace wai ku meye matsalan ku da yarinyar nan don Allah ?
Rufaida tace I just hate her wallahi balle yanzu da take clean sai nake ganin gaskiyan maganan dasu Rubby suka fada ranan a kanta.
Ashe bani kadai ke ganin canzawan yarinyar nan ba tundai wanan kayan da mami ta saka aka dinka mata suna fitar mata da suranta na asali waje.
Zakace badaga kauye take ba har wani tafiyan sallo take tana yanga idan tana magana yanzu.
Kai ku din nan kuna da wani magana wallahi koma dai yaya ta koma kunsan ba zata taba kaiku asali ba dai ko ?
Sallama na fadan haka Nazifa tace yanzu waye ya damu da wani asalin mutum can zamanin nan boko ai mutane basu duban haka idan sunga abinda yai masu .
Dariya sosai salma ta kwashe dashi don dama irin du baka ganin dariyan su sai ta baci ni dai ina diban abincin ina jin cinmutuncin da suke min kala ban tankasu ba.
Saidai na kudurta duk ranan da wata daga cikin su ta kara zagan min uba bazan kyaleta ba sai inda karfina ya kare koda hakan na nufin inbar gidan ne na masan hjy ba zata yarda ba da hakan.
Don takan fada min Zainab ina son in ga na taimakeki kin zama wani a rayuwa ki samu ki taimaki yan uwanki tunda dukan ku matane har ku bakwai .
Shiyasa nake son ki dage ga karatun don wata rana ki taimakawa innan ki da yan uwan ki Asabe tasan diya mata ma diyane abin alfahari kuma.
Ire iren wanan tunanen nakanyi inshanye wani abinda ake min a gidan don kawai manufar mami a kaina don kuma burina ya cika.
Karatuna bai hanani yin abinda nazo yi gidan mami ba har na kai wata shida da zuwa gidan .
Iyakata da anty safiya idan tazo in fito in gaida ita tare da tambayan yayan ta da mijin ta ta bani amsa da suna lafiya suna gaida ke.
Sai kuma ta tambaya injin dai baki wani abin asha zainab kada ki manta da kinzo cin arziki ne a nan don haka kiyi biyayya sosai.
Irin maganan da anty safiya takan min ke nan idan tazo gidan ina nan kafin ta tafi
Gashi banji wani zancen kudin aikatauna ba ga bakin kowa nima kuma ba damuwa dana san komai a kan albashi na nayi ba.
Mun samu hutu makaranta naji mami na fadin ya kamata in je in duba gida tunda su basu neme ni ba har yau.
Don tasan yanzu inna na tacan cikin damuwan halin da nake ciki babu dai yadda zatayi ne ta sawa sarautan Allah ido.
Ban san mami har ta saka ranan zuwana gida ba sai dai tace inje aimin kitso a makwabtan mu don akwai wata yar makarantar mu a gidan kusan tare muke dawowa da ita kullun.
Itama takan zo gidan mu in mata nan yan gidan suka san na iya kitso sosai don har mami nakan wa kitso yanzu tunda ta gane na iya kitso sosai da yan matan ta.
Sai dai bankan so yi masu kitso don muna kitson suna zagina har mu gama.
Washe gari na shiga wurin mami in gaida ita da kwana sai na sameta zaune ta fitar da kayan data dawo daren jiya dasu don nice na kwaso zuwa dakin ta.
Sallama nayi ta dago kai tana fadin yawa samu wuri ki zauna dama yanzu nake da niyar kiran ki sai gaki.
Zama nayi kamar yadda ta umurce ni kafin ta fara fadin kinga wa yan nan turamen ta nuna min su da hannu nace eh mami.
Tace yan uwanki zaki kaiwa su guda shiddane iri daya ne saidai nasa a bambanta kallar su wanan kuma na innan ki ne ta nuna min wasu uku a guri daya.
Sai wanan kiba Sabe daya lantana daya wanan shaddan kuma ki ba mahaifin ki sai sabulai da omo kiba yan uwa da abokan arzikin ku .
Kwana hudy zakiyi ki dawo driver daya kaiki zai dawo ya daukeki ranan ki gaiyar min da innan ki sai wanan ki ba mahaifiyar ki tana miko min wani abu a cikin leda wanan kuma mahaifin ki zaki ba albashin kine na watannin da kikayi a wurin mu na tara maki shine na raba biyu innar ki rabi mahaifin ki rabi.
Kada ki manta ina gaida innar ku kwarai kice na gode sosai sai watarana idan mun hadu.
Hawaye na fara yin a wurin ina tsugune sai mami tace ko kin fasa zuwa gidan ne in aika masu da sakon da sauri nace a, a mami na dai rasa godiyan da zan makine yanzu.
To maza ki tashi ki shiya ga sabbin kayan kinan saman gado sai ki zabi wanda zaki dasu tsufin kuma duk ki hadasu ki kawai kannen ki su karasa su can .
Ko mahaifiyar ki tana sa kwance ki zaba mata wa yan nan dana ware da za a kyautar .
Da gudu nace tana sawa mana mami to jeki ki zabar mata kala biyar daga ciki da sauran tarkacen daya dace ki kai mata .
Na mike don na rasa bakin da zanwa mami godiya don ta hanani yin hakan gareta.
Kayane mai yawa har na rasa wanda zan cirewa inna sai da mami tace ki cire mata zannu da dogon riga zatafi son su ai.
Haka muka dauki hanyar ANCAU da tsaraba taf a bayan mota da zankaiwa iyayyena koma in ce mahaifiyata don itace mai tsaraba da yawa ciki.
Don hjy tafi son inna na fahinta sama da mahaifin mu Abba kodon tana mace yar uwantane ban sani ba.
Malam Usman driver mami bai tsaya ko ina ba dani sai kofar gidan mu tun daga nesa na hango wata na suyar wani abu an baibaiye ta.
Saida muka matso kuss ne na gane saratu ce kanwata ashe ganin mota ya nufo kofan gidan ya kuma ja ya tsaya.
Duk wanda ke wurin ya kurawa motar ido don son ganin kowaye a motar ban fito ba saida na gama dauko kayan dana rike a hannu na fito daga motar.
Saratu zoki kama min kayan nan kin tsaya kina kallona haka muryana kawai ta sheda yasa ta gane ni a lokacin.
Ido ta waro waje tana kallona tare da fadin yayan mu maimakon ta yo wurina sai kawai ta kwasa da gudu tayi cikin gida tana fadin.
Allah mun godema Allah mungodema yau ga yayar mu ta dawo garemu innan mu fito yau Allah ya dawo muna da yar uwarmu gida.
Ashe ba sayar da ita akayi ba a birni ji abinda saratu ke fada yasa sayran kanne fitowa da gudu kafin su ja su tsaya suna ina take ta kwasa tayi hanyan fita suka bita da gudu.
Mun hade dasu a kofan shiga gida sukayo kaina da murnan su da ihu suna jin dadin gani sai ihu sukeyi yayan mu ta dawo yayan mu ta dawo garemu yau.
Jin ihun da yaran gidan suka dauka na murnan zuwana yasa Asabe fitowa daga shiyan ta dan kwali a hannu tana fadin.
Shin Abu Abu kuke fadan tazo ina Abun take ne in ganta tana kokarin wuceni da yan uwana.
Gani nan Asabe na fada ina kokari zuwa wurin ta sai taja baya tana dafe kirji tare da fadin Abuce haka ?
Zonan na ganki na karasa wurin ta sai ta rungumeni tana kuka tana fadin yar nan ina kika shige haka babu duriyan ki har an fara zargina a gari na sayar dake ga yan birni.
Ina gidan hajiyar da kuka kaini tun barina garin nan na da kwana bakwai gun anty kafin ta kaini gidan.
A a ai dada kin dawo garemu ke nab dai yanzu ba komawa wanan birnin kuma dai ta fada tana share hawaye.
Ni dai ban ce mata komai ba sai waige nake ko zanga innar mu ta fito banganta ba yasani sakin Asabe na nufi dakin mu da sauri ina sallama.
Ina shiga da hango ina zaune saman dan gadon dake dakin tayi tagumi ns karasa gareta ta da sauri ina fadin inna gani nazo gare ku yau.
Murmushi inna tayi kawai sai dayan kanwar mu data sawa kira daga dakin a daidai lokacin da yara suka fara shigo da kayana dakin.
Irin surutun da yaran dake shigo da kayana gidane ya sa hankalin lantana dake daki bakin cikin dawowa ya hanata shakat tunda saratu tazo tana ihun na dawo wani tukukin bakin ciki ya sokar mata zuciya.
Don Lantana sam bata so in dawo gidan ba a lokacin don so tayi ace ba bata da gaskiya kamar yadda ta kulla sherin haka har zance yabi gari gaba daya kowa ya dauka hakan ne.
Inna eta bada kudi wai a sayo min ruwan leda nace basai an sayo min ba inna a dai sayawa driver hjy daya kawoni.
Wai wanan mutumin driver ne yanzu saratu ta fada nace drivern gidan hjy ce shi ke kai yaran ta makaranta ya dauko su idan da aike kuma sai a aike shi.
Bawada ya ankara da zuwan lantana daki namu tazo ta tsaya a kofan dakin ta tokare hannayen ta da katon kofan dukka gefe biyu.
Saida ta gama saurarebn mu ta kalleni tsaba ta fara fadin eyya Abuce ta koma haka ?
Gaba daya dakin muka juyo muna kallon ta lokaci guda taci gaba da fadin halan a cikin injin suka sakaki aka wankeki haka.
An maidoki kamar wata karuwan birni koda yake wasan abinda kike a burnin wanan bude idon haka lokaci daya.
Amarya ke nan ai inkiga mutum yayi abu yana da gadon shi ne ban gada ba babu dana da zai taba zina da yardan Allah inna ta bata amsa.
Kinsan aikin mutum sai ya dauka shi kowa keyi ko ina ya samu kansa ni Allah ya tsare mi yata a birni don bata gaji watsar da kai ba.
Kaina yana duke kasa ina tunanen wai yaushe inna ta fara magana haka sai naji lantana na fadin wa kike nufin ya gada to ?
Wanda yasan ana haka har furtawa yata dashi nakeyi abu yaso zama rigima don har saratu taso shiga maganar inna ta kwabe ta.
Andaiyi abin kunya ta fada tana batin kofan dakin don bata zaci innan mu zata bata amsar maganan taba.
A kofa ta hadu da asabe da takawo min zogale data gyara tana shirin ci cewa lantana tayi muna ganin kilibibi a gidan nan.
Ya tadawo yawo tazubar har ake wani riritata don kwadayin duniya muna jin ta a daki nace har yanzu wanan matar tana wanan haukan duk data haihu girma yazo mata yanzu.
Ina girma a nan banda iya shegen data karo cin mutunci dai ne mutum ya guji karshen shi.
Asabe ta shigo da sallaman ta tana aje min kwanon ganye a gaba tana fadin kici yar nan dan ganye na gyara sai gaki.
Saratu takai hannu zata diba takaiwa saratu dundu a baya tana fadin mara kunya ba a ke nakawo ba bakuwa na kawowa.
Sai dana huta nayi sallah kafin malam usman ya aiko wai zai tafi na samu inna ta dan dama fura ta aika mai kafin yayi sallah yasha ga awara da saratu ta cika mai leda dashi har kwan zabbi inna ta aika a nema cikin gari ba a samu dayawa ba hakan ma naji dadi yadda akai mai.
Bayan mun dawo daga rakashi ne na bude kayan don saratu ta ta demeni da tambaya mena kawo masu ?
Tundana fara bude kayan jikin kowa yayi sanyi kafin ma in farawa inna bayani kamar yadda mami tayi min.
Nan dai na labartawa inna rayuwana a gidan hjy saidai na boye mata irin cin fuskan da yan matan hjy kemun a gidan.
Don tsakanin mahaifa da diyan su sai Allah sararu ce ta dauki na Asabe da lantana takai masu nasan don fitina tace itace zata kai.
Lantana ta fara kai ta karbi kayan a tsune tana fadin duk da ance kayan zina kamar kayi zinane kaima.
Amma wanan zani ya shereni ba zan barshi ya tafi ga banza ba tunda a haka aka sameshi.
Saratu tace dadai yafi tunda ba yau aka fara cin kayan zina ba don har na tsohuwa an saba ci cewa da uwar lantana din.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣1️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH KA KAWO MUNA TSARO A KASAR MUNA NIGERIA, KASAWA WANDA IF,TILLA,I YA FARU DASU HAKKURI DA SANIN KADDARA A RAYUWAN SU, , , , , , ,
DARI UKU NE NOVEL DINA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALLAMA YAR UWA DON TURA KUDI GA NOMBA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN KO EIRTEL NA DARI UKKU.
Abba bai shigo gida ba sai gap da magariba ya dawo lokacin ina alwala a tsakar gidan mu dani ya fara arba.
Ja yayi ya tsaya tare da fadin wa nake gani nan kamar Abu ya fada cikkn mamaki don bai san da zuwana ba ashe sai wanan shigowan da yayi ya ganni.
Amsa na bashi ina mikewa a daidai lokacin ina kai dan ruwa a baki kamar yadda yin hakan ya zama min al,ada tun ina gida ba tafi kaduna har yanzu kuma ban daina yin hakan ba idan na idar da alwala don sallah.
Abba nice na fada cikin dan murmushi Abu ina kika shiga haka babu labarin ki ga kowa ita din da tazo ta dauke ki bamu kara jin wani zance a gareta ba har wanan lokaci.
Safiya bata kyauta muna ba ta barmu cikin zargi da fargaba don ba haka mukai alkwari da ita ba.
Ayi hakkuri Abba kasa anty ma,aikaciya ba ko yaushe take da lokacin tafiya ba irin hakan.
Yar mairo koma menene ai ya dace ta dan waiwayo musan halin da ake ciki dake a can .
Yanzu kai ganin ta yasa ka tsaya nan kana zuba har ka mata irin bakin cikin data jefa ku a tafiyan ta .
Lantana ce ke fadawa Abba hakan tare da mika hannu tana fadin ban ledan kafin ka shiga can a wawashe.
Tana mika hannu ta fisgi ledan daga hannun Abba ta juya tana fada abin kunya yarinya taje gantali tsawon wani lokaci saida tagaji don kanta ta dawo har kuna wani jin dadin hakan.
Abba yai tsaye kamar ba Abban dana sani ba yana bin inda tabi da kallo kafin ya juyo har na bar wurun ina kokarin shiga dakin innan mu ko.
Da mamaki a raina yadda naga komai na gidan namu ya kara hargitsewa ga baki daya na tayar da sallah.
Bayan na idar da sallah muka zauna da inna sai lokacin nayi mata bayanin komai a tsanake har sakon mami na dauko na bata na nuna mata na Abban mu da tace a bashi.
Inna tace aidai bata don wanan yarinyar tana kyala ido a kansu sai taga bayan su a lokaci guda.
Nace koma meye ai dai na isar da sako saidai inna nifa wasu abubuwa da nake gani a gidan suna daure min kai tun zuwana.
Me kika gani daya daure maki kai ai dama shi ramin mugunta kurarene idan wanda akewa yayi hakuri.
Bai wuce dai abinda kikaji ba tsakanin umma da lantana ko wanda kika gani yanzu tsakanin ta da mahaifin ki.
Duk waya ja hakan sai umma gashi kuma tun ba,aje ko ina ba abin ya koma tsakanin su yanzu.
Tana ji tana gani ganin danta yana batun gagaran ta a gidan nan tayi fada har ta gaji ta saka ido idan da can tayi mai aure ne don ni a gidan nan, yanzu bani kaida ke ganin bakin cikin ba harda ita.
Shiru jayi ina tunane a raina tare da fadin mai yai zafi tsakanin Asabe da lantana kuma yanzu.
Abba bai shigo dakin inna ba sai bayan sallah isha,i zama yayi muka gaisa na mike na dauko mai sakon shi kamar yadda mami tace in bashi.
Duban kaya yayi yana juyawa tare da fadin ikon Allah duk wanan matar ta bayar a kawo min nace Abba ai mami mutumiyar arzikice.
Zamanta mai kudi baisa ta raina tallaka ba nan dai na gutsura mai dan labarin mami din da aiyukan da nakeyi a gidan.
Abba ya kalli takardan dake hannun shi yana juyawa a hankali kafin ya fara kokarin budewa kudi suka soma zubowa daga cikin takardan yan dubu daya sabbi fil dasu.
Da mamaki yake fadin yahanasu kudine fa matar nan tayo muna sako a cikin takardan nan.
Na amsa da fadin cewa tayi kudin aikina ne in kawo maka da zanzo duban kudin Abba yayi kafin ya juyo ya dubi inna da ko kallon inda yake batayi a lokacin.
Wanan matar wani irin kudine gareta haka yar mairo ko harda wani sana,a kike mata bayan wanan ?
Gaskiya matar kwarai Allah ya hadaki da ita a birni don ba kowa bane zai iya maka hakan .
Mamaki kalaman Abba ya bani don na dauka zai tambaye fiye da hakan sai ga Abba ya buge da fadin in kara kwazo don gaba ta aiko da wanda yafi wanan din yana mikewa.
Malam iya abinda zaka fada mata ke nan dan ka rike kudin da baka tabbatar daga ina suka fito ba kamar yadda matarka ke fadi kullun.
Bana zargin tarbiyan diya na ko kadan don nasan tarbiyan da muka basu tun farko.
Allah yasa a kanshi take don nina tsuke da sakon wanan matar gaba daya hankalina bai kwanta da hakan ba ko kadan.
Abba yana kokarin tura kudin cikin aljihu yake fadin ance kudi kare magana ganin wanan kudin yanzu ya kara tabbatar min da gidan kwarai diyata take.
Bayan fitan Abba a dakin ne yai shiru na dan lokaci kafin mu fara jiyo hayaniyar Abba da Lantana daga kofan ta.
Lantana ba kunya take fadin yau sai dai a rabamu a gidan nan amma wallahi sai ka fada min abinda kajeyi dakin can ranan girkina.
Kinji ko haka muke fama da fitinan su a gidan nan koda shi koda umma don ni ba shiga shirginta nakeyi ba sai ta koma yi da yara yanzu.
Allah yasa har na tafi kada wani matsala ya faru tsakanin mu nace lokacin inna ke tambayan kwana nawa zanyi nace kwana hudu mami tace driver zai dawo ya daukeni.
Ba zan yarda ki koma garin nan ba batare da wani ya biki yaga a inda kike ba koda malam ba zai tafi ba zan hada ki da kawun ki lawal kuje tare.
Inna hakan yayi daidai don mami ma bataji dadin hakan da aka barni ba wanda ya biyo sawuna tunda naje garesu bayan anty safiya data kaini.
Matar kirkine tunda tayi tunanen hakan duk wata uwa ta gari wanan tunane ne zaizo mata a rai.
Yadda za a sake diya mace haka ba tare da wani nata yabi sawunta yaga inda take rayuwana.
Nagodewa Allah daya karba min addua na danake kullun gare ku hankalina bai taba kwaci ba tun bayan tafiyan ki sai dana samu sakon safiya a boye tana min bayanin halin da kike ciki tare da kwantar min da hankalina.
Tun wanan lokacin na falwala ma Allah al,amarin na kara dagewa da addua a gareku sosai.
Mun sha hira ranan don bamuyi barci ba sai da inna ta labarta min abindaya faru tsakanin Asabe da lantana tun bayan haihuwan lantana gidan nan.
Tunda lantana taga ta haifi namiji kamar yadda umma ke muradin haka a kanta shike nan take ganin ta gama da kowa a gidan nan shi kanshi malam gaba daya an rasa gane kanshi yana ganin itace hasken rayuwan shi ita da danta.
Bata yarda kowa ya taba danta a gidan nan dama ga dan bai faye lafiya ba wai yana da ciwon numfashi.
Subbahanallahi gaskiya banganshi ba tunda nazo ai ba zaki ganshi ba don ba barin shi gidan nan takeyi ba wai kada wani ya halaka matashi.
Tunda an fada masu wurin biye biyen bokayen su cewa wai asiri akai mai yazo hakan ba lafiya.
Jin hakan yasa na ra,ya a raina har na koma bazan taba yaron ba in Allah ya yarda .
Me zai kai ki shiga shirmen wanan mara mutuncin barsu ya kare a kan su ranan dai mun dauki lokaci muna tataunawa da inna.
Washe garin kukan yaron Lantana ne ya karade gidan dashi ina mamakin karfin halin inna data ki kulla al,amarin yaron.
Na fito don gaida Asabe da Abba da lantana sai na samu Abba yana tsaye yana rarashin yaron a waje sai tsala ihu yakeyi uwar na shafa mai magani.
Kasa nakai na gaida Abba na juya don gaida Lantana samu nayi tana hararana a wullakance.
Ban damu da hakan ba na fara gaida ita da kwana kafin nnace Abba meke samun shi tun dare nake jin kukan shi.
Kafin Abba ya furta Lantana ta karba da fadin kuka kan ai dole ne tunda an jefe shi bamu da hutu shi wahala ni a wahalce kullun idan dan ruwa ya tabeshi ko sanyi.
An kaishi asibiti na tambaya ina kallon Abba don ban yarda na kalli lantana ba don yadda naji ta fara maganan ke nan zancen innan mu gaskiya ne da take fadin sune suka jefa mata da don ana bakin ciki dashi.
Ina wanan tsohuwar gidan zata bari akaishi asibiti tace ina saka danta wahala ko yaushe yana kashe muna kudi.
Tunda ni ban yarda ta juyani yadda ta saba ba ace uwar miji komai danta keyi da matar shi idon ta na a kai.
Da dai Abba ka daure an kaishi asibitin birni bana kauyen nan ba aji mai zasu fada tunda yana wahala haka.
Tab abu mai wuya ke nan yaya muka kare da asibitin mu ma na nan balle har nawani birni can tunda ansan abinda aka kulla a kai ai ba a bada shawaran haka ba.
Koke don bakya nan ne ai da an sakaki a cikin wanan sherin don ni yanzu na san zamana da kowa a gidan nan ai.
Allah ya sauwaka sannu kaji na fada ina kallon yarin kafin in juya in wuce zuwa lungun Asabe dana sama tana zuba ruwa a buta zata zagaya ban daki.
Ban manta ba don ban yarda na shiga dakin ba a wajen na gaida ita na juyo na dawo dakin mu inda na samu kannena na shirin zuwa makaranta islamiy a lokacin don boko ana hutu.
Na taimaka suka shirya saida suka fice bayan inna ta basu ashirin ashirin din cin masa idan sun tafi.
Don ba ai abin karyawa ba alokacin lantana ce da girki kuma bata dora wanda za a ci din ba don yaron ta da ya kwana yana rigiman dare.
Wanka nayi na shirya cikin wani dogon rigan atamfa dinkin shi mai kyau ya dan matseni kadan .
Inna sai fadi takeyi mai za,a sayo min in karya dashi nake cewa ta bari a gyara dumame shi zanci don kada in takurawa rayuwan inna din.
Sai ga Abba ma ya shigo gida da leda biyu ya tsaya daga tsakar gida yana sa min kira na amsa na fito ya miko min ledan ya tafi da daya dakin Lantana.
Kosai ne da bread sai kayan shayi a ciki dana bude nake fadin inna ga kosai din ki diba ki karya da bread din don ni ba zan sha ba.
Nace bazan sha shayi ba inna dan dama kosai din zanci sai inna tace daidai ki sha abin ki mu in da sabo mun saba da wanan ai a gidan nan.
Inna tunda ga kudi a hannun ki me zai hana ku sai abinci rabi kuma sai ki juya shi kina dan sana,a dashi.
Shawaran da nayi ke nan a zuciyana Allah ne ya dubemu ya jefoki a lokacin da muke cikin bukata hakan.
Amma malam ya canza yanzu gaba daya a gaban kowa gari zai waye zai fita ya samowa matar shi abin karyawa muna kallo a gidan nan.
Inna ki daina damuwa da wanan tunda ubangiji yana kawo maki mafita da zaki duba diyan ki ki basu abinda zasuci.
Ire iren hiran da muke tayi ke nan a dakin inda na tillasawa innan mu sai data karya kafin yaran ta su dawo su hana taci tunda nasan tana son sha itama.
Karfe goma suka dawo gida da shigowan su abinci suka fara nema a gida suka samu ba a gyara ba zasu ci shi hakana da sanyi na basu kudi suka sayo taliya saratu ta dafa kowa yaci.
Na zaga wurin yan uwa da abokan arziki irin matan da nai sabo dasu ina masu kitso kafin tafiyana kaduna.
Har ya saura kwana daya ya rage min duk da zaman gidan namu babu dadi amma nake ji kamar kada in koma kadunan kuma.
Inna ta danyi kokatin ta sosai wurin yiwa hjy tsaraba irin na kauyen mu da zankai wasu mami din.
Washe gari karfe goma driver yazo daukana inna taso muje tare da kawuna kaninta yaga inda nake saidai anyi rashin sa, a kawun nawa yana da uzuri a ranan don haka muka dauki hanya dagani sai malam usman driver gidan mami a motar..
Tunda muka tunda muka tun karo gifan naga wasu canji a cikin dan kwana hudun da nayi bana garin.
Ni dai sai bin ko ina nake da kallon da mamaki a raina don ganin bakin fuskokin dake gidan namu tun daga get har zuwa cikin gidan.
Na fito daga cikin motar tare da dora hijjabi da kyau a kaina na nufi hanya shiga gida don na tsaya daukan kayana malam usman yace za a shigo min dasu ciki.
Da sallama a bakina na shigo falon sai dai abinda nayi arba dashi ne yasa gabana faduwa don ganin mutane a falon gidan kusan kowa na gidan yana falo ga bakin fuska.
Wa nake gani kamar diyan mami haka muryan mami ya dawo dani daga tunanen dana fara a lokacin.
Da dan gudu na karasa na fada jikin mami data ware min hannayen ta alaman inzo gare ta a lokacin.
Kai kai kai mamana me innar taki ta baki haka cikin kwana biyu kika kara kiba haka kinyi wani fresh dake mami ke fadi.
Tsuki yaya jamal yaja yana fadin ko dai ta kara kauyanci ji wanan bindata saka don Allah da cewa hijjab din jikina wai.
No dan Allah malam usman bace muna da wanan kayan kazantan wurin nan ka shiga dashi wurin kande suna kice cewar Rufaida dake nufin a kauce masu da kayana a wurin.
Malam usman dake shirin aje kayan ya dauka da sauri ya nufi hanyar kitchen dasu na dago ina fadin ban jakkana in kai daki bayan mun gama gaisawa da mami ban kalli kowa a falon ba.
Jeki kai ki fito ki ci abinci wai ai kunsha tafiya don wurin bai kasa ba akwai dan nisa da kaduna.
Shiyasa nace malam usman yayi sakko yaje ya dauko ki don ku dawo da wuri bana son tafiyan dare.
Na dauki kayana zan shige naji muryar yaya jalal na fadin baki iya gaisuwa bane ke idan kin samu mutane ?
Ke tafi ki aje kayan daki ki dawo mami tace haka yasa ban tsaya sauraren shi ba don bin umurnin mami din.
Na kai kayan na dan dade ban fito ba azatona bakin zasu tafi kafin lokacin sai dai har na fito suna nan a inda suke sai lokacin na gaidasu sai dai sun ragewa a fLin don ko su yaya Jamal basa falon yanzu.
Abinci na diba kamar yadda mami ta umurce ni na koma dakina ban kara fitowa ba sai dare bayan nayi sallah isha, .
Don na kwanta ina tunanen gida ina tuna innar mu da na dan saba zama da ita a yan kwanakin danayi a can gida sai nake ji kewan su na damuna yanzu.
Hjy na samu a falo kishigide saman kujera sai wani matashi dake zaune kasan kafet dake tsakiyan falo.
Ya mike kafafuwan shi sambala sabala tare da dora daya saman daya kanshi yana daidai cinyar hajiya.
Suna hira a cikin natsuwa su biyune kadai a falon, kowa yagan su zasu bashi sha, awa alokacin.
Ni dai kallo daya na iya masu na kawar da idona garesu don kyawon mutumin da kwarjini ga zati da Allah yai mashi kamar shiyayi kanshi.
Da ina ganin kyawon su yaya jamal kamar su sukai kansu gasu da iya kwalliya da tsabta shiyasa zaginsu gareni bai damuna da sukece min yar kauye amma sai ganin wanan ya dushe duk kyaun da suke dashi a idona yanzu.
Zeey ga yayan ku yayan su jamal jiya yazo sai kanwarshi da tazo ranan da kika tafi.
Sannu da zuwa yaya ya hanya nace mai ina dan rusunnawa don bashi girma da Allah ya bashi a kaina.
Fuska a sake ya amsa min gaisuwa bazakace bakin shi na motsi ba yadda yake magana da hausarshi da baya fita da kyau.
Daga haka na mike don barin wurin ina tafiya a harde don rudewa da nayi don ban taba ganin mutum yai min kwarjini irin haka ba a idona.
Muryan mami naji tana fadin zeey dauko ma yayan ki abinci nan yaci yau a kasa yake so ci yace don kiuya.
Taci gaba da fadin ki dauko har dani don nima din kiuyan nake ji sosai in samu inci in shige daki duk na gaji yau munyi yawo sosai yau.
Kulolin abincin dana gani a jere sabbi fil dasu wanda ban taba ganin irin su ba a idona don kyau.
Saida na dauko na karshe zan kawo naji karan bude kofa a part din mu wata matashiyan budurwace ta fito daga dakin dake kusa da nawa tana fadin.
Mami na dauka baku dawo ba har yanzu naga yanzu is aftre eight ashe kun dawo sannun ku da zuwa ta fada fuska a sake.
Mun dawo mami ta bata amsa lokacin da budurwan ke zama kusa da na zaune a kasa tana fadin bros yau kaga kd ke nan ashe ?
Yamutsa fuska yayi yana fadin mami ta kaini gurin yan uwanta dana daddy har na gaji a cikin turanci suke maganan wanda ba ko wani abin nake ganewa ba saboda kwarewan su da yaren.
Ina wuni nace mata da hausa ina durkushe kasa a lokacin lfy ta fada tana kallona kafin ta juya wurin mami tana fadin who is she mami ?
Zainab ke nan da nake fada maki tayi tafiya yarinyar da nake zama da ita yanzu wace gwaggon safiya ta kawo min yar uwar safiya din ce.
Oh itace she look quit ai ba kamar yadda su Rufaida ke fada ba a kanta mami tace rabu da yan rainin wayau kawai ban san me yarinyar nan ta tare masu ba gidan nan.
Mami me za a zuba maki na tambaya sai ta dago tana fadin fara zuba mai shi da baison cin abinci sai shiririta ya saba da abincin su na shirme can.
Lokacin ne na saci kallon shi na fara bude kulolin abincin ina son tambayan shi abinda zan zuba mai kuma ina jin tsoron ko bai iya hausa ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣2️⃣
ALHERIN ALLAH YA CIN MAKU MASOYA A DUK INDA KUKE A FADIN DUNIYAR NAN ALLAHUMA AMIN ALLAH.
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA DAUKAN NAUYIN HAKKIN WANI A KANKI BA.
Nidai na kula tun dawowana kowa ke walwala ga yawan bakin dake ta zuwa gidan babu wanda zan dan tambaya ko meke faru a gidan haka.
Naga kowa na gidan yazo ga kuma baki daketa zuwa daga ban garori daban daban sai gidan ya cika da baki sosai.
Wurin kande naje ina tambayan ta abinda ke faruwa take fada min ai zancen hjy ne ya tabbata za, a tafi Abuja a rantsar dasu.
Itace a jahar kaduna wace ta samu mukamin sai wasu daga sauran jahohin kasan nan kafin in furta wani abu larai take fadin.
Wai mukamin me hjy ta samu hakane wanan cikar da akeyi gidan nan haka mama kande tace waya sani yar nan su dai suka san abinsu can.
Shigowan anty safiya kitchen din tare da yar uwarta yasa muka katse hiran da mukeyi muka shiga gaidasu da zuwa.
A, a ke yaushe kika dawo me tafiya babu sallama koda yake baki da laifin hjy ta fada min komai daga baya.
Tana magana take karasawa cikin kitchen din tare da fadin kande zamu kawo maki wasu yan aikin da zasu kwana biyu suna aiki tare daku a gidan nan don aiki zai maku yawa ku biyun nan yanzu.
Duk da dai maza da matane zasu zo din ba lalai bane ma ku taba masu aikin su sai dai idan suna nema wani abu zaku iya basu.
Iyakar ku ke da larai shine zaku taimaka muna wurin bawa ko wani bako abinci idan an gama daga na karyawa har zuwa dare.
Ta juya tana fadin ke naji hjy tana neman ki tun dazun ashe kina nan gurin su kande.
Da sauri na mike zuwa wurin kiran da ake min na barsu kitchen din dasu kande tana masu bayani .
Cikan da gidan yayi a lokacin yasa na fara dan rabe rabe har na isa wurin hjy din dake dakin ta tare da wasu jiga jigan mata farare tas kamar ta sai dai sunfi hjy jiki da tsayi sosai.
Haka na rabasu har nakai wurin hjy nake fadin mami gani ance kina kirana ina kitchen wurin su mama kande ne.
Tace yawa zee wanan kawar tawace ke son kitso sai kuma Autana da naji tana tambayana ke dazun din.
Kallon matar data nuna min zanwa kitso nayi ina fadin yanzun zamuyi mama naji dayan race kai hjy wanan yar taki tayi min kyau wallahi.
Kafin daya tace hjy maria ke nan kedai diya mata suna burgeki tace wallahi naso dai in haifi mace kamar yadda hjy iyami ta rufe da ya mace bayan maza amma ban samu ba.
A raina nace duniya ke nan wasu na gudun mata wasu kuma suna son su kowa da irin bukatan shi duniyan nan.
Nidai ganin dukkan su manyan matane yasa na juya da sauri na bar dakin tun kan ta bani amsa lokacin da zan mata kitso.
Ina fita daga dakin mami dakin Anty Nuriya na shiga daga kofa na tsaya ina sallama kafin ta ban amsa in shigo.
Dakin yana da dan duhu ba haske sosai a lokacin tana kwance saman gadon ta makale da waya a kunnen ta.
Anty ina kwana na fada tare da dan rusunnawa kadan ta amsa min da fadin ina zuwa please taci gaba da wayan da takeyi abinta.
A hankali na juya zan bar dakin don ganin ta shagala ga waya naji tana fadin ki dan jirani please kayan da zan tafi dasu Abuja nake son ki shirya min.
A raina nace masu duniya ke nan kayan ma sai wani ya shirya mashi idan Allah ya ba wasu sai su manta kowa ma rai gare shi ai.
Dole naja na tsaya din ta gama wayan ta juyo tana kallona tare da fadin yawa tun dazun nake neman ki ai mami tace kina cikin gida.
Ina gun mama kande na bata amsa tace dama kayan da zan tafi dasu ne nake son ki shirya min su don ba wani dadewa zamuyi a can ba bai wuce ki saka min kala biyar ko hudu ba.
Nuna min jakka da zan saka mata kayan nayi na nufi wurin tare da tambayanta a ina kayan suke ?
Bude wanan drower suna ciki na zaba yadda tace hakan nayi na bude kayana daga sama har kasan wardrobe din.
Kinga na tsakiya din nan sune ban taba amfani dasu ba a ciki so ki dinga daga min dinkin su ina gani ko zanga wanda yayi min.
Bani da zabi sai yadda tace din na shiga daga mata kayan kamar yadda ta umurceni idan na daga wanda yai mata zatace muga wanan ta dan mike ta gwada a jikin ta idan kuma na dauko wani tace No bar wanan miko wancan da nake gani.
A haka har muka zabi kalla hudu zuwa biyar na gyarasu na saka mata a dan karamin troler na tafiya mai masifan kyau.
Na gyara sauran na juya don barin dakin take fadin kinga kwaso dagayen rigunan can mu gani.
Sai naji raina ya baci don dai ba wani gitma na tayi ba kila amma ta kafeni da aiki haka ba wani aiki ba.
Na nufi wirun kayan tare da kwaso mata ina dagawa take fadin aje wanan nan ko jefa wancan can har muka gama ta sake nuna min wanda zan mayar na nafe na marya inda suke.
Na juyo in kwashi sauran don in mayar take fadin wa yanan ki kwasa ina ganin ai zasuyi maki wanda naje dasu school ne wanan time wani ma sau daya nayi amfani dashi.
Ikon Allah ashe shi yasa ubangiji yace idan zakayi kayi don Allah idan zaka bari kabari don sa.
Nagodewa Allah da ban nuna komai ba duk da raina ya baci amma na tsaya nayi mata abinda take so a dakin.
Don kayana na yayan wani da wance masu tsada da kyau sun fi kalla goma wai duk ni kadai keda su tace min.
Na juya kaina a sunkuye ina fadin nagodd tace kai haba dai da baki nan ma ai duk a nan zan barsu saida hjy ta bayar dasu ga wanda take so.
Jin dadin kyautan yasa na ranan harda dakin ta na gyara mata da zuciya daya sai dai ta dawo ta samu dakin a gyara na gyara mata ko ina.
Nayiwa kawar mami kitso haka yaja hankalin sauran matan suke ta kwadayin in masu suma sai naji mami tace su bari a dawo Abuja don tare dani zata tafi.
Wani dadi naji sosai a raina jin mami tace dani za a tafi abuja din garin da nake jin labarin shi yau gani zan tafi cikin sa duk da nasan ba fita zanyi ko ina ba amma dai zan karasa ince ai na taba zuwa.
Tun da naji na fara shiri nima duk da naji Nuriya ta fadi ba dadewa za ayi a can ba nima kaya kala biyar na zaba daga cikin wa yanda ta bani ranan.
Naso sai na nunawa mami kafin inyi amfani dasu hakan bai samu ba don busy da mami take a ranan .
Bata da lokacin kowa har kanta ma da tashigo zata fice daga gidan ko ace ana mata sallama.
Sai ya kasance ina daki ko ina wurin su mama kande sai idan zanwa mami din wani abinda ya shafi rayuwan ta za a kirani.
Dan taron da akayi a dan kwana biyun dana dawo kauyen mu a gidan mami yasa na koyi wasu abubuwa da dama a furin jama,an da suka cika gidan.
Su kansu yan mata gidan mami suna ta kansu ne yanzu kowa na shirin tafiya saidai na kula cewa kamar ba wani shiri tsakanin su da yar mami din Nuriya don ban faye ganin su a tare ba.
Ko banza duk tafisu aji da kyau sosai ga wayewa da tsari don ko maganan ta abin koyone.
Washe garine za ai tafiyan inda wasu zasubi jirgi wasu kuma a mota zasu tafi inda ina cikin wa yanda zasubi mota da farko.
Amma mami tana duba list din lokacin ina dakin take fadin ban yarda abar zeey nan ba idan mun isa can waye zai kula damu kafin su iso sai dai a cire sunan wani a sakata cikin tawagan da zamu tafi.
Wayyo Allah na ashe in Allah yasoka tsuntuwa yake maga ko a dakin ka yau nice wai zan shiga jirgi tunda mami ta furta ai kamar na shiga ne in Allah ya nufa.
Karfe shidda yai muna a filin jirgi ranan nasha zagi gun yan matan mami don tafiyan nan da mami tayi dani a jirgi tare da kawayen ta da yaranta dama wasu daga cikin dangin su.
Koda muka isa can motoci muka samu sunzo daukan mu nidai basai na fada ba don bakauya na koma a cikin duk da dai kowa yana harkan gaban shine.
Amma hakan bai hana tsaraguwa ba a cikin su da rakubewa a guri daya tunda ba wanda ya sanni ko nasan shi sai mami da yaran ta sukuma bata kaina sukeyi ba.
Duk da akwai yan aiki irina kalian da wasu sukazo dasu daga wasu wurare sai dai hakan baisa na mamesu ba ina falo ko da yaushe don kada mami ta nemeni ban kusa kamar yadda naji ta fada kafin muzo.
Haka komai ke tafiya a tsare kamar yadda suka tsara abinsu gwanin ban sha,awa sai kallon mamaki nakeyi maza da mata ana ta cudanya a guri daya ba wanda ya damu da hakan .
Da kauyen mune ai da hakan ya zama abin magana a gurin mutana amma nan ba wanda ya damu da hakan .
Wai washe garine za ayi rantsuwar su mami din tunda muka iso wasu maza sukazo gidan suka fita tare da mami da yaranta manyan mazan biyu.
Haka yasa kadaicin rashin gabnin su mami a gidan ya dameni na dawo katon falon na zauna tare da wasu mata suna ta hiran su nidai sai sani lokaci nake dan jin hiran da sukeyi din.
Ina kallon duk mai shiga da fita don na jawo kofan da muka sauka a cikin hikima na zare key din kofan ina ji daga inda naje zaune ana tambaya na kyalesu.
Don ba wanda zai daukacewa nice na kulle kofan sai dai da mutum yazo ya murda yaji a rufe kofan yake ya juya inda ya fito.
Har masu tafiya a mota suka iso gidan ya kara rikicewa da hayaniyar jamma, a haka yasa na fito daga cikin falon na dawo waje na zauna.
Balle tun isowar ya matan suke aika min harara da warning ya karasa na gudo daka ciki na dawo wajen gidan.
Nan ma motocine ke faman shige da fice tun ina aunawa a raina ince wanan yafi kyau a, a ta dazun tafi har na gaji na zubawa sarautan Allah ido.
Can naga dawowan su mami hakan yasani mikewa tsaye daga inda nake zaune ina kallo na nufo wurin motar nasu.
Sannu da zuwa mami na fada daga bayan ta hankalin ta naga daddy su siyama jikokin ta suna magana.
Hakan bai hana mami dan juyowa tana amsa min gaisuwan ba ta juya taci gaba da maganan da sukeyi na juya zan bar wurin .
Sai kuma ta juyo tana fadin zeey karbi jakkan nan nawa ki rike min nazo da sauri na karba na ja dan nisa dasu na tsaya.
Sun dan gama magana ta fara tafiya yana biye da ita yana fadin amma mami sai naga kamar dai bayanin farkon nan shine shawaran bi koda yake barin gashi Jafar din duk da ban san inda ya shiga ba.
Kuje kuyi shawara dai zan dan shiga inyi sallah kafin wani abu ya dauke min hankali kuma ta fada ta fara tafiya makarrabanta suka biyo bayan ta ruuuu dasu.
Nima binsu nayi da kallo ina mamaki duk wanan taron haka don mami akayi shi haka ?
Naji tace on Allah ku bari inyi sallah yanzu zan fito ta nufi kofan dakin da nake zaton shine nata wanda na riga dana rufe tunda na fahinci hakan.
Mami ai kofan a rufe yake wata ke fadi daga gefenta lokacin da hjy ta murda kofan dakin da zuman shiga dakin..
Tun dazun ai dakin yana rufe an rasa inda key din yake da dan mamaki ta tsaya tana juyowa kafin na karso ina fadin ga key din mami a hannu nice na rufo kofan dazun.
Ok zeey key din yana hannun ki ashe thank god wallahi yarinyar kirki shaf na manta da zan fita in rufo dakin.
Da sauri na ciro a cikin aljihun dogon rigan dake jikina tunda ta dan jaye wurin na gane nufin ta na isa da sauri ina bude kofan.
Juyawa mami tayi tana fadin don Allah a dan jirani in fito tasa kai tsshiga tana fadin zeey shigo ki hada min wanan maganin nabi bayan ta muna shiga tace don Allah rufo kofan nan in huta hakana.
Ki duba akwai magani a cikin jakka ban samu shaba da safe na fita take fadi tana shiga bandakin.
Maganin na dauko daga cikin jakkata don nasan shi na saba hada mata na balla daidai yadda take sha na dauko goran ruwa mara sanyi dake dakin na a je akusa.
Daidai tana fitowa ne ake buga kofan taja tsuki tare da fadin mutanen nan idan nabita nasu bana samun sallah ko azahar ban samu yiba yau balle la,asar ga lokaci na shigewa.
Dukan kofan da aka karayi da karfi take fadin wai waye zeey bude kofan idan maishi ya shigo yaga ina sallah dole yajira idan zai iya.
Kofan na nufa na bude daga ciki aka turo ana fadin haba mami kin fita tun safe kin dawo kuma kin shige kin rufe kofa.
Aisha yar mami ke magana tana shigowa dakin a cikin shagwaba idon ta ya sauka kan mami dake kabara sallah kafin ta juyo tana kallona tana fadin.
Tare kuka fita ke nan da mami din kai na girgiza bakina kuma na fadin ina nan gida ina falo zaune na bata amsa.
Wuri ta samu ta zauna tana maida hankalin ta furin wayan ta yayin da na shiga gyara dakin don wanan daman na samu a yanzu tun zuwan mu garin..
Har mami ta idar da sallolin dake kanta ta juyo tana fadi Esha ya akayi ne wai ma kunci abinci kuwa ?
Zeey kinci abinci ita dai wanan din nasan halin ta balle yau taga wanan taron haka a gidan nan ?
Kaina girgiza daga inda nake tsaye ba tare da nayi magana ba kina jiran me wanan yarinyar da gidanci kike wallahi ga abinci nan ki tambayi safiya mana tunda ta iso idan baki san wanda zaki tambaya anan.
Waya ta dauko ta kira wani layi aka dauko ku kawo min abinci na mutum uku a hada komai a ciki ta fada.
Tana kashe wayan tare da jan tsoki kafin Aisha ta ce mami gobe fa ni dinner kawai zan yi attending.
Kina haukane gaba dayan ku da tan uwaki zamu tafi don duniya ta san ku ta fada sai yarinyar tace but mami kinsa, , ,
Hannu ta daga tare da fadin ban son korafi idan na fada kinsan iyakar maganata ke nan aka turo kofa wace ta kirane dauke da abincin wata hamshakiyar hajiya zakace ba zatai bara gidan kowa ba don bunkasanta sai gata itacs mai kasowa mami abincin .
Bayan ta aje suka dan tsaya magana da mami nidai duk sai naji na takura a cikin su don Aisha ita tana dawainiya ne da wayanta bata ma saurareb su.
Can mami ta juyo tana fadin zeey zuba muna abincin muci ko ?
Matar ta juyo tana kallon daidai lokacin dana tashi tana fadin wanan yar ina kika samotane don ban santa ba gaskiya.
Yata ce ta bata amsa kai tsaye tana jawo plate din abincin dana aje mata a gabanta inda ta idar da sallah.
Kije ki lissafa min matan nan da suka zo da yamman nan za a kaisu masaukin su idan sunci abinci tafadawa matar.
Yan kaduna ko na wani gari eh toh zaki iya lissafo min group group daga nan ki kiramin safiya tazo.
An gama hjy ta fada tana fita daga dakin Esha aje wayan nan ki dauki abincin nan kici ta fadawa yarta.
Ke kuma zuba naki idan kina zama da yunwa zaki jawa kanki matsala ba ruwana tana kai abinci a bakin ta.
Zuba wanda nasan zai isheni nayi na dauka zan fita daga dakin take fadin ina kuma zaki dawo ki zauna muci a nan .
Aka turo kofan yaya Mamud ne daddy su siyama ya shigo dakin da sallama ta karba mai tare da fadin har kun dawo ke nan yace .
Eh mami an samu inda ya dace saidai kudin kusan duk dayana ne ma mamud kasan kudi ba matsala bane ai a dai samu inda ya kamata din shine abu yanzu.
An samu mami kuma danki yace a tura mai ko nawa ne kudin zai biya munyi waya dashi ban samu ganin shi ba.
Ai da ya barshi tunda akwai kudi a hannu na don gwaunati ta bamu dan kudi a hannun mu ai.
Sun dade a dakin suna magana shigowan anty safiiya dakin yasa yafita ni dai ins zaune cikin su a tsawale.
Bayan na gama na fito na barsu tare da anty safiya din suna magana kayan abincin na kwasa nakai kitchen inda ake tarawa.
Nafito da zuman komawa falo in zauna muka hade da anty Rufaida wani irin shock naji lokaci guda saida na dan ja baya don tsoro.
Yar iska masuwa mutane asiri kin dauka ba wanda yasan abinda kukewa mami daga ke har wace ta kawo kine gidan.
Mu zuba dake a gidan nan ki gani idan zaki sha ruwa ya fada maki a ginan nan bakince kun iya mallake mutane ba ku.
Duk da ban gama fahintar inda zancen ta ya nufa ba na dan gane wani bangare na zancen nata kadan.
Tana fadin haka ta juya tabar wurin ba anty rufaida ba gaba dayan su yan kaduna dana sani a gidan wani kallo na kyamata suke bina dashi .
Na kulla da hakan ne idan sun hangoni sai inga suna kallona ana gulmata ma,ana dai sun sani a baki sun tsargeni ke nan a yanzu.
Wanda bansan wanan dalilin ba kuma banda wanda zaimin bayanin hakan sai kawai na fara kama kaina da kowa fiye da dacan baya dan dama anty salma idan mun hadu ba wanan kallon raini ko wullakanci sai dai idan na gaishe tace zeey din mami ke nan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAN UWA FATAN ALHERI A GAREKU KO DA YAUSHE UBANGIJI YASA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA YA TSARE YA KARE MUNA IMANIN MU A DUK INDA MUKE AMIN.
YAR UWA KADA KI DAUKI HAKKIN WANI KARAMIN ABUNE KI GUJI CIN HAKKIN DA DAUKAN ALHAKI WASU MAI IMANI A ZUCIYA TA GANE MAI NAKE NUFI NAN KIWA KAN KI DA KANKI HISSABIN IMANIN KI TUN A DUNIYA.
DARI UKU NE NOVEL KI BIYA KI KARANTA CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA NAUYI KOWA BA A KANKI, , , , ,
Yau gidan ga baki daya ya kicime da shirin fita zuwa wurin taro duk da tun cikin dare an kwashe baki a gidan an kaisu hotel din da aka kamawa mutane.
Hakan bai hana gidan cika ba da wa yanda suka kwana a gidan basu samu zuwa hotel ba din mutane sunzo da yawa sosai.
Ban bar dakin mami ba tunda safe dana shiga don a falo na kwanta abina bayan na gama yiwa mami duk wani abinda zan mata a lokacin.
Tunda asuba kuma na tashi na yi sallah ko alwala a famfon dana gani wajen gidan na fita nayi alwala duk wanda ya wuce a cikin mazan dake haraman zuwa sallah asuba sai ya dan kalleni.
Nidai na gama na shigo ciki na shimfida dan kwalina nayi sallah daga gefen da mutane ke bi a lokacin.
Na idar na dan dade zaune gurin ina kallon masu shige da fice ina dakon mami ta idar don nasan a lokacin tana saman salayan ta tana zikiri ga ubangjin talikai don wanan dabi,an mami ce hakan.
Can na daidaici ta gama a lokacin na mike zuwa dakin don shine aikina kuma don shi akazo dani watau kula da al,amarin mami din.
Sai kuma yanzu da nakan dan wa yarta wasu hidima a gidan don bata da damuwa ko ci fuska gata bata shiga lamarin kowa halin su yana yanayi dana anty salma itama saidai salman wani lokaci zumace ita ga zaki ga harbi idan halinta ya tashi.
Da sallama na tura kofan na shiga sai dai nayi mamakin ganin su yaya mamud a dakin lokacin shida wanan bakon danta da yazo.
Da gani wani maganan suri suke a tsakanin su a lokacin hakan yasa na juya da sauri zan bar dakin har su fita don ban san shigarsu ba lokacin sai ganin su nayi kawai a dakin.
Muryan mami ke fadin shigo mana zeey ina kika shiga ne tun jiya da dare ban sakaki a ido ba na dauka nan zaki kwana ai tunda dakunan duk akwai mutane.
Yaya mamud ya juyo yana kallo na shiko dayan ko dago kai baiyi ba ya kalli inda nake na fara takowa ina fadin.
Falo na kwana mami na bata amsa kai tsaye kafin in karasa shiga dakin na durkusa har kasa gaban ta yadda na saba gaida ita kafi in jiyo i gaidasu daya bayan daya na mike.
Kada ki sake kwana a falo baki gudun sanyi ya kamaki ne ko wani abu ya sameki nan.
Nace mami akwai wa yanda muka kwana dasu ai koma dai menene amana kike a gareni ta fada ta juya tana fadin mamud kana da son gardama.
Nikan nasa kai na shige ban daki don in fara gyara nan kafin su gama su fuce in gyara dakin ga baki daya.
Har na gama da bandakin na fito suna cikin dakin basu fita ba haka yasa na koma falo na zauna har su fita .
Ina nan zaune falon saiga Rufaida ta fito daga dakin da suka kwana tana ganina tace yauwa ke zo nan ki dibo muna ruwa a waje.
Tashi nayi na karbi bucker din a hannun ta na nufi hanya tana fadin kiyi sauri don gaba daya dakin zaki debo muna ruwa muyi wanka.
Ni dai na tafi bance komai ba na diba a mayawa na uku ne na samu masu aikin break fast suna wanke kayan miya dole na tsaya jiran su.
Don gaba daya ruwan gidan ya tsaya ba,a san dalilin haka ba sai ga Rufaida ta fito tana fadi ke karamar yar iska ko ?
Tun dazun ki debowa mutane ruwa kin tsaya iskanci dama ai tsiyan matsiyata ke nan basu iya samun arziki ba sai su ganshi a banza.
Excuse me ya fada daga baya ta inda take tsaye da hannuwa saman west din ta sai masifa take dani ni kuma na juyo ina fadin nba tsayawa nayi ba wa yan nan na sama suna aiki wurin.
Maza ki debowa mutane ruwa ko ranki ya baci shine taji ana ce mata excuse me ta dan juya don jin muryan wanda tayi a bayan ta.
Da sauri ta jaye mai a hanyar da tai banga banga tana masifa dani daga saman step din.
Wurin security din shi ya nufa yana saye da farar jallabiya kal mai sulbi a jikin sai kamshi ke tashi har inda muke saida kamshi yakai ga hancin mu.
Jin ta gaida shi bai aksa ba ya wuce ina jin matan dake wurin na fadin wanan duk cikin diyan hjy yafisu kyau da kwarji saidai shi din miskilin karshe ne sosai.
Sai lokacin na dago kai na dan saci kallon shi kafin in koma kallon Rufaida data suma a tsaye wurin da take kan kallon shi.
Dauko ruwan da ta farga nayi harna zo gabanta ina jin tana sauke wani irin ajiyan zuciya na shige ta biyoni a baya.
Daga ban dakin dana aje ruwan ina jin tana fadin kai yanzu naga hero a waje ashe fitan danayi bana banza bane tunda har na samu yai min magana yau.
Wai me kike nufi Rufaida kin san dai alkawarin su daddy ai ko tace ina ruwana da wani alkawarin su can in dai na samu ya kyasa min.
Da wanan cece kucen har na fito daga dakin suna kanyi na barsu nan dakin mami na nufa kai tsaye daga nan don in gyara.
Ina shiga ranan ne karo na farko da mami tayi min fada kan aikinta don ina sallama tace zeey mena kawo kinan kiyi tun dazun kin shige ba a ganki kin san zan fita yau da wuri.
Me ke damun ki yanzu ne tunda kikaje gida naga kina son ki sukurkuce min fa sai ayi ta neman ki kiyiwa mutum abu baki san kizo don kanki ba.
Mami kiyi hakkuri ba wucewa nayi ba dama daga bayana naji ana fadin is OK mami tunda tazo din.
Muryan ne ko mai maganan abin kallo na juya don ganin mai magana suka karaso tare da jamal, sai jamal ke fadin .
Wata kila wani ne yasa ta aiki don naga tana diban ruwa a waje zuwa ciki cikin harshen turanci yake magana shidai tun maganan farko bai kara magana ba ya samu wuri ya zauna.
Wa kike diban wa ruwa mami ta juyo tana tambayana tare da tsureni da idanuwan ta a kaina.
Anty Rufaida ne tace in diban masu ruwan wanka dukka dakin shine na tsayayi dama na bata amsa.
Wai mai Rufaida take nufi ne akan yar nan mami ta fada da hausa barta zamu hadu bari a watse gurin taron nan in mata tsiya.
Kayan dake saman gadon na fara tatarawa ina nadewa na tara gefe guda sun dan dade dakin don maganace mai muhinmanci sukeyi a lokacin naga an aiki jamal mami na fadin don Allah kada ka tsaya don munyi waya dashi yanzu.
Tare suka fita lokacin mami ta fara shiri tana fadin in miko mata wanan in bata wancan har ta shirya cikin wani rantsantsen lace da akai mata dinki ya sauko zuwa gwiwan ta.
Ga wani sarka da na fitar a cikin wani gida mai kyau da dauka ido ta nuna min yadda zan saka mata shi.
Ta tsaya a gaban mirrow dakin tana gyara kwalliyan ta da kyau da sauri na karasa gyaran dakin na share don ta fita zuwa falo.
Dakin ya koma tsab na saka mai kamshi gadon yayi kamar ba a kwana saman shi ba lokacin.
Gaba daya mami da yaranta har anty Aisha suka shigo dakin tare da ita sun sha ankon farar shada sai maiko jikin shadan da motsi yakeyi sun saka mami a tsakiya sai Aisha ce da wanab bakon da ban san dunan shi a baya suma magana sukeyi a cikin rada kamar Aisha zata shige mai jiki.
Ganin yadda suka shigo suna magana haka yasa da sauri na zo fita sai muryan jalal ke fadin ke yarinyar hajjaju ana magana dake fa.
Key ya mika mai yace ya bani shi jalal din ke min bayani wai inje in gyara mashi dakin shi yana bukatan gyara.
Na rusunan na karbi key din harna juya sai kuma na juyo ina fadin ina dakin yake yaya ?
Kwatance jamal ya fara min naji yaya mamud na fadin jeka nuna mata dakin mana har zan fita mami tace ki rike key din dakin nan guda tana nuna min kofa.
Na tsaya na cire na tafi yana waje yana jirana har muka nufi wani part ya nuna min da hannu.
Daga kofan shiga part din na hango wasu irin zaratan maza kartai dasu su shida kowa ya saka bakaken kaya a jikin shi.
Tsoron sune ya kamani da fargaba na nufi wurin na gaidasu na sa key ina bude kofan kafin in tura da sallama in shiga.
Bin ko ina na falon da nagani nayi da kallo komai yana a tsare ga wani kamshi yana tashi a dakin ta ko ina kada in tsaya kallo wani ya sameni haka yasa nasa kai zuwa kuryan dakin .
Nan ma nasha kallon saidai ban yarda na tsaya ba ina kallo ina abinda ya kaini dakin ko ina sako da lungun dakin saida na sharo shi tasa na goge kafin in fito sha daya saura.
Tun tun karowana part din da muka sauka naji gidan yai min tsit babu hayaniya har haraban wajen gidan babu wani motsi sosai kamar yadda na barshi .
Babu kowa a part din sai motsin masu aiki da nake ji a kitchen din gidan tsayawa nayi ina tunanen sun tafi ke nan inda zasu ashe ?
Ke nan na dade a dakin ina gyara ban sani ba har aka wuce akabarni sai kuma naba kaina amsa da fadin ke yar aiki wazai kaiki wurin taron manya haka.
Wanka bake bukata don haka na nufi dakin mami tunda can kayana suke tunda mukazo ina shiga na rufo kofan dakin na shiga ban daki a gurguje da tsoro nayi wanka har na shirya na fito na rufe dakin.
Kitchen din gidan na nufa don yunwa nakeji lokacin sosai gaida masu aikin dana sama nayi ina tambayan abinci.
Daya daga cikin su mai hausar gwarawa take fadin abinci yanzu sun cinye komai nasu sun tafi ai sai ta hada da yaren su kuma naji daya na mata yare sai matar tace in tsaya ta debo min akwai wanda suka ajewa wasu basu zo ba.
Suna ta yaren su har ta hado min na karba ina godiya tare da dawowa falo na zauna naci saida na koshi na kwashi kayan na mayar kitchen din da zuman in wanke da sauri matar tace ka bari wanan zaita wanke ai.
Nikan na fito na barsu don jin abinda ta fada na zauna a falon ina kallon tv dake aiki ganin yadda aka bar falin na mike na gyaro ko ina na gidan ban samu kaina ba sai daya da wani abu.
Alwala nake daidai lokacin dana fara jiyo hayaniyan dawowan mutanen gidan nayi alwalana na shige ciki a falon kamar yadda nayi da asuba ko wanan ma nan na tsaya nayi.
Suka fara shigowa daya bayan daya kowa a gajiye sai shigowan anty Aisha na mike da dan sakin fuska nake gashe ta.
Ta amsa min tare da fadin a, a yarinyar mami yaya bakije gurin taron bako kinje banganki bane tana fadin tana magana nidai nayi murmushi kawai.
Har ta danyi nisa ta juyo tana fadin zo zo zo yarinyar mami tana miko min hannu na nufi gurun ta tare muka shiga dakin bayan ta bude ta fara yarda jakkan hannun ta saman gado na dauka nakai wurin filon na aje mata shi.
Taje help me to remove dis cloth don Allah tun dazun duk na gaji dasu a jikina ja min zep please ko zanji dadi haba wanan wahalan yai yawa.
Naja mata zip tana ta tsuki da fada bata tsaya komai ba ta kwabe kayan ina kawar da kaina gefe ta fada ban daki tare da barin kayan a watse.
Tattara kayan na farayi ina nadewa kafin ta fito wanka na gyara ko ina na fito haka yayi daidai da shigowan mami gidan yan bambadanci suna bayan ta suna fadin saike hjy maryam mace mai kamar maza mata a gidan Alh ma,azu gin sun buga sun barki Allah dai yajikan maza maza sun kwanta.
Ko yanzu yasan baiyi zaben banza ba yabar baya a duniya uwar zaratan maza kece uwar gwaunan gobe kece uwar shugaban kasa, .
Wata ta karbe da fadin kece uwar manyan duniya ga gobe gaba sallama baya sallama yar manyan mutane.
Nikan na suma wurin kallon yadda ake masu barin kudi kamar ba neman su akeyi ba.
Zama mami tayi yayin da kawayen ta suka kewayeta ta ko ina ni sai lokacin ma naga wasu da ban gansu jiya ba.
Take falon ya cika da jama, a ta ko ina babu masaka tsunke a gidan wuri ya kaule da ci dasha ina labe daga kofa ina kallon ikon Allah don ni ban taba ganin bukin manya ba irin haka.
Wasu nacin abincin wasu na haraman sallah wasu kuma suna mayar da magana mai rabon abinci suna rabo kungiya kungiya.
Nama girman shi yakai dunkulen hannun mutum don girma duk nau,in da kake so na abunci shi za a baka a wurin.
Daga inda nake rakube naji mami ta fara kiran sunana da sauri na amsa da gani mami na isa guri ina gaida ita.
Gaba daya mutanen dake gurin sun zuba min idanuwan su hannu mamu ta mika min na isa wurin ta da sauri tajawoni tana rada min in shiga daki in duba cikin turamen zanin dake zube gefe a kasa in dauko guda biyar in ba matan dake mata kirari .
Na amsa ina gyada kai na matsu in bar wurin daki naje na bude na dauko kayan kamar yadda taimin bayani nazo dasu falon kowa ya saka min ido.
Ina takowa da zannuwan a hannu na daya daga cikin matan da akace in kawowa tana kyala ido ta fara fadin kaga inda kyau asali yake farar mace alkyaban mata.
Diyar hjy takawan ki lafiya dayan tace fari kun gadane ba ku ba shagon maida baka fara kaga jinin larabawa asali irin gado bana gada ba.
Yarinya sai gidan gwauna ko minister minister ma mai fada aji irin uwarki ba muna minister ba akoma gefe ba office .
Dayan ta karba da fadin haka yake don yau mun sheda mun gane bambamcin ayyah da tsakuwa a bainan jama, a.
Nidai har jiri nake gani don idanun da aka watso min a falon na nufesu na mika masu zan juyo mukayi arba da yan matan Rufaida da Nazifa tare da wasu mata a zaune suna magana kasa kasa sai hararana sukeyi.
Na raba na koma dakin mami na gyara wurin dana dauko kayan na fito har lokacin sai kirari sukewa mami din.
Ance massadan ka fadawan ka a inda na tsaya idanun su ya rufe basu san ina wurin tsaye suke gulma akan mami.
Wai haka duniya yake ai gashi bai gina kowa ba sai matarshi da diyan shi kawai ya inganta rayuwan su.
Har mami tana daga kai dama ba,a san asalinta bane ko yar waye yar hakimin kauye kawai da ita yanzu ta samu duniya taba ganin kamar tafi kowa.
Jifa kai duniya ina zaki damu kan hassada wai kuma sun zo ne har Abuja dalilin ta don tayata murna fa kuma suka koma gefe suna gulman ta.
Kafin dayan ta dago kai mu hada ido ina kallo ta zuguri dayan matar dake magana ta dago mukai arba na watsa mata wani kallo don girman ta ya gama zubewa a idona ko tunda na shedata tana zuwa wurin mami ko a kaduna.
Tun yamma nake ta kallon ana shiri muna idar da sallah mami tayi kirana muka shige dakin da wasu kawayen ta biyu.
Shiga ta alfarma mami tayi ina ciki sai faman miko muna wancan mayar da wanan dauko muna wancan abin ko mami ta ce zee ina abu kaza din nan ?
Haka dai har mami ta shirya wai dinner za, a tafi a wani katafaren hotel nan cikin garin Abuja.
Mami kan hankalin ta ya dauke bata takan kowa a gidan don uzurin gaban ta yau data zauna za a kirata gefe da magana kus kus.
Har aka fara tafiya gurin dinner din ina kallo su Nazifa da Rufaida da su Rubby suka fito sai wani shakiyanci sukeyi a tsakanin su.
Wanan na fadin yau kan akwai babban kamu don bazan fito ba sai na sace zukatan mutane da yawa .
Wanan ta daga tayi wani juyi tana gwada tafiya har suka gama iya shegen su suka fice gidan sai wani yauki da yanga suke yi nasan harda kari don inji haushi.
Saboda ina jin Nazifa na fadawa wata tsohuwa da ban santa ba a cikin dangin su tsofi da mara gata su zauna gida ba, a zuwa daku taron manya don darajan wasu baikai can ba .
Tsohuwar dai tayi mata dakuwa da hannu ta fita tana dariya ajiyan zuciya na sauke bayan fitan su falon ina wasa da yan yatsuna sai ga anty salma ma sun fito da wasu yan mata guda biyu ina ganin su nace anty salma sai kun dawo don dai tace inzo mu tafi.
Tunda nayi dan kwalliyana a lokacin amma sai ta daga min hannu kawai suka fita na koma na zauna ina tunanw kala kala a raina.
Can an dan dade sai ga anty Aisha ta fito tana tako daya daya tana waya na dago ina fadin anty Aisha sai kun dawo .
Ta juyo tare da fadin yarinyar mami baki tafi bane daga haka ta sa kai ta fice a gidan bayan fitan ta naji gaba daya zaman wurin ya isheni.
Don haka na yanke shawaran fita haraban gidan in sha iska duk da darene amma wajen kamar rana don hasken da ke akwai a wurin.
Wuri na samu na zauna gefen flowers ni daya sai tunane barkata da kalle kalle nakeyi kafin kamshin turaren nan da tun rana dana aiki a dakin yake a jikina badon na cire kayan na daina jin shi a yanzu ba.
Ta dan nisa kadan yazo ya wuce ni zuwa wurin motar shi lokacin ne na san da mutane a wurin sai ga bodyguard din nan nasa dana gani da rana sun taso zuwa wurin shi.
Kallona ya koma can na samu abin gani da zagi a raina ganin yadda suke mai kamar ba mutum ba dan uwan su.
Mota ya shiga suma suka shiga dayan motan bayan sun rufe mai suka tayar da motar hasken motar su ya haskani sosai inda nake nayi saurin dukar da kaina kasa.
Shiru shiru motar bata tashi ba na dago kai da zuman in kalle su sai ganin mutum nayi a gabana yana fadin cikin harshen turanci boss yace ki zo.
Na nuna kaina tare da fadin ni yace eh ya juya na mike na bi bayan shi zuwa wurin motar tun kan in karaso aka bude motar ina zuwa naji ance shiga mu tafi.
Murna zanyi ko mamaki duk babu daman wanan saboda tsoron daya rufeni lokaci daya banda zabi na shiga gefen da aka bude min din.
Wani sanyi da rabane ga kamshi ya dakeni lokaci daya sai dana zauna nake fadi ina wuni a cikin hausa ban sani ba ko ya amsa min don an rufe kofa a lokacin.
Har muka kai wuri ba wanda yai magana a motar ga wurin da gidan akwai nisa sosai a nawa ganin.
Wurin ya cika da motoci da ababen hawa ga jama, a wasu a wajen wurin sai security kala kala dana gani gani da tsoron yan sanda tun a kauyen mu.
Motar ta samu wuri driver ya tsaya daga inda muke muna jin magana da kidan dake tashi a cikin wurin.
Duk muna a cikin motar zaune nidai na kurawa sarautan Allah ido sai can aka bude motar duk da an bude ya dan dade bai fito daga cikin motar ba.
Can ya sauko katan mazan nan suka wani zo suka tsaya wurin motar wani ke fadin in fito na fito da sauri har sunyi gaba na bi bayan su.
Gap da zai shiga wayab shi yai kara ya tsaya a wurin yana amsa waya haka yasa na yanke shawaran fara shiga cikin inda ake taron.
Sai masu tsaron get din wurin suka hanani shiga wai sai na nuna masu pass dina wanda mutum yafi a kirga sun shiga ni ina wurin tsaye.
Har sojan dake kofan yana son ture da hannu biyu kyaleta tare muka zo ya bashi amsa bamu shiga ba saida akai muna bincike.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
JUMMA, AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA SADA MU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN MAI ALBARKA UBANGIJI YA YAFE MUNA KURAKUREN MU AMIN YA ALLAHU, , , ,
YAR UWA LITTAFIN KUDINE DON DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BANA FITAR MAKI DA HAKKIN RASHIN SANI NA FADA MAKI ALLAH YASA MU DACE AMIN, , , , ,
DARI UKU NE KUDIN SHI DON SHIGA GROUP ZAKI IYA TURA WA TA WANAN ACC 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN NA DARI UKU KACAL, , , , ,
Ina tsaye duk na kagu in shiga inga abinda ake a cikin dakin taron da nake ganin mutane kala kala suna shiga wasu ma ba mudulmai bane daga cikinsu..
Nayi kamar zan bi wani tawagan yan mata da naga zasu shiga sai sojan dake kofa ya kalleni yai warning dina da bulalan hannun shi .
Dole naja baya na tsaya ina mazurai da idanuwa tare da dan bin ko ina da kallon mamaki a wurin don gaskiya ban taba zuwa irin wurin nan .
Sojojin kofan na naganin shi ya gama waya bodyguard din shin sun sashi tsakiya suka fara jayewa a hanya suna girmama shi.
Hannu ya daga masu yana kokati shiga nayi saurin shiga cikin su da saurina don kada su barni gurin ban san yaya zanyi ba gashi tunda nazo banga wani wanda na sani ba a wurin.
Sojan ne yayi azaman riko ni sai ya juyo a hankali kamar mai rowan magana yace don't sojan yaja baya da sauri ya kame.
Wani iri naji kaina ya amsa lokaci guda ganin irin taron mutanen dake wajen gasu zaune saman kujeru masu kyau kowa yayi kwalliya gwanin ban shawa,a.
Ba zan iya sheda kowa a wurin ba idan ba karya zanyi ba saima ince kowa ya zubu muna idanune shigowan mu ashe ban sani ba mai magana ke sanar da shigowan dan mami dana biyo tawagan su.
Biye nake dasu a baya kamar jela har aka nuna mashi wurin zama wani table babba yasha kayan ado dana ciye ciye saman shi.
Da idanu yai nune sai wani ke ce min in zauna wai na dan kai zaune a hankali kamar yadda kowa ya zauna kaina na sade kasa.
Ba mami ba duk wanda ke dakin taron hankalin shi ya dawo garemu ne ance yaro da kudi abokin manya.
Wai ashe da Done nake zaune ban sani ba a wurin sai mamakin koni wacece wanda basu sanni ba suke yi.
Wa yanda suka sanni kuma suna mamakine meye hadina dashi muka shigo tare ni yar aikin gida abinda ko yan gida basu samu gatan hakan ba sai karamar yar aiki kamana.
Anci gaba da gudunar da shagalin da ake inda mawakan hausa dana sauran yare suke nuna bajintan su a wurin.
Ga masu rabon gifts suna faman rabawa table table don komai a wurin a tsare ake yin shi tun ina kallo har gajiya ya fara kamani don zaman kurame muke a table din mu.
Dan gara su dan motsi kadan zaiyi sai kaga daya daga cikin bodyguard din nan sun duka suna magana dashi a kunne.
Har lokacin da muka tashi sai dai mutane suzo su gaisa dashi su wuce yana zaune bai daga ba sai da zasu tafi ne dayan ke min magana kamar rada yana fadin in tashi mu tafi.
Haka na taso shike gaba sai ni a baya bodyguard din dun samu a tsakiya kusan ince shine farkon fita wurin da gani baison hayaniya don sai faman murza goshin shi da yake yi kadan kadan zai murza goshi har yakai ga mikewa muka fita.
Kamar yadda mukazo haka muka koma ba wanda yai magana a motar har muka kai gida ni ban ma sani ba saida naga mota na shiga gidan nasan mun kawo.
Aka bude motar zan fita na juyo inda yake zaune kamar ba zai fita ba nace na gode yaya don ban san sunan shi ba dan mami bako nake kiran shi dashi.
Ina hawa steps din ne naji muryan dayan bodyguard din shi na fadin hjy ga wanan wai ki dauka inji boss wai ashe abinda aka rabane a wurin daya yakai a mota shine yanzu suka ban.
Haka na shiga da jakkan niki niki don gifts din manya daban aka bada su ba irin wanda aka rabawa kowa bane wurin.
Daki mami nakai jakkar har biyu mai kama data matafiya shake da kayan da ban san ko meye a ciki ba na aje.
Hayaniya ne ya fara karde gidan lokacin har barci ya soma daukana don ban dauki hakan a komai a raina ni dai nasan ya taimaka min saboda halin kirki irin na uwarsa ya kaini naga buki haka na aje kawai a raina.
Sabanin sauran jama,an wurin dake tunane kala kala yadda aka ganni dasu kowa da irin nashi fassaran a ran shi.
Nikan ganin mami bata shigo ba yasa na kwanta kasa nayi filo da jakkunan kayan da nashigo dasu har barci ya daukeni hakana ban sanni ba a wurin.
Ko da mami ta dawo ta samu ina barci a dakin ta a kasa na dunkule a wuri daya kallon tausayi tayi min yadda na kwanta a maraice a kasa.
Sai taji komai da take son tambayana data dawo ya kawu a zuciyar ta bata tayar dani ba sai dai can hayaniyar suce ta tayar dani daga barcin.
Da sauri na mike ina fadin mami sannuku da dawowa maki ina murzan ido .
Sai mami ta juyo tana fadin tashi kikayi kuma koma ki kwanta nima a gajiye nake ai yanzu sallah zanyi in kwanta.
Mami me zan maki yanzu na tambaya ta juyo tana fadin bakiji mena fada ba ki koma ki kwanta abin ki dare yayi yanzu sosai.
Washe gari da safe na tashi kowa nata sallahfita nayi waje ca wurin famfo wajr inda na saba yin alwala nayi na dawo falo nayi sallah.
Na dan zauna don jiran mami ta idar kafin in kwatanta in tashi zuwa dakin tana zaune suna magana dasu anty safiya da anty sa,a da wata mata.
Gaidasu nayi na mike na shiga bandaki na fara wankewa kagin in hadawa mami ruwan zafi na fito yanzu sun karu a dakin yasa na fita na barsu a ciki na dawo falo saman kujera na takure a wuri daya .
A yadda na lura wasu daga cikin bakin suna shirin komawane a ranan garuruwan da suka fito dan yiwa mami kara sai yanzu nasan mami mutumiyar mutane ne sosai.
Yauwa zonan yar iska manya kawai mai mugun nufi dama nasan ba banza kika bar mami ba shegiya.
Na dago kai ina duban dawa anty Rufaida ke wanan magana haka na fara waige waige ina duba sai naga tana nufo inda nake tana fadin .
Bada ke nake ba kin tsaya kina kallon mutane yar iska nuna kaina nayi da hannu cikin mamaki ina fadin ban san dani kike ba ai anty na mike tsaye.
Juyawa tayi haka yasa ba gane nufin ta nace anty mami zata nemeni yanzu don tace in bar nisa da ita jiya da kika sani diban ruwa tayi min fada.
Ke ni kike fadawa wani mami tace kibar nisa da ita kizo dakin mu yanzu ina jiran ki idan baki zoba kuma kin san sauran.
Juyawa nayi na kalli dakin mami kamar zanyi magana sai kuma na bi bayan Rufaida din zuwa dakin su.
Ina shiga takai min mangara a kai da niyar kaimin mari saina dafe ta samu kaina kallon mamaki nake mata don ban san abinda nayi mata ba haka ?
Ke yar iska yaya akayi kibi hero zuwa gurin jiya wai tana zare min idanuwanta waje tana son jin amsa daga bakina.
Shiru nayi don bansan abinda take magana a kaiba lokacin ra kara maimaita tambayan ta nayi shiru Nazira tace idan ma ke manyace kici kanki kisha bakin ruwa don bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane.
Sai wace akecewa rubby tace wanan ai na fada maku snake ce a ciki ku ga kyau ga daukan hankali ga duk wanda yasan abinda ake kira da matar manya.
Don Allah rubby ki daina wanan maganan haka karta dauka ita din wata tsiyane can ta ban amsa kawai don jiya shegiya ta hanani barci da dadi duk na rufe ido yar iska nake gani a cikin su.
Turo kofan da akayine ya dauki hankalin kowa a dakin ba kowa bane sai anty zulfa yar gurin kanin mahaifin su Rufaida tana fadin ke kina nan ga mami can na kira ki.
Ban tsaya jin komai ba na mike na bar dakin da ssuri na nufi dakin mami na dauka zatayi min fadan haka sai naga sabanin hakan tana fadi yauwa zainab don Allah zauna ki hada min wanan kayan kafin in fito wanka zan tafi dasune in sallami mutanen yola don karfe tara jirgin su zai tashi.
Na amsa da to mami tana fadin ki saka komai daya daya a cikin ko wani jakka tana fadin haka ta shige ban dakin.
Zama nayi na saka kayan kamar yadda mami ta umurce ni inyi mata tana fitowa ta zauna shafan mai tana umartana dana bude jakkunan ta gani.
Har ta gama shiri a gurguje tana fadin in kwasa zuwa cikin motar ta dake wajen gidan fake na na aje sai ga driver yazo yana fadin za a saka a cikin motar ne nace eh mami tace in kawo nan zata fito yanzu.
Sai gata mun hangota suna tafe suna magana ta kawo inda nake tsaye take fadin idan kin gyara dakin zeey ki mayar min da sadkokin ida muka dauko su jiya.
Sai kin dawo mami na bata amsa ina juyawa zusa cikin gidan kai tsaye dakin na shiga na samu mami ta barshi a bude.
Gyara komai nayi tsab na shiga ban dakin a gurguje don nayi wanka sai dai kuma har lokacin ina tunanen abinda su Rufaida sukai min wanda bansan akan me suke magana ba akai.
Mami ta dawo bayan bakin nata sun tafi nan kuma ta shiga sallaman masu tafiya a mota don komawa kaduna.
Suma tana daki tare da su anty safiya da kannenta biyu suna kasafa abinda ake bawa masu tafiya.
Zuwa karfe biyu gida ya koma sai mu kadai a cikin sa sai kuma kannen mami da basu tafi ba suna daki da anty salma wace sai yanzun na fahinci akwai mahaifiyarta a cikin su ashe don basu da kama sosai da uwar da mutum zaiyi saurin gane hakan.
Mami ta tashi don yin sallah azahar saboda dan barcin daya dauketa a lokacin don gajiyan dake jikinta.
Nima na danyi barci bayan gyara falon gidan danayi duk da girman falon amma hakan bai dameni ba na tsaya na gyara shi fes.
Ina zaune ni kadai a katon falin sai tv dake aiki jefi jefi nake dan mayar da hankali wurin kallon abinda akeyi a ciki.
Eyyeh zama ma kikayi saman kujara ke nan ke gaki mara ta ido ko a gidan ku akwai irin sane halan da zaki zaunawa mutane harda dora kafa sama.
Ina sauke kafan naji muryan Anty Aisha na fadin me kuma tayi yanzu dan ta zauna kawai a kasa kike son ta zauna ke nan .
Aisha baki san wanan munafukar yarinyar bane wallahi sai ta dinga yin abu simi simi kamar wata ta Allah can da ita nan ko munafukace ta gaske.
Ku daina yin hakan mana yarinyar nan bata da wani aibun da za,ace kuna mata haka ai tana fitowa daga daki dauke da chip's tana ci a hankali ta nufo wurin mu.
Wai kin san wanan bata aje kanta a kusa ba jifa jiya harda mannewa yaya J zuwa wuri dinner.
Kin san yan kauyen nan da bakin shishigin tsiya ko ya akayi ma tabi bayan shi ko tsoro babu.
Wanan she most go back to her village kafin rigiman ta ya fi nan don wallahi ni gaba daya nama tsaneta kwata kawata wallahi.
Haba haba Aisha tace cikin muryan ta na sanyi irin nasu meye a cikin har kina fadin kin tsaneta haka yarinyar nan she is good and beside mami tana jin dadin zama da ita sosai so kima bar wanan magana kada ku hadu da mami.
Ta mike tana fadin ashe na kusa barin gidan nan don ba zan iya zama da wanan yar iskan ba da take neman nuna ita watace a gidan nan.
Har abi yakai can haba bai kamata ba kina fadin haka kan zainab don ba ruwan mu da ita don Allah kada hakan ya jawo wani matsala mai girma.
Ina laifin wanan yarinyar a nan itace fa dazun ta gyara falon nan haka muna sharan barci a daki ita bata huta ba.
Tace a fusace ni dai bana son ganin ta gidan nan ne tare damu I just hate d girl wallahi.
Aisha tayi murmushi tare da daukan chip's din ta tasa a baki kafin tace ni banga wani aibunta ba wallahi.
A gadarance tace tana wa mutane shishigi da yawa a gidan nan ko don tana ganin mami na kama matane oho ?
Ru,faiidaaahta fada a wani irin yanayi kamar mai warning din ta sai kuma taci gaba da cin abinda ke hannun ta ba tare data furta komai ba kuma .
Juyawa Rufaida tayi a fusace tabar falon ta bita da kallo tana girgiza kai kafin ta dago ta dubeni inda nake tsaye a rakube tace zauna.
Ba bata lokaci nayi kokarin zama kasa don warning din da rufaida tayi min dazun kan kujeran da har ta zagi gidan mu.
A, a kasa zaki zauna zauna a nan tana nuna min gefen da take zaune na girgiza kai tare da fadin akan hawa kujera yanzu anty Rufaida ta zageni.
To ai yanzu ni nace ki zauna ko ta fada cikin rashin damuwa sai dana danyi jimm kafin in zauna a saman dayan kujaran a takure daga bakin kujeran don ban yarda na zauna ciki sosai ba kada kuma a kara zagan min iyayyena wanan karon.
Kaina a kasa sai wasa nake da yan yatsun hannuna jin ta kira sunana yasani dago kai na dan kalleta kadan tare da kara sunkuyar da kaina a kasa.
Sai naji ta dan sake murmushi tare da fadin feel free with me zee I am not like Rufaida OK.
Na kula baki da walwala a gidan nan ko yaushe kamar a takure kike ina son sanin damuwan ki idan ba matsala.
Jin tayi shiru yasa na dago kai na dan dubeta kadan ni take kallo a lokacin ganin na kalleta ta dan daga min kai tare da fadin ke nake saurare zainab.
Ta sake fadin tell me meye matsalan ki ne meke damuwan ki ko yaushe kike a takure ?
Ina son sanin menene sirin kin san ABU A CIKIN DUHU SIRINE, jin haka yasa na dago kai na dan kalle ta tare da fadin sirin me kuma Anty Aisha ?
Sirin rashin jittuwan ki dasu mana nake son sani sai da dalilin ai hakan ke faruwa.
Da kyat na bude bakina na nace banda matsala a komai sai dai su anty Rufaidane suke yawan takura min har tana zagina da iyayyana don kawai taga nazo yin aiki a gidan su.
Zagi kuma zee koda yake koni yanzu naji yadda kukayi ko dukan ki zata iya ai a yadda ta nuna din .
To wai me ya kawo hakan a tsakanin ku ne don na kula tunda na dawo hutu da abubuwan dake faruwa a gidan nan.
Ko kina tunanen wani abune ya jawo hakan ke a tunanen ki zainab don naga dai ba shiga harkan su kikeyi ba ke a gidan nan.
Idona ya kawo kwalla nace sai nake gani kamar don irin yadda mami take min ne sukewa haushin hakan don mami bata daukeni yar aiki ba kamar yarta ta daukeni ta jini.
Sai suke ganin kamar ban cancanci hakan ba tunda nidin ba jinin ku bane da mami zata sakani a jikin ta.
Umm, umm inda wanan da wanan gaskiya amma hakan ai ba zai jawo wanan tsanar haka ba a tsakanin ku tunda mami bata ragesu da komai ba su din ma tana nuna ita ta haifemu ga baki daya ai ga nawa ganin.
Anyway koma dai meye ki kara nisa dasu duk da nasan kina hakan zangan su inyi warning din su ba tare da zancen yakai kunnen mami ba.
Nagode Anty Aisha nace a sanyaye koba komai ta nuna min kaunarta a gareni ai tunda na samu kula a wurinta.
Muryan tane ya katseni tana fadin ke din ce zeey da shegen kyau wallahi kila hakan sukewa kyashi kin san mu mata ai yadda muke.
Nima kaina shigarki ta jiya saida naji kamar karna baki kayan nan don ban dauka haka suke da kyau ba.
Saida nagan ki dashi a jiki nasan yadda sukewa mutum kyau ashe idan ya sakasu don jiyan nan gaskiya kin dauki hankalin mutane da yawa gaki kuma tare da big boss da yan mata da yawa a wurin suke son kasancewa tare dashi.
Sai kawai aka ganki dashi by surprice kin ba kowa mamaki a wurin sosai don ba wanda ya zata hero zai tsaya duban wata mace ko wacece .
Saidai bamu san sirin ba don abin ya bawa kowa dai mamaki gaskiya har mami kanta tayi maganan haka.
Tausayina yaji shine kawai anty Aisha kin san irin ku irun tausayin na kasa dasune .
Kafin tayi magana wayan ta yai kara ta dauka sai naji tana fadin gamu a falo tare da ita yasa nayi saurin dagowa ina duban ta.
Kije mami na neman ki a daki ina jin haka na mike da sauri zuwa amsa kiran mami din yayin da Anty Aisha ta bini da kallo har na shige dan lungun da zai sada mutum da dakununin gidan.
Zaune na samu mami tana duban wayan ta, na shigo da sallama ta dago tana fadin duba min ko masu girki sun gama a kawo min nan don bazan fita dakin nan yanzu ba hutu nake so yau.
Da sauri na tashi zuwa kitchen din inda na samu anty Aisha tabar falin ita ma na shiga kitchen na fadawa madu aikin sakon mami din.
Nan danan suka shiga hada hadan hada nata abincin cikin wani katon try na dauko na kawo mata .
A dakin na samu anty Aisha tare da uwar suna magana shigowana sai sukai shiru mami na kula da tana bina da kallo kafin nace ga abinci mami.
Yau ajeshi nan don har ruwa da drinks sun saka a ciki na juya zan fita take fadin zo nan zeey na dawo da sauri zuwa gareta.
Nakai kasa take fadin yau zeey yaya akayi na ganki tare da jafar jiya a gurin buki ?
Da sauri na dago kai ina fadin Jafar mami a, a bani bace nikan da yayan nan da yazo na tafi koshi an barni ni kadai a gida sai tsofi na fita waje na zauna shine da zasu wuce yace inzo mu tafi shine na bishi mami.
Ok mami tace yayin da take saukowa saman gadon don wani lokaci mami a kasa take zama taci abincinta.
Saida na tsaya na zuba mata ta fara ci tana fadin oya dauki wanan sauran kije kici don nasan bakico komai ba yanzu haka.
Na dauka tare da fadin na gode mami na fita da ture din a hannu na ina murna zan sha ferfesun kai yau har in bari duk da ina ci sai dai diban tsoro nakanyi wa abinci wanan kuma an bani shine kai tsaye.
ZAINAB IDRIS MAKAWA[04/12, 22:48] +234 903 349 8278: Tnx
[04/12, 23:33] +227 98 36 59 34: 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣5️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
IDAN NACE NA KUDINE INA NUFIN IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI KO ?
Ranan nasha dadi don a dan lungun shiga dakin mami na zauna a kasa na kwashi garabasa na a wurin ina tsotson kanshi ne su yaya mamud suka shigo zasu shiga dakin mahaifiyar su su uku babu jamal a cikin su.
Kunya ne ya kamani yadda suka sameni ina gwigwiyan kashin kafan saniya ina kuma tsotson ruwan miyan da ya lake a cikin sa don dadi.
See dis village girl jalal ke fadi dubeki don Allah a kasa kika wani zauna kamar wata kazama can.
Dan kallona yaya mamud yayi ya kawar da kanshi gefe daya yana fadin wai a ina mami ta samo wanan yarinyar ne ?
Haka yayi daidai da shigar su dakin mami din inda direct wurin da mami ke zaune a kasa Jafar ya nufa ya zauna a kasa tare da karban cibi a hannun mami din.
Kallo shi mami tayi kafi ta mayar da kallon ta ga mamud tana fadin me naji kana tambayane ?
Sai jalal din yace dis your village girl mami kinga yadda tawani zauna a kasa tana cin abinci kamar wani zai daka mata tsawa ta sheka a wurin.
Ina ruwan ka da ita mami tace tana kawar dakai zuwa kallon Jafar da yakai ruwan miya a bakin shi ya fara taunawa da kyat kamar an sashi ci dole.
Yanzu haka nasan baka karya ba tun safe maimakon yai magana sai cikin shi ya shafa yana lumshe idanuwan shi a hankali.
Yaya jalal zainab tana da gaskiyan ta ta fita falo kuma a zageta shiyasa ta labe nan nasan tana ci hankali kwance.
Waye zai zage ta mami ta fada a hasale ciki ko in kulla kai tsaye tace your daughters don dazun nan na raba ta da Rufaida a falon .
Wai kawai ta zauna a kan kujera in kaga yadda Rufaida kewa yarinyar nan abin ba kyau wallahi .
Shine na zauna da zeey din ina tambayanta take fasin bata san abinda tayi masu ba suka tsane ta ita zagin ne ke ci mata rai dasu ai sosai.
Wanan Rufaidan badon mahaifinta ba da nake jin nauyin shi a yanzu wallahi akan yarinyar na dana mata tsiya sosai a gidan nan ko ta koma gidan su.
Mami akan wanan yarunyar har kike fadin haka yarinyar fa ba yar kowa bace balle har ki fadi haka nasan shi, , , ,
Karbi nan jalal mami ta jefa mai dakuwa da hannun ta tana fadin uwarka ma kaji ance ba yar kuwa bace face dagacin kauye.
A haka kuma mahaifin ku ya aureni har muka haife ku ka san mai Allah zai mayar da ita gobe ita kanta Rufaida data sani da batai mata hakan ba don Allah yasan goben ta.
Yaya mamud yace ni ban ma san yarinyar ba shine yanzu nake tambaya ko wacece ita ina dai yawan ganin ta gidan nan all d time idan na shigo.
Ina zaka sani tunda ba a gida kake zaune ba itace yanzu mai koyawa diyan ka karatu a gida .
Yace so tasan abu ke nan sosai ma mami ta fada tana budan baki ta karbi abincin da jafar ya debo ya bata.
Ni dai bana son takurawan da su rufaida ke mata Allah mami yarinyar tana cikin damuwa haka sosai wallahi.
Ido ya runtse kafun ya bude ya juyo yana fadin you are too talkative now kin fadi wanan maganan tun farko yake cewa Aisha.
No mami ta tsawata masu su daina muzanta ta don yarinyar she is beautiful sosai sai dai tsiyar abin yar tallakawace ita.
Mamud ya fada yana gyara zaman shi oh shi tallaka ba mutum bane ko don kawai tana tallaka sai akace a muzantata.
Is OK mami ku bar zancen nan don Allah ya fada rai bace yana kai mata cibin abinci a bakin ta ta karba.
Sai mamud ya kwashe da dariya yace mami ba fa nufina ke nan ba kin sani so iam sorry for dat ta dago tana hararan shi kawai.
Hummm hummm in dai a kan wanan maganan ne mami zatayi fada da kowa ai a gidan nan na rasa me wanan yarinyar tazowa mami dashi haka.
Anyway naji suna fadan wai sun asirce mami ne ita da , , , ,
Jalal getout bana son yawan zuba haka tin dazun nayi warning kan zancen nan kun kama magana kan abu daya haka.
Yana gamawa ya mike tsaye zai bar dakin mami tace ina kuma zaka zansa a kawo maku abinci kunci yanzu a gabana.
But mami , , , shiru yayi don hannun data daga alaman yai mata shiru dole ya dawo ya zauna waya ta daga ta kira wani layi tare da bayanin abinda za ai mata.
Kafin wani lokaci an hada dining din tashi sukayi tana gaba suna biye a bayan ta a falon dai nake sai dai ba a zaune ba ina gutfane raben jikina na saman kujera hankalina yana gun kallon tv dake aiki tun safe a falon gashi ban iya canza chenal din ba, don haka nake kallon dole hakana.
Zeey kina nan kina kallo mami ta fada saina dago da sauri don jin muryan ta danayi ina fadi cikin fara, a sannu da fitowa mami.
Namike tsaye tace no koma abinki ki zauna don me baki zauna da kyau ba ta fada kamar bata san abinda ya faru ba tsakanina da Rufaida da rana ba.
Dan murmushi nayi ta nuna min kujeran tana fadin zauna sama daga yau duk abinda kike son yi a gidan nan kiyi shi kamar kowa kinji abinda na fada ko ?
Na gyada kai ina kaiwa zaune Nazifa dake fitowa daga kitchen a gaban ta mami ke min fada ta juya zuwa dakin su nasan zata fada masu abinda mami ta fada min ne yanzu.
Mami basu bar wajen ba sai da magariba ya kawo jiki suka mike don zuwa sallah lokacin har na fita naje waje don yin alwalani.
A wajen suka sameni sai dai ban samu gaidasu ba suma ba wanda ya kula dani kuma sun ganni din wurin ina alwalan.
Na dawo na samu mami ta shige dakin ta nan falo na tayar da sallah sai da na idarne Rufaida ta fito tazo ta tsaya a kaina tana fadin.
Sai kin bar gidan nan munafukar yarinya kawai don nayi maki fada kan hawa kujera dazun shine kika fadawa mami ko ?
Da sauri na dago kai tare da fadin wani bamuyi wanan zancen da mami bani .
Rufamin bakin nan naki mai warin tsiya zaki cikani da surutun tsiya to bari kiji tunda nan ba gidan ubanki bane sai kin barshi walla, , , ,
Ke menene haka me tayi maki keki zaginta haka kawai don cin zalin zaki saka yarinyar mutane da zaki haka.
Yaya mamud ne tsaye daga bayan mu yake fada da Rufaida ta dan tabe baki tana fadin wallahi yaya yariny sai yace wanan ba daidai bane ya juya ya nufi dakin mami rai bace.
Yana shiga yake fadin mami gaskiyan Aisha yaran nan sun matsawa yarinyar nan haka ashe yanzu na same su a falo rufaida na shirin dukan ta badan Allah ya kawoni ba data kai ga dukan nata ma kila.
Innalillahi me yaran nan suke nufi newai kan yarunyar nan a to mami indai zamanta nan tare dasu zai zama matsala gara dai ki sallameta yace tare da mika mata ledan maganin daya sayo mata.
Ranan ma a dakin mami na jena kwanta a kasa kamar yadda na kwana a jiya a takure don gani nake idan nayi dogon motsi zan dameta a dakin ta.
Washe gari tunda na tashi nake jin kamar zazzabi a jikina hakana na daure nayi duk wani aikin da zanwa mami nayi shi cikin daurewa.
Inda Allah ya taimakeni mami ta fita tun goma na safe na samu na shige dakinta na kwanta ba tare da nasha magani ba.
Har lokacin da mami ta dawo daga unguwa data fita ta zauna falo bataji motsina ba kota ganni da ido sai tambayan mutane take suna fadin suma tun safe basu ga giccina ba.
Aka kama fadin ina na shiga hankalin mami ya tashi ranta kuma ya baci dani sosai kan hakan don dai tasan ban san kowa ba a garin.
Saida mami ta shigo dakine ta ganni a kwance na dunkule cikin hijjabina ina rawan sanyi.
Ja tayi ta tsaya da mamaki tana fadin ke zeey lafiya ko kin shige daki kin kwanta kin tayarwa mutane da hankali.
Jin muryan mami sama sama a kaina yasani bude ido da kyar na buda baki jikina na rawa zazzabi mai karfi nake fadin massarara nake ji mami tunda na tashi da safe.
Jin haka yasa ta karaso inda nake kwance tana fadin saiki shige daki ba tare da kin fadawa kowa ba ki rufe kanki a ciki don rashin wayau ko me ?
Da kin fada da an samu wanda ya baki magani ko a kaiki asibiti kinzo kin shige hijjab kina rawan sanyi haka kinki jan bargo saman gado ki rufe jikin ki dashi.
Tana wanan fadan takai hannun ta a jikina tana tabawa taji zafi radau da sauri naga ta juya ta fita dakin.
Sai gasu da jamal da Jafar sun shigo dakin da saurin su jamal ne ya kai hannun shi saman goshina yaji zafin da jikina yayi da sauri ya cire hannun shi yana fadin mami dis is serious fa jikin yayi zafi sosai.
A hankali yaya jafar ya tako zuwa inda nake kwance saman rough shima ya taba jikin nawa wani irin shock ne ya ratsa jikina lokaci guda duk da yanayin zazzabin da nake ciki haka bai hanajin wani yanayi da ban san na meye ba lokacin.
Idona na runtse daga inda nake kwance nunfashina har yana sarkewa yayin dashi har lokacin yana duke a kaina ya dago yana fadin les take her to the hospital dis is serious mom.
Mamice ta dagani daga kwancen da nake sai na kasa tsayi tsaye da kyau jamal kamata da kyau a kaita wurin mota mami tace.
No barta a kira wasu daga cikin yaran nan su taimaka su riketa zuwa motan ya fada yana juyawa ya fita daga dakin.
Fita yayi ya tsaya yana fadin matar dayaga tana falo ta kira masa sisters din shi dakin su don baisan dakin da suke bama.
Sai gasu sun zo suka same shi tsaye inda kowa sai mamakin kiranda yake masu sukeyi don da farko da matar tace shine basu yarda ba saida suka fito suka same shi a tsaye yana jiran su din.
Bai tsaya kallon su ba ganin sun fito ya juya yana fadin help dis girl please kallon juna sukayi don basu gane wace yarinya yake magana a kanta ba lokacin.
Ganin ya nufi dakin mami suka bi bayan shi sai ga mami ta fito tana ganin su tare dashi tace yawa don Allah wata ta taimakawa zainab zuwa wurin mota mu kaita asibiti.
Jin an ambaci sunana yasa Nazira ta fara ja da baya Rufaida ko ko motsi batayi ba a inda take sai salma ne tace mami bata da lafiyane dama.
Wallahi salma ki san yarinyar nan bata da hankali bata jin dadin jikinta ta shige daki ta kulle kanta a ciki haka.
Salma ta matso tana dafani tare da fadin sannu zainab tana kokarin tayar dani zaune.
Haka ta dan rikeni har zuwa wurin mota data ganshi tsaye shida jamal an bude kofar motar.
Mamine tacewa salma shiga salma muje tare don Allah da sauri tace to mami ko mami ta dauka driver ne zai jamu sai ji tayi yace jamal shiga muje tare.
Turkish hospital ya nufa damu da kwantace har ya gane wurin munyi sa, a akwai likitoci bamu dade ba muka shiga bayan yankar katin da jamal yayi baisan sunan baba na ba dole sunan mahaifin su yasa a katin don sauri.
Tare da mami muka shiga ganin likitan ya dubani bayan yan tambayoyin da nake amsawa da kyat gareshi.
Allura da maganguna aka ban sunso wai su dan kwantar dani mami tace aimin dai allura mu koma gida washe gari sai indawo in karbi sauran allura.
Haka muka juyo muka dawo gida zuwa lokacin har na fara dan jin saukin jikina haka muka shigo gidan a falo muka samu wa yanda suke gidan a lokacin.
Da ganin su akwai maganan da sukeyi a lokacin don yadda suke gaida mami da dawowa ba wanda ya tambayi yaya jikina daga cikin su.
Dakin mami ta kaini ina jin anty salma na fadin ku baku iya gaida mara lafiya bane ?
Ta fada tana shigewa dakin ta suka bita da fadin Amebo Olopopo suna hararan inda tabi zuwa dakin Nazifa tace waya sani.
Ko taje ta daukowa mutane ciki ne a gida Rufaida tace ko cikin wa yan nan katan na waje wani ya taushe yar iska yafi karfin ta ba.
No ku daina fadin haka don Allah Ruby dataki bin iyayyenta su tafi ta fada tace kun san fa wanan zargin abu mai girma idan kun zargeta da aikata zina alhalin batayi ba Allah na iya jarabtan ku kan hakan.
Kawai dai mu barta da samun wuri don samun wuri kan yarinyar nan ta same shi har ta batun zarta mu a yanzu.
Ku diba yadda guy din na ya fito a gigice dazun yana neman wai wanda zai taimaka ya kaita wurin mota.
Kyale dan rainin wayon banza kawai yana wani abu kamar bakin baturen dake jin warin mutane nina rasa me wanan yarinyar tayi haka gaba dayan su suke ji da ita a gidan nan haka Nazifa ta fada tana jan tsuki a karshe.
Ya kamata dai mu san mafita don wallahi garin kallon wuta kada kwado ya fada ciki muna nan zaune tazo ta samemu har tafimu kima a wurin su .
To yanzu meye abinyi kawai Rufaida ta fada a cikin damuwa sai Ruby tace a abinyi shine mu san mafita .
Don wata kila ladabin ta garesu ne yake ja mata kauna a wurin su kin san su don son girma kamar gyabo ai.
Kai ba wanan bane gaskiya Rufaida tace ni kawai nasan shegiya asiri taje gida aka kara bankadawa mami dasu gaba dayan su.
Ki duba ko jalal da jamal da muke zama tare duk a yanzu sun bari wallahi ke ni na tsani wanan yarinyar gaba daya sai na halakata ko inyi sanadin barinta gidan barni da yar iska kawai nasan abinda zan mata ai.
Daga dakin shi inda yake zaune yake kallon su shida jamal da shi kanshi baisan gidan akwai cctv ba sai yau ya girgiza kai tare da fadin wasu irin yara mami ta aje haka a gida.
Yaran nan ko mami ba zasu barta ba idan sun samu wuri ya fada yana mikewa zai shige daki sai kuma ya juyo yana fadin .
Kada inji zancen tv din nan a bakin wani a gidan nan ko mami kafadawa dashi zamu samu matsala sosai dakai a rayuwan mu.
Na dade ina zargin yara nan ba zaman banza sukeyi tare da mami ba tunda naji suna gidan nan zaune yanzu.
Hannu jamal ya daga duka biyu yana fadin believe me yaya kowa ba zan fadawa wana magana ba ko jalal ne yace is better for you don ban son yawan magana.
Nikan barci nayi sosai a dakin mami na samu gadon mami na haye ka laushi kamshi da sanyi na tashi yana shiga min hanci a hankali.
Duk da halin rashi lafiyan da nake ciki bai hanani jin dadin kamahin dake shiga min hanci ba lokacin.
Sai goma da rabi na dare na falka koshi mami ce da Aisha a dakin suke magana yasani bude idona sannu zee mami ta fada tana kallona tare da tambayana jikina.
Me zakici yanzu Aisha ta tambaya tana kishingide saman gadon mamanta da waya a hannunta tana kallo.
Mami ta kura mi ido tana so jin amsa da za bayar a hankali hannna ina share wayen dake kokarin zubo min a idona.
Tambayan ki ake ba kuka akace kiwa mutane ba a na tun safe nasa bakici komai ba a cikin ki .
Na amsa cikin karfin hali da fadin tea zan sha ina kokarin mikewa tsaye ina kuma zaki Aisha ta fada zanje inyi fitsarine na bata amsa.
Ina koarin nufar kofan fita daga dakin don ba daman in kewaya mami tana dakin ta don haka nake kokatin fita ba tare da nasan inda zan nufa ba a lokacin.
Sosai mami da yarta suka kula dani don sun nuna damuwan su a kaina sai anty salma da itama ba laifi don tana zuwa a kai akai tana gaidani da jikin.
Har naji sauki na fara fitowa falon don in bawa mami dakin da ko yaushe a dan kwana biyun nan ina kwance.
Ranan dana fara fitowa falon ne naga canji sosai wurin yan matan mami wanda hakan ya bani mamaki don fuska sosai suka sakarmin harda zolaya wai an taya naki sallamawa.
Ni dai nayi murmushi tunda ba saba haka nayi dasu ba dama duk da yadda nake hakana mike na yi aikin da zanyi a ranan don sai naga aikin da akeyi kamar baya fita da kyau.
Aiko mami na dawowa ta hauni da fada don ta gane nice nayi aikin cewa kawai nayi naji sauki mami.
Tadaiyi min fada ta fara cire kayan jikinta na fita dakin don bata wuri ta shirya a tsanake kamar yadda muka sabayi.
Sai data fito falo na koma dakin na gyara tare da nade kayan data cire a jikinta na wanko har bathroom din tas.
Tun ina jiran inji ance gobe ko jibi zamu tafi sai naji shiru saidai kawai ranan da muka cika sati da zuwa ranan da dare mami ke fadin su Rufaida su shirya zasu koma kaduna do hutun su ya kare .
Ina gurin jin haka yasa na kallo mami don banji tayi magana ba a ciki sai naji mami na fadin ina sane dake zainab ban manta da karatun ki ba ai.
Wata kila nan karatun naki zai dawo yanzu do zaman mu zaifi yawa yanzu a nan sai dai na duba naga abinda ya dace mami ta fada.
Basuji dadin yadda mami ta tsara ba don ba karamin dadi duke ji ga wanan zaman namu ba don ko yaushe suna fita shoping da yawo sun samu dakewa sosai don mami bata zana gida sai yamma take dawowa gida.
Dole ba don sun so ba suka fara shirin komawa kaduna salmace kawai bata nuna damuwanta a fili akan hakan ba wucewab sune yasa mami bani daki na kaina inda zan zauna kamar yadda nake da dakina a kaduna gidan ta.
Haka ba karamin dadi yai min ba sosai a raina don dama a takure nake saboda zama da mami da nakeyi daki daya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣6️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAU DA GOBE NA ALLAH NE YAN UWA MU RIKA SHUKA ALHERI DON WATA RANA A FADE MU KO BAMA KUSA, UBANGIJI ALLAH KA KARA MUNA IMANI DA DOGARO DA KAI YA ALLAH, , ,
IDAN NACE KI BIYA INA NUFIN NA KUDINE YAR UWA KI GUJI SHIGA HAKKIN DABA NAKI BA DON ALLAH ALLAH YASA MU DACE .
DARI UKU NE KACAL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA AMINCI.
Zance tafiyan su rufaida baimun dadi ba don gidan ya kara komawa silent yanzu da suka tafi ashe dan mutum ko yaya kake dashi yana da rana a gareka.
Yau na kara fahintar hakan wanda dama nasan da hakan tun barina gidan da har nakan ji kewan yan gidan mu ga baki daya har Asabe da lantana.
Sai gashi dan sabon da nayi da zama da ukuban su Rufaidama yanzu ina kewan hakan gareni.
Sai ya kasance in zauna ni kadai ina faman tunane a guri daya idan kowa ya fita zuwa nasa tsabgan sai in rage dagani sai gwarawan yan aikin nan dake gidan.
Gashi ni ban saba dasu ba don ko yaushe a cikin yare suke su yau ma kamar kullun bayan fitan mami da Aisha data wuce school na gama gyaran dakin mami na koma dakina nayi wanka.
Na shirya a cikin wani bakin dogon riga da Anty Aisha ta ban zuwan mu Abuja don ganina da yan kayana kala hudu dana dauko da zamuzo kullun.
Dan kalin rigan na daura a kaina mai kawai na shafa a fuskana don ni ba gwanan kwaliya bace dama haka.
Duk da hakan fuskana ya dan fito fayau falo na dawo na zauna ina karyawa ina kallon tv daya zama min abokin hira yanzu.
Cibi biyu na kai ga bakina na orth din da nake sha muryan Nuriya matar yaya mamud ya ziyarci kunnena don ni nikan manta da itama a gidan tunda ita bata shiga mutane kuma bata barin yayan ta suna mamuwar kowa a gidan.
Fadi take ke zeey ki zo ki gyara min part dina yayi datti da yawa yau ina son a gyara min shi don Abbani yai magana kan hakan da cewa yaya mamud kamar yadda take kiran da dashi.
Yau kan na turza don bansan sanda bakina ya furta anty Nuriya yanzu nake karyawa idan na gama zanzo na bata amsa.
Ke yaushe har raini ya shiga tsakanin ni dake haka ta fada niko a raina nace wata sabuwa kuma waini mena tarewa mutane haka kowa yake jin haushina dan abu kadan zai zama min matsala babba ga kowa.
Maza ki tashi kije kiyi abindana sakaki kafin na bata maki rai ta fada a hasale tana mai tsureni da idon warning gareni.
Kokarin aje cup din dake hannuna nake naji muryan Jamal na fadin ke dauki cup din ki ki karasa karyawan ki kafun ya juya wurinta yana fadin.
Baki da tausayi wallahi yarinyar nan tun safe take tsaye sai yanzu ta samu kanta take karyawa zakice ta bar karyawa tazo maki aiki.
Wani juyawa tayi tana masa wani kallo tare da fadin kai kuma fa dan rainin wayau da zakazo kaja min raini a wurin yar aiki haka.
Aiki na sakata a part din mu kuma dole ta tashi ta tafi yanzu don yanzu nake bukatan ai min shi.
Bazata ba sai ta gama karyawa ya kara bata amsa yana kallona tare da fadin koma ki zauna nace ki karya idan kin gama sai ki tafi.
Ba abun mamaki bane don ka fadi haka jamal tunda kaganta haka kana da mugun nufi a kanta kamar yadda kuka saba yi a turai ai.
Sheri zaki min ya fada a hasale yana nufota ni kan hannu na dora a kai ina shirin yin ihu don yadda ya nufota sai Allah zai gyara yau a tsakanin su.
No no no jamal don Allah please kada ka tabata be a man kada ka karasa wurinta please.
Nan dai hayaniya ya kaure a tsakanin su ta fadi ya fadi karshe dai ta juya tana fadin ke kuma karamar yar iska kada kizo ki min abindana saki kiga abinda zan maki yau gidan nan.
Ba zatazo ba din kiyi duk abinda kikai niya a kanta jalal shima ya fada a hasale ta juyo tana fadin sai ku gayawa wanda baisan abinda kukeyi da ita ba a gidan nan.
Innalillahi ai bansan lokacun dana dora hannu a kai na fara rusa kuka ba karyawan da banyi ba ranan ke nan.
Don sukan tana wucewa suka tafi suna fadin yau zasu gamu a gidan nan dole sai ta fada abinda take nufi ko su casa ta son ransu nan suka barni tsaye ina kukan takaicin zargin da maman su Amir da Amirah tayi min kan tagwayen mami din.
Banda yadda zanyi duk da sunce kada in tafi haka na aje abin karyawa na na nufi part din anty nuriya din da zuman mata aikin data sani.
Gaskiyane part din kan yayi datti kamar ba mace a cikin sa da take rayuwa ko namiji yabar gutin shi haka za a iya kiranshi da kazamin namiji.
Sai kaga mace fes a waje amma kaje muhalinta sai ka raina mata wayau kan rashin gyaran wurin zaman ta.
Kayan dake saman kushin na duka na fara nadewa hankalina ya dauku ga abinda nakeyi kawai ba tsamani naji saukan mari a fuskana lokaci guda.
Na dago dan gani waye yai min wanan aikin na kara jin wani a tsakiyan fuskana tana fadin gobe in kara saki aiki wani dan iska a gidan nan yace kada kiyi.
Ke har kin isa me kika dauki kanki banda matsiyaciya kaskantatar yar aiki kawai kina nufin ni kyauki da wani halin ki can zai rudeni ne matsiyaciya mai zubin karuwai kawai.
An walla, , , , kofan da aka bankadone yasa ta kasa karasa maganan da take son furta min ta juya tana kallon wanda ke tsaye a kofan nasu.
Ni dai ina tsaye har lokacin zafin marin bai gama sauka min ba sai wani dishi dishi nake gani idan nayi yunkurin bude idanuna lokaci guda.
Muryan Jalal ne yake fadin idan kika kara dukan ta yau sai kin raina kanki gidan nan wallahi kinji na fada maki.
Jalal ya juya gareni yana fadin ke kuma fito part din nan tun kan ranki ya kai ga baci yayin da Nuriya ke kokari daukan waya don kiran mijin ta tana durawa jalal din zagi ta uwa ta uba.
Bayan mun fita part din ne ta kira mijin ta fada mai karya da gaskiya shi kuma ya hau karfe uku duk suna gida gaba dayan su don mami tace su hadu a gida.
Yayin da har lokacin ina daki tundana shige ban fito ba ga fuskana gefen idanuna ya hau ya rufe sosai har bana gani dashi.
Sai faman tunane nake a raina duk kokarina wajen kaskantar da kaina a garesu don gujewa faruwan irin haka .
Wanda mami da yaranta a kullun suke kokarin jana a jikin su suga dai na sake a cikin su wanda ni na kasa hakan don kada in shaga irin wanan matsalan a cikin su.
Ina nan a kwancen da nake ina faman tunane muryan Anty Aisha ya daki kunnena tana fadin zainab mami na kiranki a falo.
Na dago dan mata sannu da dawowa tana ganin fuskana tace ke meye haka fuskanki ya sauya lokaci daya ?
Cikin dakewa da karfin hali nake fadin sannu da dawowa Anty Aisha yyawa me ya sameki haka ta kara fada.
Ba komai anty na fada ina kokarin tashi daga saman gadon ta juya ta fita daga dakin.
Ina tafe na sa gefen gyalen dake kaina na dafe idon dashi abu ga farin mutum lokaci daya fuskan nawa gaba daya ya canza kala ga alamun hannun Nuriya radau a fuskana.
Gaba dayan su sun zuba min idanuwan su a kaina har na karaso inda suke zaune na kai kasa na fara gaida mami data kura min ido kamar ta suma da mamaki.
Kafin in dan dago ina kare fuskana ina gaida yayan nata zeey meye wanan ya bata maki fuska haka mami ta fada tana kallona don jin abinda zan fada.
Kowa falin ni yake kallo yayin da mami ta kara maimaita maganan ta gareni kafin in magana Nuriya tace nice na mareta.
Har mijin ta saida ya juya yana kallon ta don abinda ta fada lokaci guda cikin rashin damuwan da hakan.
Akan me kika duketa haka Nuriya mami take tambayan ta cikin mamaki har lokacin.
Don me zan sakata aiki mami take zuwa lokacin dana umurceta tazo don kawai wanan dan rainin wayau yace kada taje tana nuna jamal a hasale.
Shi dagowa yayi don yin magana sai lokacin Jafar ya dakatar dashi don tun zuwana kanshi na kasa yana dakilan wayan shi cikin ko in kula da wanda ke wurin gaba dayasu.
Jamal me zaka fada tunda ta riga data fadi itace tai mata hakan da bakinta yanzu ta kuma fadi dalilin yin hakan gareta.
Sai akace a duketa haka ko boyace na sayo ai ba za ai mata wanan dukan ba haka balle ba boya bace karbo ta nayi hannun iyayyen ta don kawai ta taimakawa rayuwana.
Ban kawo don wani aiki ko aikin wani a gudan nan sai nawa bukatan ni kadai da take min kuma tana da kokatin wurun aiwatar min da komai tun kan na fada mata abinda zatayi min.
Haba wanan dukan haka ai abin yayi muni komai tayi maki ai zaki bari in dawo ki fada min sai nayi mata fadan hakan .
Koni dana karbota wurin iyayyen ta aiba zan taba mata wanan duka haka ba don itama mutum ce kamar kowa a gidan nan.
Ok mami ke nan dai yanzu na fahinci da sa bakin ki yaran nan sukai min rashi mutunci ke nan wanan banzan yarinyar mara mutunci da asali ta fini yanzu a gidan nan.
Nuriya mind your language bakin ki yasan abinda yake fada bayan kiyiwa yarinyar nan irin haka kuma zaki kirani ki fada min karya don kawai ki hadani fada da yan uwana.
Dama nasan haka zai kasance ai don wanan yarinyar ba karya su Rufaida ke fada ba ta asirce kowa a cikin ku har mami din gaba dayan ku tasa an maku asiri a kanta.
Enough enough Nuriya bakin ki yasan abin fada a nan kada ki kawo muna wanan shirmen naku ba banza yaya mamud ya kara fada a hasale.
Tashi tayi tana fadin aida rama mata kayi zaifi da wanan hasalan da kakeyi don kawai na mari wanan .
Mami ne ta daka masu tsawa tana fadin ya isa haka ki dawo ki zauna idan ki gama fadin abinda ke ranki.
Kamar ba zata zauna di ba kome ta tuna sai ta kai zaune din tana kada kafa mami ta sauke ajiyan zuciya ta fara magana.
Da farko ke Nuriya a kanki zan fara don ba zan tsaya kina fada min magana cikin rashin mutunci a gaban diyana ba haka.
Don dan kuka shike jawa uwar shi jifa, sai dai kinci albarkacin darajan abu biyu da kike ci gareni har kullun a wurina.
Shine auren dana da kuma kasancewar ki uwar jikokina a yanzu wanan damar kike ci har kullun a wurina don ba zan so saka matar dana a gaba idan ba haka ba ke kinsan wani abin ko ance kiyi min shi ba zakiyi shi ba duk da kudin da kike takama iyayyen
Sai yaya mamud ya dukar da kanshi don ya gane me mami take nufi da maganan ta saboda halin Nuriya a ku)un magana ya taso itace bata da gaskiya.
Mami taci gaba da fadin saidai zanso ki gane cewa ba zan lamunci aibanta mi diya ba ko zargi su a kan zina.
Mami ni kar,a laka min abinda ban fada ba fa a nan don kawai ana jin zafina kowa ya taso sai yace banyi daidai ba .
Don hakane nake nisantar kowa a gidan nan hakan baiyi ba har sai wani ya takaleni kuma inyi magana ace banyi daidai ba.
Yanzun wanan mara galihun tafini daraja da kima a wurin ku ake nufi tunda itace mai gaskiya ke nan don kawai taimin ba daidai ba na hukuntata.
Who are Nuriya who are you by the way har kina wani fadin tayi maki laifi kin hukuntata akanahi ke kika dauketa aiki a gidan nan ko wurin ki take.
Ke ba zaki iya yin aiki ba ki zauna da masu aiki kuma kin hana hakan saboda bakin kishin dake damun ki.
Mikewa tayi tana fadin na hana ka dauki yar aiki mamud don ban so kai din ban yarda da kaiba da har zan dauko wata yar aikican in aje wurina.
Daga yau na hana kowa saka wanan yarinyar aiki ko taba lafiyan jikinta wallahi wallahi ko yaya nake da mutum a gidan nan ranan zai hadu da fushina.
Wanan yazama na farko na karshe a gidan nan da wani zai kara taba lafiyan wani zainab yace kamar kowan ku nan dan haka a bani guri ban son wani magana kuma daga yau.
Tana fadin haka ta mike zuwa dakin ta a fusace yayin da nake durkushe a gefe kujera tafiyan mami Nuriya ta mike tana fadin wallahi mu zuba da kowa a gidan nan kan wanan yar iskan kowa ya tabani tabashi zanyi.
Binta da kallo sukayi kafin su dawo da kallon su gareni inda nake rakube ina hawaye don tashin hankali dana gani ranan.
Da hannu ya nuna min hanya na mike simi simi na basu wuri yaya mamud ne ya kawar da shirun da fadin.
Ni Nuriya zata watsawa kasa a ido haka kwata kwata banji dadin zaman mu da ita kullun a cikin fitina muke.
Yau ma nasan haushi fadan da nayi mata na gyaran wuri ne ta sauke akan yar mutane haka.
Bai bari dan uwan ya gama zancen shi ba ya mike zuwa dakin mahaifiyar su data shige ranta a bace ya sameta dakin.
Shiko yaya mamud yaci gaba da fada da matar shi ranshi a bace yake fadin.
Ya mike yana fadin nasan maganin yar iska ai bazata zan mata a gidan nan sai ta gane bata da wayau.
Saidaya shige jalal ke fadin kamar da gaske din zai iya hakan yanzu kila hakkuri zaije ya bata.
Suma mikewa sukayi zuwa dakin mahaifiyar tasu suka samesu a nan suna wani hira da dan lelen nata a gurin.
Karfe biyar na bar dakina zuwa na mami don gyarawa ita kadai na samu a dakin da sallama na shigo dakin na duka har kasa ina gaida ita kafin in dago don fara aikin dakin.
Kinsha maganin dana aika akai maki dazun take tambayana nasha mami na fada ina wasa da yan yatsun hannuna a hankali.
Kamar zata sake magana sai kuma tayi shiru taci gaba da duban takardan dake hannun ta ko ina na dakin saidana gyara kafin in fito dakin kusa magariba yayi nan na samu matar da aka dauka don shara tazo ta fara aikin ta .
Don faruwan avi mami tasa a kawo mata yar aiki wanan mai sharan bahaushiyace ita don ina gaida ita take amsawa naji hausanta na gane ita din bahauace ba kamar matan nan biyu gwarawa masu girki bane.
Tun ranan shakuwa ya shiga tsakanin mu da matar da ake kira da hannatu yar ktsinawa irin matan nan ne da suka dade da fitowa bariki don har sigari take sha a boye.
Nima dai rabon in gan tane a cikinyanayin yasa na rutsa da ita can bayan daki ta labe tana shan abinta na juya da sauri zan koma naji tana fadin a cikin kokarin kashe tabar da sauri yar hjy kamar yadda take kirana dashi.
Ina nan ina wanan jarabar tsiyar da muka sawa kanmu ina dai ba zaki fadawa kowa ba halin da kika sameni wanan zancen.
Da sauri na girgiza kai tare da fadin indai nice babu maijin wanan a abakina insha Allahu ina kokatin wucewa don natsani warin taba a rayuwana.
Duk dan dakata min inzo har lokaci bata yarda dani don ta fahinci jikina yana rawa a lokacin.
Ina kallo ta ballo goro daga haban zanin ta tura baki tana taunawa ta kakabe zanin inda ta zauna a kasa tana fadin wanan abin ya zama muna jaraba a rayuwa.
Kinsan a zamani mu idan budurwa takai budurwa har bata shan sigari to bata cika wayayyan mace ba ke nan.
Tun wanan lokacin mula koyi wanan cacan kashi kudin don ko nairan ka ta karshe ke nan sai ka fitar kaya zakaji dadi.
Ni dai a kage nake na bar wurin nake fadin dama ban ganki bane a cikin gida sai nayi tunanen ko kina nan shine na biyo ki.
Yo ai ina nan kedai jarabarce ta motso min shine nazo indan rage zafi kai.
A tare muka jera zuwa cikin gidan idon ta mirsisi kamar bata sha komai ba taci gaba da sha,aninta
Cikin sati daya kawai mun saba da hanne wace na lakawa mama hanne nake kiranta da hakan don girmamawa .
Zama da mama hanne yasani cikin farin ciki da walwala sosai don zata zauna tayi hira dani kamar sa, anta nake gun ban iya bata amsa har yakai yazu ina bata zamu zauna tana ban labari ina kwasan dariya.
Da sunan kwana hudu sai gashi mun share wata a abuja lokacin ne mami ta fara shirin ziyaran kaduna.
Wanda gaba dayan mune zamu tafi gidan a yadda naji suna fada mahaifiyar mami ce bata da lafiya shine za a tafi gaida ita.
Shiri sosai mami keyi don zuwa gida nikan nafi kowa murnan hakan kamar ance damun isa zan tafi ancau ne ranan.
Ni kan na dauka yaya Jafar ya koma inda ya fito ne ashe wai tafiya sukayi tare da su jamal sai kwatsam gasu sun dawo ana saura kwana daya mu tafi kaduna.
Mama hanne kan tunda tayi arba dashi tasha jinin jikin ta a zaton ta wai yanayin sa yai kama dana yasanda tunma dataga security din shi ta kara tsurewa da al,amadin shi.
Take tambayana nake fada mata dan mami ne amma ni ban san aiki da yakeyi ba, ta sake fadan mutum.haka ba yar dariyan nan ko fara,a a fuskanshi.
Dariya sosai nayi har ina dukawa a inda nake zaune sai kamshin turaren shi mukaji lokaci guda.
Key din shi yake miko min ba tare da yayi magana ba, amma na gane me yake nufi dakin shi yake so a gyara mai ke nan.
Yana miko min ya juya ya futa a cikin wani irin tako na mazan zamani da suka suka san ta kan duniya sosai yake tafiyan.
Ban tsaya jiran komai ba na mike don cika umurni duk da mami ta hana inyiwa kowa wani aiki ita da kanta takan umurceni da inje in gyara mai dakin nasa.
Tura kofan nayi na shiga dakin da sallama duk da nasan ba kowa a daKin hakan bai hanani inyi sallama ba.
Idonane ya fara arba da wani kwalba dake aje saman table din dakin nasa ga abin cikin sa an zuba a kofi ansha an aje rabi.
Da mamaki nake kallon abin don ban taba ganin kwalban abin sha irin sa ba nidai na fara kawar da takardun dana gani a saman wani table naji an turo kofa da karfi an shigo dakin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH KA GAFARATA MUNA ZUNUBBAN KABA MU IKON AIKATA ALHERI A RAYUWAN MU DUNIYA DA LAHIRA AMIN.
DO MIN SAMUN LITTAFIN NAN CIKKAKE ZAKI IYA TURA DARI UKU TA WANAN ACC 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN NA DARI UKU KACAL NAGODE UBANGIJI YA HORE YA BADA IKON BIYA ALLAHUMA AMIN ALLAH, , , ,
Idona a kan abin ina dan juyawa a cikin kofi naji wanan tsawan daya daka min sai da hanjin cikina ya kada don tsoro lokaci guda.
Allah ya gyara ban sale cup din ba ya shigo ya karbi abinsa yana mai bina da wani kallo mai kamar na tsana.
Wayace ki taba min wanan ya fada rai bace kamar da gangan na taba mashi abin bashi ya turoni dakin in gyara ba.
Dan marairaicewa nayi ya karbi abin shi zuwa daki sai gashi ya fito da cup din ban san inda ya juye abin ba.
Fita yayi daga dakin ba tare da yayi min magana ba hakan ya bani daman yin aikin a tsanake.
A gurguje na gyara komai duk da hakan dakin ya gyaru da kyau na kulle masa na fito na kai key din dakin mami.
Nikan don doki har na shirya kayana tafiya kawai nake jira washe gari na zata tun safe zamu wuce sai naga sabanin hakan.
Saida yamma bayan la,asar muka bargidan zuwa filin jirgin ashe da jirgi zamuyi tafiyan kuma.
Karfe shidda na yamma duk muna gida a lokacin har na bude dakin mami ina gyara don tun tafiyan ta dakin a rufe yake.
Sai yau da muka dawone ta miko min key na bude duk da a gyare muka barshi da zamu tafi hakan bai hana yadan yi kuraba.
Na gyara har bathroom na fito zuwa dakina shima na gyaro na shiga wanka dongon riga silk mai adon kamfala ne na dauko daga cikin kayab da anty Aisha ta bani na saka.
Saida nayi sallah har isha,i na fito falon don yunwa da nake ji lokacin in samu abinda zanci a cikina.
Suma mutanen gidan gaba daya a falo na same su saman dining suna cin abinci mami da yaranta maza su hudu sai yan matan mami din gaba dayan su har anty Aisha.
Simi simi na fito na zo diban abincin wasun su suka kuro min ido hannuna rawa na dibi abincin ina jin mami tana waya tana fadin muna kaduna yanzun haka.
Insha Allahu da safe zamu shigo Igabin naji tana fadi haka yasa na san zasuyi tafiya washe gari saidai ban san ko dani bane.
Diban abincin na juya zan wuce naji muryan yaya Jafar na fadin ke saida hanjin cikina ya kada don jin muryan shi saidai ban tabbatar ba ko dani yake don kaina na duke na basu baya.
Na kara takawa gabana na mumunan faduwa da ban san dalilin haka ba duk lokacin danaji muryan yaya jafar din duk da ina tsron kowa a gidan saidai nashi yafi yawa a zuciyana.
Ko dan ganin kowa ma yana shakarshi ne a gidan don tsare gida irin nasa .
Haka naci gaba da takawa cikin karfin halin zan tafi dakina inda na saba zama inci abinci hankali kwance zuciyana cike da addua nake tafiya.
Ya sake fadin come and join us ina zaki da abinci ga kowa nan a zaune hakan yasa nasan lalai dani yake magana na juyo a hankali.
Yana rike da cibin abinci da yake ci a hannun shi ya rike baikai a baki ba gabana na faduwa yace.
Daga yau a nan zaki rika cin abinci tare da kowa kinji abindana fada maki yana nuna min kujera da hannun shi .
Kai na gyada mai, tare da nufar gurin kujeran dake saiti da inda yake zaune babu kowa saman kujeran na zauna.
Idanuwan yan matan gidan duk a kaina bama su kadai ba har mami dake waya a lokacin idonta yana kaina.
Ko ban daga kaiba nasan akwai idon dake kallona a lokacin don jikina ya bani hakan ba ido daya ba ba biyu ba kodana dago kai duk idanuwan su na a kaina suna kai cibin abinci a bakin su.
Tundana zauna ya maida hankali gun abincin dake gaban shi hankali kwance yake kai cibi a bakin shi a hankali .
Daga mami har ya matan dama su jamal suka dago ido a sukwane suna kallon shi shiko ko a jikin shi.
Sai juya cibin dake hannuna nakeyi na kasa sakin jiki inci abincin yadda ya kamata a wurin.
Yadda kika san guba haka nake hadiyan abincin ba wai don baya da dadi ba don hadine na musanman akayi don zuwan su yau din su mama kande suka girka abincin mai rai da lafiya.
Mikewa yayi tsam mami tace har ka gama cin abincin ke nan ko rabin plate fa baka ci ba ba tare daya juyo ba yace mami iam ok zanje na kwantane.
Allah tashe mu lafiya mami tace yace amin yana tafiya sai jalal yace but yaya security dinka za a fada masu sutafi ke nan tunda ka shige ko ?
Na sallamesu tunda muka fito massalaci dazun idan sun gama zasu tafi ya bashi amsa yana tafiya da dan sauri kamar mai uzuri.
Mami ma bata dade ba wurin ta mike tabar falon sai mazan da suma suka mike lokaci daya falin ya rage mu kaida a ciki.
Duk lokacin danayi yunkurin dago ido sai in samu ana aika min da wani irin mugun kallo da tsana dan dama salma da Aisha su ba kallon tsana bane saidai kallone mai kama dana mamaki lokacin.
Amma dai yarinyar nan kina da sa, a yau kece yaya hero ke ba umurnin zama a saman table kici abinci tare da kowa a gidan nan.
Ke ko ba dole ba tunda ta iya makirci kamar ta mutu ta mairaraice ita gata Allah ba dole ta bashi tausayi ba Nazira ta fada
To kodai kin zauna a cikin mu ba a dai taba canza maki suna daga zainab yar aikin mami zuwa diyar gidan nan kamar kowa Rufaida a fada .
A, a, za a yi kiranta ki da yar gida mana duba yarda yan kwanakin nan gaba daya tayi fresh da ita haka duk sai suka kalloni lokaci daya.
Nagaji da cin fuska na mike don barin wurin, dama abincin ya fita min rai lokaci daya na dauki plate din zuwa kitchen.
Ina ruwan ba saban ba yau har wanan ce zata bar abinci haka bataci don samun wuri.
Ban kara fitowa dakin ba don na gamawa mami komai itama nasan ta gaji ta kwanta tunda akwai tafiya garesu washegari.
Nasan da zancen tafiyan mami don naji tana waya kan tafiyan yasa na tashi da wuri na nufi dakin ta koda abinda zata sakani a lokacin.
Aikuwa iba shiga dakin na samu ta fito daga wanka saida nayi mamakin hakan don bata ko tsaya jira inzo in wanke bandakin ba ta shiga.
Gaisheta nayi na nufi bandakin har ta karasa shirinta na dawo na fara gyara don ko kadan ban kawo dani za a tafi tafiyan ba don banga alaman hakan ba.
Hankali kwance nake aikina ina shiryawa maki kaya kamar yadda ta umurceni inyi mata anty Aisha ta shigo dakin tana gaida mahaifiyar nasu.
Bayan dun gaisa mami ke fadin ina fatan kin shirya dai don banson bata lokaci ga tafiya kin sani dai.
Mami wani shiri zanyi kauyefa zamu tafi banga abinda zan shirya bani ko haka zan iya tafiya ai ta fada cikin zolaya.
Mami tace da ita ai kauye garine don akawai yan Adam a ciki na dauka dai daji zaki tafi ai ta kwashe da dariya don tasan ta tabo mami din .
Gaba dayan mu zamu tafine mami ta tambaya tana kallon mahaiyar nata lokacin da ni kuma nake masu dan murshi don jin amsan da mami din ta bata.
Naji mami tace eh dake da yan uwanki maza ba na fadawa kowa tunjiya don kada yau su kawo min wani zance na daban.
Hae su Nazima ta sake tambayan mahaifiyar nata sai mami din tace haba dai Aisha ai ba zan sake zuwa dasu ba tunda da biyu suke zuwa
Tun wancan zuwan da sukai min tsiya nasha alwashin ba zasu sake zuwa garin nan da yawuna ba.
Mami samu,naka ne fa ba wani gari ba can Aisha ki fice mun a ido tun raki bai kai ga baci ba a dakin nan.
Zainab jeki ki shirya kada ku bata min lokaci ta juyo inda nake tana fadi hakan yasa na gunde dariyan da nake masu jin an abamci sunana ga tafiyan nasu da za,ayi wanda ni banso hakan ba don sati biyu da komawan school ke nan mu.
Dole na mike ba yadda na iya na koma dakina na fara dan shiryawa yan kayana kala uku a dan karakin jakkar da Aisha taban da zamu tafi kaduna.
Karfe goma safe mun karya sai kaya ake ta fita dashi ana sakawa a mota yan matan sunso subita amma mami tace ba zata dasu ba tunda suna raina mata gari idan sunje.
Ga motocin da za ai tafiyan dasu sai wani sheki suke ga hasken ranan daya fara gama gari suna daukan ido a ranan.
Suna falo zaune na fito da kayan mami zuwa wurin mota kamar yarda ta umurceni indauko zuwa bakin mota jamal yana gurin zai nuna min inda za,a saka jakkar kayan nata.
Wanan wau da ita za,a tafi halan Nazifa ta fada sai Rufaida take fadin kema ai kin sani itace yar miko min kawo min dole a tafi da banza.
Maganan yai min zafi sosai saida ai aikina ne din hakan don sun fadi hakan bakomai bane gareni tunda kowa yasan abinda ya kawo ni gidan ai shine aikatau.
Mota guda muka shiga nida mami da Anty Aisha sai driver nice a gaba zaune tare da driver suna baya a zaune su.
Tun kan a baro gida banyi magana da kowa ba har mukai nisa ga tafiya naji Aisha tana fadin waiko mami lafiya yarki take ?
Kodai abinda su Rufaida suka fadane ya bata maki rai kikai shiru tun dazun ?
Mami tace ai kinsan ita din ba gwana bace wurin surutu barta da saurin aiki kan kamar inji mema suka fada matane daya bata mata rai haka ?
No ba wani abu bane serious maganan su necan suke fadin wai ita dni ai dole aje da ita don yimin miko min .
Kai wa yan nan yaran akwai tsegumi garesu bari Allah ya dawo damu lafiya sai na masu tsiya dai a kan yarinyar nan .
Don banga abinda ta tare masu a gidan nan ba da suke matsa mata haka ko da yaushe.
A raina nace kayya mami kullun haka dai kike fada kin kasa yin maganin su haryau su kuma basu barni ba da fitinan su.
Wai mami yaya Jafar din ya yarda zai tafi gidan kawar taki ya duba yarinyar Aisha ta fada don a kawar da zancen .
Don tsuki mami tayi tana dauko abu a cikin jakarta tana fadin ai kin san hali shi dai.
Danayi mai magana dariya kawai yayi min ya mayar dani karamar yarinya sai na masa da gaske zai maida hankali wurin abinda nake son shi dashi ai.
Mami da kin barshi ya zaba da kanshi nima ban goyi bayan wanan auren hadin ba kindai ga yadda na yaya mamud ya zama a karshe ai.
Ni dai ina gaban mota ina faman tunane a raina har muka kai garin samu,naka din sai bin garin nake da kallon irin ni,imomin da Allah yai masu a garin.
Wani gida motan mu ya tsaya duk da anyi gyaran gidan daga wajen shi amma mutum zai iya gane tshon ginane na mutanen da masu shi a lokacin akaiwa gyara.
Tundai in ka shiga daga cikin gidan zaka samu part part gidane babba da ya kumshi jama, a masu yawa sosai a cikin sa.
Sai tafiya muke ana faman yi muna sannu da zuwa har muka kai kofan wani part daya sha gyara sosai an masa irin ginan zamanin nan .
Wasu mata biyu ne suka fito daga part din suna faman yi muna sannu da zuwa dukkan su na shedasu don sunje abuja na san su a lokacin.
Da sallama muka shiga falin babba wanda yasha gyara da kujeru manya manya na zamani komai dai na bukata a kwashi a falon.
Sai hoton wata dattijuwa dana gani tayi gwagoron irin daukan da akaiwa photon sai kuma photon mami da mijin ta duk da bantaba gani wanan photo ba amma na san fuskan marigayin mijin nata don akwai photunan manya a falin mami har gidan su na Abuja a saka a falon gidan.
Mami bata zauna falon ba ta shiga daga cikin dakunan a ca nake jiyo muryan ta ni da Anty Aisha ne a falon zaune muka gaisa da sisters din mami din suna tambayan mu yaya hanya ?
Can murya mami ke fadin ina kuke ne ku shigo ga hjyn a daki zaune kuzo ku gaisa kafin wa yancan su shigo.
Mikewa mukayi zuwa dakin wata tshuwace a zaune saman gadon alfarama kamar ba dakin tsofi ba duk da tsohuwace matar hakan bai hanata kwaliya ba tana cikin atamfar supar a jikin ta.
Aisha kan muna shiga gadon da take zaune ta haye tana fadin wanan ce mara lafiyan da mami ta tayar muna da hankali ga mutum na gani garau haka ba alaman ciwo.
Tsohuwa mai barkwanci tana fadin ke kuma wanan shiga haka kamar matar limami chochi fa ?
Duke nayiwa shi dan Allah dai udan zaki tafine ki tafi kiba mutane wuri kina dagawa iyayyen mu hankali haka.
Daga inda nake zaune kafin taba Aisha amsa nace ina wuni mama sai ta mayar da hankalin ta a gurina tana fafin kedai yar albarka kunzo lafiya ?
Yaya hanya ya kuka barsu a can nace lafiya yaya jikin mama Allah sa kafara ne ?
Da alama taji dadin yadda muke gaisawa da ita din sai wasan baki take tana fadin amin yar albarka.
Niko ko yar taki da ake fadi kin samu ke nan yarinya haka mai hankali Allah yasa ku raka tare.
To mu da ba, awa addu,an a hana mu raka din kaji min tsohuwa daga ma kin samu anzo gaidake har da zaben yiwa mutane addu,a.
Muryan yaya mamud ke fadin ni ina matar take gani nazo kada ki tafi muna son ki a hakan ko dan kwanciyan hankalun uwayen mu.
Kaji ja,iri kice dasu kike tafe ashe yau ina da babban bako a garin nan mamuda yaushe ranon ka da garin nan tana kokarin mikewa tsaye da kyar.
Aisha ta mayar da ita ta zauna mami takai mata duka tana fadin Aisha yo ga tsiya karki balla muna tsohuwa garin shashancin ki.
Barta ai gani take kamar ta fini kwari a hankan yanzu sai in lankada maki dukan tsiya a wurin nan.
Duk aka sa dariya sai ga daya sister din mami ta shigo tana fadin hjy yau fa kinyi baki harda Jafar akazo gaida ke.
Mami tace har kwana kuwa zasuyi maki a nan sai ki shirya ke nan kedasu yau a gidan nan.
Tana tafin dadi da murna ta samu ta mike da kyar tana lale marhabi da manyan bakina yau kuce amarya nake sai na zaba ashe tana fita daga uwar dakin nata din zuwa wurin su ta taresu.
Zeey jeki dauko mi kayana ki shigo dashi dskin nan mami ta fada na mike saida tsohuwar ta gama fita na dan bi gefen ta na fito daga dakin.
Suna zaune dukkan su tana masu lale marhabin cikin jin dadi har na fito kayan da mukazo dashine aketa faman shigowa dashi gidan.
Jakkar mami dana Anty Aisha na dauko na shiga dashi daga cikin daki kafin i koma in dauko nawa sai kuma na rasa yadda zanyi da jakkar nawa.
Na dan tsaya daga kofa ni ban shiga ba sai da dayan sister din mami takece min dan Allah shiga da ruwan nan mikawa su anty in gama da wayan nan.
A lokacin na samu komawa dakin na samu mami ta kewaya ban daki Aisha kuma tana rashe rashe saman gadin tsohuwar tana waya.
Ruwan na aje masu kafin in dan samu sakon gado na aje dan jekar kayana a wurin na juyo ina fadin anty Aisha ga ruwan .
Da hannu tayi min alaman a, a na dai samu wuri na tsugunna duk da kishin ruwan da nakeji ban yarda nasha ba tun kan mami ta fito tasha.
Ta fito tana fadin an shigo da kayan nan duka zeey don miyan nan kada a zubar dashi don Allah fadawa Ramatu ta kawar dashi kada a zubar.
Don miyane mai yawa na zabbi dana kan saniya banda nama da mami ta saka a soya a zuba a babban ruba mai marfi kuma.
Na mike da sauri duk da ban san wacece Ramatun ba a cikkn su sai dai nayi sa, a suna falon dukkan su nake fadin mama Ramatu mami tace akwai miya a waje akawar dashi kada a zubar.
Ke wanan muryan wa zaisan kina magana a hanka yaya jalal ke fadi yana nunawa mama ramatun ni a lokacin.
Na sake maimaita abindana fada da farko tana fadin aikuwa gara da aka fada muna bari yanzu a kawar dashi gurin.
Umma ina key din dayan dakin yake akai kayan a ciki tana tambayan tsohuwar data mayar da hankalinta kan diyan mami da suka sakata tsakiya da hira.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GAREKU MASOYANA UBANGIJI YABA WUNI LAFIYA YA SADAMU DA RAHAMIMIN SA AMIN YA ALLAHU.
KI BIYA HAKKIN MU KI KARANTA A CIKIN SALAM DA SAKEWA DARI UKUNE KACAL 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA NA DARI UKU.
Ranan naga yadda ake nunawa jika so da kauna na gaskiya don tsohuwar kamar ta hade yaran su koma cikinta take ji basu kadai ba harni da nake bakuwa a cikin su bata nuna min bambancin hakan ba.
Ga tawa kakar saboda wani dalilu nata na daban ta turoni bitnin yin aikatau badon Allah ya hadani da uwar daki ta Allah ba.
Allah kadai yasan yadda rayuwata zata kasance a birni ba tare data damu da hakan ba ita nata butin dai shine ta samu kudi ta gareni kawai.
Basu bar dakin ba nan kowa ke zuwa taron su suna gaisawa su yaya jamal ne suka mike don zaga gari zama wuri daya ya ishesu.
Yaya mamud ya dade da fita daga dakin ya barsu yana fadin zai leka wani abokin shi ko yana nan suka bar yaya jafar dake faman aiki a cikin sytem din shi yamai da hankalin gaba daya ga abinda yakeyi din.
Ina zaune takure wuri daya na kurawa tv dake aiki ido ana wani shiri a kscm kaduna hakab yasa hankalina ya dauku ga kallon.
Ai bata jikaba tshohuwar ke fadi me take da suna tana murmushi take kallona nayi firgigit in dago kai sai naga ido shi a kaina.
Bakiji me na fadaba yake tambayaba kai na girgiza mai ina tasowa daga inda nake ki dauke kayan nan da suka bari a nan ya kara fada.
Sai lokacin nasan meya fada da farko na tashi da sauri na fara tattara kayan dake saman karamin table din.
Waini kan dan gidan iyami yaushene zaka kawo muna sarakuwa tshohuwar ta fada tana kallon shi.
Cikin basarwa da kalan maganan shi ba tare da ya dago kaiba yake fadin banga matar aure ba har yanzu.
Allah na tuba duk matan daka baro kaduna har Abuja bakaga mata a cikin su ba don tsaban ruwan ido idan an fada uwarka ta tare maka.
Ni yanzu nafi dason yaro yayi auren shi a cikin lokacin don wanan rayuwan baida tabbas dan rayuwan yanzu kadan ne.
Ba sai ki nema min ba tunda ke kinga matan a ko ina birjit yo ko cikin yan uwanka ka nema mana ko wanan yar ta uwarku ai irice ta kwarai gata da hankali har naji dama ace ta shigo cikin zuria na.
Ke kiji da kanki don Allah da wanan shirme da kikeyi an fada maki kowa irin kune halan ya fada yana zareww tshohuwar ido.
Ta sake dariya tana fadin kaji min dan kawai ido ma zaka zare min don kawai na fadi gaskiya ko sai mun kaika mararaba mun ma wankane kafin a soka.
Kinga idan kina matsa min da wanan magana idan na tashi na tafi ke nan ba zan dawowa ba ya fada kanshi duke.
Nasan zaka iya dan nema mai zubin jan fata kai dama Allah yaga abinda ya gani ya kaika can cikin su da zama.
Wanan karo kan tare dake zamu koma ai don naga kema dasu kikafi kama ai barni na mutu musulma tsohuwar ta fada.
Saiga mami ta shigo falin tana fadin hjy dake dawa kike magana sai ta ganshi a zaune take fadin a a aboki kai kana ciki ashe na dauka tare kuka fita ai.
Ina nan mami idan wanan tsohuwar bata daina damuwana ba zan bar garin nan yanzu ba sai anjima ba.
Zaka iya na sani damuwar dai nasan fadan so kankane takema da baka son ai maka ko ?
Kamar kin sani yar albarka daga zancen aure yake wanan halakon haka kamar an mashi maganar mutuwa shi.
Wai shi baiga mata ba duk garin nan nakece mai ga wannan yar taki tun ba a kai ko ina ba don ni na yaba da halaiyar wanan yar taki.
Da sauri mami ta juya inda nake ina daukan gorunan drinks a kasa take fadin haba dai hjy har abin nasa yakai haka kuma ?
Ai ba zan barshi ya tafi ba sai ya tsayar da matar da zai aura in yaso sai ya koma idan bukin ya karaso ya dawo ayi buki nima zaman shi haka a can shi kadai ya dameni yanzu.
Kaji maganar gaskiya don wanan da kike gani idan bakiyi da gaske ba baida niyar aure yanzu gashi ya fara zama magidanci.
Wani kallo yaiwa tshohuwar tare da mikewa lokaci daya sai kuma naji ta koma rarashin shi tana fadin ai kasan bama haka dakai.
Kada kasa mamuda yai muna dariya tun ba,aje ko ina ba yanzun fa na gama mashi tsiya a kanka yai fushi ya fita don nace kai nake so.
Yanzu ma zan fada mai ya dawo nabar masa ke ya dauka bana so ni don kin faye jininini da yawa yanzu.
Dawo dawo ka zauna na bar wanan jininin indai a kankane na isheka ni kadai ai dama ai baikai ciki ba zancen nawa ina ka taba ganin mutum ya dabawa cikin sa wuka ?
Komawa yayi ya zauna sai abin ya bani dariya har bansan lokacin da sautin dariyan ya fito min fili ba.
A, a a takwarana dariya kike min kuma don ina neman shiri da maigida a gaban ki ?
Hararana yayi yasa na bar falon na koma daga wajen dakin na zauna saman dan dakalin dake wajen ina kallon mutanen gidan dake gittaya tako ina.
Sai da ta fito da niyar zuwa sallah mami ta biyo shi suna magana dashi mami ke fadin zeey a nan kuma kika zauna ne ?
Na juyo ina dan gaida ita take fadin shiga mana ciki koda yake ma anyi sallah azahar yanzu sai ki shiga wancan dakin dake gefe akwai bandaki a cikin sa a gyare dakin yake ku zauna keda Aisha.
Jin haka yasa na mike ina kokarin shiga dakin don kallon da yai min mai kama dana warning a lokacin.
Dakin da mami tayi min kwatance na shiga dakine gyarare da katon gado hade da mirrow din shi sai kujera three seater dake dakin gadon yasha gyara dakin yana ta kakahin turaren wuta.
Ban dakin na nufa na samu ruwa a manyan robobi aje dashi nayi amfani na dauro alwala nafito na tayar da sallah saman salyan dake dakin.
Ko dana idar ban zauna ba falon na fito na gyarashi tsab har waje duk suna cikin daki basu sani ba sai da mama habiba tazo fitane ta ganni take fadin yar nan kina nan kina aiki baki huta ba.
Hjyn su mami ke tambaya wace yace kuma sai kuma ta tuna dani take fadin au yar iyami ko ?
Wani aiki take kuma yarnan ki huta hakana mana ina hankalce da ke baki da son kazanta ta juya inda mami take kwance tana fadin.
Kin samu ya sai ki rike tada amana don Allah yarinyar tana da shiga rai lokaci guda gata da ladabi.
Sai naji ina kwadayin hada iri da ita don irice mai amfani ita din ba abin yarwa bane haka.
Hjy nima yarinyar ta kwanta min a rai sosai ina kulla da ita tankar yar cikina don bata da kyashi ga sanin ya kamata kamar wata babba can.
Tarbiyane idan kinga haka ta samu tun daga gida uwarta ta tarbiyartar da abinda yadda akeson ko wani da ya kasance sai ki kara himma wurin riko Allah ya taya ki rikasu.
Don tafi min wa yan nan marasa moriyan sau dubu a wurina sai hjyn tasu tace tafisu kan gaskiya yaron da ba sai kace ya tashi yayi ba yake abu ai yana da dadin zama.
Hjy kin san wancan zuwan da nayi da yaran nan iskancin da sukai min saida muka koma gida nake ji nayi masu tas wallahi.
Kiyi hakkuri dasu tunda su suka kawo kansu gare ki inma sunyi maki don kansu kowa ma zai girbi tsiyar shi ai.
Ke dai ki rike wanan bisa ga amana da yarda idan dai bata kauce bane don mutum mugun icce ne sai yaga ya ginu yace kaine makiyin sa daga baya Allah ya kare mami ta amsa da amin.
Sai dare mazan suka sake shigowa ina daki naji hayaniyan su ban daga daga inda nake zaune ba naji muryan mami ta fito daga uwar daka tana fadin.
Garin yai maku dadi ke nan ko kun shige cikin gari tun dazun ina shi aboki yake ne banganshi tare daku ba.
Wanan friend naki saike mami yana masallaci mun barshi wai yanzu yake son sallam guards din shi su koma kaduna su kwana.
Da daren nan tau haka dai yace don wai baiga inda zakaisu ba nan suwa ke nan tsohuwar ta tambaya.
Security din da mijin ki ke tafiya dashi don tsaro yaya jamal ya bata amsa a takaice take fadin.
Ikon Allah tafiyan ma sai anyi shi da masu tsaro ko may sai yaya mamud yace kin san su can hakan ai wani abu ne tundaga can aka hadu shi dasu aikin su sukeyi su.
Duniya inda ranka kasha kallo yanzu shi wanan dan figegen aron ne harda wasu masu tsaron shi.
Hjy mu a nanne ba a dauki tsaro da mahinmanci ba amma su can idan har kai wani abune dole kana da masu binka a baya ai massanman shi da sukeji da shi a can.
Waini na kasa gane aikin yaton nan sai jalal yace bako zaki gane ba don shi bros telent ne sosai ilimin shi yaja masa hakan.
Yanzu zai iya kera maki wani abu a wurin nan wanda sai kinyi mamaki don har abin yai tafiya da kafansa su ake kira da sciencetics mana masu fasahan kwakwalwa ikon Allah tace.
Tare da fadin gaskiya yaki aure haka har yana batun rufe arbain fa don in ba zan manta ba tun mulkin shagari na farko aka haifeshi ai.
Kai hjy wanan tashin tasgin haka kan friend dina yanzun dai ni abinda nake so kafin ya tura mutanen nan a cikin daren nan ai masu kokarin wurin kwana hjy.
Tshohuwar ta tambaya su nawane akace hudu hudu ta fada da mamaki tana fadin har karte hudu ke yawo dashi wanan abindai da nake gani.
Ikon Allah yafi gaban mamaki yau ace wai dannan ne Allah yaiwa bawa haka Allah ya ciyar daku baki daya suka amsa da amin.
A daidai lokacin da dan bawan ke shigowa yana waya tsohuwar ke fadin gama yanan ya shigo dayani.
Kai yanzu don baka da tausayi zaka tura yaran mutane da daren nan su koma kaduna don rashin imani.
O lord wanan kuma wani zance take hakane da shigowan mutum ya fada yana kaiwa zaune yana aje wayan da yakeyi.
Aboki wai yanzu da daren nan zaka tura security din nan su koma kaduna sai naga dare yayi ai.
No sun fasa ai mami uncle bello ya sama masu wuri zama da zasu zauna suna can sun tafi suga wurin kafin su dawo su dauki abinci.
Ko kaifa nace ko kai fa dan nan amma ka tura bayin Allah a cikin daren nan haka ai abin baiyi ba kamar dai ba mutane a nan.
Enough dan Allah waiwa ya fadawa wanan mai wa,azin ta damu mutane da wa,azin nan nata a gurin nan.
Kai rufamin baki aini yanzu nasan ba cikkaken namiji kake ba don a matsoraci nake kallon ka yanzu tunda sai an rakoka har karkaran mu matsoraci.
Daidai lokacin nake fitowa daga dakin don kira da mami tayi na amsa daga ciki.
Dariya ya bushe dashi bashi kadai ba duk wanda ke falon saida maganan ya bashi dariya yadda suke kwasa dashi din.
Barin gani idan baki tsorona din da gaske ya fada yana mikewa ya harota ta juya tana neman abinda zata kare kanta kafin ya iso gareta .
Tayi sa,a filo na kusa da ita ta dauka wai dashi zata kare kanta din tana kaimai duka yana dariya ya juyo a daidai lokacin na kawo wurin zan wuce sai ji nayi kumus nayi baya tangal tangal zan fadi.
Mami tace zaka karya min da da wanan karfin naka haka kamar na doki shi kuma ya juyo yana fadin oh sorry .
Tsohuwar nan kinga zaki saka in karyawa mami yarta don fitinan ki to yaushe rabo damuyi fitinan haka.
Ai rabu a gana arzikine dan nan wata ran idan kunzo sai kun tunani da wanan wasan da mukeyi yau ina Alh ina mahaifin ku sun kare.
Kowa yai wani iri a dakin don abinda tsohuwar ta fada wallahi hjy gashi yau muna kewan tsohon nan don da zaran zan shigo naga part din shi sai in tuna da lokacin da muke zuwa yana bamu mazzakwala muna sha yaya mamud ke fadi.
Kai mukan bamu sanshi ba gaskiya sai dai a photo jalal ya fada ai old man din nan ya kware mu daya tafi bamu sanshi ba.
Waike zeey kin debi abincin nan kuwa na juyo ina fadin ban diba ba mami yanzu na idar da sallah dama.
Jeki ki dibi abinci da wanan halin naki ga abincin mu can ankai mana daki tun dazu wanan nasu sai na mutane yayan ku yacan sai a samu yaro yakai masu idan sun dawo.
Juyawa nayi zan koma dakin don ban iya sake jiki suna wurin don haka na juya don na koma dakin hjyn su mami.
Banji me yake fada ba yaya jamal yace ke wai kizo ki zuba mai abinci yar mami.
Jin an ambaci sunana yasa na tsaya tare da juyowa na dawo zuwa inda abincin yake aje dan kallon yaya jamal nayi ina fadin wa zan zubawa.
Yaya jackson ya fada hankalin shi naga wayan shi rasa abinda zan zuba mai nayi don kuloli ne gurin zasu kai biyar duk an cikasu da abincin alfarma har da fate da mami tace tana so yaji gyada a cikin sa.
Fara bude masu kulan abincin nayi don ya zabi abinda ranshi ke so sai dai baya kallona hankalin shi naga waya yana rubutu.
Yaya me zan zubama na tambaye shi ina dan gurfane a gaban shi don ba dining table falon tsohuwar kamar can gida kaduna.
Ya dan dago kai yana fadin anything zaki iya zuba min Aisha ta fito daga dakin yaya mamud daya karbi plate din da mami ke shan fate yana dan sha yake fadin Essha kina gidan nan ashe tun zuwan mu ban ganki ba.
Ina kwance ne yaya ta fada tare da ratsowa ta zauna a hannun kujera tsakiyan su shi da yaya Jafar din.
Ke may kike a wurin nan ne haka ta tambayeni ya Jalal yace wai abinci akace ta zuba take tunane na dan kalleta ina fadi a hankali ban san may zan zubabane ai.
Oh shine kike tsaye a gurin ya mamud yace ka duba ai tana da gaskiyar ta kada ta zubama abinda baka so ne.
Wanan dai ina so inga matar shi kafin in mutu yaro da izza da isa kamar wani basarake dashi matar ka tana da hakkurin zama dakai haka.
Hjy naga fa yau sai yar tsama kuke da yaya Jackson tunda muka zo Jalal ya fada don shi yafi yawan dan magana bisaga Jamal dake da zubin yanayi ya jafar din wasu halaiyan su suna da kama sosai.
Aure nake son yayi hakana ya baku wuri kuma ku samu ku zaburo wanan gwauron ya tare maku wuri.
Muka fada maki samarin suka fada tace to ai shike nan tunda baku son a matsa mai yayi aure.
Wanan fa zata iya hada ma abincin nan duka tunda kace anything zata dauka kace tayima mix ne gaba daya Aisha ta fada tana kallona.
Ke zuba min ki daga min nan don Allah ya fada tare dan dagowa yana kallona.
Hasken kwan fitilan falon ya haskani gaba daya launina bada wani kala na daban ga mai kallona a lokacin.
Na duka ina zuba mai kullan gabana wanda sakwara ne a ciki ashe sai na bude kulan miyan shi dake dauke da miyan ganye yaji egushi da manyan nama na zuba daida don nasan shi baya cin abinci da yawa.
Mikewa nayi zan bar wurin ya kara fafin ruwan wanke hannu fa ba tare daya ko kallo inda nake bai yi ba yai magana.
Har suka bar falon ban kara fitowa ba sai bayan danaji fitan su sunawa mami saida safe na dan kara mintina na fito.
Kayan da sukaci abinci nake kwashewa yayin da nazo kan nasa naga spoon a ciki da alama dashi yaci.
A raina nace bakin bature ke nan abincin ma da cibi zaici don sallo ai kakar nan tasuce maganin shi.
Tas nayiwa falon kafin in shiga wurin mami ina tambayanta koda abinda zanyi mata kafin na kwanta.
Zeey a kwashe kayan abincin nan da sukaci nace na kwashe mami ki duba min kayan barci na a cikin kayana ki ban shike nan sai kije ki kwanta.
Har na kwanta a saman dogon kujera anty Aisha ta shigo tana fadin af namanta da charger na dakin tsohuwar nan dan Allah zeey dauko min.
A kofa na tsaya nayi sallama kafin in shiga dakin yanayin dana samesu a ciki nagane wani magana sukeyi mai muhinmanci a tsakanin su su hudu.
Tsohuwar da kuma kannen mami din duk suna zaune sunyi shiru da suka ganeni.
Sai mami ke fadin bakiyi barci ba ashe zesy a, a nace nake fadi charger anty zan dauka ganin suna kallona duk sai na tsargu .
Na dauka na fita da dan saurina daga dakin don ban son in dakatar masu da maganan da sukeyi din .
Washe gari tunda safe dana tashi nayi sallah na fara gyaran falon har zuwa waje ina jin hayaniyar su dakin har na gama wanka na shiga don mami tana cikin dakin da yan uwanta.
Sai kusan karfe goma suka fara shigowa falon ana gaisawa a tsakanin su babu muryan wanda nake jin tsoro don haka na fito na gaidasu da kwana ina jin mama Ramatu na fadin.
Ga abinci nan tun safe aka aje masu shi basu shigo ba ina shi jafar din gana yan aikin shi nan suma .
Bai fito ba jamal ya bata amsa tare da fadin mama kinsan shi baya fitowa da wuri haka ai sai idan ya gama abinda yake yi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣9️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAN UWA FATAN ALHERI HAR KULLUN A GARE KU UBANGJI YA GAFARTAWA MAGABATAN MU DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA ALLAHUMA AMIN.
YAR UWA BA ZAN GAJI DA TUNATAR MAKU BIYA KAFIN KI KARANTA BA DON KAICEWA SHIGA HAKKI GA MASU IMANI ALLAH YASA MU DACE AMIN DARI UKU NE KACAL KI GUJI RAINA HAKKIN WANI A KANKI DON ALLAH.
Saida gabana ya fadi don jin muryan dodona da ya shigo gidan bani kadai na gane ina tsoron shi ba don har salma, Rufaida da Nazifa.
Idan ya shigo na kanga sun shiga taitayin su a gidan har jamal da jalal suna wanan rawan jikin da kama kai a gaban shi idan yana kusa .
Nima hakan da nagani ya darsa min tsoron shi a lokaci guda duk da ban taba ganin wanda yaiwa cin fuska a gabana ba.
Dagowa nayi a rikece ban ko debi abincin kwarai a platen din ba don in gudu in koma dakin mu.
Na dai samu gaida shi da kwana na jakafata na shige dakin zama nayi don cin arish da kwai dana debo a falon .
Nayi loma biyu ne naji mami na kwala min kira daga falon da sauri na mike na fito falon ina fadin mami gani.
Tana can tana magana da mama Ramatu kanwarta a lokacin kafin ta juyo tana fadin .
Yauwa zeey don Allah yi serving din yayan ku gashi nan ya shigo yanzu ni zan dan fitane yanzu zan dawo.
Tana fadin haka ta mike sai naji yana fadin amma da mota zaku don akwai dan nisa daga nan gidan.
Eh ai shine yasa nace Jalal ya sauke mu kada yaje nisa yana waje yana jiran fitowan mu ai.
Amma mami jalal ne zai jaku ga driver suna waje sai shine zai jaku ban faye yarda da tukin yaran nan ba gaskiya yake fada da turanci.
Sun saba jana a mota ko a kaduna don hakane ai na yarda da tukin motar nasu.
Allah tsare yace yana mayar da kanshi ga wayan dake hannun shi aikin shi ke nan ko magana yake hankalin shi a kan waya ko sytem din shi shiya a raina nasa mashi mayen computer.
Abincin na gama zubawa lokacin falon daga shi sai tsohuwar dake zaune itama kudi take kirgawa daga haban zanin ta nakai mai abincin gaban shi na aje.
Ruwa na koma na dauko na aje mai cikin dan muryana nake fadin yaya ga abincin nan do gudun kada inyi laifi kuma gare shi.
Jin abinda nace yasa shi dan juyawa saman lafiyayyen kujeran falon tsohuwar da zaka iya da kira dakin wata amaryace can don haduwa.
Wayan ya aje daga gefe kafin yakai kallon shi ga abincin ya dago kai yana kallon tsohuwar kuma.
Kai kai kai wanan tsohuwar ko fashi kika farane haka ina kika samo wanan kudin haka masu yawa ?
Yanzun kuma bakiki kariba don baki da tausayi sai kuma kin karbewa mami dan kudin ta maimakon ki kara mata.
Kafin tsohuwar ta dago kai tana fadin ja,iri da hausan ka kamar na mai koyo uwar taka mai tausayina ita take aiko min da kudin ai.
Yau kuwa zance ta daina don ba kashewa kike yi ba boyewa kike yi idan an baki ashe.
Ina wurin fridge ina daukan ruwa insha suke wanan barkwamcin da kakar tasu na dauko ruwan na juya zan wuce daki don da farko tsoron shigowan shi ya hanani daukan ruwan .
Naji yace ke wanan uban abincin da kika zuba ni dawa zanci shi haka ?
Tsayawa nayi wuri daya da goran ruwan a hannu na ya sake fadin sai kizo ki dauka ki cinye shi tas.
Cikin karfin hali nake fadin na debi abinci yanzu yana daki na aje zanci kai wanan yaron da fitina kake wallahi ina laifin yar nan tana iya kokarin ta da kai.
An fada maki kowa irin kine dake loda abinci a cikin sa yana kiba kamar za,a tafi gasan gwaji dashi halan ?
To ba zataci ba idan zakaci kaci da yawan fitina har yaushe zaka zauna kana matsawa yarinya mutane haka.
Yar nan ko karyawa bata samu tayi ba yanzun taga ba yan uwanka abin kalaci suka fita kai kuma kazo da naka tsurkun yanzu.
Idan kayi fushi sai kaje kayi aure kowa ma ya huta mitar ka na tsiya kaji min yaro da jarabar tsiya haka.
Hjy dama naga kin gaji dani ai ki huta min gori yau kaduna zan kwana idan Allah ya yarda idan ka tashi ka wuce jos zaifi ma sauki ai.
Ina tsaye wuri daya ni ban gusa ba ina sauraren da bai karewa da tsohuwar ko da yaushe sai dai idan basu hadu ba idan kuma bata ganshi ba ta kafa mita ke nan ina ya shiga.
Zo ki dauki abincin nan na fasa ci ya fada da dan karfi simi simi na tako zuwa gaban shi ina zuwa nakai kasa tare da fadin.
Don Allah yaya kayi hakkuri na fada ina kaiwa kasa kamar zanyi kuka a gaban shi bace min dagani a nan na firgita sosai tare da kai hannu ina daukan plate din abincin.
Na juya ya sake fadin zo nan na dawo baya da sauri zuwa gareshi hjy ko sai faman yi mai masifan hakan takeyi bai kullata ba.
Baki da wasu kayane sai wanin black dress din da kullun kike sakawa ba kyau gani ?
Kallon kayan na jikina nayi ina fadin anty Aishace ta bani sune sabbin kayana yanzu dasu kawai nazo garin nan.
Fadan da kakan nasu takeyine ya hana taji me yake fada min don babu yadda zata jishi a yadda yake maganan.
Tafi don Allah ya fada in deep voice na juya da sauri don in bar wurin kafin yakai ga makeni yadda naga ya hasala din nan.
Tunda na shige ban kara fitowa ba shi kuma bai fita daga falon ba don ina jin muryan shi jefi jefi da hjy tsohuwa a falon.
Har su mami suka kai ga dawowa gidan hakan yasani kwantawa na kirkiri ciwon karya don da Anty Aisha ta ganin kwance take tambayana nace kaina ke ciwo.
Data fitane mami ke tambayan ina inane tace tana daki wai kanta ke ciwo tace .
Yo ai dole kai yayi ciwo ko don fitinan wanan masifafen dan naki da kika barta dashi ta bashi kalaci ya aza mata fitina.
Aiko ya Jackson baida fada hjy kece dai baki fahince shi ba Aisha ta fada tana kallin dan uwan nata.
Murya mami tasa ta kirani daga falon kamar ince wayo don wani irin faduwan gabane ya zuyarci zuciyana lokaci guda .
Saboda tsoracewa gashi yai min fadan jallabiya baka dana saka a jikina wanda har yanzu shine dai din a jikin nawa.
Don gigicewa ban ko tsaya daukan dan kwalina ba kaina dake da kitso tsoro hudu da nayiwa kaina a daren da zamuzo sun kwanta suyi lub dasu ga bakin gashi na sai sheki yakeyi.
Na fito nazo na zube a gaban mami din dake maganata da mahaifiyar ta kan rashin sake jikina a cikin su.
Ban iya dago kai na kalli kowa a falon ba kaina yana sade a kasa ina jiran inji abinda zatace dani.
Shiko ko kallon inda nake baimayi ba tunda nazo gaban mami din gashi a kusa dashi mami take zaune a daya kujeran dake gefen shi.
Meke damun kine zeey mami ta fada tana duban yanayina kai na dan girgiza tare da fadi cikin karfin hali mami kaina ke ciwo dama tun kan muzo nan na kuma sha magani ya fada min don kada tace a kaini asibiti.
Haka baida wuya a gurin mami dan abu kadan gare su yanzu asibiti ne za a ce akai mutum.
Mami tace dawo nan ki zauna ki daina wanan yawan zama ke kadai da kikeyi a daki ko yaushe koshi yana ja maki ciwo.
Banda zabi sai yadda mami tace dani dole haka ja mataciyan kafata da yai sanyi na hau saman kujeran data nuna min din.
Yaya jafar da ke rubutu a cikin sytem shi cikin kwanciyan hankali sai lokacin dana kai zaune ya dago kanshi yana fadin .
Ke meke damun kine wani irin magani kika sha nayi tsuru tsuru da ido don ban san me zance ba sai da mami ta kara tambayana nace.
Mami dama wanda aka ban asibiti ne a abuja sauran daya rage na sha dazun.
Sai naji yaja uban tsuki ya mike yana gyara dan riganshi daya takure don zaman daya dade a zaune.
Zaka fitane kafin ya ba mami data tambayeshi amsa sai hjy tace yo ina zai fita tunda tsoron mutane yake ji a waje.
Wurin ta ya nufa direct yana fadin zo muje ki rakani kada kada a saceni garin naku.
Wai wace ke zaune a kauye ke fadin wani na tsoron mutane ke idan ba tsoron kikeyi ba meya hanaki komawa kaduna ki zauna da mami.
Ja,iri ba zan tafi ba a dakin mijina zan mutu inda ya barni ba dakin wani ba ya fice yana dariyan maganan ta.
Ya dan jima a waje ina nan zaune falin tare dasu mami daketa baki suna fita don zuwa gaida mami din sai faman basu alheri mami keyi.
Nasan dai da yawan masu zuwa gaida ita yan uwantane saura kuma abokan arzikine.
Yayi sallama ya shigo falon suka amsa mai inda nake ya nufo yana mika min magani nasa hannu biyu na karba a cikin ladabi.
Mami ke tambaya maganin meye wanan din yace stress don kila aikine yai mata yawa yana mika min ya juya ya fita daga dakin.
Haka ya ban dama tashi na hade maganin don dole duk da ban san maganin kome yake nufi ba aiko na fara jin jikina wasai.
Ina sallah azahar sai barci ban tashi ba kuma ba wanda ya tayar dani din don sun dauka dai da gaske banda lafiya ne din sai bayan sallah la,asar na falka na tashi nayi sallah.
Ina idar da sallah nayo falon part din tsit yake babu wani hayaniya acikin sa yasa na gane mami ta fitane a lokacin.
Ko ina na gyara tunda aikinane nagama na hada kayan abincin da nagani ta nan na gane su yaya mamud sun dawo sunci abinci sun fita.
Don da alama shi yasan garin sosai kilama yana da abokai a garin sabanin shi mai zaman gida ko yaushe.
Salati naji a bayana mama Ramatu na fadin yanzu yarnan harda baki da lafiya baki kwanta kin huta ba ?
Kina nan kina tikan aiki haka mama naji sauki na bata amsa ina dauraye kwanoni dana tara wanda na wanke.
Kinga idan baki da lafiya bar matsawa kanki haka ai kowa yasan ciwo ko a daga maki kafa dashi.
Ni dai na gama ban ce uffan ba sai dan murmyshin da nakeyi kawai dakin na koma na shiga wanka kafin magariba yayi.
Iya kacin ganina da yaya Jafar ke nan tunda ya ban magani saida darene nake jin su mami na magana wai ashe fitan da yayi tunda ya kawo min magani kaduna suka nufa.
Yana zuwa kaduna gida ya nufa don yana son yayi wanka abinka da goggagen dan boko mai ilimi ashe duk zaman garin ya ishe shi .
Dan daurewa yayi kawai don ya farautawa mahaifiyar shi da kakan shi raine.
Sai dai ya kasa kanne zama har kwana biyu ko ukun da mami tace zatayi da mahaifiyarta a tare dasu don suga yan uwa yan uwa su gansu.
Tun daga kofan shiga yake jiyo hayaniyar yan matan a gida yake mamakin me suka samu hakane suke wanan hayaniya haka ?
Rawa suke tika ga kida yana tashi kamar gidan club Nazira da Ruby suna wani irin rawa wanda bai dace ace sunyi ba.
Ba wanda yasan da shigowan shi har ya tsaya yana kare masu kallo a wurin kafin kamshin shi dakewa mutum sallama ya daki hancin su.
Duk suka juya suna kallon kofan salma na zaune tana shan milk a cup tana dan kurba a hankali itama daga inda take din zaune tayi arba dashi.
Rudewa ko wacen su tayi ya tako a hankali zuwa part din shi dake gidan don wanka yake son yi da sauran abubuwan daya bari a nan.
Da sauri Nazira taje kashe kidan baiko juyo ya kara kallon inda suke ba ya shige part din bayan ya bude tare da gwauro kofan da karfi.
Duk yadda yake jin shi a da sai yaji komai ya gushe mashi bacin ran yaran nan ya mamaye zuciyar shi.
Yes yasan da yana wasu abubuwa da suka kaucewa addini da tarbiyan shi amma tsani yaga diya mace tana kauce hanya.
Zama yayi sama gado dakin tare da tokare hannaye shi ya kama haban shi yana tunanen zancen su da mami da take fadin.
Ba zanso ka ketare gidan nan ba idan baka son yar hjy hindu sai ka zaba a cikin wa yan na yaran guda uku da ke gidan nan don nasan dukkan su babu wace ba zatayi makaba a cikin su.
Tunda kai na fahinci baka da time din tsayawa dating da wata mace a yanzu tsuki yaja yana mikewa tsaye.
Deep in thought yaya za ayi ya auri daya daga cikin yaran nan da idon su ya gama budewa haka wai.
Dadai yaso bin ra,yin mami don shi ba wata macen da ta tsaya mai arai yanzu don hakane zaibi zaben mami din gareshi.
Wani tsuki ya kara ja ya fara cire aninin gaban rigan dake jikin shi fara longsilve yana maijin tarin haushin su a ranshi.
Wanka ya fada ya dan dauki lokaci kafin ya fito ya samu waya shi nata ringing ya nufi inda ya aje wayan yana dagawa.
Yaya mamud ne a layin yai mai kira biyu bai daga ba gana ukune ya samu ya daga yake fadin ya jafar kana inane haka mami tana tambayan ka ta kira layin ka not reacheble.
Ina gida yanzu haka ya bashi amsa kai tsaye gida yanzu na fito mami da hjy suna tambayan inda ka shiga yanzun hakan ina kofar gidan.
Kaduna fa nake nufi ya bashi amsa kamar a hasale don har lokacin yana jin ranshi babu dadi ga abinda idon shi ya gane mashi din nasu Rufaida.
Kokarin tayar da sallah dake kanshi yayi kafin ya gama ya shirya cikin wani jallabiya ya nufi gado ya fada.
Saidai duk yadda yaso yayi barci hakan ya gagareshi don baison ya batawa mami rai ko kadan tunda yai mata alkawari ya zama dole ya cika mata burin ta..
Mami tunda yaya mamud ke fada mata ai Jackson ya koma kaduna taji rayuwanta ya baci dashi sosai don me zai nuna bai iya zama a mahaifan ta.
Ko kuma yayi hakane don gujewa zancen auren data tasa shi gaba dashi don ko a daren jiya saida sukai mai tas itada yan uwanta da mahaifiyar su.
Wanan zance ne na sama sunayi da anth Aisha ta aikoni daukan mata charger ashe a dakin tsohuwar da dare.
Mami uwar zamanice don haka ba tare data furtawa kowa bacin ran da take ji a ranta ba ta nasa zata kyaleshi taga iya gudun shi yanzu.
Don haka ta daure taci gaba da tsabgoginta ba tare da nunawa kowa komai ba kamar ranta bai baci ba.
Haka kuma tasa a ranta wanan karon ba zata kirashi taji dalilin yin hakan dayayi ya barsu can ba tare data sani ba.
Karshe ma shigewa tayi da sunan zatayi wanka harta shiga dakin ta juyo ta fito zuwa dakin mu ta sameni kwance na rufe idanuwa na sai jin muryan ta nayi a kaina.
Da sauri na bude idanuwana cikin laushin murya nake gaida ita take fadin ya jikin naki yanzu ?
Naci sauki na fada a yar siririyar murya ina kokarin mikewa zaune ta sake fadin badai inda kike ji a jikin naki yanzu don in sani tun dare baiyi ba.
Zama tayi a gefen gafon dakin tana dan kale kale a dakin kamar tana nazarin dakin ne ko kuma wani tunane.
Na dago kai a hankali sai naga tana kallona can take ce min ko dai zancen karatun kine kika saka a rai haka zeey har yaja maki ciwon kai ?
Nace lah mami wallahi bashi bane mami dazun daine kan nawa ya fara ciwo kuma ai nasha magani yanzu naji sauki.
Tana mikewa take fadin to shike nan ina ganin zan karbar maki transfer tunda yanzu zaman mu zaifi yawa a can.
Don ba zan barki ba inda bana don ke din kamar amana kike ga hannu na ai.
Mami duk yadda kika zantar a kaina daidaine tunda kece uwana yanzu ai mami banda wata uwar dana sani kuma.
Tace to babu laifi na gode ga yadda kike nuna min nima sai dai ina tsoron watarana kar asabe ta rabani dake.
Asabe yamzu bata da iko kamar yadda kike dashi a wurina mami don ba tare nake zaune dasu ba kuma.
Sai tayi murmushi tana fadin kafin dai ki kwanta ki kara shan maganin da aboki ya sayo maki dazun don ina ganin har da gajiyan aiki din a ciki.
ZAINAN IDRIS MAKAAA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣0️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA JUMMA,AT MUBARAK FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA KARBA IBADUN MU YA SADAMU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN RANAN YA GAFARTAWA MAGABATAN MUSULMI BAKI DAYA ALLAHUMA AMIN, , , , , , ,
YAU MA DAI INA MAKI TUNI AKAN HAKKI DA KWABON KU MUKE SAMUN CIGABAN RUBUTUN MU A DAURE A BADA HAKKI DON SAUKE NAYI A KAI, , , ,
Sai faman shiyawa muke tun dare ake shirin dawowan mu kaduna taaraba mai yawa aka hadawa mami irin abinda zata bukata a birni wanda babu shi sai a irin wanan gari.
Gashi tare da wanan tsohuwar zamu koma don mami ta shawo kanta da kyar ta bari a kaita asibiti a dubata ta dan kwana mata biyu ta dawo koshi sai da wanan mami ya sa baki ta yarda da hakan.
Tun a can mami ke fadin wanan bakuntar zeey ce da Aisha ce don dai nasan hjy ba shiryawa zatayi da sauran yaran nan ba cewa su anty salma dake gida.
Bamu bar garin Samu,naka ba sai misalin sha dayan rana tafiyace maidan jayawa tsakanin kaduna da garin sai dai a gurin su yake haka nikan a wurina kamar unguwane hakan ai.
Don ko banza naga gari da kauyokan da nake jin sunan su a bakin mutane a da can da nake gida.
Allah ya kawo mu lafiya don wanan karon da motoci biyu muka juyo don mai tarin motocin ya juyo abinshi ya barmu can.
Duk da nasan mami tana wayencewa kan barin ta can da yayi don kamar rashin da,a ya nuna mata ga hakan don naji suna magana da anty Aisha a dakin da muka sauka kan hakan.
Aisha tana bata hakkuri da cewa mami ki dai bincika wata kila yana da wani uzurine yai haka don kinga ai daga baya jiya ya turo da sako a rabawa mutanen nan din.
Mun samu su mama Kande sun gyara gida tsab suna koma kan aikin girkin da za a ci idan an iso, da yake aikin nada yawa yasa basu kare ba kafin isowan mu garin.
Sun fito sun tari kowa da murna da farin ciki ina tsaye wurin mota babu wanda ya kulani a wurin nikan driver na fara fitar da kaya na fara dauka na shiga dashi cikin gidan da nakw ji yanzu kamar gidan mune.
Tsohuwarce tafe a hankali tana saye da glass din ido a fuskan ta sai farin gyale kwato dage yafe a jikinta dake saye da atamfan super mai ruwan haki da dorawa a jikin shi da manyan zane.
Da sauri na karasa ina kokarin karban ledan maganin data rike a hannun ta zata shigo gidan ga su Rufaida suna gefe suna mata tsiya.
A cikin ladabi na mika hannu ina karban ledan tace ba kaji ba yar albarka kedai kinfi wa yan nan kirki da hankali.
Barshi kinji ba wani kayan nauyi bane a cikin sa ai, aiko sukayo min caaaa a kai Rufaida na fadin wanan ai bakin iya yi ne da ita ga kowa saita nuna ita yar munafukaine ai.
Kai haba wanan zagin haka kuma fa ku daina wanan dabi,an bai da kyau ko kadan zagi harda iyayye.
Rufaida ta hasala ta watsa min harara nidai duk da tace baida nauyi bai hana in karbi ledan a hannunta ba.
Zama tayi a falo bayan ta iso da kyar don yanayin tafiyan nata yadda take yinshi a hankali ga tsufa ga ciwo dake damunta a jiki.
Nan falo gaba daya suka zube sai nuna kauna ga juna sukeyi ni dai ina tsaye da ledan nama shagala ban sani ba.
Banji fitowan shi ba sai kamshin shi daya doki hancina lokaci daya tare da muryan shi yana fadin watau nan ma kin biyoni ke nan ko ?
Na gudo na barki can bai maki ba saida kika biyosu kuka dawo tare yana magana tare da daure fuskan shi kamar gaske .
Ja,iri to baka tsira ba ai don gani ko na biyo ka din don ba fasawa zanyi ba da magana ta sai kagaji kayi zuciya ka fito muna da mata mun gani idan shika guduwa dama.
Mami yaya akayi kika zo muna da wanan yar matsalan tsohuwar gida yana magana yana kallon mami din data daure fuskanta tun fitowan shi kamar ba ita bace ke dariya yanzu .
Saidai jin ya ambaci sunan ta fake fadin cikin daga mai hannu please live me alone don't metion my name again cikin kara daure fuskanta gare shi.
Oh mami rely iam sorry for what i have done wanan tsohuwar ne ta dameni kuma nasan ba bari zakiyi in dawo ba idan na fada maki kai tsaye zanzo inyi wani abu a nan a ranan nima tafiyan ai da niyar in komane idan na gama sai gashi ban samu komawa ba.
O hjy ce ma ta dameka har kana fadi a gabana forgive me mami iam sorry wlh wani abu nazo yi garin nan na lake a cikin sa.
Alhalin tunda yazo yana gida bai fita ba yana daki yana ragewa kanshi zafi abindake tsunkularshi kwana da kwanaki.
Is your on business koma meya baro ka da garin mu dai ai ba zaka hanamu yin kwanakin da mukai niyar yi ba a can.
Ya dan laso bakinshi yana shafan kai don ya fahinci mami ta hau sosai dashi kan abinda yayi din na barin su can ya dawo nan shi kadai.
Ke wai lafiya kin tsawa mutane saman kai haka kina bin mutane da kallo don rainin wayau Rufaida ke fadi a hasale.
Keko gulma mana tana bin bakin kowa da kallon abinda ake fada kamar ba yar aiki ba ta dinga shiga cikin mutane tana kutsa kanta.
Ikon Allah da alama yar nan dai bata jin dadi a wurin ku meye matsalanta don ta tsaya a cikin mu ita din ba mutum bace kamar ku ai dan mutum daraja gare shi tsohuwar ke fada tana kallo.
Zo ki zauna a nan gaki tsaye kinyo tafiya baki zauna ba take fada tare da kallona tana nuna mi wurin zama.
Nace dama ledan nan ne ban san dakin da zan kai maki ba shine na tsaya na fada a dan marairaice.
To kuma ji da abinda ya tsayar da ita a gurin ba tsayin banza tayi ba ta mika hannu in miko mata ledan dake hannuna.
Mami tace na rasa me yarinyar nan ta tare masu a gidan nan da basu bata salama sai hattara da tsana.
A,a in kinga hakan wata kila dai sun hango wani abune a gareta sukewa kyashin sa ko don yanzu ta karbe masu fada gurin ki.
Su dai daina haka don ban so banyi sharawa da kowa ba da zan kawo ta gidan nan do haka ba zan dauki hakan ba gareta tunda ban bari uta ta raina ku ba.
Gaban mami bazo na tsuguna ina fadin mami bani key in bude daki zan gyara ne kafin ki shigo.
Ga dai key din gyara ki bari sai anjima yanzu dai ki kwashe kayan mu kikai min daki hjy kuma nata dakin ki kai mata sai ki koma dakin Aisha da zama ke .
A, a barmu mu zauna dakin ta a tare dama kawatace ki n ga ai ko tausa tayi min a dakin idan ina so naji kuma dumin mutum a kusa dani ai?
Ko ba zaki zauna tare dani ba kawata tana tambayana cikin dan dariya tana kallon fuskana.
Murmushi na sake wanda yasa fararen hakora dan baiya diple dina ya dan lutsa daga gefen fuskana ina fadin ina so sosai hjy .
Ya daifi ni dama ba zan zauna da kowa a dakina ba Aisha ta fada tana mikewa tsaye mami tace hakan baidai taso bane .
A nan na barsu ashe baya barina wurin Rufaida tayi fushi ta mike ta koma daki su waya ta jawo tana fadawa uwarta wai mami tana disgata kan yar aiki ita gida zata dawo don hakan da ake mata yana ci mata rai.
Duk da mami tace kada na gyara dakin ba yarda na barshi hakan ba don sai dana kara gyarashi tas na dawo dakina na gyarawa hjy yadda ya dace na dauko wani zanin gado dakin mami mai kyau na shimfida mata.
Falon na dawo inda na samu sun fara cin abinci har lokacin mami na zaune tare da yaran ta gaba dayan su a wurin sai salma da hjy ma kakarta ce don itace ta haifi uwarta a gurin tana nuna jin dadin ganinta.
Yau zee kici abinci ki dauko zanin gado a daki ki shimfidawa hjycdakin ki .
Nace na dauko na shimfida mami tun dazun ai tace kai zee na gode sa wanan karama hjy din da kike yi yamafi min ku zauna tare da zamanta da wanan mara moriya din tana nuna Aishan ta.
Mami nice banda moriya bari ki gani har wanka zan dingawa hjy har ta bar gidan nan kuwa hannu mami ta watsowa Aisha tana fadin karbi naki nan ko uwarki Ramatu tayi kadan tayiwa hjy wanka yanzu ai.
Abinci na diba na koma can gefe guda ina dan duban inda zan zauna mami ke fadin wanan abinci zai ishe ki ke nan zeey ?
Ya isa mami na fada ina nufar can nisa dasu don in zauna tsohuwar take fadin wanan ya da dadin zama take wallahi.
Wanan ba irin yarwa bace a cikin ahali yarinyar ta samu tarbiya a gun uwarta kada ki bar wa yan nan marasa ta ido su kore maki ita gidan nan.
Ai ba zan barsu ba mami ta fada duk wanda bai iya zama da abindanake so yayi gaba hanya a bude yake mai ai.
Baidai kai can ba kowa ya tsaya a matsayin sa tsohuwar ta fada mami ta nuna salma tana fadin sune ai marasa hankalin yarinya ta girmamasu sai sun zubar da mutuncin su gareta zasuji dadi.
No mami ba salma a ciki zancen nan don da kanta zeey ke fada min tana jin dadin zama da anty salma sosai idan muna hira da ita.
Salma tace mami ni ina ruwana da harkanta gidan nan tunda bata tare min komai ba ga kowa.
Shine daidai hakan ai kinji itama tana yabon ki a bayan ki gashi yanzu yar uwan ki tana fadi kuwa kafin ta juya wurin yaya jafar tana fadin.
Kai gwauro ba zakaci abincin bane kai ko sai yayi sanyi ka tsikara ka tashi tunda baka aje ba balle a dumama shi.
Zaki fara tsokanarshi ko hjy yaya mamud ya fada yana mikewa sai tsohuwar tace gashi ko yanzu ya iya yaji saboda korafina ba kuma zan fasa ba idan baiyi abinda nake son yayi ba.
Ya dago kai yana fadin me kike ci na baka na zuba hjy kwana zan fitar da mata kowa ya huta ina shike nan.
Shike nan kuwa kaga an wuce wurin haba ko kai fa mutum kamar me jin warin mata a tare dashi.
Barshi hjy rainawa mutane yake son yi wanan karin ko ba zan saurara mashi ba don naga wasa ya dauki zancen nan.
Mami ai na fada maki kwanan zan fitar kowama ya huta sai mami take fadin yar gidan wanene yarinyar da zaka fitar din ?
Mami ai ko yar waye zaki gani idan Allah ya kaimu ranan dinan ki sai naba kowa mamaki a gidan nan sosai.
Mami ai kin san sai yar gwauna ko wani seneter don irin su yaya Jackson sai diyan manya a kasan nan ai Aisha ta fada tana kallon shi tana dariya.
Shima murmushi yayiwa zancen Aisha din yace kedai bari zan yi surprise din kowa idan na tashi sai hjy tace kada dai kaiwa mutane zaben tumun dare garin ruwa idon kan nan.
Ni makoho ne aka fada maki ai kece mai bani shawara ki bari ki gani idan ban zabo da kyau ba sai ki fadi hakan.
Wayan shi da yai kara ya dauka yana duba kafin ya mike ya bar wurin yana wani magana kamar yare sai hjy ke fadin.
Itace ta kiraka kake gudu kar muji me kuke fada dama ka zauna da wanan yaren naku baji muke ba mu.
Daga inda nake ina dan murmushi wani tunane yazo min nake fadin a raina zanso nima inga wanan zabin na yaya jafar yadda yarinyar zata kasance.
Nasan badai kyau da kudi ba kan kamar yadda yake da kyau din nan ga ilimi ga wayewa dole wace zai aura din itama ta kasance kamar ai.
Ni daya ke faman tunane har naji abincin ma ya fita a raina ina tuna sukan sunji dadin su uwa kudi uba kudi haka.
Suma gasu kudi wai ina mutanen nan zasu da wanan dukiya hakane idan da nice su ai ba zan nemi wani kudi ba zan zauna in hutane kwai inta jin dadi na a gida.
Zeey zoki kwashe wanan kayan abincin nan wurin nan ki dawo ki kai hjy daki tayi sallah ta dan huta.
Firgigit na dago kai tare da fadin to mami ina kokarin mikewa a inda nake zaune din.
Sai dana gyara komai mami na zaune gurin tana waya da yayan ta da muka baro dazun garin su.
Hjy muje in kaiki dakin azahar yayi tun dazun na fada a cikin ladabi ina kokarin daukan kayan ta gyale da ledan maganin ta dake gefenta aje.
To yar nan har na fara gyangyadi ko a wurin ba tare dana sani ba tana mikewa tare da kokatin tattaro gyalen ta dake gefe.
A hankali muke tafiya zuwa dakin har muka kai dakin yayi dan dumi sai kamshi ke tashi a cikin sa ledan na aje a gefen gadon kafin in nufi kofan ban dakin in bude mata shi.
A, a kagani ba nan yayi min gara in zauna dake da in zauna da wanan mara moriyar Aisha wace ko kara ba zata iya kawar wa kanta ba balle wani.
Bayan mun idar da sallah dukkan mu a nan kasan muka kwanta nabawa hjy filo tayi matashin kai dashi niko ko filon ban samu matashi dashi ba sai barci.
Ban falka ba sai da hjy ta tashini don inyi sallah la,asar nasan yamma yayi saboda dadin barcin da nayi.
Na idar na mike zuwa dakin mami bata dakin yasa na samu daman kara gyara dakin da yake ba wani datti a ciki dakin
A falo mamice da yaya mamud suke magana haka yasa na juyo zan koma dakin mu indan gyara don ko ba komai da zan wa dakin ban dakin yana bukatan wanki koda yaushe.
Na wanke na fito ina daukan filon data kwanta a kasa take fadin yar nan idan kin rage sai ki kaini falo in zauna don yamma tayi yanzu.
Na amsa da to hjy muje mami ma tana falon zaune tare da yaya mamud .
Wai ni iyalin shi mamud din suna inane don banji duriyan su ba tun dazun ina a nan gidan suke zaune ne suma.
Suna Abuja an barsu a can da zamu dawo kaduna yar ta kifen tana nan dai da halin ta har yanzu bata canza zani ba ko ?
Dan dariya mai sauti nayi ba tare da nayi magana ba don ban san abinda zance da ita ba.
Falin muka fito tafiyan minti daya daga dakin mu zuwa falin saida muka biyar muna lalabawa kafin mukai saman kujeran ta zauna a hankali.
Mami na fadin kun lalabo kun fitone hjy take fadin yar nannta lalabo dani ina dan jin dadin hakan yarnan akwai kirki sosai.
Allah yasa kiga aurenta hjy amin ta juya tana fadin kada ki tsaya dogon bokon nan na zamanun nan dake batawa mutum lokaci sai a dauki lokaci yaro na zubar da irin sa duk wata.
Yaran nan da kun gane ai da ku aurar da su don har sun wuce munzali aure a yanzu .
Hjy kin san ai aure dan lokaci idan lokacin sa yayi koda shiri ko ba shiri sai ayishi a lokacin.
Zaune yake saman farar kujeran roba a gurden din gidan mai dauke da dogayen itatuwan da ba wani zugun ganye suke dashi ba sai dai tarin tsayi a gasu.
Babu wani abinda yakeyi duk da sytem din shi dake gaban shi a bude ya kasa aiwatar da komai sai faman tune a ranshi.
Yakai hannu a hankali ya rufe sytem din ya dafe kan shi dashi yana ci gaba da tunanen shi ya rasa yaya zaiyi ne da wanan hukuncin da yake kokarin yakewa a ranshi.
Allah ya gani bawai yana son yarinyar da mami ke son hadasu bane zai dai amincene don farin cikin mahaifiyar shi kawai.
Don yadda mami dasu hjy suke nuna mai muhinmancin yin hakan gareshi saidai shi Allah ya gani bawai ya shiryawa aure a wanan shekarun nasa bane.
Anya kuwa idan yayi gangancin yin aure a yanzu ba zai jawa kanshi matsala bane ga hakan.
Kai ya girgiza shi kadai tare da fadin dole yai juriya da fin karfin zuciyar shi don ya samu su rabu lafiya da mahaifiyar su.
Muryan Rufaida dake fadin ki tabbatar da kin wanke kayan nan tas wallahi kada inga jirwaye a jikin su banza kawai mun zuba ke nan dake a gidan nan.
Ke gaki kin samu wuri zaki mike kafan ki kiji dadi ko to wanki har na tufafina duk ke zaki dinga wankin su a gidan nan daga wanan ranan.
Nima ga nawa Nazira ta fada shegiya munafuka mumuke zamuyi maki a gidan nan ba tare da mami ta san da hakan ba ta jefo min unders din ta a fuska.
A daidai lokacin daya karaso wurin don jin zagin da suke min din yayi yawa a lokacin.
Yana tsaye hannun shi duka biyu zube cikin aljihun wandon shi kallon kayan yayi yayi saurin kawar da idon shi ga kayan.
Ya dago yana kallona su kuma sai dan kame kame sukeyi suna fadin sannu da hutawa yaya J ke daga daga nan ki shige ciki ya fada yana kallona.
Da sauri na bar wiein kayan na koma ciki dama wurin su mama kande nake zaune suka sameni suka ban wanan sikin wankin.
Nan nabar masu kayan nasu na shige ina share hawaye babu mami a falin sai hjy dake zaune ita kadai ta kurawa tv ido tana sauraren malam daurawa dake wa,azi a tashan sunna tv.
Na zauna take fadin yar nan akwai kura kuren da mukasha tabkawa a rayuwa sosai a baya wanda sai yanzu kake jin bayanai akan abubuwan da bamu sani ba a can baya.
Jin tana magana ban bata amsa ba yasata dago kai tana fadin kinga kamar da can baya ai bamu sancewa ga lokacin da mutum ya dace yayi , , , ,
Ido ta kura mi don hawayen data ga ina sharewa a lokacin salati ta saka hankali tashe tana fadin .
Waya tabaki me akai maki yar nan ki fada min wanda ya musguna maki yanzu don nasan ranki aka bata haka.
Muryan mami ne ke fadin hjy lafiya wa aka batawa rai zeey lafiya me ya faru yanzun fa kika bar falin nan da raha da hjy .
Mami ba komai ba komai kamat yaya ta fada tana kallona tana zama saman kujera takon kafab shine yana shigowa daga kofan baya yake fadin.
Mami kiwa yaran nan iyaka da yarinyar nan abin is too much sun mayar da ita boya a gidan nan .
Mami idan baki iya masu magana su daina don Allah ki mayar da yarinyar nan gaban iyayyenta haka cin fuskan yayi yawa.
Ya kwashe komai da yaji yana fadawa mami rai bace yana gama fadi ya juya ya fita hjy ma tana masa magana bai tsaya sauraren ta ba ya fita don bai cikin dasin rai a lokacin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣1️⃣
ZAINAB IDRIS
MAKAWA
YAR UWA FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA TARE DA IMANI A ZUKATAN MU AMIN DON ALLAH KADA KI FITAR KARKI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA KI TUNA DA AKWAI RANAN HISSABI YANA NAN TAFE.
Ki biya ki karanta a cikin salama yar uwa kan dari uku kada a tsayar dake ranan da kowa tashi ke fitar dashi sai abinda ka shuka.
Yau tun safe Lantana da haibaici ta tashi a gidan don kawai Abban mu ya kwana a dakin innar mu kuma taga Abba ya fito ban daki da asuban farko.
Saboda ta hana idon ta barci duk ranan da Abba ya shiga wurin innan mu haka take kwana leken tagar dakin ta don ganin halin da suke ciki.
Wanan dalili ke sa Abba ko zai shiga dakin sai yaji wa,azi da nasiha abokan shi ko wani na kusa dashi akan yadda yake wofintar da innan mu har yan waje suka gane hakan.
Hakan ba abin mamaki bane sanin ko wacece uwar lantana a garin dan zaman kanta takeyi tana sana,ar tuwo tuwo.
Haka kuma take mu,amula da maza bata boye halinta har mutanen gari suka ki auren yarta data taso shine Asabe kakar mu taje ta kwasowa Abban mu ita.
Don kswai a lokacin suna dan dasawa da mahaifiyar ta har suka hada wanan alakan cewa idan Abban mu yana son lantana yazo ya nemeta da aure ko za,a dace ta haifa mai diya maza a gidan.
Bayan auren yanzu kuma ya fita a tsakanin su suka koma kamar annabi da kafiri tun bayan dataga ta haifi namiji din duk da dan ba lafiyayye bane yazo.
Innan mu tana bakin murhu tana hura wuta ta fito ta zauna a kofan dakin ta tana fadi a fakace.
Yau kuma su oo me aka samu da farar safiyan nan ake wanan duke a gaban murhu ko anyo aikene daga bariki za a sha dadi haka ?
Inna dai yi tayi kamar bata jita ba taci gaba da fadin muna nan dai idan tayi wari maji ai .
Gashi dama ko a gida a shedesu da dan hannu balle anje birni anga banza aita wawurowa ana kawowa gida.
Hakan bai mata ba ta sake fadin wasu dai sunji takaici ya ko auren fari babu har ta shiga duniya yawon banza .
Har azo anawa mutane feleke a gari a saka a canza duk da kayan zina to ai haka ba mamaki tunda tsohuwa ma ta tsufa bata san ta tsufa ba ka jaraba kullun ana makale da naji ana abu daya diya tayi da kaitai a birni uwa tayi nan da tsoho.
Allah sarki dadin abun dai da tsohon sunna tsohuwar ke makale ba mazan wasu take ci ba a titi kamar macijiyar da bata ramin kanta.
Sai dai anyi rami tayi shige ko tabi darnin makwabta ana dannan ta ana sukawa akanta saman titi da tsufanta diyata dana makwabta suna kallo.
Innalillahi aikuwa dama inna takan tara mata na kwanaki kafin ta gaji ta bata amsa koshi sai idan taji ta tabo zancen diyan tane zata samu mai zafi daya ta fada mata taja bakinta tayi shiru ta barta tana haushi.
Wani lokacin har makwabta sai sun shigo rabon ta akan tayi hakkuri ta daina idan kuma sun gaji sai tayi tayi sai ta gaji zata kyale don kanta.
Wani lokaci kuma har uwarta takan tako gidan tazo taya ta fadan suyi harsu kare babu mai tankasu.
Yau din ma da taga haka jin amsan da inna ta bata ta yafa gyalenta ta fita zuwa fadawa uwarta abinda ke faruwa harda karya da gaskiya ta kwasa ta fadamata.
Sai gasu tare sun dawo ita haushi uwarta haushi Allah ya taimaka inna ta gama girka dan taliyan hausa da take dafawa yara su karya dashi din Abba yace kuntu billahi baida ko kwandala a hannun shi da zasu karya.
Amma yana fita ya shiga dakin lantana data haushi da masifan ai ta ganshi ya shiga ban daki daga yau sai ka koma ka mannewa tsohuwar matar ka tunda duk kokarin da nake maka baka gani kai.
Halin maza sai su nan Abba ya dan fara kame kame yana rarashinta har yakai ya dauko dan kudin daya kwana dashi hannun shi ya mika mata su gaba daya don kawai ya samu ya shawo kanta kada ta gujeshi kamar yadda ta fada din.
Shine bayan fitan shi inna ta fito tana hura wuta ta ja inna da wanan masifan har yakai inna ta mayat mata da martanin da yai mata zafi shine uwarta ta shigo da masifa.
Tana fadin sai tayi karan innan mu don kazafi wai inna tayi mata a cewan ta jin fitinan yayi yawa yasa Asabe fitowa don da farko batayi niyar fitowa ba.
Ji datayi tace zata kai karan inna ga hukuma yasa ta fito tana fadin ke mai tuwo baki tunanen me yarki itama ta fada mata .
Har ta bata wanan amsa itama don haka kawai ba zata fada mata ba ai don kawai an mayar da haulatu mai hakuri a gidan tana kawar da kai ga abinda yarki jeyi mata ko yaushe.
To tsohuwar banza kin fito ki shigar matane ko me yanzy haulatun ce mutum a wurun ki tunda yarta na can birni tana bin maza tana zuwa maku nan da abin duniya yanzu sun koma abin son ki kuma ?
Jin haka da innan mu tayi ta bude labulen kofan ta tana fadin saukin abindai kafin ta fara aikatau wasu sun tafi butnin sunyi har saudiya yin dandin kasa mai tsarki basu dawo da komai ba kasan nan sai tsaraban shegu.
Idan kuma suna da uba yau a fito muna da uban su mu gani don haka kafin yata taje birni bin maza tsohuwar banza ta fara zuwa ta dawo muna garin nan da tsaraban annoba.
Yau zaki san kin tabani garin nan yau zan nuna maki ko wacece ni a garin nan inna tace idan kin tashi kisa a rufeni dan makullin ya bace iyaka ke nan.
Lokacin har yara da mata da muke makwabtaka dasu sun cika gidan suna kallo da saurare.
In dai barikin ne ai iyawace don karshe sai an koro yar taki da ciki kowa ya gani a garin nan lantana ta fada cikin jin kunya da nauyin yaran dake ihu bayan fitar uwarta don halin su ya ishe mutanen unguwa dama.
Har wurin aikin Abban mu lantana da uwarta suka sameshi suna fadin sai sunyi karan innar mu don tayi masu kazafi da cin mutuncin da ba a taba masu shiba yau.
Abba ya shiga ba mahaifiyar lantana hakkuri yana fadin ta barshi da inna dama halin innan mu yakai mashi ko ina a gidan.
Haka dai Abba ya samu ya lalaba su suka bar gidan bai dade ba shima a waje sai gashi ya shigo yana kwalawa inna dake bandaki kira .
Bata amsa ba saida ta fito ta bayan shi take fadin gata ai tana sauraren shi.
Ke don baki da mutunci yanzu har kika iya bude baki kika zagi uwar lantana a gaban ta karya suka fada wayasan inda yar taki take a birni dama.
Allah sarki hakane dama ai na sani kaima yaran ba damuwan ka sukayi ba ai tunda tun lokacin daka mikata wurin yar uwarka har yau baka taba bin bayanta kaga inda take zaune ba don an hanaka zuwa gani don a samu abun fada min.
To bari kaji malam idan ku dakai da uwar matan naka bakuyi karana ba yau ni zanyi naka a garin nan duk inda kakai min ya sai ka fito min da ita don wanan abin ya isheni.
Ni ga Allah na dogara nasan irin tarbiyan dana ba diyana don bata gaji shashanci ba a gurina balle taje tayi shashanci a birni.
Yanasu yau ke da bakin kike fadin zakiyi karana kan yar cikina a mata ya baci inna tace kwarai kuwa bello ta fadi sunan Abba ba sakaye kamar yadda take kiranshi da malam.
Mamaki ya kara kashe abba jin abindata fada sunan shi gatsau haka babu sakaye data sabayi mai don gabadaya ta birkice masu a gidan.
Wani kalon kalo suka watsawa juna kafin Abba ya kuta yana fita daga gidan inda lanta taji haushi cikin daga murya take fadin tunda har kika zageni dani da iyayyena ke kuwa sai yar taki tayo abin kunya birni an korota ta dawo maki maga ta tsiya.
Nikan unda na shige daki nabar mami na fada a falo ban fito ba sai bayan sallah isha,i koshi din abinci na fito.
A falo gaba dayan su suke in ka debe mazan da basu rigada sun shigo gidan bako a lokacin don ko hjy a falon tayi sallah bata shigo dakin tayi ba nasan saboda tafiyan ne yasa ta zauna a nan bata dawo dakin tayi sallah ba.
Banda hara ba abindaya shiga tsakanina dasu Rufaida duk da na gashesu a cikin jam,i saidai su basu amsa min ba.
Sai hjy ce ke fadin yarnan yanzu nake zancen ki a raina ina batun aje a dubo min ke a daki ko lafiya kika shige har wanan lokacin ?
Ina zancen dai ai ya wuce tunda kinji uwar ku ta tsawata kan hakan suma kina ganin su da shegen son jiki suke ta yaya zaki dauki kayan kasan ki har kiba wata wanki can.
Haba haba hjy a daina wanan zancen tunda mami tayi mana fada a kanshi dazu ba wanda zai kara bata irin wanan aikin acikkn mu ai tunda mami ta hana abata Aisha ke fadi.
To uwata hanani in fadi tunda kun shuka rashin gaskiya wa yarinya baku son a fada kuma kai kuma dai kazamai ne wallahi.
Ta fada rai a bace tana mai kawar da kanta ga kallon su sukai tsuru tsuru don mami na falon itama ta kafesu da idanu.
Rufaida na shirin mikewa tabar falon don takai kololuwar cika tana batsewa wai akan yar aiki mami tana wullakantasu don kawai taga gidanta ne yanzu dan uwan mahaifin su ya rasu yasa ake masu hakan.
Batakai ga tashi ba taji sallaman jalal yana washe baki ya shigo da ledoji niki niki a hannayen shi yakai gaban mami ya aje lodojin yana zama a kujera tare da fadin.
Wassh Allah yau na gaji da yawa mami tace da kai me ke nan fa mami tunda aka fito daga sallah yaya jack , , , ,
Bai karasa fadi ba saboda hararan da mami ta watsa mai yasan me take hararan shi dashi yace a wani yanayi i am sorry mami na mantane kin hana mu kirasa hakan ni kuma bakina ya saba da hakan tun a can.
Rufamin baki ku kun fada inagana waje jalal ka fita min a ido duk kuka bari wanan sunan ya shigo kasan nan raku saiya baci sosai.
Yana dariya yace yanzu dai mami ba wanan ba kinga ledan nan wai duk na tsohuwar nan ne yaya ya ban kudi a hado mata wai kada taci abinci da dare sai wanan din shi ya dauka nan irin can ne da tsofi sukecin wanan dadin yana magana yana zamowa daga saman kujeran yana kokarin budan ledan.
Wanan ya hana rufaida dake cika tana batsewa tashi don tun shigowan shi falon ya dume da kamahin suya irin na yan gayu ba suya na gida ba wanda yasha kayan hadin sanadarin zamani.
Hannun shi mami ta buge ya jaye yana fadin wassh Allah mami zan bude ku gani ne ai ko ya fada yana dariya.
Mikawa hjy abinta babu maici a cikin ku wurin sai idan ta gama ta baku ragowa idan zaku ci.
Haba mami ta bamu ragowan ta kuma bayan ta gama zuba mai miyau da goro zamuci salma ta fada tana kallon mami din.
Hjy da sai yanzu ta fahinci me ake nufi lokacin da mami ke kallon jalal tana fadin ya mikamata take fadin au me muka samu ne wai.
Bakiji bane hjy wai Jafar ne yasa a sayo maki wanan shine syke son su saka maki rani a ciki don suna yan kwadai.
Ja,irin miskili ya gama babautan nasa yana neman shiri danine kuma yanzu dazun fa ya gama fadin me na biyo ku yi nan nazo in sakawa mutane nauyina sai gashi shiya fara daukan nauyin kuma ?
Haka kika fada ko bari ya dawo saina fada mai wai badan Allah ya saya maki ba neman shiri dake yake ya sayo maki.
Kaji ja,ira zaki hadani fada da wanan mai kama da yan ruwa yazo ya hanani shanruwa a gidan nan ke nan.
Ya jalal yaga sun tsaya surutu mami bata sab sanda ya jawo ledan ba yana fadin bari nidai na bude don inyai sanyi bana iya cinsa kuma.
Yana bude ledan farko wani kanshi ne duk ya game wurin leda daya ya tura a gaban yan mata yana fadin ku ku dau wanan wanan kuma hjy wanan nasu ne idan sun shigo.
Ya mike ya isa gaban tsohuwar tare da ledojin a hannun shi yana fadin hjy mu muci wanan ko tace kaidawa ke nan miko min nan dagani sai yar nan da take dawainiya dani zancisa.
Kaji hjy kuma ya wuce ki bata fifike ne a ciki kilama bata taba cin suya irin wanan ba ai Nazira ta fada a daidai lokacin da suke shigowa gidan shida Jamal.
Yau kan ya wanke kanshi a wurin tsohuwar da murna da lale marhabin ta tare shi tana fadin kaga mijin arziki wanda yasan zafin iyalin shi.
Mami na masu dariya yazo gaban mami ya dan dukar da kanshi wanda kamar hakan al,adan yayan mami ne don har ya mamud haka yake mata da girman sa in zai fita ko ya shigo zai duka mami ta ahafa kansu tana saka masu albarka tare da fatan alheri a garesu.
Don tun ina mamakin hakan har nagaji don na saba da ganin hakan wurin yayan gidan maza ko Aisha da take mace kamar zata koma cikin uwar wani lokaci idan abin ya motsa mata ko yanzu tana zaune tunda tai magana da farko bata kara magana ba a wurin kowan su nakan waya suna abu daya charting ko dawa soke yi oho ?
My friend an dawo ke nan mami ta fada tana shafa kanshi tare da fadin ubangiji yayi maku albarka ya kare mun ku a duk inda kuka saka kafanku.
Tashi yayi ya nufi wurin hjy ya zauna a kasan carpet tare da riko hannun da ta dauki cinyar kaza tana ci yakai a bakin shi ya gutsura kadan kafin ya kai mata itama a bakinta .
Ni dai ina gefe zaune a kasa daga gefen hjyn ina kallon ikon Allah tare da mamin wai yan gidan mami suke kwadayin nama haka ?
Wanda nama sai an mayar da saura kitchen don sunci ya ishesu wanan wani irin nama ne hakan don idan kaga mami ta sayo nama a waje to kilishi ne zata shigo dashi mai yawa kowa yaci har a ture saura su mama kande su dauka..
Dan albarka hjy ta fada tana hadiyan naman dayasa mata a bakinta ta gutsura kowa falon na busy suna cin naman suke gaidashi dashi.
Dabi,an shine kyaluwa dan haka yi yayi kamar baiji su ba hjy ta juyo tana fadin taso mana yar nan ki diba kinyi zaune kina kallon kowa nacin abin arziki.
Saiya dan juyo ya kalleni guri da nake zaune din ya kawar da kanshi kamar ba kowa a wurin .
Na mike nazo gaban hjy din yana zaune har lokacin yayi rigingine a wurin kafanta idon shi a carpet nakai hannu zan diba Nazira tace
Ke dakata don Allah menene haka zaki saka mata wanan hannun naki mai dauda a cikin abu haka kai tsaye ba tare da kin wanke hannu ba.
Cak na tsaya daga daukan naman da nasoyi din ina kokarin mikewa a inda nake gurfane don barin wurin.
Ke diba ki wuce ya fada batare daya dago kai ya kalli kowa a wurun ba ya fadi hakan sai jamal yake fadin haba Nazira ku daina irin hakan don Allah dai.
Bazasu bari ba don da zasu bari ko ance suyi wani abu kan yarinyar nan ai basuyi ba kuma yadda nayi masu yau.
Me ake mata idan ba iya yinta ba taga yan aiki a wurin nan ne ko taga su kande na zama a cikin mune haka su ?
Nazira zan saba maki a gidan nan fiye da tsamanin ki to bari kiji zeey da kike gani daya kuke da ita a gidan nan yadda na daukeku dasu Aisha haka itama nake daukanta don ba wai aikin kudi aka kawota yiba yadda kuke tsammani.
Rokota nayi gurin iyayyen ta suka taimaka min suka ban ita a cikin mutunci sau nawa wai kuke son in fada maku hakane wai ?
Look akan yarinyar nan zan sabawa yarinya a cikin gidan nan ko wacece me yarinyar nan ta tsare makune wai haka kuke sakata a gaba ko yaushe ya fada a hasale cikin daga muryan shi dasai ranshi ya baci akejin shi irin hakan.
May be don sunga ta fisu kyaune da tsari suke kyashin ta jalal sarkin barkwanci ya fada kai tsaye yana masu dariyan kyaita.
Kai amma jalal din din don Allah kada tasa taji dadi har taji dadin raina mutane a gidan nan ta dauka wani kyaune da ita.
Garin dauko naman saboda rawan da jikina keyi na dauko gefen fifiken kazan dayasha carbej da albasa dasu maggi curry da sauran hadi namike tsohuwar na fadin baki dauki abin kwarai ba nace wanan yayi min yanzu naci abinci na bar falon ga baki daya har lokacin jamal da jalal suna cacakan ya matan a kaina.
Jalal ke fadin wanan kina ganita idan tayi clean gidan nan ma baya daukanta ke zeey fa idan ta waye ba karamar classic lady bace wurin nan.
Dakin na shiga na aje naman don naji ya fita min a rai don disganin da nazira tayi wurin daukan naman a gaban kowa.
Nima fa mutum ce kamar kowa da suke min haka don kawai ina yar kauye kuma diyar tallaka tallakama mai faci.
Ina ban daki nake wanan fadan a raina na fito ban tsaya jiran komai ba na hau kujera na kwanta har barci ya daukeni ban sani ba don ban san lokacin da hjy ta shigo dakin ba bayan sun gama hiran su a falon don ko hidimar da nakewa mami ranan ban samu yimata shi ba.
Koda mami ta rako hjy dakin ta samu ina barci bata tayar dani ba ta kyaleni hakana sai cikin dare dana falkone naga wutan dakin a kashe.
Washe gari da safema motsin hjy ce ya falkar dani na tashi nima nayi sallah na idar na zauna a wurin hjy ta shafa tana fadin in koma in kwanta tunda ido akwai barci daga haka taci gaba dajan tasbahan ta.
A daidai lokacin da nake shiga na gyarawa mami dakina falka kamar an tasheni har lokacin tsohuwar tana zaune a inda take.
Mikewa nayi ba tare danayi magana ba na nufi dakin mami din ko a nan ma itama zaune take tana azzakar din safiya.
Ban fito daga dakin ba saidana karasa komai na dawo na samu hjy ta dan kwanta a lokacin banyi dogon motsi ba wanka nayi tare da kara wanke ban dakin har na shirya a hankali duk tsohuwar tana barcin safe wanda nasan na gajiyane.
Sai bayan goma da rabi ta falka lokacin mami tayi mayawa a dakin yakai sau uku tana duba mahaifiyar nata.
Ruwan wanka na hada mata tayi wanka na taimaka mata data fito har ta shirya saiga abin karyawa an kawo mata har daki yaran gidan suna shigowa daya bayan daya suna gaida ita da kwana.
Har suka dauke kafansu sai Aishace bata shigoba nasan bata tashi bane don ita sai wuraren sha biyun rana dama take tashi barcin safe ko ma zuwa dayan rana.
Nan muka zauna muna hira da hjy don ban yarda na fita ba ko karyawa a cikin na tsohuwar na karya dashi take tambayana ni yar wani garine ?
Nace ancau hjy tace ashema yar jaharnan ce ke na dauka ko yar shiyan jalingone ke ko bauchin don na ganki da zubin fulani.
Nace innatace dai bafullata Abban kuma bazzagene shi yar nan da asalin ki haka har yaran nan suke maki wanan tsiyar haka ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GAREKU MASOYA UBANGIJI YA DAUKAKA MUSULUNCI A DUNIYA AMIN, , , ,
Banyi zaton akwai macen da zata kai sha shidda a yanzu ba wace bata san zata mutu ta koma wurin ubangijin ta ba da har za a hada da Allah da annabi ta rufe kunne da ido don rashin tunawa da Allah dayai mata rai da numfashi da take takama dashi a duniya wanda ubangiji zai iya karban abinsa duk sanda yaso .
Yan uwa mu kulla da daraja da nauyin wanan sunan biyu idan ance Allah da annabi a zatona angama da musulmi ashe abin ba haka yake ba a wurin wasu.
Allah kasa mufi karfin zukatan mu ya Allah ka bamu cikawa da imani amin kada ki karanta idan baki biya ba mai turawa na barki ga Allah shi yasan tsakanin mu dake.
Sallama akayi daga kofan dakin yayin da mu kuma dariya ya dauke muna hankali a cikin dakin don tsohuwar dariyan labarina dana fara batane ina fadin garin mu ai kauyene kuma yan garin muma kauyawane a cikin sa don kaka hajiya bata kaiki tsufa ba amma bata wanka daga jumma, a sai jumma, a take wanka tunda wai bata da miji da zataiwa wanka.
Sallama ya kara yi nice na karba a cikin raha da walwala don dan zaman mu da tsohuwar yasa na mance da duk wani bacin rai dana kwana dashi a gidan.
Dan miko min wanan kawar da wanan gurin nan sai duba can ki miko min abu kaza dauki wanan kici hakan yasa na manta da komai dake a raina a lokacin.
Wa,alaikum sallam na fada don hjy ita dariya yaci karfin ta a lokacin itama dai cikin dariyan take amsa mai haka yasa ya turo kofan gaba daya ya shigo.
Saye yake a cikin farar jallabiya mai laushi sai wani maiko takeyi ashe jallabiyar ma suna suka tara sabanin da danake masu bugu daya don duk jallabiya da farko daya nake daukan su sai zuwa gidan mami ne na fara bambanta jallabiya yanzu.
Yakaraso yana tako kamar wani balarabe dashi har zuwa kujaran da hjy take zaune sama a cikin hausan shi mai kama dana dan koyon hausa din.
Yana fadin wanan dariya haka hjy kamar an gafarta maki yau fa don nidai badon nasan iyayyen su ba sai ince su din jinin labawan asaline .
Don hasken jikin su yafi kama dana larabawa a gidan ga tsayi duk dadai shi yaya jafar din ya fisu tsayi sosai a cikin su sai jamal da jalal saidai basu kaishi tsayi ba su zan iya cewa su din kamar mahaifin su suka kwaso don ko ban sanshi a fili ba na san shi a manyan photunan shi dake falon gidan.
Don shi mutum ne fari dogo ga tsayi ga kyau kamar shi yayi kansa wurin halitta duk da ya manyata a photunan lokacin dayayi su hakan bai hana kyau shi fita ba a fili.
Hakan yasa nake kasa bambanta tsakanin su da dan nasa ko a cikin su wayafi kyau haka.
Shi yaya mamud duk da farine sol baikai yan uwanshi tsayi ba yana dai da nasa gwargwado sai Aisha da ta biyo mami sak wurin kama.
Don ba inda ta rage mahaifiyar tasu sai dai idan halin mahaifin su ne ta kwaso na rashin hayaniya dason motsa jiki don mami kan ita da alama ba mai yawan son jikibane ita don wani lokaci zan samu tanayin abu da kanta sai nazo in karbe ta.
A cikin dariya hjy ke labarta mashi hiran mu tana kwasan dariya fuska a daure ya dan dago ya kalleni tare da kawar da kanshi duk lokaci guda.
Ina tsugune nake gaidashi da kwana tare da mikewa don barin dakin duk da ina tunane a raina ina zan dosa idan na fita don gudun haduwa da yan matsalan gidan mami din yan kafi mai abu iko.
Don ni sai daga bayane ma nasan ba mami ta haifesu ba a wurin anty Aisha yadda nazo gidan na samu sunayin abu a gadarance da yadda mami ke nuna kamar itace ta haifi abinta.
Ina kuma zaki muna hiran mu kin dauko ban labari ina sauraren ki indon wanan ne ai shi nasan yanzu fita zaiyi a dakin don ba zama zaiyi ba ko kunya fada a gaban shi kikeyi.
Dawo ki zauna muyi hiran mu kinji jikata ta kaina aini kin ganni nan ina son jin irin labarin nan sosai wallahi don nima kinga daga karkara na fito ai.
Idon shi a waya kamar mayen waya ko computer dana sa mai yake fadin wani No kuyi hiran ku ni nawa nakeyi nan .
Tace dada Asabe kowa kikace sunan ta nace a sanyayye don kasancewan shi wurin nake fadin Asabe ne.
Ta nuna min bakin gado tana fadin zauna mana a tsaye zamuyi hiran haka na kai zaune a dan takure.
Yanzu mahaifiyar ki dai tana tare da Abban ki ko ta tambaya take yanayi na yacanza a hankali nace suna tare da Abbanmu har yanzu.
Saidai ba a cikin dadin raiba don Asabe tasa Abban mu yai wani auren wai don innan mu diya mata take haihuwa ita kuma bataga amfanin diya mace ba.
Shima dalilin turoni birni wurin mami da Asabe da lantana sukayi wai nazo inyi aikatau a nan don hakane kawai za a morewa diya mace na karasa ina share hawaye.
Kai ya dago ya kalleni a cikin mamakin jin abindana fada din na zancen Asabe ga innan mu da muka bude ido dashi a gidan kullun sai tayiwa inna gorin shi.
Haba haba yar nan kada ki kuka mana nasan wanan zancen yana da ciwo sosai don baku ai kukayo kanku diya matan ba wasu ma nacan suna son diya matan kamar suyi hauka basu samu ba ita tasan baiwan da Allah yai maku dayayo ku diya mata a garesu.
Abin mamaki sai naji ya saka muna baki a hiran mu yana tambayana ku nawane a wurin mahaifiyar ku da har take fadin hakan ?
Mu bakwai ne nice babba a dakin mu sai kanne guda shidda dana bari tare da innar mu a gida.
Babu ma wanda aka wanke a cikin ku ke nan tunda kece babba ashe kai wasu mutane da shishigin tsiya suke har da Allah sukewa izzigili.
Shi mahaifin ki fa yaya ya tambaya sai na dago na kalleshi don ban fahinci mai tambayan shi ke nufi ba.
Saidai na basu amsa da fadin yana nan kawai yace No ina nufin wani mataki ya dauka kan wanan zance
Da Abba baya daukan zancen Asabe amma yanzu tunda ya auro lanta kuma ta haifi na miji sai ya sauyawa innar mu damu ga baki daya a gida yanzu ba ruwan Abba damu kamar da can baya na fada idanuwana suna kawo ruwan da ban iya controling din su a lokacin.
Haba yar nan ki daina kuka kada nima ki sakani kukan don wanan labari naki akwaicin zuciya gaskiya.
Do me bataga laifin danta ba dashi yake ba uwarki diya matan sai uwarku kadai zataga laifin su ta fada a hasale.
Muryan mami ne data dawo take kwala min kira daga waje yasa na mike tsab na fita dakin da sauri na barsu a zaune da hjy.
Duban hjy yayi yana fadin hjy ashe har yanzu akwai itin mutanen nan masu halin dabba a kasan nan yadda yanzu addini ya zagaye kasan nan.
Yo jafari mai za a fasa a wurin kishin muna mata wasu matan fa kishi suke da matan diyan su kila irin hakane ya ke faruwa a gidan har wanan tsana ya shiga.
Amma idan bashi ba menene laifin haihuwan diya mace a duniyan nan ni ba gani ba kai bani kadai ba har kowa ai yanzu moriyan diya mace mukeci kaf zuriam mu ga baki daya.
Don uwarkuce tsaye da gidan ni kaina da kaganni nan na fuskanci itin wanan matsalan lokacin dana jera haihuwan iyayyen ku mata har su hudu a lokaci guda ban haifi namiji ba.
Sai dai ni kishiyace ta goranta min hakan bawai uwar miji ko wani irun wanan zancen yana da shiga zuciyar bawa don yanzu Allah kadai yasan halin da uwar yarinyar nan take cikin dan bakin ciki kan tana ganin sa.
Amma idan tayi hakkuri wataran sai labari yau ba gani danayi hakkuri na shanye hakan ba uwarku sai Allah ya daukaka muna ita ta zama muna zakara a cikin mazan.
Yau zeey mami ta fada ki dauki wanan kikai dakin ku na hjy ne ki kula da bata tana ci lokaci lokaci kinji.
Nace to mami ina daukan ledan da ban san ko na meye ba a cikin sa har na juya zan tafi take fadin zeey na juyo da na,am mami sai kuma ta kasa fadin abinda zata fada tana kallon fuskana da mamaki ta furta.
Zeey kinyi kuka ko zancen jiyane har yanzu a ranki ko kuma wani ya kara tabaki gidan nan yanzu kuma ?
Kai na girgiza da sauri alaman a, a tace to me akai maki fuskan a haka ko gida kika fara tunane kuma.
Nace a a a sanyayye ina juyawa sai ta bini da kallo mikewa itama tayi ta biyoni baya ban san mami na bayana ba sai dana shiga dakin da sallama naji mami na fadin a a ashe kana nan tare da hjy ne yanzu fa nake shirin zeey ta kira min kai a waje na kira layin ka bakai picking ba.
Yacs OK mami nabar wancan wayan daki da zan fito ai nazo gaida grany ce da kwana sai kuma na zauna muna hira.
Wanan yarinyar na gani kamar tayi kuka ai shine na biyota in tambayeta ko wani abin kuma akai mata na ganta haka ?
Ba wanda ya tabata tun safe muna dakin nan tare da ita nasan kukan da tayine kan labarin yan gidan su da take bani yanzu.
Ta labarta maki jahilcin kakarta ke nan ko don shine damuwan ta a zuciya kullun Asabe ta tsani mahaifiyar su don kawai ta haifesu a diya mata.
Shine fa yanzun nake mata musali dake kika kirata irin wanan mata da yawa suna haduwa dashi a rayuwan su in Allah ya hadasu zama da mace mara imani ga ubangiji har ma a cikin masu ilimin akwaisu sosai har gobe .
Na fada mata ta kwantar da hankalinta muddin ina raye a duniyan nan sai tayi ilimin data tallafi gidan su insha Allah .
Asabe zata gane diya mata ma mutane ne kamar kowa ba abin wullakantawa bane a gida.
Mikawa hjy ledan dake hannuna nayi ina fadin mami ne tace in shigo maki dashi nan nakine na fada ina ajewa gaban hjyn nata a cikin ladabi.
Me muka samu kuma nan ta fada tana kokatin budan ledan dake gaban ta lokaci daya ba komai bane sai goron ki da sauran tarkace dazaku bukata a nan dana san kina amfani dashi mami ta fada.
Mami goro kuma ya kamata ace ta bar cin goron nan a yanzu fa don jikin tsufa daya kamata zai iya mata illa wanan goron haka.
Ungo naka da zai mun illa da tuni yayi min tun kan a haifeka nake cin goro na a duniyan nan gani ko garau kana ganina.
Allah baki hakkuri ya fada tare da mikewa tsaye yana gyara rigar shi hjy tace tafiya zakayi kuma muna zaune muna hiran mu ?
Na gama hiran ai ku karasa hiran ku damani ai ba dani aka fara ba ya fada yana ficewa tace miskili kafi gaban gayya wanan wanan zan so naga macen da zata iya zama dashi haka.
Mutum kuna zaune kalau ya birkice maka lokaci guda kuma ya hana ayi magana don tsaban miskilanci.
Fita yayi daga dakin ba tare daya kara mata magana mami na gefe tana murmushi mama kande ne ta shigo dakin da sallamanta muka amsa take.
Fadin mama ga abinci an gama na kawo maki da cewa hjy tana fadin sannu sanu yarnan sannu da kokari har kun kare na rana ban dade da cin na safeba ai.
Ai kande akwai kokari shiyasa nake son daukesu mu koma Abuja don gwarawan nan sun isheni basu iya irin cimar muba nan sai kalar tasu abincin.
Saidai kuma ina tunanen wanda zan bar yaran nan dasu a gidan nan don baka barin ya mace ita kadai a gida.
Yo da kin fada tun bamu taso ba ai da anyiwa ladidi magana me take a gidan banda yawon bin makwata sai tazo ko ta zauna dasu nan kinga an rage mata ma wahala ai.
Mami tace indai ya ladidin zata yarda hjy ai mata magana kafin mu wuce in sani don in tura su kande gida suyi sallama da mutanen su asan zasu tafi.
Zan kira yayan ku in sheda mashi yai mata magana aji me zatace wanan ai ragewa ladidi nauyi ne babba.
Kande ko baku zuwa mu koma Abuja mami ta tambaya sai kande din tace yo hjy ko ina kikace mu tafi aini mai bin umurnin ki ne.
Yafi mun zama nan da yaran nan naki da basa jin magana na gara dai ina kusa dake yafi dadi ta fita tana murna tare da fatan Allah yasa a tafi da su din.
Lokacin sallah yayi mami ta bar dakin aka barmu dagani sai hjy sai bayan mun idar ne muka zauna cin abincin rana lokacin ne kuma anty Aisha ta shigo gaida hjy da kwana.
Tana wani daure fuska don tasan hjy zatai mata tsiya nan dai sukaita barkwancin su kafin Aishan ta juyo tana fadin .
Zainab yanzu ba a ganin ki tunda hjy tazo na hadiye abincin dana saka a bakina ina fadin dazun na lekaki har sau biyu in gyara maki daki kina barci.
To ai yanzu na tashi ta fada nace bari gama naje na gyara maki sai hjy tace ke arr ke kan anyi malalaciyar yarinya a nan sam baki biyo halin uwarki ba ke kan.
Don Allah hjy ki rufa min asiri kafa mami ta shigo ta sakani gaba banda abinki don kawai ta gyara min daki shine wani abu.
Yanzu ke haka za a kaiki aure ko gyaran daki baki iya ba kina haka tace wai hjy wa ya fada maki ban iya ba kawai dai ban samun lokacin hakane a tare dani.
Haka rayuwan ke gudana yanzu zan iya cewa na samu sauki sosai iyakata in shiga dakin mami in gyara sai na anty Aisha sai bayan kwana biyu kuma a ce in gyarawa yaya dakin shi yayi datti.
Su Rufaida iyaka ta dasu gaisuwa in suga dama su amsa in basuga dama ba su kyaleni sai ko idan na gilma idan ba mami kusa su sakar min magana mai zafi sai dai kawai in hadiye ban fadawa kowa kamar yadda mami tace in fada mata idan sun min wani abu.
Ya safiya ma zuwanta biyu da muka zo tana wuni gidan a karshe kuma su kwasa da mami su fita don tunda mukazo da wuya mami ta zauna a gida.
A bakin Aisha nake jin wai kafn mu tafi za a karrama mami nan jahar ta ita da wasu manyan jahar da suka samu mukamai shine dalilin ma da zamu kara sati daya nan gaba.
Nikan naga sai manyan mutane ke shigowa suna fita gidan maza da mata suna ganawa da mami wani lokaci da yaya mamud don kome mami zatayi shine gaba wuri aiwatarwa a gidan sai dai shi baida daure fuska iri sauran fuskan shi a sake yake ko yaushe gayin ba,a da raha.
Sai ince wanan shirin dinner kamar yafi wanda aka hada masu a abuja haduwa don irin shirin da naga anayi da kudin da ake fitarwa.
Don kawai wana shagalin da za ai mata ake wanan barnar da kudin nake fadi a raina sai ga hjy itama tana fada kan hakan.
Andace rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya har gashi ana gobe buki sai faman tanadar abinda zasu saka babba da yaro sukeyi a gidan.
Ina kallo sai kiyasta abubuwa nake a raina idan naji suna ihun da shewa yasu yasun a falin har anty Aisha da yanzu kan wanan abin takan dan zauna tare dasu wani lokaci.
Da farko hakan bai damuna abu ga mace kuma mai karancin shekaru irina a lokacin don haka na saka damuwa har na gaji na bakaina lafiya danayi wani tunanen cewa kilama badani za a tafi wurin dinner din ba kamar wancan na Abuja da yaya ya taimaka min ya tafi dani naga shagali kuma na samo abin bukin da har yau nake boyon su in kaiwa innar mu a gida idan zan tafi.
Muna daki da hjy ta gama cewa in bata ledan goro taci na dauko mata na zauna ya shigo dakin suka fara gaisawa ni dai banyi gigin gaidashi ba don ko na gaidashi din ba amsawa yakeyi ba.
Bai dade da zama ba sai ga Aisha dakin tana fadin hjy ni zan fita zuwa gyaran kai hjy tace shi jan ma har sai anje gun gyaran shi kamar wata kafira can dake ina dai irin gyaran kafirai din nan kike nufin zuwa.
Kaji hjy kuma da wani zance bros ni zan tafi daga inda nake bansan lokacin danace anty Aisha nima zan tafi.
Hjy ta jiyo inda nake tana fadin kema zaki tafi ai maki wanan banzan gyaran kanbna zamani yar nan a cikin mamaki take magana .
Ballema ina zan tafi dake haka zainab don me ba zaki da ita ba ya fada fuska daure karbi nan kuje ai mata itama.
Hjy tace balle yau daine da tayi sha,awan wanan abin ai, ina nan kuke ta sha,anin ku iyakarta ido ko dinkin nan bata samu albarkan ai mata shi ba gidan nan ina kallon hankalin iyami duk da aiyuka sun mata yawa.
Har dai muka fita daga dakin bayan ya cikawa Aisha hannu da kudi masu yawa da suka sani mamaki a cikin raina.
Aisha tayi mamaki kwarai lokacin da aka bude kaina da kullun yana cikin katon hulan da nake dunkule gashina a cikin sa ko kafi aula dubara baka taba ganin gashin kaina a gidan mami.
Don haka ba wanda yasan wanan sirin dana barwa kaina sani ni kadai ba a gidan mami ba kwai ko a garin mu inna tace kan dunkula min a daki da dare.
Aisha na kallon ikon Allah wayan ta yayi kara ta dauka ta kara a kunnen ta ni sai naji tana fadin to yaya daga nan din zamu wuce can insha Allah.
Ashe ya Jafar ne ya kira ta ya umurce ta kaini wurun sayar da kaya a zaba min don hjy ta fada mashi ba a samu yu min dinkin fitar bukin bani don mami bata zauna ya kara da fasin kin san kuma tunda hjy ta fadi dole ayi basai mami ta sani ba tunda aiyuka sunyi mata yawa ranakun nan .
Muna gamawa driver na waje na jiran mu don bata jan mota ita saboda mami bata yarda da hakan ba wai bata gama sanin garin ba.
Ina mamaki idan ta dauko kayan yadda take gwadawa a jikinta kafin ta gwada a nawa jikin kayane masu kyau kala biyar babu na yarwa a cikin su.
Ina kallo ta biya bayan ta hada da jakka da takalmi ko wani kayan muka dauki hanyan gida mami ko sai kira takeyi wai mun dade a waje ga hjy na fadan haka kuma.
Dakin ta muka shiga da komai da muka sayo na wuce zuwa dakin mu ina shiga hjy fada sosai ta hau ni dashi wai na biyewa Aisha munyi dare a waje.
Kala bance ba don ba dabi,a na bane babba na magana ina bashi amsa lokacin sai bayan mun idar da sallah magariba har isha i har lokacin na kasa sakin jiki a dakin har hjy ta kare abinda takeyi ta juyo inda nake tana fadin
Yi hakkuri yar nan kin san garin kaduna ba kamar sauran garuruwa bane girma ga kuma yan daukan amarya a sasssan shi.
Shine yasa kukaga hankali bai kwanta ba don Allah ku daina fita kukai yamma garin nan.
Hjy kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zamu karan hakan ba tace ya wuce a cikin wani sauti dake nuna bacin ranta har lokacin.
Ni dai nayi shiru gefe daya nasha jinin jikina nasan tunda hjy ta hasala haka damu na mami sai yafi nata zafi.
Aikuwa ban gama tunane ba mami ta shigo dakin fada sosai mami tayi min a dakin kafin ta juya ta fita .
Duk sai naji ba dadi a raina duk da nasan ba nice mai laifin ba amma kuma anga laifina a hakan ko sun mata da ni yar rakiyace kawai.
Sai washe gari na samu hjy ta dan sake mun fuska muka koma daidai a dakin da ita har tana jana da hira tana fadin wanan gyaran kan danayi ya kara fitar min da suran fuskana a fili.
Yar nan ashe haka kike da kyau kike munanta kanki baki gyara don Allah ki rika gyara kanki kina kwalliya kina fitar da suran ki waje.
Ni dai sai dan murmushi nakeyi ina jin dadin yadda tsohuwar ke yabani koba komai dai na samu wace ta nuna min kauna nima kamar kowa.
Hankalin kowa ya dauke gaba daya a gidan ma kuma cike yake da mutane don haka na makale daki tare da hjy sai jefi nake zuwa in leka dakin mami indanyi wani abin.
Karfe bakwai kamar kowa jira yake yayi don dai shiga wanka akeyi ana shiryawa saiga anty Aisha ta shigo tana fadin ke zainab na manta da kayan nan ai da sauri na dago ina kallon kayan da take magana akai.
Kayan jiyane dana rakata ta sayo take miko min da sauri na karba ina fadin Anty nikika sayawa dama ?
No bani ba ya J ne ya bada kudi a saya maki jiya bayan fitar mu ai mantawa nayi na baki tun jiya wanan tsohuwar tasa mami na muna fada kawai kamar yara kanana ne mu.
Nikan banbi ta nasu ba hankalina yana gurin kayan duk na rikice don murna har ta gama ta fita ba,a jima ba ta aiko kirana nazo.
Da sauri na mike nabar hjy da muke kallon kayan a dakin mu tare na nufi dakin Aisha watace ke mata kwalliy a fuska ina shiga taks ce min zauna a gyara maki fuska ba tare data dubo in danake ba.
Wurin na samu na zauna saiga mami ta leko tana fadin kin san fa tare dake zan fita ki shirya ku fito mu tafi haka yasa akaiwa anty Aisha a gurguje ta shirya ta fita ta barni a dakin da mai kwalliyan.
Ina mamain yadda mai kwalliyan ta zauna ta shiryani kafin in fito gidan har ya koma shiru duk an watse zuwa wurin buki.
Raina naji ya baci ina raya ni yanzu wa zanbi kuma tunda wayanda na sani sun wuce sun barni a gida ba tare da kowa ya kulani ba.
Rigar da mai kwalliyan ta shirya ni aciki nake faman tatarawa don kada in fadi kasa don yayi min dan tsawo saidai tace dana saka takalma zai zauna daidai a jikina .
Har tafiyan da zanyi da yadda zan rike jakka ta nuna min ni dai sai dariya take bami a raina ina fadin wa zai tsaya kallona a wurin balle yaga tafiyana.
Takon takalma da kamshin shi ya dawo da hankalin mu surin da muke jiyo takon ya fito naji matar na fadin sir mun gama you can go now.
Thank you yace da ita nikan na nufi dakin mu tunda naji sun fara magana ban tsaya ta kansu ba tunda naga mai tafiya dani yau ko bai amsawa zanyi kundun bala in daure in tambayeshi ya tafi dani.
Sai gashi dakin yana sallama hjy ke fadin a,a miskili kafi gaban gaiya ba,a fita ba ashe yace sai yanzu hjy ko munyi sauri zuwa ba farawa zasuyi da wuri ba.
Ke fito mu tafi ya fada fuska daure hjy tace dan albarka kamar ka sani yanzu ta shigo tana min korafin an tafi an barta har ina shirin kiran uwarku ta turo a dauke ta yanzu.
Mun tafi sai mun dawo ya fada ba tare daya tsaya ya bata amsa ba don da alama sauri yake kada ya makara a wurin taron.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
UBANGIJI ALLAH KA SADAMU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN RANAN KA KAREMU DAGA DUK WANI ABIN CUTARWA DUNIYA DA LAHIRA AMIN.
Ba a karanta min labari idan baki bani dan na saka data ba don posting idan kin karanta na biki bashi zaki biya.
Gabana ya fadi don jin abinda ya fada ba shiri na mike nabi bayan shi saida hjy tace takalman fa na dawo na saka na dauki dan jakkar hannun na rike.
Tsaye yake a falo na zata zan gansu da wanan mai kwalliyan sai naga babu ita babu labarinta wurin.
Sai shi kadai yana kallon kofan fitowa jin takona tafe ya fara tafiya saida ya fita daga kofan falon yaja ya tsaya wuri daya.
A nan na same shi ba tare daya kalleni ba ya fara magana kamar haka ki kama kanki ki natsu fiye da yadda kowa ya kama kanshi a wurin banda kauyanci da kalle kale duk abinda nayi maki ban son musu ko gardama so be cool kamar yadda na umurce ki.
Duk da hausa yakeyi wai saidai kamal turanci yayi yawa ga maganan shi amma ba laifi ga dan turancin dana iya ina fahintar shi hakana.
Ma,ana dai akwai abinda ke shirin faruwa a wurin yake min indirect akai wanda na kasa fahintar hakan a raina.
Har ya fara tafiya naga yaja ya tsaya sai na tashi karo dashi wani wawan tsuki yaja yana fadin idan kikai min wanan wautar taki wurin nan tun acan zan balbalaki.
Saboda haka kada ki bari in kara wuceki tunda ba dodo nake ba kuma ba sauri nakeyi ba.
Ya takalman kafanane ban iya tafiya dashi don ban taba saka irin shi ba kallon kafan nawa yayi ya kawar da kai don gaba daya shigar tawa ya tsorata shi wurin sai take ganin bani bace a gaban shi.
Kamar yadda yace hakan muka jero gabana sai faduwa yake min kamshin shi kamar a hancin na aka zuba turaren.
Security din shi suna hango mu mun fito sukayo kan mu suna gaidashi tare dani tunda sun gani tare dashi.
Umurni naji ya basu cikin turancin da baikai can ba suka amsa da yes boss da sauri wani daga ciki ke bude motar maimakon ya shiga sai kawai naji ya riko min hannu sai da gabana ya fadi uku uku don tsoro da bazatan da yai min lokacin .
Kofan da zan zauna ya nufa ya bude min na shiga ya ya rufo a hankali sai ya juya ya nufi dayan bangaren da daya daga cikin security din ke rike da kofan yana shiga aka rufe motar suma suka shiga nasu.
Mami dake zaune cikin taron duk rashin ganin shi hankalinta bai kwanta ba duk da ga sauran yan uwansa a gurin.
Table daya aka ware mata daga ita sai diyan ta sai anty Nuriya da ban san da zuwan taba a gurin, kujera biyu ya rage shine kujeran da Jafar zai zauna tare da matar dayace wa mami yau zai nunawa kowa a gurin wanda mami ta rigada ta gama sanarwa MC ya fada tun dazun kuma yake faman sanar da yau dan mami din nan matashi da duniya ke ji dashi saboda ilimi da nagartan iya sarrafa computer zai bayanawa kowa abin kaunar shi.
Haka yasa mami zaran ido kadan kadan ta kalli hanyar shigowa don ganin bai karaso ba yau dai tana son ganin wanan yar mai sa, a haka a duniya da har ta iya sace zuciyar danta dake gudun mata.
Wanda har ta fara zargin kodai aljannu ne suka aure shi bata farga ba don duk yar data nuna mai sai yace batai mashi ba shi.
A lokacin kuma shima yana faman tunane a ranshi ne yadda mutane zasu dubi zabin nasa yadda aka kwallafa rai da cewa diyar wani kusa zai kawo ko diyar wani hamshakin mai kudi a kasan .
Yes yasan ba mami ba kowa ma a wurin zai iya ganin rashin dacewan su to saboda me ita din ba mace bace kamar kowa tunda mami ita ta matsa mai sai yayi aure .
Wanan itace kadai zai zaba ya zauna lafiya a rayuwan shi don zabin mami sam yasan ba zasuyi daidai.
Lumshe ido yayi yana gyara zama kodai ya fasa wanan shirmen da yake shirin aikatawa ne idan hakan zai kawo masu matsala da mami.
Shin meye laifin shi har in ya gabatar da wanan yarinyar a yau a matsayin macen da zai aura.
Itace yaji rashin ya kwanta da ita a matsayin abokiyar rayuwa kamar yadda mami ke shan fada mashi kullun idan tana masa nasiha yayi aure.
Shi gaba daya ya yarda da hakan har zuciyar shi da gangan jikin shi ya amince da wanan zabin nasa matukar zasu zauna lafiya.
Yasan yarinyar is pretty shi ba wanan yabi ba nashi tsarin ne a hakan aure dai akace yayi kuma ita din zai aura yasan ta hanyan shi yarinyar itama zata zama wani abu a duniya muddin dai tana tare dashi.
Ya dan muskuta kadan tare da gyara zaman shi yaci gaba da tunane yace a ransa yasan ko bai samu goyon nayan kowa ba zai samu na hjy matukar ba mamice ta zugata ba funda itace ta fara kawo mai wanan idea din a falonta.
Yasan amsan da zai ba duk wanda ya tun kareshi da rashin yardan wanan zabin nasa duk na kowa bai damesa kamar na mami ba.
Ko ita din a yanzu ya tanadi hujjojin da zai bata idan idan har ta nuna bata yarda ya auri yar nan nata ba.
Ido ya kara lumshewa a hankali yasan dole akwai aiki ja a gaban shi ba shi kadai ba yanzu har wanan yarinyar ya jefata a cikin dabon tashin hankali don dole ta fuskaci kalubali daga mutane da dama daga yau .
A yanzu kan yayi niyar hakan bayajin kiran kowa ko dakatarwan wani bai damu da duk abinda wani zai furta akan hakan da zaiyi ba.
Ya shirya daukan duk wani rigiman da zai taso na barazana a kan mu duk yadda mutane zasu kalli abinda zai aikata din shi a shirye yake .
Wurin ya hadu da manya da yara da masu ruwa da tsaki a gwaunati tarone na yan boko da suka amsa sunan boko a wurin.
Haka motar ta danno kai a cikin get din wurin inda hankalin yan sa ido ya dawo garta akwai daya a gaban mu sai wace muke ciki a tsakiya dayana bayan mu ma,ana dai sun saka mu a tsakiya ke nan.
A daidai lokacin da motar ta tsayane driver ya fita da sauri sai ya rage dagani sai shi a motar .
Ya dan ja lokaci ba tare da yai magana ba sai can ya danyi gyaran murya yana fadin ke ina son ki kara saurarena da kyau kiji me zan fada maki.
Na dan daga kai a cikin tsoro kamar kadangaruwa ya furzu wani iska kamar abinda zai fada ansashi ya fada dole ne lokacin.
Ya fara magana a cikin muryan nan nasa mai fidda wani irin amon sauti ya fara ratsa kunnuwana.
Na fada maki tun gida wanan wuri akwai yan uwan mahaifina akwai na mahaifiyan mu kin sa wasu wasu baki sansu ba.
Don haka duk abinda wani ko wata zasu fada maki iyakarsu dake murmushi kada ki yarda ki wani abinda zai ba dani a gurin duk yadda nace dake haka zakiyi.
Zanso idan mun zauna zandan rika jan ki da hira ke kuma kina murmushi a cikin wayewa kada ki yarda ki nuna min kauyancin ki a nan.
Idan kinyi abinda nake so kin taimaki rayuwan ki har na yan uwanki nan gaba sai duniya tasan da diya mace ma yace kamar kowa.
Yana fadin haka ya dan yun kura kamar zai tashi daga wurin dai kuma ya dawo ya zauna tare da fadin nasan mami zata bincikeki idan mun dawo gida kice da ita ni kike so idan kuma kin ki ruwan ki wanan duk abinda mami zatayi ki nuna mata ni kike so.
Yana fadin haka ya juya ya bude motar ya jefa kafanshi daya waje tare da juyowa hana fadin ki dakata an fito in bude maki motar aikin ki ya fara daga yanzu ke nan.
A zuciya na amsa cikin damuwa da tsoron me haka ke nufi ke nan ga yanayi ya canza a lokaci guda duk murna da daukin da nakeyi in shiga wurin bukin inga irin kallon da su Rufaida zasu min sai naneme shi na rasa don yadda nake jina kamar wata mara lafiya dani.
Daga haka ya fita a motar ya bani gabana na faduwa don har lokacin na kasa hada maganan shi wuri daya in gane me yake nufi da hakan.
Kayan jikin shi kawai abin kallone don ina kulla yana sha,awan fararen kaya don duk kyau tufafi farin kala zai saka a jikin shi.
Yau ma rigace da wando da ban san ko na wani yarene ba sai yar karamar hula fara mai zagaye a kanshi rigar tana da aninaiya a gaba manya dasu har uku sai wani adon zaiba na manyan zane da akaiwa jikin rigar.
Idan nace wurin taron nan gaba daya ba wanda yakai haduwa banyi karya ba don yadda kyaushi da kayan jikin shi suka kara haska wurin.
Don yayi matukar kyau yau fiye dama kullun ko dan yau adon buki yayi ya kara haskawa haka oho sai na nemi nawa kwalliyan na raina kaina a wurin.
A hankali na fito daga motar tsikar jikina yana wani tashi yarrr daga kaina har zuwa kafana dole badan naso ba muka jera har muna hada kafada a yadda muke tafiyan.
Da sauri na dan jada baya don yadda muka manne mind your self OK ya fada ba tare dako na bayan mu sunji yai magana ba.
Buki bidiri birede wurin ya cika ya batse don tun daga ganin haraban kai ma kasan yau babu kama hannun yaro sai dai muce Allah sa a watse lafiya.
Saida muka dan tsaya a wajen na yan mintina kafin a bude mu shiga kamar an bada sanarwa shigan mu don idanuwan da sukayo kan mu can.
Masha Allah mai sanarwa ya fada kunsan kaduna da izala ko dan gala yana izala kaduna kowa sunna Allah yasa muga Annabi Allahuma amin.
Kamar in shige kasa in nutse dan kunyan abinda mc din ke fada a kanmu da shigowan mu hakan ya kara jawo hankalin kowa gare mu.
Tafiya muke guda guda wanda zai nuna muna inda zamu zauna yana gaba security din shi suna daga bayan mu.
Kwalliyan da gyaran da mai kwalliyan tayi min yasa basuyi saurin gane nice ba kunsan yadda kwaliya yanzu ke canza siffan mutum lokaci daya tundai in an hadu da wace ta iya tsarawa.
Haka muke ta tafiya kafada da kafada har zuwa wanan table da aka tana da don mami da iyalin ta a wurin.
Tunda naga yan gidan na soma kokarin sunkuyar da kaina kasa don nauyi da kunyan su daya kamani lokaci daya saboda kallon mamakin da suke muna gaba dayan su.
A, a, a ya J yau yar mami ne haka ka, , , , hannun daya daga mai yasa jalal ya kasa karasa abinda yai niyar fada sai ya zagaya ya ja min kujera tare da dan nuna min in zauna.
Nakai zaune a hankali godiyana yau ga Allah da baiyini mai garaje ba sai sanyin jikin nawa a yau yaba da kala a wurin.
Saidana zauna ya zagaya ya zauna a dayan kujeran a daidai lokacin da mc ke fadin yanzu dai kujeran hjy iyami ya gama haduwa tare da sanar da shigowa ya Jafar da bayanin ko waye shi da kuma inda yake aikin sa sai kuma ya kara da fadin.
Sai bride to be insha Allah kamar yadda kuke ganin wa yan nan masoya sun shigo muna da haske mai haska gidan kowa a wurin nan.
Ya jafar ya dan rankwafo inda nake yana fadin kinji me mc din nan ya fada game damu ko ?
A dan razane na dan sake murmushi yake na bude bakina da mai kwaliyan nan ta fesa min wasu abubuwa tare da wani sweet na tsotse tun a gida sai hakan yasa bakina fitar da wani kamshi mai ma,ana har yana jin shi a hancin shi lokacin.
Sai ka dauka kai dake kallon mu kaga masoya na asali a wurin yadda muke mami kan imani ya hanata magana da kawar da kai daga garemu.
Ba mami ba har yaran ta da muke zaune gaba dayan su sun kasa boye mamakin su a wurin ;
Hakama sauran kujerun dake kusa dana mami din inda yan uwane da abokan arziki suke zagaye damu a wurin kowa imanin ganin hakan.
Rufaida tunda salma tace waike baki ganeta bane zee ce yar mami fa yarinyar mami dai da muka bari a gida.
Ai bata san lokacin data mike tsaye ba tana fadin kutumar uban nan zeey zeey dai zeey yar aikin mami dai.
Amma wai yaya hakan ya faru dama yarin yar nan haka take ashe ?
Shike nan dama Ruby ta fadi hakan gashiko yanzu hakan ya tabbata muna nan shekara da shekaru muna dakon wahala ashe ?
Yau ga wata yar kauye mara asali da tushe tazo ga banza ta sameshi a saukake a wanan lokacin muka danyi wanan magana Rubby tace ku duba ku gani wallahi soyayya sukeyi ki duba yadda suke nuna kauna a gaban mami.
Kai haba ina wallahi sam sam wallahi ina hakan ba zai taba yuyuwa ba muna zaune wata banza kamar zee tazo ta kwace muna shi.
Tunda kowa wurin nan cikin ku zaman jiran ya zabeta takeyi haka kawai zamu kyale muna kallo wanan yarinyar kauyen ta rushe muna plain din mu.
Humm yazu na yarda da zancen ki Rufaida yarinyar nan matsafiya ce ta sace zuciyar mami yanzun kuma ga wanda ko a zato bamu taba kawo hakan ba a ran mu wai yaya J zai kali wanan banzan yarinyar yar aiki ya kyasa.
Wallahi da sake sam hakan ba zai taba yuyuwa ba kan sai dai inda wata manufa yazo da ita wuri nan wanan kan na yarda kai koma dashine wanan yarinyar ta gama shammatan mu yau.
Da hannu aka kira Nazira daga table din da iyayyen su mata ke zaune ciki harda uwar nazira din dake zaune da matan yayyun ta a wurin.
Tana zuwa ta dan duka dafata matar tayi tana fadin wai wanan yar yar gidan waye a garin ko kuma a kasan nan ?
Wanan mama baki ganeta bane zeey ce yar mami mawa mami hidimar nan muma abinda mukewa magana yanzu ke nan a can.
Mami tace Jafar wai me nake ganine nan haka meke shirin faruwa ne wai haka ta tabaya tana tsure shi da idanu babu ko kakautawa a wurin.
Please mami kada kiyi wani motsi a nan idan mutane yana a kan ku yanzu don Allah mami kibar komai har a koma gida.
Jafar din baiyi magana ba sai murmushi yakeyi yana fadin surprise mami aina fada maki zan baki mamakine da zabina a yau ko ?
Please ya J gaji me ya mamud ya fada ai so a daina wana maganan a nan please Aisha ta fada kanta na duke kamar ba itace ke magana ba.
Daga inda Nuriya ke zaune kusa da mijin ta take fadin wai mamaki a nan kuma aka kare gun yar , , , ,
Hannu mami ta daga mata yasa tayi shiru bata karasa maganan da zata fada ba lokacin taja bakinta tayi shiru.
Koda aka kira mami tashi tayi friends din ta suka mara mata baya sai da ya bari an dan rage muka tashi zuwa wuri mami tayi niyar juyawa tabar wurin kafin mu iso saida wata kawarta ta dan rada mata kada tayi hakan don Allah.
Kudin daya saka min a yar jakan hannuna nima na bude jakkan ina likawa mami din ya dan rada min zakace mudin wasu masoyane na gaske sai ji mami tayi mun rungumeta a lokaci guda.
Masu photo suka shiga daukan mu a cikin karfin hali mami ta rungumomu a jikin ta don kawai ta kawar da hankalin kowa ga zargi komai a wurin kanmu baki daya.
Saidai na ciki na ciki a zuciyar mami don in ma wasa jafar yai mata haka dani wasan yayi yawa haka don hankalinta ba karamin tashi yayi ba da ganin hakan.
Tsoron ya Allah shine kada wanan abin ya zama gaskiya ga jafar don zuwa yazun bataga alaman wasa a idanun dan nata ba yau.
Daga inda nake na dan dago ido na saci kallon mami din dake tsaye suna magana da wata kallon da taimin yasani jin wani irin ba dadi a raina.
Haka yasa na fara shan jinin jikina gabana sai faduwa yake uku uku riko hannuna naji anyi daga bayana yasa na dago da sauri yayane dan rankwafo yana rada min zaki gaisa da abokainane gasu can .
A haka muka bar wurin yana rike da hannu na har inda ya barsu kai maginet wanan irin zabin naka a ina kashiga kasan nan ka samon wanan pretty girl din.
Suka shiga wasa shi duk su ukun yana tsaye kimkam ko murmushi baiyi kamar an tsayar dashi a wurin dole.
Muryan wani daga cikin su ke fadin dole mc ya bamu fili mu gwadawa duniya farin cikin mu da zabin ka.
Bai tsaya jirab komai ba ya nufi wurin mc tun kan ma ya dawo inda muke mc yasa muna wakan tare da sanarwa zamu fito fili abokan JM nason su nuna mai farin cikin su da wanan ranan.
Ance ana buki da dollars ranan koda bansan darajan kudin ba nasan masu daraja ne wanan kudin yadda wurin ya dauki ihu ga baki daya ya jafar yana rike dani da hannu daya.
Dayan hannun kuma yana cikin aljihun wandonshi muke takawa a hankali sai photuna ake zuba mana babu kama hannun yaro.
Sai daya gaji yaja hannuna ko ya fahinci ina gab da bashi kunyane don kiris ya rage in duka in cire takalmin dake kafana kada in fadi.
Daurewa kawai nakeyi a hakan sai gashi yaja hannuna mu fita daga hilin wasa bama nan ba kawai gaba daya dakin taron muka bari lokaci guda security dinshi na biye damu duk inda muka saka kafan mu a wurin.
Maroka suka sakashi gaba yana rike da hannu na har muka fice daga dakin yayin da suka dan sarara muna ke nan.
Wani iska mai sanyi naji ya dokeni sai da nayi wani irin ajiyan zuciya kamar an gafarta min a wurin.
Mota muka shiga ba wanda yai magana a cikin to nima me zance nida nawa umurni kuma in aiwatar don dole na.
Sai da muka shigo unguwar ne ko ina yayi tsit alaman dai dare yayi sosai a lokacin duk mutane sun shige gidajen su.
Mota na tsaye kofan gidan mami din ana jiran maigadi da akewa horn ya bude get din gidan naji yana fadin kin taka matakin farko a cikin shirin mu.
Yanzu saiki shirya mataki na gaba shine amsa tambayan mami a gareki kaina na fada maki abu daya nake so dake shine.
Idan mami ta tambaye ki a kaina ki fada mata nine nace ina son ki nasan zata tambayeki ke kina sona ko bakya sona ?
Kada ki manta da amsan dana fada maki dazun ki basu idan sun maki wanan tambayan.
Kai na gyada don ba bakin bashi amsa don duk a cikkn fargaban abinda zai faru idan mami ta dawo nake yi.
A kofan shiga gidan ma mun dan jima ana buga kofan kafin lami ta bude mana daga ciki don su aka bari jiran gida dakuma hjy dake dakina.
Har dakin ya kaini tsohuwar na zaune saman sallaya taji shigowan mu take fadin a, a har kun dawo ke nan eeh gatanan na dawo maki da ita ya fada yana wucewa bai yarda ya tsaya a dakin ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
UBANGIJI ALLAH KA KAREMU DAGA SABA MAKA TAKO WANI HANYA A RAYUWAN MU ALLAHUMA AMIN, , , ,
Gaba na faduwa ina tsaye ban iya gusawa a inda nake ba tunda ya bar dakin jin muryan hjy ce data juyo gareni tana fadin.
Yar nan lafiya kuwa hawaye ne yazo min lokaci daya nayi karfin halin girgiza mata kai ina daga kafa da kyat nace ba komai hjy.
A cikin karfin hali na karasa cikin dakin ina kokarin aje jakkar dake hannuna da naji ya kara min nauyi a wurin.
Bandaki na nufa tukun na fara sake fitsarin tsoro daya taru mi a mara na dan dade tsugune ina sake shi kamar ba zai tsaya ba lokacin.
Na dade a zaune ina tunane kafin in samu inyi tsarki in fito daga bandakin duk jikina a sabule har lokacin yau kan nasan na taro mach a gidan mami wanda mai fitar dani sai Allah.
Ni da wani ido zan kalli mami dashi wai yau ni zainab yar aikin ta ke ikirarin zama sarakuwar mami a duniya.
Ni zainabu wani hali da rikici na jefa kaina a ciki aikin dana sani daga baya ke nan yake zuwa don nayi dana sanin yarjewa yaya Jafar bukatan shi yafi sau dubu a wurin.
A gurguje na shiga dakin mami a cikin daren nan don daya saura na dare a lokacin na gyara ko ina na dakin ban tsaya ba don kada mami ta riskeni a ciki na jawo kofan ina dawo na haye kujera dama na cire kayan jikina tun kan in shiga dakin mami din.
Tundana kwanta ba dunkule a cikin hijabina ban yarda nayi ko motsiba wurin.
Ina jin hjy na magana tana fadin su a can zasu kwanane har wanan lokacin basu dawo ba haka.
Shiru nayi kamar ina barci haka yasa ta kyaleni sai can na fara jin hayaniyan mutane a gidan alaman an fara dawowa ke nan daga dinner din.
Can aka turo kofan dakin da karfi ana kiran sunana muryan Aisha ce sai naji hjy na fadin yau naga sha shanci a gidan nan.
Zaki turo kofa haka babu sallama to boyar taku tayi barci tunda yaron nan ya dawo da ita don da alaman a gajiye takema ko da ta shigo.
Mami ke kiran ta yanzun nan a dakin ta ta fada a cikin wani murya da ban santa dashi ba sai ranan.
Kada ki soma ki tada yar nan daga barcin nan kije ki fadawa uwar taku tayi barci tun dazun inji ni haba kowa fa rai gare shi kamar kowa ace mutum ba zai huta ba haka dare ai mahutane ta fada cikin bacin rai.
Ina jin lokacin data rufo kofan hakan yasa nasan ta tafi na sauke wani iri ajiyan zuciya daga kwancen hjy taci gaba da fada ita kadai a dakin.
Sai muryan sallaman mami tana fadin hjy ashe baki barci ba ina zanyi barci kuna waje har wanan lokacin iyami.
Ki duba lokaci fa karfe nawa yanzu zaku biyewa shedanu kukai lokacin nan a waje dare fa mahutun muminine don a daren yake raya rayuwan shi walau ta hanyar barci ko na samun ganawa da ubangijin shi a natse.
Wallahi hjy taron ne ba, a fara da wuri ba tana magana hankalinta na inda nake kwance zata tayar dani .
Yar nan tayi barci tun dazun haba ku rika sauwaka mata hakana tana iya kokarin ta gidan nan yanzu sha shan yarki ta shigo tayar da ita.
Koma me zatayi ita Aishan tai maki mana baku bari yaron ya samu albarka a wurin ku saboda karyan zamani har yaushe kamar Aisha za ace ba zata iya aikin da wanan yar zata iya maki ba.
Ba aiki zatai min ba hjy dama dai tambayan ta nake son yi kawai mami ta fada sai hjyn tace.
Koma menene tunda tayi barci ai sai a kyaleta har safe a tambaye ta itama fa mutum ce kamar kowa a cikin ku.
Hjyce ta ceceni a ranan don mami fita tayi a dakin ba tare data tasheni ba kamar yadda mahaifiyar ta ta hana.
Ranan idan nayi barci barawo ne ya sace ni don haka na kwana ina sake sake bani kadai ba har wanda duk abin ya shafa banda ya jafar dashi ko a jikin shima hakan.
Aiko gari na wayewa sai ga sakon mami inzo gabana na duka uku uku na mike daga inda nake zaune a takure na nufi dakin mami din.
Addu,a kan nasha shi yafi cikkn kwando ranan da sallama na shigo dakin daga ita sai Aisha da mama Ramatu.
Mami tayi tagumi tana zaune kasa a inda ta idarda sallah asuba ta rasa abinda ke mata dadi a rai so kawai take taji na bakina abindake wakana a tsakanina da danta.
Nayi sallama na shiga sai mama Ramatu ne ta amsa min a lalace koshi Aisha ko tana bina da wani irin kallon mai kama da mamakina a fuskanta.
Kasa nakai cikin karfin hali ina fadin ina kwana mami ban jira amsawan ta ba na juya airin mama ramatu itama na gaida ita na juya gun anty Aisha itama hakan ne.
Shiru dakin yayi na dan lokaci ina tsugune kafin inyi yunkurin mikewa don shiga ban daki in wako yaddana saba yi.
Dakata zainab komaki zauna mami tace dani na koma da sauri inda na tashi ta dan dago kai ta kalleni kafin tace zeey ban saki da karya ba ko wani abu makamancin hakan.
Balle boye magana don baki taba min shi ba tun zuwan ki gidan nan wurina.
Kaina dan gyada a hankali yayin da gabana yaci gaba da faduwa sosai jiya tare da wa na ganki zeey ?
Kai na dan dago da sauri na dan saci satan kallon mami na samu ta kafeni da ido tana son amsa daga gareni.
Shiru na danyi tare da dukar da kaina kasa ina kallon carpet din da nake saman shi.
Bakiji me aka tambaye ki bane mama Ramatu ta fada daga inda take zaune din da dan karfi hakan yasa na dan zabura tare da dago kaina ina fadin babu komai mami.
Babu komai kuke haka jiya tare dashi a gaban kowa Aisha ta fada a dan hasale tana watso min harara.
Ni ban san komai ba tun bayan da kikace mai kwaliya ta shiryani yadda ya kama kika fita kika barni da ita mun gama na fito na samu duk kun tafi babu kowa da zanbi sai gashi shi yace nazo mu tafi.
Wani ajiya zuciya mami ta sauke har ina jinta daga inda nake Aisha ko na kokarin fadin wai kina nufin ni No wallahi mami ban san komai ba a kai kawai dai ya ban kudi a gyara mata kai daga can kuma ya kara turo kudi waina saya mata kaya expensive one don kin manta ki saya maya yanzu hjy ke fada mai.
Jeki zan kara nema ki mami ta fada tana kallon mama Ramatu da itama din ita take kallo don jin abinda ta fada.
Kai mami ta gyada mata alaman ta bari in fita daga dakin tukun suci gaba da magana zan shiga ban daki tace barshi anjima ki dawo idan mun fita.
Na juya na fita nan na barsu a dakin sai da na fita ta juya tana kallon Aisha dake zaune tana fadin duk abinda aka kitsa tare dake aka shirya hakan ashe kika boye muna.
Wani mami wallahi ban san komai a kai nima iya abindana sani ke nan na ta fada yanzu dana sani ai dana fada maki komai tuni.
Daki na koma na takure a wuri daya ina faman funane a raina don na kara daure kaina again ban san da wani ido zai kalleni ba kuma nasa bangare ga mami bawai ta yarda dani bane tunda har tayi mi abinda bata taba min ba yau shine.
Wai in fita idan sun gama na dawo in gyara dakin kenan da sauran maganan da zasuyi a kaina ke nan a dakin.
Shirun da nayi yasa hjy dake magana still kan daren dasu mami sukayi jiya a waje taji nayi shiru hakan yasata jutowa gareni.
Hawayen da ban san yana zubane daga fuskana ta ganin haka ta fara sake salati tana tafa hannu tare da fadin yarnan an maki wani abi ne ko kiranda iyami ke maki jiya na hana a tasheki tai maki fada a kansa yanzu don naga bata so hakan ba dama.
Saboda shine ta bata maki tunda farar safiyan nan ko da sauri na girgiza kai don nasan baida wuya yanzu ta sauke wa mami bala,i akai ta kara jamin wani tsana.
Kofan dakin aka turo Aisha ce tsaye a kofan tana fadin zainab mami na kira daidai lokacin da hjy ke fadin.
Ke kan yar nan arr da halin nan naki ace dan musulmi bai iya sallama idan zai shiga guri gara dai da uwarku ta raboku da kasan kafiran nan tun kan kufi haka ai.
Sai kuma jin abinda ta fada ta sake fadin wai wani laifi tayi maku haka baku bari yarnan ta hutane wai ?
Ba laifi tayi ba naji Aishan ta fada a daidai lokacin da zan fita daga dakin bayan fitana asheta fada mata komai dake faru tun daren jiya din a bayana.
Sai da tsohuwar ta gama ji take fadin meye laifi a cikin zancen nan idan shi jafarin yace itace zabin sa ai baiyi zabin banza ba nake gani ko ?
Haba hjy yar aiki ce fa wanan yarinyar da bata waye bane zai dauka a matsayin matarshi yadda ya J yake wayayye dan boko mai ilimi din nan dashi.
Yo wani waye akwai wanda yafi wani a gurin Allah ne idan ba Annabin rahama ba shi kadai zai fadi haka sai ko wa yanda sukai zamani dashi aka tabbatar masu da aljanna .
Kai don Allah hjy ki daina danganta wanan da yayan mu please ai abin kunyane ace wai wanan ce zabinsa haba dai.
Kaji min ya da wani maganan banza meye laifin zabin nasa har idan da gaske yakeyi ba wasa ba uwarku da ubanku ya aureta takai wanan din wayewa ne a lokacin.
Aida ba yanzu bane Aisha ta bata amsa tana fita tace kinci gidan ku nace kinci gidan ku yarnan da wanan maganan banza kece zaki zauna mashi da ita koshi zai zauna da abinsa.
Fita tayi ta kyale tsohuwar tana jin zancen ta na kara mata takaici a ranta sai ta dauki zancen tsohuwar ga tsufane kawai ke damun ta ba wani abuba don da tasan abinda takeyi da bata fadi hakan ba ai.
Ina shiga dakin mami ba tare data kalleni ba tana jin sallamana take fadin jeki ki wanke muna bandakin nan idan kin gama ki daukowa hjy abin karyawanta a kitchen.
Don mami ta dauki zugin mama Ramatu da wata kawarta da tun jiya ta zugeta a kaina baki daya don haka ta kudurta canza min daga wanan lokacin tun ban dauko mata magana ba a cikin diyan ta.
Wanan zugin kan mami ta haushi ta zauna akai sosai har yakai ta fara ganin aibuna a gareta yanzu.
Kafin in fito har ta shirya zata fita ta gaisa da mutane take fadin yi ki karasa ki fufo min dakina na amsa da toh kawai a cikin sanyin jiki ga canjin da nagani gareta.
Dakin mu tashiga gaida mahaifiyar ta inda ta samu hjy har lokacin tana mitan zancen ita kadai a dakin.
Koda mami ta shiga amsa sallama dai tsohuwar tai mata babu sakin fuska suka gaisa tayi mata ya jiki ?
Mami bata tsaya ba ta juya tana fadin bari ta leka yan uwa a dakin in dawo tana fadar haka ta fice daga dakin.
Har na gama gyaran dakin na jawa kamar yadda ta umurceni in mata da dakin na wuce kitchen na karbowa hjy abincin.
Ban daki na shiga nayi wanka na fito na shirya a cikin wani atamfa da Aisha ta bani dinkin buje da riga bujen dai bai matseni sosai ba yadda ita yakan matse jikinta idan ta saka a jikinta kafinta bani .
Ban zauna a dakin ba na nufi kofan fita daga dakin ina zuwa kawata hjy ta fada zan je in karbo abincine a kitchen na bata amsa.
Yau kuma ba a nan mukeci tare ba dake mazaki dawo ki dibi abincin nan kici karna saba maki.
Ko ta fahinci tsoron mami nake sai tace kowa yasan tare dake nake cin abinci sai yaune zasu kawo min wani zance.
Dole na dawo na rakube a gefe ba tare dana yi yadda na saba muna wasa da dariya a gurin ci ba haka hjy ta sakani gaba dole na debe abinci mai yawa tana kara ina ya isheni haka ta kyaleni.
Na fara ci ke nan mami ta shigo dakin tana magana sai ta dagata da maganan tana fadin ke kuma meye haka ?
Me tayi hjy ta tambaya tana kallonta da mamaki hjy don me zata zo ta zauna tare dake a nan tana cin maki abinci ?
Yau din kuma iyami ina har ke muna zama da ita ana aci abinci baki taba fadan wani magana sai yau ?
Daga yau din ban son in kara ganin hakan ta koma can wurun yan aiki ta dinga ci tare dasu kande da lami.
A, a iyami bana son irin haka wanan ba halinki bane hakan ban san kuma yaushe kika fara hakan ba.
Hjy na canza tsarinane yanzu a gidan nan don a fara bambamta yan aiki da yan gidan nan iyami dakata hakana hjy ta fada tare da juyawa inda nake tana kallona kafin tace dani kinga kawata.
Jeki falo kici abincin ki ki bamu wuri zamuyi magana da uwar ki ina jin hakan na mike da sauri don barin dakin.
A daidai lokacin mami ta kai zaune a kusa da mahaifiyar ta saidai ita saman kujeran ta zauna ba a kasa ba inda hjy take zaune.
Ko dana fita ban nufi cikin falon inda nake jin dan dararakun mutane na zauna dan filin da zai sadaka da falon da gefen dakunan mu din.
Ina kallon abincin ba tare danayi ko yunkurin cin cibi daya daga abincin ba sai idon dana zuba mai kawai.
Iyami kada ki bari shedan ya rudeki kiyi yunkurin yaki da ubangijin ki kan abinda Allah shida kanshi ya halasta hakan.
Yarki dazun ta fada min komai dake faruwa daku tun jiya wanda na hango kina kokarin fita daga ilimin ki da irin tarbiyan ki dana sanki na girmama dan adam a duk yadda yake.
Hjy ba hakana bane ni yaran nan zasu kunyata a cikin taron jama, an arzikina wai yaron nan ya nemi ya raina min wayau ya hada baki da yar nan a kunyatani hjy ?
Akunyataki kamar yaya hjy ta tambaya shi auren ne kunya ko yarinyar ce kunya a gareki yau kuma kina kunyan a santa da ahakin ki kika ajeta a gidan ki har kika jata a jikin ki kamar kece kika haifi abinki.
Wani irin shedani ne yayi saurin tasiri haka a jikin ki har kika manta da bayan ki ke ?
Da sauri ta dago kai ta kalli tsohuwar hjy tace eh kin manta da naki bayan kina son ki maimaita tarihi a kanki yau.
Hjy bawai hakana bane ni abinne yai bala,in bata min rai kawaion su wullakantani har jafa, , , , ,
Hannun da tsohuwar ta daga matane ya dakatar daga karasa maganan ta datayi niyar fadi a kanmu.
Iyami na haneki tun wuri da wanan halin abinda zai kawo dana sani daga baya wanda zai zama keya gareki.
Yaya zaki idan Allah ya nufa wanan abin mai yuyuwane garesu ko kina son in kin matsa da jayayya da ubangiji ya dauki ranki ayi a bayan ki.
To ina baki shawara ki natsu ki shiga hankalinki tun wanan abin bai fita waje an dawo ana maki dariya ba daga bayan ki.
Ina yar nan ke kika kawota gidan nan har danki ya ganta ya nuna sha, awan shi gareta duk ko da yadda take ba yar kowa ba kamar yadda ku kuke gani.
Shin iyami kin manta da yadda akayi lokacin auren ki da mahaifin yaran nan sam ban taba zaton zaki manta da hakan ba har ace yau ke da kanki kike kokarin yin wanan halin da ba, a san musulmin kwarai dashi ba.
Ina wanan abin ke kanki kamar darasine a gareki ban taba zaton har zaki yada kiyi ko maka mancin hakaba a yanzu.
Daga inda nake zaune naji takon tafiya haka yasa na dago kai da sauri ina kallon mai zuwa a lokacin ya Jafar ne da yaya mamud suna tafe suna magana a tsakanin su.
Saidai ganina a wurin yasa sukaja suka tsaya suna kallona da sauri na gyara zaman da nayi da farko ina gaidasu.
Duk kallon mamakin ganina a wurin sukeyi sai ya mamud ke fadin lafiya kanwata kika zauna a nan haka a kasa baki je dinning kin zauna ba.
Wani kallo ya Jafar ke min ba tare dayayi magana ba sai hannayen shi daya zuba a cikin aljihun wandon shi bakin wandon jeans dake ciki ya dan fito waje ya wani kara haske ko kallon tsoro nayi masa oho.
Badake ake magana ba ya jafar din ya fada na dan dago kai na kallesu sai nayi saurin dukar da kaina don duk idon su yana a kaina.
Ganin ina kokarin mikewa yasa ya mamud ya fara tafiya shima ya mara masa baya zuwa dakin dana baro su mami din da hjy.
Da sallama suka shiga dakin saidai ganin yadda daga hjyn har mami suke sai yasa suka dan tsaya daga kofa basu karaso ba sai ya mamud ke tambaya lafiya dai mami ko wani abinne ya faru ?
Shike nan ma hjy ta fada ga magani ga ciwo Allah ya kawo ki tambayi dan ki a gaban mu yanzu aji idan da gaske yakeyi ko wasan da kike tsamani kika tsani yar mutane haka ba gaira ba dalili lokaci guda .
Kin hana yar mutane tun jiya kwanciyan hankali duk kunbi kun rikita yarinya ga baki daya ni bani son irin haka wallahi abu baikai abin daga hankali ba zaku sakawa mutane rigima a gida.
Kallon mami yayi ya karaso inda take yana kaiwa zaune ta gefen gujeran tare da kamo hannun mami din yana fadin wani abu ya farune mami ?
Bai faru ba zai dai faru ka gaya muna meke tsakanin ka da Abu dana ganku jiya a gurin taro har kana nuna muna wai surprise din ka ke nan garemu ta fada rai a bace.
Abu mami ?
Waye hakana mami ban gane wa kike nufi ba hannun ta dake rike a nashi ta fisge tana fadin zeey yar aikina nake nufi ba wani ba.
Kai ya girgiza tare da dukar da kanshi kasa can ya dago yana fadin mami ba ke kikace na fito da yarinyar data kwanta min a kasan nan ko diyar waye ba ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUKU 🦅
2️⃣5️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH MUNA ROKON RAHAMANKA DA KARIYAN DAGA DUK WANI ABIN CUTARWA A GAREMU ALLAHUMA AMIN, , , , ,
To ka samo din ta tambaye shi a cikin gatse ?
Eh na soma mana mami kuma ai a karkashin ikon ki take itama yarkice kamar su Aisha.
Wa ke nan ya mamuda ya tambaya wanan yatinyar taki da kika dauko a kauye mana ga zahiri kun gani jiya tunda kun gamu tare.
Mami kan yake tayi wanda yafi kuka ciwo kafin ta tattaro natsuwa don hjy dake wurin a zaune bata da halin furta mai wani abu a lokacin.
Saidai duk da hakan sai da mami tayi bajintar fadin wai zeey dai kake nufi ai zee din kasan a matsayin dana daukota kuma bayan haka karatu take a yanzu.
Mami nasan da hakan saidai ai takai munzalin aure a yanzu don haka aurena da ita ba zai hanata karatun ta ba.
Ko kin manta kin fada muna kema kina karatun secondry daddy ya ganki ya aure ki lokacin.
Look jafar bana son shirmen banza mata nace ka fito da ita in maka aure at dis stage bawai ka tsaya kana min wanan shirmen ba haka.
Zainab na fadama karatu take kuma bata cikin zabin matan da nake son ka aura don tayi kankanta gare ka yanzu.
Hjy dai da yaya mamud na gefe zaune suna sauraren draman uwa da danta sai murmushi suke masu kawai.
Mami to aini ita din ce chooice dina sai ta karasa girman ta a gurina don ni a hakan da take yayi min daidai.
Jafar kada ka mayar dani abokiyar wasan ka idan kai tayi mani ba, , , ya mamud ne yace mami please.
Ki barshi ya zabi abinda yake so a rayuwan shi tunda shine zai zauna da ita bake ba kada a tillasta mai yayi abinda baiso a dawo ana dana sani daga baya kuma.
Hjy tacs fada mata dai dan nan ko kai zataji maganan ka tunda ni ban kai matsayin da zan tsawata mata ta saurare ni ba
Hjy bawai haka bane na lura yaron nan rainawa mutane wayau yake son yiwa mutane tunda mun tursasashi yayi aure bari ya zabo wace bata yuyuwa a gareshi yanzu ya rama abinda mukai masa ko ?
Wallahi mami tunane baikai ga hankan ba itace dai din naga tana daidai da rayuwana ita kuma din nake so a matsayin a bokiyar rayuwana.
To ban yarda bami ta fada a hasale tana mikewa hjy tace iyami dawo ki zauna mu kai karshen wanan maganan a nan tun wani bai kaiga ji ba.
Shiko jafar jikin shi ne yayi sanyi lakwas don bai taba tunanen mami zata dauki abin da zafi haka ba.
Ya mamud ne ya kawar da duk wata magana ta hanyar fadin tunda ita ka zaba din ba laifi ga hakan saidai yana da kyau itama muji ta bakinta ai idan tana son ka shike nan aurene mami ba wani abuba ai.
Mai yuyuwa kai itace zabinka ka ganta kana sonta a haka karamar ta ita kuma yarinyar ba kai mata ba a ranta .
Kaga ba zamuyi mata dole ba a kanka a matsayin na yar amana a wurin mami din don haka sai muji ta bakin ita yarinyat kuma.
Ban gane abinda kake nufi ba mamud mami ta fada tana kallon yaya mamud din taci gaba da fadin kaima kasan tunda ya tursasa mata ai bazatace batayi ba tunda duk mace ko banza neman irinsa takeyi.
Mata ma masu aji da ilimi da wayewa suna binsa su sameshi yana gudu sai akan wanan yar kauyen yarinyar idon ka zai sauka sai dai idan kana da wani manufane a kan hakan dai.
Banda manufar kome mami ita din ce nagani nake kuma so a hankan don banga wani matsalan da zaisa a hanani aurenta ba a tare da ita.
Mtss mami taja wani matsiyacin tsuki tana fadin Jafar kana son bacin raina da jefa yarinyar nan ga fushi wallahi.
Mami kiyi hakkuri yanzun nan zan kira ita yarinyar a gaban sa muji ta bakinta idan tace ta yarda dashi shike nan mami sai ki masu fatan alheri a rayuwan su.
Me zata fada tunda tana son shi mamud karka mata fa yar kauyece dama nema tafito yi a birni kuma ta samu a yanzu.
Gashi ta samu wanda darajan ta da kimarta baikai ta samu ba a yanzu, abinda bata taba tsamanin samun shi ba sai tace maka a a kuma ?
Mami please ayi hakkuri aji ta bakin ta idan ta amince ai masu fatan alheri shiyafi yanzu.
Mamud na fada maku yarinyarce bana son ya aura gaba daya don haka abar wanan na zancen tambayan ta please mamud.
But mami ni kuma ita din nake don banga wata da hankalina ya kwanta da ita ba bayan wanan din.
Jafar idan ma tausayinta ne yakaika fadin kana son ta ai ba sai ka furta kalman aure a tsakanin ku ba kana iya taimaka mata ta hanya da dama basai wanan hanyar ba daka fito dashi wai auren ta zakayi.
Jafar dake ta faman latsan wayan hannun shi tankar ba da shi ake zancen ba sai lokacin ya dago kai yana fadin.
Mami bawai taimakonta kawai nakeson yi ba ni kawai dai auren ta nakeso nayi dan tayi min a raina yana magana a cikin daure fuskan shi.
Daga inda hjy take zaune tace da kyau na mijin duniya kai mamuda kira muna yarinyar muji na bakinta yanzu.
Na bar gurin da suka sameni zaune don abincin ya gagara ci gareni don haka na dauka na kai kitchen.
Daga nan ne na tsaya don yin wanke wanken kayan da akaci abincin safe gasu nan an tara birjit don bakin da akayi gidan.
Maganan da mami tayi nake son in fara kiyayyewa da tace in dinga zama a cikin su lami da kande sune yan aiki irina.
Ina tsaye na fara tara kayan ne lami na faman sakamin albarka don haka suke min duk lokacin da nashigo zan tayasu wani aiki daya shafesu.
Muryan yaya mamud ne a kofan kitchen din yake fadin ke zainab zo mami na magana dake a dakin hjy.
Yana tsaye ya tokare hannayen shi a kofan shigowa kitchen din yayin daya zubamin idanuwan shi sai tausayin yadda ya sameni ya kamshi.
Juyawa yayi ya fara tafiya haka yasa na dauraye hannaye da sauri nabi bayan yaya mamud din ina jin wa yanda ke falo zaune na fadin.
Yar iska yarinya yau zakici uban ki gidan nan don yarinya kin tarowa kanki bala,i da hannun ki.
Idona ne ya kawo kwalla don ban kaunan abinda zakai a zagi iyayyena ko kadan saboda sanin daranjan su da nakeyi suko yan gida mami zagi a wurin su ba bakin komai bane a wurin su.
Zaune suke su hudu a dakin mami hjy ya mamud dashi gabana ne ya fadi don ganin su har lokacin a dakin .
Sallama nayi cikin yar siririyar murya hjy da ya mamud suka amsa min mami kan kai ta dago ta dan kalleni tare da kawar da kanta ga kallona.
Zauna a nan ya mamud yace dani yana nuna min wuri daga gefen kofa da nake tsaye saina kai rusunne da sauri ba tare dana zauna ba kamar yadda ya bukaci inyi din ba.
Kaina kasa ya mamud naji ya kira suna sai na dago kai a hankali na kalleshi yace mun kirakine muji ta bakin ki a kan wani maganan daba musan dashi ba tsakanin ki da jafar gashi zaune.
Ya nuna min shi da hannu sai lokacin na dan saci kallon Jafar din da idonshi sun kada a lokacin da gani shima yana cikin bacin rai ke nan.
Jafar ga yanan ya gabatar muna dake a matsayin wace zai aura kamar yadda mami ta bukaci da yakawo mata, matar da zai aura a yanzu.
Da sauri na sake dago kai nakai kallona ga Jafar din da shima a yanzu nice yake kallo da idanuwan da suka kade mai lokaci guda.
Don haka muke son jin ko kin amince da wanan ra,ayin nasa kema kin shirya da zaki aure shi kamar yadda ya bukata dake.
Dukar da kaina nayi kasa don ban san amsan daya dace in bada ba a wurin ga gardadin dayai min tun daren jiyan a mota ina tunane.
Ga mami dana hango tsanata saboda wanan zancen daya taso tsakanina dashi mami ta canza min gaba daya daga dare zuwa wanan lokacin kamar ba mami bace a gabana.
Don ba wanan yanayin na tausayina data min yau a gare ta ko kadan illa tsana karara da take nuna min a fuskanta.
Kiyi magana ke muke saurare ya mamud ya fada yana kallona don jin amsan da zan basu a lokacin.
Kai na fara girgizawa a hankali na samu na bude baki da kyat ina fadin ban san da maganan bani koma na sani ya jafar ba sa, an aurena bans shi don matsayina dana iyayyena baikai ko na yaron shi ba yaya.
Tunda na fara magana ido kowa ya zuba min sai mami dake fadin nikan nayi mamaki ina hankalin zeey da yatafi har take shirin tafkamin wanan kuskuren duk, , , ,
Dakata iyami ke a matsayin ki na uwa kin taba ganin inda aka tsiye yarinya haka wai ana tambayanta zabinta kai tsaye.
Kiwa Allah kiwa yaran nan adalci iyami tunda ni yanzu ba magana ta kike ji ba ban isa ba ko dan nima din banda mutuncine tunda nima daga kauyen nake ko ?
Yarasulu hjy me ya kawo wanan zance kuma har kina danganta kanki da hakan Allah ya gani ni ba manufa ke nan ba ta fada tana kallona az cikin yanayin daba zan iya fassarashi ba a lokacin.
Ke tashi ki tafi ya jafar ya fada a tsawace kuma ranshi bace ga wasu jijiyoyin kai da suka mai jasur a goshi abu fa farar fata sai suka mike sukai wani layi layi a saman goshin shi kamar mai tsananin ciwon kai a lokacin.
Da gani hankalin shi gaba daya a tashe yake mai a lokacin zainab jeki abinki ya mamud ya sake fada da sauri na mike nabar dakin.
Don dama a kage nake dana bar aurin saboda rikicin da nake hangowa a idanuwan su wurin.
Ina barin dakin kitchen na nufa har ina hadawa da tuntube don sauri saboda gaba daya na gama tsoracewa da lamarin nasu ga baki dayan su.
A daki kan hjy ta tubure tana fadin ya mamud yazo ya mayar da ita dakin ta ba zata zauna inda ba,a san darajan ta ba.
Hankalin mami ya tashi tsohuwar taci gaba da fadin yaron nan yace ga zabin shi ta yaya bayan kun gama tsorata yarjnya tun safe yanzu za a kirata ace ta fadi ra, ayinta a gaban kowa ?
Ke lokacin da akai maki aure haka mukai maki mami tace hjy kina dai son ganin laifina ne yanzu.
Wanan shawaran yaran nan sukazo da shirmen su a gaban kifa akai komai yanzu don Allah hjy kada kija zancen nan inda bai kai ba.
Yarinya dai tace ba zatayi dashi ba final Allahu akabar don kuma hankalin ki ya bata yanzu sai kikaji dadin hakan ke.
Allah na tuba ashe gaskiyane mace komai tsufanta wayau ta ragagge ne.
Ke yanzu har kina murna yar da kika raina kike gani ba a bakin komai ba ta iya budan baki a gaban idon ki yau tace maki batayi da dan naki da kike dauka wani kayan gabas a wurin ki.
Niyi tir da wanan hukuncin da kika bari yaron nan ya yanke a gaba me zan zauna inyi tunda banda sauran kima a idon ki.
Gidan ki nazo zaki iya min duk wani rashin da, a don yanzu kina ganin ke kin isarwa kanki a komai sai dai da badon jafari ba da sai ince yarinyar nan zainabu ta burgeni sosai .
To jinin ka jinin kane banji dadin yadda ta watsawa jafarin kasa a ido ba a gaban kowa don kawai tsoron idon ki data gani a daure kin sakar mata na mujiya .
Wanan maganan kuma sai yasa mami ta ji daci a zuciyar ta da kyat dai ta samu ta shawo kan yar tsohuwar ta fasa tafiya saidai mami bataji dadin yadda tsohuwar ta dauki zafi da ita ba haka.
Ya jafarko tunda ya fita ya bar mami da su ya mamud a dakin ya bar gidan tun mami bata damu da rashin ganin shi ba har dare yasa ta tambaya ko ina ya shiga haka bai dawo gida ba don hakan ba dabi a shi bane yin dare a waje .
Har yakai ta fara tambayan duk wanda ya shigo gidan a cikin mazan dake gidan amsa dayane dai daga shi har security din shi fun safe basa gidan.
Ta kira wayan shi yafi a kirga wayan ba ya shiga kwata kwata ba, a samun shi gaba gaba daya ranan.
Tunane kala kala mami tayishi ga zafin yarinyar daya mamaye mata rai gaba daya taji ta tsani yarinyar tana dana sanin daukoni dayi ta jefa a cikkn iyalin ta.
Gashi kuma hjy ma a nata ban garen haka ya jawo masu matsala da ita don tana matukar son mahaifiyar nata sosai.
Gaba daya gidan sai yai min zafi a yan kwanaki biyun nan babu wurin wanda nake dafawa inji sanyi kowa tsanata yake a gidan ga baki daya.
Sai gurin hjy kawai ita kuma yanzu ba zama muke sosai ba idan na shiga dakin sai zanyi wani abu don ina gudun mami tashigo ta sameni a ciki zaune yasa na koma kitchen wurin yan aikin da dukkan mu kawomu akayi gidan don aiki.
Hjy tayi fadan hakan har ta gaji ta saka min ido ta kyale ga yadda lamarin ya juye muna.
Ga zagi da nake sha a gun yan matan gidan a yanzu yayi yawa har takai ranan Rufaida tayi min mari biyu masu kyau.
Saida anty Aisha tayi mata fadan hakan kan su dan sasautamin don Allah tunda ba laifina bane shine ya ganni yace yana sona ai.
Ba nice na leke mashi ba kuma yanzu ba wanan zancen budan bakin Rufaida sai cewa tayi Aisha kece baki san halin yan kauyen nan ba.
Mudake tare dasu muka san halin su basu shigowa gari sai sun shirya an asirce su yadda duk namijin daya gansu ba zai iya kawar da idon shi a kansu ba meye ba a yi yanzu halan.
Gasu da sihiri mai dafi da kaifi wanda in basu ba kainan dan birni kace ai maka saidai aci kudin mu ga banza.
Tace au hakane nima fa abin yaban mamaki ace wai duk wanan baiwa da jin kan na ya jafar ga ilimi da wayewa amma ace wai zee yake so shi .
Wanan to zarcin da suke min ne yasa hankalina ya kara dagawa sosai a gidan naji ina son komawa kauyen mu baki alaikum ba tare dana fadawa kowa ba.
Sai dai kuma ina jin tsoro don ban san kan garin ba kada in fita ni kadai a ganni ba kauya a saceni.
Tunda na fara jin ana fadin jibine tafiya Abuja na fara funane a raina don nagama yankewa kaina hukunci .
Gara kawai in gudu in koma gida ko ta kan anty safiya data kawoni da itama tazo tayi min tas kan wanan zancen a gaban mami ta wanke tas wanda nasan hakan tayi shine don kawai ta wanke kanta a wurin mami din.
Saida na bari hjy tayi barci na mike na fara hada kayana a cikin jakkata inayi ina juyowa ina kallon ta kada ta tashi ta ganni.
Aiko ban tsira ba don ashe idon ta biyu tun dana fara take kallon abinda nakeyi.
Juyowan da zanyi sai ganin ta nayi zaund ta kura min ido kaduwa nayi don ban zaci hakan ba na dauka tayi nisan barci a lokacin.
Ikon Allah yar nan me kike kokarin yine karda ace guduwa kike son yi daga gidan nan sai kawai na durkushe a wurin ina kuka ina fadin hjy gida zan tafi.
Babu mai sona a gidan nan mami ma fushi take dani har su anty Aisha da nake dan dafawa naji sanyi yanzu itama bata sona suncewa asiri nakeyiwa mutane suke sona.
Sai naga tsohuwar ta danyi murmushi can kuma tace kai yaro dai yarone ke in banda abinki dama ai duk wanda Allah ya mayar sani abu a duniya saiya fuskaci kalubali mai tsanani kafin ya taka nasaran shi.
Ba wanda ya tsamaci haka gareki sai gashi kwatsam Allah ya doraki a kan kowa dake gaban ki ga yanzu sun san da sani ke din yar bawaice kinga dole ko su nuna hassadan hakan gareki
Yanzu kinga mayar da kayan nan kafin gari ya waye wani ya shigo dakin nan yasan abinda kikai kokarin aikatawa har makiyan naki suji suyi maki dariya.
Hjy Abujan ne da za a koma ban son zuwa gara dai in tafi tun muna nan kusa da gida.
Yar nan ashe haka kike da gardaman banza ko dai kin san inda Jafarin din yake ne ?
Hakan data fada yasani fadi wallahi hjy babu komai a tsakanin mu ban san komai ba game dashi.
To wanan tafiyan da zakiyi ne zai sa a kara zargin ki a dauka kun hada baki dashine kan ki gudu hakan kuma na iya jefa iyayyen ki dake a cikin wani mawuyaci hali.
Kallon ta nayi da mamaki tace kwarai kin dai san iyami na da halin da zata sa a daure kowa naki a kasan nan ko.
Tsoron maganan da hjy ta fada ya kamani sai na kara fashewa da wani irin kuka tace kinga ki shiru kin san yanzu darene kada wani yajiyo mu a waje.
Na maki alkawari muddin ina raye zan tsaya maku har burin ku yaci ka duk da naga kin sare kin ji tsoron barazanan uwar taku har kina fadin shine ya tsara hakan.
Da sauri nace wallahi hjy ban san komai ba a kan zancen nan ni dai kawai komai da yace nayi a wurin nayi.
Da haka har ta shawo kaina muna dan hira kafin ta mike ta shiga ban daki ta dauro alwala tana fitowa nima na shiga don cewa da tayi min in yawaita yawan ibada in roki ubangiji sauki.
Naji dadin wanan shawaran da tsohuwar ta bani sosai don duk kunci dake zuciyana sai na nemeshi na rasa washe gari naji na tashi raina ya sake duk da mutanen gidan basu daina halin da suke min sai dai ko dunyima hakan bai damuwa na yanzu don shawaran dana samu daga tsohuwar.
Ga kuma iyayyena da nakejin tsoron lefin da basuji ba basu gani ba yazo ya shafesu ya zama dole a gareni in daure ga duk abinda zan gani don yakin nawa ni kadai kamar yadda hjy din ta fada min kar in yarda in kada iyayyena ga tashin hankali.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
ZAINAB IDRIS MAKAWA
JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI FATAN ALHERI GA MUSUMAI DUNIYA BAKI DAYA AMIN, , , , ,
Yar uwa ban son ki da shiga hakkin wani ko wata don Allah kiyi kokari ki biya kafin ki karanta kada ki raina hakkin wani a kanki gara ace kece mai bi da abiki.
Allah ubangiji ya bamu ikon aikata alheri da fin karfin zukatan mu Allah ka sadamu da rahamomin sa amin.
Mami ta shigo dakin wurin hjy a lokacin ina zaune ina gyarawa hjy kayan ta da aka wanke don da ta cire kaya zan dauka in hada danawa in wanke tas.
Shine hjy ta tsayar dani in gyara mata jakkar kayanta muna dan hira ina dariya don gareta kadai nake jin dadi a gidan bayan ita sai dan dama anty Aisha duk da yanzu itama akwai sauyi sosai a fuskanta gareni.
Mami na shigowa dakin saidana kadu dan fargaban daya ziyarci zuciyana lokaci guda don yanzu ina tsoron ta sameni a dakin tare da hjy saboda kada ta yi min cin mutunci.
Don haka nake iya kokarina wajen kaskantar da kaina a garesu kamar yadda suke nufi da zancen su gareni.
Ba wai suna takuramin ga hakan bane saidai ko sakin fuska ance rahamane to babu wanan yanzu tsakani da kowa a gidan sai hjy sai ko yan samarin mami jalal da jamal da basu taba nuna min wani canji ba a fuskokin su.
Kamar yadda muka saba hakan ne har yanzu a wurin su do shi jalal sarkin wasa har yakan min ba, a da fadin amaryan mu.
A cikin wasa hakan yasa yanzuma dana fito daga dakin hjy na sameshi zaune tare da yan matan gidan yana cin abinci suna hira nazo zan wuce zuwa kitchen wurin su mama kande.
Muryan shi naji yana fadin a, a ke kuma armaryan mu yau ko dan gaisuwan ban samu ko dai har kin fara amarcin ne mu fara kawo gaisuwa don yanzu ke dan kin zama key a gurin mu sai an murdaki za a bude,
Kai kai haba jalal wanan irin maganan kesa kuna kara hurawa yarinyar nan kai amaryan wa kuma wanan yar kauyen yar aikin kakewa irin wanan maganan.
Sai ta dauka kamar daidai take da kowa a gidan nan yanzu don dan kauye bai iya samun wuri ba.
Wuce daidai yanzu tunda har ta iya halbo zuciyar ya J aiko tafi kowa ke nan dai a yanzu tunda ta doke duk yan matan dake garin nan kai bama garin nan kadai ba duk kasan nan zance.
Ya jamal naci karo dashi da sauri na dan duka ina gaidashi da kwana yadda na saba na shige kitchen haka yasa ban ji sauran maganganun su ba a wurin.
Ashe a bayana har zancen yaso koma masu fada don Rufaida ta dauki zancen da zafi har gaban mami saida maganan ya kaisu.
Mami kan jalal taiwa fada sosai a wurin jamal yace haba mami kina wanan maganan haka gaban kowa bayan yarinyar nan kin sanda cewa itace dai ya jafar ya tsayar zai aure kice kika sanda wanan zancen a yanzu.
Amma shi ya J din ai ya dade da nuna yana kaunar zeey din ki tun muna abuja da kika fara ganin su wurin dinner rantsar daku .
Dalilin kine fa har ya J ya fara kula yarinyar nan yanzu kuma kina fadan wanan irin maganan a kanshi idan bakya son wanan abin ki mayar da yarinyar hannun iyayyenta kowa ya huta idan yana so sai yaje can gurin iyayyenta ya nemeta.
Kai jamal ka rufa min baki da wanan bakar maganan da kake fadi duk yan matan dake garin nan ace baiga wace tayi mashi sai wanan zeey din da bata da asali yar kauye.
Meye to aciki mami ya tambaya da mamaki yana kallon ta tare da fadin itace fa zabinsa mami don me kike kokarin kawo matsala a cikin zancen nan yanzu ?
Jamal ta fada a cikin tsawa tare da fadin ka fita a idona tun kan ranka yakai ga baci dama halin ku daya da Jafar ai don baku san ciwon kanku ba.
Mami don kawai na fadi gaskiya ki barshi mana yayi abinda yake so zaifi ace kin takura kanki akan wanan magana.
Yana fadin hakan ban tsaya sauraren me zata fadaba ya juya wurin jalal yana fadin kai ya mutafi ko ?
Jalal din dakewa mamin su kallon mamakine ya mike yana fadin mami zamu tafi wurin ticket din don a samu da wuri sai dai bamu san na mutum nawa za,a saya ba idan munje.
Ajiyan zuciya mami ta sauke don yanda ranta ya baci da zancen yaran da safen nan tana fadin naku sainawa da hajiya da Aisha Nuriya da yaran tunda shi mamud din ya tafi tun jiya.
Mami zeey din bada ita za, a tafi bane wanan karon ko a nan za a barta ne wanan karon kinsan fa basu haduwa dasu Rufaida a wuri daya ko banza.
Ya za a barta a nan jamal ya fada dole ai da ita za a tafi ko dan taimakawa hjy wa zai iya da lalurar ta idan ba ita ba.
Jin wanan zancen yasa mami ta danyi tunane kafin tace da ita zamu tafi amma mota zatabi wanan karin ita dasu kande da lami da drivobi.
Haba mami ai hakan ba girman ki bane yarinyar nan meye laifin ta dankine fa duk yaja mata koma meye a wurin ku zeey din nan tana da halin kirki gun kowa.
Kallon data watsa masune yasa su fita daga dakin da sauri har suka kai wurin sayar da ticket din suka sayo jamal yace su hada da nawa su saya koma me mami zatace dai sun saya ai.
Hjy kawai zamu fadawa da mun koma gidan zai fi suna wanan maganan ne wayan ya jamal yayi kara ya dauka da mamaki yake kallon wayan daya nuna lamban kasar South Africa.
Waye kuma ya kirani daga south africa ya fada yana nunawa dan uwan nasa dayake tuki a lokacin.
May be wani friend din kane ko ya fada shima yana kallon lamban kafin ya mayar da hankalin shi ga tukin da yakeyi din.
Jamal kuma ya dauki wayan da hello muryan dan uwan shi jafar yaji yana fadin kai jamal ya kuna lafiya ya mami.
Ya Jackson kaine kayi nisa fa ka daga hankalin mami sosai don har yanzu bata koma daidai ba rashin jin inda ka shiga.
No ball kawai nazo kallo don in samu natsuwa a tare dani ya kana gidane ko waje ya tambayi dan uwan nasa.
Wallahi ya gamu nan munzo yankar ticket gobe zamu koma Abuja mami zasu fara aiki monday din nan mai zuwa.
Wanan yarinyar fa ya tambaya sai jamal din yace yanzun haka zancen ta muke a mota don mami tace wai kada mu yanki ticket da ita a mota zasu tafi ita da sauran yan aiki kamar ta.
Yanzun fa ya tambaya No mun yanko da ita zamu hada da hjy saitawa mami magana fine idan ka koma gida kayi flashing layin nan zan yi magana da ita ok ya nagode take care.
Sun dan biya wani guri kafin su dawo sai bayan sallah azahar suka dawo gidan a dakin hjy suka sameta ita kadai a dakin sun gaisa take fadin yau bata gansu ba tun safe.
Jalal yace dazun na shigo da niyar idan nagama karyawa in shigo mu gaisa sai wa yanan yan rainin hankalin suka so raina min wayau suka ja har mami tayi min fada kan yarinyar nan zainab.
Nan dai yake fada mata komai har zancen sayo ticket din da sukayi dani take fadin sun mata daidai don daba haka ba ko ita ba zata tafi ba idan ba wanan yarinyar cikin su don ko taje wa zai kula da ita a can kamarta.
Karbi waya wani ke son magana dake ya fada a dake sai ta watso mai wani irin kallo tana fadin wani wa ka samomin da yake son magana dani.
Wayan ya kara mata a kunne jafar din yana jin rikicin da sukeyi a dakin yana murmushi kafin yace ke tsohuwa kanki nake so nawa zaki sayar min a turo maki kudi gobe nazo na sare.
Dan nema mai muryan turawa ka dauka ba zan sheda muryan ka bane halan ?
Jafari ina ka shige kabar mutane a cikin damuaa haka kan dan magana kankani ka yankewa kanka wanan hukucin.
Ashe kai baka cika jarumi ba kaja fadan da baka iyawa da uwarka na dauka kai cikkaken jarumi ne ashe ba haka ba.
Matsoraci kawai yace lailai tsohuwar nan kin gama sani yau zan ko gwada maku ni jadumine da bai magana biyu.
Ni baka da bakin fadar komai yanzu a gabana tunda kaja fada kabar yar mutane nan da yaki ita kadai.
Hjy wa ya isa ya yakar min mata ban gama dashi ba ai ita mami ta sani tasan bana magana biyu yasa na bata wuri ta sauko daga fushin data dauka.
Yanzun dai ba wanan ba wallahi tafiya ne ya kamani gani nan a kasan africa ta kudu nazo wani abu zan dawo da yardan Allah nan zuwa jibi idan Allah ya kaimu.
Nikan daka ban mamaki sai ince wanan jarumin nawa bai cika jarumin maza ba ashe a duniya.
Yanzu dai hjy ina yarinyar take don nasan nabar sarkin yaki a gida yasa ban daga hankaliba ga zancen.
Yarinya kan na nan tana fuskantar matsi da tsangwama don har tayi niyar guduwa wallahi na dakatar da ita daga hakan.
Kallon juna jamal da dan uwanshi sukayi shikuma yana fadin hjy don Allah kada ki bari ta gudu daga gidan nan idan na dawo zan sake zama na karshe da mami akan zancen.
Bazata ko ina ba a yanzu kan sai dai ban sanarwa gaba ba idan ka kasa shawo kan uwartaka kan zancen.
Ba jamal waya yace jamal din ya karba yake fadin idan mami ta tambaya ka fada mata nine nace a saya da ita.
An gama yaya ya fada yana dariya suka danyi maganan su kafin yace jamal din ya ban wayan.
Ina kitchen abinci lami ke kwasa ina mika mata ledan da take saka tuwon data tuke a cikin sa naji muryan ya jalal na fadin ke zeey karbi waya ana magana dake a bayana..
Sai da gabana ya fadi kanfin in juyo ina fuskanta shi bai tsaya jiran komai ba kawai ya ban wayan na karba.
Tare da karawa a kunnena gami da sallama duk da bansan mai magana ba a lokacin amma sai da nayi sallaman dan koyi da sunan ma,aiki S A W .
Ajiyan zuciya naji an sauke wanda hakan ya tabbatar min dashi ne a layin duk da ban tabbatar da hakan ba lokacin.
Ido lumshi yana maijin wani iri a zuciyar shi ya amsa sallaman tare da fadin ya kike kina lafiya ko kina nan kina aikin kuka da tunane ?
Ko baki maganane ya fada kamar bashine jafar din mami mai yawan daure fuska ga kowa na gidan ba in badon ina yawan zama da hjy ba ina ganin yadda yake sakin jiki a gaban tsohuwar zan iya rantsaewa da baya dariya tunda yake don yawan daure fuskanshi koda yan uwan shi maza.
Sai yau gashi shike min magana mai kama da ba,a a kunnena haka ina jin shi.
Sake maimaita abinda ya fada yayi yana fadin ko bakiji mena fada ba kina nan kin saka kanki a damuwa ko ?
Aa,a na samu kaina da fadi a cikin sanyin murya ina mai girgiza kai kamar yana gabana a lokacin.
To ki daina damuwa don banga laifin ki ba ko kadan a ranan don na gama fahintar dama ke matsoraciyace sosai.
Ko kin fasa taimakawa yan uwar ki da innan kine in sani don in kyaleki in neme wata.
Daga inda nake na dan runtse idanuwa don da ace shidin sa,a nace da zan so haka ya kasance ko dan kyaushi da wayewan shi saidai nasan shirme nakeyi don wutsiyan rakumi yayi nisa da kasa.
Shi din ba ajin irin mu bane yayan talakawa kamar yadda mami ta fada muryan shine ya katse min tunane yana fadin.
Da kun koma abuja zakici gaba da karatun ki don nayiwa mamud magana yanzu ma abinda ya kaishi Abuja ke nan zancen karatun ki don zanfi son sai kin kamala secondary kafin in aure ki mu tafi.
Nagode yaya na fada a dan kunyace danaji zancen karatu Allah yasa dai kina da kokaerin karatun kamar yadda nake zafo ya fada.
Gane bazanyi magana kamar yadda yakeso ba yasa shi fadin ni zan kashe tunda har da magana a hanaki yi dani yanzu.
Sai an jima nace a kage don na matsu ya kashe wayan in huta da wanan bugun zuciyar danake ji a lokacin.
Maimakon naji ya kashe din sai ji nayi yana fadin kingaji dajin muryana ne to idan kin gaji ni ban gaji ba zan iya barin wayan a haka har lokacin dana gama sauran bugun zuciyarki da numfashin ki tunda naga a tsorace kike.
Ban kaiga sani anmsar da zan bashi ba sai muryan Nazira ke fadin ji min yar iska ana aiki kinzo nan kin labe kina waya da maza ko ?
Uban wama ya baki wanan wayan dake hannun ki haka ko sato wayan mutane kikayi kina waya dashi yar iska muga wayan har sata kika fara a gidan nan ashe yau Allah ya tona maki asiri magen banza mai kwanciyar kwanto ayi sake tayi wuf da abin mutum.
Duk abinda take fada a cikin kunnen ya Jafar yana ji bata farga ba don bata kai ga karban wayan ba tana shirin tara min mutane a wurin.
Shigeya yar kauye mara gata da asali watau ke kinzo birni kinsha jan miya har kina kokarin sace zuciyar dan masu gida da kissan ki na yan kauye ko ?
Ki rasa wanda zaki likewa kamar chewing gun sai ya J da kowan mu a nan take zaman jiran shi mutumin da ko ganin shi tsadane a wurin mu.
Ke amma dan bakin tsafin ki da maitar ki har kika iya sanin yadda kika ja hankalinki gareshi yasan da zaman ki gidan nan maza ban wayan naga ko wayan waye kika sace.
Idona ya riga daya ciko da ruwan hawaye a cikin karfin hali nake fadin ni ba barauniya bace kuma bana maita waya kuma ba satan shi nayi ba ya jalal ne ya kawo min shi yanzu da kansa.
Lami daga gefena take fadin haba Naziran hjy yanzu fa jalal ya kawo mata wayan nan muna tsaka da aiki ya miko mata shi.
Karyane wallahi satoshi tayi yar iska watau ke zaki goya mata baya ta dinga muna barna a gidan nan wallahi yau sai kowa yaji sata ta fara muna don kowa ya kankanta kayan shi tunda muna tare da barauniya.
Wallahi ni ba sata nayi ba na fada don ni ko tsinken wani ban taba tabawa a gidan nan na samu kaina da fada cikin sheshekar kuka sai ga Rufaida da salma dake falo sun shigo suna tambaya take fada masu.
Wallahi yarinyar nan na kama ta sato waya tana magana dashi a nan Allah ya kawoni da maishi yau yayi hasara iphone ce kamar ta jamal salma ke fada.
Ba sata nayi ba anty salma yanzu ya jalal ya kawo min wayan inyi magana karya take Nazifa da Rufaida suka hada baki wurin fada.
Satan shi kikayi ke har kina da darajan da zasu baki wayan su shegiya yau Allah ya tona maki asiri don dole sai kin bar gidan nan yau.
Hasken da wayan yayi daga hannuna yasa salma fadin dawa kike waya yar mami a hankali na dago kai na kalleta kafin in mayar da kaina a kasa ba tare dana bata amsa ba.
Dawa ko zatai waya banda munafukan iyayyen tan nan dake mata tsafi a gida.
Nazifa kin san koda ya J take waya kike fadan wanan maganan haka don duk abinda kike fada yana jin ki tun dazun don wayan sai yanzu aka kashe ta.
Sai jikin ta yai sanyi ta juya tana fadin ke ki bari don Allah dama wayan a kunne take ashe salma tace wallahi shi yasa nake fada maki ku fita harkan yarinyar nan ku kyaleta ba kuji.
Zeey yar mami kin gama wayan ki miko min muryan ya jalal ne daya dawo yake fadan haka daga kofa sai kuma yai shiru yana binsu da kallo lokaci guda.
Ina sharan hawaye nake miko mai wayan tare da fadin nagode duk suna tsaye suna kallon mu a wajen lami tace haka kawai kinzo kin dafawa yar mutane sata ba gaira ba dalili kina neman tara mata mutane ki kunyata ta.
Na fada maki shi ya kawo mata wayan yanzu muna aiki a wurin nan amma bakiji ba.
Ba dole in zargeta ba ta fada tana watso min wani kallon tsana daga inda take tsaye Rufaida kuma wani irin kallo mai nuna matukar tsana gareni take jifana dashi kafin tace.
Ya J din kike waya dashi a boye ashe shigiya mai bakin sihiri kin rantse sai kin sace mai zuciya a gidan nan ko to tsaya kiji .
Ya J ba sa, an yin ki bane gaja irin ki yar kauye idan ko ba aikin asiriba me ya gani a jikin ki yake wanan haukan haka akanki .
Jeki ki tambaye sa ai dan uwan ki ne don me zaku ga laifin yar mutane a banza ga mailefin daya nace mata hjy tsohuwa ta fada daga bayan su don layin jalal daya kira yake fada masu hankali tashe abinda suke min a kitchen din.
Hjy bashi keda laifi ba wanan dince mai laifin ita da batar aika mai da asiri ba ke rufaida ki shiga hankalin ki dani kada ki kawo min diban albarka a gaba wurin nan.
Ba kunya har kike maganan asiri haka a gabana yaushe kika san wani aikin asiri can idan ma shi kuke tunane ai da asiri tai masa daba hakan ba.
Da sauri ta dago ido tana kallon hjy din tace eh da idan ya zare a gidan nan baijin assh a kanta wanan ake kira da asiri.
Wanan ko kauna zallasa so da kaunane nata yaja hankalin shi har don sa ya rufe ya gama mutuwa a kanta ta yadda bai iya jin kiran kowa a yanzu.
Mami dake kwance salma ta kirata ta fito da dan saurin ta zuwa kitchen din ta samu hjy na yanka sababi a kofan shiga kitchen din.
Tsaye take bata san abinda ke mata dadi a wurin ba sai faman tunane take a ranta ita kan ta daukowa kanta jidali da hannun ta.
Ita kan dame wanan abin yai kama me jafar dinta ya gani gun wanan yar haka ya mace a kanta ya hanata sakat a zuciyar ta yan kwanakin nan kan wanan magana.
Wai me ya kawo wanan zace mami ta fada daga bayan mahaifiyar nata inda take tsaye.
Mami wanan munafukan ne na kama a kitchen yanzu da wayan su jalal a hannun ta shine na zata satowa tayi take waya dashi nake mata magana hjy ta taso.
Dawa kike waya zeey ya akayi wayan su ma yazo hannun ki har kike waya dashi.
Diyan ki zaki tambaya wanan don su suka bata wayam ba sata tayi ba a gurin su hjy ta fada a hasale ta juya wurina tana fadin fito mu tafi daki ba zan barki a nan ba tunda basu da imani.
Daga mami har yan matan dake tsaye su biyu suka dago ido suka kalli junan su .
Ina tsaye rakube a jikin bango ban ko motsaba don tsoro naji mami tace ba dake ake magana bane kinyiwa mutane tsaye haka.
Na dago matacciyar kafata daya gama sanyi da sarewa na fara dan tafiya nazo na ratsa tsakiyan su na fice daga kitchen din ina jin wani iri a zuciyata sosai.
Nazo wucewa gaban mami dake tsaye a kofan naji tana fadin ku fito daga kitchen din nan kuma da tada zaune tsaye kuke wallahi ina ruwan ku tunda ba wayan ku ta dauka ba.
Da kyat naga dakin don nisan da yai min lokacin ina shiga na zauna daga kofa na fara rera kuka a fili hjy na shigowa dakin tana mitan zancen.
Nace hjy don Allah don so da kikewa Annabi ki roki mami ta mayar dani gidan mu hannun iyayyena .
Ba sai ta rokeni ba ma zeey nima wanan abjn ya fara isata hakana don haka ki shirya gobe a mayar dake gida.
Mudai shirya a maidamu gida zaki fada don ba yar nan kadai zata tafi a gobe har dani yar kauyen uwar yan kauye zamu tafi kafanta kafana a gidan nan goben, har gaban iyayyen ta zan kaita in yaso dan naki yaje gurin iyayyen ta ya nemeta idan yafi maki sauki.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GARE KU YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN, , , , ,
Jin abinda hjy ke fadi yasa dole na daina kuka don ba zanso nayi sanadin mami da mahaifiyar ta arayuwana ba don na samesu cikin so da kauna iri ta da mahaifi a tsakanin su.
Ni na bar shiri sai ga tsohuwar ita tana hada kayan ta wai ita gida zata bata kara kwana gidan mami.
Hakan ya tayar da hankalin kowa a gidan don mami har kasa take tana ba hjy hakkuri hjy ko sai fada take tana fadin.
Sam bazan zauna inga wanan cin fuskan da yaran ki kewa yar mutane ba haka idan ke kin kasa da ita ni zan tafi da ita can kauyen mu in yaso shi Jafari yazo gurina ya nemi auren ta.
Kin dauko amana dadi dadi kina riko tsakani da Allah ashe rikon naki ga yar baikai ciki ba da har dan ki zaiji shawan hada iri da ita ki fito kina fadin baki yarda ba don ita din ba diyar kowa bane a kasan nan.
Gasu nan birjit a gari dan naki yaje ya zabi daidai dashi a kadarta yau Aisha ce dan tallakawa ya fito nema ashe ba zaki iya bada aurenta ba ga wanda take so ?
Don kawai yanzu kudi ya bude maki ido kowa kuna kallon shi a mutumin banza koko samun abokai yan duniya dakikayi ne yanzu ya sauya maki yanayi.
Idan ma hakan ne sai kije ki aura mashi wacce duk kike son aure mai din ita kuma wanan din zan tafi da ita gurina in sakata karatu idan ina raye wata ran sai kince ba ita bace a gidan nan.
Kuma ki sani koda danki zai mutu ne idan yazo ba zan bashi yar nan ba muddin na bar gidan nan da ita.
Inda nake ta kalla tana fadin tashi muje yar nan nasan dai ko ban san kowa a garin nan bazan kwana a waje ba yau zan samu na Allah da zasu duba tsufana su tausaya min.
Tana kokarin sungumar jakkan kayan ta daga saman gado inda yake ajiye mami tayi saurin dafe jakkar tana fadin hjy don Allah ki rufa min asiri a garin nan kada kije ko ina gwiwa biyu nakai kasa tare da daga hannaye biyu sama ina fadin.
Hjy don girman Allah kiwa mami hakkuri karki fushi da mami ba laifin ta bane laifin zuciyane.
Da yau danta bai bijiro da wanan zancen ba da mami batai fushi dani ba har gobe mami uwace a gareni mai mutunci da kima a idona.
Bazan taba mance mutuncinta a gareni ba don Allah kiyi hakkuri ni in tafi ko mami da yaran ta zasu zauna lafiya.
Hjy ba zan biki ba zan koma gidan ubana in zauna duk abinda Allah yayi min mai kyaune a rayuwata Allah ne shedata wani kalami na soyayya bai taba hadani dasu yaya ba a gidan nan wanan yana daga cikin kaddaran rayuwata.
Don Allah hjy kiyi hakkuri ki zauna a cikin gatan ki kada ki fushi da mami sabodani kada laifin hakan nima yazo ya shafeni watarana.
Ina fadin hakan na fashe da wani irin kuka mai tsanani na mike tare da nufar wardrobe inda kayana yake cikin jakka a jere ina kokarin daukan jakkar.
Takwara ina yanzun kika gama bani hakkuri akan uwarki idan nayi hakkuri ke kuma ina zaki a cikin daren nan .
Ko so kike in fasa hakkuri da uwar taku mu tafi tare kafata kafarki mubar gidan nan a yau din nan basai gobe ba.
Hjy ba Anchau zan tafi yau din ba zanyi kokari in kai kaina gidan anty safiya har kashe gari ta sakani mota in koma gida nufina ke nan muddin barina gidan mami zaisa ta samu sallama tsakanin ta daku.
Ba zaki bar gidan nan ba koda bana raye sai idan aure ya rabaku da uwarki kamar yadda aure zai rabata da yarta Indo.
Muryan mami ke fadin ke zeey mayar da kayan nan ki fice daga nan ki ban wuri da hjy kije gun su kande ko dakin Aisha ki jirani.
Mami ta bani umurni da hakan da sauri na juya na bar dakin nan na barsu tare da mahaifiyar ta na nufi gurin su mama kande na zauna.
Sun dade da mami da hjy a dakin har bayan magariba san nan salma tace dani hjy tana kirana a daki.
Na mike na tafi ina addu,a a raina Allah yasa sun yake hukuncin in koma gidane gaban iyayyena zaifi min wanan zaman rashin yancin kai da banda shi a gidan mami yau har ni zainab Nazifa ta dafawa satan waya.
Hajiya ta idar da sallah har isha,i ina shiga da sallama fuskan tar a kaina tana son ta fahinci halinda nake ciki take tambayana da nayi sallah na bata amsa da nayi tun dazun hjy.
Zauna ki zuba muna abinci ta fada kai tsaye dai umurni ta bani babu daman yin mussu gareta ke nan.
Itama ba wani cika mata nayi sosai ba na dai zuba kadan kadan sai dai nawa din yafi zama kadan don nasan ba zan iya cinye wanda ma na zuba din ba.
Sai faman cakulan abincin nakeyi cikin sanyin jiki itama dai hjyn haka dai take kokari tura abincin a bakin ta can naji tace kada ki yarda in hada nawa baki karasa cinye wanan dan abincin da kika zuba ba kamar za,abawa yaron goye.
Dole na fara tura abincin da sauri ds kyat nake hadeshi gaba daya raina babu dadi a lokacin har na samu na gama kamar yadda ta umurceni dayi.
Ba zancen hira garemu sai kowa yayi shiru a dakin dan dama hjy ma takan dan jefo min magana jefi jefi.
Washegari aka tashi da shirin tafiya kamar in dora hannu akai ince wayo ni Allah don banson inyi nisa da gida kuma.
Dan dama nan na rike sunan unguwar da muke dana su anty safiya don bam manta da sunan unguwar ba har yanzu a raina.
Ina ji ina gani har aka fara fadin a fito da kayan da za a wuce dashi a mota don masu mota zasu rigamu tafiya nake gani.
Jakkunan kayan mu gaba daya an labta su a mota hakan yasa naji raina ya kara baki nasan yanzu kan zuwa ba fashi gareni.
Hjy ta aikeni dakin mami don in tuna mata zancen maganin ta da za a saya mata nan kaduna.
Ina gab da shiga dakin nake jin muryan mami na fadin saida nace kada ku sayo ticket da zeey mota zatabi ita dasu kande baku maganata ba sai da kuka sayo.
Ba laifin mu bane mami ya J yasa mu saya mata kinga ko ba zamu ce masa a a ba tunda kudin sane.
Gulman ku zai ciku daku har jafar din in dai akan wanan yarinyar ne ido na zuba dani da jafar din a gidan nan za,aga waye zai sare a karshe.
Jikina ya sake yaraf kamar kayan wanki inaji kamar in juya kada in shiga dakin a lokacin sai dai na ba zuciyata sanyi na fada dakin da sallama.
Duk suka juyo suna amsa min shigowana ya basu daman sulalewa daga dakin suka bar mami tare dani ina fada mata sakon da hjy ta aikoni.
Naji ki fada mata za a saye na daga don barin dakin sai naji ta dakatar dani ta hanyar kiran sunana.
Da sauri na koma na tsuguna a inda nake tare da dukar da kaina kasa ina sauraren abinda zata fada min a lokacin.
Mami ta dan dade tana kallona na dan wani lokaci kafin ta bude baki ta soma magana dani.
Zeey ina son ki saurareni dakyau kiji abinda zan fada maki kaina gyada ina wasa da yan yatsun hannuna dana hade a wuri daya ina saurenta.
Ba zan taba bari ki bar gidan nan ba koda hjy bata nuna hakan ba don in taimakeki ki taimakeni na raboki da iyayyen ki zuwa nan.
Saidai zanso kiyi nisa da duk wani dana bawai jafar ba kwai a a ina nufin gaba dayan su muddin kina son mu zauna lafiya dake a zaman mu.
Zancen karatu kuma da mun koma abuja zan sa a nema maki wani makaranta gwaunati ki karasa karafun naki a nan.
Saboda haka in kinyi abinda na fada maki kiji dadina idan kuma kinki to ina mai fada maki zeey zaki kwammace dama baki sanni ba a duniyan nan.
Na riga nagiwa jafar mata amma saboda ke yana kokarin ya bijire min kan umurni na don kawai ya nuna min shi dan zamani ne.
Mami kiyi hakkuri in Allah ya yarda zan kiye ni ban taba magana dashi ba kuma bazan taba ko a bayan ki mami.
Shike nan zeey zaki iya tafiya mami ta fada ba sakin fuska a tare da ita zuwa gareni a yanzu haka na mike na fita daga dakin.
Karfe biyun rana muka fito mami tana makale da yan matan ta dake mata sallama mu kuma muna guri daya dasu ya jalal da hjy sai Aisha dake daga gefen mu tsaye tana sana,an ta da waya.
Ba wanda ya kula da yai min sallama kamar yadda suke sallaman su hjy da su jalal dan dama salma dace zeey za a tafi ke nan na danyi dariyan yake ina fadin sai mun dawo anty salma tace ko sai munzo ba.
Haka motar mu ya daga kamar su jawoni su fidani daga cikin motar yadda suke watsa min harara daga sama har kasa kuma kowa ya kula da hakan.
Karfe hudu duk muna cikin gidan mami na Abuja da farko mami taso raba muna daki ni da hjy don tace naje daki daya zamu zauna dasu kande a nan.
Sai hjy tace ni kuma na zauna dawa idan kin kaita can kinsan ko a gida da yaran yayan ki nake zama ai.
Don haka barmin ita mu zauna tare kawatace ko banza tare muke kashewa mu bisa a dakin mu daga ni sai ita.
Haka yasa na koma da zama a dakina dana bari da farko kafin mu wuce kaduna don yanzun ma a nan zamu zauna da hjy din.
Mami bata da lokacin zama gida tare da mu karfe taran safe baya mata a gida don hakane nake tashi da sassafe nai mata aiyukan dana saba mata a dakin ta harta shirya ta tafi.
Kamar yadda mami ta canza min hakan nima nake canza don a gurguje zan karasa aikina kafin ta fita na bar mata dakin sai idan ta gama zata rufo dakin ta kawo makulli gurin hjyn ta ta fice.
Satin mu daya da zuwa wani yammaci muna zaune da dare a falon dukan mu ya mamud ya shigo muka shiga gaida shi da dawo yana amsa muna.
Ina zaune kusa da kafan hjy naji yana fadin mami monday fa yarki zata fara shiga school don na samo mata makaranta a nan garin.
Da bakin wa kayin wanan mami ta fada a daidai lokacin da nake murnan hakan ina kuma gode masu a raina sai naji wanan furcin nata a bazata.
Gabana ya yanke ya fadi lokaci guda naji taci gaba da fadin ko akwai wanda ya kawo min ita gidan nan ne a cikin ku da kuke nuna min gaba gadi game da yarinyar nan.
Meye gaba gadi cikin wana zancen iyami ina taimaka maki yayi kan abinda baki samu lokacin yin sa ba kuma nautin kine kiyi hakan.
Ko haka yar taki zata zauna a gida ita bata karatu ta taimaki rayuwan ta nan gaba tunda a zamanin nan kome ka zama idan ba wanan karatun baka cika cikkaken mutum ba a idon jama,a..
Hjy kikan so tarewa yaran nan fada a kan gaskiyata da zai tafi nema mata ai sai ya nemi shawarata yaji abinda na yanke a kanta.
Fada muna yanzu ai gashi zaune me kika yanke a kan yar nan a yanzu tunda an hutar dake baki ga hakan ba.
Iyami bansan yaushe hali ki ya sauya ya zama na mutanen zamanin nan wajen , , ,
Hjy ba nufina ke nan ba bandai jin dadin yadda yaran nan suke min abu gaba gadi haka kamar banda daraja a gunsu kamata yayi yazo ya fada min kafin ya samo mata din.
Sai kawai yazo yanzu yana fada min magana haka kai tsaye wai mondaya zata fara tafiya wani makarantar ma ka samo mata din.
Mami inda yaran nan suke zuwa a nan na sama mata itama sai su dinga zuwa tare duk da ita a secondary section zata zauna.
What har nawa za a dinga kashewa a kanta ke nan ina kosu yaran nan kana min korafin yayi yawa da farko saidana haneka.
Mami indai zatayi kararun ai karuwan kowa ne nan gaba don haka kiyi hakkuri nayi kuskure ya fada yana dukkar da kanshi kasa alaman ban hakkuri a gareta.
Allah ya kyau hjy ta fada tare da dafani tana fadin yar nan nayi maki murna ubangiji yasa a shiga da kafan dama nace.
Yaya na gode Allah ya karawa arziki albarka yace ba komai ki dai dage da karatu sunce idan sun gwada ki kinyi nasara zasu iya barin ki inda kike a can kaduna.
Allah yasa hjy ta fada tana tattara takardun dake gaban ta alaman zata bar falon ke nan nayi saurin mikewa ina karban kayan daga hannun ta.
Sai naji tana fadin wa zai dinga sauke su a school din kai ko driver zai kaiku ya amsa da fadin.
Dama ai nike saukesu kafin in shiga office yanzun ma nidin dai ne zan dinga sauke su idan zan fita .
Ka nema masu driver daga yanzu da zai dinga sauke su kai ka wuce office din ka kaji abindana fada ta juya wurin hjy tana fadin hjy zan shiga in karasa aiki a daki.
Ni dai na aje kayan na fito daga dakin don babu wani abinda zan mata a lokacin don haka na dawo falon na samu hjy da yaya mamud suna hira Aisha ta shige dakinta ko lokacin.
Har kasa nakai na kara mai godiya yacs Jafar ne ya saka in sama maki nan don haka shi zaki godewa idan ya dawo.
Sai ki mai da hankali ki samu abinda kikaje mema banda wasa ko wani hali na banza don Allah.
Nagode yaya na kara fada kaina yana kasa nake fadin hakan don gabana na faduwa tun lkkacin daya ambaci sunan ya Jafar din.
Suna ta hiran su da hjy ni kuma ina faman tunanen gargadin hjy a raina a wani bangare kuma ina Allah Allah in ga na fara zuwa makaranta ranan monday din.
Rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya hausa suka fada don yau gani a class tare da diya manyan mutane don an gwadani na ketare da kyat don su ba wani gata da zaka nuna masu su yarda su kaika gaba saidai idan kokarin kane ya kaika.
Na mayar da hankalina sosai ga karatuna banyi kawa ko aboki ba kamar yadda naga wasu sunayi a school din koda yaushe ni kadai zaka sama a class din ina bitar takarduna da akai mana darasi.
Ranan kwatsan mun dawo daga school tun a haraban gidan idona yayi tozali da bodyguard din shi suna tsatsaye waje suna mazurai da idanu don motan mu daya danno kai gidan.
Gabana ya shiga faduwa haka na daure na shiga cikin part din mu da sanda nayi arziki babu kowa a falon sai tv dake aiki a falon shi kadai babu mai kallo.
Da sauri na shige dakin mu inda na samu hjy zaune ta idar da sallah la,asar a gurin tana zaune.
A gurguje na tube uniform din jikina na fada bandaki ban fito ba saidana shirya a cikin wani dogon riga duk kayan da Aisha ta ban ne nake sakawa a jikinao.
Na fito na o da sallah nacewa hjy zan leka kitchen in fito daga can na zauna abina ina taya su mama kande aiki har muka karasa na dawo don yin sallah lokacin har mami ta dawo tana dakin ta .
Tunda na tun karo wuein kamshin turaren shi ya daki hancina na tsaya na dan saurara ko yana dakin in koma kitchen in zauna har ya fita.
Naji banji wani hayaniya a dakin ba na shiga hjy ne zaune ita kade tana ganina take fadin wai ina kika shiga haka daga barin je in dawo naji shiru sai yanzu.
Har yaron nan ya dawo daga balaguron da yayi yana tambayan ki bai dade da fita daga dakin nan ba.
Wa ke nan na tambaya kamar ban fahince ta ba tace wanan bayahuden mana jafari ai ya dawo tun dazun da ranan nan wai wata kasa yaje kallon ball kawai don barnan kudi.
Shiru nayi don ban san me zan fada ba sai kuma hakan yaiwa hjy zafi take fadin anya yar nan kinko damu da yaron nan kamar yadda ya damu dake.
Don shi da zuwan shi ke ya fara tambayana na fada mai kindan fita sai gashi shiru shiru baki leko ba dakin nan sai yanzu daya fita.
Ko uwar taku tayi nasara a kanki ne tun yanzu nace hjy dan Allah ki daina zancen shi dani kada mami taji ta riga da tayi min kashedi a kanshi tun a kaduna hjy.
Ita iyami din hjy ta fada nace hjy kada kiyi mata magana ko dan karatun nan da yanzu nakeyi kada in rasa sa,ata ta wanan dalilin.
Wai maryama kanta daya kuwa gaba daya yarinyar nan ta rikice min lokaci guda na kasa gane inda ta dosa kan zancen nan.
Haka mukai ta shan bambam dashi ban yarda mun hadu ko sau daya ba a gidan tundaya dawo garin.
Ran ba makaranta ina zaune inawa kaina kitso muna hira da hjy ya fado dakin namu daga sallaman shi ya kutso kai ciki.
Ba daman in gudu in shige koda bathroom ns don ya riga daya ganni ko dole na daure na gaida shi tare damai an dawo lafiya.
Shima yadda ya amsa min naji dadin hakan don ba yabo ba fallasa gareni sai na mike zan bar masu dakin don dai kawai in kaucewa warning din mami gareni.
Ki zauna fita zanyi na leko hjy ya fada daga inda yake tsaye yana magana da hjy gashi ya kara haske sosao yayi wani kyau dashi bakin gashin kanshi yayi lub kwace a kanshi sai sheki yakeyi ga wani saje daya bari a fuska tasa wanda bai saba bari shi a fuska ba.
Yana gama magana ya sa kai ya fita ya bar dakin gabana sai faduwa yakeyi min don abinda idona ya gane min din duk da ban kalleshi sosai ba ma ke nan.
Tun daga wanan rana ban yarda mun kara haduwa dashi ba a gidan don ina ganin shima bai faye zama a gidan ba sosai sai jefi jefi.
Ranan zan fito daki ke nan don hjy na falo mami tafita gurin aiki bata dawo ba ina ganin shi na ruga da gudu na koma daki a zatona ko bai ganni ba ne.
Saida ya dan dade a zaune kafin ya mike ya nufi dakin namu hjy dai tana zaune tana kallon shi tare da tausayi mu a ranta.
Ya tsaya daga bakin kofa dakin bai karasa shigowa dakin ba sai hannun daman shi dayayi amfani dashi wurin rike labulen dakin dashi.
Wa kike gudu haka ya fada a cikin muryan nan nasa mai fida sauti mai dadin saurara kunnuwa suka jiyo min hakan.
A razane na juyo ina kallon shi yana tsaye a kofan yadda yake a wurin wani irin tsoro da damuwane suka ziyarci zuciya sosai take jikina ya fara kyarna ta yadda har ya fahinci hakan.
Hannun ya sauke daya tokare kofa dashi yana gyara suit din dayake sagale a hannun nasa karya fadi.
Takowa naga ya fara yi zuwa inda nake haka yasa gana ya tsananta da faduwa sosai a haka ya iso inda nake rakube ga bango ginan dakin.
Wani abu naji yana taso min wanda yasa na duntse idona a hankali kafin ya kara tako ya cin min a gurin.
Jin kamshin turaren jikin shi gab dani yasa na bude idona na dube shi kadan babu sauran tako a tsakanin mu ko daya a yadda muke tsaye a dakin.
Kokarin ja nayi baya sai dai babu inda zan daga don gaba daya ya tare wurin ya tokare hannayen shi a ginan dakin.
Shiru ya ratsa dakin ba wanda yai magana a cikkn mu kamar babu kowa a dakin lokacin.
Inan tsakiyan hannayen shi har lokacin idanuwa na a rutse kamar naga dodo a gabana.
Ga ba hanyar da zanbi in gudu daga wajen don ya hana hakan gareni ya kankame ko wane gefe da zan iya guduwa mashi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DON TURA KUDI ZAKI TURO GA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU NE KACAL KATIN WAYA KI TURA GA WANAN LAYIN 08036959257
YAR UWA DON ALLAH KI DAURE KINA BIYAN HAKKIN MUTANE DON ABIN BAN YAFE BA KALMACE MAI NAUYI GA MUSULMI NAGODE.
Har lokacin idanuwana suna a rufe ga numfashinsa ina jin saukan su a kunnuwana idon na kara budewa don jin shirun da yai yawa na dauka nike haukana a lokacin shi baya ko wurin.
Yana nan tsaye a yadda yaken haka yasa na soma kokarin sunkuyawa ta kasan hannun shi in samu in wuce don tserar da rayuwata ga mami dashi.
Ji nayi ya kamoni ya kankame ni a jikin shi tare da mamaye ni cikin wasu irin abubuwan da ban taba tsintar kaina a cikin ba ko a mafalki ban san da wanan nau,in abinba.
Haka kuma ban taba sanin ana wanan abin ba na dauka sai kafiran turawa da nake ganin haka a film danazo gidan mami.
Suma din kuma idan sunayi kawar da ido nakeyi koma na tashi na bar wurin ga baki daya.
Can kasan makogorna na iya furta innalillahi don Allah ya jafar ka bari kada kayi min sanadin da mami zata koreni gidan nan.
Bai kula da abinda nake fadi din ba yaci gaba da abinda yake min kamar ma zancena ya kara mashi kaimi ne .
Babu inda baya karkarawa a jikinsa don abinda yake min din nikan na sadakar sai hawayen da ke zubomin kamar an sake famfo na barwa Allah lamarin sa duk abinda Allah ya kaddara min mai kyaune.
Muryan shi naji a kunne kamar mai rada yana fadin mami kike tsoro yasa har kika fara guduna kina boyewa ?
Idan mami din ta sakaki ki min hakan ko ta hana ki aure ni kamar yadda na bukata ai ba zata hanani wanan bako ?
Abinda mami taji ke nan a karshe wurin da take tsaye ta mutu a tsaye don mamakin ganin halin data same mu a ciki a dakin.
Da sauri mami ta juya kafin ko wanin mu ya ankara mu farga tana gidan a lokacin ta nufi dakin ta da sauri duk maganan da hajiya ke mata a falon bata jita ba.
Karan sakin kofan da mami tayi ne ya farga damu don dai kawai tsoron dake yawa a zuciyana ne daya rufemin ido ban farga da ita ba tun shigowan ta dakin.
Yanzu kan sheshekan kuka na fara mai don na kula in dai ba mami ba hjy tsohuwa ce ta rutsamu a halin da muke ciki.
Ya jafar don girman Allah don ya rasulillahi ka, , , , , shhh yace tare da fufe min baki da hannun sa na kasa karasa abinda nake nufin fadi karshe.
I boldly care da duk wanda zai shigo ya same mu a haka dake dakin nan idan su basu san soyayya yada yake ba wanan ni bai taba damuna tunda sun hana min abinda nake so.
Naji yaya ba zaka taba damuwa ba don kai nan gidan kune bayan hakan kuma kai na miji ne dama mace itace da kunya ai.
Idan mami ne ta bar wurin nan na tabar da yau ban kwana a gidan nan don ta riga da tayi warning dina tun kan muzo garin nan a kanka.
Babu inda zaki tafi matukar ina raye a gidan nan doIn ko kin tafi dawowa zakiyi ita mami tasan halina idan ke baki sani ba.
Ban taba cewa ina son abu har in sashi a raina ban in rasa samu wanan abin don haka ba zan soma shi a kanki ba.
Naji amma don Allah ka barni in bar gidan nan yanzu tun mami bataji wanan maganan ba yau ta kasheni gidan nan.
Don girman Allah ka daga, daga nan in fice na fada cikin wani irin kuka daya zo min mai karfi.
Maimakon ya daga daga wurin saima naji yana kokarin kara matseni a jikin shi.
Kayi ma Allah kaimun alfama na hadaka da girman iyayyen ka ka daina rike ni haka kana hadani da fushin ubangijin mu.
Ka rabu dani ya jafar ka kyale rayuwana hakana ya huta da wanan ukuban daka sakani a cikin sa yanzu.
Ka taimakeni ka taimaki rayuwana da kake shirin rusa min yau karatuna shike nan na rasa shi tunda mami kauye zata mayat dani ina gap da gamawa.
Nima ki taimake ni zainab don ke kadai zan aura a kasan nan in zauna lafiya dake bani na sawa kaina son ki ba Allah ne ya zaba min ke don hakkurin ki da tarbiyan ki.
Abu daya nake so dake shine ki daina cewa zaki bar gidan nan ko karatun ki zai tsaya ba wanda zai faru daga insha Allahu.
A razane na dago kai na kalle shi kafin in mayar da kan kasa don kwarji da nauyin da yai min ga kallon shi.
Ya daga min gira yana fadin nasan mami zata yarda da bukata na idan na kafe a kanki a cikin sauki.
Don farin cikin ta shine nawa itama nawa shine nata bata taba hanani abu nayi shi ba a duniyan sai wanan karon kinga ko zatayi min adalci a nan.
So da sannu mami zata fahinta ta yarde mana muyi aure in dauki mu tafi can inda zaki karatu sai kince kin gaji da karatu a rayuwan ki.
Wani irin takaicin sa da tsanar sa yake tokare min zuciya ga tausayin kaina danakeji nida kaina kamar in dora hannu aka in ta kurma mai ihun a dakin sai anzo an ceceni.
Sai da ya fahinci ya gama hada min zafi akaina don kansa ya janye min daga banga bangan dayi da farko ya tare ko ina da zan iya sulalewa in gudu daga tsayin dayayi a gaba.
Kamar jira nake ya nuna min kofa in gudu aiko yana nunawa na sheka da gudu ina kuka mukai karo da hjy a kofa da tazo shiga kamar.
Duk da nayi murnan ganin ta amma naji haushin da sai yanzu ta zo dakin duk dadewa da mukayi a tsaye tare dashi zuwan ta yai min kama da zuwan yan sandan indiya da sai an gama cin gari suke isowa.
Fadawa nayi a jikin ta ina kuka take ta rude a wurin tana fadin a rikice maikai mata jafari na fadama kabi yarinyar nan a sannu akwai kurciya a tare da ita yanzu sai ka lalabata tukunna.
Ask her idan nai mata wani abin just magana nayi mata kan guduna da takeyi kawai.
Ba dole ta gujeka ba kaida uwar ka kun saka yar mutane a gaba haka wanan hattaran yai wa yar nan yawa a gidan nan.
Ai saika tashi kaje don uwar taku ta dawo har ta leko nan baka sani ba kana nan kana gyara kanka a wurin mace.
Hjy kefa kikace sai na jata a hankali zata fahinceni na fara hakan kuma laifine yanzu hjy ?
Laifine kan indai zaka dinga sakata kuka haka ko wani lokaci murmushi ya sake mai laushi yana kada kai tare da fadin well i know what to do next barin leka mami ya fada yana mikewa har lokacin ina a jikin hjy ina dan sheshekan kuka.
Yana fita daga dakin na dago kai ina fadin shike nan hjy yau zamana ya kare karatun da nakewa murna ya tafi daga gareno don mami korata zatayi yau gidan nan.
Saboda kawai kun kebe dashi a nan zata kore ki hauka tayi kome daga haka sai kora kawai.
Hjy mami tayi warning dina tun a kaduna kada in yarda in tsaya da danta don ta riga da tayi mai mata ko.
Ita iyamin ta fada maki hakan na gyada mata kai kawai ba baki idan ma har ta fadin hakan ai yanzu bake kika bishi ba shi ya biyo ki ko sai tayiwa danta fada shida ke binki.
Dakin mami ya nufa direct ba tare da jin komai a zuciyar shi ba duk da hjy ta fada mai mami ta leko dakin mu yana ciki yasan kuma ta ga halin da muke ciki a lokacin.
Da sallama ya leka dakin ba,a ansa ba haka yasa kai ya shiga dakin mami ya hango a zaune gefeb gado tayi tagumi da hannayen ta dukka biyu kamar wacce ke cikin tsananin damuwa.
Ta rasa abinda ke mata dadi a duniya yaron nan wani abin kunya haka yake son jawo mata ne duk ita a zaton ta ya bar wanan zance ashe shi yanzu yakema ga zancen wata namiji dai sai a barshi ga abinda yake so ya kwallafa rai kuma.
Kallon mamaki yake mata har ya karasa bakin gadon da take zaune a kai yace mami lafiya kuwa na ganki a haka ?
Wani abu ya faru ne ko wani abin kike tunane haka ke kadai a daki kinyi tagumi.
Ido mami ta dago ta gallamai harara da idanuwan ta da suka kade sukai ja tankar zasu fado.
Ji take kamar ta wanka mai mari da tana iyawa a yanzu so yake ya tozarta ta ya kunyata ta a idon kawayen ta tozarta.
Maganan hjy da take tunawa guda biyu shike taka mata burki ga koran yarinyar nan ta koma kauye.
Saidai idan ta tuna da kalamin hjy da take fadin idan ta kori yarnan a gidan ta sai danta yaje gun iyayyen ta a bashi ita ya aure muddin yaje da waliyan shi makusanta ita kuma a barta tana hargowa a gida.
Ga kuma barazan hjy data ita kuma idan ta matsa sai ta dauke yar ta koma da ita wurinta ta inganta rayuwan ta fiye da tsamanin ta to me hjyn ke nufi da hakan.
Hannun ta ya riko don yaga ko a yanzu da take kallon shi hankalinta na ga tunanen da takeyi a lokacin.
Riko hannunta yayi yana fadin haba mami meye zai sakaki irin wanan damuwan haka kinsan fa yanzu aiki na maki ya, , , ,
Baiyi aune ba yaji saukan mari a lafiyayyen fuskan shi lokaci guda ya dago kai da mamaki yana kallonta da kyar ya iya furta mami you slap me ?
Ko zaka ramane tunda yanzu ka girma har bakajin umurnina kake ganin kaika isa har yanzu kake mamakin na mareka ko ?
Allah yasa yanzu da idona na gama ganin ku da kazaman yarinyar nan a dakin hjy ba wani ya tsegunta min hakan ba.
Yanzun kai bakaji kunya ba ace kamarka jafar kamar kafa kamar kake rugumar wanan kazaman yarinyar zainab yarinyar da wani lokaci ma tsami takeyi da wari.
Da sauri ya dago kai a karo na farko tun bayan marin data kwasheshi dashi ya dukar da kanshi bai daga ba yana dafe da wurin cikin mamaki.
Wari mami wari fa kikace yarinyar nan tanayi ban taba jin haka ba a tare da ita asalima ni yau wani kamshin ma naji a wurin ta.
Mami nifa kome takeyi ina sonta hakana da don itace zabina a duk yadda take ya fada yana kokarin mikewa tsaye.
Jikin mami ya sake yaraf kaman ruwan sanyi a gabanta yau jafar ke wanan magana kan mace macen ma wai yar aikin gidan ta wanan wani irin lalacewa ne ya kama dan nata haka?
Ganin ya soma batrin dakin don tafiya don marin ma datayi mai shiko a jikinshi ya yadda nunata take ta soma magana tana fadin.
Yau da uban ka yana raye jafar zakai min haka ince ga wace nake son ka aura kace kai ba hakan ba yaushe ka fara wanan halin banzan na kafi ban sani ba ?
Mami daddy , aiko daddy yana raye ba zai hanani zaban abinda hankalina ya kwanta gareshi don dama daddy yana raye aida yanzun akaiga matsaya ga zancen nan don shi daddy ban taba ganin ya kyamaci wani a rayuwan shi ba
And mami kin san koda daddy yake da rai mun fi shakuwa dake fiye da daddyn mu
Mami kin kasa fahintana ne kin kasa tausa zuciyar ki akan yarinyar nan why mami zaki hanani abinda nake so.
Ba zaka aure ta ba nace bazaka aureta ba ko dole zakai matane mu gani idan zaka iya No mami ba dole amma nasan itama tana sona don naga alaman hakan tare da ita.
Tsoron warning dinki gareta ne take amma ba matsala zan gwada sa, a ta tunda kinban dama a yanzu.
JAFAR mami ta fada da karfi ya fice dakin ba tare daya juyo ya kalleta ba tunda mami take da danta haka bai taba faruwa a tsakanin su ba sai akan wanan dalili.
Me yaron nan yake nufi dani da wanan kalamin nasa tursasa yarinyar nan zaiyi taso shi tunda a yadda ta samemu a dakin da alaman tsoro shi a fuskana don kuka ta samu ina masa.
Ma,ana dai shi jafar din ne ke bibiyan ta a dole meya gani ajikina har ya mace ga son yar nan haka.
Yarinyar da saida tazo nan ma tadan yi wanan clean din da yake rudin shi ta runtse idanunta tana mai fadin kada Allah yasa so ya rudi yaron na ya aikata wani abinda zaija mata kunya ga idon mutane.
Ya zama dole ta jashi a jiki tasan hanyar data bi ta lalashi da lalama ya janye kudirin shi akan yarinyar na don koranta gidanta baida wani fa,ida a yanzu idan tayi amfani da maganan hjy.
Zeey bata da laifi ta sani amma wanan dalilin ya jawo mata tsanar yarinyar ba gara ba dalili taji yarinyar ta fita mata rai ga baki daya ta wanan dalilin.
A dakin mu hjy ta samu ta lalabe ina kwance lamo sai faman ajiyan zuciya nakeyi ga tunanen abinda ya faru tsakanin mu yaki fita a rai.
Duk motsi nayi sai inga kamar a lokacin abin ke faruwa dani uwa uba ga kamshin turaren jikin shi daya dameni a hancina yana kokarin saukar min da kasala a jikina.
Mikewa nayi zubur hjy dake zaune ta kalloni tare da fadin ina zaki ban daki zan shiga inyi fitsari na fada.
Na shiga ta bini da kallon tausayi tana gyada kai Allah kadai yasan yadda take ji a zuciyar ta kan yaranan a yanzu.
Na dan jima a ciki kafin in fito rike da digana dana cire ina daure da tawul a jikina wanda nake kewayawa dashi don a dakin muka same shi wani babba haka dashi fari mai kyau da yan flawer a jikin shi kanana a gefe.
Dogon rigar yar katin da anty safiya ta saya min da zanzo gidan mami na jawo na zauna saman kujera ina dan shafawa jikina mai don kada in bushe.
Au yar nan wanka kikayi gabanin magariban nan kudai yaran yanzu baku da tadan lokacin yin abu.
Hjy na magana tana kallon gashina da har lokacin yana tuke babu kitso a kaina sai fibon dana daure gashin dashi ta bayan kaina.
Kafin ta mayar da kallonta da kyau a inda nake tanaci gaba da fadin yadda kike nan da tsari irin hakane mutanen boye ke so su shige jikin mutum a sauke.
Mutanen boye kuma hjy na fada ina juyowa gareta tace kwarai kuwa yar nan ai su abinda sukw so ke nan urin wanan sakacin da kukeyi a yanzu take sun shigeka suyi maka illa.
Kinga mu a zamanin mu duk irin wa yan nan abubuwan musanshi iyayyen mu na fada muna mukiyaye don tsaron lafiyan mu.
Hjy daga yau na daina ba zan sake kewaya a wanan lokacin ba in Allah ya yarda tace dadai yafi maki kam.
Waini meya hadaki da mutumin naki ne dazun kike ta wanan kuka ina saka riga a jikina da sauri don maganan da tayi naji wanan maganan.
Juyowa nayi da a daidai ina karasa saka rigan na dauki hulan dana dora saman gado na dawo kusa da ita na zauna tare da dan marairaicewa nace hjy ki taimake ni ya jafar yafita daga tsabgata a gidan nan don Allah idan ba haka ba mami zata koreni ta fada.
Kin taba ganin inda aka cirewa mutum rai ga abinda yake so farat daya wanab sai uwarku da take ganin tana iya hakan.
Wai yau dai ki fada min yar nan shin kina son jafarin nan ko bakya son shi inji da sauri na dago kai na kalli tsohuwar sai kuma na dukar da kaina kasa don bansan amsan da zan bata ba.
Ince ina son sa in kaishi ina ko ince banson jinin ta kiri kiri haka a gabanta anya zataci gaba da sona nima duk da nasan tun kan haduwan mu da jafar din tsohuwar take nuna min kauna sahihi.
Sai kuma yanzu da take nuna min kauna tankar itace ta haifi iyayyena ta san zafina fiye da kowa ta yaya zan iya bude baki ince banson jikanta mafi soyuwa a gareta ido da ido haka.
Nasan wani abu yanzu ma saboda shine ta tsaya min take tsare min komai a gidan yadda ya dace.
Murmushi naji tayi tana fadin to ai abu yayi kyau takwara shiya nake kara sonki saboda halin nan naki na alkunya ga kuma girmama mutum saidai iyami taki gane hakan .
Ke din wani baiwace a garesu takwara naso iyami ta gane hakan amma idonta ya rufe ta kasa hangon hakan da kanta.
Nidai har ta gama maganan daidai ana kiran magariba ga agogon dake dakin namu ta mike da sauri zuwa bandaki do bata wasa da ibanda ta kiran sallah kawai ta kan jira ta mike ko wani lokaci.
Bayan kowa ya kammala komai aka fito cin abincin dare kamar yadda aka saba da kyat hjy ta shawo kaina na yarda na fito daga dakin.
Mun samu mami a falon har ta fito tana zaune tunda muka tun karo wurin ta dago kallo daya tayi min ta kawar da idon ta gareni tana fadin hjy kin fito yanzu nake zancen ko lafiya yau baki fito da wuri ba haka.
Muna daki nida mutumiyar ina bata labari mutanen da can yadda suke rayuwan su ga wuri hjy ki zauna tana fadawa mahaifiyar nata cikin girmamawa gareta.
Kafin ta dago kai inda nake tana fadin cikin bada umurni ke jeki aka hijabi a jikin ki baki ganin gidan nan akwai samari ne kike fitow haka dake.
Ya ilahi nikan ko me zanyi mami a yanzu bata ganin haske na na juya naji hjy na fadin zancen banza ke nan yo ai shigarta yafi naki dana yarki mutuntuwa bakiwa wanan mai zama kamar arniya a gida ba haka kai babu hula ko dan kwali sai wanan da jikkn ta yake a suturce.
Hjy mu muharamin si ne ita fa irin shigar da ta dauko yi ke nan har yaro nan ya jefa kanshi a tarkon ta.
Ita yar nan din tasan ta danawa wani tarko da ace hakan take da baki fada ba da bakinki yanzu don da kin gane kabewa ruwane.
Tsohuwar ta juyo gareni tana fadi jeki ki saka hijabin ki dawo muci abinci nikan ina shiga dakin ban kara fitowa ba na neme wuri na kwanta ina sharan kwalla.
Abuja ba kaduna bane don ko sunan uguwanin su ban gama sani ba sabanin kaduna da tun ban shigo shi ba nake jin sunaye unguwanin cikin shi a bakunan mutanen kauyen mu.
Ina barin wurin mami ta mike ta nufi dakin dan lelen ta a karo na farko tun dawowa shi Nigeria don ba dabi,an ta bane zagaya dakin samari nata.
Kofan dakin yana rufe ta murda taji shi a ruwa saidai karan tv dake aiki ana wasan kwallo tana dan iya jiyo hayaniya daga inda take tsaye.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣9️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA YAR UWA DON TURA KUDINSA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN DARI UKU KACAL A WANAN LAYIN 08036959257 NAGODE GA WANDA YASAN ZAFIN ABINDA NA FADA.
Da mamaki ta juya don a zaton ta yana cikin dakin sai dai bataji alaman mutum a part din ba haka ta dawo dakin ta ta nufa direct .
Har ta zauna ta bude system dinta da niyar tayi aiki a cikin sa sai zuciyar ta ba zai barta tayi abinda take so ba a lokacin.
Har dare duk wanda ya shigo gaida ita tana tambaya idan ya dawo sai suce basuga shigowan shi ba kuma security din shi basa nan saidai ga wayan shi na shiga kuma karshe taji wayan a kashe.
Washegari wanan dalilin ya hana mami fita aiki da wuri ni dai nagama mata komai tana bandaki kafin ta fito na karasa na fita daga dakin shiryawa nayi a gurguje kar driver dake kaimu school ya jirani.
Mami ta gane me nake nufi don ta fahinci tun jiyan ina gudinta don ban fito ba ita kuma bata tambaya ba duk ta san banda laifin kan hakan amma zuciyar ta ya kasa daina jin haushina.
Zazzabi mai karfe gaske yake ji a jikin shi tunda ya falka da safe da kyat ya iya shiga bandaki yai wanka ya fito yayi sallah asuba ya koma ya kwanta.
Mami ta fito daga dakinta ta samu hjy zaune a falo ita kadai tana kallo wa,azi da takance kafin mu kai mata kafin mu fita da safe.
Mami ke fadin hjy tun jiya banga shigowan jafar ba ko kinga fitan shi da safen nan da mamaki hjy ke fadin yanzun nake maganan shi a raina ni kadai.
Ko tafiyan yayi babu salma kuma wanan karo ma mami ta dan yi tunanw tare da fadin anya don bai dade da dawowa ba da wuya ya sake fita.
1️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
BISSIMILLAHI RAHAMSNIN RAHIM DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI INA GODIYA GA ALLAH DAYA BAN DAMAN FARA WANAN LITTAFIN, UBAGIJI INA ROKON KA YADDA MUKA FARA A SA,A MU KARASA SHI CIKIN FARIN CIKI DA JIN DADIN JUNAN MU.
YAN UWA MASOYANA HAR KULLUN INA MAI KARA BAKU HAKKURI DA KUYI HAKKURI DA ZAMAN TARE ZOMU ZAUNA ZOMU SABA DA FATAN ZAMU FAHINCI JUNA DAKU DON SAI KUN KARA HAKKURI DANI SAMA DA FARKO A YANZU KASANCEWA ZAN HADA TAURA BIYU A BAKI LOKACI GUDA.
BADON KOWA BA NAI HAKA DON KUNE MASOYA NA MASU KAUNATA A KULLUN FARIN CIKIN KU SHINE NAMU DON DA BAZAN KU MUKE RAWA A KODA YAUSHE.
FADA KARWAN DAKE CIKIN LABARIN NAN UBANGIJI YASA MU AN FANA DASHI AKAN MU DA YAYAYEN MU ALLAHUMA AMIN.
DARI UKUNE HAR YANZU BAN KARA BA IDAN KINA SO SAI KU TUNTUBENI A LAYINA DON HAR YANZU DASHI NAKE AMFANI BUT ONLY TEXT DON DA WUYA KIRA YA SHIGO MIN A NAN YANZU.
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MTN KO EIRTEL NAGODE ALLAH YASA MU DACE DA RAHAMOMIN SHI AMIN.
A hankali take saukowa daga matakalan jirgin jirgin mai tambarin Nigeria Air way daya sauka a filin jirgin malam Aminu kano.
Fuskanta yana saye da bakin glass din ido sai takunkumin dake saye a fuskan nata bayan ta yan samari biyu ne masu tsanin kama suna mara mata baya.
Doguwar rigace baka a jikin ta sai gyalen shi data yafe har zuwa kanta takalman dake kafanta flat ne basu da wani tudu sosai .
Sai handback din hannun ta data riko wanda ba wani babba bane sosai dan madaidaici dashi.
Kallo daya zakai mata ka gane hamshakiyace ita din don siffan shigar da tayi kawai ya isa ya nunama hakan.
Hjy Iyami ke nan matar tsohon Ambasardor din kasar America wanda ya wakilci Nigeria a 1986 zuwa 93 .
A hankali ta runtse idanuwan ta kafin ta bude su ta kara kallon yanayin kasan nata na haihuwa wanda a yanzu ya zama mata abin kallo.
Duk da dadewan da tayi bata a cikin kasan hakan bai hanata ganin wasu abubuwan da ta bari ba a tsawon shekarun data kwashe bata kasan.
Da mamaki irin halin gwauntin kasan ta Nigeria a ranta taci gaba da saukowa a matakalan jirgin sannu a hankali duk da yanayin kasan nata hakan bai hanata son ganin ta dawo kasan ta na gado ta zauna tare da iyalan ta ba.
Easy hajjajo daya daga cikin samarin dake bayan ta ya fada don ganin irin yadda take bin ko ina da kallon mamaki don rashin ganin wani cigaba da da kasan tayi sosai a zuwa nan lokacin data dawo.
Don tun bayan barin mijin ta aiki sai take can da iyalinta dake kararu inda itama take aiki da wani company a can hakan ne ya dauke mata hankali da gida sosai.
Sai yanzu take ganin dacewan dawowa gidan a cikin yan uwa da abokan arzikin su da suka bari badon komai ba sai don tarbiyan yaran ta da jikokin ta dake tasowa yanzu.
Saboda yawan haramtatacen al,adan da yanzu ya mamaye duniya sai take ganin namu tarbiyan na malam bahaushen kamar daban yake da sauran tarbiyan wasu al,umman na duniya a yanzu .
Don shi malam bahaushe yana mayar da al,ada ya zama addini sosai a gareshi balle kuma abinda addini din ya koyar damu.
Duk da lalacewan duniya a yanzu malam bahaushe yayi kokari wurin ingata wasu tarbiyan da su koma kamar addini a garshi wanda yake taimakon al,umma a yanzu.
Hakan yasa ta yanke shawara ba tare da zaunawa ta shawarci kowa daga cikin a halin nata ba a yanzu da take shugaba a gidan ga baki daya.
Ba karamin tashin hankali ta fuskanta ba a gurin yaya da jikokin ta don jin zancen komawa sun gida Nigeria da sukayi.
Wanda hakan yasa ta rufe ido taciwa kowa daga cikin su mutumci kan umurni ta bayar ba rokon su takeyi ba.
Hajiya Iyami bata fada ma kowa ba saida komai ya gama kammala daga banhareta a yadda take son komai yazo mata daidai idan sun dawo.
Gama daga gyaran gida zuwa company da sauran abubuwan rayuwa ta rigada ta kammala komai yadda zai tafi mata idan sun zo ba tare da sun sha wahalan komai ba tunda akwai kudin su ta fitar aka aiwatar masu da komai yadda take bukatan shi.
Har zuwa yanzu da Allah ya nufa sun tataro sun dawo Nigerian da zama inda duk tawagan nata suke ransu a bace don suna ganin ta rabosu da rayuwan inda suka saba dashi yanzu ta kwasosu zuwa kasan da duhun kai da jahilci yayi katutu a ko ina.
Alhamdullahi a bangaren hjy don ta isa da kowa na ahalin nata daga mazan su har matan su babu mai iya musa mata ga bukatan nata idan ta fada.
Haka yasa abin ya kara zuwa mata da sauki sosai don bata samu tangarada a kowan su ba sai gun babban danta koshi ta daga mai kafa saboda irin aikin shi ne a can don shi tun gama karatun shi yake zaune a kasan chaina inda yake aiki tare dasu.
Ta yarda da imanin shi dari bisa dari don ta auna shi taga yana da riko da addinin shi yana kan tarbiyan da suka bashi tun farko.
Wanan dalilin yasa ta yarda ta barshi a can inda yake aikin wanda a yanzu zamuce shine dauke da nauyin komai da kowa na ahalin don iya sarrafa na,uran computer daya iya da wasu fasahana zamani kasan na chaina ta dauke shi yake aiki tare dasu dama wasu company na kere keren zamani.
Motocine a jere a da suka zo daukan su wanda duk gaba daya nasu ne da aka saye da sunanyen kowa a gidan.
Baya bo ba fallasa fuskan hjy iyami a dan sake tana farin cikin ganin yan uwanta dana mijin ta da sukazo filin jirgin don tarbon su.
Aka dan gagaisa a gurguje inda kowa ke son nuna kulawan shi a garesu kamar dai yadda akeyi ga kowani mai hali a cikin zuria,
Bayan shigar su motane inda sai a lokacin ta fata samun natsuwa a hankali ta runtse idanuwanta tana mai tuno da mijin ta marigayi Alh ma,azu ambasado.
Wanda shine dalilin gatansu a yanzu har suka kai hakan ga Allah ya azurta yaran su da ma wasu dake zaune a karkashin inuwan su ta sanadiyar shi.
Saidai ubangiji bai nufi yaga wanan baiwan ta yayan nasa ba a duniya don yanzu shekara kusan goma ke nan da Allah ya karbi rayuwan mijin nata.
Duk da hakan suna zaune a can waje kamar yadda suke zaune tun farko da yake raye rasuwan shi bai sa sun dawo gida ba tun wanan lokacin saboda aikin ta dana yayan ta da sukeyi a can.
Dan tafiya sukayi kasancew nisan kano da kaduna ba wani tazara mai tsawo bane sosai yasa basu kara wani wahala ba sosai.
Duk hjy na cikin halin tunanen irin rayuwan da zasuyi a nan din yanzu cikin yan uwa da abokan arziki a haka suka shigo garin kadunan don ita bata ga wani nisan tafiyan da yaran nata keta faman jan tsukin nisan sa ba .
A nan ma sun samu dandazom yan uwa na kusa da suka cika gidan suna murna da zuwan wanan family din.
Anci ansha an gagaisa tare da tambayan bayan rabo inda yaran nata da duk mazane sai autar ta da matar danta dayayi aure saidai bata yarda ya auri yar can ba yar nan cikin dagi ta aura mashi aka kai mata ita can suke zaune lafiya da ita don iya zama da sarakuwar nata da ta iya.
Tun wanan ranan rayuwa ta koma masu sabo a gidan ga yan uwa na nisa da kusa dasuke zuwa taron su da murnan dawowan su gida lafiya.
Dawowan ta kasan yasa ta dauko diyan yan uwa mijin ta mata biyu ta hada da yarta suke zaune a tare.
Saidai asali ba itace ta dauko su ba sudin ne dai sukaga wurin zama suka zauna a gidan tare dasu.
Hajiya bata nuna komai ba illa kara jan su a jikin da tayi suka zauna a tare da sai yar sister daya suka cike su hudu yan mata a gidan.
Rayuwa na jin dadi da sakewa sukeyi don hjy iyami na tsaye da saka ido ga motsin kowa a gidan.
Saidai ta fanin karatu da jin dadin rayuwa a cikin gida duk abinda suke so a ransu tana ganin ta kawar masu da shi don kawai kada su gani ga wani har su saka rai sukai ga dauko mata magana.
Ta farko itace salma yar gurin kanin mijin nata dake kula da duk wani al,amarin su daya shafi gida don shi suke sakawa a gaba tankar maigidan nata yana raye don mutumin yana da fahinta dakuma biyayya daya dace.
Sai Rufaida diyar autar su maigidan nata dake aure a jos a can suke zaune da mijin ta da yaranta Rufaidace yarta ta biyu itama dawowan hjy nan kasan .
Daga zuwa da sunan hutu tun lokacin bata koma ba take zaune tare dasu don jin dadin irin rayuwan da ake a gidan.
Sai ta uku jamila ke nan diyar autan su hjy da ita kanta hjy ta dauko ta don ta sahalewa yar uwan nata nauyin yaran da suke a gaban ta zata debe mata wani kewan itama a matsayinta na yar yar, uwan haihuta.
Tankar yar cikin ta take ganin ta a wurin ta don hakan ta daukesu gaba dayan su tankar diyan data haifa a cikin ta suma ba laifi a nasu bangaren hakan suke kokarin nuna mata kamar yadda itama din take kokarin nuna masu duk daya suke a wurin ta.
ANCAU
Tun a soron gidan nasu take jiyo muryan Asabe kakar su data haifi mahaufisun tana faman zazzaga bala,i.
Dukda bata shiga gidan ba tasan bada kowa Asabe ke wanan fadan ba haka illa da mahaifiyar su.
Don inda sabo aita saba da wanan hali na Asaben don tun bata da wayo da wanan hali ta bude idanuwanta a gidan.
Kusan kullun fitinan Asabe ne ke tayar dasu daga barci na yau daban na gobe daban.
Yau ma daga inda take take jiyo muryan Asaben tana fada akan iccen girki da innar tasu.
A haka ta karasa ciki rai bace duk da gajiyan ranan data kwaso ga yunwa ga kishin ruwa don tun safe da ta fita bata karya ba .
Hakan kuma ta juyo gida da kafa duk da nisan dake akwai daga makaranta zuwa gidan su.
Shigowan Abu gidan bai hana Asabe fadin abinda take fadawa mahaifiyar tasu ba a lokacin.
A daidai lokacin inna ke fadin adan maraice umma dama ba wani icce mai yawa bane dashi nayi koko da safe yanzu kuma na danyi muna danbun tsakin da akwai don yaran nan idan sun dawo su samu abinci.
Duka bakin wutan baifi guda hudu da guntu indon ruwan dumine barin hada gawayin nan sai ruwan yayi dumi ki samu ki watsa din.
Salman Abune yasa su juyowa gaba dayan su sai dai inna ce tayi karfin halin anwa a lokacin duk da tana cikin rudu da rikecewan bala,in Asaben.
Asabe na fadin to sannu issasa mai diya ke kika san zafin diyan su kin iya kokarin nema masu abinda zasuci.
Niko nawa dan dabai damu dani ba ai haka yasa kafa ya fita bai damu yasan da damuwata ba.
Saukin abindai kema yaya matane a gaban ki, kinkin zuciya duk da gorin da kike sha a gari ki haifa mashi ko da naji dayane da zai taimaka mai idan karfin shi ya kare yasan yana da magaji.
Ke kenan kullun dauksn ciki kina zuba mai diya mata a gida yau ace kitso gobe kumshi sai ko na omo.
Ta yaya zai samu ya aje kullun laluran su yana kara yawa gareshi kullun yana fita nema ba matai maki sai Allah.
Da maza kika haifa ai zai sa ran zasu taimaka mai a wani gurin ga wanan data saka kanta wani karatun boko da baida amfani a gurin ya mace.
Abu dake kallon ta da mamaki tana cire takalmin makarantar dake kafanta wanda duk ya sude a titi saboda rana da yawan bin hanya ga ba kudi balle a saya mata sabo dole haka take maneji dashi.
Saukin abin ma yanzu duk da karancin shekarun ta amma haka ta samu don kokarin ta ba,a taba mayar da ita baya ba har takai aji shida tana neman fitane yanzu.
Duk irin matsin da Asabe kewa mahaifi su akan karatun nasu baida wani rana garesu kasancewar su na yaya mata gareshi.
Don a cewar ta aure zata masu da zaran Abu ta cika shekara goma sha biyar da haihuwa a duniya don ko yanzu wasu daga cikin sa,annin ta sun riga da sunyi aure suna gidajen mazan su zaune daram.
Muryan Asabene ya dawo da ita ciki tunanen da takeyi tana fadin ke kuma munafuka ki kura mi ido kuru kuru kina kallona dasu.
Don rashin kunya rashin tarbiyan da baku samu ba tun farko ga uwar ku babba na magana yara suna kashe shi da ido don rashin kunyan da kuka gada a wurin uwar ku.
Karya nake fada ba gaskiya na fada ba komai ya samo yana gurin ku keda yan uwan ki da makiran uwar ku ku gaku ga bawa na haifar maku ko ?
Ice ma da mutum zai saka ruwan dumi ace an kona shi a gidan nan gaba daya wanan wani irin masifane yaron nan ya haifar min a gidan nan.
Baki na turo gaba don jin irin cin zarafin da kullun Asabe ke muna muda mahaifiyar mu har wata rana takan tsaya sai baba ya saki inna ko kuma ya kara auren macen da zata zo ta dinga haifa mai diya maza a gidan mu.
Da kyat Abba da wasu makwabta sukan iya shawo kan Asabe idan ta fara wanan bambamin nata lokacin.
Inna dai tana duke a bakin murhu tana kokarin hura wuta da gawayi ne data dan kashe dazun sai faman fifita wutan take don ya kama.
Daki na shiga na kwabe tufafin makaranta dake jikina don sanin bamu da clean din da zamu wanke a yau don gobe haka yasa na kwabe su na baza a dan gambun langa langan kwanon dake kofan dakin namu nafito.
Wurin madafin namu na hara ina fadin inna kawo in hura kije ki huta hakana da ranan nasan tun safe baki huta ba.
Barshi inna ta fada tana kokarin boye fuskanta gare ni don kada inga hawayen dake zubo mata a idanun ta a lokacin.
Wanda nasan ba komai inna kewa hawaye ba sai gorin diya matan da Asabe ke mata don indan don fadan barana da Asabe ke fadin tanayi ne ta saba da wanan sai dai wana gorin ne inna bata iya shayewa a ranta sai ta nuna gazawan ta anan.
Da kyar inna ta yarda ta bani maficin tana fadin kije ki huta yar mairo dan inna bata kiran sunana kasancewata yar fari a garesu.
Ina tsugune bakin murhun Abba ya shigo gidan da kayan aikin shi idannun shi ya sauka a kaina yake fadin yar mairo kece har kika shiga girki daga dawowan ki haka?
Dagowa nayi daga inda nake ina fadin Abba sannu da zuwa na nufo shi don amsar ledan dake hannun shi.
Bayan na karba na juya don zuwa dakin su in aje Asabe ta fito tana fadin to to mai zaki tura daki daga kawowa yar nema data gaji kilibibi a gurin uwarta.
Kai haba umma ba komai bane a ciki sai dan garin tuwo da kubewa ko za a samu a dan tuka da dare a samu naci .
Don na fita dazun ban samu bada ko sisi ba a samu ko abin karyawa a gidan nan ina can na damu da tunane tun safe ina faman babu kwasta duk masu zuwa sai cewa suke ai masu bashi idan sun samu zasu kawo kudi.
Kai Amma mutane sun lalace yanzu da son bashi facin ma shi kanshi bashi za ai masu shi kai Allah ya rabamu da fititinun duniyan nan .
Sai lokacin Abba yakai kasa yana fadin barka da wuni umma mun wuni lafiya ya gidan kuma.
Mun wuni lafiya ba lau ba dai tunda ko ruwan da zan dan samu in watsa a gidan nan ban kaiga samu ba har yanzu.
Don kawai nace bazan iya wanka da farar safiya ba sai kawai a hana min ruwan ina kallo wanan matar taka ta hura wuta a gidan nan har ta gama abinda take saida taga icen ya kone ga baki daya .
Amma yarinyar nan ta kasa saka min ruwan dumi in watsa don bakin ciki da rashin sanin muhinmancina a gidan nan.
Daga inda Abba yake tsaye yana jin Asabe takai ayah yace kiyi hakkuri umma .
Kin sa halin da nake ciki yanzu aikin ne nawa babu kasuwa ko ina ya rufe yau kwana uku sai ita saudatune ke dan dabara a cikin aljihun ta muna samu muna dan tabawa.
Asabe tace da mamaki karara a fuskan ta take fadin haka ka koma ban sani ba dan nan ?
Kai bakaji kunyar fadin wai ashe mace ke ciyar damu duk kwanakin nan a gidan nan ba.
Mafarin abin gari ana yadamu da fadin talaucin mu yakai haka har mace ce take ciyar damu a gidan nan kai ka kasa.
Kaga amfanin haihuwan da namijin da nake fadama ke nan da yanzu yarinyar nan namiji ne aida ta fara taimaka maka ta wani gurin.
Inna ta fito dakin ta nufi wurin madafin danbun tsakin masaran data hadane ta shiga rabawa yayin da tsakar gidan namu yayi shiru kowa ya zuba idanu yana kallon inna.
Na Asabe ta fara zubawa ta mike ta nufo ta tana fadin umma akai dakine ko a kawo maki nan aje anan in gani Asabe ta fada a hasale.
Saida Inna ta kai kasa don girmamawa ta aje kwano a gaban ta inda take zaune saman kujera dan tsugunno.
Bude kwanon samiran tayi tare da juya dan danbun dake cikin kwanon a yatsune tana tabe baki kafinta dago kai tana fadin.
Saudatu wanan abincin fa kamar za,aba dan goye shi ta juya wurin Abba tana fadin ka duba dai ka gani da idanuwan ka yanzu dan abinda aka zubamin.
Don kawai kace itace ke ciyar damu a gidan yanzu ai dole wullakanci ya shigo a bani abinda akaga dama don kawai rainin da kaja muna don kasawan ka yanzu da gidan.
Umma ba hakana bane kiyi hakkuri tsakin ne baida yawa iyakarshi ke nan dan gyara don yaran nan dake.
Nasan nida malam ba samu zamuyi bama a karshe tace duk da haka a kara min don wanan dai ba isane zaiyi ba ehhe.
Kallin Asabe nayi lokacin da naji ta fadi hakan ina mamaki hali rashin tausayi irin nata duk da jin zancen inna din da tayi.
Dakuwa ta jefo min da hannun tana hagu tana fadin daina kallo na yan nema mai kama da yanyawa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL TA BANK KO KATIN WAYA DON TURAWA A BANK ZAKI IYA TURAWA A WANAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK ALLAH YA BADA IKON BIYA A CIKIN DAUKI AMIN
Ki daure ki guji shiga hakkin wani abinda ka raina shike zama babba gareka don Allah yar uwa mu guji daukan hakkin a kan mu ki daure ki biya ki karanta don Allah.
Hjy ce zaune a falon ta hannun ta rike da waya kaya take oder da za, a turo masu dan yanzu ba sai ka fita zuwa waje ba idan kasa hutar da kanka waya ya wadatar da komai ga kowa.
Sallaman da akayi daga kofane ya dawo da ita cikin hankalinta ta dago kai tana kallon kofan shigowa falon nasu.
Da fara,a a fuskanta tana aje wayan daga gefen kujera take fadin kune tafe sannun ku da zuwa a cikin fara,a kamaf yadda ta saba tarbon duk wani dan uwa da zaizo gidan musanman daga bangareta kona mijin ta .
Yanzu ma yan uwan mijin tane su biyu sula shigo gidan barin abinda takeyi tayi ta tari bakin nata.
Yau kan mun taki sa,a kina waje don zuwan mu biyu ana fada muna kina ciki bazamu ganki ba.
A daidai lokacin ta sauke glass din dake idon ta tana fadin abako fada min zuwan ku ba gidan nan ko sau daya.
Dayan tace yau dai aimun taka sa,a mun samu kina wajen dan dariya hjy iyami ta sakeyi tana fadin mun dade bamu haduba.
Safiya ya bayan rabo wace ta kira da safiya tace wallahi haka al,amari yakan kasance ai rayuwa ke nan idan na tuna baya sai nakanji kamar abubuwan da su dawo sabo.
Dariya sosai hjy iyami ta sake tare da fadin kin tuna zamanin kurciya ke nan dai ga wanan zancen naki.
Safiya ta lumshe ido tana bin lafiyan kujera sanyin AC yana ratsa jikin ta a hankali tare da fadin bari matar yaya ai kowa tuna bara baiji dadin bana bane.
Jin hakan hjy ta fahinci mai take nufi yasa tayi saurin kawar da zancen tana fadin bari a kawo muna abinci muci nima yanzu na dawo gidan .
Yau na fita ziyarane har gidan su Ado da salihu nake don tun zuwa na garin ban leka kowa ba bako dadi mutum yana kulaka kai baka mayar da kara akace.
Tana fadin hakan ta mayar da hankali kan wayanta dake gefe dauka tayi ta kira mai aiki tare da umartan a kawo masu abinci tana da baki a falo.
Kai matar yaya wai wasu baki har yanzu dai wanan halin naki yana nan ashe ance idan kasan mutum ko shekara nawa ne kada ka tambayi halin sa.
Murmushi hjy tayi tana fadin meye duniya sa,ade wanan duniyan har nawa yake ga bawan sa.
Idan badon muzo mun gani da idanun mu bazamu taba yarda da kina nan a yadda kike ba a yanzu.
Wai sa,ade ina da wa yanda sukafi min kune a rayuwa duk mace mai hankali da tasan ya kamata ai baki nata ba ko yaya yake kuwa.
Don samun duniya sai idon ka ya rufe ka mata da goben ka ko makomar yayan ka yau fa in mune gobe bamu bane.
Wani lokacin koda kana raye sai kaga anayi ba tare da kai haka abubuwan suke zuwa ai kinga gara mutum ya gyara tun duniya bata kisa ba.
Mai aikin data kirane ta shigo dakin dauke da katon ture da manyan kuloli abinci saman shi dining ta nufa da zuman jerawa yadda ta saba.
Sai hjy iyami take fadin ki kawo muna nan yau a kasa zamu zauna muci dan dariya suka kwasa tare da fadin za a tuna da baya ke nan dai.
Lokacin da yaya yake aiki lagos muna gida tare dake ake zuba abinci a cikin katon ture mu taru munaci ana hiran arziki.
Ai wanan abin duk shigowan sadiya ya kawar muna dashi tana fadin wai muna taruwa ana gulmanta bazan manta da zuwan wanan yar uwan hjyn mu datazo daga kauye take fadin kema ai saiki fito ayi gulman dake.
Budan bakin sadiya sai cewa tayi ni ba zan shiga cikin su rainani ba ko ita wanan don diyan tallakawane ita bata san kanta ba.
Dan murmushi hjy iyami ta sake don tuna wanan labarin da safiya ke fadi yanzu sa,ade tace yau ina arzikin nata dana gidan su datake tun kaho dashi din.
Duniya ke nan alokacin tana dauka tafi kowa da komai bata san me gobe zai iya haifa ba a gare ta.
Hjy ce ke fadin bissimilah ku muci abinci ko juyowa sukayi a lokaci guda suna kallo abincin da mai aiki ta hada masu gwanin ban sha,awa kai kace wani dinner aka hada hakan .
Haka kamshin shi abin sone ga mutum balle ya kai ga baki yaji dandanon shi.
Daidai hjy na zama a kasan take fadin ance yanzu koyarwa kikeyi safiya ke kuma sa,ade nursece asibiti ?
Ashe kina da labarin mu ke nan har yanzu tana daukan cokali take fadin haba aiba zan taba mantawa da kuba a rayuwana .
Adaidai lokacin data fara bude kulan tana mika masu plate a gaban su da spoon da fork ga kofuna da lemoka don sha aka tabardar masu.
Nan kowa ya shiga dirkawa cikin sa abinci suna danci suna taba hira yayin da sanyin AC ya fara ratsa jikin su.
Sai da anty safiya ta hadiye naman da take tauna a bakin ta na kaza take fadin a gaskiya mun gode daz bamu lokacin ki da nuna rashin kyama ko babbanci a garemu yadda ake nuna muna har yanzu a gidan mu.
An mayar damu bare a cikin dangi duk kokarin da baba yayi yaga ya hada kan zurian shi kafin ya bar duniyan nan .
Zan iya cewa daga ke sai mijin kine baku nuna muna wani bambanci a tsakanin sabanin sauran dake yawan nuna mu barene a cikin su ko yaushe wani abu idan ya taso na family din mu.
Din kawai mu uwarmu kadai ta haifa a cikin su lokacin da yaya ke raye yana iya kokarin shi damu amma tun bayan rasuwan yaya din abubuwa suka kara lalace muna ga baki daya.
Wani abin saidai mu tsunci labarin faruwan shi a gare bamuci arzikin da za,a fada muna ba mu.
A hsnkali ta lumshe idanuwan ta tana maijin zafin yadda ake yawan nuna masu a cikin yan uwan su din.
Tace ku dauka har yanzu ma yayan ku yana a raye ne safiya don ya barni ya bar zurian shi komai ke damun ku kofa a bude yake dakuzo da bukatan ku nan mudin dai abin baifi karfina ba agidan nan.
Sallama yan matan hjy ne da suka dawo daga school saida su ukune kawai don farida yar wurin hjy ba a kaduna take karatun taba tun dawowan su suka sama bata gurbin karatu Abuja can take zaune tana karatun ta.
Sai hutu take dawowa gidan haka yasa idan ba hutu akeyi ba zaka gansu su uku ne kawai a gidan.
Kansu a sama suka gaidasu kamar basu sheda ko suwaye su din ba garesu don kawai raina masu arziki da sukeyi.
Safiyace take fadin wai ba Rufaida bace da salma nan dan juyowa salma tana fadin nice daga haka tasa kai tana kokarin shigewa daki.
Rufaida salma kuzo nan hjy ta fada a kausashe saiga su sun dawo da sauri suna fadin gamu mommy ta nuna su safiya da hannu tana fadin baku san wa yan nan bane halan ?
Mun sansu mama gwaggo safiyace da gwaggo sa,a salma ta fada a dan yatsune kafin hjy tace duk da kun san su saidai kamar baku san yaya suke da mahaifan ku bako ?
Nan kan shiru sukayi suna kokarin dukar da kawunan su kasa don sun fahinci mai hjy take nufi da fadan hakan.
Karna kara ganin kunyiwa wani babba wanan gaisuwan koda basu din bane wai salma sai yaushe zaku gyara halin kune don Allah ta fada a dan hasale .
We sorry mommy gajiyace dama ya hana mu tsaya dan Allah ku ban guri marasa ta ido kawai ta fada a dan hasale.
Bayan shigewar su dakunan sune anty safiya ta sauke ajiyan zuciya tana fadin kindai gani yanzu ke nan ai.
Wanan ba akidar kwarai bane ka nunawa yaro ga yadda kake da dan uwanka har abin yazo ya shafi naku yayan nan gaba.
Mikewa sa,ade tayi tana fadin antyce ma dai ta damu da wa yan nan mutane, nina dade da zubar da duk wani wanda ya nuna baison wata alaka zumunci dani ai.
Zancen ta baiwa hjy dadi ba ta fahinci akwai bacin rai a cikin halaiyan da yan uwa ke nuna masu kasancewar su su biyun yan uba ga yan uwan haihuwan nasu.
Sallama sukaiwa hjy tare da mata godiya da nuna jin dadin su irin taron data nuna masu din bata nuna masu halin da yan uwa suke nuna masu a cikin su.
Ita kanta bata samu mahaifiyar su a gidan raye ba saidai ga yadda take jin labari zamane akayi bana dadi ba a cikin gidan lokacin da mahaifan su suke a raye wanda itama ta dan ga wani abu a rayuwan datayi dasu gidan kafin Allah ya azurta mata mijin ta harsu bar gidan zuwa lagos karshe ma suka bar kasan ga baki daya.
Lokacin ita kanta sarakuwanta tana yawan nuna mata tayi hankali da yaran don su din ba jinin taz bane diyane kawai na maigidan ta da aka haifa mai auren baya daya kara na karamar yarinya daya auro.
Ga yadda take ji sarakuwar ta itace mata ta farko a guri mijin su saida sukai kusan shekara hamsim a tare ya auro mahaifiyar su safiya din.
A cewar hjy ita ba a hadawa diyan ta yan uba don haka ta hana mijin nata kara wani aure daga baya .
Surukin nasu yana sana,a a kauye har ya shigo birni ya fara sayar da kayan mata irin su dan kune da sarka da jakkuna.
Daga baya kuma daya bun kasa ne ya fara sayar da gwala gwale wanan ne ya kawo mai tarin arziki mai yawa har ya tamfasawa iyalan shi katon gida da suke zaune a ciki.
Bawai bokaye kawai ko asiri taga sarakuwar nata nbi ba saidai iri matan nan ne masu ji da izza da isa da gadara wanda take ganin yanzu diyan nata da jikoki suna koyi da wanan halin.
Saidai daga bayane kariyan arziki ya afkawa mijin nasu bayan siyasan shehu shagari da mazajen arewa da dama suka samu wanan koma bayan a sanadiyar canji da gwaunatin soja mai a lokacin ta kawowa mutane yayi sanidiyar karewa wasu bayin Allah da dama a cikin su har da surukin nata ya samu wanan iftila,in tare dashi.
ANCAU KADUNA STATE
Kamar yadda Asabe ta sha alwashi akan Abban mu dole sai ya kara aure hakan ne ya faru don Asabe taje nema mashi auren yar wata mata da ta dade tana zawarci batai aure ba a kauyen mu.
Tun innan mu bata san wanan zancen ba har yakai ta sani saboda bakin Asabe dake sake suratai barkatai na rashin ilimi da jahilci tare da kiyayya ga inna damu diyan ta.
Da yake Allah yayi inna mu mace ce mai hakkuri da kawar da ido ga komai koda tasan kaine ke cuta mata din.
Sai ma bata nuna tasan Asabe nayi ba a gidan don bata nuna damuwata ga abinda Asabe ke yawan fadi ba ko yaushe.
Mu kan mu bamu tsira ba gurin Asabe don tana nuna muna tsana karara kamar ba jinta muke ba mudin .
Daga zagi sai dungura dan abu kadan yanzu zata sauke muna bala,i a kanu komai mukayi bamuyi daidai ba.
Ainihi Asabece mahaifiyar data haifi mahaifin mu ta hayayyafa da dama basa tsayawa da sun dan tasa an yayesu sai zazabi ya kama su su mutu.
Sai ya kasance ga mahaifin mu ta samu ya fara tsayawa sai mace da muke kira da gwaggon birni don a birni take yanzu da mijin ta daya samu wani ubangida a can ya daukesu bayan aure ya mayar dasu a birnin.
Sai ya kasance mahaifin mu yanzu kawai a gaban ta sai yan jikoki da take dashi ta tsatson shi wanda kiyayyan fitowan mu diya mata a duniya yasa bata kaunar mu har cikin ranta.
Ni dana dan kawo wayau a cikin mu nasan halin da muke gidan na zaman Asabe da innar mu don su sauran yan uwana gorin inna bai taba tayar masu da hankali ba sai ma kawai ja baya da sukayi da al,amarin ta.
Don yawan fada da zagi da take muna a gidan duk da Abba ya dan kewayewa Asabe gefen ta ma,ana ya dan raba tsakanin mu da ita sai dai hakan bai hana Asabe fitowa zaman sa ido ga inna damu.
Wajen karfe dayan rana kasancewar yau asabar muna gida bamu zuwa boko mun dawo islamiya tun sha daya muna gida.
Ina daki ln mu na yara don shigata ke nan na gama wanke tufafin mu da suka dan taru nayi wanka ina shafa mai.
Naji muryan innar mu tana kwala min kira da yar mairo na amsa da Na,am inna daga dakin tare da saka hijjab a jikina na fito da sauri.
Ina fadin gani inna tace yi maza ki dauku abincin nan ki kaiwa umma kada yayi sanyi nace tau inna tare da dukawa na dauki kwanon samiran abincin Asabe.
Munace mata Asabe ne don dukka gari haka ake kiranta dashi in ka debe Abban mu da innar mu koshi Abba sai zuwan inna ne gidan ya canza mata suna dama da Asaben yake kiranta.
Na isa kofan Asabe ina ta sallama bata karba min ba haka yass na kunna kai dakin na aje mata abincin a gefen kofan ta kadan ko waige banyi ba na fito daga dakin.
Dawowa nayi na karasa shirina kafin mu zauna cin abinci tare da yan uwana don a tare mu hudu ake hada muna abinci don yana kawo dankon zumuci inji manya sukace.
Muna gab da gamawa sai ga Asabe tun kan ta karaso wurin mu take kwalawa inna kira cikin tashin hankali.
Gaba dayan mu hankalin mu ya koma gare ta muna duban hanyar kofanta tana zuwa take tambaya wa yakai min abinci a dakina ?
Cikin sanyi murya irin na innar mu da kusan kowan mu ya gado hakan take tambayan Asabe wani abin ne inna ?
A hasale asabe ke fadin tambaya nakeyi wa kika aika yakai min abincin don yanzu na aje dankali na fito bangani ba .
Haka yasa nasan duk wanda yakai min abinci shine ya daukan min shi dama an dade ana min sata a daki ina hakkuri banda dama in aje yan kwabbaina sai in nema in rasa.
Da sauri na furta Allah ya tsareni da daukan abin wani nina kai abinci kuma ko kallon dakin ki banyi ba na fito.
Ke rufa min baki kwadayayya satan naku har yakai haka ban sani ba dole in kira mai gyara ya saka min kuba a kofana don watarana kada kuyi min wanda yafi wanan.
Wani irin bakin cikine ya rufe ni a lokaci daya ina jin idona kamar zai rufemin a wurin don satan dankalin da Asabe ta laka min.
Da ba don nasan itace ta haifi mahaifin mu da naja mata Allah ya isa a gurin duk da hakkurin inna saida tayi magana wanan karon.
Haba umma a gabana yarinyar nan ta shiga takai maki abinci ta fito kuma ban ganta da komai ba a hannun ta.
Ai dada goyon bayan ta zakiyi ta fara mugun abu tun a gida idan yayi karfi sai ta zauna maki a gida ai don babu mai kwasan barauniya yakai gidan shi.
Abbane yayi sallama ya shigo ganin mu cirko cirko a tsaye bai hannashi fadin yanzu dankaline har yai yawa haka a gidan aka barwa Akuyan umma tana ci haka?
Gaba dayan mu kallon Asabe mukayi don jin abinda baba ya fada nan kuma ta fara kame kame tana fadin .
Hannu na dora akai na fasa wani uban ihu ina fadin Asabe mai nayi maki kika dafa min sata a gaban kowa.
Ashe akuyan kice ta daukar maki dankalin ki kazo kina fadin nice na satar maki harda kudi nake shiga dakin ki in sata.
Abba ya daka min tsawa tare da fadin ke ke meye haka kike fada da sauri kanwata Fatima dake bi mun take fadin Abba yanzu fa Asabe ta gama fadin wai Abuce ta sace mata dankalin ta a daki daga kawai takai mata abincin ta da innarmu taba takai mata.
A wani irin yanayi na bacin rai da mamaki lokaci guda Abba ya juyo yana fadin sata kuma umma ?
Ina yaran ne jinin kine umma koda itace ta daukar maki ai ba zaki kira hakan da sunan sata ba.
Ta daka mashi tsawa tana fadin yi min shiru wanda baisan abinda yakeyi ba.
Yau aka fara sata min abu a gidan nan bana magana don gudun irin haka in magana ku karyatani a gaban diyan ka da matan ka.
Waya sani ko itace ma ta dauko din ganin za,a ganeta ta jefawa Akuyan nawa.
Allah ya sauwaka Abba yace ya nufi hanyar dakin su bai shiga ba ya duka ya dauki buta zuwa ban daki.
Asabe ma ta juya zuwa sashenta tana fada inda take shiga ba nan take fita ba wai Abba da innar mun suna lalatamu da gurbatacen tarbiyan da suke bamu.
Inna kan daki ta shige tana kuka hankan yasa dole na tsayar da nawa hawayen don komai ya wuce a ran inna.
Tun faruwan wanan abin na ja baya da lamarin Asabe ba ruwa na da tsabganta iya kana da ita gaisuwa ban yarda in shiga ko lungunta.
Muna kallo idan jikokin ta na birni sukazo yadda take ji dasu take nuna kamar su kadaine ta haifi uwarsu sam mu bamu isa mu rabe ta ba.
Shi yasa ake fadin kakanni sun fison jika na wurin diya mace don ni na tabbatar da wanan maganan gun kakantamu.
Sannu sannu har lokacin Auren data nema wa Abban mu ya karaso buki ya tashi sosai Asabe ita tayi uwa tai makarbiya don Abba yace shi baida zarahin kara aure a yanzu.
Ta saka aka tayar damu daga dakin da muke kwana munaji muna gani aka gyarashi tsab wace kullun take kukan bata da kudi sai gata ta fitar da kudi don kawai taga ta kuntatawa innar mu rai .
Sai fadi take Allah dai ya kawo amaryan Abba tazo ta haifa masu magaji a gidan ko suma zasu shiga fagen zurian dake tun kaho da diya maza a gari.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL DON SAMUN SHI ZAKIYI TEXT A WANAN LAMBAN DON LAYIN BAYA KASAN A YANZU KO KI TURO KATI WAYA KO KI TURA BANK DA WANAN LAYIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK NAGODE DA KULAWAN KU GAREMU, , , ,
Ta dade zaune tana son mikewa zuwa daki don ta dauko takardan da take son turawa saidai jikin daya fara manyanta tana jin kiuya da nauyin tashi daga falon ta zuwa daki a lokacin.
Wani wawan tsuki taja a ranta take raya ya kamata dai ta samu wanda zai dinga taimaka mata wanan dawainiyar yayi yawa a yanzu gareta.
Wayan ta dake gefen tane ya dauki kira ta dauko tana kara jan tsuki sai dai ganin bakon lamba dake kiranta ne kuma ga layin special nomba ne ya bata mamaki.
Taso share kiran don bata san mai layin wayan dake kiran nata ba a lokacin wayan yana gap da tsukewane ta samu ta daga.
Muryan namijine yake mata sallama ta amsa da mamaki don har lokacin bata gane mai kiran nata ba dai.
Bayan sun gama gaisawa ne mai magana ke fadin hjy nasan ba zaki sheda mai kiranki ba a yanzu don an dade bamu hadu ba tun muna US rabon damu gaisa.
Sai mamaki hjy keyi a ranta tana fadin waye wanan kuma wanda ban gane ba dan tunane tayi kafin tace isma,il soba ko ?
Dan dariya ya sake tare da fadin abin mamaki gaskiya kinyi kokarin sheda muryana is about 20 years yanzu da bamu hadu ba.
Ai ba zan manta da muryan ka ba a duk inda naji shi ta fada tana daure fuska kamar wanda take wayan yana kusa a lokacin.
Yace hjy sai naji kina kasan har kusan shekara daya da rabi abin ya ban mamaki matuka har ki shigo kasan nan muna jaha daya ban san da hakan ba.
Yanzu ka sani ai wakila don bai zama dole irin ku su sanda dawowan nawa bane nan ta bashi amsa.
Watau halin na nan a yadda nasan shi hjy baki barin ko ta kwana har yanzu ashe ?
Jin tayi shiru ba amsa yace hjy dama naso muyi wani magana dake ne wanda ya shafi rayuwan ki sai dai naga kamar baki maraba da wayana a yanzu.
Kai isma,il kafi kowa sanin halina don haka babu abinda ya shafi rayuwan ka dani a yanzu dama nasan don ka bata min rai ka nemi layina don haka ina maka warning da kada ka sake kirana.
Dan murmushi taji ya sauke dama yasan za a rina idan hjy iyami ce don bata daukan maganin raini ko kadan.
Shidin yasanta ta dalilin yin karatu a tare ne duk da ya girme mata sosai ga haihuwa amma haka suke shan fama da ita don akwaita da kwazo da basira a lokacin da sukai karatun tana goyon danta na uku ne .
Kawar da zancen yayi ta hanyar tambayan ta yaran don sunayen su bai bace mai ba har wanan lokacin.
Wanan tambayan yaran daya jefo mata yasa ta dan sasauta mashi tare da amsa mai da suna lafiya .
Ance in kana son kama uwa rike yaranta yanzu zaka zama masoyi a gurin ta hakan ko ya faru da hjy har ta manta da fadan ta dashi take fada mai rayuwan yaran ta a yanzu.
Karshe dai yace sai sun zo don bashi kadai ne zaizo ba akwai magana mai muhinmanci da zasu so suzo yi da ita.
Nan ma saida hjy tayi korafi akai kafin ta kashe wayan tana kara jadda mai cewa idan yasan shirmene zai kawo shi kadama su zo din .
Shi dai dariya yayi yana fadin sai idan sunzo din zataji sukai sallama ya kashe wayan.
Kai hjy ta girgiza tana fadin mutane akwai tsegumi har suna daukan zancen abinda bai shafesu ba suna dangantawa da lamarin su.
Mikewa tayi don dauko takardan datake so daki har lokacin tana maijin zafi a ranta na ba gaira ba dalili wata kila kuma har yanzu haushin wayan da abokin karatun ta yayi matane oho ?
Kiuyan fitowa dakin tayi zuwa falon ta har akai kiran sallah ta samu ta mike don zuwa sallah.
Yanzu idan akwai abinda hjy ta tsana shine rashin son motsa jikin ta don hutu yariga da ya gama ratsa ko ina nata ga yaran da take zaune dasu baka more ne gaba dayan su son jikin su yama so yafi na hjyn yanzu don gatan da ake nuna masu.
Sai dai duk da hakan tana dan kokartawa tana sakasu wani abin can ba,a rasa ba sai dai zata sha mita da jini duk tana hakkuri da wanan.
Wani lokaci kuma zata zage tayi masu fada sosai akan rashin son motsa jikin da basa yi dan abu kadan zasuce sun gaji.
KAUYEN ANCAU
An kawo amaryan Abba wata bakace gajera bata da tsayi saidai akwai mazauna irin na mata gareta.
Ni dai banga abinda nagani gareta ba sai halin kiyayya kawai da Asabe ta dagwarawa mahaifiyar mu in bashi ba babu ta inda ta kama kafan innan mu.
Zaman su ba yabo ba fallasa don inna bata shiga tsabganta ko yaushe tana kofanta ita kuma amarya tana lungun Asabe.
Idan muna gida mune abokan hiran innar mu sai kuwa ranan da akace itace da girki ranan zan fara labe labe don ban yarda da tsarin Asabe ba .
Na cewa mu dinga kwana dakin ta haka yasa na share dan karamin dakin da ake tara tarkace a gidan mu dakin ba wani girma ke gareshi ba asalima madafane Abba yayiwa innan mu don da dama tana wahalan girki a ruwan sama.
Abba yayi fada har ya gaji don ko naje lungun Asabe da sunan kwana bana shiga dakin ta saidai in tsaya daga waje.
Idan na faki idon Abba ya shige zan dawo wanan dan dakin in kwanta dama mu uku ne masu dan wayau da muke zuwa kwana dakin Asaben.
Zakaji tunda asuba Asabe na fada wai an jawo mata kwanan wahala a daki yara sunzo sun hanata shakat daki suna damun ta da tusan dare ko tace wai an mata fitsari a daki.
Ranan da tace fitsari kanwata dake bi mun tace itama daga ranan a inda nake kwana zata dinga kwana don sherin Asabe ya isheta.
Sai lokacin Abba yasan ban kwana dakin dole yakawo ido yasa mun hakana muka mayar da dan dakin wurin zaman mu koda da rana ne a nan zamu zauna muyi tsabgogin mu.
Wanan baiwa Asabe ba don ganin yadda mukan saka innan mu a cikin nishadi wani lokacin har mu zauna ana hira da dariya .
Sai kuma hakan ya fara basu haushi suka kulla wani sherin a kaina wanda ya girgiza mu ga baki daya yan dakin mu.
Ranan monday da safe muna ta shirin makaranta tunda naga Asabe ta fito daga lungunta zuciyana ke bani akwai wani abu da zai faru a gidan don daga dakin da muke ina jin muryan ta a tsakar gida tare da Lantana Amaryan Abba suna dan zance kasa kasa.
Don ranan inna muce da girki a dan dakin mu muka kwana inna tunda ta fito ta dama kokon safe da zamu karya dashi kafin mu fita ta koma daki don ta shirya kananun da basu iya shirya kansu sai an taimaka masu.
Na fito da sauri kada in makara kofan innar mu na isa ina fadin inna ni zan tafi kada in makara.
Na juyo inda su Asabe suke da zuman in sallame su lokacin Abba daga daki yake fadin kin karyane Abu ?
Na karya na bashi amsa daga waje don ban shiga dakin ba tunda na girma innan mu ta koya muna hakan idan Abba yana ckin dakin namu.
Zoki karbi murtala ki rike ko fanke kya saya a hanya Abba ya fada daga dakin.
Tsiyan banza dama nasan kai ke koya masu kashin kudi don baka gudun Abin kunya kai kan wa yan nan yaya matan naka.
Karatun bokon dole duk yan uwanka wa kaga ya dage kan sai diya mace tayi boko haka ?
Badani za, ayi wanan abin kunyan ba kuke nan ko yaushe ku dorawa ubanku wahala don kawai baisan ciwon kanshi ba.
Gani kunan haihuwan yuyuyu da aka tara mai agida ace har mace bakwai ko daya ba kawar ba a cikin ku.
Daku da uwarku kunki ku barshi ya ji da abinda zai ciyar daku da wanda zai tara yai maku aure nan gaba.
Amma kullun in sata in maita sai ya lalube aljihun shi ya baku dan abinda ya kwana dashi ko kuma in bakuje makarantar ba uwar ku ta lalabe shi a daki.
To hakan ba zai yuyu ba don baku da uwar ku kadai na haifarwa shi ba don haka daga yau na kashe wanan bokon naki.
Aure zan maki shekara goma sha hudu ai kin isa aure har kina batun wuce munzali.
Gwanda ki tafi dakin mijin ki yaji da sauran yan uwan ki da suka rage kafin suma a fitar dasu sai gidan ya koma hondaku .
Bansan lokacin da Abba ya fito daga dakin inna ba don tunda ta fara magana na zuba mata ido ina kallon ta cikin al,ajabi da mamakinta.
Muryan Abba naji yana fadin haba dai umma aure fa yanzu ga Abu haba wani irin aure kuma kamar yadda taken nan.
Hae guda nawa Abu take da za ace za,ai mata aure a yanzu akaita gidan miji ?
Wani tsawa ta dakawa Abba tana fadin yi min shiru shanyaye kawai wanda baisan ciwon kanshi ba.
Dame su hansai da Adawiya suka fita ga shekaru da akai masu aure kuma suna zaune kalau a dakin mazan su har yanzu.
Abba yace Allah ya huci zuciyar ki umma ni gani nayi har guda nawa Abun take ne da za a ce aure yanzu.
To ai gaskiya umma ta fada inji lantana amaryan Abba ta fada aure ga ya mace shine wajibi.
Ba wani karatun boko ba can da yanzu shike kara lalata yara yanzu haka idan ance ma yarinyar mnan tasan komai game da aure kada kayi musu.
Ke lantana ahir dinki ga bata min diya da wanan kalamin naki sai Asabe tace kaji sauna yo ai gaskiya ta fada ko karya nakeyi Asabe ta tsatsareni da idanuwan ta na tsufa.
Bansan lokacin da kuka yazo min ba na juya zuwa cikin dakin da na fito don jin sherin da ake kokarin lakaka min da farar safiya haka a gidan mu.
Sauran magana ban jisu ba saboda kukan da nakeyi makarantar da ban tafi ba ke nan ranan don maganan Asabe tankar umurni ne ga Abba gama kowa a gidan.
A karshe dai na fito yin alwala nake jin lantana na fadin toke umma tunda kowa yasan kyauta na dan maciciji ne babu masunsuni gareta.
Ai baki kyale haka a zuba mata ido ba dadai kin nemi wani a cikin kauyen nan ki hadata dashi zaifi sai aji da sauran .
Don muddin tana gaban ku haka ba wanda zai kula sauran duk sai ai masu daukan daya kinsan halin garin nan sarai.
Duk wanan zance da sukeyi inna tana jin su bata ko nuna tasan ana zancen ba ta kawo ido ta sakawa kowa don nuna ka waici ga wasu mata na karkara.
Har kwana hudu sati na batun shigewa ban shiga school ba na gaji da zama daki mu don ko tsakar gidan mu na daina fita idan ba wani abu zanyi wajen ba.
Daki innar mu na shiga na saneta tana nade kayan data wanke na yara gaida ita nayi ta juyo tana amsawa fara nade kayan nayi sai inna tabar min nadin ta juya tana fadi.
Saliha tazo tambayan kitso nace ta tafi ta dawo don nasan halin ki sarai dan ajiyan zuciya na sauke ina fadin.
Ni inna banwa kowa kitso a barni inji da abinda yake damuna sai naga inna tayi murmushi tana kaiwa zaune gefen gadon famekan ta.
Tace ai dama haka ake son a ganki cikin kuntatawa da damuwa sai bukatan lantana da umma ya biya idan sunga kina wanan takura dama abinda ake so ke nan damu.
Shiru nayi ina nazarin maganan inna da bata kara dora wani lafazi ba bayan wanan data fada hawaye ne yadan biyo fuskana na share da sauri.
Don nasan ran innan mu ba zaiyi dadi ba itama don ban taba jin ta furta komai cikin zancen hanani zuwa makarantar ba sai yau da tayi mi hannun ka mai sanda.
Dan hira muke jefi jefi mukaji muryan saliha ta dawo tana tambayan kitson ina jin tana kwada sallama lantana na fadin wai waye haka ke damun mu da sallama ne.
Fitowa nayi daga dakin inna ina amsawa tare da fadin saliha shigo dama yanzu inna ke gaya min kin zo ai ina barci.
Saliha race wallahi nazo ko zan samu ki kwashe min kai zamu birni wurin bukin dan uwan maigidan mu ne.
Nace bissimilah shigo bari na dauko tabarma na juya zuwa dakin innan mu na dauko mata tabarma muka zauna zaman kitson.
Na koyi kitsone akan yan kanne na don yawan yawon neman kitso da kashin kudin da inna takeyi kan kitson mu.
Wanan yasa har na koyi kitso ina zama in masu har na hannu na iya ba wevean ba kawai don ina dake son kitson hannu wanan kuma a kanta na koya.
Yanzu kuma in muna makaranta nakan koyi kumshi a pepper har na fara zanawa kannena sai dai ba sosai na iya ba.
Wasa wasa tun daga ranan da naiwa saliha kitso mutanen unguwan namu ke shigowa wurina yin kitso ko su turo yaran su in masu.
Sai ya kasance har na fara mantawa da zancen hanani karatun da umma tayi yanzu.
Ga kudi baya katse muna dan abinda zamu kashe a kauye baya buwayan inna yanzu.
Don a wuni akalla muna dan rike dari biyu ko dari uku tundai idan akave weekend ne don ba wani kudi bane mai yawa kudin kitson kauye talati hamsim ne wani a kyauta zan mai ya tashi.
Ga Abba abin kara lalacewa yayi mai tun shigowan Lantana gidan shi abinda zamuci ma yana batun gagaran mu a gidan.
Don haka muke dan dora karamin tukunya mu dafa dan cimar da zamuci iyamu damu don Asabe ta fara a gaban mu zata dan dafa abu.
Saidai muji tana kwalawa Lantana kira tazo ta karba idan lantana ta karbo a gaban mu zasu zauna suci har tana santi don muji haushi.
Wani lokacin yan kannen mu sai su sa ido suna son ci sai inna ta doke su ko Asabe ta dinga fada ita ba zata iya ciyar da taron yan mata ba uwar mu data haifo mu ta nema ta bamu muci.
Da ku mazane ai da bamu kai haka ba a gidan nan da yanzu kuna wurin nema kuna taimakawa mahaifin ku.
IIrin wanan maganganun na kakar mu yasa muka dan fara dafa tukunyar gefe don kada kannen mu su koyi daukan ido ta wanan dalili.
Ranan inawa wata makwaciyar mu kitso kanwa saratu tana dafa fate don shi zamu gyara muci don Abba bai kawo komai a gidan ba tun safe.
Girkim ya dauko kamshi duk ya dume gidan da kamshi saratu na bakin murhu tana faman fita wuta don iccen baya ci sosai.
Sai ga lantana ta fito lungun Asabe gurin kwata inda muke wanke wanke kakarin amai ta fara da karfe da yaji.
Sai duk mukayi tsaye cirko cirko muna kallon ta da mamaki don bamu dade da jin dariyan su ba da asabe kamar ba sarakuwar ta bace lantana.
Sai ga Asabe da sauri ta fito tana salati tare da fadin yau may zangani haka Lantana lafiya meya same ki ?
Asabe ke tambayan ta a rude sai ga inna ta ma tafito daga dakin ta tana fadin Lantana meya faru.
Ganin Lantana na nuna gurin da saratu ke girki da hannun ta alama dai warin girkin namu wai ya jawo mata aman a yanzu.
Ja inna tayi baya don ta fahinci makircin da Lantana ke shiryawa a kan girkin da mukeyi din don muci tun safe bamu karya ba.
Wani guda mukaji Asabe ta sake wanda bamu fahinci ko na menene ba sai da tace .
Ahhaye nanaye Allah nagodema yau magaji ya bayana a gidana da yardan Allah.
Ta juya wurin saratu tana fadin ke kashe wutan nan ki bar girkin nan kada kija min hasara a gida don ku ba damuwan ku bane tunda bata son kamshin dahuwan naku.
Saratu ta mike tsaye ta fara buga kafa tana yaya zan kashe wuta kina ganin tun safe bamu karya ba.
Kada ki kawo min diban albarka nace a kashe wutan ku mutu idan bakuci ba mana waya damu daku wanan matsalan uwarku ce.
Wallahi bazan kashe ba tunda bai dahu ba saratu ta bata amsa saiga inna ta laiko daga daki tana fadin saratu jaye itace don Allah banson gardama da manya.
Tamayi gardaman dani Asabe ta fada tana nufar wurin randan ruwan mu ta debo ruwa a roba tana zuwa ta lemawa itacen da garwashin wuta lokaci guda wutan ya mutu.
Aiko saratu ta sake wani uban ihu tana fadin wallahi ban yarda Asabe tunda ba bamu abinda zamuci zakiyi ba tana magana ta nufi wurin murhun tana hawaye.
Muryan innace ke fadin karkiyi barshi hakana kuci ko bai dahu ba idan zai ciyu.
Wallahi inna bandade da zubawa ba tazo ta kashe wutan matar makwabtan mu da nakewa kitsone tace dauki dahuwan ki shiga gidan mu ki karasa girkin naki don Allah ku bar wanan magana.
Saratu tana sharan hawaye take fadin wallahi Asabe saina rama don ba yarda zanyi ba kun dafa naku kunci zaki hanamu dafawa yanzu.
Ranan dai sai gidan makwabciyan mu saratu ta karasa dafa abincin da zamuci ga Abba bai dawo ba har dare don haka da bafon faten ba haka zamu kwana da yunwa a ciki mu.
Saida safe ne nake jin muryan Abba cikin jin dadi yana fadin masha Allah abu yayi kyau Allah ya raba lafiya.
Ma,ana dai watau lantana ta samu ciki a gidan mu ke nan ni banji komai a raina ba a lokacin .
Don ban gama mallakan hankalin kaina ba da zan gane may hakan ke nufi damu sai can naji muryan Abba nawa saratu fada don me tayiwa Asabe rashin kunya kamar Abba zai doki saratu din.
Ban san ina Asabe ta tafi ba wai ashe ta fitane zuwa gidan wata mata mai bada magani ta ansowa lantana maganin baki kada innan mu ta zubar mata da cikin jikin ta.
A daidai wanan lokacin saratu ta shige lungun Asabe ta fasa mata babban randan ruwanta ba wanda yasan da shigan ta har ta fito daga sashen.
ZAINAB IDRI MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL GA MAI BUKATA TARE DA IMANI DA SANIN AKWAI HISABI GOBE KIYAMA.
DON ALLAH YAN UWA MUJI TSORON ALLAH GA DAUKA HAKKI A KAN MU TA WANAN HANYAN SAYAR DA LITTAFI A ONLINE MUKE SAMUN CIGABA DA RUBUTUN DA MUKE MAKU KADA KIJI HASARAN BAMU HAKKIN MU KODA KADAN NE .
Sai salatin Asabe mukaji a tsakar gida tana ta faman rabka salati da fada tare da zagi ga duk wanda yai mata wanan aikin.
Babu wanda ya tanka a cikin mu har innan mu saiga Lantana ta fito tana fadin meya farune umma ?
Meye ma bai faru ba randar ruwana tun tele tele na samu a fashe yau sai nasan wanda yai min wanan ta,asan a gidan nan ta fada tana zare ido.
Lantana tace kema umma da wani zance kike ai wa zaiyi wanan banda yaran gidan nan ko Akuyar ki ta fada mata.
Badai Akuya ba su din daine zasu aikata min haka saboda bakin ciki da mugun hali yau dai ai za,a yita ta kare ko a biyani randan ruwana ko kuma yasan inda zaiyi dasu nagaji wallahi .
Ta karasa tare da juyawa wurin randan ta nufa tana hada guntayen sakainan da suke wurin a warwatse a kasa.
Ranan wuni jininin wanan abin tayi babu wanda ya fito yace shi ya aikata hakan sai lantanane ke taya ta fadan.
Abba na dawowa da wanan zancen aka tare shi kira ya kwalawa innan mu dake daki ta fito.
Cikin yaran nan wayaiwa umma wanan barnan ya tambaya yana kallon fuskan ta.
Malam ina zan sani tunda ba yawo nake dasu ba balle duk cikin su babu wanda ke yawan shiga wajen umma ko tana nan balle bata gidan yau tun safe.
Asabe tayi caraf tana fadin waya sani ko ita dince tayi wanan abin don kawai tsaban bakin ciki dake cinnta.
Aure daine na karawa dana ga kuma abin arziki har an samu saidai bakin ciki ya kashe mutum din sai anyi ma yayan ki dan uba a gidan nan.
Wanan bai taba damuna ba umma kin sani in ma za a karo mai biyune rana guda su shigo su haihu a rana daya bai taba damun rayuwana.
Kana dai jin wuyan matar ka yayi kauri har tana fada min bakar magana haka a gaban ka.
To kisha kurmin ki wanan din ce dai guda na aura mai kuma baki so hakan ba dake da diya matan naki da suke tayaki kishin.
Allah ya baku hakkuri umma randan ruwa ne dai ban san wanda ya kashe maki shiba .
Makirci daine kiyi tayi aiga diya mata nan maki zube a gida har yau babu wanda ya sallama da sunan kiran su.
Shiga dakin inna yayi daidai da soma fadan Abba Asabe na fadin in fito da miji cikin samarina Abba yace kwarai kuwa da gara dai in fara rage su nima zaifi min sauki tunda har sunyi wayau yin hakan yanzu.
Idan ma bata da tsayayyene akwai wanda zan hada ta dashi ai shi a shirye yake ko yanzu idan har na bashi.
Abba yace a, a umma gara dai a bari ta kawo din da kanta zaifi tunda kin ga yadda yar gidan muddi suka kare kan hakan yanzu.
Gashi kullun maigari maganan shi ke nan a bar yara su zaba da kansu da ai masu dole.
Ai ba dole bane tunda shidin wanda zan hadasu din yana son ta ai itama zata so shi tunda bata kaishi gata ba.
Koma dai menene umma don Allah kada a soma hakan banda zarahin zuwa birni sharia tunda kinga can ake kai mutun kai tsaye.
Jin hakan yasa Asabe tabe baki tana juyawa zuwa wurin ta tare da fadin ni banga ranan haihuwan diya mata ba a rayuwana ko kadan.
Inna dake daki kuka take darza a hankali batare da fitar da sauti ba balle wani ya jita.
Alwala nayi na nufi dakin ta sanin Abba ba dakin yake ba na samu inna zaune tayi tagumi a wurin data idar da nata sallah.
Inna kada zancen su Asabe ya tayar maki da hankali har ki shiga damuwa tunda bake kika ba kanki diya mata ba ai.
Meye laifina a cikin wanan zance yar mairo don kawai na haife a mata yasa umma ta dauko tsangwama ta dora min ni meye nawa a ciki.
Su suke raina diya mata ina saboda in kin kula Asabe ba da bukatan ilimin addini ko kadan ne matar da ko alwala bata tsaya ta koya ba .
Idan kuma za a gyara mata tace ina mutum ya fito ta kashe shi ai kinga fadin hakan daga bakinta ba abin mamaki bane jahilcine ke damunta daga ita har yar koran nata.
Bashi yafi damuna ba yar mairo yadda yanzu mahaifin ku yake kokarin juya min baya tun lokacin zancen cikin matanshi da umma tayi.
Ina kallo zai sayo mata abu a gaba zai bata idan nayi magana yace min tana da lalura dole a lalabata ai.
Inna kema idan kina son abin ai sai ki fitar da kudi ki saya idan baifi karfin ki ba kiyi hakkuri ki saka masu ido Allah ba azzalumin kowa bane ai.
Sallah nayi har na idar tana zaune tana faman tunane kafin ince niko inna sai nake ganin kamar saratu ne tayi wa randan ruwan Asabe ta,asa don abinda tai muna ranan .
Don dazun naga sanda ta fita zuwa lungun Asabe bata dade ba ta dawo daki tana dariyan kyata.
Amma idan itace ta aikata hakan sai na bata mata rai yau inna ta fada a hasale.
Da sauri na tare inna ina fadin a, a inna idan kin doke ta zasu gane kiyi mata fada kawai don Allah idan ta shigo.
Kwafa innayi ba tare da kara furta komai ba ta mike tsaye ta tada sallah don isha,i da ake kira lokacin.
A daidai lokacin saratu ta shigo gida tana wakan ta mai kama da habaici a fakaice .
Gamu munzo taron dangi, bama tsoro kugafar bama tsoro har zuwa karshen wanka tanayi tana rawa kafin sallama ta shigo dakin inna kai tsaye.
Ganin muna sallah yasa itama ta juta ta suri buta ta shiga bandaki ta dade a ciki kafin ta fito tayi alwala lokacin har sauran sun shigo dakin ko suna sallah.
Nice na fara idarwa don Inna ta tsaya dogon adduan da takeyi bayan sallah.
Fatima ki tashi kuci abinci kada kiyi barci bakuci abinci ba cewa da yar karaman kanwar mu data kwanta tana shirin barci.
Mikewa nayi don in raba muna abincin da mukayi tunda rana tuwo ina tayi muna da miyar ganye da gyada shine mukaci da rana sai koko da take cika roba ta aje don mai yara bata yarda ta rabu da koko a dakinta a kauye.
Saratu na shigowa take fadin yanzu ma tuwon ne zamu kara ci nace idan kin tanadar muna wani abin ba sai kici ba.
Sallah ta tayar har ta idar daga inda take fadin Abu bani abinci na zanci in kwanta ne yau barci nake ji.
Ba zaki biya karatun ki ba ke nan yau barci zakiyi tace na gaji ne yau sosai na dibar muna abincin sai da muka faraci dakin hayi tsit a lokacin.
Don inna ta horemu da hakan tun muna yara har muka gama kowa yaje ya wanke hannu muka dawo tana gyara wurin kwanciya inna tace.
Saratu may yakaiki wurin inna har kika fasa mata randar ruwanta yau don kawai ki jawo min sabon masifa cikin gidan nan ina fama da kaina.
Juyowa tayi inda nake ta dan kalleni kafin tace wani inna wallah, , , , bata karasa ba don tsawan da inna ta daka mata da rufe min baki tun kan na mareki wurin nan.
Shiru tayi har inna ta kare mata fada bata sake magana ba don fada sosai inna tayi mata tana shiru har inna din ta gama.
Ina jin tayi shiru nace ni inna gaskiya gobe zanyiwa Abba maganan karatuna gashi har zamu fara exam din shiga wani zango ban tafi ba.
Idan kinga zaki iya ai gaki gashi nidai babu ruwa na tunda kikaji umma tace kin daina boko to ki barwan nan zacen a hakan.
Har muka kwanta ba kara magana ba sai faman tunane nake a raina don ba abindake damu kamar rashin karatu da ban fita yanzu na riga da na kwallafa rai ga boko nace ni nurse zan zama idan na girma.
Washe gari baba bai fito dakin lantana da wuri ba har kowa ya gama shiri ya fita don sauran suna zuwa makaranta basu fada kangin Asabe.
Hankalina yana wurin fitowan baba daga daki lantana sai wuran goma ya fito tare da ita tana mai rakiya don kawai kada yace zai biya wurin innar mu su gaisa.
Har yasha dan kwanan fita daga ciki gida na fito da sauri na same shi ina fadi Abba ina kwana.
Ya tsaya tare da juyowa yana fafin yar mairo kun tashi lafiya ina kannen naki sun fita ko ke nan ?
Nace a sanyayaye sun tafi baba sai na fara hawaye daga inda nake tsungune ina dan gogewa da gefen hijabi na.
Me ya sameki kike kuka haka da safe Abba ya tambayeni cikin kullawa kasa bashi amsa nayi sai sharan hawayen da nakeyi a lokacin.
Lantana dake tsaye gefen shi kamar bodyguard din shi ta tabe baki tana fadin ya wuce dai zancen auren ta da umma ke fadi.
Kai haba lantana wani zancen aure kuma yanzu gun yar mairo adaiyi hakkuri ta karasa karatun nan datasa a gaba har kwana nawa yarage ta karasa idan muna raye.
To ai naga kai umma take tausayawa a cikin zancen nan kamar rage maka nauyine umma ke kokarin yi ga hakan.
Ya juyo wurina yana fadin kinga yar mairo kije kiyi hakkuri har in zauna da umma in fahintar da ita ko Allah zai bamu sa,a a kanta.
Lantana dake jin mu ta karyar da kanta gefe tana fadin gamu gani ai indai umma ce a gidan nan.
Na bude baki da kyar ina fadin don Allah Abba ka taimaka min na karasa karatuna ko iya secondary din ne in tsaya.
Taysayinane ya kama Abba lokaci guda sanin yadda gun ina kankanuwa nake son boko har irin dagewan da nakeyi kan karatun a yanzu.
Yayi karfin halin fadin kada ki damu yar mairo insha Allahu zaki karasa karatun ki har ki more a rayuwan ki, duk da lantana na fadin malam kasan fa ka makara kada kwastama su dinga mitan hakan.
Haka yasa Abba ya wuce badon yaso ba don tausayina da yaji a lokaci guda ya rufe mashi zuciya.
Bayan fitan baba lantana ta juyo ta dubeni a lalace tana fadin iska na wahal da mai kayan kara.
Lantana wurin Asabe ta nufa ta fesa mata yadda mukayi da Abba tunda naga ta nufi can zuciyana ya raya min hakan.
KADUNA GARIN GWAUNA
Wanka tayi ta shiya a gurguje cikin shigar manyan mata da boko ya gama ratsa su.
Fuskanta babu wani kwaliyan zama a tare da ita sai dan maikon mai data shafa sai man lebe data murza don yanayin garin.
Gurin takalma ta nufa ta saka wanda yai shige da kayan jikinta da sauri ta fito daga dakin duk da sauri takeyi amma idan ka ganta sai ka dauka takon isa da iza takeyi saboda wayewa.
Makullin mota ta dauka don bata bukatan driver a inda zata tafi yau don gidan safiya take son kaiwa ziyara da sa,a.
Tana bude falo sukayi kicibis da bakin ta dake hawo steps din da zai sada mutum da kofan shiga gidan.
Tsayawa sukayi suna kallon kallo a tsakanin su kafin hjy iyami ta fara fadin kune tafe banda labarin hakan.
Sai lokacin Alh isma,il yayi dan murmushi yana kawar da abin kunyan dayaso yi lokaci guda don ganin hjy dayayi a yau bayan tsawon shekarun daya dauka basu hadu ba.
Shima ya wayence da fadin af na manta da gidan bakar baturiya zamu ziyarta dole saida notice.
Kai ta girgiza tare da kallon wanda suke tare tana fadin sannu da zuwa kaidai shi wanan har kullun baya tsufa halin shi na kurciya yana nan a yadda yake da zolaya.
Ke kuma zolayan ne bakya so ba bissimillah ku mana ku shigo kasa na tsaya mun bar bako a waje.
Bako ko baki don nima bokon ne tunda ban taba zuwa gidan ba ai kinga na zama bako.
Hjy iyami tace kaidai ka sani tana ja dan gefe guda tare da nuna masu hanyar shiga don bata yarda su sakata gaba ba kasancewar su maza.
Falon suke bi da kallon yadda ake tsara komai zakace a kasan turai gidan yake don tun a waje suke bin ginan gidan da kallon sha,awa.
Zama sukayi saman kujerun alfarman dake falon kafin aka fara gaisawa tare da tambayan iyali.
Alh isma,il yana tambayan samarin hajiya daya sani take fadin kai ai yanzu sun zama magidanta in ka debe shi na biyun da har yanzu baiyi aure ba yana chaina yana aiki dasu a yanzu.
Kai masha Allahu Alh yace sai kuma yayi mata gausuwan rashin mijin ta don tun lokacin basu hadu ba dashi yace koda suka zo gaisuwa mata sunyi yawa basu shigo ba.
A lokacin yanayin hjy yadan canza take fadin hakane saidai bamu dade ba muka koma don yara dake karatu a can.
Bayan sun dan sha abin shanda aka cika masu gaba dashi yake fadin hjy dama kamar yadda nace dake magana ce tafe damu sai fuska da fuska zamuyi maganan .
Hjy tace kwarai hakan kace yanzu ku nake saurare ai dayan mutumin ne ya karbe zancen da fadin hjy nasan baki sanni ba ni.
To ni sunana Aliyu zaki kubau dan majalissan dake wakiltan nahiyar uku dake makwabtaka damu.
Munzo nan ne da wani bukata ko shawara na duba a gareki wansn ba wani zance bane sai sunan ki da muke son mu bayar don zaman ki macen data cancanci wani mukami da muke son a samu a tamu nahiyar a cikjn gwaunatin nan.
Ni kuma Alh har yaushe na dawo kasan nan da zan iya shiga wanan harkan na siyasan kasan nan yanzu.
Bayan haka kuma ni yanzu duk wani mukami na gwaunati ko wani aiki ban ra, layin shi saboda hutu nake so a yanzu a cikin iyalina.
Me nake nema a yanzu wanda Allah bai ban ba sai hamdala da shukura ga ubangijina ga yara sun kawo karfi suma Allah yana duba mana duk a yanzu.
Mun san da hakan hjy sanin hakan ma yasa mukaga cancantan ki ga wanan matsayin don kece zaki tsaya muna badon kudi ba sai don tausayawa jama,an mu.
Kada kace haka Alhaji don shi mukami da kake gani ba haka yake ba na rike na kuma san meke cikin sa sarau.
Balle mukamin irin gwaunatin kasan nan sai a hankali don mutane ba gaskiya suke so ba a yanzu niko kasan a bisa tubalin mijina nake komai shine gaskiya.
Don haka tun zancen baiyi nisa ba ina rokon ku da ku janye wanan magana a duba wata da ake ganin ta cancanci hakan a bata don Allah.
May na fadama Alh isma,il ya fada yana kallon abokin nasa cikin dan murmushi nasan wanan matar ba zata canza ba ai a yadda na santa tun farko.
Kaji ke nan ina nan a yadda nake har yanzu hjy iyami ta fada sai dayan mutumin yace hjy zamu baki lokaci kiyi shawara yadda ya dace don bamu son wanan daman ya kubbuce muna a yanzu.
Don dama ne da hujja da muke dashi akan ki na mace mai ilimi da matsayi irin wanda ake nema a wanan nahiyar tamu a yanzu.
Shiya sanni yasan ko wacece ni banda ra,ayin irin wanan mukamin ko a majalissan dunkin duniya danayi aiki dasu acan da ka fadi sunana sun san dani a wurin.
Hjy ki dai kara shawara a duba abin kamar yadda nake fada maki a yanzu don wani abin ansan badon kudi mutum ke rike sa ba sai don al,umman nahiyan ka.
Zatayi shara yanzu dai mun fada maki bukatan mu don Allah muna son kiyi duba ga wanan abin kafin mu sake dawowa muji shawarab da kika yanke akai.
Hakana dai sukai sallama ba tare da sunga alaman yarda daga gurin hjy iyami ba shi dayan mutumin daya kira kanshi da Ali zaki kubau yana cike da mamakin hjy iyami din don bai dauka akwai irin matan nan a jaharsu ba haka.
Unguwar da hjy bata fita ba ke nan a ranan don bayan tafiyan bakin ta sai taji kasalan fita ya kamata lokaci guda don tunanen maganan bakin nata da sukazo mata dashi.
Tsuki taja tana gyara kafan ta saman kujera data dagwara don taji dadin zama da kyau tana fadin ina zaman zamana kuja min sabon zagi da tonon asiri da tsufana.
Nikan dariya nayiwa hjy ina fadin hjy ina tsufan yake a nan saidai inda babu tsofin ko za a kiraki da tsohuwa ko dadtijuwa din.
Don babu mai ganin ta a yanzu yace itace mahaifiyar wa yan nan yaran nata a yanzu.
Sai data dan dade zaune ta tuna da zancen unguwar da zata tafi do yau taso ta ba su safiya mamaki ta ziyarci gidajen su su sanda suma yan uwane kamar kowa.
Don kawai sun fito ba ciki daya da yan uwan su ba bai kamata ana ware su haka ba a cikin dangi don tasha alwashin ida nufin marigayin mijin ta duk akan yan uwanta idan tana raye a duniyan nan .
Saidai muce Allah ubangiji ya ida nufi na alheri hjy da haka mata suke duka wurin raya zumucin da zumunci a yanzu bai tabarbare ba a duniyan nan.
Shigowan yaran ta dake gida suna hutu ne ya dawo da hankalinta garesu gurinta suka nufo kamar yara kanana muhsin ya zauna a gefen ta tare da rankwafo kanshi saman wuyan ta yana fadin wallahi mami na gaji sosai.
Kafin dayan ya zauna a makari kujera dayan gefeb yana fadin hajjaju zaman garin nan fa ya fara isata wallahi.
Gashi ko a nan zaku zauna don ba zan yarda wani cikin ku ya kara niss dani ba kamar yadda kewan dan uwanku ke wahal dani a yanzu.
Wai mami idan an tashi magana sai ki kawo zancen yaya jackson shifa ina jima yanzu ya manta da Nageria a ranshi.
Dan duka takai mai ga kai tana fadin daga min ya daga da sauri yana fafin wassh Allah na yana shafan wurinda ta dukeshi din.
Tana fadin har daku cikin batawa dan uwanku sunan shi na musulunci da kiranshi wai wani jackson cen ba dadin ji.
Allah hajjaju idan ba kince haka ba a turai babu mai gane shi ake afadi don jackson din ko jack ya rufe sunan nasa a yanzu.
Bai rufe ba ta fada a hayayyake shima idan yazo zan mashi magana kan hakan idan baso yake yaje lahira ana tayar dashi da wanan sunan kafiran ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAN UWA MASOYA ANNABI ALLAH YA KARAWA ANNABI DARAJA YABA MU IMANIN A MAI ANFANI A ZUKATAN MU AMIN, , , , ,
DON SAMUN LITTAFI BA TARE DA DAUKAN HAKKI DA NAUYI A KANKI BA SAI KI TURA DARI UKU A BANK DINA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA TA WANAN LAYIN 08036959257 KO 09036
Tun bayan fitan Abban mu ban koma daki ba wankin dana tara na farayi muna kafin yan kitso su fara shigo min su hanani aikin komai.
Ina shanya kayan ne nake jiyo zagin da Asabe ke durawa wanda ba sosai nake jiyo su ba daga inda nake har na samu na gama ruwa na diba naje nayi wanka.
Ban kai ga karasawa aikai sallama ko ban leka ba nasan masi kitsonane suka fara shigowa lokacin .
Makwabciyar mu hassana ce da yaranta yan mata biyu da zan wa kitso suka shigo fitowa nayi na dauko tabarman da innan mu ta bani don yan kitso din na shifinda tare da gaida ita.
Dakin inna na shiga tana zaune tana gyaran sarkan kanwarmu daya katse nake fadin inna ko zan dora abinci ne kafin in zauna.
Jekiyi tsabgan gaban ki gunda ga mata sun fara shigowa barni in gama in dafa muna fate da guntun tsakin daya saura muna shekaran jiya.
Ko zai kaimu har dare tunda ba abinda zamu dafa da daren inna Allah zai bamu da yardan ubangiji tunda ga yan kitso nan sun fara shigo min yanzu sai a sayo ko taliyan hausa a dafa da daren.
To kije ku zauna kada matar mutane ta dade a zaune inna ta fada na juya na fita raina babu dadi a lokacin don a yanzu kan ina iya fahintar halin da mahaifiyar namu ke ciki na mijinta da sauran mutanen gidan mu din.
Daga kofan innan mu kadan nake zama muyi kitso don Asabe tace bata yarda ana sake masu gashin mata barkatai a gida ba kada azo a barbada masu tsiya a gida.
Ina kitson ina tunanen halin da innar namu take ciki na bakin cikin rayuwa duk saboda kasancewan mu mata a gareta don kila badon mun fito a yaya mata ba da bata fuskanci duk wanan nakin cikin haka ba.
Muryan lantanane ya dawo dani ga dogon tunanen dana lula ina rike da kan yar karamar yarinyar dana farawa kitson lokacin.
Wai har an zauna wanan bakar sana,an da babu karuwa a kullun a cika muna gida da yan gulma da sunan kitso nikan malam ya dawo ya tare min wurina don wanan abin ya isheni hakana.
Kai ke nan duk abinda kakeyi idon mace na kanka a zubama ido a fita dakai waje ana baradawa a cikin gari.
Dagani har matan da nakewa kitso ba wanda ya tanka a cikin mu don idan da sabo sun saba da wanan halin na habaici idan sun zo kitson don kiri kiri ake nuna min hassada ga yin kitson kuma.
Maimakon ta shiga dakin datayi niyar shiga da farko sai kuma ta juya ta koma lungun Asabe ta dade kafin ta fito.
Lokacin har na gamawa yaran duka biyu na farayiwa uwar saura kadan mu karasa kitson namu tana yan wake waken ta na hausa mai kama da habaici.
Naji matar da nakewa kitson tace uhumm wanan matar baban naki da jan magana take naga dai kullun nazo kitso gidan nan sai ta samu abindata fada a kanmu.
Ina jin dadin yadda baki kulata kike aikin gaban ki ba tare dakin damu da ita ba don irin su saboda bakin ciki suke haka don tayi sanadin da zata saka a hanaki kitson ga baki daya tunda sun san kina samu a nan.
Ba komai ai wata ran sai labari na fada mun gama ta dauko dari biyar sabuwa ta mika min na girgiza kai tare da fadin a, a wallahi ki ban dari ko dari da hamsin .
Haba Abu kullun na turo yara a kyauta kike min kitson nan ki karba baban sune ya bamu mu kawo maki da nake fada mai alherin da kikewa yaran shi kullun.
Dole na karbi kudin badon naso ba damun wanan kudin ya zama kamar buduwar hanyar alherina ranan don duk wa yanda sukazo kitso mun samu alheri sosai a wurin su.
Bansan yaya Asabe sukayi da mahaifin mu ba ya dai bani hakkuri kan in hakkura da karatun nan kawai a yanxu.
Ranan nayi kuka sosai kamar ba gobe tun innan mu na ban hakkuri har ta gaji ta kyaleni ta saka min ido.
Saratu ne abinka da dan uwa data dawo innan muke fada mata wuni nayi ina kuka a daki yau don Abba yace ba zancen komawa makaranta a wurina.
Tashi tayi ta sameni a dakin tana ban hakkuri tare da ban shawaran da muke ganin zai fitar dani daga kuncin da Asabe ds lantana ke shirin jefani s ciki.
Fitowa nayi don taya innan aiki gitkin dare haka ma su sararu da sauran yan uwan mu suna debo ruwa daga rijiyan uguwar mu suna cika duk kayan dake gidan na ruwa.
Har sun kusa cika na kofan lantana don sheri kawai lantana tace wai habiba ta saka hannu a ruwan don haka bata so sai dai su zubar su debo mata wani.
Wanan ya kawo rikici a gidan mu sosai ranan don har inna takai ga tanka masu Abba kuma ya dawo ya hau innan mu da fada ta inda yake shiga ba nan yake fita ba.
Wai inna ke goya muna baya muna iya shegen da mukaga dama a gidan ai lantana ma kamar uwa take a gurin su tunda tana auren shi.
Saratu dai taki komawa diban ruwa kuma ta hana yan uwa zuwa su debo suka kada guga a riya karshe dai ruwan da ba,a deboba ke nan har Abba ya dawo hake wanan fadan .
Kwala min kira yayi wai na kwashe ruwan randan innan mu guda in zubawa lantana a nata randan in yaso mu mu zauna ba ruwan tunda saratu ta zama abinda ta zama a yanzu duk gaba daya zai hadamu yai muna aure lokaci guda tunda ba finta nayi da wani girma ba.
Inna kan bata da aiki sai kuka don hakane kowa ke kokarin takata yadda yaso a gidan don rashin maganan da bata yi idan suna mata abinda sukaga dama, mu a namu ganin ke nan.
Hjy iyami abin duniya y isheta ga matsin da gwaunati da yan siyasa ke mata dole ta zauna da yaranta da yan uwanta kan maganan.
Inda suka bata shawaran karban mukamin don taimakawa rayuwan tallakawa da sauran al,umman nahiyar su din.
Haka yasa ta shedawa Alh Aliyu zaki kubau amincewan ta wanda ba karamin farin ciki yayi da jin hakan ba daga bakinta ,.
Duk da yana hangen da wuya su iya tafiya a yadda suke so da ita don ra,ayin daya hango a tare da matar duk da ba laifi ko yaya ne ai wayau maza yafi na mata ya fada.
Tawaga guda sukayo zuwa gidan sun dade suna tataunawa da ita kafin suyi mata godiya su tafi.
Hakan yasa taji duk ta gaji ga ranan don yan aikin ta kawai bazasu iya mata abinda take so ba daidai a hakane safiya suka zo gidan suka same ta cikin gajiya.
Bayan sun gaisane tare da mata murnan abin arzikin dake shirin faruwa da ita take fadin anya safiya zan iya wanan abin yanzu.
Yau kawai duk nabi na gaji dan dawainiyar dana wuni inayi da jama,a agidan nan .
Shiyasa nake son a samo min yarinya yar maidaidaciya da take da rikon Amana in zauna da ita don wa yan nan kinga su ba zama sukeyi ba ko ba school sai sun kirkuro fita sam basu zama a tare dani.
Na rasa inda zan samu irin yarinyar da nake bukata na kusa wace zata dinga min hidima ko yaushe.
Dan shiru safiya tayi kafin tace za a duba a gani indaya dace sai a samo maki yarinyar kamar yadda kika bukata.
Zanje kauye in duba maki mai dama mu gani idan zata iya idan kuma ta gaza sai a mayar da ita a sake duba wata.
Dakin mun hakan dana gode kuwa safiya shiyasa nake kara jin dadin ki wallahi na dade ina tunanen ta ina zan fara duba yarinyar data dace yadda nake so nan gari.
Da wanan maganan suka rabu ranan inda safiyan ta koma gida da tunanen inda zata duba yarinyar data dace takawowa hjy a yanzu gashi tayi alkawarin hakan gare.
Kafin gari ya waye ta yanke shawara a ranta zata duba ta gefen mahaifiyarsu ta gani idan hakan zai samu garesu.
Don koma meye zata iyayiwa hjy iyami indai zata iya baifi karfinta ba don ko meye hjy ta cancin hakan garesu .
Don ta nuna a duniya su yan uwan mijintane a yanzu don ko wani wuri zata tafi na alfarma suna daga cikin masu mata rakiya.
Wanan abin yana ba mutane da dama haushi har suka fara fadin asiri sukai mata suka shiga zuciyan hjyn a lokaci guda.
Daga hjy harsu suna jin ire iren wanan magana saidai ba abin mamaki bane hakan da mutane suke fadi don yanzu mutane basu dogara ga Allah sun manta da ba duga aka zama daya ba.
ANCAU
Tunda safe na samu masu kitso don haka na zauna muna kitson ga innan mu tana aikin girkin gida don yau Abba yayo cefane ana dafawa aci duka gida.
Ditin mota mukaji a kofan gidan mu sai dai bamu dauki hakan wani abu ba don ba wanda zaizo gidan mu da mota ai.
Haka yasa muke zaton ko makwabtan mu motar tazo yin wani abu sai can mukaji sallaman mata na shigowa gidan namu lokaci guda.
Amsa masu sallama mukayi dani da matan da nakewa kitso sai inna ta dago dan ganin masu shigowa gidan lokacin.
Tarbon su tayi tana fadin wa nake gani yau kamarsu hjy safiya garin namu ?
Ba kama bane mune dai din kike gani don kasancewar su kamar tobasai tunda tana auren yaya a garsu.
Dakinta ta kaisu don Asabe bata gidan lokacin ba laifi don dakin inna duk da yawan mu koda yaushe tsab yake don tsabtan ina yara basu hanata gyaran daki da tsakar gida har din muka koyi hakan.
Don ko a kauye akwai masu hali irin na yan birni da zaka samu a talauci amma komai nasu yana tsab.
Tabarma ta shimfida masu saman sumintin dakin dake sheki sai dan kamshin turaren wutan dake tashi ba wani mai kamshi ba amma duk da hakan ba laifi dai dakin don ba zakace dakin mai yara bane.
Ruwa ta kawo masu a kofin silver tana fadin ga dai ruwan namu babu sanyi don har yanzu yayan naku baija wuta ba gidan nan.
Ikon Allah duk wutan nan daya kewaye garin nan ba a ja maku wuta ba har yanzu inna dai bata ce komai ba kada zancen yayi nisa a hakan.
Safiya ta dauka ta dan kurba kadan ta mikawa anty Sa, a kaita girgiza alaman ba zata sha ba ta aje kofin a gefen ta.
Lokacin na sakewa matar kai nazo don in gaidasu da zuwa a dakin innar mu din .
Saida nakai har kasa na fara gaida su da zuwa anty safiya na fadin wai kada dai ince wanan ce nan wa take da sunama don mantawa da sunana da tayi a ranta.
Inna tace ki dai tuna don kinsan niba fada maki zanyi ba dai ta fada tana mikewa don barin dakin.
A hankali nace Abu sunana gwaggo tace naji dayan da ake kira da anty sa, a tace min haba wani irin Abu kuma keda kanki kike batawa kanki suna haka?
Zainab din ne kike kira da Abu wai kamar sunan wani abu can daban wanan ai suna tsofine nagani.
Nidai na fita ina dan murmushi don jin may suke fada a gatin nan kan wa zai tsaya kirana da wani zainab can.
Nakai kofa naji tana tambayana ina yan uwan ki suke nake fadin suna makaranta na fita daga dakin kai tsaye na koma inda nake kitso .
Yaro inna ta nema ta tura a kira mata Asabe datace zata shiga makwabta tana jin lokacin da take fadawa Lantana hakan.
Ba, a jima ba sai ga Asabe da dan saurin ta ta shigo tana fadin bakin daga birni su waye umma yayan kine su safiya inna tace.
Sai lokacin na tuna dasu da suna yawan zuwa gidan muna kanana amma daga baya suka daina zuwa ban san dalilin hakan ba garesu.
Suna ina Asabe ta tambaya inna ta nuna mata dakinta sai ta dan tabe baki ta nufi dakin inna din .
Muryan lantana ne ya dakatar da ita shiga dakin lokacin lantana na fadin umma kin dawo ashe ?
Na dawo yar nan yanzu yaro ya sameni wai nayi baki daga birni sai lantana tace au baki akayi ashe mu dake gidan ma bakin ciki ya hana a sanar damu.
Dago kai nayi na kalli lantana da take maganan don nasan da innan mu take wanan maganan haka.
Asabe ta shiga basu dade ba suka fito zuwa sashen ta tare da bakin sai lokacin lantana ta tafi gaida su.
Don a nata nufin bazata shiga dakin innan mu ta gaida bakin da zuwa ba don innan mu bata kai mata can ba .
Inna tana gama abinci ta zuba masu a kwano mai kyau ta dauka takai masu ta dawo ta debi ruwa ta sake kai masu a can.
Abba ya shigo gidan yana fadin yanzu ake fadamin anga munyi baki a gidan yasa na garzayo in ga su waye suka zo.
Can ya samesu a aurin Asabe suka zauna sun dan dade a tare kafin su fito suce zasu tafi sai da suka sake shiga dakin innan mu sukai mata alheri kafin su fito su tafi din.
Bayan kwana biyu naji lantana na fadin duk kyau da bokon wasu ga aikatau zasu kare rayuwan su karshe ma su kare ga auren maigadin gida.
Dagani har innan mu kallon juna mukayi lokaci guda don ba wanda ya fahinci may zancen ta ke nufi a lokacin.
Share ta kowa yayi abu kadan yan kwanajkin nan zata ce kyau wasu ya kare ga banza tunda zasu tafiyin bauta a gidan wasu.
Banga wanda ya isa ya tura min dana yawon bauta ba a gidan kamar banda kowa a duniya har dai ranan da dare muna zaune muna hira a dakin inna gaba dayan mu inna ke fadin.
Nikan wanan zancen bautan da amaryan baban ke fadi na rasa gane inda maganan ta ya dosa da fadin haka ko yaushe .
Wanan inna ai ita ko ba dalili kirkiro magana take ta yabawa mutane don kawai ayi fitina tunda bata son a zauna lafiya ita na fada.
To dan wataga za,a tura yin bauta da take fadin haka inna karma magananta ya dameki don Allah saratu ta fada tana jan tsuki.
Shiru mukayi kowa na nazari a cikin ranshi kan zancen don innan mu tafimu fahintan da akwai wani abinda zai faru da diyan ta don haka kawai bai saka lantana tayi ta gorin haka a tsakar gida.
Aiko ranan da safe baba yai kiran mu nida innan mu yana lungun Asabe muka tafi don amsa kiran Abba din.
A zaune muka same su a dakin kowa yai shiru saidai yanayin su ya nuna kowa na cikin bacin rai a lokacin.
Wuri muka samu muka zauna nikan ina daga kofan dakin don ban shiga ba a lokacin inna tace gamu malam.
Zuwan lantana yasa yayi shiru ya kasa maganan da zaiyi sai Asabe take fadin kayi magana ka tsaya kana wani kimbiya kumbiya kamar kana tsoron matar taka da yarka.
Ke yahanasu bawani abu bane yake son fada maku ke da yarki sai zancen tafiyan yar ki birni da nace a turrata aikatau.
Koba komai zai dan samu abinda zai rage saya mata kayan daki a nan tunda kunki bari ya aje komai gashi sun cika muna gida zagada zagada dasu.
Aikatau kuma umma ina ta fada da mamaki karara a fuskan ta sai naji asabe tacd eh aikatau ko yar taki tafi karfin yin sikatau din ne.
Ina ko tafi umma wanda yake nema ya samu duk wata za,a lalo mashi yaji dumus ai yafi zaman wanan kitson da takeyi kullun tana tara muna munafukai a gida lantana ta fada daga inda take.
Koba zaki bari ta tafi bane Asabe ta fada a hasale tana duban inda inna take zaune.
Abba yayi karfin halin fadin a barta suyi shawara da yarta umma don kinga daga sama sukaji wanan maganan yanzu.
Shawaran me zasuyi wanda yafi wanda na fada yanzu a gaban ta kuma ko kuma sai abinda tace zamubi tunda itace ta ajemu bamu ba.
Ai shike nan tunda kace haka dama ni kai nakejiwa nake tausaya maka tunda hakan ne kawai zatayi ma a matsayinta na ya mace ta taimakawa rayuwan ku na dan lokaci.
Umma ai Allah daya bamu su yasan yadda zai iya mana dasu basai mun kaisu inda bamu san kowa ba don neman abin duniya.
To mara kunya akan yar fadin ki kike kokarin musayan magana dani to kiji ki karaji zuwa birni babu fashi ga Abu.
Idan ta samo kudin bakuso ku bani wani ya hana ki haifota a namiji halan birni daine kamar taje tagama yanzu haka na fada babu fashi ga zancena kuma.
Inyaso idan ta tafi ta shiga duniya karewan rashin sanin kowa inds zata ke nan aikatau daine sai ta tafi.
Wani kuka ne na fashe dashi lokaci guda don jin hukuncin da asabe ta yanke min yau a gidan mu.
Ta hanani karatu don wani manufanta yanzu kuma zata turani birni yin aikatau do kawai a musgunawa innan mu.
Daki inna ta sameni ina rusa kuka itama kukan ta shigo dashi a dakin muka taru muka rasa wanda zai ba wani hakkuri a cikin mu lokaci guda.
Sai nice nayi karfin halin fadin inna kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zan tafi yin aikatau ba a birni.
Yar mairo me nayiwa umma take min haka a raguwana ko yaushe take kokarin sai taga bakin cikina a rayuwan ta.
Ita ya mace ba diya bace da za ai alfahari da ita cikkn zuria da wasu basu gane hakan.
Ban taba bakin ciki da nadaman samun ku a diya matan da kukazo min ba don ban san kyautan da Allah yai min ba don haka bazan butulcewa Allah na ba.
Amma umma kulun magana ya tashi a gidan maganan ta daya ne shine na cika masu gida da diya mata bafa san yadda zatayi da diya matan da nake haifo masu ba.
Innan mu kiyi shiru ki barsu nasan munafuncine aka kula a turani yin bauta a gidan wasu.
Koda Allah ya nufa zan tafi inna nayi maki alkawarin kula da kaina a duk inda na samu kaina din.
Balld ba zaki tafi ba yar mairo muddin nina haifeki ba zaki tafi wanan bautan da umma ke nufin kije ba don kawai ta musgunawa rayuwan mu a gidan nan.
Innan mu don Allah kada kice zakiyi wani abinda auren ki zai tamu gun Abba tunda shima ya nuna baison hakan a gaban mu amma asabe tace sai na tafi.
Kiyi hakkuri ki bini da addua a duk inda zasu kaini ya zama kariya a gareni ko yaushe.
Sai naji ta kara rushewa da wani kukan nima kukan na fara lokaci guds mun dauki lokaci a haka a dakin.
Ranan da wanan bakin cikin gaba dayan mu muka kwana tare da tunanen ina za,a turani shine abinda ke damuna a raina .
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
6️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA LITTAFINA NA KUDINE DON DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA KI DAUKI HAKKIN HAKAN A KANKI SAI WACE TA BIYA TAKE DA ALHAKIN KARANTAWA A SAUWAKE NA FITAR DA HAKKIN KI NA FADA MAKI GASKIYA.
Don Allah ki guji daukan alhaki akanki don gujewa fita ko yaushe abinda ka raina shike zama babba gareka wata rana.
Ban gaskanta zancen tafiyana ba sai ranan da anty safiya ta dawo garin wanan karon ita kadai tazo ba tare da yar uwarta ba.
Ina wa wata mata kitso kamar yadda na saba yiwa mata kitso a kullun aka tare ta cikin mutunci ta samu Asabe na gida a lokacin.
Bata wani jima ba a dakin naji asabe ta kwalawa innan mu kira daga lungunta inna ta amsa taje sai Asaben ke fadi Abun ta shirya don anzo tafiya da itane yanzu kamar yadda na fada maku za a kaita birni aikatau.
Cikin karfin hali inna tace basan da wanan zance ba tunda tun ranan na fada karatunta nake so ta karasa ai.
Yahanasu ni kike fadawa hakan ko kinyatani kike son yi a bainar jama, a yanzu ki nuna min kina da iko kan yarki ko ?
Tama nuna in bashi ba umma zaki bada umurni har ta tsaya tana gardama a kanshi don kawai ta nuna ta isa lantana ta fada.
Eh ai naga alaman hakan kedai yar nan don kawai tana ganin an zuba mata ido dasu a gidan ko ?
A,a umma anty safiya ta fada kin san fa irin wanan abin natsuwa yake so tun farko idan har baku sharwace ta bane ta hanyar daya dace gskiya ba,a kyauta wa matar yaya ba Anty safiya ke fadin hakan.
Wani irin a fada mata ko yau kika zo daukan yarinyar nan nace na yarda ga abindana tsara ai in ita mai tunane ba zata tsaya jayaya dani ko ?
Umma ni ba jayyaya nake dake ba gaskiya ta na fada don yatinyar ban diya mace ce kowa ko bs zaiso hakan ga nasa ba a dauki yarinya akai inda ban sani ba kamar bata ds gata.
Eh lalai magana kike son daukowa kanki yahanasu umma tace tana kumfar baki ga innar mu wanda hakan yasa nayi shiru ina sauraren shiru na sauraren su daga inda nake zaune zaman kitso.
Hawaye ne ya fara zubo min sannu a hankali don na fahinci akan me suke magana naga Abba ya shigo gidan da kyat na iya budan baki na fara gaidashi.
Bai tsaya amsa min yadda ya saba ba ya nufi shiyan Asaben inda yake jin muryan Asabe yana tashi a can.
Wai yaya ne meke faruwa kuma ya fada lokacin da yake shiga wurin Asabe din yana mai binsu da kallo gaba dayan su wurin.
Wanan matar takace ke son ta raina min wayau yanzu wai bata sanda wanan zancen ba ita ba mai tafiya da yarta do ita keda abinta.
Anty safiya tace a, a umma bata fadi hakana ba ta dai nuna bata san da zancen ba sai kuma ra,ayinta na son yarta taci gaba da karatun ta tace.
Abba ya juya wurin inna yana fadin idan mugun wuri za a kai yarunyar nan ai ba za,a hada baki da safiya ko muba a kaita.
Tunda umma tace a kaita din ke meye naki a ciki yanzu banda yiwa yarinya fatan alheri kawai.
Amma dai malam kasan ba ai muna adalci ba idan akai muna haka ke nan bamu da inci daga har yaran sai yadda akayi damu ke nan.
Gunma dai kaji da kunnuwan ka yanzu abinda take nufi ke nan tun dazun ita yar nan bata fahinci hakan ba da cewa anty safiya.
Kinga ki kwantar da hankalin ki kada ki tayarwa yarinyar nan da nata hankalin taje can ta kasa tsayar da hankalin ta wuri daya.
Inna batacewa anty safiya komai ba illa mikewa da tayi ta bar dakin muna jin Asabe na fadin in ba wanan ba wani taimakone ya mace zatayi a gidan nan dayafi wanan na dan lokaci.
Dagani har matan da nakewa kitso a gurguje don inyi in gama mata ta tafi kada taji me gidan mu ke ciki batu yabi gari.
Matar ke fadi wai rikicin me ake hakane nace maganar sune ta manyan gida kawai .
Ina gama mata ta tafi na wanke hannu na na nufi dakin inna kuka na samu inna nayi wiwi zaune a dakin haka yasa nima na samu wuri na fara rera kukan kamar yadda innan mu takeyi.
Muryan Abban mune ya leko falon yake fadin wai ina yar mairon takene ta fito su kama hanya kada a yi yamma a hanya.
Kin tashi nayi sai gashi dakin ya shigo yana fadin bakiji me nace ba tashi ki shirya ku tafi Allah ya tsare hanya.
Wani kuka mai karfi na sake tare da ambatan sunan Abba din ina fadin don Allah Abba kada ku kaini birni bauta.
Har zai fita ya dawo ya tsaya yana fadin kinga kin saka yarinyar nan hankalin ta ya tashi ga tafiyan nan.
Na rasa me kike nufi da hakan gaba daya yanzu kin canza a gidan nan kin dauko rayuwan banza kin sakawa kanki saboda bakin kishi dake cin ki.
Ji Abba fa wai duk haklurin da inna keyi a yanzu Abban mu bai gani har yake fadin haka kai tsaye.
Wani tsawa ya daka min tare da fadin zaki tashi a nan ko sai na makeki wurin nan maza ki tashi ku kama hanya.
Ai gaskiyan umma data kawo sharan turaki birni aiki idan kin zauna nan uban me zaki tsinanawa mutane a nan in bada kullun ku saka uwarku a daki tana koya maku kilibibin baza.
Mikewa nayi ba shiri na shiga daukan kayana a dakin inna ya juya ya fita ganin na fara tsuntar kayana.
A cikin muryan kuka inna ke fadin yar mairo kiyi hakkuri da halin da muka riski kanmu a ciki ki tsare mutuncin ki ibadan ki da kima.
Kije har kullun Allah yana tare da mai gaskiya komai wuya komai dadi ki kula da yin addua kinji sai kuma ta kasa karasa sauran zancen saboda kukan da yazo mata lokaci guda.
Anty safiya ce tashigo dakin inna da kanta tana fadin na fahinci halin da kike ji yahanasu.
Babu dadi ace ba,a fitar maki da hakkin ki ba su sanar dake ku sasanta kanku sai dai nayi maki alkawari insha Allahu wanan tafiyan nata zai zama alheri a gareku baki daya.
Yanzu na kara fahintar rayuwan dake gudana a gidan nan naku na fahinci komai yan mintinan danayi daku a nan .
Murmushin karfin hali inna tayi cikin kukan da takeyi take fadin na yarda dake safiya Allah ya iya muna ya tsare min ita aduk inda take .
Ba komai kitafi da ita din tunda haka suka zabar mata insha Allahu tafiyan nan nata zai zama maku alheri tunda bada zuciya daya suka tura maki itaba.
Ta bude jakka ta ciro kudi masu yawa tana fadin hjyn da zan kaitane ta bada wanan kudin aba iyayyen ta.
Nayi niyar baiwa umma su sai na fahinci akwai kulli cikin harkan nan don haka ki karba kiyi maza ki boye albashin tama idan an bayar nasan yadda zan dinga maku dashi insha Allahu.
Don sam ban dauka ita za a bamu ba nadai zowa umma da zancen muna son yarinya a garin nan idan da akwai yadda za a samu.
Sai yau danazone naga ashe itace zamu tafi da ita ki dauka kamar tana gaban kine insha Allahu.
Jin hakan da anty safiya ke fadi ya kara kwantarwa umma da hankali sosai muryan Asabe ne ke fadin .
Wai ina safiyan take ne in kin soma ki bar bata bakin ki wurin lalashin ta ko ta yarda ko kada ta yarda tafiyan nan ba fashi .
Muna ji muna gani haka muka kama hanya da yan kayana cikin ledan bacco don banda jakkana tafiya da zan saka kayan a ciki.
Inama na taba zuwa hana rantsu daga makaranta mukazo zaria kuma ba a bari an kwana ranan muka koma gida wurin iyayyen mu.
Har kofan gida wurin mota asabe ta biyo mu da lantana tana fadin atafi can a dandadi duniya aji yadda take.
Kina nan zaune gida ba wanda ya taya balle a sallama muna da sunan kiranki zance.
Umma wa zaiso ta a haka tana zama ko yaushe kamar kucaka gari kamar a kansu talauci ya kare a duniya.
Allah yasa dai ta iya abinda taje yi din kar taje ta jawowa mutane abin kunya a can don dai sanin hakin kam.
Kallon Abba nayi don jin abinda lantana ta fada sai naga Abba ya kawar da kanshi gefe daya na mayar da kallona kofan cikin gida namu ko Allah zaisa inga inna ta leko sai dai har motar ta daga banga inna din ba.
KADUNA
Hjy iyami zaune a dining din gidan bata da hutu a yanzu tun soma wanan zancen aikin data samu din koda yaushe tana makale da waya a kunnen ta.
Yanzu ma wayan ta kare da wani lauyanta kan kammala mata duk wani takarda da take bukatan samu wanda za a tura abuja a tura zauren majalissa.
Abincin dake gaban ta ta kalla tana dan jan tsuki kafin ta kai hannu ta sama warmer din abincin dake gaban ta.
Budewa tayi sai ga tururin abincin dake cikin kulan yana tashi kamshi ya daki hancin ta tabe baki tadab yi don tasan ba lalai ne yayi dan danonon da take so ba.
Plate ta jawo zuwa gaban ta ta fara diban abincin kadan ta tsakura don ba gwana bace wurin loda abinci a cikin taba.
Lemo ta tsiya ta fara kaiwa a bakinta tana lumshe ido do sanyi da dandanon shi dake shiga cikin ta lokaci guda.
Sallama akeyi a kofa ta amsa tana ba maishi umurnin ya shigo tafiya yake a cikin isa da izza har ya karaso inda take zaune.
Daga tsayen da yake suka fara gaisawa dashi idon shi ya sauke kan abincin dake gaban ta kafin ya amsa mata gaisuwan nata.
Bissimillah ka zauna take nuna mashi kujeran zama dake wurin yace ba zama nazo yi ba nazone in kara jin abinda kika yanke ga maganan mu.
Alh Adamu ina dai yanzu kasan ba,a karskshin ku nake ba don mai rabawa ya raba tsakani da yayan ku ko.
So banga wani abinda zaisa ka jefa kanka a cikin lamarin rayuwana ba kuma.
Yara daine babu taulali a cikim su gaba dayan su sun kawo girma don haka ka barmu muyi rayuwan mu a cikin sallama don Allah.
Jin abinda ta fada yasa ya dan sakd murmushi a fuskan shi yana jawo kujeran yakai zaune tare da fadin zaki iya fadin haka tunda baki so gaskiya.
Kin sani sarai wanan abinda nake neman ki dashi ba haramttacen abu bane sunnan ma aiki zamu raya ta hakan.
Wani kallo ta watso mai tare da fadin Alh Adamu na fada ma ka fita hanya da maganan banzan ne shin wai yin aure dolene ?
Ya dan kara sake murmushi yana fadin amma kinsan aikin ladane ko na rasa meke damun ki kan hakan idan don ta matatace kinsan dai a yanzu kinfi karfin ta ta ko ina.
Mikewa tayi a fusace tana nuna mai kofa tare da fadin fita min daga gida tunda kai bakasan abin arziki ba.
Kai ko kunya bakaji kazo ka kalli idona kace wai aurena kake son yi don kawai kunga kasa ya fufewa mijjna ido.
Yace shi kansh miijin maki ai da zai tasone a yanzu zaiyi alfari da abinda nake shirin aikatawa a yanzu.
Eh na yarda lalai namiji baida kunya yau Adamu kaine da kanka wai kazo neman yardana akan in aureka don kasa ya gama rufe minin idon miji ko ?
Har kamanta da irin tsana da kiyayyan da matarka ta saka min a gida lokacin da kuke ganin kowa a banza a idon ku shine yanzu don baka da kunya zaka dawo da wani zance a kaina.
Matsalan ku ku mata ke nan dawo da abinda ya wuce baya kada ki hada wancan lokacin kurciya da yanzu garemu.
Ni niyana na alheri ne gareki nasan ko yaran ki zasu farinciki da zaben dan uwan mahaifin su a matsayin mijin ki a yanzu.
Ka fice min gida kafin in saka a fitar min dakai ta tsiya ya ce bazan gaji da tunkaran ki da wanan zancen ba har lokacin da zaki sauko don kanki.
Yana fadab haka ya juya ya bar gidan bishi tayi da kallon takaici da kunan rai wanan yana daya daga cikin abinda ya hanata dawowa kasan tun rasuwan mijinta.
Yana fita gidan wuri motar shi ya nufa kai tsaye yashiga ya dade a zaune yana karewa gidan kallo yata da motar ya tafi.
Mun kawo lokacin yamma baiyi ba sosai don la, asar ya wuce a lokacin kai tsaye gidan anty safiya muka nufa.
Gidane tsarare mai ban sha,awa gaskiya ba laifi gidan ya hadu ni dai a ganina ciki muka shiga yayin da muka zauna a falo.
Tau zainab kinga gida yau dai don har umma bata san inda muke zaune ba duk zumuntan mu da ita yau sai gashi ke Allah ya kawo ki gidana.
Mikewa tayi zuwa wurin fridge ta dauko min ruwa mai sanyi a fridge ta aje min tare da fadin sha ruwa kafin ki shiga ki watsa ruwa kiyi sallah sai ki fito muci abinci.
Daukan ruwan nayi da zuman sha sai naji sanyin shi yayi min yawa a bakina ta yadda bazan iya sha ba.
Mayar da kofin nayi na aje saman dan table din ta dawo tana fadin taso in nuna maki dakin da zaki zauna kafin in kai gidan da zaki aikin.
Dakine da gado sai mirrow ta nufi wani kofa tana fadin nan bandakine ki shiga kiyi wanka da alwala ki fito.
Tana fadin hakan ta juya ta fita daga dakin kayana na fara cire na nufi bandakin kamar wace za,a cewa na sheka na sheka da gudu.
Ina shiga naja na tsaya wuri daya ina karewa wurin kallo da mamakin ban dakine haka a gyare tsab.
Saida na gama karewa wurin kallo na nufi bakin famfon dake ciki badon na taba amfani dashi ba a fili amma dai nasan yadda ake kunnawa ruwa yazo.
Don an koyamu a makaranta nagani wanka nayi a tsanake zuciyana fam da tunanen inna mu da yan uwana.
Sai kuma tunanen Abban mu dasu Asabe irin maganganun batanci da sukeyi lokacin da zan baro gida don wai kawai ina ya mace suke min hakan.
Sallah na tayar saman kafet din dakin ban tsaya neman sallaya ba don wurin tsab yake ni a ganina ina zaune a gurin bayan na idar da sallah.
Sai ga anty safiya ta shigo dakin tana ganina kasa take fadin subbahanallahi zainab badai a kasa kiyi sallah ba sam na manta da na kawo maki abin sallah a dakin taso muje kici abinci ko ?
Mikewa nayi na biyo ta zuwa falon na samu yaranta da sukaje islamiya sun dawo gida a lokacin.
Ku gaida anty tace wa yaran da suke kallona da mamaki a fuskokin su suka fara gaidani din kamar yadda mahaifiyar nasu ta umurce su.
Wuri ta nuna min na zauna tana fadin ki saki jiki ki nan kamar gidane a gare ki zainab.
Nakai zaune ina murmushi abincin ta debo ta kawo min a gabana tana fadin ci abinci nasan rabon ki da abinci tun safe.
Kallon abincin nayi dan shikafane da miya sai taliya da ganye da nama tsoka uku a sama.
Dan tsakura nayi duk da ya zamo min bakon abincin daya dace inyi dsukin cin shi a lokacin tunda ban saba cin abinci haka ba.
Sai gashi halin da zuciyana yake ciki ya hanani cin abincin sai tunanen yan uwana da innarmu nakeyi a raina.
Gashi yan uwa basu gida aka wuto dani balle ko sallama in samu inyi dasu tunda bansan tsawon lokacin da zan dauka a wurin wanan bautan ba dabazo yi garin kaduna kamar yarda umma tace.
Bansan mijin anty yana gidan ba saida naji yana magana da yaran shi na dago da sauri ina kallon shi.
Gaidashi nayi hakan yasa ya dago yana kallona tare da amsa min gaisuwan da nayi mai yake cewa.
Itace kuka zo din tare eh yar dan uwanane sukai min karamci suka ban ita kaga abin yazo min da sauki ke nan.
To Allah yasa a dace sai ki ja mata kunne sosai don kin san zama a irin gidajen nan ba kowane zai iya rawayu dasu ba.
Daki na mike zan koma anty ke fadin zaki shiga cikin ne kuma kifa sake jiki nan gidane na fada maki.
Nace zan kwantane ina shiga naji mijin na anty na fadin wanan yar yarinyar suka turo ban san me yasa mutanen kauye suke da wanan akidar ba kan yaya mata.
Yadda wanan rayuwa take a yanzu kosu masu dauko yarab dasun gane su dogara da shiga fadawa wani rikici sam duniyan nan cike yake da rudani daban daban.
Sai dai daman ita wanan din da kika dauko ansan gidan su da kuma inda zaki kaita din in don haka ba gaskiya da zan baki shawara ki mayar masu da yarsu inda kika dauko ta.
Nima kaina saida naje naji banji dadin ganin wanan yarince zasu ban ba don uwarta ba karamin rikici akayi da ita ba kafin ta yarda muzo nan din.
Yace ke nan uwar tasan kanta da abinda take yi ga yarinya kallo daya zaikai mata kasan tana cikin wani yanayi.
Zaka iya sani tunda aikin kune hakan ai don nuna fin karfi kawai aikai masu daga ita har mahaifiyar ta aka ban ita.
Shine kuma kika dauko masu ya safiya baki tsoro abinda kaje ya dawo nan gaba kada faki lalata maku zumunci .
Wallahi don dai hjy iyami ce kuma na riga da nayi mata alkawarin hakan kaga idan na saba mata ba zataji dadin hakan ba.
Yace Allah ya sauwa ka saidai kija mata kunne sosai kafin ki kaita na fada maki zama irin gidan nan akwai kalubalin masu yawa ga wanda bai saba hakan ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
RAYUWA KE NAN YAN UWA MU FADI ALHERI KO MUYI SHIRU SHINE KOYI DA SUNNAN ANNABI SAW , , , ,
DON ALLAH YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA DON ALLAH KI GUJEWA KAYAN ALLAH YA ISA A KANKI
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK 300 NE KACAL ZAKI TURA SABODA ALLAH SHINE HAKKINA GAREKU.
Na dade kwance a dakin badon nayi barci ba tun ina jin karan tv da muryoyin su a falon har nazo na daina jin komai ina jin anty ta shigo tana ja min abin rufa sai naji sonta na yan uwan taka ya kara shiga raina sabanin dazun da nake jin haushinta ina ganin da hadin bakin ta wurin rabani da yan uwana da innan mu.
Tambayan kaina na karayi karo na batkatai mai Asabe da lantana suke nufine a kaina.
Mau ye lafin innar mu da bata ganin laifin Abba shi tunda ba inna kadai ta haifomu a mata ba.
Meye laifin kasancewar yaya mata da asabe ke gani ga innan mu damu wanan halin shi a kowani gida da yaya mata sukafi biyu zuwa ukku kamar mu.
Ba addinine yace a kyamaci diya mace ba wanan hain rayuwane na wasu mutane da hakan ya zama masu al,ada.
A ganina duk da da aka haifa ta sunna walau mace ko namiji albarkan rayuwa ya kamata iyayye su newa yaro.
Ni dai ba zan iya cewa nayi wayau naga inna da Asabe a cikin dadin raiba a gidan mu duk ko da irin biyayyan da ina ke mata sau da kafa.
Ba zan manta a da can baya har talla asabe ta fara dora min idan na dawo boko zan dauki tallan goro ko gyada in fita dashi duk da ina kankanuwa a lokacin.
Da kyat Abba ya samu ya hana wanan tallan ranan kan yasha fitina wurin Asabe ba Abba kawai ba har innan mu ba,a barta ba don cewa Asabe tayi inna ce ta zuga Abban mu don tana bakin ciki ina fita mata talle.
Haka muke abu kamar marayu a gidan mu bawai don mun rasa uwa da uba a raye ba sai don kawai zama da fitinaniyar uwar miji da Allah ya hada inna da ita.
Yanzu kuma tsanar yakai har Asabe ta turoni yin aikatau a birni ba tare da kowa ba gidan mu yasan inda za a kaini ba.
A haka naci gaba da sake saken abinda zan tafi in taras gidan da Anty safiya zata kaini din.
Juyawa nayi ina lumshe idanu tare da fadin Allah yasa hakan shine alherin mu gaba daya kamar yadda anty safiya ta fadawa inna da zamu zo.
Har barci ya daukeni ban sani ba ga dai gadon laushi ga fanka a dakin na samu amma haka bai hanani barci a cikin damuwa ba.
Karfe biyar da wani abu na falka kamar yadda inna ke tayar damu don sallah asuba idona bude nabi daki da kallo .
Sai a lokacin na tuna da inda nake a yanzu da sauri na sauko saman gadon na fada bandakin dake dakin da nake ciki .
Alwala nayi a gurguje na fito na tayar da sallah ina idarwa na dan zauna nayi addua kafin in mike na bude kofan a hankali na fito dakin.
Duk da sauran duhun dare gari bai gama haskawa ba a lokacin amma na gane hanyan kitchen din anty safiya da jiya naga tana shiga tana fitowa da abinci.
Wanke wanke na sama tare a kitchen din ban tsaya jiran komai ba na shiga wanke su a hankali don kada in tayar da mutanen gidan don har lokacin banji motsin kowa a gidan ba.
Na gama na share kitchen din na fito zuwa falo na fara shara da kakabe kujeru da suka kewaye falon can naji motsi alaman wani na fitowa daga dayan dakunan su na kwana.
A, a naji muryan anty safiya na fadi zainab kece a nan kuma har kin tashi ashe ban sani ba yau na gajine sosai dan tafiyan nan da mukayi jiya duk jikina ciwo yake min wallahi.
Ban bata amsa ba sai kaiwa da nayi kasa ina gaida ita da kwana ta amsa min a gurguje tana shiga kitchen din ta.
Sai kuma gata ta fito tana fadin ke yaushe kika tashi halan da kikayi wanan uban aikin haka zainab kin koyi barci da dare ko kin kasa barcine kina tunanen gida.
Nace nayi barci dana tashi nayi sallahne na fito na wanke su tace ikon Allah toh sannu da kokari ashe tafiya zatayi kyau tunda baki da son jiki haka ?
Abinci ta hadawa yaranta yayin da ni kuma na share ko ina na gidan sai gaidani da aiki takeyi tana fadin kinga idan har zakici gaba da hakan ina mai tabbatar maki zaki ji dadi sosai a wurin hjy.
A raina nace watau ma wurin hjyce za a kaine kenan matar mai kudine tunda naji harda hjy anty ta kirata matar yanzu.
Ni tace in shiga in shirya yaranta a wani daki nayi ta bin dakin da kallon mamaki a raina tana min bayanin abinda zan masu.
Ta fita ta barni da yaran a dakin ina shirya su bayan nayi masu wanka da broshe tsab suka fito a tare muka fito daga dakin tace dani kinga koma ki gyaro min dakin nasu in karasa shirya su a nan.
Dakin na koma na fara tattara kayan da suka watsar kafin in hau gadon dakin da gyara kafin wani lokaci sai ga dakin tsab dashi kamar bashi bane suka bata dazun da tarkace ko ina.
Nan anty safiya ta yaba min sosai tana kara min bayanin kinga tun da safe idan kin tashi kinyi sallah.
Kada ki tsaya sanyin jiki ki yi duk wani aikin da kika san naki ne a gidan tunda kina da kwazom tashi haka da safe.
Don Allah zainab kada ki yarda ki bani kunya don inda zan kaiki nima gidan kunyanane can tayi bugun gaba ne dani tasa in samo mata yarinya natsatsiya mai kwazo da tsabta da amana.
Idan kinga abu ba a baki ba kada ki yarda ki taba shi komai son da kikewa wanan abin a ranki.
Na amsa da to anty tace zaki ga kudi kamar a banza mai yuyuwa zata gwada ki na dan lokaci taga idan kina da amanan hakan kafin ta yarda dake bandai sani ba.
Zan fada mata gaskiya ke din yar uwatace ta jini don ba zan lamunci suyi maki wullakanci irin wanda akewa yan aiki ba ke kuma sai ki rike min amana sosai don Allah wanan abin taimakon kai da kai zamuyi tsakani nidake zainab.
Insha Allahu anty na fada don idan ta kirani da zainab din nan yanzu sai inji kamar badani take magana ba.
Wasa wasa na share sati daya gidan anty safiya banji zancen tafiya gidan da za a kaini din ba, nima kuma ban tambaya ba.
Ashe hikimar ta na barina a gidan ta don dai in koyi wani abinda ta fahinci ban sani ba kada ta kaini a sha wuya a can .
Gashi kullun cikin yi min bayani take da fahintar dani komai na rayuwa a birni wanda mu can kauye bama yin su.
Har na dan fara sabawa da yaranta yanzu sosai ranan da dare muna zaune falo muna kallon wani shiri na yara naji anty ta ambaci sunana .
Hakan yasa na juyo ina kallon ta cikin ladabi take fadin ina ganin gobe zan kaiki wajen hjy dazun muyi waya da ita take tambayana ke .
Wani irin ba dadi naji a raina lokaci guda damuwa da fargaba ya dira min a zuciyana lokaci daya.
Ganin canjin yanayina take fadin ki kwantar ds hankalin ki can ma nafada maki gidane a garemu ai tunda gidan babban yayan mu ne saidai shi a yanzu bai raye matarce kawai da yaran su a gidan kuma yaran ba yara kana bane sun girma kananan ma zaku zo yan sa,a daya dasu.
Sai dai daga mazan har mata kada ki shiga tsabangan kowa duk abinda suka saki indai baya kaucewa idini bane wanda kuma ya shafi gaban kowa a cikjn gida kiyi.
Na fahinci may anty ke nufi a nan ma, ana na kama mutuncina da kimata ga kowa a gidan dai.
Haka na kwanta da tunane mai yawa sai kewan gida ya dawo min sabo sosai a raina don haka ban samu barci sosai a ranan saboda tunane.
Karfe goma na safe muka bar unguwan su anty safiya wanda nake jin ana kira da barnawa muka doshi inda zasu kaini a motar mijin anty safiya din.
Anty ta ban wani jakka nata na saka yan kayana wanda ta sai min kala hudu dana zo don tace nawa ba zasu tafi ko ina ba a haka.
Sai bin garin nake da kallo yayin da anty suke gaba da mijinta zaune suna dan hiran su da ban san ko a kan wa suke zancen su ba.
Kafin mu bar gidan anty safiya sai da sukai min nasiha sosai mjin anty safiya yace in kiyaye ibadana inyi hakkuri da duk yanayin da zangani a gidaba, ainyi biyayya ga wa yanda na sama a gidan.
Shiga nan bullo nan har muka kawo unguwar mai kama da kasan waje muka fita ba jahata na kaduna ba.
Uguwar kanshi abin kallo ne ba mutane sai motoci jefi jefi da suke wulgawa saman shimfudeden kwaltan da aka zuba a titin.
Idan kaga wanan ginan sai kace shiyafi kyau sai kuma idan kaga wani kallo ya koma sabo.
Wani katon gida daya tafi da imanina tundaga nisa mijin anty ya tsayar da motan shi yana danna horn.
Kafin wani mutum daba tsoho ba ya fito yana dan lekowa naji anty na fadin bude get mune da mijina.
Ya amsa yana washe baki tare da saurin komawa sai naga kofan na budewa kamar injin.
Ya danna kan motar zuwa cikin gidan naji mutumin gidan yanayi masu sannu da zuwa da alama dai yasan anty din sosai .
Saida mijinta ya tsayar da motar shi ne take fadin amma dai kasa yau zaka shiga ku gaisa da hjy ko ?
Yace zan shiga kodon ta san yarinyar nan tana da muhinmaci sosai a garemu ai don ni dai da kinbi tanawa da ba, , ,
Please dear ina mun gama wanan zancen tun a gida sai kuma ta juya da harshen turanci tana magana.
Ko ta dauka bokona baikai indanji abinda take fada bane oho do maganan da sukeyi da alama mijin nata yace a mayar danine kota rikeni tunda yar uwarta nake.
Allah sarki nace a raina wanda ma suka haifeni suka san zafina sun kasa barina a gaban su balle anty da daga sama ta ganni haka.
Don ina jin tana fada mai taso hakan amma kawo ni nan din shine mafita a gareta naji yace to shike nan Allah ya tsaya mata da hausa.
Su suka fara fita daga motar kafin anty din ta zagayo ta bude min gefen da nake tana fadin in fito.
Na fito sai bin gidan nake ko ina da kallon mamaki ina rayawa a raina wai yanzu mutane ne sukai wanan ginan haka da hannun su ?.
Nidai ina bisu a baya ina karewa gidan kallo ta danna wani abu a bango ba, a dauki lokaci ba sai ga wata yar dattijuwa farace tafito tana fadin waye sai sukayi arba da anty dake tsaye a kofa.
Hjy kece take cewa anty safiya nice kande ko hjyn tana ciki ta tambaye ta ?
Tana nan yanzu ko tashiga daga cika ta fadi tana matsawa daga kofan da take tsaye.
Shiga mukayi kai tsaye saida naja baya don abindana fara takawa ko ina na falon sai kyali yake da daukan ido.
Zama sukayi a kujerun dake katon falon yayin da nakai kasa daga gefen anty din mijinta ya kalleni tare da fadin ki zauna saman kujera mana.
Naji anty tace kasan ta ai da halin su na yan kauye barta kawai zata zo ta saba wata rana ai.
Matar da naji anty ta kira da kande ne ta dawo falon dauke da tire da abin sha a ciki.
Ga kan shin girki yana tashi a wani bangare na gidan duk da kamshi da falin keyi bai hana na girkin ziyaran hancina ba.
Ga abin sha hjy kafin hjy ta fito, ta fada tana ajewa a gaban su bin abinda ta aje din nayi da kallo.
Saida suka dan taba hira da mijin ta muna zaune ni dai sai bin hotunan dake tsaye a falon manya manya dasu kamar mutun ne tsaye a wurin nakeyi da kallo.
Sai ga matar gidan ta fito da fara,a a fuskanta tana fadin ashe kuna tafe yanzun nan na shiga ciki.
Tun safe yaran nan suka tayar dani da rigimar su na fito tarba na mutunci naga tana masu tana saki fuska da jiki dasu.
Ta kalli mijin anty tana fadin yau baka fita aiki ba ke nan ta fada tana kallon shi.
Ban fita daga nan zan wuce ya bata amsa da kara fadin yarinyar nan muka kawo dama.
Ta juyo tana kallona tare da dan kuramin ido na dan lokaci tace masha Allah.
Yarinya kamar kin shiga zuciyana kinga irin age din da nake so ta kasance min gashi ko kin samu ai anty safiya ta bata amsa.
Menene sunan ki ta juyo tana tambayana kafin ince Abu naji anty safiya tace zainab ce sunanta.
Kai zainab kice uwata ce ashe yarinya kin samu suna mai kyau kuwa tana kallona da kulawa.
Aikuwa na manta sunan mama na unguwar rimi ke nan fa dacewa kanwar mahaifiyar hjyn .
Mijin anty ne yake fadin ni zan tafi hjy don Allah sai a hada da hakkuri don kin san yarinyar akwai kurciya da kauyanci a tare da ita yanzu.
No no no kada kuji komai wallahi muma ai kauyene asilin mu a da ko kowa ka gani daga kauye yake ai.
Shigowa wasu yara kanana su biyu mace dana miji falon yasa zancena ya tsaya a nan suka juya magana kan yaran.
Anty ke fadi a a ashe mutanena suna nan sai hjy tace wai yau hutu sukeyi basu je school ba sun shiga meet time break ne.
Hannu anty safiya ta mika masu suki tare da make kafadun su suka nufi sirin kakan su kai tsaye.
Tafiya ya fara yi tare da fadin to zainab a kulla kinji banda rashin ji anty safiya tace in tayi rashin ji ai zata gamu da nine sosai.
Karfe nawa zaka dawo yace na fada maki sai yamma don haka idan kin gama ki koma gida don yara kada su dawo school bakya nan.
Wai har yanzu motar bai tashi bane hjy ke tambayan anty motar ta kafin anty tace wanan motar ai sai wata yanzu gashi yaki ya saya min wata ina ta faman bin shi yana ja mi rai.
Ki bar kanina ya huta safiya indon motace zan sa a duba maki idan ba zaki raina ba dai kai kai kai kice wanan zuwan takice ashe mijjn ta ya fada .
Kasan ai safiya ta hannun damana ce sosai tafi danan a gurina in dai tana so.
Ya tafi tare da ma hjy sallama nabishi da dan kallo kamar ince don Allah kada ya tafi ya barni.
Anty ta mike tabi bayan shi bayan tafiyan tane falon ya danyi shiru tana ta danne danne a wayan ta sai ga anty safiya din ta dawo falon.
Zama tayi sukaci gaba da hira a cikin hiran nasu ne take fada mata yadda muke da ita .
A hiran na kara fahintar irin zumuntar dake tsakanin mu da ita din wai ashe mahaifiyar su da Asabe ce ya da kanwa.
Asabece ya mahaifiyar su kanwarta tace kai kice min ita din ta gidace ashe eh ta gidace gaskiya sai dai gaskiya kin san yadda zumuncin zamanin nan yake ai.
Koma dai yaya ne ai takice ita zan duba inga yadda zamu zauna sai ta kira wanan matar ta dazun data kawo ruwa tana fadin.
Kande ga bakuwa ki bata daki wanan na kusa dani zaki bata don ni tazo gidan nan don kula da harkokina.
Don haka zaku zauna tare sai dai kowa da aikin shi daban ke naki kula da kitchen ne da sauran ayukan da kika sa kinayi.
Ita din dai ki barta dani sai zuwa gaba idan ta saba zan fara nuna mata aiyukan ta yadda ya dace.
Sannu da zuwa kande tace min tana kokarin daukan jakkar kayana da anty ta shigo dashi ta aje a kuss dani.
Kagin anty tace na karbs ni har na mike ina karba matar na fadin ai da ki barta bakuwace fa nace a a mama kawo in dauka.
Jeki ta kaiki daki da zaki zauna kafin in shigo hjy ta fada tana dora kafanta saman dan table din dake kusa da ita.
Muka nufi cikin gidan wanda bai isata da kallo matar na gaba ina binta har zuwa cikin dakin da akace ta kaini din.
Dakin ta bude tana fadin bissimila shigo daga ciki nabi bayanta muka shiga.
Wanan shine dakin ki sai ki zauna ki huta kafin girki ya sauka a wuta muci ni nawa dakin yana can daga waje kadan ta hanyar kitchen idan kina nemana.
Daga haka ta juya ta barmin dakin ina tsaye sai bin dakin nakeyi d kallo nida ke santin gidan anty safiya sai gani a wanan dakin da fadin tsaruwan shi bata lokaci ne.
Anty safiya bata bar gidan ba sai karfe dayan rana bata tafi ba saida ta shigo dakin ta kara min nasiha kan nayi biyayya ga kowa a gidan .
Ta tafi ta barni cikkn kadaici da damuwa a gidan da ban san kowa a cikinsa ba ban ma san a inda nake ba dai.
Wani irin kuka ne na rushe dashi ganin ta tafi ta barni daga ni sai halina sai wa yanda a yanzu zan zauna dasu din.
Ganin kuka ba zai min bane yasa ni tashi na shiga bandaki dukda ba a nuna min ba dan zaman da nayi gidan anty na dan fahinci ya ginan birni yake yanzu.
Alwala na dauro nazo na tayar da sallah ban daga ba na dade a wurin ina addua kafin na dan kai kwance sai ga barci ya daukeni a haka ba tade dana sani ba a wurin.
Babu komai a raina sai tunanen halin da mahaifiyata take ciki a yanzu tare ds yan uwana a raina.
Nasan innan mu zata kara shiga wani hali a yanzu don barina kusa da ita dan taimakon su daya ne wanan kudin da ban san ko nawa bane da anty ta bata da zamu zo.
Irin wanan tunanen nakeyi sai hawaye yazo mi lokaci guda don tunanen hakin da inna zata shiga yanzu da ban kusa dasu dama da dan kudin kitson da nake muke tallafawa ake samun abinda akaci.
Gashi yanzu lantana da Asabe sunyi makarkashiyan da aka raba tsakanina da mahaifiyata da yan uwa anya zan iya mantawa da wayan nan mutanen a raina kuwa , ?
.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ALLAH KA SADA MU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN RANAN TA JUMMA,AT ALLAHUMA AMIN , , , , , ,
DOMIN SAYA SAI KI TURA KUDI TA WANAN ACCOUNT DON KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK, , , , , ,
Ni Abu ban taba tunanen zan gani a cikin irin wanan dakin ba ko a mafalki ban taba hango wanan irin gidan a malkina ba.
Yau sai gani nayi barci na falka na ganin cikin wanan gidan ga sanyin AC da kande ta kunna kafin ta fita ya hade dana ties din dakin yana ratsa balgon jikina a hankali.
Duk da sanyin yana damuna ban tashi a yadda nake kwance ba a kasan na dunkule a wuri daya sai faman tunane nakeyi na rayuwa.
Muryan hjyn ce yasani dagawa daga inda nake kwance wanan karon ta sauya kayan dake jikin ta zuwa dogon riga mai laushi da daukan ido jikin shi wani dabbara dabbara ne kamar jikin zabra.
Taci gaba da fadin ke zainab bakya gudun sanyin kasan nan ya ja maki illa kiyi ciwo fa.
Da sauri na dago ina gaida ita dakin take bibda kallo ta sauke idon ta ga jakkan kayana tana fadin ga wardrobe nan ki saka kayan ki a ciki .
Taci gaba da fadin ki dunga kula da kani ki kula da tsafta sai muyi zaman mu lafiya.
Mu gaimaki juns tsakanin mu don kingani nan bana shiri da wanda baida tsafta sam.
Iyakar sikin ki a gidan nan yanzu shine kula da sashina da komai wanda ya shafi rayuwana a cikin gidan nan.
Yarana duka manya ne kuma duk zasu girme maki kinga kenan suna matsayin yayyin ki ne.
Ni a yanzu yar kasuwace kuma mai rike da mukamin gwanatin kasan nan .
Kinga ina da manyan hidimomi a tare dani wanda hakan yasa banda lokacin kaina shine dalilin da yasa nace a samo min yarinya da zata dinga taimakamin.
Sai gashi ke Allah ya nufa a sama min na kuma yaba da irin yanayin dana ganki dashi na natsuwa .
Ina fatan zaki zauna damu gaba daya gidan nan da zuciya daya cikin amana da yarda.
A hankali na dago kai tare da fadin insha Allahu hjy nayi alkawarin hakan.
Ban iddasa rufe bakina ba tace ba hjy nake a gurin ki ba mami nake don ni uwarkice a yanzu ki dauke ni yadda sauran yaran gidan nan suke daukana.
Da fatan kin fahince ni tace ta fara tafiya don fita dakin tare da fadar ki fito kici abinci a falo yanzu idan kin gama saka kayan a ciki.
Na amsa da to hjy da sauri nace mami tayi murmushi ta fita yayin da baki na yake dafe don katobaran dana farayi.
A gurguje na jera kayan kamar yadda tace saidai saida nasha wahala wurin gane yadda zan bude wardrobe din.
Falon na fito na dauka ita kadai ce kamar dazun sai dai naga sabanin hakan don sun kai su gama zaune wurin a ganina.
Ja nayi na tsaya dan nisa kadan dasu ban karasa wurin da suke ba hjy ce ta dago tana fadin.
Zainab zo ki zauna mana kici abincin tana kallon inda naja na tsaya dan nisa dasu kadan.
Firgigit nayi daga sana,ata dana fara watau tunane don yanzu ya zama min abin yi ko yaushe.
Sai lokacin sauran dake zaune suka farga da fitowana falon gaba dayan su juyowa sukayi suna kallona lokaci guda.
Karaso mana kizo nan ga abinci nan ki diba ta kara fada sai naji sun kwashe da wani dariya.
Wai mami sabuwar mai aikice kika dauko kuma take tambayan hjy tare da juyawa taji amsan da zata bayar.
Haba dai mai aiki a haka kuma sai a rasa wace za a dauko aiki sai wanan yar kauyen haka irin yan kauyen nan fa wahalan sha,ani garesu kafin kansu ya waye don basu iya komai ba sai shirme da kauyanci wata yar farafara ta fada.
Dayan ta yamutsa fuska tana fadin but she is dirty mami don Allah kada ta karaso nan inda muke.
Ai kin san halin hajjajo da son mutane yanzu haka wani wurin ta kwasota itama ya fada yana mayar da kai ga abincin da yake ci.
Yar uwan gwaggon Safiya ce kuga kenan kuma ta zama yar uwarku ai .
Yanzu a nan gidan zata zauna damu ke nan ko dai tazo yin wani abune Rufaida ta tambaya a yatsune ?
A haka mami zata zauna damu Nazifa ta fada tana kyabe baki tare da fadin ashe zamu sha kauyanci a gidan nan kuwa.
Hjy tayi murmushi tana fadin in dai wanan da kuke ganine cikin kwana biyu zata goge ta zama yar birni tayi fes kamar kowa.
Dariya suka sa gaba dayan su a lokaci guda nidai ina tsaye a inda nake ina kallon su kasa kasa ina jin cin mutuncin da suke min.
Zainab kinja kinyi tsaye karaso mana ki dibi abinci kici hjy ta fada tana yafutoni da hannu.
A, a mami don Allah dai karta matso nan ta bari idan mun gama sai ta zo ta diba amma ai haka raina mu zatayi ta dauka daya muke da ita.
Tsawa hjy ta dakawa mai maganan tana fadin karna sake jin haka daga gareki ita din ba mutum bace kamar kowa nima a haka mahaifin ku ya daukoni ai.
Shiru sukayi suna cigaba da cin abincin su yayin dana karaso inda hjy take na dan labe ina kaiwa kasa na fara gaida su.
Ku duba yadda ta baku girma yanzu a cikin mutunci amma ku kuna kokarin zubar da darajan ku a idanunta, baku san cin fuska baida dadi ba.
Shiru sukayi kowa na kai abinci ga bakin shi tashi ki dibi abinci hjy ta sake fada karo na barkatai.
Plate wace batai magana ba ta jawo ta fara zuba min salma ke nan ta juyo tana fadin may za, a zuba maki ?
Na nuna wanda ke cikin plate din dayan namijin dashima baiyi magana ba sai kallon banza da yake min.
Dariya suka kwashe dashi ya dago kai yana tambayan menen suke cewa choice din ku daya da yarinyar nan abincin ka ta nunafa.
Ware idanuwa yayi waje tare da fadin ke ni sa,arkice bakiga kowa ba a wurin nan saini halan.
Yana fadin haka yai kwafa ya ture abincin ya tashi daga wurin sai suka kara fashe mai da dariya.
Miko min abincin tayi na karba tare da dan rusunawa ina fadin nagode na juya zan bar wurin naji hjy na fadin ina kuma zaki tafi kici abincin ?
Dan marairaicewa nayi ina fadin dakina hj, , mami ba zaki sake jikin ki ba har yanzu kina kewan gidane ko nidai na danyi murmushi na juya na tafi.
Ina kallon abincin wai duka wanan naman da aka zuba a ciki nawane ni kadai kai yan birni kan suji dadin su.
Wanan ai shine zamuci duka gidan mu da sallah idan yazo don sallah kadai muke cin nama sai ko idan rabo ya ratsa Abba ya sayo muna a ci.
Gaba daya na cinye abincin tas na dauko plate din zuwa kitchen don na fahinci a nan kitchen din yake dazun da mama kande ta fito da abinci.
Na canka daidai na samu baba larai tare da wata mata tana juya miyan da zasuci da dare miyan kaine saidai ban san ko kan me bane na daiga ya ciko tukunya sosai tana motsawa.
Gaida su da aiki nayi kande ke fadi kin kamala ci yar nan ina jin marasa ta idon gidan nan dazun sunayi maki shakiyanci da suka iya.
Ki fita batun su dan haka halin su yake da rainin wayau tsiya tundai in sun raina da kuran mutum sai suso su raina shi.
Don ma hjy tana taka masu burki aida abin nasu yafi nan wallahi dayan matar ta fada.
Inda wanke wanke suke na nufa na shiga hadawa da sauri kande tace yar nan me zakiyi nace wankewa zanyi mama.
Rufa min asiri kada hjy tazo tagane ki tace na baki aikin da yafi karfin ki ko dazun saida ta kara jaddamin zance a kanki.
Zan iya ai basu da yawa na fada ina kokarin hada kayan wa yanda sukaci abinci dasu da yamma.
A gurguje na wanke kayan tas dayan matar da ake kira larai tana saka min albarka na kare tare da fadin aikwai wani aikin da zanyi kuma mama na tambaya ?
Babu yar nan sai dai kizo muje dakin hjy na fara gwada maki aiyukan datace a nuna maki na bangaren ta.
Hannu ta dauraye tana gaba ina binta baya muka nufi inda sashen hjy yake don gyarawa a kofa muka tsaya.
Tana kwankwasawa kafin a bamu izinin shiga daga ciki hjy tana kwance kishingide saman wani kujera mai kaman gado a dakin.
Ga wani abu babba kamar waya a gaban ta tana latsawa ta dago tana fadin kande baki bar yar nan ta huta ba yau yau da kawota.
Ai sai taga aibun kan hakan to hjy nayi laifi wai gani nayi dai ta fara sani tun yanzu ai ba aikin zatayi ba a yanzu gani kawai zatayi ta koya.
To shi ke nan hjy ta fada tana mayar da hankalin ta wurin abinda takeyi a lokacin.
KAUYEN ANCAU
Iska na wahal da mai kayan kara a gidan nan yarinyace dai ta tafi ba dawowa zatayi ba balle mutum ya shige daki yaki fitowa.
Lantanace ke magana ita kadai a tsakar gida inna na daki tun bayan tafiyan mu har yara suka dawo boko suka tafi islamiya taki fitowa waje.
Gashi sai tambayana suke inna ina yayar mu bamu ganta ba tun dazun tace dasu ta fita kawai daga haka kowa ya shiga harkan gaban shi.
Sun tafi islamiya sun dawo sun samu inna a yarda suka barta haka yasa saratu mai dan wayau a cikin su sake tambayan inna.
Inna wai lafiya kike yau kuwa ina yayan mu tajene tun dazun bata dawo ba kuma ban santa da zuwa unguwa haka ba ai.
Hawayene ya fara zubawa inna da sauri saratu ta juya wurin jakkan kayana tana dubawa tare da fadin inna sun dauke yayan mu sun turata aikatau ke nan ?
Wani irin kuka inna ta kara fashewa dashi lokaci guda saratu ma kukan ne yazo mata sai hakan ya jawo hankalin sauran yan uwan mu dake wasa kofan inna.
Saratu ke fadin wayo yayan mu ki dawo kada kije aikatau don Allah an ce ana lalacewa wurin aikatau din nan.
Haba dakin inna ya koma dandalin kuka da tashin hankali don kuka sosai yaran keyiwa inna.
Da gudu lantana taje ta kira Asabe tana mayar mata da karya wai ga inna can ta tasa yara a gaba sai kuka sukeyi don tafiyana.
Asabe ta fito babu ko dan kwali a kanta sai a hannu ta rike tana fadin bamu cikin abin kuka da yamman nan .
Kuyi muna shiru masu mugun manufa da sheri don tafiyar yar uwarku zaki zauna ki dasa muna kuka ke da yara haka kamar anyi mutuwa a gidan.
Asabe wallahi sai kin dawo muna da yayan mu ko zaman gidan nan ya gagareki keda munafukanki da cewa lantana.
Mara kunyar banza da wofi koke can kika nufa idan naji dadin yar uwanki ana turo min kudi irin haka marasa hankali kawai.
Da kuna zaune a gida kara zube ina zamu samu irin kudin da muka samu yau a gidan ba gashi har kun dawo kun samu anyi abinci ba yau.
Kowan nan sai ya dandani wanan hanyar aini yanzu gaba haihuwan ku ya kaini tunda na samu mafita daku.
Ana cikin hakane Abba ya shigo yana fadin yaya yayane tun a kofa nake jin muryan ki umma.
Asabe tace barni da mutanen kawai din nan wai tafiyar yarinyar nan yahanasu ta saka yaran nan a gaba suka mayar muna da gida gidan makoki.
Yahanasu kina da hankali kuwa ke yanzu idan kina da tunane ai wani nauyi aka rage maki Abba ya fada.
Fada mata dai ko zata gane hakan ina nan gashi dan kudin da hajiya ta fara bayarwa kowa ya fara amfana dashi gidan nan ba gashi kunci shinkafa da wake ba yau a gidan.
Umma kyale ta barin ganta ni yahanasu har mamaki take bani yanzu kan yarunyar nan babu nuna kawaici a kanta ko kadan.
Idan ma bata nuna ba ita ta sani nidai na nuna mata nike da iko da abina daga diyan ko har kai a gidan nan ko wa yan nan na samu mai daukan su bayar dasu zanyi zuwa birni.
Ba saki bada muba tunda ke kika haife mu cewan Saratu sai inna takai mata duga daidai Abba na shigowa dakin inna din.
Bar dukan ta rabuwa da dan uwa nada zafi tundai irin wanan na yarsu nima dai ba haka naso tafiyan nataba kai tsaye so nayi muje tare inga wurin.
Koma dai menene yanzu aikun nuna min kukeda yarku saidai ina son ku sani naji umma na fadin har wa yan nan za a tura min can birni aikatau.
To wallahi hakan ba zai yuyuba wanan ya isa haka idan da hali dawo da yata zanyi gabana yafi mun kwanciyar hankali idan kasa mukeci mu kwaba muci tare.
Toto to ya isa haka yana sa hannu ga aljihun shi ya ciro yan dubu guda biyu yana fadin ga wanan kya samu ko sabulun wanki ku saya.
Da da nake saya kai kake ban kudi katafi da kudin Allah ya isan ka can kuci ku kadai ku gani.
Kwadan ku ya fada kun raba ni da yata kun rabata da gatan ta da Allah yai mata don kawai tana diya mace.
Shiru Abba yayi don inna bata taba tsayawa ta fada mai magana ba haka kai tsaye irun ranan.
Kwafa yayi ya fita bayan ya mikawa saratu kudin yana fafin karbi ki aje mata idan ta sauko zata karba a wurinki.
Yana fadin haka ya fita daga dakin don kada yayi laifi a gurin lantana dake tsaye ta rike kugunta tun shigan Abba dakin inna.
Yana fitowa fuskanta ya fara kallo ta watsa mai wani harara ta juya zuwa dakin ta shima abba yasan sauran zancen ranan a guri lantana don haka wani dabara ya fado mai.
Yana shiga dakin ta juyo zata fara fada yace me zakiwa fitina kin san dai ba zama nayi a can ba rufe mata baki nayi da dubu biyu ke kuma ga naki dubu biyar ki rike.
Sai lokacin lantana ta dan saki murmushi tana fadin wallahi yau Allah yaso ka da kakoma can ka kwana surin tsohuwar matar ka
Nina fara hakan gani da dalleliya kamar ki inje dakin da warin fitsari da kwamatse ya ciki.
NEW G R A KADUNA
A hankali mama kande take koyar dani komai duk wani abinda ya shafi mami da zirga zirgan ta na cikin gida nice mai mata hidinar shi..
Da na zauna zaki ta kirani da zeey zan amsa da na,am mami in zo da sauri don biya mata bukatun ta wanda ba wani aiki bane.
Sai dauko min kaza jiki mayar da wanan a cikin wardrobe ko dauko min ruwa shine aikin nawa kawai dawai mami bata iyawa sai an dauko mai mata wanan hidimar da ban daukeshi a aikin komai ni.
Sai gashi cikin sati daya kacal na gane komai na mami nasan lokacin tashin ta daga barci .
Zan shiga dakin in gyara gado in wanko mata ban daki zan koma in hada mata ruwan wanka tana zaune tana lazumi don mami akwaita da yawan ibada sosai.
Zan dawo dakina in jirata tana tashi zata kirani in dawo in share dakin duk da ba wani datti ke ga dakin ba amma kullun sai nayi gyaran shi sau biyu a wuni.
Kafin ta fito wanka nagama hada komai sai in koma dakina can kuma idan ta fito zata kirani da zeey zan zo in je dining in hada mata tea wanda wani ruwa ne baki kawai sai dan sugar kadan bata shan madara da suga ita.
Idan na gama zan koma dakina inyi wanka in shirya in dan huta kafin ai mi wani kiran kuma inzo.
Kai masu kudi suna shagalin su banda abin aikin kudi wai wanan dinne aikin da aka raboni da gida do shi aikin da mutum zaiwa kansa ba sai ya nemi mataimaki ba.
Amma hjy gashi tana ganin ina aiki sosai sai fadi take yarinyar akwai kwazo da sanin ya kamata.
Do ita gani take yanzu komai na zuwa mata da sauki a nata bangare har zata samu tayi barci ta huta na dan lokaci.
A bangaren yaran gidan hjy kuwa ba ruwab su da shiga tsabgata nima hakan ne dasu.
Saidai su wani lokacin zasu sakani wani aiki a gidan wanda ya shafi rayuwan su suma ga tsana karara da ko wace ke nuna min.
Dan gara salma da har yanzu ba zance tsanane ko tausayina ba a ranta don na kasa fahintar inda ta dosa dani a ranta.
Wani lokaci inji sanyi a wurin ta wani lokaci kuma idan ta daka min tsawa sai na gigice don tsoro.
Ita irin mutanen nan ne shiru shiru da mugun ta don surutu bai dameta ba ko kadan za a zauna wuri ba zakaji bakin ta ba sai wani lokaci ta furta idan ta furta daya kuma shike nan.
Duk wanan abinda suke min bai damuna naka ma raya a raina idan naga sun dau wanka zasu tafi school nakan ce inama a ce nice a matsayin su haka.
Nasan da ko Asabe ba zatayi gigin takani ba balle lantana dana tsana fiye da kowa a gidan mu yanzu.
Ni dai na rasa dalilin da yasa yaran gidan hjy suka tsaneni a baki dayan su in ka debe hjy da mama kande da suke nuna min kulawa a gareni.
Tun dai ace yan matan don a fili suke nuna min kin jini da kyama duk da yanzu nasan nima ina tsabta fiye dacan da nake Ancau din mu.
Na kanyi tunane indon dun kauyancine da kazanta yazu duk na daina wanan a ganina do na canza nayi fes na kara zama shar kamar bani ba.
Ga mai da turare na yan gagu da hjy taban tace in dinga shafawa idan nayi wanka gun kashe gari dana zo.
Komai ina yi shi a taka tsamtsam a gidan ban yarda in ketare iya inda aka ajeni ga aikina dan dama wani lokaci idan zama ya isheni nakan shiga kitchen in taya su mama kande aiki do su basu da hutu kamarni.
Ko yaushe a cikk girki suke dan hutun su kadan ne tundai idan yaran gidan suna gida wancan yace kaza yake so wana yace baya cin kaza yau.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
9️⃣
YAR UWA NOVEL DINA NA KUDINE KIJI TSORON ALLAH KI BAN HAKKINA KAFIN KI KARANTA DON GUJEWA SHIGA HAKKIN WANI, , , ,
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI TURO KATIN WAYA DARI UKU NE KACAL BA YAWA, , , ,
Ina daki naji muryan hjy tana kwalla min kira daga dakin ta nima na amsa da karfi da Na,am mami.
Fitowana daga wanka ke nan lokacin don haka na dauki riga a gurguje na saka a jikina don zuwa amsa kira hjy din.
Na sameta zaune tana waya saman gadon da yasha gyara a wurina tunda safe nake gyaran dakin mami din don duk wani aiki da zata kai ga bude baki tace inyi kafin ma tace nayi din tunda yanzu nasan aikina a gidan.
Bana jin kiuya ko kasala tunda na saba aikin daya fi wanan a kauye don hakane hjy bata samun matsala dani koda an samu din ma saidai gyaran dan abinda ba,a rasa ba kawai.
Ganin tana waya yasa naja na tsaya daga nesa kadan ina jiran ta gama waya ta bani umurnin abinda zan mata lokacin.
Wasu kaya data fitar ta nuna min da hannu alaman in dauko mata su ban tsaya ba na juya zuwa wurin kayan na fara dauko su ina ajewa a gaban ta.
Sai waya take ta faman yi mai kama da fada da alama dai da danta ne ko wani kanin ta take waya yadda nake jin tana fitar da kalamai gareshi.
Bayan na gama kwaso kayan ne naje gefe na tsaya don bata ban umurnin in tafi ba.
Hango tawul din data fito wanka ta goge jiki nayi gefen gadon ta na juya zuwa wurin na dauke tare da nufar kofan ban daki na shiga na baza shi a dan karfen da ake bazawa.
Unders din da suka taru a duk da na ranan dana daren jiya datai amfani dasu ne kamar rigan nono da buje da handkacin amfanin ta.
Sai na tsaya na wanke tun ina jin muryan mami tana waya har nazo na daina ji da alaman ta dai gama wayan ne a lokacin.
Nafito ta bini da kallo tana fadin wai dama kina cikin dakin nan zeey ?
Ina ciki ina wanke under din da ke ajene tace min kai zee bakya hutu ko yaushe kina cikin aiki ai kiranki nayi kawai don ki miko min kayan nan in gani don jiya aka turo min su daga Dubai.
Daga min su daya bayan daya nagani na duka na fara dauko kayan ina dagawa daya bayan daya tana daga kai idan na nuna mata.
Amma sai naga kamar wanan yafisu tsaruwa zeey tana tambayana ta hanyar dago kanta taji me zan fada.
Mami duk suna da kyau sai dai wanan din zai fi maki kyau gaskiya don kallan jikin ki.
Ido ta kura min kamar tana nazarina kafin tace ashe kin iya zaben abu mai kyau kema ni dai murmushi nayi kawai ina kawar da kaina gefe.
Sai dai ke har yanzu dadina dake kinki sake jiki a gidan nan ki nuna nina haifeki kamar kowa .
Kullun kina abu kamar bakuwa a gidan nina rasa wanan halin naki kodai bakijin dadin zama da mune zainab ?
Da sauri na dago kai ina fadin mami ina ji haka dai yanahina yake ko a gida nan ma aina sake ke nan .
Sai tayi dan murmushi tare da fadin a hakan da kikeyi sai na dinga tunane ko bamu kyauta makine wani sa, an.
Shigowan Rufaida dakin ne a daidai lokacin da nake kwashe kayan zuwa wardrobe din mami kamar yadda ta umurceni inyi.
Rufaida tayi sallama ta shigo ina jin suna gaisawa da mami din take fadin kunga dama kun tashi ke nan yau weekend kun samu wuri kun kwanta kuna ta barci ina sauran mashiriritan suke basu tashi bako har yanzu ?
Ban dubasu ba ta bata amsa gefen hjyn naga ta zauna ysyin da nazo wurin da niyar incewa hjy din akwai wani abinda zan matane ko in wuce.
Kafin in furta Rufaida ta daka min wani uban tsawa malama may kikeyi kuma a nan bakin gama aikin ki ba ki fita magana nake son yiwa mami yanzu.
No no no Rufaida na fada maku bana son wanan hattaran da kukewa yarinyar nan bari ganin tazo tana aiki a karkshin mu.
Ku dauka hakan gazawa ne ko wani abu ni da kaina na rokota hannun iyayyen ta kuma aikaimin karamci aka ban ita don haka duk daya na dauke ku gareni don jinta nake kamar diyar cikina itama.
Bana son wanan halin da kuke nuna mata a gidan nan to ai mami biyan ta akeyi bata daya damu ai.
Na fada maku ban son hakan da kukeyi nan aikin ta yake tare dani dole kuma ta shigo dakin nan tunda abinda tazo yi ke nan a gidan nan.
Baki Rufaida ta zunburo wai ita an mata fada ni dai ina tsaye ina sauraren su can nace mami da wani abinda zan maki yanzu ne wanka na fito dama ?
Yamm yamm yamm don Allah fita kiba mutane wuri inda aikin ma zan karasa mata shi amebo kawai.
Nidai na juya na fice daga dakin raina bai min dadin hakan ba ko kadan yadda yan matan nan suke min a gidan gashi naga duk da mami na tsawata masu sai dai bata son ransu ya baci ko kadan.
Yanzun na gama waya da yayan ku yana son ya raina min wayau wai ba zai samu zuwa rantsar damu ba da za ayi.
Abinda naji mami tana fada ke nan lokacin da zan fita daga dakin bayan korar da Rufaida tayi min.
Dakina na koma na karasa shirina duk da ba wani shiri bane dan dongon rigar da anty safiya ta sai min sune nake sakawa yanzu saidai naji hjy tana wakan tana son a samu lokaci aje a sai min kaya don tana kunyar wanan kayan da nake sakawa haka.
Ban sa raina ba sai na gani balle zumudin hakan ya hana zuciyana shakat da damuwa na fito na nufi kitchen don samawa cikina abin karyawa.
Ruwan shayi da soyayyen dankalin turawa nagani a cikin kula shina diba na hada tea na dawo inda Larai ke gyara kayan miya na zauna kusa da ita na fara sha ke nan naji muryan Rufaida na kwala min kira da yar aikin hjy don sunan da suke kirana dashi ke nan dashi a gidan in ka debe hjy dake ce min zeey sai su mama kande da suke kirana da zainab.
Amsawa nayi da na,am tana karyawa Larai ta fada yadda zata iya jiyo ta tana karyawa shine ba zata zo ba Rufaida ta fada.
Dole na mike zuwa amsa mata kiran a tsakiyan falo na sameta tsaye ta rike kugu tana jirana a hasale.
Ina zuwa take fadin ke don uban ki zan kiraki kice kina karyawa haba Rufaida wanan zagin fa haka ?
Muryan Anty salma ce dake zaune wurun dinning tana karyawa lokacin ba dole in zage ta ba don daukan kanta take daya damu wanan yarinyar.
Kin san dan kauye bai iya samun wuri ba dama idan yaga ya waye sai yake gani yafi kowa waye wa ki shige dakina kaya na nan na tara a bayi na ki wanke min ta fada tana juyowa inda nake tsaye ina kallon ta da idanuwa da suka ciko da hawaye don zagin da tayi min.
Bazaki tafi yin abinda nasaki bane ta fada cikin tsawa da sauri na juya na nufi hanyar dakin nata don kwaso kayan datace din.
Saurara ta fada naja na tsaya cak wuri guda ina saurarenta kada ki fara ki satar min wani abu a dakin nan don ranki zai baci sosai idan kinyi hakan.
Haba haba hakan baida kyau fa Rufaida and kuma kinsan mami ba zataji dadi ba idan tasan da hakan anty salma tace.
Mami kina nufin banda right din sakata aiki ko warning dinta akan kayana tana yar aiki gidan nan.
Nidai na juya na wuce ina shara hawaye don abu biyu ga zagin dana samu ga kuma zargin sata yanzu.
Dakin na shiga na same shi a ya mutse kamar ba mace ke kwana a cikin sa ba don daki babu gyara ko kadan yadda na ganshi.
Bai da banbanci da dakin da nake bambancin su dai wanan mirrow shi cike yake tab da kayan shefe shafe sai manyan akwatuna dake gefe ajiya ga kuma tv bango babba.
Duk a fakaice na kalli dakin nasan da hakan don wanan ne shigana na farko wani daki daya shifi gidan in kin debe na mami da kullun ina cikin sa.
Mami bata taba ce min wani abu game da dakinta da zanga kudi ko agogo ko sarka da sauran su sai dai in dauka in mayar inda take aje sarka ko agogo kudi kuma zan daga filo in aje mata shi yadda suke.
Ina shiga ban dakin idona ya fara arba da pant din ta saman kayan su rigan nono da bujen ciki kai kaya daine na unders da mace ke sakawa a jikin ta ta tara gudan masu yawa a wurin.
Tattarawa nayi na a bucket din dana gani a bayin nafito tana tsaye tana kokarin cire rigan dake jikinta take fadin ki tsaya ki gyara min daki kafin kije wankin.
Dole ba yadda na iya tunda nazo cin arziki ne gidan su na fara gyaran dakin ita kuma ta shige bayi don yin wanka kafin ma ta fito na gama na bar dakin.
Can baya naje inda ake wanki da sauran aiyuka na wanke na shanya mata tunda wanan ba aiki bane a wurina.
Na gama na dawo na samu ruwan tea di dana aje har yayi sanyi haka na dauka nakarasa shan shi da sanyi.
Fitowa nayi da niyar komawa dakina na samu yan matan gidan zaune da kawayen su a falo zaune.
Zuwa nayi zan wuce ba tare da nayi masu magana ba nakai tsakiyan naji muryan Nazifa na fadin amma wanan yarinyar bata kunya.
Sai duk suka dawo da kallon su wurina wanan wacece yaushe tazo gidan nan cewar wata daga cikin bakin.
Rufaida dake cin chewing gun ta tabe baki tana fadin a kauye mami ta dauko ta .
A hakan mami ta dauko yar aiki wanan wani aiki zata iya kazama da ita haka ga ruwan kauyanci ko ina tare da ita.
Gaba daya suka sa dariya lokaci guda ke zoki gaidasu ki shige salma ta fada a dake ba tare da tayi dariya ba ita.
Nazo gaban su na tsuguna ina gaidasu basu amsa ba sai dayan ke fadin kina gani ta nan idan ta waye sai duk kun girgiza a gidan nan.
Amma dai kin gama damu Laila wanan din ne zamu girgiza don tayi clean .
Oh kina raina irin kauye ke nan ai barsu yadda kika gansu ba wani zancen clean gareta don tana clran aurin nan ba karamin taksici zakuci ba duk wanda ya zo kanta zai tsaya rabu da mutum ka barshi a ranan da yake kawai don idan kace zaka kaishi innuwa shiko yana turaka rana .
Salma ta kalleni cikin takaici tace ba kingaida su ba me kike jira kuma a nan yanzu ?
Sai ta gama jin abinda muke fada mana Rufaida tace tana watsa min harara na mike ba bar wurin ina jin bakin na fadin ke wanan ai idan tayi clean ko yaran gidan nan ba zasu barta ba tana hakama yaya aka kare da suranta duk mai hankali yasan anyi halitta a nan ai.
Ire iren haka yasa nakan shige daki in zaune in dai ba mami ke gida ba dole ina falon don aike ko wani aiki da zan mata.
Yan matan basu bar gidan ba har mami ta dawo daga unguwar data tafi tana shigowa ta samesu a falon gaisawa suka farayi bata ko amsa masu ba ta fara fadin ina wanan yarinyar zeey take ne ?
Sai kawai ta shiga kwala min kira ina cikin daki na kulle kaina naci kuka har na gaji naji an bankado min kofan dakina da karfi .
Haka yasa na dago kai ina kallon mai shigowa dakin lokacin ba kowa bane sai Nazifa ke kina nan zaune to mami tana kiran ki.
Mikewa nayi da sauri ban ko tsaya share fuskana daya gama dan hawa ba saboda kukan da nasha.
Mun iso falin daidai mami ta dauki ruwa zata kurba nake fadin sannu da dawowa mami ta dago kai ta kalleni sai ta furzo da ruwan lokaci guda daga bakin ta.
Gaba daya hankalin kowa ya koma kanta don ganin me ya faru tana fadin zainab mamana kuka kikayi ne ?
Kaina na girgiza mata kafin in ce a a ahankali ina wasa da yatsun hannuna haba bana son inganki cikin damuwa ko kadan.
Shiru ta danyi ta mayar da hankalin ta ga wayan ta kafin tace kwashe kayan nab ki kai min daki.
Na duka na dauki kayan zuwa dakinta kallo ta bini dashi tana fadin na rasa me yake samun wanan yarinyar taki ta sake jiki damu har yanzu.
Cikin ko in kula salma tace mami tambayi yaran ki don su suka bata mata rai suka kirata da yar kauye a gaban ta dazu nasan shi takema kuka dai.
Salma haka take bata shiga harkan kowa kuma bata boye gaskiya fadin shi takeyi komai dacin sa a cikin su.
Amma na fada maku tun randa yarinyar nan tazo kan ku kiyayyeta a gidan nan ko ban fada ba ranan kan mami tayi masu tas a kaina a gaban kowa don sauran ma ashe ba baki bane duk yan gidane suma.
Wanan fadan ne ya kara jawo mi bakin jini a gurin su sosai suka saka kafan wando daya dani dole idan mami bata gidan ina daki ko wurin kande.
Haka kuma bai hanasu sakani aikin wahala da suke gani suna ban ba gashi mami bata zama gida yanzu don shirye shiryen da ake na zuwa rantsar dasu Abuja.
Wanan ya dauke mata hankali daga komai dake faruwa a gidan ba wankin unders ba har tufafin su yanzu suke bani in wanke wai nafi mai wankin gidan iya wankin kaya sufita a cewar su don mugunta kawai.
Ranan ina dakina kwance mami ta kirani kande aka aiko ta kirani nazo da sauri tare da wani na samesu ina zuwa ta nuna mashini tana fadin ka ganta nan duk ita zaka dinkawa kayan .
Kallona tellan yayi yana fadin bari a aunata ke nan da sauri hjy tace tana daga mai hannu ina warning din ka da wanan awon da kukewa mata yana daga cikin aikata alfashan zama koda kuwa namijine dan uwanka ko mace yar uwar mace haramun ne yin hakan.
Hjy za,a kiyaye ya fada yana dan sosa kai tare da dan jin kunyan abinda hjy ta fada mai sai kuma ta dago yana fadin kayab zasu matse ne ko a danyi mata su free ne.
Kafin mami ta bashi amsa na karbe da fadin free nake so kada ya matseni don Allah.
Ji mun yarinya kin san abinda yake nufi ke nan ko ni dai nayi dan murmushi kawai ina dukar da kaina kasa cikin kunya.
Kudi masu yawa taba tella ya tafi yana mata sallama tare da godiya gareta wuri na samu sama kafet din dake tsakiya a daidai inda mami ta dora kafanta tana zauna cikin limtsetsen dogon kujeran falon.
Hjy ta kalleni tayi murmushi kafin tace min wai zee yaushe zaki daina wanan hali naki ga kuja zaki wani zauna a kasa kamar marainiya.
Dama ina son jin wani abu a dangane da rayuwan ki mahaifiyar ki tana da rai ?
A bazata tambayan yazo min da sauri na dago kai na kalli hjy kafin ince tana da rai sai kuma tace mahaifin ki fa ?
Shima yana nan na bata amsa kai tsaye kuma suna tare da babar ki kai na gyada mata wanan karon idanuna yana kawo hawaye.
Yaya akayi suka barki zuwa inda basu sani ba kina matsayin kina ya mace zeey basu gudun ki fada mugun hannu ne ?
Hawaye bakeyi sosai tare da fadin Asabe ne tace sai nazo birni suka hada kai da lantana aka turoni don innan mu na haihuwan yaya mata wai.
Tace idan ba aikatau ba bamu da wani moriya nan gaba tunda aure zamuyi mu barsu gida.
Tauuu ita Asaben ta fadi haka diya mace bata da amfani sai aikatau ta tambaya tana kallona.
Kaina gyada mata alaman eh sai naga tayi wani dan murmushi iya fuska kawai.
Wacece Asabe ta tambaye ni nace kakar mu ce wacce ta haifi Abban mu tare muke zaune gida daya .
Mami tace kuma ita ta haifi Abban naki itace ta haifeshi shida gwaggon habiba subiyu ne yaranta kawai.
Ina ita gwaggon naki take yanzu nace ance tana aure a zaria ne tace ikon Allah zarian nan dai tamu kaina gyada nan ma..
Bata san an kawoki gidan nan bane aiki daga garin ku nace nima ban sani ba mami don tana dadewa bata zo garin mu ba.
Amma ai bata rasa samun labarin an kawo ki kaduna in har yar uwan haihuwan mahaifin kice ta hakika ya kamata acs suzo suga inda kike nawane kaduna da zaria .
Sai ga hawaye nabin idona nace itama yanzu tunda Abba ya auri lantana ba ruwanta da innan mu kuma.
Ikon Allah ita innan taku ina yan uwanta suke nace cikin ancau suke da zama saidai it inna iyayyen ta duk sun rasu kafin mu girma bamu sansu ba.
Tace mahaifin ki kika kwaso da kama ko babar ki nace Asabe kullun in tana fada sai tace wai zubin innan mu kwaso sak.
Kenan ita kika biyo da dirin jikin kin ga ai wata rana nasan zamu hadu da innar take idan ta kawo maki ziyara nan ko ?
Yana da wuya inna tazo nan don Asabe ba zasu bari inna din tazo nan ba don ko zuwa za ayi sai dai Abba yazo kila.
Kina da kanne da kuka fito ciki daya dasu nace mu bakwaine mata innar mu ta haifa shine Asabe ke mata gorin hakan.
Ta auro lantana yanzu na barta da ciki wai za a haifawa Abban mu magajin gida tunda inna ta kasa haifa mai namiji.
Innalillahi hjy ta fada tare da rike baki tana fadin har yanzu akwai irin jahilcin nan ashe ?
Zata kara magana waya ta yai kara ta dauko haka yasa na mayar da hankalina ga tv dake aiki ga falon .
Saiga yan jikokin ta su shigo do basu faye shigowa wurin kakar tasu ba uwarsu ma baifi sau uku na ganta a part din hjy ba.
Daga bayane ma nasan a gida daya suke zaune da ita saidai ita tana nasu bangaren ne daban.
Tunda nazo ban taba taka ko wurin get din gidan ba kullun ina cikin gida idan ma na fito iyakata backyard din gidan inda su mama kande kan zauna da yamma su sha iska.
ZAINAB IDRIS MAKAWA*_
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
🔟
RAYUWA YANA FARUWA WUCEWA YAKE KAMAR BA, AYI BA ALLAH KABAMU IKON AIKATA ALHERI A KWANAKIN DA SUKA RAGEWA MUSULMI BAKI DAYA AMIN, , , , ,
2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU KACAL NE HAKKINA KAFIN KI KARANTA NAGODE, , , ,
Kamar yadda mami ke yawan jana a jiki yanzu na fara sake jiki a gidan mami saidai bada yan matan ta ba dan gara samarin ko a gaban mami zasu sakani wani aiki mami na fada tana komai zan masu shi.
Hakama yau ya kasance kowa na gidan yana falo zaune ana hira ban dade da fitowa falon ba mami ta kirani in dauko mata wani takarda sunan shi kawai ta fada min nace nagane shi na juya da sauri zuwa dauko takardun.
Rufaida ta kalleni tana fadin wanan akwai iya yin tsiya ko ina ta iya karatu balle ta san shi wai ta gane bari ta dauko shirme yau sai na mata tsiya a gidan nan kuwa.
Yo aini tafi min ku kodai bata gane ba ai zata dauko din da kwatace ballema tunda tace ta gane ta gane din ne.
Wani lokaci yarinyar tana bani mamaki sai in manta in mata magana cikin turanci sai kuma ta gane me na fada mata din.
Hajjaju ko dai tayi karatu ne watakila ta danyi boko a can garin su fa yaya jalal ya fada yana dakilan wayar shi.
Sai jamal yace boko for ware kana ganin yarinya yar tipical yar kauye da ita na maganan wani education nan.
Sai gani da saurina nazo har gaban mami ina mika mata takardan mami ta karba tana fadin tau Rufaida dake da ita duk kun kuru yau a gidan nan .
Lah mami ashe kin hakeni kimin tsiya idan na taba maki yar ki ke nan Rufaida ta fada tana dariya kafin ta juyo ta watsa min wani harara.
Oh wellcome my boy jalal ke fada don shigowan jikokin hjy falon rike da takardun makarantar su yaron na zuwa ya fada jikin kanin mahaifin shi da sauri.
Saiga uwarsu a bayan su itama ta shigo falon ashe tare suke tafe har yaran sun fara zuba mami tace oya great us cikin daure fuska.
Take yaran suka fara bin kowa a falon suna gaida su har zasu gaidani Nazifa tayi saurin fadin she is not your aunt .
Nazifa ki fice min a idona akan yarinyar nan kafin rayukan mu yakai ga baci a gidan nan don ba zan lamuci hakan ba.
Jamal ya mike yana fadin ke stop interrupt your self akan wanan yar mami din a gaban ta don yanzu itace da mami baku ba.
Ashe ka gane gaskiya bana son ana raina dan Adam a rayuwana idan ka sanni a da ban kokai zeey wayewa ba kuma a haka mahaifin ku yace sai ni.
Duk aka kwashe da dariya falon wurin Rufaida yarinyar karama ta nufa tana fadin anty ki koya min assigment dina mommy tace bata iya ba.
Karban littafin tayi tana dubawa kafin da namijin ya juyo zuwa gareta shima ta karba tana duba kafin tace wanan sai Nazifa kila don ban gane me ake nufi ba gaskiya.
Wani subject ne Nazifa ta tambaya tace mathematics ne fa wanan ai sai ku Nazifa wace nazifan ta fada tana fadin su dai kaiwa salma ta duba.
Salma dake zaune tana duban wayan ta tace kada ma su haroni don ban iyawa zanyi ba indai maths ne.
Fuska yaran suka bata mami na fadin amma ko kunji kunya ta mika hannu yaran su kawo ta gani .
Ban san lokacin da nace mami barin duba masu ko zan iya ba mami ba kowa dake falon dago kai yayi yana kallona da mamaki.
Ke wanan fa ba tallan goro bane karatune na boko ake fada don kinji mami tace kina daidai da kowa zaki kawo muna rigima.
Ban damu da abunda Nazifa ke fadi na karbi littafin tare da jawo yarinyar a jikina.
Tsayawa nayi tare da nazarin abinda aka basu kafin in fara rubutu duk idanuwan su a kaina yake.
Tiryan tiryan nakewa yarinyar bayani yadda zata gane har muka gama da nata na dago kai ina fadin namijin ya kawo nasa.
Sai lokacin naga kallon mamakin da kowa ke min a falon lokaci guda mami tace dani kinyi boko ne mamana ?
Nayi na bata amsa a hankali duk yan matan mami suka zaro ido waje kinyi boko kike haka kuma a aikatau ?
Ban kulasu ba naci gaba da koyawa yaron assigment bamu dauki lokaci ba na karasa yaron ya dago yana murmushi.
Mami ta mika hannu ta karba da wanda nayi mai musali ya kwashe ciki tana bin rubutu na da kallon mamaki.
Wani maki kika tsaya a karatu ne zeey ta tambaya cikin kureni da idanu tana son jin amsa daga bakina.
Ina ss3 Asabe ta fitar dani da banan nan zan gama karatu tace wai bata ga amfanin boko gun ya mace ba tunda ba namiji nake ba shine karshe ta turo ni nan.
Kowa a falon shiru yayi yana kallon yadda hawaye ke zuba min a idanuna lokaci guda don maganan da nakeyi.
Yanzu kina son karasa karatun ki ko aure zasuyi maki kauye kina da tsayayye acan .
Kai na girgiza tare da fadin banda kowa sai Asabene tace wai zata sama min miji ta hadani dashi.
Kai waiko wanan Asaben ita ta haifi mahaifin ku da cikin ta wanan abinda take gwada maku yayi yawa gaskiya.
Karatun ma da zakiyi ki samu madogara a rayuwan ki saida ta hana kiyin shi gaskiya na tsani wanan matar damai irin halin ta.
Muryan Nuriya matar yaya mubarak ke fadin mami ashe kuma an daga tafiyan ?
Mami ta juyo tana ce mata sun daga kedai kin san abin gwaunatin kasan nan baida tabbas ai yanzu kuma sai dai sun kiramu kuma.
Ai wa yan nan sun kwafsa muna wallahi don kila yaya Jafar ya fasa shigowa kasan nan ke nan sai wani jikon .
Yasan an daga ne mami ta tambaya tana kallon jamal dayayi magana sai jamal din ya juya yana kallon jalal yana dariya.
Kudai kuka sani da tsegumi kamar mata haba mami don mun fada mai an daga ranan shine tsegumi shifa ya tambaye mu muka fada mai gaskiya.
Waya aike ku fada mai da ku barshi sai idan yazo yaji ai ba shike nan ba zai kirani ai zamu gamu dashi ta fada a hasale tana mayar da hankali kan sytem din ta data bude a gaban ta.
Nice ta farkon mikewa a falin bayan Nuriya matar yaya mubarak data ja yaran ta suka koma part din su ba don yaran sun so haka ba don ko shigowan nan nasu don assigment din yaran tashigo har dasu.
Dakina na shiga nabi gadona mai laushi na kwanta ga sanyin A C dana sake ya game dakin sai barci.
Bada masaniya ba mami ta sama min makaranta don inci gaba da karatuna a wani college dake gaba da unguwaelr kadan.
Ranan da dare take fadamin zancen ci gaba da karatun nawa lokacin nema kowa a gidan yasan da zancen cigaban karatuna yanzu.
Wanan yasa yan matan nata kara jin haushina sosai banda daman bin motar su kamar yadda mami tace mu rika tafiya tare da safe idan zan tafi.
Ganin haka ban fadawa mami ba nake takawa da kafa ina zuwa makaranta don nisan shi ai bai kai na kauyen mu dana baro.
Zan tashi da asuba inyiwa mami duk wani abinda nasan nice mai mata shi kafin gari ya haska na karasa zan karya in taka da kafa inje school.
Sam mami bata san da zancen tafiyana da kafa zuwa school ba sai wata rana zata unguwa da safe hakan yasa ta fito da wuri daga dakin ta.
Yan matan ta samu zaune suna karyawa take tambayan ina nake nan suka fara kallon kallo a tsakanin sai salmace take fadin mami wayen garin nan banganta ba ai.
Tafa tafi school Nazifa ta bada amsa sai mami tace usman ne ya kaita ya dawo ya dauke ku sai sukayi shiru don sun san da kafa nake tafiya school duk dadewan nan.
Bana son irin haka sai kuyi kwanciyar ku a daki kuna sharan barci sai lokacin da yai maku dadi zaku fito .
Alhalin kunsan da cewa ita nasu school din ana duka idan an makara ko shi malam usman din yayi ta zaman jiran fitowan ku.
Fada sosai mami tayi masu kafin ta fita can ta hadu dani na kusan shiga school din mu ta tsaya tana tambayana yaya akayi na tako da kafa ?
Nace mami bana sin in makara ana duka idan mun makarane maza shige mota in karasa dake ke baki tsoron wanan titin namu gashi shiru babu kowa a wanan lokacin.
Har ta saukeni fada take min ta bude jakka ta zaro five hundred tana miko min tare da fadin karbi wanan kiyi break dashi don nasan baki tsaya karyawa ba kika fito.
Lah mami wallahi na karya kafjn in fito ki bar kudin don mami bata ban kudi sai dai tace na karya kona dauki abinci inje dashi school din.
Ina kallo ta wuce karfe biyu da yan mintoci na shigo gida har lokacin mami bata dawo daga unguwar da ta tafi ba.
Haka yasa na samu daman samun dan barci rana bayan nayi sallah azahar ban sake fitowa ba duk da yunwan da nake ji don kudin da mami ta ban na kasa kashe su don ban saba da kashin kudi ba.
Ban farka ba sai bayan la,asar wanka nayi lokacin ne naga fashin sallah yazo min don haka nayi wanka kawai na fito na dauki always na kimtsa jikina dashi.
Abinci ya fito dani naga ashe yamma yayi sosai a lokacin haka yasa na gane na dade ina barcin rana yau.
Don na samu har yan university sun dawo suna cin abinci mam kande ne ta dauko kuloli take fadin yau kan yar gidan hjy kin sha barcin rana.
Ba dole tayi barci ba tunda taga arzikin banza wanan irun kune idan kun samu wuri kuke mayar da yan gida daga kofa.
A a saidai tasan wanda zata mayar Nazifa tace tana amsawa Rufaida sai naji salma tace wai ku meye matsalan ku da yarinyar nan don Allah ?
Rufaida tace I just hate her wallahi balle yanzu da take clean sai nake ganin gaskiyan maganan dasu Rubby suka fada ranan a kanta.
Ashe bani kadai ke ganin canzawan yarinyar nan ba tundai wanan kayan da mami ta saka aka dinka mata suna fitar mata da suranta na asali waje.
Zakace badaga kauye take ba har wani tafiyan sallo take tana yanga idan tana magana yanzu.
Kai ku din nan kuna da wani magana wallahi koma dai yaya ta koma kunsan ba zata taba kaiku asali ba dai ko ?
Sallama na fadan haka Nazifa tace yanzu waye ya damu da wani asalin mutum can zamanin nan boko ai mutane basu duban haka idan sunga abinda yai masu .
Dariya sosai salma ta kwashe dashi don dama irin du baka ganin dariyan su sai ta baci ni dai ina diban abincin ina jin cinmutuncin da suke min kala ban tankasu ba.
Saidai na kudurta duk ranan da wata daga cikin su ta kara zagan min uba bazan kyaleta ba sai inda karfina ya kare koda hakan na nufin inbar gidan ne na masan hjy ba zata yarda ba da hakan.
Don takan fada min Zainab ina son in ga na taimakeki kin zama wani a rayuwa ki samu ki taimaki yan uwanki tunda dukan ku matane har ku bakwai .
Shiyasa nake son ki dage ga karatun don wata rana ki taimakawa innan ki da yan uwan ki Asabe tasan diya mata ma diyane abin alfahari kuma.
Ire iren wanan tunanen nakanyi inshanye wani abinda ake min a gidan don kawai manufar mami a kaina don kuma burina ya cika.
Karatuna bai hanani yin abinda nazo yi gidan mami ba har na kai wata shida da zuwa gidan .
Iyakata da anty safiya idan tazo in fito in gaida ita tare da tambayan yayan ta da mijin ta ta bani amsa da suna lafiya suna gaida ke.
Sai kuma ta tambaya injin dai baki wani abin asha zainab kada ki manta da kinzo cin arziki ne a nan don haka kiyi biyayya sosai.
Irin maganan da anty safiya takan min ke nan idan tazo gidan ina nan kafin ta tafi
Gashi banji wani zancen kudin aikatauna ba ga bakin kowa nima kuma ba damuwa dana san komai a kan albashi na nayi ba.
Mun samu hutu makaranta naji mami na fadin ya kamata in je in duba gida tunda su basu neme ni ba har yau.
Don tasan yanzu inna na tacan cikin damuwan halin da nake ciki babu dai yadda zatayi ne ta sawa sarautan Allah ido.
Ban san mami har ta saka ranan zuwana gida ba sai dai tace inje aimin kitso a makwabtan mu don akwai wata yar makarantar mu a gidan kusan tare muke dawowa da ita kullun.
Itama takan zo gidan mu in mata nan yan gidan suka san na iya kitso sosai don har mami nakan wa kitso yanzu tunda ta gane na iya kitso sosai da yan matan ta.
Sai dai bankan so yi masu kitso don muna kitson suna zagina har mu gama.
Washe gari na shiga wurin mami in gaida ita da kwana sai na sameta zaune ta fitar da kayan data dawo daren jiya dasu don nice na kwaso zuwa dakin ta.
Sallama nayi ta dago kai tana fadin yawa samu wuri ki zauna dama yanzu nake da niyar kiran ki sai gaki.
Zama nayi kamar yadda ta umurce ni kafin ta fara fadin kinga wa yan nan turamen ta nuna min su da hannu nace eh mami.
Tace yan uwanki zaki kaiwa su guda shiddane iri daya ne saidai nasa a bambanta kallar su wanan kuma na innan ki ne ta nuna min wasu uku a guri daya.
Sai wanan kiba Sabe daya lantana daya wanan shaddan kuma ki ba mahaifin ki sai sabulai da omo kiba yan uwa da abokan arzikin ku .
Kwana hudy zakiyi ki dawo driver daya kaiki zai dawo ya daukeki ranan ki gaiyar min da innan ki sai wanan ki ba mahaifiyar ki tana miko min wani abu a cikin leda wanan kuma mahaifin ki zaki ba albashin kine na watannin da kikayi a wurin mu na tara maki shine na raba biyu innar ki rabi mahaifin ki rabi.
Kada ki manta ina gaida innar ku kwarai kice na gode sosai sai watarana idan mun hadu.
Hawaye na fara yin a wurin ina tsugune sai mami tace ko kin fasa zuwa gidan ne in aika masu da sakon da sauri nace a, a mami na dai rasa godiyan da zan makine yanzu.
To maza ki tashi ki shiya ga sabbin kayan kinan saman gado sai ki zabi wanda zaki dasu tsufin kuma duk ki hadasu ki kawai kannen ki su karasa su can .
Ko mahaifiyar ki tana sa kwance ki zaba mata wa yan nan dana ware da za a kyautar .
Da gudu nace tana sawa mana mami to jeki ki zabar mata kala biyar daga ciki da sauran tarkacen daya dace ki kai mata .
Na mike don na rasa bakin da zanwa mami godiya don ta hanani yin hakan gareta.
Kayane mai yawa har na rasa wanda zan cirewa inna sai da mami tace ki cire mata zannu da dogon riga zatafi son su ai.
Haka muka dauki hanyar ANCAU da tsaraba taf a bayan mota da zankaiwa iyayyena koma in ce mahaifiyata don itace mai tsaraba da yawa ciki.
Don hjy tafi son inna na fahinta sama da mahaifin mu Abba kodon tana mace yar uwantane ban sani ba.
Malam Usman driver mami bai tsaya ko ina ba dani sai kofar gidan mu tun daga nesa na hango wata na suyar wani abu an baibaiye ta.
Saida muka matso kuss ne na gane saratu ce kanwata ashe ganin mota ya nufo kofan gidan ya kuma ja ya tsaya.
Duk wanda ke wurin ya kurawa motar ido don son ganin kowaye a motar ban fito ba saida na gama dauko kayan dana rike a hannu na fito daga motar.
Saratu zoki kama min kayan nan kin tsaya kina kallona haka muryana kawai ta sheda yasa ta gane ni a lokacin.
Ido ta waro waje tana kallona tare da fadin yayan mu maimakon ta yo wurina sai kawai ta kwasa da gudu tayi cikin gida tana fadin.
Allah mun godema Allah mungodema yau ga yayar mu ta dawo garemu innan mu fito yau Allah ya dawo muna da yar uwarmu gida.
Ashe ba sayar da ita akayi ba a birni ji abinda saratu ke fada yasa sayran kanne fitowa da gudu kafin su ja su tsaya suna ina take ta kwasa tayi hanyan fita suka bita da gudu.
Mun hade dasu a kofan shiga gida sukayo kaina da murnan su da ihu suna jin dadin gani sai ihu sukeyi yayan mu ta dawo yayan mu ta dawo garemu yau.
Jin ihun da yaran gidan suka dauka na murnan zuwana yasa Asabe fitowa daga shiyan ta dan kwali a hannu tana fadin.
Shin Abu Abu kuke fadan tazo ina Abun take ne in ganta tana kokarin wuceni da yan uwana.
Gani nan Asabe na fada ina kokari zuwa wurin ta sai taja baya tana dafe kirji tare da fadin Abuce haka ?
Zonan na ganki na karasa wurin ta sai ta rungumeni tana kuka tana fadin yar nan ina kika shige haka babu duriyan ki har an fara zargina a gari na sayar dake ga yan birni.
Ina gidan hajiyar da kuka kaini tun barina garin nan na da kwana bakwai gun anty kafin ta kaini gidan.
A a ai dada kin dawo garemu ke nab dai yanzu ba komawa wanan birnin kuma dai ta fada tana share hawaye.
Ni dai ban ce mata komai ba sai waige nake ko zanga innar mu ta fito banganta ba yasani sakin Asabe na nufi dakin mu da sauri ina sallama.
Ina shiga da hango ina zaune saman dan gadon dake dakin tayi tagumi ns karasa gareta ta da sauri ina fadin inna gani nazo gare ku yau.
Murmushi inna tayi kawai sai dayan kanwar mu data sawa kira daga dakin a daidai lokacin da yara suka fara shigo da kayana dakin.
Irin surutun da yaran dake shigo da kayana gidane ya sa hankalin lantana dake daki bakin cikin dawowa ya hanata shakat tunda saratu tazo tana ihun na dawo wani tukukin bakin ciki ya sokar mata zuciya.
Don Lantana sam bata so in dawo gidan ba a lokacin don so tayi ace ba bata da gaskiya kamar yadda ta kulla sherin haka har zance yabi gari gaba daya kowa ya dauka hakan ne.
Inna eta bada kudi wai a sayo min ruwan leda nace basai an sayo min ba inna a dai sayawa driver hjy daya kawoni.
Wai wanan mutumin driver ne yanzu saratu ta fada nace drivern gidan hjy ce shi ke kai yaran ta makaranta ya dauko su idan da aike kuma sai a aike shi.
Bawada ya ankara da zuwan lantana daki namu tazo ta tsaya a kofan dakin ta tokare hannayen ta da katon kofan dukka gefe biyu.
Saida ta gama saurarebn mu ta kalleni tsaba ta fara fadin eyya Abuce ta koma haka ?
Gaba daya dakin muka juyo muna kallon ta lokaci guda taci gaba da fadin halan a cikin injin suka sakaki aka wankeki haka.
An maidoki kamar wata karuwan birni koda yake wasan abinda kike a burnin wanan bude idon haka lokaci daya.
Amarya ke nan ai inkiga mutum yayi abu yana da gadon shi ne ban gada ba babu dana da zai taba zina da yardan Allah inna ta bata amsa.
Kinsan aikin mutum sai ya dauka shi kowa keyi ko ina ya samu kansa ni Allah ya tsare mi yata a birni don bata gaji watsar da kai ba.
Kaina yana duke kasa ina tunanen wai yaushe inna ta fara magana haka sai naji lantana na fadin wa kike nufin ya gada to ?
Wanda yasan ana haka har furtawa yata dashi nakeyi abu yaso zama rigima don har saratu taso shiga maganar inna ta kwabe ta.
Andaiyi abin kunya ta fada tana batin kofan dakin don bata zaci innan mu zata bata amsar maganan taba.
A kofa ta hadu da asabe da takawo min zogale data gyara tana shirin ci cewa lantana tayi muna ganin kilibibi a gidan nan.
Ya tadawo yawo tazubar har ake wani riritata don kwadayin duniya muna jin ta a daki nace har yanzu wanan matar tana wanan haukan duk data haihu girma yazo mata yanzu.
Ina girma a nan banda iya shegen data karo cin mutunci dai ne mutum ya guji karshen shi.
Asabe ta shigo da sallaman ta tana aje min kwanon ganye a gaba tana fadin kici yar nan dan ganye na gyara sai gaki.
Saratu takai hannu zata diba takaiwa saratu dundu a baya tana fadin mara kunya ba a ke nakawo ba bakuwa na kawowa.
Sai dana huta nayi sallah kafin malam usman ya aiko wai zai tafi na samu inna ta dan dama fura ta aika mai kafin yayi sallah yasha ga awara da saratu ta cika mai leda dashi har kwan zabbi inna ta aika a nema cikin gari ba a samu dayawa ba hakan ma naji dadi yadda akai mai.
Bayan mun dawo daga rakashi ne na bude kayan don saratu ta ta demeni da tambaya mena kawo masu ?
Tundana fara bude kayan jikin kowa yayi sanyi kafin ma in farawa inna bayani kamar yadda mami tayi min.
Nan dai na labartawa inna rayuwana a gidan hjy saidai na boye mata irin cin fuskan da yan matan hjy kemun a gidan.
Don tsakanin mahaifa da diyan su sai Allah sararu ce ta dauki na Asabe da lantana takai masu nasan don fitina tace itace zata kai.
Lantana ta fara kai ta karbi kayan a tsune tana fadin duk da ance kayan zina kamar kayi zinane kaima.
Amma wanan zani ya shereni ba zan barshi ya tafi ga banza ba tunda a haka aka sameshi.
Saratu tace dadai yafi tunda ba yau aka fara cin kayan zina ba don har na tsohuwa an saba ci cewa da uwar lantana din.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣1️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH KA KAWO MUNA TSARO A KASAR MUNA NIGERIA, KASAWA WANDA IF,TILLA,I YA FARU DASU HAKKURI DA SANIN KADDARA A RAYUWAN SU, , , , , , ,
DARI UKU NE NOVEL DINA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALLAMA YAR UWA DON TURA KUDI GA NOMBA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN KO EIRTEL NA DARI UKKU.
Abba bai shigo gida ba sai gap da magariba ya dawo lokacin ina alwala a tsakar gidan mu dani ya fara arba.
Ja yayi ya tsaya tare da fadin wa nake gani nan kamar Abu ya fada cikkn mamaki don bai san da zuwana ba ashe sai wanan shigowan da yayi ya ganni.
Amsa na bashi ina mikewa a daidai lokacin ina kai dan ruwa a baki kamar yadda yin hakan ya zama min al,ada tun ina gida ba tafi kaduna har yanzu kuma ban daina yin hakan ba idan na idar da alwala don sallah.
Abba nice na fada cikin dan murmushi Abu ina kika shiga haka babu labarin ki ga kowa ita din da tazo ta dauke ki bamu kara jin wani zance a gareta ba har wanan lokaci.
Safiya bata kyauta muna ba ta barmu cikin zargi da fargaba don ba haka mukai alkwari da ita ba.
Ayi hakkuri Abba kasa anty ma,aikaciya ba ko yaushe take da lokacin tafiya ba irin hakan.
Yar mairo koma menene ai ya dace ta dan waiwayo musan halin da ake ciki dake a can .
Yanzu kai ganin ta yasa ka tsaya nan kana zuba har ka mata irin bakin cikin data jefa ku a tafiyan ta .
Lantana ce ke fadawa Abba hakan tare da mika hannu tana fadin ban ledan kafin ka shiga can a wawashe.
Tana mika hannu ta fisgi ledan daga hannun Abba ta juya tana fada abin kunya yarinya taje gantali tsawon wani lokaci saida tagaji don kanta ta dawo har kuna wani jin dadin hakan.
Abba yai tsaye kamar ba Abban dana sani ba yana bin inda tabi da kallo kafin ya juyo har na bar wurun ina kokarin shiga dakin innan mu ko.
Da mamaki a raina yadda naga komai na gidan namu ya kara hargitsewa ga baki daya na tayar da sallah.
Bayan na idar da sallah muka zauna da inna sai lokacin nayi mata bayanin komai a tsanake har sakon mami na dauko na bata na nuna mata na Abban mu da tace a bashi.
Inna tace aidai bata don wanan yarinyar tana kyala ido a kansu sai taga bayan su a lokaci guda.
Nace koma meye ai dai na isar da sako saidai inna nifa wasu abubuwa da nake gani a gidan suna daure min kai tun zuwana.
Me kika gani daya daure maki kai ai dama shi ramin mugunta kurarene idan wanda akewa yayi hakuri.
Bai wuce dai abinda kikaji ba tsakanin umma da lantana ko wanda kika gani yanzu tsakanin ta da mahaifin ki.
Duk waya ja hakan sai umma gashi kuma tun ba,aje ko ina ba abin ya koma tsakanin su yanzu.
Tana ji tana gani ganin danta yana batun gagaran ta a gidan nan tayi fada har ta gaji ta saka ido idan da can tayi mai aure ne don ni a gidan nan, yanzu bani kaida ke ganin bakin cikin ba harda ita.
Shiru jayi ina tunane a raina tare da fadin mai yai zafi tsakanin Asabe da lantana kuma yanzu.
Abba bai shigo dakin inna ba sai bayan sallah isha,i zama yayi muka gaisa na mike na dauko mai sakon shi kamar yadda mami tace in bashi.
Duban kaya yayi yana juyawa tare da fadin ikon Allah duk wanan matar ta bayar a kawo min nace Abba ai mami mutumiyar arzikice.
Zamanta mai kudi baisa ta raina tallaka ba nan dai na gutsura mai dan labarin mami din da aiyukan da nakeyi a gidan.
Abba ya kalli takardan dake hannun shi yana juyawa a hankali kafin ya fara kokarin budewa kudi suka soma zubowa daga cikin takardan yan dubu daya sabbi fil dasu.
Da mamaki yake fadin yahanasu kudine fa matar nan tayo muna sako a cikin takardan nan.
Na amsa da fadin cewa tayi kudin aikina ne in kawo maka da zanzo duban kudin Abba yayi kafin ya juyo ya dubi inna da ko kallon inda yake batayi a lokacin.
Wanan matar wani irin kudine gareta haka yar mairo ko harda wani sana,a kike mata bayan wanan ?
Gaskiya matar kwarai Allah ya hadaki da ita a birni don ba kowa bane zai iya maka hakan .
Mamaki kalaman Abba ya bani don na dauka zai tambaye fiye da hakan sai ga Abba ya buge da fadin in kara kwazo don gaba ta aiko da wanda yafi wanan din yana mikewa.
Malam iya abinda zaka fada mata ke nan dan ka rike kudin da baka tabbatar daga ina suka fito ba kamar yadda matarka ke fadi kullun.
Bana zargin tarbiyan diya na ko kadan don nasan tarbiyan da muka basu tun farko.
Allah yasa a kanshi take don nina tsuke da sakon wanan matar gaba daya hankalina bai kwanta da hakan ba ko kadan.
Abba yana kokarin tura kudin cikin aljihu yake fadin ance kudi kare magana ganin wanan kudin yanzu ya kara tabbatar min da gidan kwarai diyata take.
Bayan fitan Abba a dakin ne yai shiru na dan lokaci kafin mu fara jiyo hayaniyar Abba da Lantana daga kofan ta.
Lantana ba kunya take fadin yau sai dai a rabamu a gidan nan amma wallahi sai ka fada min abinda kajeyi dakin can ranan girkina.
Kinji ko haka muke fama da fitinan su a gidan nan koda shi koda umma don ni ba shiga shirginta nakeyi ba sai ta koma yi da yara yanzu.
Allah yasa har na tafi kada wani matsala ya faru tsakanin mu nace lokacin inna ke tambayan kwana nawa zanyi nace kwana hudu mami tace driver zai dawo ya daukeni.
Ba zan yarda ki koma garin nan ba batare da wani ya biki yaga a inda kike ba koda malam ba zai tafi ba zan hada ki da kawun ki lawal kuje tare.
Inna hakan yayi daidai don mami ma bataji dadin hakan da aka barni ba wanda ya biyo sawuna tunda naje garesu bayan anty safiya data kaini.
Matar kirkine tunda tayi tunanen hakan duk wata uwa ta gari wanan tunane ne zaizo mata a rai.
Yadda za a sake diya mace haka ba tare da wani nata yabi sawunta yaga inda take rayuwana.
Nagodewa Allah daya karba min addua na danake kullun gare ku hankalina bai taba kwaci ba tun bayan tafiyan ki sai dana samu sakon safiya a boye tana min bayanin halin da kike ciki tare da kwantar min da hankalina.
Tun wanan lokacin na falwala ma Allah al,amarin na kara dagewa da addua a gareku sosai.
Mun sha hira ranan don bamuyi barci ba sai da inna ta labarta min abindaya faru tsakanin Asabe da lantana tun bayan haihuwan lantana gidan nan.
Tunda lantana taga ta haifi namiji kamar yadda umma ke muradin haka a kanta shike nan take ganin ta gama da kowa a gidan nan shi kanshi malam gaba daya an rasa gane kanshi yana ganin itace hasken rayuwan shi ita da danta.
Bata yarda kowa ya taba danta a gidan nan dama ga dan bai faye lafiya ba wai yana da ciwon numfashi.
Subbahanallahi gaskiya banganshi ba tunda nazo ai ba zaki ganshi ba don ba barin shi gidan nan takeyi ba wai kada wani ya halaka matashi.
Tunda an fada masu wurin biye biyen bokayen su cewa wai asiri akai mai yazo hakan ba lafiya.
Jin hakan yasa na ra,ya a raina har na koma bazan taba yaron ba in Allah ya yarda .
Me zai kai ki shiga shirmen wanan mara mutuncin barsu ya kare a kan su ranan dai mun dauki lokaci muna tataunawa da inna.
Washe garin kukan yaron Lantana ne ya karade gidan dashi ina mamakin karfin halin inna data ki kulla al,amarin yaron.
Na fito don gaida Asabe da Abba da lantana sai na samu Abba yana tsaye yana rarashin yaron a waje sai tsala ihu yakeyi uwar na shafa mai magani.
Kasa nakai na gaida Abba na juya don gaida Lantana samu nayi tana hararana a wullakance.
Ban damu da hakan ba na fara gaida ita da kwana kafin nnace Abba meke samun shi tun dare nake jin kukan shi.
Kafin Abba ya furta Lantana ta karba da fadin kuka kan ai dole ne tunda an jefe shi bamu da hutu shi wahala ni a wahalce kullun idan dan ruwa ya tabeshi ko sanyi.
An kaishi asibiti na tambaya ina kallon Abba don ban yarda na kalli lantana ba don yadda naji ta fara maganan ke nan zancen innan mu gaskiya ne da take fadin sune suka jefa mata da don ana bakin ciki dashi.
Ina wanan tsohuwar gidan zata bari akaishi asibiti tace ina saka danta wahala ko yaushe yana kashe muna kudi.
Tunda ni ban yarda ta juyani yadda ta saba ba ace uwar miji komai danta keyi da matar shi idon ta na a kai.
Da dai Abba ka daure an kaishi asibitin birni bana kauyen nan ba aji mai zasu fada tunda yana wahala haka.
Tab abu mai wuya ke nan yaya muka kare da asibitin mu ma na nan balle har nawani birni can tunda ansan abinda aka kulla a kai ai ba a bada shawaran haka ba.
Koke don bakya nan ne ai da an sakaki a cikin wanan sherin don ni yanzu na san zamana da kowa a gidan nan ai.
Allah ya sauwaka sannu kaji na fada ina kallon yarin kafin in juya in wuce zuwa lungun Asabe dana sama tana zuba ruwa a buta zata zagaya ban daki.
Ban manta ba don ban yarda na shiga dakin ba a wajen na gaida ita na juyo na dawo dakin mu inda na samu kannena na shirin zuwa makaranta islamiy a lokacin don boko ana hutu.
Na taimaka suka shirya saida suka fice bayan inna ta basu ashirin ashirin din cin masa idan sun tafi.
Don ba ai abin karyawa ba alokacin lantana ce da girki kuma bata dora wanda za a ci din ba don yaron ta da ya kwana yana rigiman dare.
Wanka nayi na shirya cikin wani dogon rigan atamfa dinkin shi mai kyau ya dan matseni kadan .
Inna sai fadi takeyi mai za,a sayo min in karya dashi nake cewa ta bari a gyara dumame shi zanci don kada in takurawa rayuwan inna din.
Sai ga Abba ma ya shigo gida da leda biyu ya tsaya daga tsakar gida yana sa min kira na amsa na fito ya miko min ledan ya tafi da daya dakin Lantana.
Kosai ne da bread sai kayan shayi a ciki dana bude nake fadin inna ga kosai din ki diba ki karya da bread din don ni ba zan sha ba.
Nace bazan sha shayi ba inna dan dama kosai din zanci sai inna tace daidai ki sha abin ki mu in da sabo mun saba da wanan ai a gidan nan.
Inna tunda ga kudi a hannun ki me zai hana ku sai abinci rabi kuma sai ki juya shi kina dan sana,a dashi.
Shawaran da nayi ke nan a zuciyana Allah ne ya dubemu ya jefoki a lokacin da muke cikin bukata hakan.
Amma malam ya canza yanzu gaba daya a gaban kowa gari zai waye zai fita ya samowa matar shi abin karyawa muna kallo a gidan nan.
Inna ki daina damuwa da wanan tunda ubangiji yana kawo maki mafita da zaki duba diyan ki ki basu abinda zasuci.
Ire iren hiran da muke tayi ke nan a dakin inda na tillasawa innan mu sai data karya kafin yaran ta su dawo su hana taci tunda nasan tana son sha itama.
Karfe goma suka dawo gida da shigowan su abinci suka fara nema a gida suka samu ba a gyara ba zasu ci shi hakana da sanyi na basu kudi suka sayo taliya saratu ta dafa kowa yaci.
Na zaga wurin yan uwa da abokan arziki irin matan da nai sabo dasu ina masu kitso kafin tafiyana kaduna.
Har ya saura kwana daya ya rage min duk da zaman gidan namu babu dadi amma nake ji kamar kada in koma kadunan kuma.
Inna ta danyi kokatin ta sosai wurin yiwa hjy tsaraba irin na kauyen mu da zankai wasu mami din.
Washe gari karfe goma driver yazo daukana inna taso muje tare da kawuna kaninta yaga inda nake saidai anyi rashin sa, a kawun nawa yana da uzuri a ranan don haka muka dauki hanya dagani sai malam usman driver gidan mami a motar..
Tunda muka tunda muka tun karo gifan naga wasu canji a cikin dan kwana hudun da nayi bana garin.
Ni dai sai bin ko ina nake da kallon da mamaki a raina don ganin bakin fuskokin dake gidan namu tun daga get har zuwa cikin gidan.
Na fito daga cikin motar tare da dora hijjabi da kyau a kaina na nufi hanya shiga gida don na tsaya daukan kayana malam usman yace za a shigo min dasu ciki.
Da sallama a bakina na shigo falon sai dai abinda nayi arba dashi ne yasa gabana faduwa don ganin mutane a falon gidan kusan kowa na gidan yana falo ga bakin fuska.
Wa nake gani kamar diyan mami haka muryan mami ya dawo dani daga tunanen dana fara a lokacin.
Da dan gudu na karasa na fada jikin mami data ware min hannayen ta alaman inzo gare ta a lokacin.
Kai kai kai mamana me innar taki ta baki haka cikin kwana biyu kika kara kiba haka kinyi wani fresh dake mami ke fadi.
Tsuki yaya jamal yaja yana fadin ko dai ta kara kauyanci ji wanan bindata saka don Allah da cewa hijjab din jikina wai.
No dan Allah malam usman bace muna da wanan kayan kazantan wurin nan ka shiga dashi wurin kande suna kice cewar Rufaida dake nufin a kauce masu da kayana a wurin.
Malam usman dake shirin aje kayan ya dauka da sauri ya nufi hanyar kitchen dasu na dago ina fadin ban jakkana in kai daki bayan mun gama gaisawa da mami ban kalli kowa a falon ba.
Jeki kai ki fito ki ci abinci wai ai kunsha tafiya don wurin bai kasa ba akwai dan nisa da kaduna.
Shiyasa nace malam usman yayi sakko yaje ya dauko ki don ku dawo da wuri bana son tafiyan dare.
Na dauki kayana zan shige naji muryar yaya jalal na fadin baki iya gaisuwa bane ke idan kin samu mutane ?
Ke tafi ki aje kayan daki ki dawo mami tace haka yasa ban tsaya sauraren shi ba don bin umurnin mami din.
Na kai kayan na dan dade ban fito ba azatona bakin zasu tafi kafin lokacin sai dai har na fito suna nan a inda suke sai lokacin na gaidasu sai dai sun ragewa a fLin don ko su yaya Jamal basa falon yanzu.
Abinci na diba kamar yadda mami ta umurce ni na koma dakina ban kara fitowa ba sai dare bayan nayi sallah isha, .
Don na kwanta ina tunanen gida ina tuna innar mu da na dan saba zama da ita a yan kwanakin danayi a can gida sai nake ji kewan su na damuna yanzu.
Hjy na samu a falo kishigide saman kujera sai wani matashi dake zaune kasan kafet dake tsakiyan falo.
Ya mike kafafuwan shi sambala sabala tare da dora daya saman daya kanshi yana daidai cinyar hajiya.
Suna hira a cikin natsuwa su biyune kadai a falon, kowa yagan su zasu bashi sha, awa alokacin.
Ni dai kallo daya na iya masu na kawar da idona garesu don kyawon mutumin da kwarjini ga zati da Allah yai mashi kamar shiyayi kanshi.
Da ina ganin kyawon su yaya jamal kamar su sukai kansu gasu da iya kwalliya da tsabta shiyasa zaginsu gareni bai damuna da sukece min yar kauye amma sai ganin wanan ya dushe duk kyaun da suke dashi a idona yanzu.
Zeey ga yayan ku yayan su jamal jiya yazo sai kanwarshi da tazo ranan da kika tafi.
Sannu da zuwa yaya ya hanya nace mai ina dan rusunnawa don bashi girma da Allah ya bashi a kaina.
Fuska a sake ya amsa min gaisuwa bazakace bakin shi na motsi ba yadda yake magana da hausarshi da baya fita da kyau.
Daga haka na mike don barin wurin ina tafiya a harde don rudewa da nayi don ban taba ganin mutum yai min kwarjini irin haka ba a idona.
Muryan mami naji tana fadin zeey dauko ma yayan ki abinci nan yaci yau a kasa yake so ci yace don kiuya.
Taci gaba da fadin ki dauko har dani don nima din kiuyan nake ji sosai in samu inci in shige daki duk na gaji yau munyi yawo sosai yau.
Kulolin abincin dana gani a jere sabbi fil dasu wanda ban taba ganin irin su ba a idona don kyau.
Saida na dauko na karshe zan kawo naji karan bude kofa a part din mu wata matashiyan budurwace ta fito daga dakin dake kusa da nawa tana fadin.
Mami na dauka baku dawo ba har yanzu naga yanzu is aftre eight ashe kun dawo sannun ku da zuwa ta fada fuska a sake.
Mun dawo mami ta bata amsa lokacin da budurwan ke zama kusa da na zaune a kasa tana fadin bros yau kaga kd ke nan ashe ?
Yamutsa fuska yayi yana fadin mami ta kaini gurin yan uwanta dana daddy har na gaji a cikin turanci suke maganan wanda ba ko wani abin nake ganewa ba saboda kwarewan su da yaren.
Ina wuni nace mata da hausa ina durkushe kasa a lokacin lfy ta fada tana kallona kafin ta juya wurin mami tana fadin who is she mami ?
Zainab ke nan da nake fada maki tayi tafiya yarinyar da nake zama da ita yanzu wace gwaggon safiya ta kawo min yar uwar safiya din ce.
Oh itace she look quit ai ba kamar yadda su Rufaida ke fada ba a kanta mami tace rabu da yan rainin wayau kawai ban san me yarinyar nan ta tare masu ba gidan nan.
Mami me za a zuba maki na tambaya sai ta dago tana fadin fara zuba mai shi da baison cin abinci sai shiririta ya saba da abincin su na shirme can.
Lokacin ne na saci kallon shi na fara bude kulolin abincin ina son tambayan shi abinda zan zuba mai kuma ina jin tsoron ko bai iya hausa ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣2️⃣
ALHERIN ALLAH YA CIN MAKU MASOYA A DUK INDA KUKE A FADIN DUNIYAR NAN ALLAHUMA AMIN ALLAH.
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA DAUKAN NAUYIN HAKKIN WANI A KANKI BA.
Nidai na kula tun dawowana kowa ke walwala ga yawan bakin dake ta zuwa gidan babu wanda zan dan tambaya ko meke faru a gidan haka.
Naga kowa na gidan yazo ga kuma baki daketa zuwa daga ban garori daban daban sai gidan ya cika da baki sosai.
Wurin kande naje ina tambayan ta abinda ke faruwa take fada min ai zancen hjy ne ya tabbata za, a tafi Abuja a rantsar dasu.
Itace a jahar kaduna wace ta samu mukamin sai wasu daga sauran jahohin kasan nan kafin in furta wani abu larai take fadin.
Wai mukamin me hjy ta samu hakane wanan cikar da akeyi gidan nan haka mama kande tace waya sani yar nan su dai suka san abinsu can.
Shigowan anty safiya kitchen din tare da yar uwarta yasa muka katse hiran da mukeyi muka shiga gaidasu da zuwa.
A, a ke yaushe kika dawo me tafiya babu sallama koda yake baki da laifin hjy ta fada min komai daga baya.
Tana magana take karasawa cikin kitchen din tare da fadin kande zamu kawo maki wasu yan aikin da zasu kwana biyu suna aiki tare daku a gidan nan don aiki zai maku yawa ku biyun nan yanzu.
Duk da dai maza da matane zasu zo din ba lalai bane ma ku taba masu aikin su sai dai idan suna nema wani abu zaku iya basu.
Iyakar ku ke da larai shine zaku taimaka muna wurin bawa ko wani bako abinci idan an gama daga na karyawa har zuwa dare.
Ta juya tana fadin ke naji hjy tana neman ki tun dazun ashe kina nan gurin su kande.
Da sauri na mike zuwa wurin kiran da ake min na barsu kitchen din dasu kande tana masu bayani .
Cikan da gidan yayi a lokacin yasa na fara dan rabe rabe har na isa wurin hjy din dake dakin ta tare da wasu jiga jigan mata farare tas kamar ta sai dai sunfi hjy jiki da tsayi sosai.
Haka na rabasu har nakai wurin hjy nake fadin mami gani ance kina kirana ina kitchen wurin su mama kande ne.
Tace yawa zee wanan kawar tawace ke son kitso sai kuma Autana da naji tana tambayana ke dazun din.
Kallon matar data nuna min zanwa kitso nayi ina fadin yanzun zamuyi mama naji dayan race kai hjy wanan yar taki tayi min kyau wallahi.
Kafin daya tace hjy maria ke nan kedai diya mata suna burgeki tace wallahi naso dai in haifi mace kamar yadda hjy iyami ta rufe da ya mace bayan maza amma ban samu ba.
A raina nace duniya ke nan wasu na gudun mata wasu kuma suna son su kowa da irin bukatan shi duniyan nan.
Nidai ganin dukkan su manyan matane yasa na juya da sauri na bar dakin tun kan ta bani amsa lokacin da zan mata kitso.
Ina fita daga dakin mami dakin Anty Nuriya na shiga daga kofa na tsaya ina sallama kafin ta ban amsa in shigo.
Dakin yana da dan duhu ba haske sosai a lokacin tana kwance saman gadon ta makale da waya a kunnen ta.
Anty ina kwana na fada tare da dan rusunnawa kadan ta amsa min da fadin ina zuwa please taci gaba da wayan da takeyi abinta.
A hankali na juya zan bar dakin don ganin ta shagala ga waya naji tana fadin ki dan jirani please kayan da zan tafi dasu Abuja nake son ki shirya min.
A raina nace masu duniya ke nan kayan ma sai wani ya shirya mashi idan Allah ya ba wasu sai su manta kowa ma rai gare shi ai.
Dole naja na tsaya din ta gama wayan ta juyo tana kallona tare da fadin yawa tun dazun nake neman ki ai mami tace kina cikin gida.
Ina gun mama kande na bata amsa tace dama kayan da zan tafi dasu ne nake son ki shirya min su don ba wani dadewa zamuyi a can ba bai wuce ki saka min kala biyar ko hudu ba.
Nuna min jakka da zan saka mata kayan nayi na nufi wurin tare da tambayanta a ina kayan suke ?
Bude wanan drower suna ciki na zaba yadda tace hakan nayi na bude kayana daga sama har kasan wardrobe din.
Kinga na tsakiya din nan sune ban taba amfani dasu ba a ciki so ki dinga daga min dinkin su ina gani ko zanga wanda yayi min.
Bani da zabi sai yadda tace din na shiga daga mata kayan kamar yadda ta umurceni idan na daga wanda yai mata zatace muga wanan ta dan mike ta gwada a jikin ta idan kuma na dauko wani tace No bar wanan miko wancan da nake gani.
A haka har muka zabi kalla hudu zuwa biyar na gyarasu na saka mata a dan karamin troler na tafiya mai masifan kyau.
Na gyara sauran na juya don barin dakin take fadin kinga kwaso dagayen rigunan can mu gani.
Sai naji raina ya baci don dai ba wani gitma na tayi ba kila amma ta kafeni da aiki haka ba wani aiki ba.
Na nufi wirun kayan tare da kwaso mata ina dagawa take fadin aje wanan nan ko jefa wancan can har muka gama ta sake nuna min wanda zan mayar na nafe na marya inda suke.
Na juyo in kwashi sauran don in mayar take fadin wa yanan ki kwasa ina ganin ai zasuyi maki wanda naje dasu school ne wanan time wani ma sau daya nayi amfani dashi.
Ikon Allah ashe shi yasa ubangiji yace idan zakayi kayi don Allah idan zaka bari kabari don sa.
Nagodewa Allah da ban nuna komai ba duk da raina ya baci amma na tsaya nayi mata abinda take so a dakin.
Don kayana na yayan wani da wance masu tsada da kyau sun fi kalla goma wai duk ni kadai keda su tace min.
Na juya kaina a sunkuye ina fadin nagodd tace kai haba dai da baki nan ma ai duk a nan zan barsu saida hjy ta bayar dasu ga wanda take so.
Jin dadin kyautan yasa na ranan harda dakin ta na gyara mata da zuciya daya sai dai ta dawo ta samu dakin a gyara na gyara mata ko ina.
Nayiwa kawar mami kitso haka yaja hankalin sauran matan suke ta kwadayin in masu suma sai naji mami tace su bari a dawo Abuja don tare dani zata tafi.
Wani dadi naji sosai a raina jin mami tace dani za a tafi abuja din garin da nake jin labarin shi yau gani zan tafi cikin sa duk da nasan ba fita zanyi ko ina ba amma dai zan karasa ince ai na taba zuwa.
Tun da naji na fara shiri nima duk da naji Nuriya ta fadi ba dadewa za ayi a can ba nima kaya kala biyar na zaba daga cikin wa yanda ta bani ranan.
Naso sai na nunawa mami kafin inyi amfani dasu hakan bai samu ba don busy da mami take a ranan .
Bata da lokacin kowa har kanta ma da tashigo zata fice daga gidan ko ace ana mata sallama.
Sai ya kasance ina daki ko ina wurin su mama kande sai idan zanwa mami din wani abinda ya shafi rayuwan ta za a kirani.
Dan taron da akayi a dan kwana biyun dana dawo kauyen mu a gidan mami yasa na koyi wasu abubuwa da dama a furin jama,an da suka cika gidan.
Su kansu yan mata gidan mami suna ta kansu ne yanzu kowa na shirin tafiya saidai na kula cewa kamar ba wani shiri tsakanin su da yar mami din Nuriya don ban faye ganin su a tare ba.
Ko banza duk tafisu aji da kyau sosai ga wayewa da tsari don ko maganan ta abin koyone.
Washe garine za ai tafiyan inda wasu zasubi jirgi wasu kuma a mota zasu tafi inda ina cikin wa yanda zasubi mota da farko.
Amma mami tana duba list din lokacin ina dakin take fadin ban yarda abar zeey nan ba idan mun isa can waye zai kula damu kafin su iso sai dai a cire sunan wani a sakata cikin tawagan da zamu tafi.
Wayyo Allah na ashe in Allah yasoka tsuntuwa yake maga ko a dakin ka yau nice wai zan shiga jirgi tunda mami ta furta ai kamar na shiga ne in Allah ya nufa.
Karfe shidda yai muna a filin jirgi ranan nasha zagi gun yan matan mami don tafiyan nan da mami tayi dani a jirgi tare da kawayen ta da yaranta dama wasu daga cikin dangin su.
Koda muka isa can motoci muka samu sunzo daukan mu nidai basai na fada ba don bakauya na koma a cikin duk da dai kowa yana harkan gaban shine.
Amma hakan bai hana tsaraguwa ba a cikin su da rakubewa a guri daya tunda ba wanda ya sanni ko nasan shi sai mami da yaran ta sukuma bata kaina sukeyi ba.
Duk da akwai yan aiki irina kalian da wasu sukazo dasu daga wasu wurare sai dai hakan baisa na mamesu ba ina falo ko da yaushe don kada mami ta nemeni ban kusa kamar yadda naji ta fada kafin muzo.
Haka komai ke tafiya a tsare kamar yadda suka tsara abinsu gwanin ban sha,awa sai kallon mamaki nakeyi maza da mata ana ta cudanya a guri daya ba wanda ya damu da hakan .
Da kauyen mune ai da hakan ya zama abin magana a gurin mutana amma nan ba wanda ya damu da hakan .
Wai washe garine za ayi rantsuwar su mami din tunda muka iso wasu maza sukazo gidan suka fita tare da mami da yaranta manyan mazan biyu.
Haka yasa kadaicin rashin gabnin su mami a gidan ya dameni na dawo katon falon na zauna tare da wasu mata suna ta hiran su nidai sai sani lokaci nake dan jin hiran da sukeyi din.
Ina kallon duk mai shiga da fita don na jawo kofan da muka sauka a cikin hikima na zare key din kofan ina ji daga inda naje zaune ana tambaya na kyalesu.
Don ba wanda zai daukacewa nice na kulle kofan sai dai da mutum yazo ya murda yaji a rufe kofan yake ya juya inda ya fito.
Har masu tafiya a mota suka iso gidan ya kara rikicewa da hayaniyar jamma, a haka yasa na fito daga cikin falon na dawo waje na zauna.
Balle tun isowar ya matan suke aika min harara da warning ya karasa na gudo daka ciki na dawo wajen gidan.
Nan ma motocine ke faman shige da fice tun ina aunawa a raina ince wanan yafi kyau a, a ta dazun tafi har na gaji na zubawa sarautan Allah ido.
Can naga dawowan su mami hakan yasani mikewa tsaye daga inda nake zaune ina kallo na nufo wurin motar nasu.
Sannu da zuwa mami na fada daga bayan ta hankalin ta naga daddy su siyama jikokin ta suna magana.
Hakan bai hana mami dan juyowa tana amsa min gaisuwan ba ta juya taci gaba da maganan da sukeyi na juya zan bar wurin .
Sai kuma ta juyo tana fadin zeey karbi jakkan nan nawa ki rike min nazo da sauri na karba na ja dan nisa dasu na tsaya.
Sun dan gama magana ta fara tafiya yana biye da ita yana fadin amma mami sai naga kamar dai bayanin farkon nan shine shawaran bi koda yake barin gashi Jafar din duk da ban san inda ya shiga ba.
Kuje kuyi shawara dai zan dan shiga inyi sallah kafin wani abu ya dauke min hankali kuma ta fada ta fara tafiya makarrabanta suka biyo bayan ta ruuuu dasu.
Nima binsu nayi da kallo ina mamaki duk wanan taron haka don mami akayi shi haka ?
Naji tace on Allah ku bari inyi sallah yanzu zan fito ta nufi kofan dakin da nake zaton shine nata wanda na riga dana rufe tunda na fahinci hakan.
Mami ai kofan a rufe yake wata ke fadi daga gefenta lokacin da hjy ta murda kofan dakin da zuman shiga dakin..
Tun dazun ai dakin yana rufe an rasa inda key din yake da dan mamaki ta tsaya tana juyowa kafin na karso ina fadin ga key din mami a hannu nice na rufo kofan dazun.
Ok zeey key din yana hannun ki ashe thank god wallahi yarinyar kirki shaf na manta da zan fita in rufo dakin.
Da sauri na ciro a cikin aljihun dogon rigan dake jikina tunda ta dan jaye wurin na gane nufin ta na isa da sauri ina bude kofan.
Juyawa mami tayi tana fadin don Allah a dan jirani in fito tasa kai tsshiga tana fadin zeey shigo ki hada min wanan maganin nabi bayan ta muna shiga tace don Allah rufo kofan nan in huta hakana.
Ki duba akwai magani a cikin jakka ban samu shaba da safe na fita take fadi tana shiga bandakin.
Maganin na dauko daga cikin jakkata don nasan shi na saba hada mata na balla daidai yadda take sha na dauko goran ruwa mara sanyi dake dakin na a je akusa.
Daidai tana fitowa ne ake buga kofan taja tsuki tare da fadin mutanen nan idan nabita nasu bana samun sallah ko azahar ban samu yiba yau balle la,asar ga lokaci na shigewa.
Dukan kofan da aka karayi da karfi take fadin wai waye zeey bude kofan idan maishi ya shigo yaga ina sallah dole yajira idan zai iya.
Kofan na nufa na bude daga ciki aka turo ana fadin haba mami kin fita tun safe kin dawo kuma kin shige kin rufe kofa.
Aisha yar mami ke magana tana shigowa dakin a cikin shagwaba idon ta ya sauka kan mami dake kabara sallah kafin ta juyo tana kallona tana fadin.
Tare kuka fita ke nan da mami din kai na girgiza bakina kuma na fadin ina nan gida ina falo zaune na bata amsa.
Wuri ta samu ta zauna tana maida hankalin ta furin wayan ta yayin da na shiga gyara dakin don wanan daman na samu a yanzu tun zuwan mu garin..
Har mami ta idar da sallolin dake kanta ta juyo tana fadi Esha ya akayi ne wai ma kunci abinci kuwa ?
Zeey kinci abinci ita dai wanan din nasan halin ta balle yau taga wanan taron haka a gidan nan ?
Kaina girgiza daga inda nake tsaye ba tare da nayi magana ba kina jiran me wanan yarinyar da gidanci kike wallahi ga abinci nan ki tambayi safiya mana tunda ta iso idan baki san wanda zaki tambaya anan.
Waya ta dauko ta kira wani layi aka dauko ku kawo min abinci na mutum uku a hada komai a ciki ta fada.
Tana kashe wayan tare da jan tsoki kafin Aisha ta ce mami gobe fa ni dinner kawai zan yi attending.
Kina haukane gaba dayan ku da tan uwaki zamu tafi don duniya ta san ku ta fada sai yarinyar tace but mami kinsa, , ,
Hannu ta daga tare da fadin ban son korafi idan na fada kinsan iyakar maganata ke nan aka turo kofa wace ta kirane dauke da abincin wata hamshakiyar hajiya zakace ba zatai bara gidan kowa ba don bunkasanta sai gata itacs mai kasowa mami abincin .
Bayan ta aje suka dan tsaya magana da mami nidai duk sai naji na takura a cikin su don Aisha ita tana dawainiya ne da wayanta bata ma saurareb su.
Can mami ta juyo tana fadin zeey zuba muna abincin muci ko ?
Matar ta juyo tana kallon daidai lokacin dana tashi tana fadin wanan yar ina kika samotane don ban santa ba gaskiya.
Yata ce ta bata amsa kai tsaye tana jawo plate din abincin dana aje mata a gabanta inda ta idar da sallah.
Kije ki lissafa min matan nan da suka zo da yamman nan za a kaisu masaukin su idan sunci abinci tafadawa matar.
Yan kaduna ko na wani gari eh toh zaki iya lissafo min group group daga nan ki kiramin safiya tazo.
An gama hjy ta fada tana fita daga dakin Esha aje wayan nan ki dauki abincin nan kici ta fadawa yarta.
Ke kuma zuba naki idan kina zama da yunwa zaki jawa kanki matsala ba ruwana tana kai abinci a bakin ta.
Zuba wanda nasan zai isheni nayi na dauka zan fita daga dakin take fadin ina kuma zaki dawo ki zauna muci a nan .
Aka turo kofan yaya Mamud ne daddy su siyama ya shigo dakin da sallama ta karba mai tare da fadin har kun dawo ke nan yace .
Eh mami an samu inda ya dace saidai kudin kusan duk dayana ne ma mamud kasan kudi ba matsala bane ai a dai samu inda ya kamata din shine abu yanzu.
An samu mami kuma danki yace a tura mai ko nawa ne kudin zai biya munyi waya dashi ban samu ganin shi ba.
Ai da ya barshi tunda akwai kudi a hannu na don gwaunati ta bamu dan kudi a hannun mu ai.
Sun dade a dakin suna magana shigowan anty safiiya dakin yasa yafita ni dai ins zaune cikin su a tsawale.
Bayan na gama na fito na barsu tare da anty safiya din suna magana kayan abincin na kwasa nakai kitchen inda ake tarawa.
Nafito da zuman komawa falo in zauna muka hade da anty Rufaida wani irin shock naji lokaci guda saida na dan ja baya don tsoro.
Yar iska masuwa mutane asiri kin dauka ba wanda yasan abinda kukewa mami daga ke har wace ta kawo kine gidan.
Mu zuba dake a gidan nan ki gani idan zaki sha ruwa ya fada maki a ginan nan bakince kun iya mallake mutane ba ku.
Duk da ban gama fahintar inda zancen ta ya nufa ba na dan gane wani bangare na zancen nata kadan.
Tana fadin haka ta juya tabar wurin ba anty rufaida ba gaba dayan su yan kaduna dana sani a gidan wani kallo na kyamata suke bina dashi .
Na kulla da hakan ne idan sun hangoni sai inga suna kallona ana gulmata ma,ana dai sun sani a baki sun tsargeni ke nan a yanzu.
Wanda bansan wanan dalilin ba kuma banda wanda zaimin bayanin hakan sai kawai na fara kama kaina da kowa fiye da dacan baya dan dama anty salma idan mun hadu ba wanan kallon raini ko wullakanci sai dai idan na gaishe tace zeey din mami ke nan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAN UWA FATAN ALHERI A GAREKU KO DA YAUSHE UBANGIJI YASA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA YA TSARE YA KARE MUNA IMANIN MU A DUK INDA MUKE AMIN.
YAR UWA KADA KI DAUKI HAKKIN WANI KARAMIN ABUNE KI GUJI CIN HAKKIN DA DAUKAN ALHAKI WASU MAI IMANI A ZUCIYA TA GANE MAI NAKE NUFI NAN KIWA KAN KI DA KANKI HISSABIN IMANIN KI TUN A DUNIYA.
DARI UKU NE NOVEL KI BIYA KI KARANTA CIKIN SALAMAN UBANGIJI BA TARE DA NAUYI KOWA BA A KANKI, , , , ,
Yau gidan ga baki daya ya kicime da shirin fita zuwa wurin taro duk da tun cikin dare an kwashe baki a gidan an kaisu hotel din da aka kamawa mutane.
Hakan bai hana gidan cika ba da wa yanda suka kwana a gidan basu samu zuwa hotel ba din mutane sunzo da yawa sosai.
Ban bar dakin mami ba tunda safe dana shiga don a falo na kwanta abina bayan na gama yiwa mami duk wani abinda zan mata a lokacin.
Tunda asuba kuma na tashi na yi sallah ko alwala a famfon dana gani wajen gidan na fita nayi alwala duk wanda ya wuce a cikin mazan dake haraman zuwa sallah asuba sai ya dan kalleni.
Nidai na gama na shigo ciki na shimfida dan kwalina nayi sallah daga gefen da mutane ke bi a lokacin.
Na idar na dan dade zaune gurin ina kallon masu shige da fice ina dakon mami ta idar don nasan a lokacin tana saman salayan ta tana zikiri ga ubangjin talikai don wanan dabi,an mami ce hakan.
Can na daidaici ta gama a lokacin na mike zuwa dakin don shine aikina kuma don shi akazo dani watau kula da al,amarin mami din.
Sai kuma yanzu da nakan dan wa yarta wasu hidima a gidan don bata da damuwa ko ci fuska gata bata shiga lamarin kowa halin su yana yanayi dana anty salma itama saidai salman wani lokaci zumace ita ga zaki ga harbi idan halinta ya tashi.
Da sallama na tura kofan na shiga sai dai nayi mamakin ganin su yaya mamud a dakin lokacin shida wanan bakon danta da yazo.
Da gani wani maganan suri suke a tsakanin su a lokacin hakan yasa na juya da sauri zan bar dakin har su fita don ban san shigarsu ba lokacin sai ganin su nayi kawai a dakin.
Muryan mami ke fadin shigo mana zeey ina kika shiga ne tun jiya da dare ban sakaki a ido ba na dauka nan zaki kwana ai tunda dakunan duk akwai mutane.
Yaya mamud ya juyo yana kallo na shiko dayan ko dago kai baiyi ba ya kalli inda nake na fara takowa ina fadin.
Falo na kwana mami na bata amsa kai tsaye kafin in karasa shiga dakin na durkusa har kasa gaban ta yadda na saba gaida ita kafi in jiyo i gaidasu daya bayan daya na mike.
Kada ki sake kwana a falo baki gudun sanyi ya kamaki ne ko wani abu ya sameki nan.
Nace mami akwai wa yanda muka kwana dasu ai koma dai menene amana kike a gareni ta fada ta juya tana fadin mamud kana da son gardama.
Nikan nasa kai na shige ban daki don in fara gyara nan kafin su gama su fuce in gyara dakin ga baki daya.
Har na gama da bandakin na fito suna cikin dakin basu fita ba haka yasa na koma falo na zauna har su fita .
Ina nan zaune falon saiga Rufaida ta fito daga dakin da suka kwana tana ganina tace yauwa ke zo nan ki dibo muna ruwa a waje.
Tashi nayi na karbi bucker din a hannun ta na nufi hanya tana fadin kiyi sauri don gaba daya dakin zaki debo muna ruwa muyi wanka.
Ni dai na tafi bance komai ba na diba a mayawa na uku ne na samu masu aikin break fast suna wanke kayan miya dole na tsaya jiran su.
Don gaba daya ruwan gidan ya tsaya ba,a san dalilin haka ba sai ga Rufaida ta fito tana fadi ke karamar yar iska ko ?
Tun dazun ki debowa mutane ruwa kin tsaya iskanci dama ai tsiyan matsiyata ke nan basu iya samun arziki ba sai su ganshi a banza.
Excuse me ya fada daga baya ta inda take tsaye da hannuwa saman west din ta sai masifa take dani ni kuma na juyo ina fadin nba tsayawa nayi ba wa yan nan na sama suna aiki wurin.
Maza ki debowa mutane ruwa ko ranki ya baci shine taji ana ce mata excuse me ta dan juya don jin muryan wanda tayi a bayan ta.
Da sauri ta jaye mai a hanyar da tai banga banga tana masifa dani daga saman step din.
Wurin security din shi ya nufa yana saye da farar jallabiya kal mai sulbi a jikin sai kamshi ke tashi har inda muke saida kamshi yakai ga hancin mu.
Jin ta gaida shi bai aksa ba ya wuce ina jin matan dake wurin na fadin wanan duk cikin diyan hjy yafisu kyau da kwarji saidai shi din miskilin karshe ne sosai.
Sai lokacin na dago kai na dan saci kallon shi kafin in koma kallon Rufaida data suma a tsaye wurin da take kan kallon shi.
Dauko ruwan da ta farga nayi harna zo gabanta ina jin tana sauke wani irin ajiyan zuciya na shige ta biyoni a baya.
Daga ban dakin dana aje ruwan ina jin tana fadin kai yanzu naga hero a waje ashe fitan danayi bana banza bane tunda har na samu yai min magana yau.
Wai me kike nufi Rufaida kin san dai alkawarin su daddy ai ko tace ina ruwana da wani alkawarin su can in dai na samu ya kyasa min.
Da wanan cece kucen har na fito daga dakin suna kanyi na barsu nan dakin mami na nufa kai tsaye daga nan don in gyara.
Ina shiga ranan ne karo na farko da mami tayi min fada kan aikinta don ina sallama tace zeey mena kawo kinan kiyi tun dazun kin shige ba a ganki kin san zan fita yau da wuri.
Me ke damun ki yanzu ne tunda kikaje gida naga kina son ki sukurkuce min fa sai ayi ta neman ki kiyiwa mutum abu baki san kizo don kanki ba.
Mami kiyi hakkuri ba wucewa nayi ba dama daga bayana naji ana fadin is OK mami tunda tazo din.
Muryan ne ko mai maganan abin kallo na juya don ganin mai magana suka karaso tare da jamal, sai jamal ke fadin .
Wata kila wani ne yasa ta aiki don naga tana diban ruwa a waje zuwa ciki cikin harshen turanci yake magana shidai tun maganan farko bai kara magana ba ya samu wuri ya zauna.
Wa kike diban wa ruwa mami ta juyo tana tambayana tare da tsureni da idanuwan ta a kaina.
Anty Rufaida ne tace in diban masu ruwan wanka dukka dakin shine na tsayayi dama na bata amsa.
Wai mai Rufaida take nufi ne akan yar nan mami ta fada da hausa barta zamu hadu bari a watse gurin taron nan in mata tsiya.
Kayan dake saman gadon na fara tatarawa ina nadewa na tara gefe guda sun dan dade dakin don maganace mai muhinmanci sukeyi a lokacin naga an aiki jamal mami na fadin don Allah kada ka tsaya don munyi waya dashi yanzu.
Tare suka fita lokacin mami ta fara shiri tana fadin in miko mata wanan in bata wancan har ta shirya cikin wani rantsantsen lace da akai mata dinki ya sauko zuwa gwiwan ta.
Ga wani sarka da na fitar a cikin wani gida mai kyau da dauka ido ta nuna min yadda zan saka mata shi.
Ta tsaya a gaban mirrow dakin tana gyara kwalliyan ta da kyau da sauri na karasa gyaran dakin na share don ta fita zuwa falo.
Dakin ya koma tsab na saka mai kamshi gadon yayi kamar ba a kwana saman shi ba lokacin.
Gaba daya mami da yaranta har anty Aisha suka shigo dakin tare da ita sun sha ankon farar shada sai maiko jikin shadan da motsi yakeyi sun saka mami a tsakiya sai Aisha ce da wanab bakon da ban san dunan shi a baya suma magana sukeyi a cikin rada kamar Aisha zata shige mai jiki.
Ganin yadda suka shigo suna magana haka yasa da sauri na zo fita sai muryan jalal ke fadin ke yarinyar hajjaju ana magana dake fa.
Key ya mika mai yace ya bani shi jalal din ke min bayani wai inje in gyara mashi dakin shi yana bukatan gyara.
Na rusunan na karbi key din harna juya sai kuma na juyo ina fadin ina dakin yake yaya ?
Kwatance jamal ya fara min naji yaya mamud na fadin jeka nuna mata dakin mana har zan fita mami tace ki rike key din dakin nan guda tana nuna min kofa.
Na tsaya na cire na tafi yana waje yana jirana har muka nufi wani part ya nuna min da hannu.
Daga kofan shiga part din na hango wasu irin zaratan maza kartai dasu su shida kowa ya saka bakaken kaya a jikin shi.
Tsoron sune ya kamani da fargaba na nufi wurin na gaidasu na sa key ina bude kofan kafin in tura da sallama in shiga.
Bin ko ina na falon da nagani nayi da kallo komai yana a tsare ga wani kamshi yana tashi a dakin ta ko ina kada in tsaya kallo wani ya sameni haka yasa nasa kai zuwa kuryan dakin .
Nan ma nasha kallon saidai ban yarda na tsaya ba ina kallo ina abinda ya kaini dakin ko ina sako da lungun dakin saida na sharo shi tasa na goge kafin in fito sha daya saura.
Tun tun karowana part din da muka sauka naji gidan yai min tsit babu hayaniya har haraban wajen gidan babu wani motsi sosai kamar yadda na barshi .
Babu kowa a part din sai motsin masu aiki da nake ji a kitchen din gidan tsayawa nayi ina tunanen sun tafi ke nan inda zasu ashe ?
Ke nan na dade a dakin ina gyara ban sani ba har aka wuce akabarni sai kuma naba kaina amsa da fadin ke yar aiki wazai kaiki wurin taron manya haka.
Wanka bake bukata don haka na nufi dakin mami tunda can kayana suke tunda mukazo ina shiga na rufo kofan dakin na shiga ban daki a gurguje da tsoro nayi wanka har na shirya na fito na rufe dakin.
Kitchen din gidan na nufa don yunwa nakeji lokacin sosai gaida masu aikin dana sama nayi ina tambayan abinci.
Daya daga cikin su mai hausar gwarawa take fadin abinci yanzu sun cinye komai nasu sun tafi ai sai ta hada da yaren su kuma naji daya na mata yare sai matar tace in tsaya ta debo min akwai wanda suka ajewa wasu basu zo ba.
Suna ta yaren su har ta hado min na karba ina godiya tare da dawowa falo na zauna naci saida na koshi na kwashi kayan na mayar kitchen din da zuman in wanke da sauri matar tace ka bari wanan zaita wanke ai.
Nikan na fito na barsu don jin abinda ta fada na zauna a falon ina kallon tv dake aiki ganin yadda aka bar falin na mike na gyaro ko ina na gidan ban samu kaina ba sai daya da wani abu.
Alwala nake daidai lokacin dana fara jiyo hayaniyan dawowan mutanen gidan nayi alwalana na shige ciki a falon kamar yadda nayi da asuba ko wanan ma nan na tsaya nayi.
Suka fara shigowa daya bayan daya kowa a gajiye sai shigowan anty Aisha na mike da dan sakin fuska nake gashe ta.
Ta amsa min tare da fadin a, a yarinyar mami yaya bakije gurin taron bako kinje banganki bane tana fadin tana magana nidai nayi murmushi kawai.
Har ta danyi nisa ta juyo tana fadin zo zo zo yarinyar mami tana miko min hannu na nufi gurun ta tare muka shiga dakin bayan ta bude ta fara yarda jakkan hannun ta saman gado na dauka nakai wurin filon na aje mata shi.
Taje help me to remove dis cloth don Allah tun dazun duk na gaji dasu a jikina ja min zep please ko zanji dadi haba wanan wahalan yai yawa.
Naja mata zip tana ta tsuki da fada bata tsaya komai ba ta kwabe kayan ina kawar da kaina gefe ta fada ban daki tare da barin kayan a watse.
Tattara kayan na farayi ina nadewa kafin ta fito wanka na gyara ko ina na fito haka yayi daidai da shigowan mami gidan yan bambadanci suna bayan ta suna fadin saike hjy maryam mace mai kamar maza mata a gidan Alh ma,azu gin sun buga sun barki Allah dai yajikan maza maza sun kwanta.
Ko yanzu yasan baiyi zaben banza ba yabar baya a duniya uwar zaratan maza kece uwar gwaunan gobe kece uwar shugaban kasa, .
Wata ta karbe da fadin kece uwar manyan duniya ga gobe gaba sallama baya sallama yar manyan mutane.
Nikan na suma wurin kallon yadda ake masu barin kudi kamar ba neman su akeyi ba.
Zama mami tayi yayin da kawayen ta suka kewayeta ta ko ina ni sai lokacin ma naga wasu da ban gansu jiya ba.
Take falon ya cika da jama, a ta ko ina babu masaka tsunke a gidan wuri ya kaule da ci dasha ina labe daga kofa ina kallon ikon Allah don ni ban taba ganin bukin manya ba irin haka.
Wasu nacin abincin wasu na haraman sallah wasu kuma suna mayar da magana mai rabon abinci suna rabo kungiya kungiya.
Nama girman shi yakai dunkulen hannun mutum don girma duk nau,in da kake so na abunci shi za a baka a wurin.
Daga inda nake rakube naji mami ta fara kiran sunana da sauri na amsa da gani mami na isa guri ina gaida ita.
Gaba daya mutanen dake gurin sun zuba min idanuwan su hannu mamu ta mika min na isa wurin ta da sauri tajawoni tana rada min in shiga daki in duba cikin turamen zanin dake zube gefe a kasa in dauko guda biyar in ba matan dake mata kirari .
Na amsa ina gyada kai na matsu in bar wurin daki naje na bude na dauko kayan kamar yadda taimin bayani nazo dasu falon kowa ya saka min ido.
Ina takowa da zannuwan a hannu na daya daga cikin matan da akace in kawowa tana kyala ido ta fara fadin kaga inda kyau asali yake farar mace alkyaban mata.
Diyar hjy takawan ki lafiya dayan tace fari kun gadane ba ku ba shagon maida baka fara kaga jinin larabawa asali irin gado bana gada ba.
Yarinya sai gidan gwauna ko minister minister ma mai fada aji irin uwarki ba muna minister ba akoma gefe ba office .
Dayan ta karba da fadin haka yake don yau mun sheda mun gane bambamcin ayyah da tsakuwa a bainan jama, a.
Nidai har jiri nake gani don idanun da aka watso min a falon na nufesu na mika masu zan juyo mukayi arba da yan matan Rufaida da Nazifa tare da wasu mata a zaune suna magana kasa kasa sai hararana sukeyi.
Na raba na koma dakin mami na gyara wurin dana dauko kayan na fito har lokacin sai kirari sukewa mami din.
Ance massadan ka fadawan ka a inda na tsaya idanun su ya rufe basu san ina wurin tsaye suke gulma akan mami.
Wai haka duniya yake ai gashi bai gina kowa ba sai matarshi da diyan shi kawai ya inganta rayuwan su.
Har mami tana daga kai dama ba,a san asalinta bane ko yar waye yar hakimin kauye kawai da ita yanzu ta samu duniya taba ganin kamar tafi kowa.
Jifa kai duniya ina zaki damu kan hassada wai kuma sun zo ne har Abuja dalilin ta don tayata murna fa kuma suka koma gefe suna gulman ta.
Kafin dayan ta dago kai mu hada ido ina kallo ta zuguri dayan matar dake magana ta dago mukai arba na watsa mata wani kallo don girman ta ya gama zubewa a idona ko tunda na shedata tana zuwa wurin mami ko a kaduna.
Tun yamma nake ta kallon ana shiri muna idar da sallah mami tayi kirana muka shige dakin da wasu kawayen ta biyu.
Shiga ta alfarma mami tayi ina ciki sai faman miko muna wancan mayar da wanan dauko muna wancan abin ko mami ta ce zee ina abu kaza din nan ?
Haka dai har mami ta shirya wai dinner za, a tafi a wani katafaren hotel nan cikin garin Abuja.
Mami kan hankalin ta ya dauke bata takan kowa a gidan don uzurin gaban ta yau data zauna za a kirata gefe da magana kus kus.
Har aka fara tafiya gurin dinner din ina kallo su Nazifa da Rufaida da su Rubby suka fito sai wani shakiyanci sukeyi a tsakanin su.
Wanan na fadin yau kan akwai babban kamu don bazan fito ba sai na sace zukatan mutane da yawa .
Wanan ta daga tayi wani juyi tana gwada tafiya har suka gama iya shegen su suka fice gidan sai wani yauki da yanga suke yi nasan harda kari don inji haushi.
Saboda ina jin Nazifa na fadawa wata tsohuwa da ban santa ba a cikin dangin su tsofi da mara gata su zauna gida ba, a zuwa daku taron manya don darajan wasu baikai can ba .
Tsohuwar dai tayi mata dakuwa da hannu ta fita tana dariya ajiyan zuciya na sauke bayan fitan su falon ina wasa da yan yatsuna sai ga anty salma ma sun fito da wasu yan mata guda biyu ina ganin su nace anty salma sai kun dawo don dai tace inzo mu tafi.
Tunda nayi dan kwalliyana a lokacin amma sai ta daga min hannu kawai suka fita na koma na zauna ina tunanw kala kala a raina.
Can an dan dade sai ga anty Aisha ta fito tana tako daya daya tana waya na dago ina fadin anty Aisha sai kun dawo .
Ta juyo tare da fadin yarinyar mami baki tafi bane daga haka ta sa kai ta fice a gidan bayan fitan ta naji gaba daya zaman wurin ya isheni.
Don haka na yanke shawaran fita haraban gidan in sha iska duk da darene amma wajen kamar rana don hasken da ke akwai a wurin.
Wuri na samu na zauna gefen flowers ni daya sai tunane barkata da kalle kalle nakeyi kafin kamshin turaren nan da tun rana dana aiki a dakin yake a jikina badon na cire kayan na daina jin shi a yanzu ba.
Ta dan nisa kadan yazo ya wuce ni zuwa wurin motar shi lokacin ne na san da mutane a wurin sai ga bodyguard din nan nasa dana gani da rana sun taso zuwa wurin shi.
Kallona ya koma can na samu abin gani da zagi a raina ganin yadda suke mai kamar ba mutum ba dan uwan su.
Mota ya shiga suma suka shiga dayan motan bayan sun rufe mai suka tayar da motar hasken motar su ya haskani sosai inda nake nayi saurin dukar da kaina kasa.
Shiru shiru motar bata tashi ba na dago kai da zuman in kalle su sai ganin mutum nayi a gabana yana fadin cikin harshen turanci boss yace ki zo.
Na nuna kaina tare da fadin ni yace eh ya juya na mike na bi bayan shi zuwa wurin motar tun kan in karaso aka bude motar ina zuwa naji ance shiga mu tafi.
Murna zanyi ko mamaki duk babu daman wanan saboda tsoron daya rufeni lokaci daya banda zabi na shiga gefen da aka bude min din.
Wani sanyi da rabane ga kamshi ya dakeni lokaci daya sai dana zauna nake fadi ina wuni a cikin hausa ban sani ba ko ya amsa min don an rufe kofa a lokacin.
Har muka kai wuri ba wanda yai magana a motar ga wurin da gidan akwai nisa sosai a nawa ganin.
Wurin ya cika da motoci da ababen hawa ga jama, a wasu a wajen wurin sai security kala kala dana gani gani da tsoron yan sanda tun a kauyen mu.
Motar ta samu wuri driver ya tsaya daga inda muke muna jin magana da kidan dake tashi a cikin wurin.
Duk muna a cikin motar zaune nidai na kurawa sarautan Allah ido sai can aka bude motar duk da an bude ya dan dade bai fito daga cikin motar ba.
Can ya sauko katan mazan nan suka wani zo suka tsaya wurin motar wani ke fadin in fito na fito da sauri har sunyi gaba na bi bayan su.
Gap da zai shiga wayab shi yai kara ya tsaya a wurin yana amsa waya haka yasa na yanke shawaran fara shiga cikin inda ake taron.
Sai masu tsaron get din wurin suka hanani shiga wai sai na nuna masu pass dina wanda mutum yafi a kirga sun shiga ni ina wurin tsaye.
Har sojan dake kofan yana son ture da hannu biyu kyaleta tare muka zo ya bashi amsa bamu shiga ba saida akai muna bincike.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
JUMMA, AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA SADA MU DA ALHERUN DAKE CIKIN WANAN RANAN MAI ALBARKA UBANGIJI YA YAFE MUNA KURAKUREN MU AMIN YA ALLAHU, , , ,
YAR UWA LITTAFIN KUDINE DON DARAJAN ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BANA FITAR MAKI DA HAKKIN RASHIN SANI NA FADA MAKI ALLAH YASA MU DACE AMIN, , , , ,
DARI UKU NE KUDIN SHI DON SHIGA GROUP ZAKI IYA TURA WA TA WANAN ACC 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN NA DARI UKU KACAL, , , , ,
Ina tsaye duk na kagu in shiga inga abinda ake a cikin dakin taron da nake ganin mutane kala kala suna shiga wasu ma ba mudulmai bane daga cikinsu..
Nayi kamar zan bi wani tawagan yan mata da naga zasu shiga sai sojan dake kofa ya kalleni yai warning dina da bulalan hannun shi .
Dole naja baya na tsaya ina mazurai da idanuwa tare da dan bin ko ina da kallon mamaki a wurin don gaskiya ban taba zuwa irin wurin nan .
Sojojin kofan na naganin shi ya gama waya bodyguard din shin sun sashi tsakiya suka fara jayewa a hanya suna girmama shi.
Hannu ya daga masu yana kokati shiga nayi saurin shiga cikin su da saurina don kada su barni gurin ban san yaya zanyi ba gashi tunda nazo banga wani wanda na sani ba a wurin.
Sojan ne yayi azaman riko ni sai ya juyo a hankali kamar mai rowan magana yace don't sojan yaja baya da sauri ya kame.
Wani iri naji kaina ya amsa lokaci guda ganin irin taron mutanen dake wajen gasu zaune saman kujeru masu kyau kowa yayi kwalliya gwanin ban shawa,a.
Ba zan iya sheda kowa a wurin ba idan ba karya zanyi ba saima ince kowa ya zubu muna idanune shigowan mu ashe ban sani ba mai magana ke sanar da shigowan dan mami dana biyo tawagan su.
Biye nake dasu a baya kamar jela har aka nuna mashi wurin zama wani table babba yasha kayan ado dana ciye ciye saman shi.
Da idanu yai nune sai wani ke ce min in zauna wai na dan kai zaune a hankali kamar yadda kowa ya zauna kaina na sade kasa.
Ba mami ba duk wanda ke dakin taron hankalin shi ya dawo garemu ne ance yaro da kudi abokin manya.
Wai ashe da Done nake zaune ban sani ba a wurin sai mamakin koni wacece wanda basu sanni ba suke yi.
Wa yanda suka sanni kuma suna mamakine meye hadina dashi muka shigo tare ni yar aikin gida abinda ko yan gida basu samu gatan hakan ba sai karamar yar aiki kamana.
Anci gaba da gudunar da shagalin da ake inda mawakan hausa dana sauran yare suke nuna bajintan su a wurin.
Ga masu rabon gifts suna faman rabawa table table don komai a wurin a tsare ake yin shi tun ina kallo har gajiya ya fara kamani don zaman kurame muke a table din mu.
Dan gara su dan motsi kadan zaiyi sai kaga daya daga cikin bodyguard din nan sun duka suna magana dashi a kunne.
Har lokacin da muka tashi sai dai mutane suzo su gaisa dashi su wuce yana zaune bai daga ba sai da zasu tafi ne dayan ke min magana kamar rada yana fadin in tashi mu tafi.
Haka na taso shike gaba sai ni a baya bodyguard din dun samu a tsakiya kusan ince shine farkon fita wurin da gani baison hayaniya don sai faman murza goshin shi da yake yi kadan kadan zai murza goshi har yakai ga mikewa muka fita.
Kamar yadda mukazo haka muka koma ba wanda yai magana a motar har muka kai gida ni ban ma sani ba saida naga mota na shiga gidan nasan mun kawo.
Aka bude motar zan fita na juyo inda yake zaune kamar ba zai fita ba nace na gode yaya don ban san sunan shi ba dan mami bako nake kiran shi dashi.
Ina hawa steps din ne naji muryan dayan bodyguard din shi na fadin hjy ga wanan wai ki dauka inji boss wai ashe abinda aka rabane a wurin daya yakai a mota shine yanzu suka ban.
Haka na shiga da jakkan niki niki don gifts din manya daban aka bada su ba irin wanda aka rabawa kowa bane wurin.
Daki mami nakai jakkar har biyu mai kama data matafiya shake da kayan da ban san ko meye a ciki ba na aje.
Hayaniya ne ya fara karde gidan lokacin har barci ya soma daukana don ban dauki hakan a komai a raina ni dai nasan ya taimaka min saboda halin kirki irin na uwarsa ya kaini naga buki haka na aje kawai a raina.
Sabanin sauran jama,an wurin dake tunane kala kala yadda aka ganni dasu kowa da irin nashi fassaran a ran shi.
Nikan ganin mami bata shigo ba yasa na kwanta kasa nayi filo da jakkunan kayan da nashigo dasu har barci ya daukeni hakana ban sanni ba a wurin.
Ko da mami ta dawo ta samu ina barci a dakin ta a kasa na dunkule a wuri daya kallon tausayi tayi min yadda na kwanta a maraice a kasa.
Sai taji komai da take son tambayana data dawo ya kawu a zuciyar ta bata tayar dani ba sai dai can hayaniyar suce ta tayar dani daga barcin.
Da sauri na mike ina fadin mami sannuku da dawowa maki ina murzan ido .
Sai mami ta juyo tana fadin tashi kikayi kuma koma ki kwanta nima a gajiye nake ai yanzu sallah zanyi in kwanta.
Mami me zan maki yanzu na tambaya ta juyo tana fadin bakiji mena fada ba ki koma ki kwanta abin ki dare yayi yanzu sosai.
Washe gari da safe na tashi kowa nata sallahfita nayi waje ca wurin famfo wajr inda na saba yin alwala nayi na dawo falo nayi sallah.
Na dan zauna don jiran mami ta idar kafin in kwatanta in tashi zuwa dakin tana zaune suna magana dasu anty safiya da anty sa,a da wata mata.
Gaidasu nayi na mike na shiga bandaki na fara wankewa kagin in hadawa mami ruwan zafi na fito yanzu sun karu a dakin yasa na fita na barsu a ciki na dawo falo saman kujera na takure a wuri daya .
A yadda na lura wasu daga cikin bakin suna shirin komawane a ranan garuruwan da suka fito dan yiwa mami kara sai yanzu nasan mami mutumiyar mutane ne sosai.
Yauwa zonan yar iska manya kawai mai mugun nufi dama nasan ba banza kika bar mami ba shegiya.
Na dago kai ina duban dawa anty Rufaida ke wanan magana haka na fara waige waige ina duba sai naga tana nufo inda nake tana fadin .
Bada ke nake ba kin tsaya kina kallon mutane yar iska nuna kaina nayi da hannu cikin mamaki ina fadin ban san dani kike ba ai anty na mike tsaye.
Juyawa tayi haka yasa ba gane nufin ta nace anty mami zata nemeni yanzu don tace in bar nisa da ita jiya da kika sani diban ruwa tayi min fada.
Ke ni kike fadawa wani mami tace kibar nisa da ita kizo dakin mu yanzu ina jiran ki idan baki zoba kuma kin san sauran.
Juyawa nayi na kalli dakin mami kamar zanyi magana sai kuma na bi bayan Rufaida din zuwa dakin su.
Ina shiga takai min mangara a kai da niyar kaimin mari saina dafe ta samu kaina kallon mamaki nake mata don ban san abinda nayi mata ba haka ?
Ke yar iska yaya akayi kibi hero zuwa gurin jiya wai tana zare min idanuwanta waje tana son jin amsa daga bakina.
Shiru nayi don bansan abinda take magana a kaiba lokacin ra kara maimaita tambayan ta nayi shiru Nazira tace idan ma ke manyace kici kanki kisha bakin ruwa don bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane.
Sai wace akecewa rubby tace wanan ai na fada maku snake ce a ciki ku ga kyau ga daukan hankali ga duk wanda yasan abinda ake kira da matar manya.
Don Allah rubby ki daina wanan maganan haka karta dauka ita din wata tsiyane can ta ban amsa kawai don jiya shegiya ta hanani barci da dadi duk na rufe ido yar iska nake gani a cikin su.
Turo kofan da akayine ya dauki hankalin kowa a dakin ba kowa bane sai anty zulfa yar gurin kanin mahaifin su Rufaida tana fadin ke kina nan ga mami can na kira ki.
Ban tsaya jin komai ba na mike na bar dakin da ssuri na nufi dakin mami na dauka zatayi min fadan haka sai naga sabanin hakan tana fadi yauwa zainab don Allah zauna ki hada min wanan kayan kafin in fito wanka zan tafi dasune in sallami mutanen yola don karfe tara jirgin su zai tashi.
Na amsa da to mami tana fadin ki saka komai daya daya a cikin ko wani jakka tana fadin haka ta shige ban dakin.
Zama nayi na saka kayan kamar yadda mami ta umurce ni inyi mata tana fitowa ta zauna shafan mai tana umartana dana bude jakkunan ta gani.
Har ta gama shiri a gurguje tana fadin in kwasa zuwa cikin motar ta dake wajen gidan fake na na aje sai ga driver yazo yana fadin za a saka a cikin motar ne nace eh mami tace in kawo nan zata fito yanzu.
Sai gata mun hangota suna tafe suna magana ta kawo inda nake tsaye take fadin idan kin gyara dakin zeey ki mayar min da sadkokin ida muka dauko su jiya.
Sai kin dawo mami na bata amsa ina juyawa zusa cikin gidan kai tsaye dakin na shiga na samu mami ta barshi a bude.
Gyara komai nayi tsab na shiga ban dakin a gurguje don nayi wanka sai dai kuma har lokacin ina tunanen abinda su Rufaida sukai min wanda bansan akan me suke magana ba akai.
Mami ta dawo bayan bakin nata sun tafi nan kuma ta shiga sallaman masu tafiya a mota don komawa kaduna.
Suma tana daki tare da su anty safiya da kannenta biyu suna kasafa abinda ake bawa masu tafiya.
Zuwa karfe biyu gida ya koma sai mu kadai a cikin sa sai kuma kannen mami da basu tafi ba suna daki da anty salma wace sai yanzun na fahinci akwai mahaifiyarta a cikin su ashe don basu da kama sosai da uwar da mutum zaiyi saurin gane hakan.
Mami ta tashi don yin sallah azahar saboda dan barcin daya dauketa a lokacin don gajiyan dake jikinta.
Nima na danyi barci bayan gyara falon gidan danayi duk da girman falon amma hakan bai dameni ba na tsaya na gyara shi fes.
Ina zaune ni kadai a katon falin sai tv dake aiki jefi jefi nake dan mayar da hankali wurin kallon abinda akeyi a ciki.
Eyyeh zama ma kikayi saman kujara ke nan ke gaki mara ta ido ko a gidan ku akwai irin sane halan da zaki zaunawa mutane harda dora kafa sama.
Ina sauke kafan naji muryan Anty Aisha na fadin me kuma tayi yanzu dan ta zauna kawai a kasa kike son ta zauna ke nan .
Aisha baki san wanan munafukar yarinyar bane wallahi sai ta dinga yin abu simi simi kamar wata ta Allah can da ita nan ko munafukace ta gaske.
Ku daina yin hakan mana yarinyar nan bata da wani aibun da za,ace kuna mata haka ai tana fitowa daga daki dauke da chip's tana ci a hankali ta nufo wurin mu.
Wai kin san wanan bata aje kanta a kusa ba jifa jiya harda mannewa yaya J zuwa wuri dinner.
Kin san yan kauyen nan da bakin shishigin tsiya ko ya akayi ma tabi bayan shi ko tsoro babu.
Wanan she most go back to her village kafin rigiman ta ya fi nan don wallahi ni gaba daya nama tsaneta kwata kawata wallahi.
Haba haba Aisha tace cikin muryan ta na sanyi irin nasu meye a cikin har kina fadin kin tsaneta haka yarinyar nan she is good and beside mami tana jin dadin zama da ita sosai so kima bar wanan magana kada ku hadu da mami.
Ta mike tana fadin ashe na kusa barin gidan nan don ba zan iya zama da wanan yar iskan ba da take neman nuna ita watace a gidan nan.
Har abi yakai can haba bai kamata ba kina fadin haka kan zainab don ba ruwan mu da ita don Allah kada hakan ya jawo wani matsala mai girma.
Ina laifin wanan yarinyar a nan itace fa dazun ta gyara falon nan haka muna sharan barci a daki ita bata huta ba.
Tace a fusace ni dai bana son ganin ta gidan nan ne tare damu I just hate d girl wallahi.
Aisha tayi murmushi tare da daukan chip's din ta tasa a baki kafin tace ni banga wani aibunta ba wallahi.
A gadarance tace tana wa mutane shishigi da yawa a gidan nan ko don tana ganin mami na kama matane oho ?
Ru,faiidaaahta fada a wani irin yanayi kamar mai warning din ta sai kuma taci gaba da cin abinda ke hannun ta ba tare data furta komai ba kuma .
Juyawa Rufaida tayi a fusace tabar falon ta bita da kallo tana girgiza kai kafin ta dago ta dubeni inda nake tsaye a rakube tace zauna.
Ba bata lokaci nayi kokarin zama kasa don warning din da rufaida tayi min dazun kan kujeran da har ta zagi gidan mu.
A, a kasa zaki zauna zauna a nan tana nuna min gefen da take zaune na girgiza kai tare da fadin akan hawa kujera yanzu anty Rufaida ta zageni.
To ai yanzu ni nace ki zauna ko ta fada cikin rashin damuwa sai dana danyi jimm kafin in zauna a saman dayan kujaran a takure daga bakin kujeran don ban yarda na zauna ciki sosai ba kada kuma a kara zagan min iyayyena wanan karon.
Kaina a kasa sai wasa nake da yan yatsun hannuna jin ta kira sunana yasani dago kai na dan kalleta kadan tare da kara sunkuyar da kaina a kasa.
Sai naji ta dan sake murmushi tare da fadin feel free with me zee I am not like Rufaida OK.
Na kula baki da walwala a gidan nan ko yaushe kamar a takure kike ina son sanin damuwan ki idan ba matsala.
Jin tayi shiru yasa na dago kai na dan dubeta kadan ni take kallo a lokacin ganin na kalleta ta dan daga min kai tare da fadin ke nake saurare zainab.
Ta sake fadin tell me meye matsalan ki ne meke damuwan ki ko yaushe kike a takure ?
Ina son sanin menene sirin kin san ABU A CIKIN DUHU SIRINE, jin haka yasa na dago kai na dan kalle ta tare da fadin sirin me kuma Anty Aisha ?
Sirin rashin jittuwan ki dasu mana nake son sani sai da dalilin ai hakan ke faruwa.
Da kyat na bude bakina na nace banda matsala a komai sai dai su anty Rufaidane suke yawan takura min har tana zagina da iyayyana don kawai taga nazo yin aiki a gidan su.
Zagi kuma zee koda yake koni yanzu naji yadda kukayi ko dukan ki zata iya ai a yadda ta nuna din .
To wai me ya kawo hakan a tsakanin ku ne don na kula tunda na dawo hutu da abubuwan dake faruwa a gidan nan.
Ko kina tunanen wani abune ya jawo hakan ke a tunanen ki zainab don naga dai ba shiga harkan su kikeyi ba ke a gidan nan.
Idona ya kawo kwalla nace sai nake gani kamar don irin yadda mami take min ne sukewa haushin hakan don mami bata daukeni yar aiki ba kamar yarta ta daukeni ta jini.
Sai suke ganin kamar ban cancanci hakan ba tunda nidin ba jinin ku bane da mami zata sakani a jikin ta.
Umm, umm inda wanan da wanan gaskiya amma hakan ai ba zai jawo wanan tsanar haka ba a tsakanin ku tunda mami bata ragesu da komai ba su din ma tana nuna ita ta haifemu ga baki daya ai ga nawa ganin.
Anyway koma dai meye ki kara nisa dasu duk da nasan kina hakan zangan su inyi warning din su ba tare da zancen yakai kunnen mami ba.
Nagode Anty Aisha nace a sanyaye koba komai ta nuna min kaunarta a gareni ai tunda na samu kula a wurinta.
Muryan tane ya katseni tana fadin ke din ce zeey da shegen kyau wallahi kila hakan sukewa kyashi kin san mu mata ai yadda muke.
Nima kaina shigarki ta jiya saida naji kamar karna baki kayan nan don ban dauka haka suke da kyau ba.
Saida nagan ki dashi a jiki nasan yadda sukewa mutum kyau ashe idan ya sakasu don jiyan nan gaskiya kin dauki hankalin mutane da yawa gaki kuma tare da big boss da yan mata da yawa a wurin suke son kasancewa tare dashi.
Sai kawai aka ganki dashi by surprice kin ba kowa mamaki a wurin sosai don ba wanda ya zata hero zai tsaya duban wata mace ko wacece .
Saidai bamu san sirin ba don abin ya bawa kowa dai mamaki gaskiya har mami kanta tayi maganan haka.
Tausayina yaji shine kawai anty Aisha kin san irin ku irun tausayin na kasa dasune .
Kafin tayi magana wayan ta yai kara ta dauka sai naji tana fadin gamu a falo tare da ita yasa nayi saurin dagowa ina duban ta.
Kije mami na neman ki a daki ina jin haka na mike da sauri zuwa amsa kiran mami din yayin da Anty Aisha ta bini da kallo har na shige dan lungun da zai sada mutum da dakununin gidan.
Zaune na samu mami tana duban wayan ta, na shigo da sallama ta dago tana fadin duba min ko masu girki sun gama a kawo min nan don bazan fita dakin nan yanzu ba hutu nake so yau.
Da sauri na tashi zuwa kitchen din inda na samu anty Aisha tabar falin ita ma na shiga kitchen na fadawa madu aikin sakon mami din.
Nan danan suka shiga hada hadan hada nata abincin cikin wani katon try na dauko na kawo mata .
A dakin na samu anty Aisha tare da uwar suna magana shigowana sai sukai shiru mami na kula da tana bina da kallo kafin nace ga abinci mami.
Yau ajeshi nan don har ruwa da drinks sun saka a ciki na juya zan fita take fadin zo nan zeey na dawo da sauri zuwa gareta.
Nakai kasa take fadin yau zeey yaya akayi na ganki tare da jafar jiya a gurin buki ?
Da sauri na dago kai ina fadin Jafar mami a, a bani bace nikan da yayan nan da yazo na tafi koshi an barni ni kadai a gida sai tsofi na fita waje na zauna shine da zasu wuce yace inzo mu tafi shine na bishi mami.
Ok mami tace yayin da take saukowa saman gadon don wani lokaci mami a kasa take zama taci abincinta.
Saida na tsaya na zuba mata ta fara ci tana fadin oya dauki wanan sauran kije kici don nasan bakico komai ba yanzu haka.
Na dauka tare da fadin na gode mami na fita da ture din a hannu na ina murna zan sha ferfesun kai yau har in bari duk da ina ci sai dai diban tsoro nakanyi wa abinci wanan kuma an bani shine kai tsaye.
ZAINAB IDRIS MAKAWA[04/12, 22:48] +234 903 349 8278: Tnx
[04/12, 23:33] +227 98 36 59 34: 🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣5️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
IDAN NACE NA KUDINE INA NUFIN IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI KO ?
Ranan nasha dadi don a dan lungun shiga dakin mami na zauna a kasa na kwashi garabasa na a wurin ina tsotson kanshi ne su yaya mamud suka shigo zasu shiga dakin mahaifiyar su su uku babu jamal a cikin su.
Kunya ne ya kamani yadda suka sameni ina gwigwiyan kashin kafan saniya ina kuma tsotson ruwan miyan da ya lake a cikin sa don dadi.
See dis village girl jalal ke fadi dubeki don Allah a kasa kika wani zauna kamar wata kazama can.
Dan kallona yaya mamud yayi ya kawar da kanshi gefe daya yana fadin wai a ina mami ta samo wanan yarinyar ne ?
Haka yayi daidai da shigar su dakin mami din inda direct wurin da mami ke zaune a kasa Jafar ya nufa ya zauna a kasa tare da karban cibi a hannun mami din.
Kallo shi mami tayi kafi ta mayar da kallon ta ga mamud tana fadin me naji kana tambayane ?
Sai jalal din yace dis your village girl mami kinga yadda tawani zauna a kasa tana cin abinci kamar wani zai daka mata tsawa ta sheka a wurin.
Ina ruwan ka da ita mami tace tana kawar dakai zuwa kallon Jafar da yakai ruwan miya a bakin shi ya fara taunawa da kyat kamar an sashi ci dole.
Yanzu haka nasan baka karya ba tun safe maimakon yai magana sai cikin shi ya shafa yana lumshe idanuwan shi a hankali.
Yaya jalal zainab tana da gaskiyan ta ta fita falo kuma a zageta shiyasa ta labe nan nasan tana ci hankali kwance.
Waye zai zage ta mami ta fada a hasale ciki ko in kulla kai tsaye tace your daughters don dazun nan na raba ta da Rufaida a falon .
Wai kawai ta zauna a kan kujera in kaga yadda Rufaida kewa yarinyar nan abin ba kyau wallahi .
Shine na zauna da zeey din ina tambayanta take fasin bata san abinda tayi masu ba suka tsane ta ita zagin ne ke ci mata rai dasu ai sosai.
Wanan Rufaidan badon mahaifinta ba da nake jin nauyin shi a yanzu wallahi akan yarinyar na dana mata tsiya sosai a gidan nan ko ta koma gidan su.
Mami akan wanan yarunyar har kike fadin haka yarinyar fa ba yar kowa bace balle har ki fadi haka nasan shi, , , ,
Karbi nan jalal mami ta jefa mai dakuwa da hannun ta tana fadin uwarka ma kaji ance ba yar kuwa bace face dagacin kauye.
A haka kuma mahaifin ku ya aureni har muka haife ku ka san mai Allah zai mayar da ita gobe ita kanta Rufaida data sani da batai mata hakan ba don Allah yasan goben ta.
Yaya mamud yace ni ban ma san yarinyar ba shine yanzu nake tambaya ko wacece ita ina dai yawan ganin ta gidan nan all d time idan na shigo.
Ina zaka sani tunda ba a gida kake zaune ba itace yanzu mai koyawa diyan ka karatu a gida .
Yace so tasan abu ke nan sosai ma mami ta fada tana budan baki ta karbi abincin da jafar ya debo ya bata.
Ni dai bana son takurawan da su rufaida ke mata Allah mami yarinyar tana cikin damuwa haka sosai wallahi.
Ido ya runtse kafun ya bude ya juyo yana fadin you are too talkative now kin fadi wanan maganan tun farko yake cewa Aisha.
No mami ta tsawata masu su daina muzanta ta don yarinyar she is beautiful sosai sai dai tsiyar abin yar tallakawace ita.
Mamud ya fada yana gyara zaman shi oh shi tallaka ba mutum bane ko don kawai tana tallaka sai akace a muzantata.
Is OK mami ku bar zancen nan don Allah ya fada rai bace yana kai mata cibin abinci a bakin ta ta karba.
Sai mamud ya kwashe da dariya yace mami ba fa nufina ke nan ba kin sani so iam sorry for dat ta dago tana hararan shi kawai.
Hummm hummm in dai a kan wanan maganan ne mami zatayi fada da kowa ai a gidan nan na rasa me wanan yarinyar tazowa mami dashi haka.
Anyway naji suna fadan wai sun asirce mami ne ita da , , , ,
Jalal getout bana son yawan zuba haka tin dazun nayi warning kan zancen nan kun kama magana kan abu daya haka.
Yana gamawa ya mike tsaye zai bar dakin mami tace ina kuma zaka zansa a kawo maku abinci kunci yanzu a gabana.
But mami , , , shiru yayi don hannun data daga alaman yai mata shiru dole ya dawo ya zauna waya ta daga ta kira wani layi tare da bayanin abinda za ai mata.
Kafin wani lokaci an hada dining din tashi sukayi tana gaba suna biye a bayan ta a falon dai nake sai dai ba a zaune ba ina gutfane raben jikina na saman kujera hankalina yana gun kallon tv dake aiki tun safe a falon gashi ban iya canza chenal din ba, don haka nake kallon dole hakana.
Zeey kina nan kina kallo mami ta fada saina dago da sauri don jin muryan ta danayi ina fadi cikin fara, a sannu da fitowa mami.
Namike tsaye tace no koma abinki ki zauna don me baki zauna da kyau ba ta fada kamar bata san abinda ya faru ba tsakanina da Rufaida da rana ba.
Dan murmushi nayi ta nuna min kujeran tana fadin zauna sama daga yau duk abinda kike son yi a gidan nan kiyi shi kamar kowa kinji abinda na fada ko ?
Na gyada kai ina kaiwa zaune Nazifa dake fitowa daga kitchen a gaban ta mami ke min fada ta juya zuwa dakin su nasan zata fada masu abinda mami ta fada min ne yanzu.
Mami basu bar wajen ba sai da magariba ya kawo jiki suka mike don zuwa sallah lokacin har na fita naje waje don yin alwalani.
A wajen suka sameni sai dai ban samu gaidasu ba suma ba wanda ya kula dani kuma sun ganni din wurin ina alwalan.
Na dawo na samu mami ta shige dakin ta nan falo na tayar da sallah sai da na idarne Rufaida ta fito tazo ta tsaya a kaina tana fadin.
Sai kin bar gidan nan munafukar yarinya kawai don nayi maki fada kan hawa kujera dazun shine kika fadawa mami ko ?
Da sauri na dago kai tare da fadin wani bamuyi wanan zancen da mami bani .
Rufamin bakin nan naki mai warin tsiya zaki cikani da surutun tsiya to bari kiji tunda nan ba gidan ubanki bane sai kin barshi walla, , , ,
Ke menene haka me tayi maki keki zaginta haka kawai don cin zalin zaki saka yarinyar mutane da zaki haka.
Yaya mamud ne tsaye daga bayan mu yake fada da Rufaida ta dan tabe baki tana fadin wallahi yaya yariny sai yace wanan ba daidai bane ya juya ya nufi dakin mami rai bace.
Yana shiga yake fadin mami gaskiyan Aisha yaran nan sun matsawa yarinyar nan haka ashe yanzu na same su a falo rufaida na shirin dukan ta badan Allah ya kawoni ba data kai ga dukan nata ma kila.
Innalillahi me yaran nan suke nufi newai kan yarunyar nan a to mami indai zamanta nan tare dasu zai zama matsala gara dai ki sallameta yace tare da mika mata ledan maganin daya sayo mata.
Ranan ma a dakin mami na jena kwanta a kasa kamar yadda na kwana a jiya a takure don gani nake idan nayi dogon motsi zan dameta a dakin ta.
Washe gari tunda na tashi nake jin kamar zazzabi a jikina hakana na daure nayi duk wani aikin da zanwa mami nayi shi cikin daurewa.
Inda Allah ya taimakeni mami ta fita tun goma na safe na samu na shige dakinta na kwanta ba tare da nasha magani ba.
Har lokacin da mami ta dawo daga unguwa data fita ta zauna falo bataji motsina ba kota ganni da ido sai tambayan mutane take suna fadin suma tun safe basu ga giccina ba.
Aka kama fadin ina na shiga hankalin mami ya tashi ranta kuma ya baci dani sosai kan hakan don dai tasan ban san kowa ba a garin.
Saida mami ta shigo dakine ta ganni a kwance na dunkule cikin hijjabina ina rawan sanyi.
Ja tayi ta tsaya da mamaki tana fadin ke zeey lafiya ko kin shige daki kin kwanta kin tayarwa mutane da hankali.
Jin muryan mami sama sama a kaina yasani bude ido da kyar na buda baki jikina na rawa zazzabi mai karfi nake fadin massarara nake ji mami tunda na tashi da safe.
Jin haka yasa ta karaso inda nake kwance tana fadin saiki shige daki ba tare da kin fadawa kowa ba ki rufe kanki a ciki don rashin wayau ko me ?
Da kin fada da an samu wanda ya baki magani ko a kaiki asibiti kinzo kin shige hijjab kina rawan sanyi haka kinki jan bargo saman gado ki rufe jikin ki dashi.
Tana wanan fadan takai hannun ta a jikina tana tabawa taji zafi radau da sauri naga ta juya ta fita dakin.
Sai gasu da jamal da Jafar sun shigo dakin da saurin su jamal ne ya kai hannun shi saman goshina yaji zafin da jikina yayi da sauri ya cire hannun shi yana fadin mami dis is serious fa jikin yayi zafi sosai.
A hankali yaya jafar ya tako zuwa inda nake kwance saman rough shima ya taba jikin nawa wani irin shock ne ya ratsa jikina lokaci guda duk da yanayin zazzabin da nake ciki haka bai hanajin wani yanayi da ban san na meye ba lokacin.
Idona na runtse daga inda nake kwance nunfashina har yana sarkewa yayin dashi har lokacin yana duke a kaina ya dago yana fadin les take her to the hospital dis is serious mom.
Mamice ta dagani daga kwancen da nake sai na kasa tsayi tsaye da kyau jamal kamata da kyau a kaita wurin mota mami tace.
No barta a kira wasu daga cikin yaran nan su taimaka su riketa zuwa motan ya fada yana juyawa ya fita daga dakin.
Fita yayi ya tsaya yana fadin matar dayaga tana falo ta kira masa sisters din shi dakin su don baisan dakin da suke bama.
Sai gasu sun zo suka same shi tsaye inda kowa sai mamakin kiranda yake masu sukeyi don da farko da matar tace shine basu yarda ba saida suka fito suka same shi a tsaye yana jiran su din.
Bai tsaya kallon su ba ganin sun fito ya juya yana fadin help dis girl please kallon juna sukayi don basu gane wace yarinya yake magana a kanta ba lokacin.
Ganin ya nufi dakin mami suka bi bayan shi sai ga mami ta fito tana ganin su tare dashi tace yawa don Allah wata ta taimakawa zainab zuwa wurin mota mu kaita asibiti.
Jin an ambaci sunana yasa Nazira ta fara ja da baya Rufaida ko ko motsi batayi ba a inda take sai salma ne tace mami bata da lafiyane dama.
Wallahi salma ki san yarinyar nan bata da hankali bata jin dadin jikinta ta shige daki ta kulle kanta a ciki haka.
Salma ta matso tana dafani tare da fadin sannu zainab tana kokarin tayar dani zaune.
Haka ta dan rikeni har zuwa wurin mota data ganshi tsaye shida jamal an bude kofar motar.
Mamine tacewa salma shiga salma muje tare don Allah da sauri tace to mami ko mami ta dauka driver ne zai jamu sai ji tayi yace jamal shiga muje tare.
Turkish hospital ya nufa damu da kwantace har ya gane wurin munyi sa, a akwai likitoci bamu dade ba muka shiga bayan yankar katin da jamal yayi baisan sunan baba na ba dole sunan mahaifin su yasa a katin don sauri.
Tare da mami muka shiga ganin likitan ya dubani bayan yan tambayoyin da nake amsawa da kyat gareshi.
Allura da maganguna aka ban sunso wai su dan kwantar dani mami tace aimin dai allura mu koma gida washe gari sai indawo in karbi sauran allura.
Haka muka juyo muka dawo gida zuwa lokacin har na fara dan jin saukin jikina haka muka shigo gidan a falo muka samu wa yanda suke gidan a lokacin.
Da ganin su akwai maganan da sukeyi a lokacin don yadda suke gaida mami da dawowa ba wanda ya tambayi yaya jikina daga cikin su.
Dakin mami ta kaini ina jin anty salma na fadin ku baku iya gaida mara lafiya bane ?
Ta fada tana shigewa dakin ta suka bita da fadin Amebo Olopopo suna hararan inda tabi zuwa dakin Nazifa tace waya sani.
Ko taje ta daukowa mutane ciki ne a gida Rufaida tace ko cikin wa yan nan katan na waje wani ya taushe yar iska yafi karfin ta ba.
No ku daina fadin haka don Allah Ruby dataki bin iyayyenta su tafi ta fada tace kun san fa wanan zargin abu mai girma idan kun zargeta da aikata zina alhalin batayi ba Allah na iya jarabtan ku kan hakan.
Kawai dai mu barta da samun wuri don samun wuri kan yarinyar nan ta same shi har ta batun zarta mu a yanzu.
Ku diba yadda guy din na ya fito a gigice dazun yana neman wai wanda zai taimaka ya kaita wurin mota.
Kyale dan rainin wayon banza kawai yana wani abu kamar bakin baturen dake jin warin mutane nina rasa me wanan yarinyar tayi haka gaba dayan su suke ji da ita a gidan nan haka Nazifa ta fada tana jan tsuki a karshe.
Ya kamata dai mu san mafita don wallahi garin kallon wuta kada kwado ya fada ciki muna nan zaune tazo ta samemu har tafimu kima a wurin su .
To yanzu meye abinyi kawai Rufaida ta fada a cikin damuwa sai Ruby tace a abinyi shine mu san mafita .
Don wata kila ladabin ta garesu ne yake ja mata kauna a wurin su kin san su don son girma kamar gyabo ai.
Kai ba wanan bane gaskiya Rufaida tace ni kawai nasan shegiya asiri taje gida aka kara bankadawa mami dasu gaba dayan su.
Ki duba ko jalal da jamal da muke zama tare duk a yanzu sun bari wallahi ke ni na tsani wanan yarinyar gaba daya sai na halakata ko inyi sanadin barinta gidan barni da yar iska kawai nasan abinda zan mata ai.
Daga dakin shi inda yake zaune yake kallon su shida jamal da shi kanshi baisan gidan akwai cctv ba sai yau ya girgiza kai tare da fadin wasu irin yara mami ta aje haka a gida.
Yaran nan ko mami ba zasu barta ba idan sun samu wuri ya fada yana mikewa zai shige daki sai kuma ya juyo yana fadin .
Kada inji zancen tv din nan a bakin wani a gidan nan ko mami kafadawa dashi zamu samu matsala sosai dakai a rayuwan mu.
Na dade ina zargin yara nan ba zaman banza sukeyi tare da mami ba tunda naji suna gidan nan zaune yanzu.
Hannu jamal ya daga duka biyu yana fadin believe me yaya kowa ba zan fadawa wana magana ba ko jalal ne yace is better for you don ban son yawan magana.
Nikan barci nayi sosai a dakin mami na samu gadon mami na haye ka laushi kamshi da sanyi na tashi yana shiga min hanci a hankali.
Duk da halin rashi lafiyan da nake ciki bai hanani jin dadin kamahin dake shiga min hanci ba lokacin.
Sai goma da rabi na dare na falka koshi mami ce da Aisha a dakin suke magana yasani bude idona sannu zee mami ta fada tana kallona tare da tambayana jikina.
Me zakici yanzu Aisha ta tambaya tana kishingide saman gadon mamanta da waya a hannunta tana kallo.
Mami ta kura mi ido tana so jin amsa da za bayar a hankali hannna ina share wayen dake kokarin zubo min a idona.
Tambayan ki ake ba kuka akace kiwa mutane ba a na tun safe nasa bakici komai ba a cikin ki .
Na amsa cikin karfin hali da fadin tea zan sha ina kokarin mikewa tsaye ina kuma zaki Aisha ta fada zanje inyi fitsarine na bata amsa.
Ina koarin nufar kofan fita daga dakin don ba daman in kewaya mami tana dakin ta don haka nake kokatin fita ba tare da nasan inda zan nufa ba a lokacin.
Sosai mami da yarta suka kula dani don sun nuna damuwan su a kaina sai anty salma da itama ba laifi don tana zuwa a kai akai tana gaidani da jikin.
Har naji sauki na fara fitowa falon don in bawa mami dakin da ko yaushe a dan kwana biyun nan ina kwance.
Ranan dana fara fitowa falon ne naga canji sosai wurin yan matan mami wanda hakan ya bani mamaki don fuska sosai suka sakarmin harda zolaya wai an taya naki sallamawa.
Ni dai nayi murmushi tunda ba saba haka nayi dasu ba dama duk da yadda nake hakana mike na yi aikin da zanyi a ranan don sai naga aikin da akeyi kamar baya fita da kyau.
Aiko mami na dawowa ta hauni da fada don ta gane nice nayi aikin cewa kawai nayi naji sauki mami.
Tadaiyi min fada ta fara cire kayan jikinta na fita dakin don bata wuri ta shirya a tsanake kamar yadda muka sabayi.
Sai data fito falo na koma dakin na gyara tare da nade kayan data cire a jikinta na wanko har bathroom din tas.
Tun ina jiran inji ance gobe ko jibi zamu tafi sai naji shiru saidai kawai ranan da muka cika sati da zuwa ranan da dare mami ke fadin su Rufaida su shirya zasu koma kaduna do hutun su ya kare .
Ina gurin jin haka yasa na kallo mami don banji tayi magana ba a ciki sai naji mami na fadin ina sane dake zainab ban manta da karatun ki ba ai.
Wata kila nan karatun naki zai dawo yanzu do zaman mu zaifi yawa yanzu a nan sai dai na duba naga abinda ya dace mami ta fada.
Basuji dadin yadda mami ta tsara ba don ba karamin dadi duke ji ga wanan zaman namu ba don ko yaushe suna fita shoping da yawo sun samu dakewa sosai don mami bata zana gida sai yamma take dawowa gida.
Dole ba don sun so ba suka fara shirin komawa kaduna salmace kawai bata nuna damuwanta a fili akan hakan ba wucewab sune yasa mami bani daki na kaina inda zan zauna kamar yadda nake da dakina a kaduna gidan ta.
Haka ba karamin dadi yai min ba sosai a raina don dama a takure nake saboda zama da mami da nakeyi daki daya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣6️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAU DA GOBE NA ALLAH NE YAN UWA MU RIKA SHUKA ALHERI DON WATA RANA A FADE MU KO BAMA KUSA, UBANGIJI ALLAH KA KARA MUNA IMANI DA DOGARO DA KAI YA ALLAH, , ,
IDAN NACE KI BIYA INA NUFIN NA KUDINE YAR UWA KI GUJI SHIGA HAKKIN DABA NAKI BA DON ALLAH ALLAH YASA MU DACE .
DARI UKU NE KACAL YAR UWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DA AMINCI.
Zance tafiyan su rufaida baimun dadi ba don gidan ya kara komawa silent yanzu da suka tafi ashe dan mutum ko yaya kake dashi yana da rana a gareka.
Yau na kara fahintar hakan wanda dama nasan da hakan tun barina gidan da har nakan ji kewan yan gidan mu ga baki daya har Asabe da lantana.
Sai gashi dan sabon da nayi da zama da ukuban su Rufaidama yanzu ina kewan hakan gareni.
Sai ya kasance in zauna ni kadai ina faman tunane a guri daya idan kowa ya fita zuwa nasa tsabgan sai in rage dagani sai gwarawan yan aikin nan dake gidan.
Gashi ni ban saba dasu ba don ko yaushe a cikin yare suke su yau ma kamar kullun bayan fitan mami da Aisha data wuce school na gama gyaran dakin mami na koma dakina nayi wanka.
Na shirya a cikin wani bakin dogon riga da Anty Aisha ta ban zuwan mu Abuja don ganina da yan kayana kala hudu dana dauko da zamuzo kullun.
Dan kalin rigan na daura a kaina mai kawai na shafa a fuskana don ni ba gwanan kwaliya bace dama haka.
Duk da hakan fuskana ya dan fito fayau falo na dawo na zauna ina karyawa ina kallon tv daya zama min abokin hira yanzu.
Cibi biyu na kai ga bakina na orth din da nake sha muryan Nuriya matar yaya mamud ya ziyarci kunnena don ni nikan manta da itama a gidan tunda ita bata shiga mutane kuma bata barin yayan ta suna mamuwar kowa a gidan.
Fadi take ke zeey ki zo ki gyara min part dina yayi datti da yawa yau ina son a gyara min shi don Abbani yai magana kan hakan da cewa yaya mamud kamar yadda take kiran da dashi.
Yau kan na turza don bansan sanda bakina ya furta anty Nuriya yanzu nake karyawa idan na gama zanzo na bata amsa.
Ke yaushe har raini ya shiga tsakanin ni dake haka ta fada niko a raina nace wata sabuwa kuma waini mena tarewa mutane haka kowa yake jin haushina dan abu kadan zai zama min matsala babba ga kowa.
Maza ki tashi kije kiyi abindana sakaki kafin na bata maki rai ta fada a hasale tana mai tsureni da idon warning gareni.
Kokarin aje cup din dake hannuna nake naji muryan Jamal na fadin ke dauki cup din ki ki karasa karyawan ki kafun ya juya wurinta yana fadin.
Baki da tausayi wallahi yarinyar nan tun safe take tsaye sai yanzu ta samu kanta take karyawa zakice ta bar karyawa tazo maki aiki.
Wani juyawa tayi tana masa wani kallo tare da fadin kai kuma fa dan rainin wayau da zakazo kaja min raini a wurin yar aiki haka.
Aiki na sakata a part din mu kuma dole ta tashi ta tafi yanzu don yanzu nake bukatan ai min shi.
Bazata ba sai ta gama karyawa ya kara bata amsa yana kallona tare da fadin koma ki zauna nace ki karya idan kin gama sai ki tafi.
Ba abun mamaki bane don ka fadi haka jamal tunda kaganta haka kana da mugun nufi a kanta kamar yadda kuka saba yi a turai ai.
Sheri zaki min ya fada a hasale yana nufota ni kan hannu na dora a kai ina shirin yin ihu don yadda ya nufota sai Allah zai gyara yau a tsakanin su.
No no no jamal don Allah please kada ka tabata be a man kada ka karasa wurinta please.
Nan dai hayaniya ya kaure a tsakanin su ta fadi ya fadi karshe dai ta juya tana fadin ke kuma karamar yar iska kada kizo ki min abindana saki kiga abinda zan maki yau gidan nan.
Ba zatazo ba din kiyi duk abinda kikai niya a kanta jalal shima ya fada a hasale ta juyo tana fadin sai ku gayawa wanda baisan abinda kukeyi da ita ba a gidan nan.
Innalillahi ai bansan lokacun dana dora hannu a kai na fara rusa kuka ba karyawan da banyi ba ranan ke nan.
Don sukan tana wucewa suka tafi suna fadin yau zasu gamu a gidan nan dole sai ta fada abinda take nufi ko su casa ta son ransu nan suka barni tsaye ina kukan takaicin zargin da maman su Amir da Amirah tayi min kan tagwayen mami din.
Banda yadda zanyi duk da sunce kada in tafi haka na aje abin karyawa na na nufi part din anty nuriya din da zuman mata aikin data sani.
Gaskiyane part din kan yayi datti kamar ba mace a cikin sa da take rayuwa ko namiji yabar gutin shi haka za a iya kiranshi da kazamin namiji.
Sai kaga mace fes a waje amma kaje muhalinta sai ka raina mata wayau kan rashin gyaran wurin zaman ta.
Kayan dake saman kushin na duka na fara nadewa hankalina ya dauku ga abinda nakeyi kawai ba tsamani naji saukan mari a fuskana lokaci guda.
Na dago dan gani waye yai min wanan aikin na kara jin wani a tsakiyan fuskana tana fadin gobe in kara saki aiki wani dan iska a gidan nan yace kada kiyi.
Ke har kin isa me kika dauki kanki banda matsiyaciya kaskantatar yar aiki kawai kina nufin ni kyauki da wani halin ki can zai rudeni ne matsiyaciya mai zubin karuwai kawai.
An walla, , , , kofan da aka bankadone yasa ta kasa karasa maganan da take son furta min ta juya tana kallon wanda ke tsaye a kofan nasu.
Ni dai ina tsaye har lokacin zafin marin bai gama sauka min ba sai wani dishi dishi nake gani idan nayi yunkurin bude idanuna lokaci guda.
Muryan Jalal ne yake fadin idan kika kara dukan ta yau sai kin raina kanki gidan nan wallahi kinji na fada maki.
Jalal ya juya gareni yana fadin ke kuma fito part din nan tun kan ranki ya kai ga baci yayin da Nuriya ke kokari daukan waya don kiran mijin ta tana durawa jalal din zagi ta uwa ta uba.
Bayan mun fita part din ne ta kira mijin ta fada mai karya da gaskiya shi kuma ya hau karfe uku duk suna gida gaba dayan su don mami tace su hadu a gida.
Yayin da har lokacin ina daki tundana shige ban fito ba ga fuskana gefen idanuna ya hau ya rufe sosai har bana gani dashi.
Sai faman tunane nake a raina duk kokarina wajen kaskantar da kaina a garesu don gujewa faruwan irin haka .
Wanda mami da yaranta a kullun suke kokarin jana a jikin su suga dai na sake a cikin su wanda ni na kasa hakan don kada in shaga irin wanan matsalan a cikin su.
Ina nan a kwancen da nake ina faman tunane muryan Anty Aisha ya daki kunnena tana fadin zainab mami na kiranki a falo.
Na dago dan mata sannu da dawowa tana ganin fuskana tace ke meye haka fuskanki ya sauya lokaci daya ?
Cikin dakewa da karfin hali nake fadin sannu da dawowa Anty Aisha yyawa me ya sameki haka ta kara fada.
Ba komai anty na fada ina kokarin tashi daga saman gadon ta juya ta fita daga dakin.
Ina tafe na sa gefen gyalen dake kaina na dafe idon dashi abu ga farin mutum lokaci daya fuskan nawa gaba daya ya canza kala ga alamun hannun Nuriya radau a fuskana.
Gaba dayan su sun zuba min idanuwan su a kaina har na karaso inda suke zaune na kai kasa na fara gaida mami data kura min ido kamar ta suma da mamaki.
Kafin in dan dago ina kare fuskana ina gaida yayan nata zeey meye wanan ya bata maki fuska haka mami ta fada tana kallona don jin abinda zan fada.
Kowa falin ni yake kallo yayin da mami ta kara maimaita maganan ta gareni kafin in magana Nuriya tace nice na mareta.
Har mijin ta saida ya juya yana kallon ta don abinda ta fada lokaci guda cikin rashin damuwan da hakan.
Akan me kika duketa haka Nuriya mami take tambayan ta cikin mamaki har lokacin.
Don me zan sakata aiki mami take zuwa lokacin dana umurceta tazo don kawai wanan dan rainin wayau yace kada taje tana nuna jamal a hasale.
Shi dagowa yayi don yin magana sai lokacin Jafar ya dakatar dashi don tun zuwana kanshi na kasa yana dakilan wayan shi cikin ko in kula da wanda ke wurin gaba dayasu.
Jamal me zaka fada tunda ta riga data fadi itace tai mata hakan da bakinta yanzu ta kuma fadi dalilin yin hakan gareta.
Sai akace a duketa haka ko boyace na sayo ai ba za ai mata wanan dukan ba haka balle ba boya bace karbo ta nayi hannun iyayyen ta don kawai ta taimakawa rayuwana.
Ban kawo don wani aiki ko aikin wani a gudan nan sai nawa bukatan ni kadai da take min kuma tana da kokatin wurun aiwatar min da komai tun kan na fada mata abinda zatayi min.
Haba wanan dukan haka ai abin yayi muni komai tayi maki ai zaki bari in dawo ki fada min sai nayi mata fadan hakan .
Koni dana karbota wurin iyayyen ta aiba zan taba mata wanan duka haka ba don itama mutum ce kamar kowa a gidan nan.
Ok mami ke nan dai yanzu na fahinci da sa bakin ki yaran nan sukai min rashi mutunci ke nan wanan banzan yarinyar mara mutunci da asali ta fini yanzu a gidan nan.
Nuriya mind your language bakin ki yasan abinda yake fada bayan kiyiwa yarinyar nan irin haka kuma zaki kirani ki fada min karya don kawai ki hadani fada da yan uwana.
Dama nasan haka zai kasance ai don wanan yarinyar ba karya su Rufaida ke fada ba ta asirce kowa a cikin ku har mami din gaba dayan ku tasa an maku asiri a kanta.
Enough enough Nuriya bakin ki yasan abin fada a nan kada ki kawo muna wanan shirmen naku ba banza yaya mamud ya kara fada a hasale.
Tashi tayi tana fadin aida rama mata kayi zaifi da wanan hasalan da kakeyi don kawai na mari wanan .
Mami ne ta daka masu tsawa tana fadin ya isa haka ki dawo ki zauna idan ki gama fadin abinda ke ranki.
Kamar ba zata zauna di ba kome ta tuna sai ta kai zaune din tana kada kafa mami ta sauke ajiyan zuciya ta fara magana.
Da farko ke Nuriya a kanki zan fara don ba zan tsaya kina fada min magana cikin rashin mutunci a gaban diyana ba haka.
Don dan kuka shike jawa uwar shi jifa, sai dai kinci albarkacin darajan abu biyu da kike ci gareni har kullun a wurina.
Shine auren dana da kuma kasancewar ki uwar jikokina a yanzu wanan damar kike ci har kullun a wurina don ba zan so saka matar dana a gaba idan ba haka ba ke kinsan wani abin ko ance kiyi min shi ba zakiyi shi ba duk da kudin da kike takama iyayyen
Sai yaya mamud ya dukar da kanshi don ya gane me mami take nufi da maganan ta saboda halin Nuriya a ku)un magana ya taso itace bata da gaskiya.
Mami taci gaba da fadin saidai zanso ki gane cewa ba zan lamunci aibanta mi diya ba ko zargi su a kan zina.
Mami ni kar,a laka min abinda ban fada ba fa a nan don kawai ana jin zafina kowa ya taso sai yace banyi daidai ba .
Don hakane nake nisantar kowa a gidan nan hakan baiyi ba har sai wani ya takaleni kuma inyi magana ace banyi daidai ba.
Yanzun wanan mara galihun tafini daraja da kima a wurin ku ake nufi tunda itace mai gaskiya ke nan don kawai taimin ba daidai ba na hukuntata.
Who are Nuriya who are you by the way har kina wani fadin tayi maki laifi kin hukuntata akanahi ke kika dauketa aiki a gidan nan ko wurin ki take.
Ke ba zaki iya yin aiki ba ki zauna da masu aiki kuma kin hana hakan saboda bakin kishin dake damun ki.
Mikewa tayi tana fadin na hana ka dauki yar aiki mamud don ban so kai din ban yarda da kaiba da har zan dauko wata yar aikican in aje wurina.
Daga yau na hana kowa saka wanan yarinyar aiki ko taba lafiyan jikinta wallahi wallahi ko yaya nake da mutum a gidan nan ranan zai hadu da fushina.
Wanan yazama na farko na karshe a gidan nan da wani zai kara taba lafiyan wani zainab yace kamar kowan ku nan dan haka a bani guri ban son wani magana kuma daga yau.
Tana fadin haka ta mike zuwa dakin ta a fusace yayin da nake durkushe a gefe kujera tafiyan mami Nuriya ta mike tana fadin wallahi mu zuba da kowa a gidan nan kan wanan yar iskan kowa ya tabani tabashi zanyi.
Binta da kallo sukayi kafin su dawo da kallon su gareni inda nake rakube ina hawaye don tashin hankali dana gani ranan.
Da hannu ya nuna min hanya na mike simi simi na basu wuri yaya mamud ne ya kawar da shirun da fadin.
Ni Nuriya zata watsawa kasa a ido haka kwata kwata banji dadin zaman mu da ita kullun a cikin fitina muke.
Yau ma nasan haushi fadan da nayi mata na gyaran wuri ne ta sauke akan yar mutane haka.
Bai bari dan uwan ya gama zancen shi ba ya mike zuwa dakin mahaifiyar su data shige ranta a bace ya sameta dakin.
Shiko yaya mamud yaci gaba da fada da matar shi ranshi a bace yake fadin.
Ya mike yana fadin nasan maganin yar iska ai bazata zan mata a gidan nan sai ta gane bata da wayau.
Saidaya shige jalal ke fadin kamar da gaske din zai iya hakan yanzu kila hakkuri zaije ya bata.
Suma mikewa sukayi zuwa dakin mahaifiyar tasu suka samesu a nan suna wani hira da dan lelen nata a gurin.
Karfe biyar na bar dakina zuwa na mami don gyarawa ita kadai na samu a dakin da sallama na shigo dakin na duka har kasa ina gaida ita kafin in dago don fara aikin dakin.
Kinsha maganin dana aika akai maki dazun take tambayana nasha mami na fada ina wasa da yan yatsun hannuna a hankali.
Kamar zata sake magana sai kuma tayi shiru taci gaba da duban takardan dake hannun ta ko ina na dakin saidana gyara kafin in fito dakin kusa magariba yayi nan na samu matar da aka dauka don shara tazo ta fara aikin ta .
Don faruwan avi mami tasa a kawo mata yar aiki wanan mai sharan bahaushiyace ita don ina gaida ita take amsawa naji hausanta na gane ita din bahauace ba kamar matan nan biyu gwarawa masu girki bane.
Tun ranan shakuwa ya shiga tsakanin mu da matar da ake kira da hannatu yar ktsinawa irin matan nan ne da suka dade da fitowa bariki don har sigari take sha a boye.
Nima dai rabon in gan tane a cikinyanayin yasa na rutsa da ita can bayan daki ta labe tana shan abinta na juya da sauri zan koma naji tana fadin a cikin kokarin kashe tabar da sauri yar hjy kamar yadda take kirana dashi.
Ina nan ina wanan jarabar tsiyar da muka sawa kanmu ina dai ba zaki fadawa kowa ba halin da kika sameni wanan zancen.
Da sauri na girgiza kai tare da fadin indai nice babu maijin wanan a abakina insha Allahu ina kokatin wucewa don natsani warin taba a rayuwana.
Duk dan dakata min inzo har lokaci bata yarda dani don ta fahinci jikina yana rawa a lokacin.
Ina kallo ta ballo goro daga haban zanin ta tura baki tana taunawa ta kakabe zanin inda ta zauna a kasa tana fadin wanan abin ya zama muna jaraba a rayuwa.
Kinsan a zamani mu idan budurwa takai budurwa har bata shan sigari to bata cika wayayyan mace ba ke nan.
Tun wanan lokacin mula koyi wanan cacan kashi kudin don ko nairan ka ta karshe ke nan sai ka fitar kaya zakaji dadi.
Ni dai a kage nake na bar wurin nake fadin dama ban ganki bane a cikin gida sai nayi tunanen ko kina nan shine na biyo ki.
Yo ai ina nan kedai jarabarce ta motso min shine nazo indan rage zafi kai.
A tare muka jera zuwa cikin gidan idon ta mirsisi kamar bata sha komai ba taci gaba da sha,aninta
Cikin sati daya kawai mun saba da hanne wace na lakawa mama hanne nake kiranta da hakan don girmamawa .
Zama da mama hanne yasani cikin farin ciki da walwala sosai don zata zauna tayi hira dani kamar sa, anta nake gun ban iya bata amsa har yakai yazu ina bata zamu zauna tana ban labari ina kwasan dariya.
Da sunan kwana hudu sai gashi mun share wata a abuja lokacin ne mami ta fara shirin ziyaran kaduna.
Wanda gaba dayan mune zamu tafi gidan a yadda naji suna fada mahaifiyar mami ce bata da lafiya shine za a tafi gaida ita.
Shiri sosai mami keyi don zuwa gida nikan nafi kowa murnan hakan kamar ance damun isa zan tafi ancau ne ranan.
Ni kan na dauka yaya Jafar ya koma inda ya fito ne ashe wai tafiya sukayi tare da su jamal sai kwatsam gasu sun dawo ana saura kwana daya mu tafi kaduna.
Mama hanne kan tunda tayi arba dashi tasha jinin jikin ta a zaton ta wai yanayin sa yai kama dana yasanda tunma dataga security din shi ta kara tsurewa da al,amadin shi.
Take tambayana nake fada mata dan mami ne amma ni ban san aiki da yakeyi ba, ta sake fadan mutum.haka ba yar dariyan nan ko fara,a a fuskanshi.
Dariya sosai nayi har ina dukawa a inda nake zaune sai kamshin turaren shi mukaji lokaci guda.
Key din shi yake miko min ba tare da yayi magana ba, amma na gane me yake nufi dakin shi yake so a gyara mai ke nan.
Yana miko min ya juya ya futa a cikin wani irin tako na mazan zamani da suka suka san ta kan duniya sosai yake tafiyan.
Ban tsaya jiran komai ba na mike don cika umurni duk da mami ta hana inyiwa kowa wani aiki ita da kanta takan umurceni da inje in gyara mai dakin nasa.
Tura kofan nayi na shiga dakin da sallama duk da nasan ba kowa a daKin hakan bai hanani inyi sallama ba.
Idonane ya fara arba da wani kwalba dake aje saman table din dakin nasa ga abin cikin sa an zuba a kofi ansha an aje rabi.
Da mamaki nake kallon abin don ban taba ganin kwalban abin sha irin sa ba nidai na fara kawar da takardun dana gani a saman wani table naji an turo kofa da karfi an shigo dakin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH KA GAFARATA MUNA ZUNUBBAN KABA MU IKON AIKATA ALHERI A RAYUWAN MU DUNIYA DA LAHIRA AMIN.
DO MIN SAMUN LITTAFIN NAN CIKKAKE ZAKI IYA TURA DARI UKU TA WANAN ACC 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN MTN NA DARI UKU KACAL NAGODE UBANGIJI YA HORE YA BADA IKON BIYA ALLAHUMA AMIN ALLAH, , , ,
Idona a kan abin ina dan juyawa a cikin kofi naji wanan tsawan daya daka min sai da hanjin cikina ya kada don tsoro lokaci guda.
Allah ya gyara ban sale cup din ba ya shigo ya karbi abinsa yana mai bina da wani kallo mai kamar na tsana.
Wayace ki taba min wanan ya fada rai bace kamar da gangan na taba mashi abin bashi ya turoni dakin in gyara ba.
Dan marairaicewa nayi ya karbi abin shi zuwa daki sai gashi ya fito da cup din ban san inda ya juye abin ba.
Fita yayi daga dakin ba tare da yayi min magana ba hakan ya bani daman yin aikin a tsanake.
A gurguje na gyara komai duk da hakan dakin ya gyaru da kyau na kulle masa na fito na kai key din dakin mami.
Nikan don doki har na shirya kayana tafiya kawai nake jira washe gari na zata tun safe zamu wuce sai naga sabanin hakan.
Saida yamma bayan la,asar muka bargidan zuwa filin jirgin ashe da jirgi zamuyi tafiyan kuma.
Karfe shidda na yamma duk muna gida a lokacin har na bude dakin mami ina gyara don tun tafiyan ta dakin a rufe yake.
Sai yau da muka dawone ta miko min key na bude duk da a gyare muka barshi da zamu tafi hakan bai hana yadan yi kuraba.
Na gyara har bathroom na fito zuwa dakina shima na gyaro na shiga wanka dongon riga silk mai adon kamfala ne na dauko daga cikin kayab da anty Aisha ta bani na saka.
Saida nayi sallah har isha,i na fito falon don yunwa da nake ji lokacin in samu abinda zanci a cikina.
Suma mutanen gidan gaba daya a falo na same su saman dining suna cin abinci mami da yaranta maza su hudu sai yan matan mami din gaba dayan su har anty Aisha.
Simi simi na fito na zo diban abincin wasun su suka kuro min ido hannuna rawa na dibi abincin ina jin mami tana waya tana fadin muna kaduna yanzun haka.
Insha Allahu da safe zamu shigo Igabin naji tana fadi haka yasa na san zasuyi tafiya washe gari saidai ban san ko dani bane.
Diban abincin na juya zan wuce naji muryan yaya Jafar na fadin ke saida hanjin cikina ya kada don jin muryan shi saidai ban tabbatar ba ko dani yake don kaina na duke na basu baya.
Na kara takawa gabana na mumunan faduwa da ban san dalilin haka ba duk lokacin danaji muryan yaya jafar din duk da ina tsron kowa a gidan saidai nashi yafi yawa a zuciyana.
Ko dan ganin kowa ma yana shakarshi ne a gidan don tsare gida irin nasa .
Haka naci gaba da takawa cikin karfin halin zan tafi dakina inda na saba zama inci abinci hankali kwance zuciyana cike da addua nake tafiya.
Ya sake fadin come and join us ina zaki da abinci ga kowa nan a zaune hakan yasa nasan lalai dani yake magana na juyo a hankali.
Yana rike da cibin abinci da yake ci a hannun shi ya rike baikai a baki ba gabana na faduwa yace.
Daga yau a nan zaki rika cin abinci tare da kowa kinji abindana fada maki yana nuna min kujera da hannun shi .
Kai na gyada mai, tare da nufar gurin kujeran dake saiti da inda yake zaune babu kowa saman kujeran na zauna.
Idanuwan yan matan gidan duk a kaina bama su kadai ba har mami dake waya a lokacin idonta yana kaina.
Ko ban daga kaiba nasan akwai idon dake kallona a lokacin don jikina ya bani hakan ba ido daya ba ba biyu ba kodana dago kai duk idanuwan su na a kaina suna kai cibin abinci a bakin su.
Tundana zauna ya maida hankali gun abincin dake gaban shi hankali kwance yake kai cibi a bakin shi a hankali .
Daga mami har ya matan dama su jamal suka dago ido a sukwane suna kallon shi shiko ko a jikin shi.
Sai juya cibin dake hannuna nakeyi na kasa sakin jiki inci abincin yadda ya kamata a wurin.
Yadda kika san guba haka nake hadiyan abincin ba wai don baya da dadi ba don hadine na musanman akayi don zuwan su yau din su mama kande suka girka abincin mai rai da lafiya.
Mikewa yayi tsam mami tace har ka gama cin abincin ke nan ko rabin plate fa baka ci ba ba tare daya juyo ba yace mami iam ok zanje na kwantane.
Allah tashe mu lafiya mami tace yace amin yana tafiya sai jalal yace but yaya security dinka za a fada masu sutafi ke nan tunda ka shige ko ?
Na sallamesu tunda muka fito massalaci dazun idan sun gama zasu tafi ya bashi amsa yana tafiya da dan sauri kamar mai uzuri.
Mami ma bata dade ba wurin ta mike tabar falon sai mazan da suma suka mike lokaci daya falin ya rage mu kaida a ciki.
Duk lokacin danayi yunkurin dago ido sai in samu ana aika min da wani irin mugun kallo da tsana dan dama salma da Aisha su ba kallon tsana bane saidai kallone mai kama dana mamaki lokacin.
Amma dai yarinyar nan kina da sa, a yau kece yaya hero ke ba umurnin zama a saman table kici abinci tare da kowa a gidan nan.
Ke ko ba dole ba tunda ta iya makirci kamar ta mutu ta mairaraice ita gata Allah ba dole ta bashi tausayi ba Nazira ta fada
To kodai kin zauna a cikin mu ba a dai taba canza maki suna daga zainab yar aikin mami zuwa diyar gidan nan kamar kowa Rufaida a fada .
A, a, za a yi kiranta ki da yar gida mana duba yarda yan kwanakin nan gaba daya tayi fresh da ita haka duk sai suka kalloni lokaci daya.
Nagaji da cin fuska na mike don barin wurin, dama abincin ya fita min rai lokaci daya na dauki plate din zuwa kitchen.
Ina ruwan ba saban ba yau har wanan ce zata bar abinci haka bataci don samun wuri.
Ban kara fitowa dakin ba don na gamawa mami komai itama nasan ta gaji ta kwanta tunda akwai tafiya garesu washegari.
Nasan da zancen tafiyan mami don naji tana waya kan tafiyan yasa na tashi da wuri na nufi dakin ta koda abinda zata sakani a lokacin.
Aikuwa iba shiga dakin na samu ta fito daga wanka saida nayi mamakin hakan don bata ko tsaya jira inzo in wanke bandakin ba ta shiga.
Gaisheta nayi na nufi bandakin har ta karasa shirinta na dawo na fara gyara don ko kadan ban kawo dani za a tafi tafiyan ba don banga alaman hakan ba.
Hankali kwance nake aikina ina shiryawa maki kaya kamar yadda ta umurceni inyi mata anty Aisha ta shigo dakin tana gaida mahaifiyar nasu.
Bayan dun gaisa mami ke fadin ina fatan kin shirya dai don banson bata lokaci ga tafiya kin sani dai.
Mami wani shiri zanyi kauyefa zamu tafi banga abinda zan shirya bani ko haka zan iya tafiya ai ta fada cikin zolaya.
Mami tace da ita ai kauye garine don akawai yan Adam a ciki na dauka dai daji zaki tafi ai ta kwashe da dariya don tasan ta tabo mami din .
Gaba dayan mu zamu tafine mami ta tambaya tana kallon mahaiyar nata lokacin da ni kuma nake masu dan murshi don jin amsan da mami din ta bata.
Naji mami tace eh dake da yan uwanki maza ba na fadawa kowa tunjiya don kada yau su kawo min wani zance na daban.
Hae su Nazima ta sake tambayan mahaifiyar nata sai mami din tace haba dai Aisha ai ba zan sake zuwa dasu ba tunda da biyu suke zuwa
Tun wancan zuwan da sukai min tsiya nasha alwashin ba zasu sake zuwa garin nan da yawuna ba.
Mami samu,naka ne fa ba wani gari ba can Aisha ki fice mun a ido tun raki bai kai ga baci ba a dakin nan.
Zainab jeki ki shirya kada ku bata min lokaci ta juyo inda nake tana fadi hakan yasa na gunde dariyan da nake masu jin an abamci sunana ga tafiyan nasu da za,ayi wanda ni banso hakan ba don sati biyu da komawan school ke nan mu.
Dole na mike ba yadda na iya na koma dakina na fara dan shiryawa yan kayana kala uku a dan karakin jakkar da Aisha taban da zamu tafi kaduna.
Karfe goma safe mun karya sai kaya ake ta fita dashi ana sakawa a mota yan matan sunso subita amma mami tace ba zata dasu ba tunda suna raina mata gari idan sunje.
Ga motocin da za ai tafiyan dasu sai wani sheki suke ga hasken ranan daya fara gama gari suna daukan ido a ranan.
Suna falo zaune na fito da kayan mami zuwa wurin mota kamar yarda ta umurceni indauko zuwa bakin mota jamal yana gurin zai nuna min inda za,a saka jakkar kayan nata.
Wanan wau da ita za,a tafi halan Nazifa ta fada sai Rufaida take fadin kema ai kin sani itace yar miko min kawo min dole a tafi da banza.
Maganan yai min zafi sosai saida ai aikina ne din hakan don sun fadi hakan bakomai bane gareni tunda kowa yasan abinda ya kawo ni gidan ai shine aikatau.
Mota guda muka shiga nida mami da Anty Aisha sai driver nice a gaba zaune tare da driver suna baya a zaune su.
Tun kan a baro gida banyi magana da kowa ba har mukai nisa ga tafiya naji Aisha tana fadin waiko mami lafiya yarki take ?
Kodai abinda su Rufaida suka fadane ya bata maki rai kikai shiru tun dazun ?
Mami tace ai kinsan ita din ba gwana bace wurin surutu barta da saurin aiki kan kamar inji mema suka fada matane daya bata mata rai haka ?
No ba wani abu bane serious maganan su necan suke fadin wai ita dni ai dole aje da ita don yimin miko min .
Kai wa yan nan yaran akwai tsegumi garesu bari Allah ya dawo damu lafiya sai na masu tsiya dai a kan yarinyar nan .
Don banga abinda ta tare masu a gidan nan ba da suke matsa mata haka ko da yaushe.
A raina nace kayya mami kullun haka dai kike fada kin kasa yin maganin su haryau su kuma basu barni ba da fitinan su.
Wai mami yaya Jafar din ya yarda zai tafi gidan kawar taki ya duba yarinyar Aisha ta fada don a kawar da zancen .
Don tsuki mami tayi tana dauko abu a cikin jakarta tana fadin ai kin san hali shi dai.
Danayi mai magana dariya kawai yayi min ya mayar dani karamar yarinya sai na masa da gaske zai maida hankali wurin abinda nake son shi dashi ai.
Mami da kin barshi ya zaba da kanshi nima ban goyi bayan wanan auren hadin ba kindai ga yadda na yaya mamud ya zama a karshe ai.
Ni dai ina gaban mota ina faman tunane a raina har muka kai garin samu,naka din sai bin garin nake da kallon irin ni,imomin da Allah yai masu a garin.
Wani gida motan mu ya tsaya duk da anyi gyaran gidan daga wajen shi amma mutum zai iya gane tshon ginane na mutanen da masu shi a lokacin akaiwa gyara.
Tundai in ka shiga daga cikin gidan zaka samu part part gidane babba da ya kumshi jama, a masu yawa sosai a cikin sa.
Sai tafiya muke ana faman yi muna sannu da zuwa har muka kai kofan wani part daya sha gyara sosai an masa irin ginan zamanin nan .
Wasu mata biyu ne suka fito daga part din suna faman yi muna sannu da zuwa dukkan su na shedasu don sunje abuja na san su a lokacin.
Da sallama muka shiga falin babba wanda yasha gyara da kujeru manya manya na zamani komai dai na bukata a kwashi a falon.
Sai hoton wata dattijuwa dana gani tayi gwagoron irin daukan da akaiwa photon sai kuma photon mami da mijin ta duk da bantaba gani wanan photo ba amma na san fuskan marigayin mijin nata don akwai photunan manya a falin mami har gidan su na Abuja a saka a falon gidan.
Mami bata zauna falon ba ta shiga daga cikin dakunan a ca nake jiyo muryan ta ni da Anty Aisha ne a falon zaune muka gaisa da sisters din mami din suna tambayan mu yaya hanya ?
Can murya mami ke fadin ina kuke ne ku shigo ga hjyn a daki zaune kuzo ku gaisa kafin wa yancan su shigo.
Mikewa mukayi zuwa dakin wata tshuwace a zaune saman gadon alfarama kamar ba dakin tsofi ba duk da tsohuwace matar hakan bai hanata kwaliya ba tana cikin atamfar supar a jikin ta.
Aisha kan muna shiga gadon da take zaune ta haye tana fadin wanan ce mara lafiyan da mami ta tayar muna da hankali ga mutum na gani garau haka ba alaman ciwo.
Tsohuwa mai barkwanci tana fadin ke kuma wanan shiga haka kamar matar limami chochi fa ?
Duke nayiwa shi dan Allah dai udan zaki tafine ki tafi kiba mutane wuri kina dagawa iyayyen mu hankali haka.
Daga inda nake zaune kafin taba Aisha amsa nace ina wuni mama sai ta mayar da hankalin ta a gurina tana fafin kedai yar albarka kunzo lafiya ?
Yaya hanya ya kuka barsu a can nace lafiya yaya jikin mama Allah sa kafara ne ?
Da alama taji dadin yadda muke gaisawa da ita din sai wasan baki take tana fadin amin yar albarka.
Niko ko yar taki da ake fadi kin samu ke nan yarinya haka mai hankali Allah yasa ku raka tare.
To mu da ba, awa addu,an a hana mu raka din kaji min tsohuwa daga ma kin samu anzo gaidake har da zaben yiwa mutane addu,a.
Muryan yaya mamud ke fadin ni ina matar take gani nazo kada ki tafi muna son ki a hakan ko dan kwanciyan hankalun uwayen mu.
Kaji ja,iri kice dasu kike tafe ashe yau ina da babban bako a garin nan mamuda yaushe ranon ka da garin nan tana kokarin mikewa tsaye da kyar.
Aisha ta mayar da ita ta zauna mami takai mata duka tana fadin Aisha yo ga tsiya karki balla muna tsohuwa garin shashancin ki.
Barta ai gani take kamar ta fini kwari a hankan yanzu sai in lankada maki dukan tsiya a wurin nan.
Duk aka sa dariya sai ga daya sister din mami ta shigo tana fadin hjy yau fa kinyi baki harda Jafar akazo gaida ke.
Mami tace har kwana kuwa zasuyi maki a nan sai ki shirya ke nan kedasu yau a gidan nan.
Tana tafin dadi da murna ta samu ta mike da kyar tana lale marhabi da manyan bakina yau kuce amarya nake sai na zaba ashe tana fita daga uwar dakin nata din zuwa wurin su ta taresu.
Zeey jeki dauko mi kayana ki shigo dashi dskin nan mami ta fada na mike saida tsohuwar ta gama fita na dan bi gefen ta na fito daga dakin.
Suna zaune dukkan su tana masu lale marhabin cikin jin dadi har na fito kayan da mukazo dashine aketa faman shigowa dashi gidan.
Jakkar mami dana Anty Aisha na dauko na shiga dashi daga cikin daki kafin i koma in dauko nawa sai kuma na rasa yadda zanyi da jakkar nawa.
Na dan tsaya daga kofa ni ban shiga ba sai da dayan sister din mami takece min dan Allah shiga da ruwan nan mikawa su anty in gama da wayan nan.
A lokacin na samu komawa dakin na samu mami ta kewaya ban daki Aisha kuma tana rashe rashe saman gadin tsohuwar tana waya.
Ruwan na aje masu kafin in dan samu sakon gado na aje dan jekar kayana a wurin na juyo ina fadin anty Aisha ga ruwan .
Da hannu tayi min alaman a, a na dai samu wuri na tsugunna duk da kishin ruwan da nakeji ban yarda nasha ba tun kan mami ta fito tasha.
Ta fito tana fadin an shigo da kayan nan duka zeey don miyan nan kada a zubar dashi don Allah fadawa Ramatu ta kawar dashi kada a zubar.
Don miyane mai yawa na zabbi dana kan saniya banda nama da mami ta saka a soya a zuba a babban ruba mai marfi kuma.
Na mike da sauri duk da ban san wacece Ramatun ba a cikkn su sai dai nayi sa, a suna falon dukkan su nake fadin mama Ramatu mami tace akwai miya a waje akawar dashi kada a zubar.
Ke wanan muryan wa zaisan kina magana a hanka yaya jalal ke fadi yana nunawa mama ramatun ni a lokacin.
Na sake maimaita abindana fada da farko tana fadin aikuwa gara da aka fada muna bari yanzu a kawar dashi gurin.
Umma ina key din dayan dakin yake akai kayan a ciki tana tambayan tsohuwar data mayar da hankalinta kan diyan mami da suka sakata tsakiya da hira.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GAREKU MASOYANA UBANGIJI YABA WUNI LAFIYA YA SADAMU DA RAHAMIMIN SA AMIN YA ALLAHU.
KI BIYA HAKKIN MU KI KARANTA A CIKIN SALAM DA SAKEWA DARI UKUNE KACAL 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA NA DARI UKU.
Ranan naga yadda ake nunawa jika so da kauna na gaskiya don tsohuwar kamar ta hade yaran su koma cikinta take ji basu kadai ba harni da nake bakuwa a cikin su bata nuna min bambancin hakan ba.
Ga tawa kakar saboda wani dalilu nata na daban ta turoni bitnin yin aikatau badon Allah ya hadani da uwar daki ta Allah ba.
Allah kadai yasan yadda rayuwata zata kasance a birni ba tare data damu da hakan ba ita nata butin dai shine ta samu kudi ta gareni kawai.
Basu bar dakin ba nan kowa ke zuwa taron su suna gaisawa su yaya jamal ne suka mike don zaga gari zama wuri daya ya ishesu.
Yaya mamud ya dade da fita daga dakin ya barsu yana fadin zai leka wani abokin shi ko yana nan suka bar yaya jafar dake faman aiki a cikin sytem din shi yamai da hankalin gaba daya ga abinda yakeyi din.
Ina zaune takure wuri daya na kurawa tv dake aiki ido ana wani shiri a kscm kaduna hakab yasa hankalina ya dauku ga kallon.
Ai bata jikaba tshohuwar ke fadi me take da suna tana murmushi take kallona nayi firgigit in dago kai sai naga ido shi a kaina.
Bakiji me na fadaba yake tambayaba kai na girgiza mai ina tasowa daga inda nake ki dauke kayan nan da suka bari a nan ya kara fada.
Sai lokacin nasan meya fada da farko na tashi da sauri na fara tattara kayan dake saman karamin table din.
Waini kan dan gidan iyami yaushene zaka kawo muna sarakuwa tshohuwar ta fada tana kallon shi.
Cikin basarwa da kalan maganan shi ba tare da ya dago kaiba yake fadin banga matar aure ba har yanzu.
Allah na tuba duk matan daka baro kaduna har Abuja bakaga mata a cikin su ba don tsaban ruwan ido idan an fada uwarka ta tare maka.
Ni yanzu nafi dason yaro yayi auren shi a cikin lokacin don wanan rayuwan baida tabbas dan rayuwan yanzu kadan ne.
Ba sai ki nema min ba tunda ke kinga matan a ko ina birjit yo ko cikin yan uwanka ka nema mana ko wanan yar ta uwarku ai irice ta kwarai gata da hankali har naji dama ace ta shigo cikin zuria na.
Ke kiji da kanki don Allah da wanan shirme da kikeyi an fada maki kowa irin kune halan ya fada yana zareww tshohuwar ido.
Ta sake dariya tana fadin kaji min dan kawai ido ma zaka zare min don kawai na fadi gaskiya ko sai mun kaika mararaba mun ma wankane kafin a soka.
Kinga idan kina matsa min da wanan magana idan na tashi na tafi ke nan ba zan dawowa ba ya fada kanshi duke.
Nasan zaka iya dan nema mai zubin jan fata kai dama Allah yaga abinda ya gani ya kaika can cikin su da zama.
Wanan karo kan tare dake zamu koma ai don naga kema dasu kikafi kama ai barni na mutu musulma tsohuwar ta fada.
Saiga mami ta shigo falin tana fadin hjy dake dawa kike magana sai ta ganshi a zaune take fadin a a aboki kai kana ciki ashe na dauka tare kuka fita ai.
Ina nan mami idan wanan tsohuwar bata daina damuwana ba zan bar garin nan yanzu ba sai anjima ba.
Zaka iya na sani damuwar dai nasan fadan so kankane takema da baka son ai maka ko ?
Kamar kin sani yar albarka daga zancen aure yake wanan halakon haka kamar an mashi maganar mutuwa shi.
Wai shi baiga mata ba duk garin nan nakece mai ga wannan yar taki tun ba a kai ko ina ba don ni na yaba da halaiyar wanan yar taki.
Da sauri mami ta juya inda nake ina daukan gorunan drinks a kasa take fadin haba dai hjy har abin nasa yakai haka kuma ?
Ai ba zan barshi ya tafi ba sai ya tsayar da matar da zai aura in yaso sai ya koma idan bukin ya karaso ya dawo ayi buki nima zaman shi haka a can shi kadai ya dameni yanzu.
Kaji maganar gaskiya don wanan da kike gani idan bakiyi da gaske ba baida niyar aure yanzu gashi ya fara zama magidanci.
Wani kallo yaiwa tshohuwar tare da mikewa lokaci daya sai kuma naji ta koma rarashin shi tana fadin ai kasan bama haka dakai.
Kada kasa mamuda yai muna dariya tun ba,aje ko ina ba yanzun fa na gama mashi tsiya a kanka yai fushi ya fita don nace kai nake so.
Yanzu ma zan fada mai ya dawo nabar masa ke ya dauka bana so ni don kin faye jininini da yawa yanzu.
Dawo dawo ka zauna na bar wanan jininin indai a kankane na isheka ni kadai ai dama ai baikai ciki ba zancen nawa ina ka taba ganin mutum ya dabawa cikin sa wuka ?
Komawa yayi ya zauna sai abin ya bani dariya har bansan lokacin da sautin dariyan ya fito min fili ba.
A, a a takwarana dariya kike min kuma don ina neman shiri da maigida a gaban ki ?
Hararana yayi yasa na bar falon na koma daga wajen dakin na zauna saman dan dakalin dake wajen ina kallon mutanen gidan dake gittaya tako ina.
Sai da ta fito da niyar zuwa sallah mami ta biyo shi suna magana dashi mami ke fadin zeey a nan kuma kika zauna ne ?
Na juyo ina dan gaida ita take fadin shiga mana ciki koda yake ma anyi sallah azahar yanzu sai ki shiga wancan dakin dake gefe akwai bandaki a cikin sa a gyare dakin yake ku zauna keda Aisha.
Jin haka yasa na mike ina kokarin shiga dakin don kallon da yai min mai kama dana warning a lokacin.
Dakin da mami tayi min kwatance na shiga dakine gyarare da katon gado hade da mirrow din shi sai kujera three seater dake dakin gadon yasha gyara dakin yana ta kakahin turaren wuta.
Ban dakin na nufa na samu ruwa a manyan robobi aje dashi nayi amfani na dauro alwala nafito na tayar da sallah saman salyan dake dakin.
Ko dana idar ban zauna ba falon na fito na gyarashi tsab har waje duk suna cikin daki basu sani ba sai da mama habiba tazo fitane ta ganni take fadin yar nan kina nan kina aiki baki huta ba.
Hjyn su mami ke tambaya wace yace kuma sai kuma ta tuna dani take fadin au yar iyami ko ?
Wani aiki take kuma yarnan ki huta hakana mana ina hankalce da ke baki da son kazanta ta juya inda mami take kwance tana fadin.
Kin samu ya sai ki rike tada amana don Allah yarinyar tana da shiga rai lokaci guda gata da ladabi.
Sai naji ina kwadayin hada iri da ita don irice mai amfani ita din ba abin yarwa bane haka.
Hjy nima yarinyar ta kwanta min a rai sosai ina kulla da ita tankar yar cikina don bata da kyashi ga sanin ya kamata kamar wata babba can.
Tarbiyane idan kinga haka ta samu tun daga gida uwarta ta tarbiyartar da abinda yadda akeson ko wani da ya kasance sai ki kara himma wurin riko Allah ya taya ki rikasu.
Don tafi min wa yan nan marasa moriyan sau dubu a wurina sai hjyn tasu tace tafisu kan gaskiya yaron da ba sai kace ya tashi yayi ba yake abu ai yana da dadin zama.
Hjy kin san wancan zuwan da nayi da yaran nan iskancin da sukai min saida muka koma gida nake ji nayi masu tas wallahi.
Kiyi hakkuri dasu tunda su suka kawo kansu gare ki inma sunyi maki don kansu kowa ma zai girbi tsiyar shi ai.
Ke dai ki rike wanan bisa ga amana da yarda idan dai bata kauce bane don mutum mugun icce ne sai yaga ya ginu yace kaine makiyin sa daga baya Allah ya kare mami ta amsa da amin.
Sai dare mazan suka sake shigowa ina daki naji hayaniyan su ban daga daga inda nake zaune ba naji muryan mami ta fito daga uwar daka tana fadin.
Garin yai maku dadi ke nan ko kun shige cikin gari tun dazun ina shi aboki yake ne banganshi tare daku ba.
Wanan friend naki saike mami yana masallaci mun barshi wai yanzu yake son sallam guards din shi su koma kaduna su kwana.
Da daren nan tau haka dai yace don wai baiga inda zakaisu ba nan suwa ke nan tsohuwar ta tambaya.
Security din da mijin ki ke tafiya dashi don tsaro yaya jamal ya bata amsa a takaice take fadin.
Ikon Allah tafiyan ma sai anyi shi da masu tsaro ko may sai yaya mamud yace kin san su can hakan ai wani abu ne tundaga can aka hadu shi dasu aikin su sukeyi su.
Duniya inda ranka kasha kallo yanzu shi wanan dan figegen aron ne harda wasu masu tsaron shi.
Hjy mu a nanne ba a dauki tsaro da mahinmanci ba amma su can idan har kai wani abune dole kana da masu binka a baya ai massanman shi da sukeji da shi a can.
Waini na kasa gane aikin yaton nan sai jalal yace bako zaki gane ba don shi bros telent ne sosai ilimin shi yaja masa hakan.
Yanzu zai iya kera maki wani abu a wurin nan wanda sai kinyi mamaki don har abin yai tafiya da kafansa su ake kira da sciencetics mana masu fasahan kwakwalwa ikon Allah tace.
Tare da fadin gaskiya yaki aure haka har yana batun rufe arbain fa don in ba zan manta ba tun mulkin shagari na farko aka haifeshi ai.
Kai hjy wanan tashin tasgin haka kan friend dina yanzun dai ni abinda nake so kafin ya tura mutanen nan a cikin daren nan ai masu kokarin wurin kwana hjy.
Tshohuwar ta tambaya su nawane akace hudu hudu ta fada da mamaki tana fadin har karte hudu ke yawo dashi wanan abindai da nake gani.
Ikon Allah yafi gaban mamaki yau ace wai dannan ne Allah yaiwa bawa haka Allah ya ciyar daku baki daya suka amsa da amin.
A daidai lokacin da dan bawan ke shigowa yana waya tsohuwar ke fadin gama yanan ya shigo dayani.
Kai yanzu don baka da tausayi zaka tura yaran mutane da daren nan su koma kaduna don rashin imani.
O lord wanan kuma wani zance take hakane da shigowan mutum ya fada yana kaiwa zaune yana aje wayan da yakeyi.
Aboki wai yanzu da daren nan zaka tura security din nan su koma kaduna sai naga dare yayi ai.
No sun fasa ai mami uncle bello ya sama masu wuri zama da zasu zauna suna can sun tafi suga wurin kafin su dawo su dauki abinci.
Ko kaifa nace ko kai fa dan nan amma ka tura bayin Allah a cikin daren nan haka ai abin baiyi ba kamar dai ba mutane a nan.
Enough dan Allah waiwa ya fadawa wanan mai wa,azin ta damu mutane da wa,azin nan nata a gurin nan.
Kai rufamin baki aini yanzu nasan ba cikkaken namiji kake ba don a matsoraci nake kallon ka yanzu tunda sai an rakoka har karkaran mu matsoraci.
Daidai lokacin nake fitowa daga dakin don kira da mami tayi na amsa daga ciki.
Dariya ya bushe dashi bashi kadai ba duk wanda ke falon saida maganan ya bashi dariya yadda suke kwasa dashi din.
Barin gani idan baki tsorona din da gaske ya fada yana mikewa ya harota ta juya tana neman abinda zata kare kanta kafin ya iso gareta .
Tayi sa,a filo na kusa da ita ta dauka wai dashi zata kare kanta din tana kaimai duka yana dariya ya juyo a daidai lokacin na kawo wurin zan wuce sai ji nayi kumus nayi baya tangal tangal zan fadi.
Mami tace zaka karya min da da wanan karfin naka haka kamar na doki shi kuma ya juyo yana fadin oh sorry .
Tsohuwar nan kinga zaki saka in karyawa mami yarta don fitinan ki to yaushe rabo damuyi fitinan haka.
Ai rabu a gana arzikine dan nan wata ran idan kunzo sai kun tunani da wanan wasan da mukeyi yau ina Alh ina mahaifin ku sun kare.
Kowa yai wani iri a dakin don abinda tsohuwar ta fada wallahi hjy gashi yau muna kewan tsohon nan don da zaran zan shigo naga part din shi sai in tuna da lokacin da muke zuwa yana bamu mazzakwala muna sha yaya mamud ke fadi.
Kai mukan bamu sanshi ba gaskiya sai dai a photo jalal ya fada ai old man din nan ya kware mu daya tafi bamu sanshi ba.
Waike zeey kin debi abincin nan kuwa na juyo ina fadin ban diba ba mami yanzu na idar da sallah dama.
Jeki ki dibi abinci da wanan halin naki ga abincin mu can ankai mana daki tun dazu wanan nasu sai na mutane yayan ku yacan sai a samu yaro yakai masu idan sun dawo.
Juyawa nayi zan koma dakin don ban iya sake jiki suna wurin don haka na juya don na koma dakin hjyn su mami.
Banji me yake fada ba yaya jamal yace ke wai kizo ki zuba mai abinci yar mami.
Jin an ambaci sunana yasa na tsaya tare da juyowa na dawo zuwa inda abincin yake aje dan kallon yaya jamal nayi ina fadin wa zan zubawa.
Yaya jackson ya fada hankalin shi naga wayan shi rasa abinda zan zuba mai nayi don kuloli ne gurin zasu kai biyar duk an cikasu da abincin alfarma har da fate da mami tace tana so yaji gyada a cikin sa.
Fara bude masu kulan abincin nayi don ya zabi abinda ranshi ke so sai dai baya kallona hankalin shi naga waya yana rubutu.
Yaya me zan zubama na tambaye shi ina dan gurfane a gaban shi don ba dining table falon tsohuwar kamar can gida kaduna.
Ya dan dago kai yana fadin anything zaki iya zuba min Aisha ta fito daga dakin yaya mamud daya karbi plate din da mami ke shan fate yana dan sha yake fadin Essha kina gidan nan ashe tun zuwan mu ban ganki ba.
Ina kwance ne yaya ta fada tare da ratsowa ta zauna a hannun kujera tsakiyan su shi da yaya Jafar din.
Ke may kike a wurin nan ne haka ta tambayeni ya Jalal yace wai abinci akace ta zuba take tunane na dan kalleta ina fadi a hankali ban san may zan zubabane ai.
Oh shine kike tsaye a gurin ya mamud yace ka duba ai tana da gaskiyar ta kada ta zubama abinda baka so ne.
Wanan dai ina so inga matar shi kafin in mutu yaro da izza da isa kamar wani basarake dashi matar ka tana da hakkurin zama dakai haka.
Hjy naga fa yau sai yar tsama kuke da yaya Jackson tunda muka zo Jalal ya fada don shi yafi yawan dan magana bisaga Jamal dake da zubin yanayi ya jafar din wasu halaiyan su suna da kama sosai.
Aure nake son yayi hakana ya baku wuri kuma ku samu ku zaburo wanan gwauron ya tare maku wuri.
Muka fada maki samarin suka fada tace to ai shike nan tunda baku son a matsa mai yayi aure.
Wanan fa zata iya hada ma abincin nan duka tunda kace anything zata dauka kace tayima mix ne gaba daya Aisha ta fada tana kallona.
Ke zuba min ki daga min nan don Allah ya fada tare dan dagowa yana kallona.
Hasken kwan fitilan falon ya haskani gaba daya launina bada wani kala na daban ga mai kallona a lokacin.
Na duka ina zuba mai kullan gabana wanda sakwara ne a ciki ashe sai na bude kulan miyan shi dake dauke da miyan ganye yaji egushi da manyan nama na zuba daida don nasan shi baya cin abinci da yawa.
Mikewa nayi zan bar wurin ya kara fafin ruwan wanke hannu fa ba tare daya ko kallo inda nake bai yi ba yai magana.
Har suka bar falon ban kara fitowa ba sai bayan danaji fitan su sunawa mami saida safe na dan kara mintina na fito.
Kayan da sukaci abinci nake kwashewa yayin da nazo kan nasa naga spoon a ciki da alama dashi yaci.
A raina nace bakin bature ke nan abincin ma da cibi zaici don sallo ai kakar nan tasuce maganin shi.
Tas nayiwa falon kafin in shiga wurin mami ina tambayanta koda abinda zanyi mata kafin na kwanta.
Zeey a kwashe kayan abincin nan da sukaci nace na kwashe mami ki duba min kayan barci na a cikin kayana ki ban shike nan sai kije ki kwanta.
Har na kwanta a saman dogon kujera anty Aisha ta shigo tana fadin af namanta da charger na dakin tsohuwar nan dan Allah zeey dauko min.
A kofa na tsaya nayi sallama kafin in shiga dakin yanayin dana samesu a ciki nagane wani magana sukeyi mai muhinmanci a tsakanin su su hudu.
Tsohuwar da kuma kannen mami din duk suna zaune sunyi shiru da suka ganeni.
Sai mami ke fadin bakiyi barci ba ashe zesy a, a nace nake fadi charger anty zan dauka ganin suna kallona duk sai na tsargu .
Na dauka na fita da dan saurina daga dakin don ban son in dakatar masu da maganan da sukeyi din .
Washe gari tunda safe dana tashi nayi sallah na fara gyaran falon har zuwa waje ina jin hayaniyar su dakin har na gama wanka na shiga don mami tana cikin dakin da yan uwanta.
Sai kusan karfe goma suka fara shigowa falon ana gaisawa a tsakanin su babu muryan wanda nake jin tsoro don haka na fito na gaidasu da kwana ina jin mama Ramatu na fadin.
Ga abinci nan tun safe aka aje masu shi basu shigo ba ina shi jafar din gana yan aikin shi nan suma .
Bai fito ba jamal ya bata amsa tare da fadin mama kinsan shi baya fitowa da wuri haka ai sai idan ya gama abinda yake yi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
1️⃣9️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAN UWA FATAN ALHERI HAR KULLUN A GARE KU UBANGJI YA GAFARTAWA MAGABATAN MU DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA ALLAHUMA AMIN.
YAR UWA BA ZAN GAJI DA TUNATAR MAKU BIYA KAFIN KI KARANTA BA DON KAICEWA SHIGA HAKKI GA MASU IMANI ALLAH YASA MU DACE AMIN DARI UKU NE KACAL KI GUJI RAINA HAKKIN WANI A KANKI DON ALLAH.
Saida gabana ya fadi don jin muryan dodona da ya shigo gidan bani kadai na gane ina tsoron shi ba don har salma, Rufaida da Nazifa.
Idan ya shigo na kanga sun shiga taitayin su a gidan har jamal da jalal suna wanan rawan jikin da kama kai a gaban shi idan yana kusa .
Nima hakan da nagani ya darsa min tsoron shi a lokaci guda duk da ban taba ganin wanda yaiwa cin fuska a gabana ba.
Dagowa nayi a rikece ban ko debi abincin kwarai a platen din ba don in gudu in koma dakin mu.
Na dai samu gaida shi da kwana na jakafata na shige dakin zama nayi don cin arish da kwai dana debo a falon .
Nayi loma biyu ne naji mami na kwala min kira daga falon da sauri na mike na fito falon ina fadin mami gani.
Tana can tana magana da mama Ramatu kanwarta a lokacin kafin ta juyo tana fadin .
Yauwa zeey don Allah yi serving din yayan ku gashi nan ya shigo yanzu ni zan dan fitane yanzu zan dawo.
Tana fadin haka ta mike sai naji yana fadin amma da mota zaku don akwai dan nisa daga nan gidan.
Eh ai shine yasa nace Jalal ya sauke mu kada yaje nisa yana waje yana jiran fitowan mu ai.
Amma mami jalal ne zai jaku ga driver suna waje sai shine zai jaku ban faye yarda da tukin yaran nan ba gaskiya yake fada da turanci.
Sun saba jana a mota ko a kaduna don hakane ai na yarda da tukin motar nasu.
Allah tsare yace yana mayar da kanshi ga wayan dake hannun shi aikin shi ke nan ko magana yake hankalin shi a kan waya ko sytem din shi shiya a raina nasa mashi mayen computer.
Abincin na gama zubawa lokacin falon daga shi sai tsohuwar dake zaune itama kudi take kirgawa daga haban zanin ta nakai mai abincin gaban shi na aje.
Ruwa na koma na dauko na aje mai cikin dan muryana nake fadin yaya ga abincin nan do gudun kada inyi laifi kuma gare shi.
Jin abinda nace yasa shi dan juyawa saman lafiyayyen kujeran falon tsohuwar da zaka iya da kira dakin wata amaryace can don haduwa.
Wayan ya aje daga gefe kafin yakai kallon shi ga abincin ya dago kai yana kallon tsohuwar kuma.
Kai kai kai wanan tsohuwar ko fashi kika farane haka ina kika samo wanan kudin haka masu yawa ?
Yanzun kuma bakiki kariba don baki da tausayi sai kuma kin karbewa mami dan kudin ta maimakon ki kara mata.
Kafin tsohuwar ta dago kai tana fadin ja,iri da hausan ka kamar na mai koyo uwar taka mai tausayina ita take aiko min da kudin ai.
Yau kuwa zance ta daina don ba kashewa kike yi ba boyewa kike yi idan an baki ashe.
Ina wurin fridge ina daukan ruwa insha suke wanan barkwamcin da kakar tasu na dauko ruwan na juya zan wuce daki don da farko tsoron shigowan shi ya hanani daukan ruwan .
Naji yace ke wanan uban abincin da kika zuba ni dawa zanci shi haka ?
Tsayawa nayi wuri daya da goran ruwan a hannu na ya sake fadin sai kizo ki dauka ki cinye shi tas.
Cikin karfin hali nake fadin na debi abinci yanzu yana daki na aje zanci kai wanan yaron da fitina kake wallahi ina laifin yar nan tana iya kokarin ta da kai.
An fada maki kowa irin kine dake loda abinci a cikin sa yana kiba kamar za,a tafi gasan gwaji dashi halan ?
To ba zataci ba idan zakaci kaci da yawan fitina har yaushe zaka zauna kana matsawa yarinya mutane haka.
Yar nan ko karyawa bata samu tayi ba yanzun taga ba yan uwanka abin kalaci suka fita kai kuma kazo da naka tsurkun yanzu.
Idan kayi fushi sai kaje kayi aure kowa ma ya huta mitar ka na tsiya kaji min yaro da jarabar tsiya haka.
Hjy dama naga kin gaji dani ai ki huta min gori yau kaduna zan kwana idan Allah ya yarda idan ka tashi ka wuce jos zaifi ma sauki ai.
Ina tsaye wuri daya ni ban gusa ba ina sauraren da bai karewa da tsohuwar ko da yaushe sai dai idan basu hadu ba idan kuma bata ganshi ba ta kafa mita ke nan ina ya shiga.
Zo ki dauki abincin nan na fasa ci ya fada da dan karfi simi simi na tako zuwa gaban shi ina zuwa nakai kasa tare da fadin.
Don Allah yaya kayi hakkuri na fada ina kaiwa kasa kamar zanyi kuka a gaban shi bace min dagani a nan na firgita sosai tare da kai hannu ina daukan plate din abincin.
Na juya ya sake fadin zo nan na dawo baya da sauri zuwa gareshi hjy ko sai faman yi mai masifan hakan takeyi bai kullata ba.
Baki da wasu kayane sai wanin black dress din da kullun kike sakawa ba kyau gani ?
Kallon kayan na jikina nayi ina fadin anty Aishace ta bani sune sabbin kayana yanzu dasu kawai nazo garin nan.
Fadan da kakan nasu takeyine ya hana taji me yake fada min don babu yadda zata jishi a yadda yake maganan.
Tafi don Allah ya fada in deep voice na juya da sauri don in bar wurin kafin yakai ga makeni yadda naga ya hasala din nan.
Tunda na shige ban kara fitowa ba shi kuma bai fita daga falon ba don ina jin muryan shi jefi jefi da hjy tsohuwa a falon.
Har su mami suka kai ga dawowa gidan hakan yasani kwantawa na kirkiri ciwon karya don da Anty Aisha ta ganin kwance take tambayana nace kaina ke ciwo.
Data fitane mami ke tambayan ina inane tace tana daki wai kanta ke ciwo tace .
Yo ai dole kai yayi ciwo ko don fitinan wanan masifafen dan naki da kika barta dashi ta bashi kalaci ya aza mata fitina.
Aiko ya Jackson baida fada hjy kece dai baki fahince shi ba Aisha ta fada tana kallin dan uwan nata.
Murya mami tasa ta kirani daga falon kamar ince wayo don wani irin faduwan gabane ya zuyarci zuciyana lokaci guda .
Saboda tsoracewa gashi yai min fadan jallabiya baka dana saka a jikina wanda har yanzu shine dai din a jikin nawa.
Don gigicewa ban ko tsaya daukan dan kwalina ba kaina dake da kitso tsoro hudu da nayiwa kaina a daren da zamuzo sun kwanta suyi lub dasu ga bakin gashi na sai sheki yakeyi.
Na fito nazo na zube a gaban mami din dake maganata da mahaifiyar ta kan rashin sake jikina a cikin su.
Ban iya dago kai na kalli kowa a falon ba kaina yana sade a kasa ina jiran inji abinda zatace dani.
Shiko ko kallon inda nake baimayi ba tunda nazo gaban mami din gashi a kusa dashi mami take zaune a daya kujeran dake gefen shi.
Meke damun kine zeey mami ta fada tana duban yanayina kai na dan girgiza tare da fadi cikin karfin hali mami kaina ke ciwo dama tun kan muzo nan na kuma sha magani ya fada min don kada tace a kaini asibiti.
Haka baida wuya a gurin mami dan abu kadan gare su yanzu asibiti ne za a ce akai mutum.
Mami tace dawo nan ki zauna ki daina wanan yawan zama ke kadai da kikeyi a daki ko yaushe koshi yana ja maki ciwo.
Banda zabi sai yadda mami tace dani dole haka ja mataciyan kafata da yai sanyi na hau saman kujeran data nuna min din.
Yaya jafar da ke rubutu a cikin sytem shi cikin kwanciyan hankali sai lokacin dana kai zaune ya dago kanshi yana fadin .
Ke meke damun kine wani irin magani kika sha nayi tsuru tsuru da ido don ban san me zance ba sai da mami ta kara tambayana nace.
Mami dama wanda aka ban asibiti ne a abuja sauran daya rage na sha dazun.
Sai naji yaja uban tsuki ya mike yana gyara dan riganshi daya takure don zaman daya dade a zaune.
Zaka fitane kafin ya ba mami data tambayeshi amsa sai hjy tace yo ina zai fita tunda tsoron mutane yake ji a waje.
Wurin ta ya nufa direct yana fadin zo muje ki rakani kada kada a saceni garin naku.
Wai wace ke zaune a kauye ke fadin wani na tsoron mutane ke idan ba tsoron kikeyi ba meya hanaki komawa kaduna ki zauna da mami.
Ja,iri ba zan tafi ba a dakin mijina zan mutu inda ya barni ba dakin wani ba ya fice yana dariyan maganan ta.
Ya dan jima a waje ina nan zaune falin tare dasu mami daketa baki suna fita don zuwa gaida mami din sai faman basu alheri mami keyi.
Nasan dai da yawan masu zuwa gaida ita yan uwantane saura kuma abokan arzikine.
Yayi sallama ya shigo falon suka amsa mai inda nake ya nufo yana mika min magani nasa hannu biyu na karba a cikin ladabi.
Mami ke tambaya maganin meye wanan din yace stress don kila aikine yai mata yawa yana mika min ya juya ya fita daga dakin.
Haka ya ban dama tashi na hade maganin don dole duk da ban san maganin kome yake nufi ba aiko na fara jin jikina wasai.
Ina sallah azahar sai barci ban tashi ba kuma ba wanda ya tayar dani din don sun dauka dai da gaske banda lafiya ne din sai bayan sallah la,asar na falka na tashi nayi sallah.
Ina idar da sallah nayo falon part din tsit yake babu wani hayaniya acikin sa yasa na gane mami ta fitane a lokacin.
Ko ina na gyara tunda aikinane nagama na hada kayan abincin da nagani ta nan na gane su yaya mamud sun dawo sunci abinci sun fita.
Don da alama shi yasan garin sosai kilama yana da abokai a garin sabanin shi mai zaman gida ko yaushe.
Salati naji a bayana mama Ramatu na fadin yanzu yarnan harda baki da lafiya baki kwanta kin huta ba ?
Kina nan kina tikan aiki haka mama naji sauki na bata amsa ina dauraye kwanoni dana tara wanda na wanke.
Kinga idan baki da lafiya bar matsawa kanki haka ai kowa yasan ciwo ko a daga maki kafa dashi.
Ni dai na gama ban ce uffan ba sai dan murmyshin da nakeyi kawai dakin na koma na shiga wanka kafin magariba yayi.
Iya kacin ganina da yaya Jafar ke nan tunda ya ban magani saida darene nake jin su mami na magana wai ashe fitan da yayi tunda ya kawo min magani kaduna suka nufa.
Yana zuwa kaduna gida ya nufa don yana son yayi wanka abinka da goggagen dan boko mai ilimi ashe duk zaman garin ya ishe shi .
Dan daurewa yayi kawai don ya farautawa mahaifiyar shi da kakan shi raine.
Sai dai ya kasa kanne zama har kwana biyu ko ukun da mami tace zatayi da mahaifiyarta a tare dasu don suga yan uwa yan uwa su gansu.
Tun daga kofan shiga yake jiyo hayaniyar yan matan a gida yake mamakin me suka samu hakane suke wanan hayaniya haka ?
Rawa suke tika ga kida yana tashi kamar gidan club Nazira da Ruby suna wani irin rawa wanda bai dace ace sunyi ba.
Ba wanda yasan da shigowan shi har ya tsaya yana kare masu kallo a wurin kafin kamshin shi dakewa mutum sallama ya daki hancin su.
Duk suka juya suna kallon kofan salma na zaune tana shan milk a cup tana dan kurba a hankali itama daga inda take din zaune tayi arba dashi.
Rudewa ko wacen su tayi ya tako a hankali zuwa part din shi dake gidan don wanka yake son yi da sauran abubuwan daya bari a nan.
Da sauri Nazira taje kashe kidan baiko juyo ya kara kallon inda suke ba ya shige part din bayan ya bude tare da gwauro kofan da karfi.
Duk yadda yake jin shi a da sai yaji komai ya gushe mashi bacin ran yaran nan ya mamaye zuciyar shi.
Yes yasan da yana wasu abubuwa da suka kaucewa addini da tarbiyan shi amma tsani yaga diya mace tana kauce hanya.
Zama yayi sama gado dakin tare da tokare hannaye shi ya kama haban shi yana tunanen zancen su da mami da take fadin.
Ba zanso ka ketare gidan nan ba idan baka son yar hjy hindu sai ka zaba a cikin wa yan na yaran guda uku da ke gidan nan don nasan dukkan su babu wace ba zatayi makaba a cikin su.
Tunda kai na fahinci baka da time din tsayawa dating da wata mace a yanzu tsuki yaja yana mikewa tsaye.
Deep in thought yaya za ayi ya auri daya daga cikin yaran nan da idon su ya gama budewa haka wai.
Dadai yaso bin ra,yin mami don shi ba wata macen da ta tsaya mai arai yanzu don hakane zaibi zaben mami din gareshi.
Wani tsuki ya kara ja ya fara cire aninin gaban rigan dake jikin shi fara longsilve yana maijin tarin haushin su a ranshi.
Wanka ya fada ya dan dauki lokaci kafin ya fito ya samu waya shi nata ringing ya nufi inda ya aje wayan yana dagawa.
Yaya mamud ne a layin yai mai kira biyu bai daga ba gana ukune ya samu ya daga yake fadin ya jafar kana inane haka mami tana tambayan ka ta kira layin ka not reacheble.
Ina gida yanzu haka ya bashi amsa kai tsaye gida yanzu na fito mami da hjy suna tambayan inda ka shiga yanzun hakan ina kofar gidan.
Kaduna fa nake nufi ya bashi amsa kamar a hasale don har lokacin yana jin ranshi babu dadi ga abinda idon shi ya gane mashi din nasu Rufaida.
Kokarin tayar da sallah dake kanshi yayi kafin ya gama ya shirya cikin wani jallabiya ya nufi gado ya fada.
Saidai duk yadda yaso yayi barci hakan ya gagareshi don baison ya batawa mami rai ko kadan tunda yai mata alkawari ya zama dole ya cika mata burin ta..
Mami tunda yaya mamud ke fada mata ai Jackson ya koma kaduna taji rayuwanta ya baci dashi sosai don me zai nuna bai iya zama a mahaifan ta.
Ko kuma yayi hakane don gujewa zancen auren data tasa shi gaba dashi don ko a daren jiya saida sukai mai tas itada yan uwanta da mahaifiyar su.
Wanan zance ne na sama sunayi da anth Aisha ta aikoni daukan mata charger ashe a dakin tsohuwar da dare.
Mami uwar zamanice don haka ba tare data furtawa kowa bacin ran da take ji a ranta ba ta nasa zata kyaleshi taga iya gudun shi yanzu.
Don haka ta daure taci gaba da tsabgoginta ba tare da nunawa kowa komai ba kamar ranta bai baci ba.
Haka kuma tasa a ranta wanan karon ba zata kirashi taji dalilin yin hakan dayayi ya barsu can ba tare data sani ba.
Karshe ma shigewa tayi da sunan zatayi wanka harta shiga dakin ta juyo ta fito zuwa dakin mu ta sameni kwance na rufe idanuwa na sai jin muryan ta nayi a kaina.
Da sauri na bude idanuwana cikin laushin murya nake gaida ita take fadin ya jikin naki yanzu ?
Naci sauki na fada a yar siririyar murya ina kokarin mikewa zaune ta sake fadin badai inda kike ji a jikin naki yanzu don in sani tun dare baiyi ba.
Zama tayi a gefen gafon dakin tana dan kale kale a dakin kamar tana nazarin dakin ne ko kuma wani tunane.
Na dago kai a hankali sai naga tana kallona can take ce min ko dai zancen karatun kine kika saka a rai haka zeey har yaja maki ciwon kai ?
Nace lah mami wallahi bashi bane mami dazun daine kan nawa ya fara ciwo kuma ai nasha magani yanzu naji sauki.
Tana mikewa take fadin to shike nan ina ganin zan karbar maki transfer tunda yanzu zaman mu zaifi yawa a can.
Don ba zan barki ba inda bana don ke din kamar amana kike ga hannu na ai.
Mami duk yadda kika zantar a kaina daidaine tunda kece uwana yanzu ai mami banda wata uwar dana sani kuma.
Tace to babu laifi na gode ga yadda kike nuna min nima sai dai ina tsoron watarana kar asabe ta rabani dake.
Asabe yamzu bata da iko kamar yadda kike dashi a wurina mami don ba tare nake zaune dasu ba kuma.
Sai tayi murmushi tana fadin kafin dai ki kwanta ki kara shan maganin da aboki ya sayo maki dazun don ina ganin har da gajiyan aiki din a ciki.
ZAINAN IDRIS MAKAAA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣0️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA JUMMA,AT MUBARAK FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA LAFIYA UBANGIJI ALLAH YA KARBA IBADUN MU YA SADAMU DA RAHAMOMIN DAKE CIKIN WANAN RANAN YA GAFARTAWA MAGABATAN MUSULMI BAKI DAYA ALLAHUMA AMIN, , , , , , ,
YAU MA DAI INA MAKI TUNI AKAN HAKKI DA KWABON KU MUKE SAMUN CIGABAN RUBUTUN MU A DAURE A BADA HAKKI DON SAUKE NAYI A KAI, , , ,
Sai faman shiyawa muke tun dare ake shirin dawowan mu kaduna taaraba mai yawa aka hadawa mami irin abinda zata bukata a birni wanda babu shi sai a irin wanan gari.
Gashi tare da wanan tsohuwar zamu koma don mami ta shawo kanta da kyar ta bari a kaita asibiti a dubata ta dan kwana mata biyu ta dawo koshi sai da wanan mami ya sa baki ta yarda da hakan.
Tun a can mami ke fadin wanan bakuntar zeey ce da Aisha ce don dai nasan hjy ba shiryawa zatayi da sauran yaran nan ba cewa su anty salma dake gida.
Bamu bar garin Samu,naka ba sai misalin sha dayan rana tafiyace maidan jayawa tsakanin kaduna da garin sai dai a gurin su yake haka nikan a wurina kamar unguwane hakan ai.
Don ko banza naga gari da kauyokan da nake jin sunan su a bakin mutane a da can da nake gida.
Allah ya kawo mu lafiya don wanan karon da motoci biyu muka juyo don mai tarin motocin ya juyo abinshi ya barmu can.
Duk da nasan mami tana wayencewa kan barin ta can da yayi don kamar rashin da,a ya nuna mata ga hakan don naji suna magana da anty Aisha a dakin da muka sauka kan hakan.
Aisha tana bata hakkuri da cewa mami ki dai bincika wata kila yana da wani uzurine yai haka don kinga ai daga baya jiya ya turo da sako a rabawa mutanen nan din.
Mun samu su mama Kande sun gyara gida tsab suna koma kan aikin girkin da za a ci idan an iso, da yake aikin nada yawa yasa basu kare ba kafin isowan mu garin.
Sun fito sun tari kowa da murna da farin ciki ina tsaye wurin mota babu wanda ya kulani a wurin nikan driver na fara fitar da kaya na fara dauka na shiga dashi cikin gidan da nakw ji yanzu kamar gidan mune.
Tsohuwarce tafe a hankali tana saye da glass din ido a fuskan ta sai farin gyale kwato dage yafe a jikinta dake saye da atamfan super mai ruwan haki da dorawa a jikin shi da manyan zane.
Da sauri na karasa ina kokarin karban ledan maganin data rike a hannun ta zata shigo gidan ga su Rufaida suna gefe suna mata tsiya.
A cikin ladabi na mika hannu ina karban ledan tace ba kaji ba yar albarka kedai kinfi wa yan nan kirki da hankali.
Barshi kinji ba wani kayan nauyi bane a cikin sa ai, aiko sukayo min caaaa a kai Rufaida na fadin wanan ai bakin iya yi ne da ita ga kowa saita nuna ita yar munafukaine ai.
Kai haba wanan zagin haka kuma fa ku daina wanan dabi,an bai da kyau ko kadan zagi harda iyayye.
Rufaida ta hasala ta watsa min harara nidai duk da tace baida nauyi bai hana in karbi ledan a hannunta ba.
Zama tayi a falo bayan ta iso da kyar don yanayin tafiyan nata yadda take yinshi a hankali ga tsufa ga ciwo dake damunta a jiki.
Nan falo gaba daya suka zube sai nuna kauna ga juna sukeyi ni dai ina tsaye da ledan nama shagala ban sani ba.
Banji fitowan shi ba sai kamshin shi daya doki hancina lokaci daya tare da muryan shi yana fadin watau nan ma kin biyoni ke nan ko ?
Na gudo na barki can bai maki ba saida kika biyosu kuka dawo tare yana magana tare da daure fuskan shi kamar gaske .
Ja,iri to baka tsira ba ai don gani ko na biyo ka din don ba fasawa zanyi ba da magana ta sai kagaji kayi zuciya ka fito muna da mata mun gani idan shika guduwa dama.
Mami yaya akayi kika zo muna da wanan yar matsalan tsohuwar gida yana magana yana kallon mami din data daure fuskanta tun fitowan shi kamar ba ita bace ke dariya yanzu .
Saidai jin ya ambaci sunan ta fake fadin cikin daga mai hannu please live me alone don't metion my name again cikin kara daure fuskanta gare shi.
Oh mami rely iam sorry for what i have done wanan tsohuwar ne ta dameni kuma nasan ba bari zakiyi in dawo ba idan na fada maki kai tsaye zanzo inyi wani abu a nan a ranan nima tafiyan ai da niyar in komane idan na gama sai gashi ban samu komawa ba.
O hjy ce ma ta dameka har kana fadi a gabana forgive me mami iam sorry wlh wani abu nazo yi garin nan na lake a cikin sa.
Alhalin tunda yazo yana gida bai fita ba yana daki yana ragewa kanshi zafi abindake tsunkularshi kwana da kwanaki.
Is your on business koma meya baro ka da garin mu dai ai ba zaka hanamu yin kwanakin da mukai niyar yi ba a can.
Ya dan laso bakinshi yana shafan kai don ya fahinci mami ta hau sosai dashi kan abinda yayi din na barin su can ya dawo nan shi kadai.
Ke wai lafiya kin tsawa mutane saman kai haka kina bin mutane da kallo don rainin wayau Rufaida ke fadi a hasale.
Keko gulma mana tana bin bakin kowa da kallon abinda ake fada kamar ba yar aiki ba ta dinga shiga cikin mutane tana kutsa kanta.
Ikon Allah da alama yar nan dai bata jin dadi a wurin ku meye matsalanta don ta tsaya a cikin mu ita din ba mutum bace kamar ku ai dan mutum daraja gare shi tsohuwar ke fada tana kallo.
Zo ki zauna a nan gaki tsaye kinyo tafiya baki zauna ba take fada tare da kallona tana nuna mi wurin zama.
Nace dama ledan nan ne ban san dakin da zan kai maki ba shine na tsaya na fada a dan marairaice.
To kuma ji da abinda ya tsayar da ita a gurin ba tsayin banza tayi ba ta mika hannu in miko mata ledan dake hannuna.
Mami tace na rasa me yarinyar nan ta tare masu a gidan nan da basu bata salama sai hattara da tsana.
A,a in kinga hakan wata kila dai sun hango wani abune a gareta sukewa kyashin sa ko don yanzu ta karbe masu fada gurin ki.
Su dai daina haka don ban so banyi sharawa da kowa ba da zan kawo ta gidan nan do haka ba zan dauki hakan ba gareta tunda ban bari uta ta raina ku ba.
Gaban mami bazo na tsuguna ina fadin mami bani key in bude daki zan gyara ne kafin ki shigo.
Ga dai key din gyara ki bari sai anjima yanzu dai ki kwashe kayan mu kikai min daki hjy kuma nata dakin ki kai mata sai ki koma dakin Aisha da zama ke .
A, a barmu mu zauna dakin ta a tare dama kawatace ki n ga ai ko tausa tayi min a dakin idan ina so naji kuma dumin mutum a kusa dani ai?
Ko ba zaki zauna tare dani ba kawata tana tambayana cikin dan dariya tana kallon fuskana.
Murmushi na sake wanda yasa fararen hakora dan baiya diple dina ya dan lutsa daga gefen fuskana ina fadin ina so sosai hjy .
Ya daifi ni dama ba zan zauna da kowa a dakina ba Aisha ta fada tana mikewa tsaye mami tace hakan baidai taso bane .
A nan na barsu ashe baya barina wurin Rufaida tayi fushi ta mike ta koma daki su waya ta jawo tana fadawa uwarta wai mami tana disgata kan yar aiki ita gida zata dawo don hakan da ake mata yana ci mata rai.
Duk da mami tace kada na gyara dakin ba yarda na barshi hakan ba don sai dana kara gyarashi tas na dawo dakina na gyarawa hjy yadda ya dace na dauko wani zanin gado dakin mami mai kyau na shimfida mata.
Falon na dawo inda na samu sun fara cin abinci har lokacin mami na zaune tare da yaran ta gaba dayan su a wurin sai salma da hjy ma kakarta ce don itace ta haifi uwarta a gurin tana nuna jin dadin ganinta.
Yau zee kici abinci ki dauko zanin gado a daki ki shimfidawa hjycdakin ki .
Nace na dauko na shimfida mami tun dazun ai tace kai zee na gode sa wanan karama hjy din da kike yi yamafi min ku zauna tare da zamanta da wanan mara moriya din tana nuna Aishan ta.
Mami nice banda moriya bari ki gani har wanka zan dingawa hjy har ta bar gidan nan kuwa hannu mami ta watsowa Aisha tana fadin karbi naki nan ko uwarki Ramatu tayi kadan tayiwa hjy wanka yanzu ai.
Abinci na diba na koma can gefe guda ina dan duban inda zan zauna mami ke fadin wanan abinci zai ishe ki ke nan zeey ?
Ya isa mami na fada ina nufar can nisa dasu don in zauna tsohuwar take fadin wanan ya da dadin zama take wallahi.
Wanan ba irin yarwa bace a cikin ahali yarinyar ta samu tarbiya a gun uwarta kada ki bar wa yan nan marasa ta ido su kore maki ita gidan nan.
Ai ba zan barsu ba mami ta fada duk wanda bai iya zama da abindanake so yayi gaba hanya a bude yake mai ai.
Baidai kai can ba kowa ya tsaya a matsayin sa tsohuwar ta fada mami ta nuna salma tana fadin sune ai marasa hankalin yarinya ta girmamasu sai sun zubar da mutuncin su gareta zasuji dadi.
No mami ba salma a ciki zancen nan don da kanta zeey ke fada min tana jin dadin zama da anty salma sosai idan muna hira da ita.
Salma tace mami ni ina ruwana da harkanta gidan nan tunda bata tare min komai ba ga kowa.
Shine daidai hakan ai kinji itama tana yabon ki a bayan ki gashi yanzu yar uwan ki tana fadi kuwa kafin ta juya wurin yaya jafar tana fadin.
Kai gwauro ba zakaci abincin bane kai ko sai yayi sanyi ka tsikara ka tashi tunda baka aje ba balle a dumama shi.
Zaki fara tsokanarshi ko hjy yaya mamud ya fada yana mikewa sai tsohuwar tace gashi ko yanzu ya iya yaji saboda korafina ba kuma zan fasa ba idan baiyi abinda nake son yayi ba.
Ya dago kai yana fadin me kike ci na baka na zuba hjy kwana zan fitar da mata kowa ya huta ina shike nan.
Shike nan kuwa kaga an wuce wurin haba ko kai fa mutum kamar me jin warin mata a tare dashi.
Barshi hjy rainawa mutane yake son yi wanan karin ko ba zan saurara mashi ba don naga wasa ya dauki zancen nan.
Mami ai na fada maki kwanan zan fitar kowama ya huta sai mami take fadin yar gidan wanene yarinyar da zaka fitar din ?
Mami ai ko yar waye zaki gani idan Allah ya kaimu ranan dinan ki sai naba kowa mamaki a gidan nan sosai.
Mami ai kin san sai yar gwauna ko wani seneter don irin su yaya Jackson sai diyan manya a kasan nan ai Aisha ta fada tana kallon shi tana dariya.
Shima murmushi yayiwa zancen Aisha din yace kedai bari zan yi surprise din kowa idan na tashi sai hjy tace kada dai kaiwa mutane zaben tumun dare garin ruwa idon kan nan.
Ni makoho ne aka fada maki ai kece mai bani shawara ki bari ki gani idan ban zabo da kyau ba sai ki fadi hakan.
Wayan shi da yai kara ya dauka yana duba kafin ya mike ya bar wurin yana wani magana kamar yare sai hjy ke fadin.
Itace ta kiraka kake gudu kar muji me kuke fada dama ka zauna da wanan yaren naku baji muke ba mu.
Daga inda nake ina dan murmushi wani tunane yazo min nake fadin a raina zanso nima inga wanan zabin na yaya jafar yadda yarinyar zata kasance.
Nasan badai kyau da kudi ba kan kamar yadda yake da kyau din nan ga ilimi ga wayewa dole wace zai aura din itama ta kasance kamar ai.
Ni daya ke faman tunane har naji abincin ma ya fita a raina ina tuna sukan sunji dadin su uwa kudi uba kudi haka.
Suma gasu kudi wai ina mutanen nan zasu da wanan dukiya hakane idan da nice su ai ba zan nemi wani kudi ba zan zauna in hutane kwai inta jin dadi na a gida.
Zeey zoki kwashe wanan kayan abincin nan wurin nan ki dawo ki kai hjy daki tayi sallah ta dan huta.
Firgigit na dago kai tare da fadin to mami ina kokarin mikewa a inda nake zaune din.
Sai dana gyara komai mami na zaune gurin tana waya da yayan ta da muka baro dazun garin su.
Hjy muje in kaiki dakin azahar yayi tun dazun na fada a cikin ladabi ina kokarin daukan kayan ta gyale da ledan maganin ta dake gefenta aje.
To yar nan har na fara gyangyadi ko a wurin ba tare dana sani ba tana mikewa tare da kokatin tattaro gyalen ta dake gefe.
A hankali muke tafiya zuwa dakin har muka kai dakin yayi dan dumi sai kamshi ke tashi a cikin sa ledan na aje a gefen gadon kafin in nufi kofan ban dakin in bude mata shi.
A, a kagani ba nan yayi min gara in zauna dake da in zauna da wanan mara moriyar Aisha wace ko kara ba zata iya kawar wa kanta ba balle wani.
Bayan mun idar da sallah dukkan mu a nan kasan muka kwanta nabawa hjy filo tayi matashin kai dashi niko ko filon ban samu matashi dashi ba sai barci.
Ban falka ba sai da hjy ta tashini don inyi sallah la,asar nasan yamma yayi saboda dadin barcin da nayi.
Na idar na mike zuwa dakin mami bata dakin yasa na samu daman kara gyara dakin da yake ba wani datti a ciki dakin
A falo mamice da yaya mamud suke magana haka yasa na juyo zan koma dakin mu indan gyara don ko ba komai da zan wa dakin ban dakin yana bukatan wanki koda yaushe.
Na wanke na fito ina daukan filon data kwanta a kasa take fadin yar nan idan kin rage sai ki kaini falo in zauna don yamma tayi yanzu.
Na amsa da to hjy muje mami ma tana falon zaune tare da yaya mamud .
Wai ni iyalin shi mamud din suna inane don banji duriyan su ba tun dazun ina a nan gidan suke zaune ne suma.
Suna Abuja an barsu a can da zamu dawo kaduna yar ta kifen tana nan dai da halin ta har yanzu bata canza zani ba ko ?
Dan dariya mai sauti nayi ba tare da nayi magana ba don ban san abinda zance da ita ba.
Falin muka fito tafiyan minti daya daga dakin mu zuwa falin saida muka biyar muna lalabawa kafin mukai saman kujeran ta zauna a hankali.
Mami na fadin kun lalabo kun fitone hjy take fadin yar nannta lalabo dani ina dan jin dadin hakan yarnan akwai kirki sosai.
Allah yasa kiga aurenta hjy amin ta juya tana fadin kada ki tsaya dogon bokon nan na zamanun nan dake batawa mutum lokaci sai a dauki lokaci yaro na zubar da irin sa duk wata.
Yaran nan da kun gane ai da ku aurar da su don har sun wuce munzali aure a yanzu .
Hjy kin san ai aure dan lokaci idan lokacin sa yayi koda shiri ko ba shiri sai ayishi a lokacin.
Zaune yake saman farar kujeran roba a gurden din gidan mai dauke da dogayen itatuwan da ba wani zugun ganye suke dashi ba sai dai tarin tsayi a gasu.
Babu wani abinda yakeyi duk da sytem din shi dake gaban shi a bude ya kasa aiwatar da komai sai faman tune a ranshi.
Yakai hannu a hankali ya rufe sytem din ya dafe kan shi dashi yana ci gaba da tunanen shi ya rasa yaya zaiyi ne da wanan hukuncin da yake kokarin yakewa a ranshi.
Allah ya gani bawai yana son yarinyar da mami ke son hadasu bane zai dai amincene don farin cikin mahaifiyar shi kawai.
Don yadda mami dasu hjy suke nuna mai muhinmancin yin hakan gareshi saidai shi Allah ya gani bawai ya shiryawa aure a wanan shekarun nasa bane.
Anya kuwa idan yayi gangancin yin aure a yanzu ba zai jawa kanshi matsala bane ga hakan.
Kai ya girgiza shi kadai tare da fadin dole yai juriya da fin karfin zuciyar shi don ya samu su rabu lafiya da mahaifiyar su.
Muryan Rufaida dake fadin ki tabbatar da kin wanke kayan nan tas wallahi kada inga jirwaye a jikin su banza kawai mun zuba ke nan dake a gidan nan.
Ke gaki kin samu wuri zaki mike kafan ki kiji dadi ko to wanki har na tufafina duk ke zaki dinga wankin su a gidan nan daga wanan ranan.
Nima ga nawa Nazira ta fada shegiya munafuka mumuke zamuyi maki a gidan nan ba tare da mami ta san da hakan ba ta jefo min unders din ta a fuska.
A daidai lokacin daya karaso wurin don jin zagin da suke min din yayi yawa a lokacin.
Yana tsaye hannun shi duka biyu zube cikin aljihun wandon shi kallon kayan yayi yayi saurin kawar da idon shi ga kayan.
Ya dago yana kallona su kuma sai dan kame kame sukeyi suna fadin sannu da hutawa yaya J ke daga daga nan ki shige ciki ya fada yana kallona.
Da sauri na bar wiein kayan na koma ciki dama wurin su mama kande nake zaune suka sameni suka ban wanan sikin wankin.
Nan nabar masu kayan nasu na shige ina share hawaye babu mami a falin sai hjy dake zaune ita kadai ta kurawa tv ido tana sauraren malam daurawa dake wa,azi a tashan sunna tv.
Na zauna take fadin yar nan akwai kura kuren da mukasha tabkawa a rayuwa sosai a baya wanda sai yanzu kake jin bayanai akan abubuwan da bamu sani ba a can baya.
Jin tana magana ban bata amsa ba yasata dago kai tana fadin kinga kamar da can baya ai bamu sancewa ga lokacin da mutum ya dace yayi , , , ,
Ido ta kura mi don hawayen data ga ina sharewa a lokacin salati ta saka hankali tashe tana fadin .
Waya tabaki me akai maki yar nan ki fada min wanda ya musguna maki yanzu don nasan ranki aka bata haka.
Muryan mami ne ke fadin hjy lafiya wa aka batawa rai zeey lafiya me ya faru yanzun fa kika bar falin nan da raha da hjy .
Mami ba komai ba komai kamat yaya ta fada tana kallona tana zama saman kujera takon kafab shine yana shigowa daga kofan baya yake fadin.
Mami kiwa yaran nan iyaka da yarinyar nan abin is too much sun mayar da ita boya a gidan nan .
Mami idan baki iya masu magana su daina don Allah ki mayar da yarinyar nan gaban iyayyenta haka cin fuskan yayi yawa.
Ya kwashe komai da yaji yana fadawa mami rai bace yana gama fadi ya juya ya fita hjy ma tana masa magana bai tsaya sauraren ta ba ya fita don bai cikin dasin rai a lokacin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣1️⃣
ZAINAB IDRIS
MAKAWA
YAR UWA FATAN ALHERI DA GAMAWA DA DUNIYA TARE DA IMANI A ZUKATAN MU AMIN DON ALLAH KADA KI FITAR KARKI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA KI TUNA DA AKWAI RANAN HISSABI YANA NAN TAFE.
Ki biya ki karanta a cikin salama yar uwa kan dari uku kada a tsayar dake ranan da kowa tashi ke fitar dashi sai abinda ka shuka.
Yau tun safe Lantana da haibaici ta tashi a gidan don kawai Abban mu ya kwana a dakin innar mu kuma taga Abba ya fito ban daki da asuban farko.
Saboda ta hana idon ta barci duk ranan da Abba ya shiga wurin innan mu haka take kwana leken tagar dakin ta don ganin halin da suke ciki.
Wanan dalili ke sa Abba ko zai shiga dakin sai yaji wa,azi da nasiha abokan shi ko wani na kusa dashi akan yadda yake wofintar da innan mu har yan waje suka gane hakan.
Hakan ba abin mamaki bane sanin ko wacece uwar lantana a garin dan zaman kanta takeyi tana sana,ar tuwo tuwo.
Haka kuma take mu,amula da maza bata boye halinta har mutanen gari suka ki auren yarta data taso shine Asabe kakar mu taje ta kwasowa Abban mu ita.
Don kswai a lokacin suna dan dasawa da mahaifiyar ta har suka hada wanan alakan cewa idan Abban mu yana son lantana yazo ya nemeta da aure ko za,a dace ta haifa mai diya maza a gidan.
Bayan auren yanzu kuma ya fita a tsakanin su suka koma kamar annabi da kafiri tun bayan dataga ta haifi namiji din duk da dan ba lafiyayye bane yazo.
Innan mu tana bakin murhu tana hura wuta ta fito ta zauna a kofan dakin ta tana fadi a fakace.
Yau kuma su oo me aka samu da farar safiyan nan ake wanan duke a gaban murhu ko anyo aikene daga bariki za a sha dadi haka ?
Inna dai yi tayi kamar bata jita ba taci gaba da fadin muna nan dai idan tayi wari maji ai .
Gashi dama ko a gida a shedesu da dan hannu balle anje birni anga banza aita wawurowa ana kawowa gida.
Hakan bai mata ba ta sake fadin wasu dai sunji takaici ya ko auren fari babu har ta shiga duniya yawon banza .
Har azo anawa mutane feleke a gari a saka a canza duk da kayan zina to ai haka ba mamaki tunda tsohuwa ma ta tsufa bata san ta tsufa ba ka jaraba kullun ana makale da naji ana abu daya diya tayi da kaitai a birni uwa tayi nan da tsoho.
Allah sarki dadin abun dai da tsohon sunna tsohuwar ke makale ba mazan wasu take ci ba a titi kamar macijiyar da bata ramin kanta.
Sai dai anyi rami tayi shige ko tabi darnin makwabta ana dannan ta ana sukawa akanta saman titi da tsufanta diyata dana makwabta suna kallo.
Innalillahi aikuwa dama inna takan tara mata na kwanaki kafin ta gaji ta bata amsa koshi sai idan taji ta tabo zancen diyan tane zata samu mai zafi daya ta fada mata taja bakinta tayi shiru ta barta tana haushi.
Wani lokacin har makwabta sai sun shigo rabon ta akan tayi hakkuri ta daina idan kuma sun gaji sai tayi tayi sai ta gaji zata kyale don kanta.
Wani lokaci kuma har uwarta takan tako gidan tazo taya ta fadan suyi harsu kare babu mai tankasu.
Yau din ma da taga haka jin amsan da inna ta bata ta yafa gyalenta ta fita zuwa fadawa uwarta abinda ke faruwa harda karya da gaskiya ta kwasa ta fadamata.
Sai gasu tare sun dawo ita haushi uwarta haushi Allah ya taimaka inna ta gama girka dan taliyan hausa da take dafawa yara su karya dashi din Abba yace kuntu billahi baida ko kwandala a hannun shi da zasu karya.
Amma yana fita ya shiga dakin lantana data haushi da masifan ai ta ganshi ya shiga ban daki daga yau sai ka koma ka mannewa tsohuwar matar ka tunda duk kokarin da nake maka baka gani kai.
Halin maza sai su nan Abba ya dan fara kame kame yana rarashinta har yakai ya dauko dan kudin daya kwana dashi hannun shi ya mika mata su gaba daya don kawai ya samu ya shawo kanta kada ta gujeshi kamar yadda ta fada din.
Shine bayan fitan shi inna ta fito tana hura wuta ta ja inna da wanan masifan har yakai inna ta mayat mata da martanin da yai mata zafi shine uwarta ta shigo da masifa.
Tana fadin sai tayi karan innan mu don kazafi wai inna tayi mata a cewan ta jin fitinan yayi yawa yasa Asabe fitowa don da farko batayi niyar fitowa ba.
Ji datayi tace zata kai karan inna ga hukuma yasa ta fito tana fadin ke mai tuwo baki tunanen me yarki itama ta fada mata .
Har ta bata wanan amsa itama don haka kawai ba zata fada mata ba ai don kawai an mayar da haulatu mai hakuri a gidan tana kawar da kai ga abinda yarki jeyi mata ko yaushe.
To tsohuwar banza kin fito ki shigar matane ko me yanzy haulatun ce mutum a wurun ki tunda yarta na can birni tana bin maza tana zuwa maku nan da abin duniya yanzu sun koma abin son ki kuma ?
Jin haka da innan mu tayi ta bude labulen kofan ta tana fadin saukin abindai kafin ta fara aikatau wasu sun tafi butnin sunyi har saudiya yin dandin kasa mai tsarki basu dawo da komai ba kasan nan sai tsaraban shegu.
Idan kuma suna da uba yau a fito muna da uban su mu gani don haka kafin yata taje birni bin maza tsohuwar banza ta fara zuwa ta dawo muna garin nan da tsaraban annoba.
Yau zaki san kin tabani garin nan yau zan nuna maki ko wacece ni a garin nan inna tace idan kin tashi kisa a rufeni dan makullin ya bace iyaka ke nan.
Lokacin har yara da mata da muke makwabtaka dasu sun cika gidan suna kallo da saurare.
In dai barikin ne ai iyawace don karshe sai an koro yar taki da ciki kowa ya gani a garin nan lantana ta fada cikin jin kunya da nauyin yaran dake ihu bayan fitar uwarta don halin su ya ishe mutanen unguwa dama.
Har wurin aikin Abban mu lantana da uwarta suka sameshi suna fadin sai sunyi karan innar mu don tayi masu kazafi da cin mutuncin da ba a taba masu shiba yau.
Abba ya shiga ba mahaifiyar lantana hakkuri yana fadin ta barshi da inna dama halin innan mu yakai mashi ko ina a gidan.
Haka dai Abba ya samu ya lalaba su suka bar gidan bai dade ba shima a waje sai gashi ya shigo yana kwalawa inna dake bandaki kira .
Bata amsa ba saida ta fito ta bayan shi take fadin gata ai tana sauraren shi.
Ke don baki da mutunci yanzu har kika iya bude baki kika zagi uwar lantana a gaban ta karya suka fada wayasan inda yar taki take a birni dama.
Allah sarki hakane dama ai na sani kaima yaran ba damuwan ka sukayi ba ai tunda tun lokacin daka mikata wurin yar uwarka har yau baka taba bin bayanta kaga inda take zaune ba don an hanaka zuwa gani don a samu abun fada min.
To bari kaji malam idan ku dakai da uwar matan naka bakuyi karana ba yau ni zanyi naka a garin nan duk inda kakai min ya sai ka fito min da ita don wanan abin ya isheni.
Ni ga Allah na dogara nasan irin tarbiyan dana ba diyana don bata gaji shashanci ba a gurina balle taje tayi shashanci a birni.
Yanasu yau ke da bakin kike fadin zakiyi karana kan yar cikina a mata ya baci inna tace kwarai kuwa bello ta fadi sunan Abba ba sakaye kamar yadda take kiranshi da malam.
Mamaki ya kara kashe abba jin abindata fada sunan shi gatsau haka babu sakaye data sabayi mai don gabadaya ta birkice masu a gidan.
Wani kalon kalo suka watsawa juna kafin Abba ya kuta yana fita daga gidan inda lanta taji haushi cikin daga murya take fadin tunda har kika zageni dani da iyayyena ke kuwa sai yar taki tayo abin kunya birni an korota ta dawo maki maga ta tsiya.
Nikan unda na shige daki nabar mami na fada a falo ban fito ba sai bayan sallah isha,i koshi din abinci na fito.
A falo gaba dayan su suke in ka debe mazan da basu rigada sun shigo gidan bako a lokacin don ko hjy a falon tayi sallah bata shigo dakin tayi ba nasan saboda tafiyan ne yasa ta zauna a nan bata dawo dakin tayi sallah ba.
Banda hara ba abindaya shiga tsakanina dasu Rufaida duk da na gashesu a cikin jam,i saidai su basu amsa min ba.
Sai hjy ce ke fadin yarnan yanzu nake zancen ki a raina ina batun aje a dubo min ke a daki ko lafiya kika shige har wanan lokacin ?
Ina zancen dai ai ya wuce tunda kinji uwar ku ta tsawata kan hakan suma kina ganin su da shegen son jiki suke ta yaya zaki dauki kayan kasan ki har kiba wata wanki can.
Haba haba hjy a daina wanan zancen tunda mami tayi mana fada a kanshi dazu ba wanda zai kara bata irin wanan aikin acikkn mu ai tunda mami ta hana abata Aisha ke fadi.
To uwata hanani in fadi tunda kun shuka rashin gaskiya wa yarinya baku son a fada kuma kai kuma dai kazamai ne wallahi.
Ta fada rai a bace tana mai kawar da kanta ga kallon su sukai tsuru tsuru don mami na falon itama ta kafesu da idanu.
Rufaida na shirin mikewa tabar falon don takai kololuwar cika tana batsewa wai akan yar aiki mami tana wullakantasu don kawai taga gidanta ne yanzu dan uwan mahaifin su ya rasu yasa ake masu hakan.
Batakai ga tashi ba taji sallaman jalal yana washe baki ya shigo da ledoji niki niki a hannayen shi yakai gaban mami ya aje lodojin yana zama a kujera tare da fadin.
Wassh Allah yau na gaji da yawa mami tace da kai me ke nan fa mami tunda aka fito daga sallah yaya jack , , , ,
Bai karasa fadi ba saboda hararan da mami ta watsa mai yasan me take hararan shi dashi yace a wani yanayi i am sorry mami na mantane kin hana mu kirasa hakan ni kuma bakina ya saba da hakan tun a can.
Rufamin baki ku kun fada inagana waje jalal ka fita min a ido duk kuka bari wanan sunan ya shigo kasan nan raku saiya baci sosai.
Yana dariya yace yanzu dai mami ba wanan ba kinga ledan nan wai duk na tsohuwar nan ne yaya ya ban kudi a hado mata wai kada taci abinci da dare sai wanan din shi ya dauka nan irin can ne da tsofi sukecin wanan dadin yana magana yana zamowa daga saman kujeran yana kokarin budan ledan.
Wanan ya hana rufaida dake cika tana batsewa tashi don tun shigowan shi falon ya dume da kamahin suya irin na yan gayu ba suya na gida ba wanda yasha kayan hadin sanadarin zamani.
Hannun shi mami ta buge ya jaye yana fadin wassh Allah mami zan bude ku gani ne ai ko ya fada yana dariya.
Mikawa hjy abinta babu maici a cikin ku wurin sai idan ta gama ta baku ragowa idan zaku ci.
Haba mami ta bamu ragowan ta kuma bayan ta gama zuba mai miyau da goro zamuci salma ta fada tana kallon mami din.
Hjy da sai yanzu ta fahinci me ake nufi lokacin da mami ke kallon jalal tana fadin ya mikamata take fadin au me muka samu ne wai.
Bakiji bane hjy wai Jafar ne yasa a sayo maki wanan shine syke son su saka maki rani a ciki don suna yan kwadai.
Ja,irin miskili ya gama babautan nasa yana neman shiri danine kuma yanzu dazun fa ya gama fadin me na biyo ku yi nan nazo in sakawa mutane nauyina sai gashi shiya fara daukan nauyin kuma ?
Haka kika fada ko bari ya dawo saina fada mai wai badan Allah ya saya maki ba neman shiri dake yake ya sayo maki.
Kaji ja,ira zaki hadani fada da wanan mai kama da yan ruwa yazo ya hanani shanruwa a gidan nan ke nan.
Ya jalal yaga sun tsaya surutu mami bata sab sanda ya jawo ledan ba yana fadin bari nidai na bude don inyai sanyi bana iya cinsa kuma.
Yana bude ledan farko wani kanshi ne duk ya game wurin leda daya ya tura a gaban yan mata yana fadin ku ku dau wanan wanan kuma hjy wanan nasu ne idan sun shigo.
Ya mike ya isa gaban tsohuwar tare da ledojin a hannun shi yana fadin hjy mu muci wanan ko tace kaidawa ke nan miko min nan dagani sai yar nan da take dawainiya dani zancisa.
Kaji hjy kuma ya wuce ki bata fifike ne a ciki kilama bata taba cin suya irin wanan ba ai Nazira ta fada a daidai lokacin da suke shigowa gidan shida Jamal.
Yau kan ya wanke kanshi a wurin tsohuwar da murna da lale marhabin ta tare shi tana fadin kaga mijin arziki wanda yasan zafin iyalin shi.
Mami na masu dariya yazo gaban mami ya dan dukar da kanshi wanda kamar hakan al,adan yayan mami ne don har ya mamud haka yake mata da girman sa in zai fita ko ya shigo zai duka mami ta ahafa kansu tana saka masu albarka tare da fatan alheri a garesu.
Don tun ina mamakin hakan har nagaji don na saba da ganin hakan wurin yayan gidan maza ko Aisha da take mace kamar zata koma cikin uwar wani lokaci idan abin ya motsa mata ko yanzu tana zaune tunda tai magana da farko bata kara magana ba a wurin kowan su nakan waya suna abu daya charting ko dawa soke yi oho ?
My friend an dawo ke nan mami ta fada tana shafa kanshi tare da fadin ubangiji yayi maku albarka ya kare mun ku a duk inda kuka saka kafanku.
Tashi yayi ya nufi wurin hjy ya zauna a kasan carpet tare da riko hannun da ta dauki cinyar kaza tana ci yakai a bakin shi ya gutsura kadan kafin ya kai mata itama a bakinta .
Ni dai ina gefe zaune a kasa daga gefen hjyn ina kallon ikon Allah tare da mamin wai yan gidan mami suke kwadayin nama haka ?
Wanda nama sai an mayar da saura kitchen don sunci ya ishesu wanan wani irin nama ne hakan don idan kaga mami ta sayo nama a waje to kilishi ne zata shigo dashi mai yawa kowa yaci har a ture saura su mama kande su dauka..
Dan albarka hjy ta fada tana hadiyan naman dayasa mata a bakinta ta gutsura kowa falon na busy suna cin naman suke gaidashi dashi.
Dabi,an shine kyaluwa dan haka yi yayi kamar baiji su ba hjy ta juyo tana fadin taso mana yar nan ki diba kinyi zaune kina kallon kowa nacin abin arziki.
Saiya dan juyo ya kalleni guri da nake zaune din ya kawar da kanshi kamar ba kowa a wurin .
Na mike nazo gaban hjy din yana zaune har lokacin yayi rigingine a wurin kafanta idon shi a carpet nakai hannu zan diba Nazira tace
Ke dakata don Allah menene haka zaki saka mata wanan hannun naki mai dauda a cikin abu haka kai tsaye ba tare da kin wanke hannu ba.
Cak na tsaya daga daukan naman da nasoyi din ina kokarin mikewa a inda nake gurfane don barin wurin.
Ke diba ki wuce ya fada batare daya dago kai ya kalli kowa a wurun ba ya fadi hakan sai jamal yake fadin haba Nazira ku daina irin hakan don Allah dai.
Bazasu bari ba don da zasu bari ko ance suyi wani abu kan yarinyar nan ai basuyi ba kuma yadda nayi masu yau.
Me ake mata idan ba iya yinta ba taga yan aiki a wurin nan ne ko taga su kande na zama a cikin mune haka su ?
Nazira zan saba maki a gidan nan fiye da tsamanin ki to bari kiji zeey da kike gani daya kuke da ita a gidan nan yadda na daukeku dasu Aisha haka itama nake daukanta don ba wai aikin kudi aka kawota yiba yadda kuke tsammani.
Rokota nayi gurin iyayyen ta suka taimaka min suka ban ita a cikin mutunci sau nawa wai kuke son in fada maku hakane wai ?
Look akan yarinyar nan zan sabawa yarinya a cikin gidan nan ko wacece me yarinyar nan ta tsare makune wai haka kuke sakata a gaba ko yaushe ya fada a hasale cikin daga muryan shi dasai ranshi ya baci akejin shi irin hakan.
May be don sunga ta fisu kyaune da tsari suke kyashin ta jalal sarkin barkwanci ya fada kai tsaye yana masu dariyan kyaita.
Kai amma jalal din din don Allah kada tasa taji dadi har taji dadin raina mutane a gidan nan ta dauka wani kyaune da ita.
Garin dauko naman saboda rawan da jikina keyi na dauko gefen fifiken kazan dayasha carbej da albasa dasu maggi curry da sauran hadi namike tsohuwar na fadin baki dauki abin kwarai ba nace wanan yayi min yanzu naci abinci na bar falon ga baki daya har lokacin jamal da jalal suna cacakan ya matan a kaina.
Jalal ke fadin wanan kina ganita idan tayi clean gidan nan ma baya daukanta ke zeey fa idan ta waye ba karamar classic lady bace wurin nan.
Dakin na shiga na aje naman don naji ya fita min a rai don disganin da nazira tayi wurin daukan naman a gaban kowa.
Nima fa mutum ce kamar kowa da suke min haka don kawai ina yar kauye kuma diyar tallaka tallakama mai faci.
Ina ban daki nake wanan fadan a raina na fito ban tsaya jiran komai ba na hau kujera na kwanta har barci ya daukeni ban sani ba don ban san lokacin da hjy ta shigo dakin ba bayan sun gama hiran su a falon don ko hidimar da nakewa mami ranan ban samu yimata shi ba.
Koda mami ta rako hjy dakin ta samu ina barci bata tayar dani ba ta kyaleni hakana sai cikin dare dana falkone naga wutan dakin a kashe.
Washe gari da safema motsin hjy ce ya falkar dani na tashi nima nayi sallah na idar na zauna a wurin hjy ta shafa tana fadin in koma in kwanta tunda ido akwai barci daga haka taci gaba dajan tasbahan ta.
A daidai lokacin da nake shiga na gyarawa mami dakina falka kamar an tasheni har lokacin tsohuwar tana zaune a inda take.
Mikewa nayi ba tare danayi magana ba na nufi dakin mami din ko a nan ma itama zaune take tana azzakar din safiya.
Ban fito daga dakin ba saidana karasa komai na dawo na samu hjy ta dan kwanta a lokacin banyi dogon motsi ba wanka nayi tare da kara wanke ban dakin har na shirya a hankali duk tsohuwar tana barcin safe wanda nasan na gajiyane.
Sai bayan goma da rabi ta falka lokacin mami tayi mayawa a dakin yakai sau uku tana duba mahaifiyar nata.
Ruwan wanka na hada mata tayi wanka na taimaka mata data fito har ta shirya saiga abin karyawa an kawo mata har daki yaran gidan suna shigowa daya bayan daya suna gaida ita da kwana.
Har suka dauke kafansu sai Aishace bata shigoba nasan bata tashi bane don ita sai wuraren sha biyun rana dama take tashi barcin safe ko ma zuwa dayan rana.
Nan muka zauna muna hira da hjy don ban yarda na fita ba ko karyawa a cikin na tsohuwar na karya dashi take tambayana ni yar wani garine ?
Nace ancau hjy tace ashema yar jaharnan ce ke na dauka ko yar shiyan jalingone ke ko bauchin don na ganki da zubin fulani.
Nace innatace dai bafullata Abban kuma bazzagene shi yar nan da asalin ki haka har yaran nan suke maki wanan tsiyar haka ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GAREKU MASOYA UBANGIJI YA DAUKAKA MUSULUNCI A DUNIYA AMIN, , , ,
Banyi zaton akwai macen da zata kai sha shidda a yanzu ba wace bata san zata mutu ta koma wurin ubangijin ta ba da har za a hada da Allah da annabi ta rufe kunne da ido don rashin tunawa da Allah dayai mata rai da numfashi da take takama dashi a duniya wanda ubangiji zai iya karban abinsa duk sanda yaso .
Yan uwa mu kulla da daraja da nauyin wanan sunan biyu idan ance Allah da annabi a zatona angama da musulmi ashe abin ba haka yake ba a wurin wasu.
Allah kasa mufi karfin zukatan mu ya Allah ka bamu cikawa da imani amin kada ki karanta idan baki biya ba mai turawa na barki ga Allah shi yasan tsakanin mu dake.
Sallama akayi daga kofan dakin yayin da mu kuma dariya ya dauke muna hankali a cikin dakin don tsohuwar dariyan labarina dana fara batane ina fadin garin mu ai kauyene kuma yan garin muma kauyawane a cikin sa don kaka hajiya bata kaiki tsufa ba amma bata wanka daga jumma, a sai jumma, a take wanka tunda wai bata da miji da zataiwa wanka.
Sallama ya kara yi nice na karba a cikin raha da walwala don dan zaman mu da tsohuwar yasa na mance da duk wani bacin rai dana kwana dashi a gidan.
Dan miko min wanan kawar da wanan gurin nan sai duba can ki miko min abu kaza dauki wanan kici hakan yasa na manta da komai dake a raina a lokacin.
Wa,alaikum sallam na fada don hjy ita dariya yaci karfin ta a lokacin itama dai cikin dariyan take amsa mai haka yasa ya turo kofan gaba daya ya shigo.
Saye yake a cikin farar jallabiya mai laushi sai wani maiko takeyi ashe jallabiyar ma suna suka tara sabanin da danake masu bugu daya don duk jallabiya da farko daya nake daukan su sai zuwa gidan mami ne na fara bambanta jallabiya yanzu.
Yakaraso yana tako kamar wani balarabe dashi har zuwa kujaran da hjy take zaune sama a cikin hausan shi mai kama dana dan koyon hausa din.
Yana fadin wanan dariya haka hjy kamar an gafarta maki yau fa don nidai badon nasan iyayyen su ba sai ince su din jinin labawan asaline .
Don hasken jikin su yafi kama dana larabawa a gidan ga tsayi duk dadai shi yaya jafar din ya fisu tsayi sosai a cikin su sai jamal da jalal saidai basu kaishi tsayi ba su zan iya cewa su din kamar mahaifin su suka kwaso don ko ban sanshi a fili ba na san shi a manyan photunan shi dake falon gidan.
Don shi mutum ne fari dogo ga tsayi ga kyau kamar shi yayi kansa wurin halitta duk da ya manyata a photunan lokacin dayayi su hakan bai hana kyau shi fita ba a fili.
Hakan yasa nake kasa bambanta tsakanin su da dan nasa ko a cikin su wayafi kyau haka.
Shi yaya mamud duk da farine sol baikai yan uwanshi tsayi ba yana dai da nasa gwargwado sai Aisha da ta biyo mami sak wurin kama.
Don ba inda ta rage mahaifiyar tasu sai dai idan halin mahaifin su ne ta kwaso na rashin hayaniya dason motsa jiki don mami kan ita da alama ba mai yawan son jikibane ita don wani lokaci zan samu tanayin abu da kanta sai nazo in karbe ta.
A cikin dariya hjy ke labarta mashi hiran mu tana kwasan dariya fuska a daure ya dan dago ya kalleni tare da kawar da kanshi duk lokaci guda.
Ina tsugune nake gaidashi da kwana tare da mikewa don barin dakin duk da ina tunane a raina ina zan dosa idan na fita don gudun haduwa da yan matsalan gidan mami din yan kafi mai abu iko.
Don ni sai daga bayane ma nasan ba mami ta haifesu ba a wurin anty Aisha yadda nazo gidan na samu sunayin abu a gadarance da yadda mami ke nuna kamar itace ta haifi abinta.
Ina kuma zaki muna hiran mu kin dauko ban labari ina sauraren ki indon wanan ne ai shi nasan yanzu fita zaiyi a dakin don ba zama zaiyi ba ko kunya fada a gaban shi kikeyi.
Dawo ki zauna muyi hiran mu kinji jikata ta kaina aini kin ganni nan ina son jin irin labarin nan sosai wallahi don nima kinga daga karkara na fito ai.
Idon shi a waya kamar mayen waya ko computer dana sa mai yake fadin wani No kuyi hiran ku ni nawa nakeyi nan .
Tace dada Asabe kowa kikace sunan ta nace a sanyayye don kasancewan shi wurin nake fadin Asabe ne.
Ta nuna min bakin gado tana fadin zauna mana a tsaye zamuyi hiran haka na kai zaune a dan takure.
Yanzu mahaifiyar ki dai tana tare da Abban ki ko ta tambaya take yanayi na yacanza a hankali nace suna tare da Abbanmu har yanzu.
Saidai ba a cikin dadin raiba don Asabe tasa Abban mu yai wani auren wai don innan mu diya mata take haihuwa ita kuma bataga amfanin diya mace ba.
Shima dalilin turoni birni wurin mami da Asabe da lantana sukayi wai nazo inyi aikatau a nan don hakane kawai za a morewa diya mace na karasa ina share hawaye.
Kai ya dago ya kalleni a cikin mamakin jin abindana fada din na zancen Asabe ga innan mu da muka bude ido dashi a gidan kullun sai tayiwa inna gorin shi.
Haba haba yar nan kada ki kuka mana nasan wanan zancen yana da ciwo sosai don baku ai kukayo kanku diya matan ba wasu ma nacan suna son diya matan kamar suyi hauka basu samu ba ita tasan baiwan da Allah yai maku dayayo ku diya mata a garesu.
Abin mamaki sai naji ya saka muna baki a hiran mu yana tambayana ku nawane a wurin mahaifiyar ku da har take fadin hakan ?
Mu bakwai ne nice babba a dakin mu sai kanne guda shidda dana bari tare da innar mu a gida.
Babu ma wanda aka wanke a cikin ku ke nan tunda kece babba ashe kai wasu mutane da shishigin tsiya suke har da Allah sukewa izzigili.
Shi mahaifin ki fa yaya ya tambaya sai na dago na kalleshi don ban fahinci mai tambayan shi ke nufi ba.
Saidai na basu amsa da fadin yana nan kawai yace No ina nufin wani mataki ya dauka kan wanan zance
Da Abba baya daukan zancen Asabe amma yanzu tunda ya auro lanta kuma ta haifi na miji sai ya sauyawa innar mu damu ga baki daya a gida yanzu ba ruwan Abba damu kamar da can baya na fada idanuwana suna kawo ruwan da ban iya controling din su a lokacin.
Haba yar nan ki daina kuka kada nima ki sakani kukan don wanan labari naki akwaicin zuciya gaskiya.
Do me bataga laifin danta ba dashi yake ba uwarki diya matan sai uwarku kadai zataga laifin su ta fada a hasale.
Muryan mami ne data dawo take kwala min kira daga waje yasa na mike tsab na fita dakin da sauri na barsu a zaune da hjy.
Duban hjy yayi yana fadin hjy ashe har yanzu akwai itin mutanen nan masu halin dabba a kasan nan yadda yanzu addini ya zagaye kasan nan.
Yo jafari mai za a fasa a wurin kishin muna mata wasu matan fa kishi suke da matan diyan su kila irin hakane ya ke faruwa a gidan har wanan tsana ya shiga.
Amma idan bashi ba menene laifin haihuwan diya mace a duniyan nan ni ba gani ba kai bani kadai ba har kowa ai yanzu moriyan diya mace mukeci kaf zuriam mu ga baki daya.
Don uwarkuce tsaye da gidan ni kaina da kaganni nan na fuskanci itin wanan matsalan lokacin dana jera haihuwan iyayyen ku mata har su hudu a lokaci guda ban haifi namiji ba.
Sai dai ni kishiyace ta goranta min hakan bawai uwar miji ko wani irun wanan zancen yana da shiga zuciyar bawa don yanzu Allah kadai yasan halin da uwar yarinyar nan take cikin dan bakin ciki kan tana ganin sa.
Amma idan tayi hakkuri wataran sai labari yau ba gani danayi hakkuri na shanye hakan ba uwarku sai Allah ya daukaka muna ita ta zama muna zakara a cikin mazan.
Yau zeey mami ta fada ki dauki wanan kikai dakin ku na hjy ne ki kula da bata tana ci lokaci lokaci kinji.
Nace to mami ina daukan ledan da ban san ko na meye ba a cikin sa har na juya zan tafi take fadin zeey na juyo da na,am mami sai kuma ta kasa fadin abinda zata fada tana kallon fuskana da mamaki ta furta.
Zeey kinyi kuka ko zancen jiyane har yanzu a ranki ko kuma wani ya kara tabaki gidan nan yanzu kuma ?
Kai na girgiza da sauri alaman a, a tace to me akai maki fuskan a haka ko gida kika fara tunane kuma.
Nace a a a sanyayye ina juyawa sai ta bini da kallo mikewa itama tayi ta biyoni baya ban san mami na bayana ba sai dana shiga dakin da sallama naji mami na fadin a a ashe kana nan tare da hjy ne yanzu fa nake shirin zeey ta kira min kai a waje na kira layin ka bakai picking ba.
Yacs OK mami nabar wancan wayan daki da zan fito ai nazo gaida grany ce da kwana sai kuma na zauna muna hira.
Wanan yarinyar na gani kamar tayi kuka ai shine na biyota in tambayeta ko wani abin kuma akai mata na ganta haka ?
Ba wanda ya tabata tun safe muna dakin nan tare da ita nasan kukan da tayine kan labarin yan gidan su da take bani yanzu.
Ta labarta maki jahilcin kakarta ke nan ko don shine damuwan ta a zuciya kullun Asabe ta tsani mahaifiyar su don kawai ta haifesu a diya mata.
Shine fa yanzun nake mata musali dake kika kirata irin wanan mata da yawa suna haduwa dashi a rayuwan su in Allah ya hadasu zama da mace mara imani ga ubangiji har ma a cikin masu ilimin akwaisu sosai har gobe .
Na fada mata ta kwantar da hankalinta muddin ina raye a duniyan nan sai tayi ilimin data tallafi gidan su insha Allah .
Asabe zata gane diya mata ma mutane ne kamar kowa ba abin wullakantawa bane a gida.
Mikawa hjy ledan dake hannuna nayi ina fadin mami ne tace in shigo maki dashi nan nakine na fada ina ajewa gaban hjyn nata a cikin ladabi.
Me muka samu kuma nan ta fada tana kokatin budan ledan dake gaban ta lokaci daya ba komai bane sai goron ki da sauran tarkace dazaku bukata a nan dana san kina amfani dashi mami ta fada.
Mami goro kuma ya kamata ace ta bar cin goron nan a yanzu fa don jikin tsufa daya kamata zai iya mata illa wanan goron haka.
Ungo naka da zai mun illa da tuni yayi min tun kan a haifeka nake cin goro na a duniyan nan gani ko garau kana ganina.
Allah baki hakkuri ya fada tare da mikewa tsaye yana gyara rigar shi hjy tace tafiya zakayi kuma muna zaune muna hiran mu ?
Na gama hiran ai ku karasa hiran ku damani ai ba dani aka fara ba ya fada yana ficewa tace miskili kafi gaban gayya wanan wanan zan so naga macen da zata iya zama dashi haka.
Mutum kuna zaune kalau ya birkice maka lokaci guda kuma ya hana ayi magana don tsaban miskilanci.
Fita yayi daga dakin ba tare daya kara mata magana mami na gefe tana murmushi mama kande ne ta shigo dakin da sallamanta muka amsa take.
Fadin mama ga abinci an gama na kawo maki da cewa hjy tana fadin sannu sanu yarnan sannu da kokari har kun kare na rana ban dade da cin na safeba ai.
Ai kande akwai kokari shiyasa nake son daukesu mu koma Abuja don gwarawan nan sun isheni basu iya irin cimar muba nan sai kalar tasu abincin.
Saidai kuma ina tunanen wanda zan bar yaran nan dasu a gidan nan don baka barin ya mace ita kadai a gida.
Yo da kin fada tun bamu taso ba ai da anyiwa ladidi magana me take a gidan banda yawon bin makwata sai tazo ko ta zauna dasu nan kinga an rage mata ma wahala ai.
Mami tace indai ya ladidin zata yarda hjy ai mata magana kafin mu wuce in sani don in tura su kande gida suyi sallama da mutanen su asan zasu tafi.
Zan kira yayan ku in sheda mashi yai mata magana aji me zatace wanan ai ragewa ladidi nauyi ne babba.
Kande ko baku zuwa mu koma Abuja mami ta tambaya sai kande din tace yo hjy ko ina kikace mu tafi aini mai bin umurnin ki ne.
Yafi mun zama nan da yaran nan naki da basa jin magana na gara dai ina kusa dake yafi dadi ta fita tana murna tare da fatan Allah yasa a tafi da su din.
Lokacin sallah yayi mami ta bar dakin aka barmu dagani sai hjy sai bayan mun idar ne muka zauna cin abincin rana lokacin ne kuma anty Aisha ta shigo gaida hjy da kwana.
Tana wani daure fuska don tasan hjy zatai mata tsiya nan dai sukaita barkwancin su kafin Aishan ta juyo tana fadin .
Zainab yanzu ba a ganin ki tunda hjy tazo na hadiye abincin dana saka a bakina ina fadin dazun na lekaki har sau biyu in gyara maki daki kina barci.
To ai yanzu na tashi ta fada nace bari gama naje na gyara maki sai hjy tace ke arr ke kan anyi malalaciyar yarinya a nan sam baki biyo halin uwarki ba ke kan.
Don Allah hjy ki rufa min asiri kafa mami ta shigo ta sakani gaba banda abinki don kawai ta gyara min daki shine wani abu.
Yanzu ke haka za a kaiki aure ko gyaran daki baki iya ba kina haka tace wai hjy wa ya fada maki ban iya ba kawai dai ban samun lokacin hakane a tare dani.
Haka rayuwan ke gudana yanzu zan iya cewa na samu sauki sosai iyakata in shiga dakin mami in gyara sai na anty Aisha sai bayan kwana biyu kuma a ce in gyarawa yaya dakin shi yayi datti.
Su Rufaida iyaka ta dasu gaisuwa in suga dama su amsa in basuga dama ba su kyaleni sai ko idan na gilma idan ba mami kusa su sakar min magana mai zafi sai dai kawai in hadiye ban fadawa kowa kamar yadda mami tace in fada mata idan sun min wani abu.
Ya safiya ma zuwanta biyu da muka zo tana wuni gidan a karshe kuma su kwasa da mami su fita don tunda mukazo da wuya mami ta zauna a gida.
A bakin Aisha nake jin wai kafn mu tafi za a karrama mami nan jahar ta ita da wasu manyan jahar da suka samu mukamai shine dalilin ma da zamu kara sati daya nan gaba.
Nikan naga sai manyan mutane ke shigowa suna fita gidan maza da mata suna ganawa da mami wani lokaci da yaya mamud don kome mami zatayi shine gaba wuri aiwatarwa a gidan sai dai shi baida daure fuska iri sauran fuskan shi a sake yake ko yaushe gayin ba,a da raha.
Sai ince wanan shirin dinner kamar yafi wanda aka hada masu a abuja haduwa don irin shirin da naga anayi da kudin da ake fitarwa.
Don kawai wana shagalin da za ai mata ake wanan barnar da kudin nake fadi a raina sai ga hjy itama tana fada kan hakan.
Andace rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya har gashi ana gobe buki sai faman tanadar abinda zasu saka babba da yaro sukeyi a gidan.
Ina kallo sai kiyasta abubuwa nake a raina idan naji suna ihun da shewa yasu yasun a falin har anty Aisha da yanzu kan wanan abin takan dan zauna tare dasu wani lokaci.
Da farko hakan bai damuna abu ga mace kuma mai karancin shekaru irina a lokacin don haka na saka damuwa har na gaji na bakaina lafiya danayi wani tunanen cewa kilama badani za a tafi wurin dinner din ba kamar wancan na Abuja da yaya ya taimaka min ya tafi dani naga shagali kuma na samo abin bukin da har yau nake boyon su in kaiwa innar mu a gida idan zan tafi.
Muna daki da hjy ta gama cewa in bata ledan goro taci na dauko mata na zauna ya shigo dakin suka fara gaisawa ni dai banyi gigin gaidashi ba don ko na gaidashi din ba amsawa yakeyi ba.
Bai dade da zama ba sai ga Aisha dakin tana fadin hjy ni zan fita zuwa gyaran kai hjy tace shi jan ma har sai anje gun gyaran shi kamar wata kafira can dake ina dai irin gyaran kafirai din nan kike nufin zuwa.
Kaji hjy kuma da wani zance bros ni zan tafi daga inda nake bansan lokacin danace anty Aisha nima zan tafi.
Hjy ta jiyo inda nake tana fadin kema zaki tafi ai maki wanan banzan gyaran kanbna zamani yar nan a cikin mamaki take magana .
Ballema ina zan tafi dake haka zainab don me ba zaki da ita ba ya fada fuska daure karbi nan kuje ai mata itama.
Hjy tace balle yau daine da tayi sha,awan wanan abin ai, ina nan kuke ta sha,anin ku iyakarta ido ko dinkin nan bata samu albarkan ai mata shi ba gidan nan ina kallon hankalin iyami duk da aiyuka sun mata yawa.
Har dai muka fita daga dakin bayan ya cikawa Aisha hannu da kudi masu yawa da suka sani mamaki a cikin raina.
Aisha tayi mamaki kwarai lokacin da aka bude kaina da kullun yana cikin katon hulan da nake dunkule gashina a cikin sa ko kafi aula dubara baka taba ganin gashin kaina a gidan mami.
Don haka ba wanda yasan wanan sirin dana barwa kaina sani ni kadai ba a gidan mami ba kwai ko a garin mu inna tace kan dunkula min a daki da dare.
Aisha na kallon ikon Allah wayan ta yayi kara ta dauka ta kara a kunnen ta ni sai naji tana fadin to yaya daga nan din zamu wuce can insha Allah.
Ashe ya Jafar ne ya kira ta ya umurce ta kaini wurun sayar da kaya a zaba min don hjy ta fada mashi ba a samu yu min dinkin fitar bukin bani don mami bata zauna ya kara da fasin kin san kuma tunda hjy ta fadi dole ayi basai mami ta sani ba tunda aiyuka sunyi mata yawa ranakun nan .
Muna gamawa driver na waje na jiran mu don bata jan mota ita saboda mami bata yarda da hakan ba wai bata gama sanin garin ba.
Ina mamaki idan ta dauko kayan yadda take gwadawa a jikinta kafin ta gwada a nawa jikin kayane masu kyau kala biyar babu na yarwa a cikin su.
Ina kallo ta biya bayan ta hada da jakka da takalmi ko wani kayan muka dauki hanyan gida mami ko sai kira takeyi wai mun dade a waje ga hjy na fadan haka kuma.
Dakin ta muka shiga da komai da muka sayo na wuce zuwa dakin mu ina shiga hjy fada sosai ta hau ni dashi wai na biyewa Aisha munyi dare a waje.
Kala bance ba don ba dabi,a na bane babba na magana ina bashi amsa lokacin sai bayan mun idar da sallah magariba har isha i har lokacin na kasa sakin jiki a dakin har hjy ta kare abinda takeyi ta juyo inda nake tana fadin
Yi hakkuri yar nan kin san garin kaduna ba kamar sauran garuruwa bane girma ga kuma yan daukan amarya a sasssan shi.
Shine yasa kukaga hankali bai kwanta ba don Allah ku daina fita kukai yamma garin nan.
Hjy kiyi hakkuri in Allah ya yarda ba zamu karan hakan ba tace ya wuce a cikin wani sauti dake nuna bacin ranta har lokacin.
Ni dai nayi shiru gefe daya nasha jinin jikina nasan tunda hjy ta hasala haka damu na mami sai yafi nata zafi.
Aikuwa ban gama tunane ba mami ta shigo dakin fada sosai mami tayi min a dakin kafin ta juya ta fita .
Duk sai naji ba dadi a raina duk da nasan ba nice mai laifin ba amma kuma anga laifina a hakan ko sun mata da ni yar rakiyace kawai.
Sai washe gari na samu hjy ta dan sake mun fuska muka koma daidai a dakin da ita har tana jana da hira tana fadin wanan gyaran kan danayi ya kara fitar min da suran fuskana a fili.
Yar nan ashe haka kike da kyau kike munanta kanki baki gyara don Allah ki rika gyara kanki kina kwalliya kina fitar da suran ki waje.
Ni dai sai dan murmushi nakeyi ina jin dadin yadda tsohuwar ke yabani koba komai dai na samu wace ta nuna min kauna nima kamar kowa.
Hankalin kowa ya dauke gaba daya a gidan ma kuma cike yake da mutane don haka na makale daki tare da hjy sai jefi nake zuwa in leka dakin mami indanyi wani abin.
Karfe bakwai kamar kowa jira yake yayi don dai shiga wanka akeyi ana shiryawa saiga anty Aisha ta shigo tana fadin ke zainab na manta da kayan nan ai da sauri na dago ina kallon kayan da take magana akai.
Kayan jiyane dana rakata ta sayo take miko min da sauri na karba ina fadin Anty nikika sayawa dama ?
No bani ba ya J ne ya bada kudi a saya maki jiya bayan fitar mu ai mantawa nayi na baki tun jiya wanan tsohuwar tasa mami na muna fada kawai kamar yara kanana ne mu.
Nikan banbi ta nasu ba hankalina yana gurin kayan duk na rikice don murna har ta gama ta fita ba,a jima ba ta aiko kirana nazo.
Da sauri na mike nabar hjy da muke kallon kayan a dakin mu tare na nufi dakin Aisha watace ke mata kwalliy a fuska ina shiga taks ce min zauna a gyara maki fuska ba tare data dubo in danake ba.
Wurin na samu na zauna saiga mami ta leko tana fadin kin san fa tare dake zan fita ki shirya ku fito mu tafi haka yasa akaiwa anty Aisha a gurguje ta shirya ta fita ta barni a dakin da mai kwalliyan.
Ina mamain yadda mai kwalliyan ta zauna ta shiryani kafin in fito gidan har ya koma shiru duk an watse zuwa wurin buki.
Raina naji ya baci ina raya ni yanzu wa zanbi kuma tunda wayanda na sani sun wuce sun barni a gida ba tare da kowa ya kulani ba.
Rigar da mai kwalliyan ta shirya ni aciki nake faman tatarawa don kada in fadi kasa don yayi min dan tsawo saidai tace dana saka takalma zai zauna daidai a jikina .
Har tafiyan da zanyi da yadda zan rike jakka ta nuna min ni dai sai dariya take bami a raina ina fadin wa zai tsaya kallona a wurin balle yaga tafiyana.
Takon takalma da kamshin shi ya dawo da hankalin mu surin da muke jiyo takon ya fito naji matar na fadin sir mun gama you can go now.
Thank you yace da ita nikan na nufi dakin mu tunda naji sun fara magana ban tsaya ta kansu ba tunda naga mai tafiya dani yau ko bai amsawa zanyi kundun bala in daure in tambayeshi ya tafi dani.
Sai gashi dakin yana sallama hjy ke fadin a,a miskili kafi gaban gaiya ba,a fita ba ashe yace sai yanzu hjy ko munyi sauri zuwa ba farawa zasuyi da wuri ba.
Ke fito mu tafi ya fada fuska daure hjy tace dan albarka kamar ka sani yanzu ta shigo tana min korafin an tafi an barta har ina shirin kiran uwarku ta turo a dauke ta yanzu.
Mun tafi sai mun dawo ya fada ba tare daya tsaya ya bata amsa ba don da alama sauri yake kada ya makara a wurin taron.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
UBANGIJI ALLAH KA SADAMU DA ALHERIN DAKE CIKIN WANAN RANAN KA KAREMU DAGA DUK WANI ABIN CUTARWA DUNIYA DA LAHIRA AMIN.
Ba a karanta min labari idan baki bani dan na saka data ba don posting idan kin karanta na biki bashi zaki biya.
Gabana ya fadi don jin abinda ya fada ba shiri na mike nabi bayan shi saida hjy tace takalman fa na dawo na saka na dauki dan jakkar hannun na rike.
Tsaye yake a falo na zata zan gansu da wanan mai kwalliyan sai naga babu ita babu labarinta wurin.
Sai shi kadai yana kallon kofan fitowa jin takona tafe ya fara tafiya saida ya fita daga kofan falon yaja ya tsaya wuri daya.
A nan na same shi ba tare daya kalleni ba ya fara magana kamar haka ki kama kanki ki natsu fiye da yadda kowa ya kama kanshi a wurin banda kauyanci da kalle kale duk abinda nayi maki ban son musu ko gardama so be cool kamar yadda na umurce ki.
Duk da hausa yakeyi wai saidai kamal turanci yayi yawa ga maganan shi amma ba laifi ga dan turancin dana iya ina fahintar shi hakana.
Ma,ana dai akwai abinda ke shirin faruwa a wurin yake min indirect akai wanda na kasa fahintar hakan a raina.
Har ya fara tafiya naga yaja ya tsaya sai na tashi karo dashi wani wawan tsuki yaja yana fadin idan kikai min wanan wautar taki wurin nan tun acan zan balbalaki.
Saboda haka kada ki bari in kara wuceki tunda ba dodo nake ba kuma ba sauri nakeyi ba.
Ya takalman kafanane ban iya tafiya dashi don ban taba saka irin shi ba kallon kafan nawa yayi ya kawar da kai don gaba daya shigar tawa ya tsorata shi wurin sai take ganin bani bace a gaban shi.
Kamar yadda yace hakan muka jero gabana sai faduwa yake min kamshin shi kamar a hancin na aka zuba turaren.
Security din shi suna hango mu mun fito sukayo kan mu suna gaidashi tare dani tunda sun gani tare dashi.
Umurni naji ya basu cikin turancin da baikai can ba suka amsa da yes boss da sauri wani daga ciki ke bude motar maimakon ya shiga sai kawai naji ya riko min hannu sai da gabana ya fadi uku uku don tsoro da bazatan da yai min lokacin .
Kofan da zan zauna ya nufa ya bude min na shiga ya ya rufo a hankali sai ya juya ya nufi dayan bangaren da daya daga cikin security din ke rike da kofan yana shiga aka rufe motar suma suka shiga nasu.
Mami dake zaune cikin taron duk rashin ganin shi hankalinta bai kwanta ba duk da ga sauran yan uwansa a gurin.
Table daya aka ware mata daga ita sai diyan ta sai anty Nuriya da ban san da zuwan taba a gurin, kujera biyu ya rage shine kujeran da Jafar zai zauna tare da matar dayace wa mami yau zai nunawa kowa a gurin wanda mami ta rigada ta gama sanarwa MC ya fada tun dazun kuma yake faman sanar da yau dan mami din nan matashi da duniya ke ji dashi saboda ilimi da nagartan iya sarrafa computer zai bayanawa kowa abin kaunar shi.
Haka yasa mami zaran ido kadan kadan ta kalli hanyar shigowa don ganin bai karaso ba yau dai tana son ganin wanan yar mai sa, a haka a duniya da har ta iya sace zuciyar danta dake gudun mata.
Wanda har ta fara zargin kodai aljannu ne suka aure shi bata farga ba don duk yar data nuna mai sai yace batai mashi ba shi.
A lokacin kuma shima yana faman tunane a ranshi ne yadda mutane zasu dubi zabin nasa yadda aka kwallafa rai da cewa diyar wani kusa zai kawo ko diyar wani hamshakin mai kudi a kasan .
Yes yasan ba mami ba kowa ma a wurin zai iya ganin rashin dacewan su to saboda me ita din ba mace bace kamar kowa tunda mami ita ta matsa mai sai yayi aure .
Wanan itace kadai zai zaba ya zauna lafiya a rayuwan shi don zabin mami sam yasan ba zasuyi daidai.
Lumshe ido yayi yana gyara zama kodai ya fasa wanan shirmen da yake shirin aikatawa ne idan hakan zai kawo masu matsala da mami.
Shin meye laifin shi har in ya gabatar da wanan yarinyar a yau a matsayin macen da zai aura.
Itace yaji rashin ya kwanta da ita a matsayin abokiyar rayuwa kamar yadda mami ke shan fada mashi kullun idan tana masa nasiha yayi aure.
Shi gaba daya ya yarda da hakan har zuciyar shi da gangan jikin shi ya amince da wanan zabin nasa matukar zasu zauna lafiya.
Yasan yarinyar is pretty shi ba wanan yabi ba nashi tsarin ne a hakan aure dai akace yayi kuma ita din zai aura yasan ta hanyan shi yarinyar itama zata zama wani abu a duniya muddin dai tana tare dashi.
Ya dan muskuta kadan tare da gyara zaman shi yaci gaba da tunane yace a ransa yasan ko bai samu goyon nayan kowa ba zai samu na hjy matukar ba mamice ta zugata ba funda itace ta fara kawo mai wanan idea din a falonta.
Yasan amsan da zai ba duk wanda ya tun kareshi da rashin yardan wanan zabin nasa duk na kowa bai damesa kamar na mami ba.
Ko ita din a yanzu ya tanadi hujjojin da zai bata idan idan har ta nuna bata yarda ya auri yar nan nata ba.
Ido ya kara lumshewa a hankali yasan dole akwai aiki ja a gaban shi ba shi kadai ba yanzu har wanan yarinyar ya jefata a cikin dabon tashin hankali don dole ta fuskaci kalubali daga mutane da dama daga yau .
A yanzu kan yayi niyar hakan bayajin kiran kowa ko dakatarwan wani bai damu da duk abinda wani zai furta akan hakan da zaiyi ba.
Ya shirya daukan duk wani rigiman da zai taso na barazana a kan mu duk yadda mutane zasu kalli abinda zai aikata din shi a shirye yake .
Wurin ya hadu da manya da yara da masu ruwa da tsaki a gwaunati tarone na yan boko da suka amsa sunan boko a wurin.
Haka motar ta danno kai a cikin get din wurin inda hankalin yan sa ido ya dawo garta akwai daya a gaban mu sai wace muke ciki a tsakiya dayana bayan mu ma,ana dai sun saka mu a tsakiya ke nan.
A daidai lokacin da motar ta tsayane driver ya fita da sauri sai ya rage dagani sai shi a motar .
Ya dan ja lokaci ba tare da yai magana ba sai can ya danyi gyaran murya yana fadin ke ina son ki kara saurarena da kyau kiji me zan fada maki.
Na dan daga kai a cikin tsoro kamar kadangaruwa ya furzu wani iska kamar abinda zai fada ansashi ya fada dole ne lokacin.
Ya fara magana a cikin muryan nan nasa mai fidda wani irin amon sauti ya fara ratsa kunnuwana.
Na fada maki tun gida wanan wuri akwai yan uwan mahaifina akwai na mahaifiyan mu kin sa wasu wasu baki sansu ba.
Don haka duk abinda wani ko wata zasu fada maki iyakarsu dake murmushi kada ki yarda ki wani abinda zai ba dani a gurin duk yadda nace dake haka zakiyi.
Zanso idan mun zauna zandan rika jan ki da hira ke kuma kina murmushi a cikin wayewa kada ki yarda ki nuna min kauyancin ki a nan.
Idan kinyi abinda nake so kin taimaki rayuwan ki har na yan uwanki nan gaba sai duniya tasan da diya mace ma yace kamar kowa.
Yana fadin haka ya dan yun kura kamar zai tashi daga wurin dai kuma ya dawo ya zauna tare da fadin nasan mami zata bincikeki idan mun dawo gida kice da ita ni kike so idan kuma kin ki ruwan ki wanan duk abinda mami zatayi ki nuna mata ni kike so.
Yana fadin haka ya juya ya bude motar ya jefa kafanshi daya waje tare da juyowa hana fadin ki dakata an fito in bude maki motar aikin ki ya fara daga yanzu ke nan.
A zuciya na amsa cikin damuwa da tsoron me haka ke nufi ke nan ga yanayi ya canza a lokaci guda duk murna da daukin da nakeyi in shiga wurin bukin inga irin kallon da su Rufaida zasu min sai naneme shi na rasa don yadda nake jina kamar wata mara lafiya dani.
Daga haka ya fita a motar ya bani gabana na faduwa don har lokacin na kasa hada maganan shi wuri daya in gane me yake nufi da hakan.
Kayan jikin shi kawai abin kallone don ina kulla yana sha,awan fararen kaya don duk kyau tufafi farin kala zai saka a jikin shi.
Yau ma rigace da wando da ban san ko na wani yarene ba sai yar karamar hula fara mai zagaye a kanshi rigar tana da aninaiya a gaba manya dasu har uku sai wani adon zaiba na manyan zane da akaiwa jikin rigar.
Idan nace wurin taron nan gaba daya ba wanda yakai haduwa banyi karya ba don yadda kyaushi da kayan jikin shi suka kara haska wurin.
Don yayi matukar kyau yau fiye dama kullun ko dan yau adon buki yayi ya kara haskawa haka oho sai na nemi nawa kwalliyan na raina kaina a wurin.
A hankali na fito daga motar tsikar jikina yana wani tashi yarrr daga kaina har zuwa kafana dole badan naso ba muka jera har muna hada kafada a yadda muke tafiyan.
Da sauri na dan jada baya don yadda muka manne mind your self OK ya fada ba tare dako na bayan mu sunji yai magana ba.
Buki bidiri birede wurin ya cika ya batse don tun daga ganin haraban kai ma kasan yau babu kama hannun yaro sai dai muce Allah sa a watse lafiya.
Saida muka dan tsaya a wajen na yan mintina kafin a bude mu shiga kamar an bada sanarwa shigan mu don idanuwan da sukayo kan mu can.
Masha Allah mai sanarwa ya fada kunsan kaduna da izala ko dan gala yana izala kaduna kowa sunna Allah yasa muga Annabi Allahuma amin.
Kamar in shige kasa in nutse dan kunyan abinda mc din ke fada a kanmu da shigowan mu hakan ya kara jawo hankalin kowa gare mu.
Tafiya muke guda guda wanda zai nuna muna inda zamu zauna yana gaba security din shi suna daga bayan mu.
Kwalliyan da gyaran da mai kwalliyan tayi min yasa basuyi saurin gane nice ba kunsan yadda kwaliya yanzu ke canza siffan mutum lokaci daya tundai in an hadu da wace ta iya tsarawa.
Haka muke ta tafiya kafada da kafada har zuwa wanan table da aka tana da don mami da iyalin ta a wurin.
Tunda naga yan gidan na soma kokarin sunkuyar da kaina kasa don nauyi da kunyan su daya kamani lokaci daya saboda kallon mamakin da suke muna gaba dayan su.
A, a, a ya J yau yar mami ne haka ka, , , , hannun daya daga mai yasa jalal ya kasa karasa abinda yai niyar fada sai ya zagaya ya ja min kujera tare da dan nuna min in zauna.
Nakai zaune a hankali godiyana yau ga Allah da baiyini mai garaje ba sai sanyin jikin nawa a yau yaba da kala a wurin.
Saidana zauna ya zagaya ya zauna a dayan kujeran a daidai lokacin da mc ke fadin yanzu dai kujeran hjy iyami ya gama haduwa tare da sanar da shigowa ya Jafar da bayanin ko waye shi da kuma inda yake aikin sa sai kuma ya kara da fadin.
Sai bride to be insha Allah kamar yadda kuke ganin wa yan nan masoya sun shigo muna da haske mai haska gidan kowa a wurin nan.
Ya jafar ya dan rankwafo inda nake yana fadin kinji me mc din nan ya fada game damu ko ?
A dan razane na dan sake murmushi yake na bude bakina da mai kwaliyan nan ta fesa min wasu abubuwa tare da wani sweet na tsotse tun a gida sai hakan yasa bakina fitar da wani kamshi mai ma,ana har yana jin shi a hancin shi lokacin.
Sai ka dauka kai dake kallon mu kaga masoya na asali a wurin yadda muke mami kan imani ya hanata magana da kawar da kai daga garemu.
Ba mami ba har yaran ta da muke zaune gaba dayan su sun kasa boye mamakin su a wurin ;
Hakama sauran kujerun dake kusa dana mami din inda yan uwane da abokan arziki suke zagaye damu a wurin kowa imanin ganin hakan.
Rufaida tunda salma tace waike baki ganeta bane zee ce yar mami fa yarinyar mami dai da muka bari a gida.
Ai bata san lokacin data mike tsaye ba tana fadin kutumar uban nan zeey zeey dai zeey yar aikin mami dai.
Amma wai yaya hakan ya faru dama yarin yar nan haka take ashe ?
Shike nan dama Ruby ta fadi hakan gashiko yanzu hakan ya tabbata muna nan shekara da shekaru muna dakon wahala ashe ?
Yau ga wata yar kauye mara asali da tushe tazo ga banza ta sameshi a saukake a wanan lokacin muka danyi wanan magana Rubby tace ku duba ku gani wallahi soyayya sukeyi ki duba yadda suke nuna kauna a gaban mami.
Kai haba ina wallahi sam sam wallahi ina hakan ba zai taba yuyuwa ba muna zaune wata banza kamar zee tazo ta kwace muna shi.
Tunda kowa wurin nan cikin ku zaman jiran ya zabeta takeyi haka kawai zamu kyale muna kallo wanan yarinyar kauyen ta rushe muna plain din mu.
Humm yazu na yarda da zancen ki Rufaida yarinyar nan matsafiya ce ta sace zuciyar mami yanzun kuma ga wanda ko a zato bamu taba kawo hakan ba a ran mu wai yaya J zai kali wanan banzan yarinyar yar aiki ya kyasa.
Wallahi da sake sam hakan ba zai taba yuyuwa ba kan sai dai inda wata manufa yazo da ita wuri nan wanan kan na yarda kai koma dashine wanan yarinyar ta gama shammatan mu yau.
Da hannu aka kira Nazira daga table din da iyayyen su mata ke zaune ciki harda uwar nazira din dake zaune da matan yayyun ta a wurin.
Tana zuwa ta dan duka dafata matar tayi tana fadin wai wanan yar yar gidan waye a garin ko kuma a kasan nan ?
Wanan mama baki ganeta bane zeey ce yar mami mawa mami hidimar nan muma abinda mukewa magana yanzu ke nan a can.
Mami tace Jafar wai me nake ganine nan haka meke shirin faruwa ne wai haka ta tabaya tana tsure shi da idanu babu ko kakautawa a wurin.
Please mami kada kiyi wani motsi a nan idan mutane yana a kan ku yanzu don Allah mami kibar komai har a koma gida.
Jafar din baiyi magana ba sai murmushi yakeyi yana fadin surprise mami aina fada maki zan baki mamakine da zabina a yau ko ?
Please ya J gaji me ya mamud ya fada ai so a daina wana maganan a nan please Aisha ta fada kanta na duke kamar ba itace ke magana ba.
Daga inda Nuriya ke zaune kusa da mijin ta take fadin wai mamaki a nan kuma aka kare gun yar , , , ,
Hannu mami ta daga mata yasa tayi shiru bata karasa maganan da zata fada ba lokacin taja bakinta tayi shiru.
Koda aka kira mami tashi tayi friends din ta suka mara mata baya sai da ya bari an dan rage muka tashi zuwa wuri mami tayi niyar juyawa tabar wurin kafin mu iso saida wata kawarta ta dan rada mata kada tayi hakan don Allah.
Kudin daya saka min a yar jakan hannuna nima na bude jakkan ina likawa mami din ya dan rada min zakace mudin wasu masoyane na gaske sai ji mami tayi mun rungumeta a lokaci guda.
Masu photo suka shiga daukan mu a cikin karfin hali mami ta rungumomu a jikin ta don kawai ta kawar da hankalin kowa ga zargi komai a wurin kanmu baki daya.
Saidai na ciki na ciki a zuciyar mami don in ma wasa jafar yai mata haka dani wasan yayi yawa haka don hankalinta ba karamin tashi yayi ba da ganin hakan.
Tsoron ya Allah shine kada wanan abin ya zama gaskiya ga jafar don zuwa yazun bataga alaman wasa a idanun dan nata ba yau.
Daga inda nake na dan dago ido na saci kallon mami din dake tsaye suna magana da wata kallon da taimin yasani jin wani irin ba dadi a raina.
Haka yasa na fara shan jinin jikina gabana sai faduwa yake uku uku riko hannuna naji anyi daga bayana yasa na dago da sauri yayane dan rankwafo yana rada min zaki gaisa da abokainane gasu can .
A haka muka bar wurin yana rike da hannu na har inda ya barsu kai maginet wanan irin zabin naka a ina kashiga kasan nan ka samon wanan pretty girl din.
Suka shiga wasa shi duk su ukun yana tsaye kimkam ko murmushi baiyi kamar an tsayar dashi a wurin dole.
Muryan wani daga cikin su ke fadin dole mc ya bamu fili mu gwadawa duniya farin cikin mu da zabin ka.
Bai tsaya jirab komai ba ya nufi wurin mc tun kan ma ya dawo inda muke mc yasa muna wakan tare da sanarwa zamu fito fili abokan JM nason su nuna mai farin cikin su da wanan ranan.
Ance ana buki da dollars ranan koda bansan darajan kudin ba nasan masu daraja ne wanan kudin yadda wurin ya dauki ihu ga baki daya ya jafar yana rike dani da hannu daya.
Dayan hannun kuma yana cikin aljihun wandonshi muke takawa a hankali sai photuna ake zuba mana babu kama hannun yaro.
Sai daya gaji yaja hannuna ko ya fahinci ina gab da bashi kunyane don kiris ya rage in duka in cire takalmin dake kafana kada in fadi.
Daurewa kawai nakeyi a hakan sai gashi yaja hannuna mu fita daga hilin wasa bama nan ba kawai gaba daya dakin taron muka bari lokaci guda security dinshi na biye damu duk inda muka saka kafan mu a wurin.
Maroka suka sakashi gaba yana rike da hannu na har muka fice daga dakin yayin da suka dan sarara muna ke nan.
Wani iska mai sanyi naji ya dokeni sai da nayi wani irin ajiyan zuciya kamar an gafarta min a wurin.
Mota muka shiga ba wanda yai magana a cikin to nima me zance nida nawa umurni kuma in aiwatar don dole na.
Sai da muka shigo unguwar ne ko ina yayi tsit alaman dai dare yayi sosai a lokacin duk mutane sun shige gidajen su.
Mota na tsaye kofan gidan mami din ana jiran maigadi da akewa horn ya bude get din gidan naji yana fadin kin taka matakin farko a cikin shirin mu.
Yanzu saiki shirya mataki na gaba shine amsa tambayan mami a gareki kaina na fada maki abu daya nake so dake shine.
Idan mami ta tambaye ki a kaina ki fada mata nine nace ina son ki nasan zata tambayeki ke kina sona ko bakya sona ?
Kada ki manta da amsan dana fada maki dazun ki basu idan sun maki wanan tambayan.
Kai na gyada don ba bakin bashi amsa don duk a cikkn fargaban abinda zai faru idan mami ta dawo nake yi.
A kofan shiga gidan ma mun dan jima ana buga kofan kafin lami ta bude mana daga ciki don su aka bari jiran gida dakuma hjy dake dakina.
Har dakin ya kaini tsohuwar na zaune saman sallaya taji shigowan mu take fadin a, a har kun dawo ke nan eeh gatanan na dawo maki da ita ya fada yana wucewa bai yarda ya tsaya a dakin ba.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
UBANGIJI ALLAH KA KAREMU DAGA SABA MAKA TAKO WANI HANYA A RAYUWAN MU ALLAHUMA AMIN, , , ,
Gaba na faduwa ina tsaye ban iya gusawa a inda nake ba tunda ya bar dakin jin muryan hjy ce data juyo gareni tana fadin.
Yar nan lafiya kuwa hawaye ne yazo min lokaci daya nayi karfin halin girgiza mata kai ina daga kafa da kyat nace ba komai hjy.
A cikin karfin hali na karasa cikin dakin ina kokarin aje jakkar dake hannuna da naji ya kara min nauyi a wurin.
Bandaki na nufa tukun na fara sake fitsarin tsoro daya taru mi a mara na dan dade tsugune ina sake shi kamar ba zai tsaya ba lokacin.
Na dade a zaune ina tunane kafin in samu inyi tsarki in fito daga bandakin duk jikina a sabule har lokacin yau kan nasan na taro mach a gidan mami wanda mai fitar dani sai Allah.
Ni da wani ido zan kalli mami dashi wai yau ni zainab yar aikin ta ke ikirarin zama sarakuwar mami a duniya.
Ni zainabu wani hali da rikici na jefa kaina a ciki aikin dana sani daga baya ke nan yake zuwa don nayi dana sanin yarjewa yaya Jafar bukatan shi yafi sau dubu a wurin.
A gurguje na shiga dakin mami a cikin daren nan don daya saura na dare a lokacin na gyara ko ina na dakin ban tsaya ba don kada mami ta riskeni a ciki na jawo kofan ina dawo na haye kujera dama na cire kayan jikina tun kan in shiga dakin mami din.
Tundana kwanta ba dunkule a cikin hijabina ban yarda nayi ko motsiba wurin.
Ina jin hjy na magana tana fadin su a can zasu kwanane har wanan lokacin basu dawo ba haka.
Shiru nayi kamar ina barci haka yasa ta kyaleni sai can na fara jin hayaniyan mutane a gidan alaman an fara dawowa ke nan daga dinner din.
Can aka turo kofan dakin da karfi ana kiran sunana muryan Aisha ce sai naji hjy na fadin yau naga sha shanci a gidan nan.
Zaki turo kofa haka babu sallama to boyar taku tayi barci tunda yaron nan ya dawo da ita don da alaman a gajiye takema ko da ta shigo.
Mami ke kiran ta yanzun nan a dakin ta ta fada a cikin wani murya da ban santa dashi ba sai ranan.
Kada ki soma ki tada yar nan daga barcin nan kije ki fadawa uwar taku tayi barci tun dazun inji ni haba kowa fa rai gare shi kamar kowa ace mutum ba zai huta ba haka dare ai mahutane ta fada cikin bacin rai.
Ina jin lokacin data rufo kofan hakan yasa nasan ta tafi na sauke wani iri ajiyan zuciya daga kwancen hjy taci gaba da fada ita kadai a dakin.
Sai muryan sallaman mami tana fadin hjy ashe baki barci ba ina zanyi barci kuna waje har wanan lokacin iyami.
Ki duba lokaci fa karfe nawa yanzu zaku biyewa shedanu kukai lokacin nan a waje dare fa mahutun muminine don a daren yake raya rayuwan shi walau ta hanyar barci ko na samun ganawa da ubangijin shi a natse.
Wallahi hjy taron ne ba, a fara da wuri ba tana magana hankalinta na inda nake kwance zata tayar dani .
Yar nan tayi barci tun dazun haba ku rika sauwaka mata hakana tana iya kokarin ta gidan nan yanzu sha shan yarki ta shigo tayar da ita.
Koma me zatayi ita Aishan tai maki mana baku bari yaron ya samu albarka a wurin ku saboda karyan zamani har yaushe kamar Aisha za ace ba zata iya aikin da wanan yar zata iya maki ba.
Ba aiki zatai min ba hjy dama dai tambayan ta nake son yi kawai mami ta fada sai hjyn tace.
Koma menene tunda tayi barci ai sai a kyaleta har safe a tambaye ta itama fa mutum ce kamar kowa a cikin ku.
Hjyce ta ceceni a ranan don mami fita tayi a dakin ba tare data tasheni ba kamar yadda mahaifiyar ta ta hana.
Ranan idan nayi barci barawo ne ya sace ni don haka na kwana ina sake sake bani kadai ba har wanda duk abin ya shafa banda ya jafar dashi ko a jikin shima hakan.
Aiko gari na wayewa sai ga sakon mami inzo gabana na duka uku uku na mike daga inda nake zaune a takure na nufi dakin mami din.
Addu,a kan nasha shi yafi cikkn kwando ranan da sallama na shigo dakin daga ita sai Aisha da mama Ramatu.
Mami tayi tagumi tana zaune kasa a inda ta idarda sallah asuba ta rasa abinda ke mata dadi a rai so kawai take taji na bakina abindake wakana a tsakanina da danta.
Nayi sallama na shiga sai mama Ramatu ne ta amsa min a lalace koshi Aisha ko tana bina da wani irin kallon mai kama da mamakina a fuskanta.
Kasa nakai cikin karfin hali ina fadin ina kwana mami ban jira amsawan ta ba na juya airin mama ramatu itama na gaida ita na juya gun anty Aisha itama hakan ne.
Shiru dakin yayi na dan lokaci ina tsugune kafin inyi yunkurin mikewa don shiga ban daki in wako yaddana saba yi.
Dakata zainab komaki zauna mami tace dani na koma da sauri inda na tashi ta dan dago kai ta kalleni kafin tace zeey ban saki da karya ba ko wani abu makamancin hakan.
Balle boye magana don baki taba min shi ba tun zuwan ki gidan nan wurina.
Kaina dan gyada a hankali yayin da gabana yaci gaba da faduwa sosai jiya tare da wa na ganki zeey ?
Kai na dan dago da sauri na dan saci satan kallon mami na samu ta kafeni da ido tana son amsa daga gareni.
Shiru na danyi tare da dukar da kaina kasa ina kallon carpet din da nake saman shi.
Bakiji me aka tambaye ki bane mama Ramatu ta fada daga inda take zaune din da dan karfi hakan yasa na dan zabura tare da dago kaina ina fadin babu komai mami.
Babu komai kuke haka jiya tare dashi a gaban kowa Aisha ta fada a dan hasale tana watso min harara.
Ni ban san komai ba tun bayan da kikace mai kwaliya ta shiryani yadda ya kama kika fita kika barni da ita mun gama na fito na samu duk kun tafi babu kowa da zanbi sai gashi shi yace nazo mu tafi.
Wani ajiya zuciya mami ta sauke har ina jinta daga inda nake Aisha ko na kokarin fadin wai kina nufin ni No wallahi mami ban san komai ba a kai kawai dai ya ban kudi a gyara mata kai daga can kuma ya kara turo kudi waina saya mata kaya expensive one don kin manta ki saya maya yanzu hjy ke fada mai.
Jeki zan kara nema ki mami ta fada tana kallon mama Ramatu da itama din ita take kallo don jin abinda ta fada.
Kai mami ta gyada mata alaman ta bari in fita daga dakin tukun suci gaba da magana zan shiga ban daki tace barshi anjima ki dawo idan mun fita.
Na juya na fita nan na barsu a dakin sai da na fita ta juya tana kallon Aisha dake zaune tana fadin duk abinda aka kitsa tare dake aka shirya hakan ashe kika boye muna.
Wani mami wallahi ban san komai a kai nima iya abindana sani ke nan na ta fada yanzu dana sani ai dana fada maki komai tuni.
Daki na koma na takure a wuri daya ina faman funane a raina don na kara daure kaina again ban san da wani ido zai kalleni ba kuma nasa bangare ga mami bawai ta yarda dani bane tunda har tayi mi abinda bata taba min ba yau shine.
Wai in fita idan sun gama na dawo in gyara dakin kenan da sauran maganan da zasuyi a kaina ke nan a dakin.
Shirun da nayi yasa hjy dake magana still kan daren dasu mami sukayi jiya a waje taji nayi shiru hakan yasata jutowa gareni.
Hawayen da ban san yana zubane daga fuskana ta ganin haka ta fara sake salati tana tafa hannu tare da fadin yarnan an maki wani abi ne ko kiranda iyami ke maki jiya na hana a tasheki tai maki fada a kansa yanzu don naga bata so hakan ba dama.
Saboda shine ta bata maki tunda farar safiyan nan ko da sauri na girgiza kai don nasan baida wuya yanzu ta sauke wa mami bala,i akai ta kara jamin wani tsana.
Kofan dakin aka turo Aisha ce tsaye a kofan tana fadin zainab mami na kira daidai lokacin da hjy ke fadin.
Ke kan yar nan arr da halin nan naki ace dan musulmi bai iya sallama idan zai shiga guri gara dai da uwarku ta raboku da kasan kafiran nan tun kan kufi haka ai.
Sai kuma jin abinda ta fada ta sake fadin wai wani laifi tayi maku haka baku bari yarnan ta hutane wai ?
Ba laifi tayi ba naji Aishan ta fada a daidai lokacin da zan fita daga dakin bayan fitana asheta fada mata komai dake faru tun daren jiya din a bayana.
Sai da tsohuwar ta gama ji take fadin meye laifi a cikin zancen nan idan shi jafarin yace itace zabin sa ai baiyi zabin banza ba nake gani ko ?
Haba hjy yar aiki ce fa wanan yarinyar da bata waye bane zai dauka a matsayin matarshi yadda ya J yake wayayye dan boko mai ilimi din nan dashi.
Yo wani waye akwai wanda yafi wani a gurin Allah ne idan ba Annabin rahama ba shi kadai zai fadi haka sai ko wa yanda sukai zamani dashi aka tabbatar masu da aljanna .
Kai don Allah hjy ki daina danganta wanan da yayan mu please ai abin kunyane ace wai wanan ce zabinsa haba dai.
Kaji min ya da wani maganan banza meye laifin zabin nasa har idan da gaske yakeyi ba wasa ba uwarku da ubanku ya aureta takai wanan din wayewa ne a lokacin.
Aida ba yanzu bane Aisha ta bata amsa tana fita tace kinci gidan ku nace kinci gidan ku yarnan da wanan maganan banza kece zaki zauna mashi da ita koshi zai zauna da abinsa.
Fita tayi ta kyale tsohuwar tana jin zancen ta na kara mata takaici a ranta sai ta dauki zancen tsohuwar ga tsufane kawai ke damun ta ba wani abuba don da tasan abinda takeyi da bata fadi hakan ba ai.
Ina shiga dakin mami ba tare data kalleni ba tana jin sallamana take fadin jeki ki wanke muna bandakin nan idan kin gama ki daukowa hjy abin karyawanta a kitchen.
Don mami ta dauki zugin mama Ramatu da wata kawarta da tun jiya ta zugeta a kaina baki daya don haka ta kudurta canza min daga wanan lokacin tun ban dauko mata magana ba a cikin diyan ta.
Wanan zugin kan mami ta haushi ta zauna akai sosai har yakai ta fara ganin aibuna a gareta yanzu.
Kafin in fito har ta shirya zata fita ta gaisa da mutane take fadin yi ki karasa ki fufo min dakina na amsa da toh kawai a cikin sanyin jiki ga canjin da nagani gareta.
Dakin mu tashiga gaida mahaifiyar ta inda ta samu hjy har lokacin tana mitan zancen ita kadai a dakin.
Koda mami ta shiga amsa sallama dai tsohuwar tai mata babu sakin fuska suka gaisa tayi mata ya jiki ?
Mami bata tsaya ba ta juya tana fadin bari ta leka yan uwa a dakin in dawo tana fadar haka ta fice daga dakin.
Har na gama gyaran dakin na jawa kamar yadda ta umurceni in mata da dakin na wuce kitchen na karbowa hjy abincin.
Ban daki na shiga nayi wanka na fito na shirya a cikin wani atamfa da Aisha ta bani dinkin buje da riga bujen dai bai matseni sosai ba yadda ita yakan matse jikinta idan ta saka a jikinta kafinta bani .
Ban zauna a dakin ba na nufi kofan fita daga dakin ina zuwa kawata hjy ta fada zan je in karbo abincine a kitchen na bata amsa.
Yau kuma ba a nan mukeci tare ba dake mazaki dawo ki dibi abincin nan kici karna saba maki.
Ko ta fahinci tsoron mami nake sai tace kowa yasan tare dake nake cin abinci sai yaune zasu kawo min wani zance.
Dole na dawo na rakube a gefe ba tare dana yi yadda na saba muna wasa da dariya a gurin ci ba haka hjy ta sakani gaba dole na debe abinci mai yawa tana kara ina ya isheni haka ta kyaleni.
Na fara ci ke nan mami ta shigo dakin tana magana sai ta dagata da maganan tana fadin ke kuma meye haka ?
Me tayi hjy ta tambaya tana kallonta da mamaki hjy don me zata zo ta zauna tare dake a nan tana cin maki abinci ?
Yau din kuma iyami ina har ke muna zama da ita ana aci abinci baki taba fadan wani magana sai yau ?
Daga yau din ban son in kara ganin hakan ta koma can wurun yan aiki ta dinga ci tare dasu kande da lami.
A, a iyami bana son irin haka wanan ba halinki bane hakan ban san kuma yaushe kika fara hakan ba.
Hjy na canza tsarinane yanzu a gidan nan don a fara bambamta yan aiki da yan gidan nan iyami dakata hakana hjy ta fada tare da juyawa inda nake tana kallona kafin tace dani kinga kawata.
Jeki falo kici abincin ki ki bamu wuri zamuyi magana da uwar ki ina jin hakan na mike da sauri don barin dakin.
A daidai lokacin mami ta kai zaune a kusa da mahaifiyar ta saidai ita saman kujeran ta zauna ba a kasa ba inda hjy take zaune.
Ko dana fita ban nufi cikin falon inda nake jin dan dararakun mutane na zauna dan filin da zai sadaka da falon da gefen dakunan mu din.
Ina kallon abincin ba tare danayi ko yunkurin cin cibi daya daga abincin ba sai idon dana zuba mai kawai.
Iyami kada ki bari shedan ya rudeki kiyi yunkurin yaki da ubangijin ki kan abinda Allah shida kanshi ya halasta hakan.
Yarki dazun ta fada min komai dake faruwa daku tun jiya wanda na hango kina kokarin fita daga ilimin ki da irin tarbiyan ki dana sanki na girmama dan adam a duk yadda yake.
Hjy ba hakana bane ni yaran nan zasu kunyata a cikin taron jama, an arzikina wai yaron nan ya nemi ya raina min wayau ya hada baki da yar nan a kunyatani hjy ?
Akunyataki kamar yaya hjy ta tambaya shi auren ne kunya ko yarinyar ce kunya a gareki yau kuma kina kunyan a santa da ahakin ki kika ajeta a gidan ki har kika jata a jikin ki kamar kece kika haifi abinki.
Wani irin shedani ne yayi saurin tasiri haka a jikin ki har kika manta da bayan ki ke ?
Da sauri ta dago kai ta kalli tsohuwar hjy tace eh kin manta da naki bayan kina son ki maimaita tarihi a kanki yau.
Hjy bawai hakana bane ni abinne yai bala,in bata min rai kawaion su wullakantani har jafa, , , , ,
Hannun da tsohuwar ta daga matane ya dakatar daga karasa maganan ta datayi niyar fadi a kanmu.
Iyami na haneki tun wuri da wanan halin abinda zai kawo dana sani daga baya wanda zai zama keya gareki.
Yaya zaki idan Allah ya nufa wanan abin mai yuyuwane garesu ko kina son in kin matsa da jayayya da ubangiji ya dauki ranki ayi a bayan ki.
To ina baki shawara ki natsu ki shiga hankalinki tun wanan abin bai fita waje an dawo ana maki dariya ba daga bayan ki.
Ina yar nan ke kika kawota gidan nan har danki ya ganta ya nuna sha, awan shi gareta duk ko da yadda take ba yar kowa ba kamar yadda ku kuke gani.
Shin iyami kin manta da yadda akayi lokacin auren ki da mahaifin yaran nan sam ban taba zaton zaki manta da hakan ba har ace yau ke da kanki kike kokarin yin wanan halin da ba, a san musulmin kwarai dashi ba.
Ina wanan abin ke kanki kamar darasine a gareki ban taba zaton har zaki yada kiyi ko maka mancin hakaba a yanzu.
Daga inda nake zaune naji takon tafiya haka yasa na dago kai da sauri ina kallon mai zuwa a lokacin ya Jafar ne da yaya mamud suna tafe suna magana a tsakanin su.
Saidai ganina a wurin yasa sukaja suka tsaya suna kallona da sauri na gyara zaman da nayi da farko ina gaidasu.
Duk kallon mamakin ganina a wurin sukeyi sai ya mamud ke fadin lafiya kanwata kika zauna a nan haka a kasa baki je dinning kin zauna ba.
Wani kallo ya Jafar ke min ba tare dayayi magana ba sai hannayen shi daya zuba a cikin aljihun wandon shi bakin wandon jeans dake ciki ya dan fito waje ya wani kara haske ko kallon tsoro nayi masa oho.
Badake ake magana ba ya jafar din ya fada na dan dago kai na kallesu sai nayi saurin dukar da kaina don duk idon su yana a kaina.
Ganin ina kokarin mikewa yasa ya mamud ya fara tafiya shima ya mara masa baya zuwa dakin dana baro su mami din da hjy.
Da sallama suka shiga dakin saidai ganin yadda daga hjyn har mami suke sai yasa suka dan tsaya daga kofa basu karaso ba sai ya mamud ke tambaya lafiya dai mami ko wani abinne ya faru ?
Shike nan ma hjy ta fada ga magani ga ciwo Allah ya kawo ki tambayi dan ki a gaban mu yanzu aji idan da gaske yakeyi ko wasan da kike tsamani kika tsani yar mutane haka ba gaira ba dalili lokaci guda .
Kin hana yar mutane tun jiya kwanciyan hankali duk kunbi kun rikita yarinya ga baki daya ni bani son irin haka wallahi abu baikai abin daga hankali ba zaku sakawa mutane rigima a gida.
Kallon mami yayi ya karaso inda take yana kaiwa zaune ta gefen gujeran tare da kamo hannun mami din yana fadin wani abu ya farune mami ?
Bai faru ba zai dai faru ka gaya muna meke tsakanin ka da Abu dana ganku jiya a gurin taro har kana nuna muna wai surprise din ka ke nan garemu ta fada rai a bace.
Abu mami ?
Waye hakana mami ban gane wa kike nufi ba hannun ta dake rike a nashi ta fisge tana fadin zeey yar aikina nake nufi ba wani ba.
Kai ya girgiza tare da dukar da kanshi kasa can ya dago yana fadin mami ba ke kikace na fito da yarinyar data kwanta min a kasan nan ko diyar waye ba ?
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUKU 🦅
2️⃣5️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YA ALLAH MUNA ROKON RAHAMANKA DA KARIYAN DAGA DUK WANI ABIN CUTARWA A GAREMU ALLAHUMA AMIN, , , , ,
To ka samo din ta tambaye shi a cikin gatse ?
Eh na soma mana mami kuma ai a karkashin ikon ki take itama yarkice kamar su Aisha.
Wa ke nan ya mamuda ya tambaya wanan yatinyar taki da kika dauko a kauye mana ga zahiri kun gani jiya tunda kun gamu tare.
Mami kan yake tayi wanda yafi kuka ciwo kafin ta tattaro natsuwa don hjy dake wurin a zaune bata da halin furta mai wani abu a lokacin.
Saidai duk da hakan sai da mami tayi bajintar fadin wai zeey dai kake nufi ai zee din kasan a matsayin dana daukota kuma bayan haka karatu take a yanzu.
Mami nasan da hakan saidai ai takai munzalin aure a yanzu don haka aurena da ita ba zai hanata karatun ta ba.
Ko kin manta kin fada muna kema kina karatun secondry daddy ya ganki ya aure ki lokacin.
Look jafar bana son shirmen banza mata nace ka fito da ita in maka aure at dis stage bawai ka tsaya kana min wanan shirmen ba haka.
Zainab na fadama karatu take kuma bata cikin zabin matan da nake son ka aura don tayi kankanta gare ka yanzu.
Hjy dai da yaya mamud na gefe zaune suna sauraren draman uwa da danta sai murmushi suke masu kawai.
Mami to aini ita din ce chooice dina sai ta karasa girman ta a gurina don ni a hakan da take yayi min daidai.
Jafar kada ka mayar dani abokiyar wasan ka idan kai tayi mani ba, , , ya mamud ne yace mami please.
Ki barshi ya zabi abinda yake so a rayuwan shi tunda shine zai zauna da ita bake ba kada a tillasta mai yayi abinda baiso a dawo ana dana sani daga baya kuma.
Hjy tacs fada mata dai dan nan ko kai zataji maganan ka tunda ni ban kai matsayin da zan tsawata mata ta saurare ni ba
Hjy bawai haka bane na lura yaron nan rainawa mutane wayau yake son yiwa mutane tunda mun tursasashi yayi aure bari ya zabo wace bata yuyuwa a gareshi yanzu ya rama abinda mukai masa ko ?
Wallahi mami tunane baikai ga hankan ba itace dai din naga tana daidai da rayuwana ita kuma din nake so a matsayin a bokiyar rayuwana.
To ban yarda bami ta fada a hasale tana mikewa hjy tace iyami dawo ki zauna mu kai karshen wanan maganan a nan tun wani bai kaiga ji ba.
Shiko jafar jikin shi ne yayi sanyi lakwas don bai taba tunanen mami zata dauki abin da zafi haka ba.
Ya mamud ne ya kawar da duk wata magana ta hanyar fadin tunda ita ka zaba din ba laifi ga hakan saidai yana da kyau itama muji ta bakinta ai idan tana son ka shike nan aurene mami ba wani abuba ai.
Mai yuyuwa kai itace zabinka ka ganta kana sonta a haka karamar ta ita kuma yarinyar ba kai mata ba a ranta .
Kaga ba zamuyi mata dole ba a kanka a matsayin na yar amana a wurin mami din don haka sai muji ta bakin ita yarinyat kuma.
Ban gane abinda kake nufi ba mamud mami ta fada tana kallon yaya mamud din taci gaba da fadin kaima kasan tunda ya tursasa mata ai bazatace batayi ba tunda duk mace ko banza neman irinsa takeyi.
Mata ma masu aji da ilimi da wayewa suna binsa su sameshi yana gudu sai akan wanan yar kauyen yarinyar idon ka zai sauka sai dai idan kana da wani manufane a kan hakan dai.
Banda manufar kome mami ita din ce nagani nake kuma so a hankan don banga wani matsalan da zaisa a hanani aurenta ba a tare da ita.
Mtss mami taja wani matsiyacin tsuki tana fadin Jafar kana son bacin raina da jefa yarinyar nan ga fushi wallahi.
Mami kiyi hakkuri yanzun nan zan kira ita yarinyar a gaban sa muji ta bakinta idan tace ta yarda dashi shike nan mami sai ki masu fatan alheri a rayuwan su.
Me zata fada tunda tana son shi mamud karka mata fa yar kauyece dama nema tafito yi a birni kuma ta samu a yanzu.
Gashi ta samu wanda darajan ta da kimarta baikai ta samu ba a yanzu, abinda bata taba tsamanin samun shi ba sai tace maka a a kuma ?
Mami please ayi hakkuri aji ta bakin ta idan ta amince ai masu fatan alheri shiyafi yanzu.
Mamud na fada maku yarinyarce bana son ya aura gaba daya don haka abar wanan na zancen tambayan ta please mamud.
But mami ni kuma ita din nake don banga wata da hankalina ya kwanta da ita ba bayan wanan din.
Jafar idan ma tausayinta ne yakaika fadin kana son ta ai ba sai ka furta kalman aure a tsakanin ku ba kana iya taimaka mata ta hanya da dama basai wanan hanyar ba daka fito dashi wai auren ta zakayi.
Jafar dake ta faman latsan wayan hannun shi tankar ba da shi ake zancen ba sai lokacin ya dago kai yana fadin.
Mami bawai taimakonta kawai nakeson yi ba ni kawai dai auren ta nakeso nayi dan tayi min a raina yana magana a cikin daure fuskan shi.
Daga inda hjy take zaune tace da kyau na mijin duniya kai mamuda kira muna yarinyar muji na bakinta yanzu.
Na bar gurin da suka sameni zaune don abincin ya gagara ci gareni don haka na dauka na kai kitchen.
Daga nan ne na tsaya don yin wanke wanken kayan da akaci abincin safe gasu nan an tara birjit don bakin da akayi gidan.
Maganan da mami tayi nake son in fara kiyayyewa da tace in dinga zama a cikin su lami da kande sune yan aiki irina.
Ina tsaye na fara tara kayan ne lami na faman sakamin albarka don haka suke min duk lokacin da nashigo zan tayasu wani aiki daya shafesu.
Muryan yaya mamud ne a kofan kitchen din yake fadin ke zainab zo mami na magana dake a dakin hjy.
Yana tsaye ya tokare hannayen shi a kofan shigowa kitchen din yayin daya zubamin idanuwan shi sai tausayin yadda ya sameni ya kamshi.
Juyawa yayi ya fara tafiya haka yasa na dauraye hannaye da sauri nabi bayan yaya mamud din ina jin wa yanda ke falo zaune na fadin.
Yar iska yarinya yau zakici uban ki gidan nan don yarinya kin tarowa kanki bala,i da hannun ki.
Idona ne ya kawo kwalla don ban kaunan abinda zakai a zagi iyayyena ko kadan saboda sanin daranjan su da nakeyi suko yan gida mami zagi a wurin su ba bakin komai bane a wurin su.
Zaune suke su hudu a dakin mami hjy ya mamud dashi gabana ne ya fadi don ganin su har lokacin a dakin .
Sallama nayi cikin yar siririyar murya hjy da ya mamud suka amsa min mami kan kai ta dago ta dan kalleni tare da kawar da kanta ga kallona.
Zauna a nan ya mamud yace dani yana nuna min wuri daga gefen kofa da nake tsaye saina kai rusunne da sauri ba tare dana zauna ba kamar yadda ya bukaci inyi din ba.
Kaina kasa ya mamud naji ya kira suna sai na dago kai a hankali na kalleshi yace mun kirakine muji ta bakin ki a kan wani maganan daba musan dashi ba tsakanin ki da jafar gashi zaune.
Ya nuna min shi da hannu sai lokacin na dan saci kallon Jafar din da idonshi sun kada a lokacin da gani shima yana cikin bacin rai ke nan.
Jafar ga yanan ya gabatar muna dake a matsayin wace zai aura kamar yadda mami ta bukaci da yakawo mata, matar da zai aura a yanzu.
Da sauri na sake dago kai nakai kallona ga Jafar din da shima a yanzu nice yake kallo da idanuwan da suka kade mai lokaci guda.
Don haka muke son jin ko kin amince da wanan ra,ayin nasa kema kin shirya da zaki aure shi kamar yadda ya bukata dake.
Dukar da kaina nayi kasa don ban san amsan daya dace in bada ba a wurin ga gardadin dayai min tun daren jiyan a mota ina tunane.
Ga mami dana hango tsanata saboda wanan zancen daya taso tsakanina dashi mami ta canza min gaba daya daga dare zuwa wanan lokacin kamar ba mami bace a gabana.
Don ba wanan yanayin na tausayina data min yau a gare ta ko kadan illa tsana karara da take nuna min a fuskanta.
Kiyi magana ke muke saurare ya mamud ya fada yana kallona don jin amsan da zan basu a lokacin.
Kai na fara girgizawa a hankali na samu na bude baki da kyat ina fadin ban san da maganan bani koma na sani ya jafar ba sa, an aurena bans shi don matsayina dana iyayyena baikai ko na yaron shi ba yaya.
Tunda na fara magana ido kowa ya zuba min sai mami dake fadin nikan nayi mamaki ina hankalin zeey da yatafi har take shirin tafkamin wanan kuskuren duk, , , ,
Dakata iyami ke a matsayin ki na uwa kin taba ganin inda aka tsiye yarinya haka wai ana tambayanta zabinta kai tsaye.
Kiwa Allah kiwa yaran nan adalci iyami tunda ni yanzu ba magana ta kike ji ba ban isa ba ko dan nima din banda mutuncine tunda nima daga kauyen nake ko ?
Yarasulu hjy me ya kawo wanan zance kuma har kina danganta kanki da hakan Allah ya gani ni ba manufa ke nan ba ta fada tana kallona az cikin yanayin daba zan iya fassarashi ba a lokacin.
Ke tashi ki tafi ya jafar ya fada a tsawace kuma ranshi bace ga wasu jijiyoyin kai da suka mai jasur a goshi abu fa farar fata sai suka mike sukai wani layi layi a saman goshin shi kamar mai tsananin ciwon kai a lokacin.
Da gani hankalin shi gaba daya a tashe yake mai a lokacin zainab jeki abinki ya mamud ya sake fada da sauri na mike nabar dakin.
Don dama a kage nake dana bar aurin saboda rikicin da nake hangowa a idanuwan su wurin.
Ina barin dakin kitchen na nufa har ina hadawa da tuntube don sauri saboda gaba daya na gama tsoracewa da lamarin nasu ga baki dayan su.
A daki kan hjy ta tubure tana fadin ya mamud yazo ya mayar da ita dakin ta ba zata zauna inda ba,a san darajan ta ba.
Hankalin mami ya tashi tsohuwar taci gaba da fadin yaron nan yace ga zabin shi ta yaya bayan kun gama tsorata yarjnya tun safe yanzu za a kirata ace ta fadi ra, ayinta a gaban kowa ?
Ke lokacin da akai maki aure haka mukai maki mami tace hjy kina dai son ganin laifina ne yanzu.
Wanan shawaran yaran nan sukazo da shirmen su a gaban kifa akai komai yanzu don Allah hjy kada kija zancen nan inda bai kai ba.
Yarinya dai tace ba zatayi dashi ba final Allahu akabar don kuma hankalin ki ya bata yanzu sai kikaji dadin hakan ke.
Allah na tuba ashe gaskiyane mace komai tsufanta wayau ta ragagge ne.
Ke yanzu har kina murna yar da kika raina kike gani ba a bakin komai ba ta iya budan baki a gaban idon ki yau tace maki batayi da dan naki da kike dauka wani kayan gabas a wurin ki.
Niyi tir da wanan hukuncin da kika bari yaron nan ya yanke a gaba me zan zauna inyi tunda banda sauran kima a idon ki.
Gidan ki nazo zaki iya min duk wani rashin da, a don yanzu kina ganin ke kin isarwa kanki a komai sai dai da badon jafari ba da sai ince yarinyar nan zainabu ta burgeni sosai .
To jinin ka jinin kane banji dadin yadda ta watsawa jafarin kasa a ido ba a gaban kowa don kawai tsoron idon ki data gani a daure kin sakar mata na mujiya .
Wanan maganan kuma sai yasa mami ta ji daci a zuciyar ta da kyat dai ta samu ta shawo kan yar tsohuwar ta fasa tafiya saidai mami bataji dadin yadda tsohuwar ta dauki zafi da ita ba haka.
Ya jafarko tunda ya fita ya bar mami da su ya mamud a dakin ya bar gidan tun mami bata damu da rashin ganin shi ba har dare yasa ta tambaya ko ina ya shiga haka bai dawo gida ba don hakan ba dabi a shi bane yin dare a waje .
Har yakai ta fara tambayan duk wanda ya shigo gidan a cikin mazan dake gidan amsa dayane dai daga shi har security din shi fun safe basa gidan.
Ta kira wayan shi yafi a kirga wayan ba ya shiga kwata kwata ba, a samun shi gaba gaba daya ranan.
Tunane kala kala mami tayishi ga zafin yarinyar daya mamaye mata rai gaba daya taji ta tsani yarinyar tana dana sanin daukoni dayi ta jefa a cikkn iyalin ta.
Gashi kuma hjy ma a nata ban garen haka ya jawo masu matsala da ita don tana matukar son mahaifiyar nata sosai.
Gaba daya gidan sai yai min zafi a yan kwanaki biyun nan babu wurin wanda nake dafawa inji sanyi kowa tsanata yake a gidan ga baki daya.
Sai gurin hjy kawai ita kuma yanzu ba zama muke sosai ba idan na shiga dakin sai zanyi wani abu don ina gudun mami tashigo ta sameni a ciki zaune yasa na koma kitchen wurin yan aikin da dukkan mu kawomu akayi gidan don aiki.
Hjy tayi fadan hakan har ta gaji ta saka min ido ta kyale ga yadda lamarin ya juye muna.
Ga zagi da nake sha a gun yan matan gidan a yanzu yayi yawa har takai ranan Rufaida tayi min mari biyu masu kyau.
Saida anty Aisha tayi mata fadan hakan kan su dan sasautamin don Allah tunda ba laifina bane shine ya ganni yace yana sona ai.
Ba nice na leke mashi ba kuma yanzu ba wanan zancen budan bakin Rufaida sai cewa tayi Aisha kece baki san halin yan kauyen nan ba.
Mudake tare dasu muka san halin su basu shigowa gari sai sun shirya an asirce su yadda duk namijin daya gansu ba zai iya kawar da idon shi a kansu ba meye ba a yi yanzu halan.
Gasu da sihiri mai dafi da kaifi wanda in basu ba kainan dan birni kace ai maka saidai aci kudin mu ga banza.
Tace au hakane nima fa abin yaban mamaki ace wai duk wanan baiwa da jin kan na ya jafar ga ilimi da wayewa amma ace wai zee yake so shi .
Wanan to zarcin da suke min ne yasa hankalina ya kara dagawa sosai a gidan naji ina son komawa kauyen mu baki alaikum ba tare dana fadawa kowa ba.
Sai dai kuma ina jin tsoro don ban san kan garin ba kada in fita ni kadai a ganni ba kauya a saceni.
Tunda na fara jin ana fadin jibine tafiya Abuja na fara funane a raina don nagama yankewa kaina hukunci .
Gara kawai in gudu in koma gida ko ta kan anty safiya data kawoni da itama tazo tayi min tas kan wanan zancen a gaban mami ta wanke tas wanda nasan hakan tayi shine don kawai ta wanke kanta a wurin mami din.
Saida na bari hjy tayi barci na mike na fara hada kayana a cikin jakkata inayi ina juyowa ina kallon ta kada ta tashi ta ganni.
Aiko ban tsira ba don ashe idon ta biyu tun dana fara take kallon abinda nakeyi.
Juyowan da zanyi sai ganin ta nayi zaund ta kura min ido kaduwa nayi don ban zaci hakan ba na dauka tayi nisan barci a lokacin.
Ikon Allah yar nan me kike kokarin yine karda ace guduwa kike son yi daga gidan nan sai kawai na durkushe a wurin ina kuka ina fadin hjy gida zan tafi.
Babu mai sona a gidan nan mami ma fushi take dani har su anty Aisha da nake dan dafawa naji sanyi yanzu itama bata sona suncewa asiri nakeyiwa mutane suke sona.
Sai naga tsohuwar ta danyi murmushi can kuma tace kai yaro dai yarone ke in banda abinki dama ai duk wanda Allah ya mayar sani abu a duniya saiya fuskaci kalubali mai tsanani kafin ya taka nasaran shi.
Ba wanda ya tsamaci haka gareki sai gashi kwatsam Allah ya doraki a kan kowa dake gaban ki ga yanzu sun san da sani ke din yar bawaice kinga dole ko su nuna hassadan hakan gareki
Yanzu kinga mayar da kayan nan kafin gari ya waye wani ya shigo dakin nan yasan abinda kikai kokarin aikatawa har makiyan naki suji suyi maki dariya.
Hjy Abujan ne da za a koma ban son zuwa gara dai in tafi tun muna nan kusa da gida.
Yar nan ashe haka kike da gardaman banza ko dai kin san inda Jafarin din yake ne ?
Hakan data fada yasani fadi wallahi hjy babu komai a tsakanin mu ban san komai ba game dashi.
To wanan tafiyan da zakiyi ne zai sa a kara zargin ki a dauka kun hada baki dashine kan ki gudu hakan kuma na iya jefa iyayyen ki dake a cikin wani mawuyaci hali.
Kallon ta nayi da mamaki tace kwarai kin dai san iyami na da halin da zata sa a daure kowa naki a kasan nan ko.
Tsoron maganan da hjy ta fada ya kamani sai na kara fashewa da wani irin kuka tace kinga ki shiru kin san yanzu darene kada wani yajiyo mu a waje.
Na maki alkawari muddin ina raye zan tsaya maku har burin ku yaci ka duk da naga kin sare kin ji tsoron barazanan uwar taku har kina fadin shine ya tsara hakan.
Da sauri nace wallahi hjy ban san komai ba a kan zancen nan ni dai kawai komai da yace nayi a wurin nayi.
Da haka har ta shawo kaina muna dan hira kafin ta mike ta shiga ban daki ta dauro alwala tana fitowa nima na shiga don cewa da tayi min in yawaita yawan ibada in roki ubangiji sauki.
Naji dadin wanan shawaran da tsohuwar ta bani sosai don duk kunci dake zuciyana sai na nemeshi na rasa washe gari naji na tashi raina ya sake duk da mutanen gidan basu daina halin da suke min sai dai ko dunyima hakan bai damuwa na yanzu don shawaran dana samu daga tsohuwar.
Ga kuma iyayyena da nakejin tsoron lefin da basuji ba basu gani ba yazo ya shafesu ya zama dole a gareni in daure ga duk abinda zan gani don yakin nawa ni kadai kamar yadda hjy din ta fada min kar in yarda in kada iyayyena ga tashin hankali.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
ZAINAB IDRIS MAKAWA
JUMMA,AT MUBARAK YAN UWA MUSULMAI FATAN ALHERI GA MUSUMAI DUNIYA BAKI DAYA AMIN, , , , ,
Yar uwa ban son ki da shiga hakkin wani ko wata don Allah kiyi kokari ki biya kafin ki karanta kada ki raina hakkin wani a kanki gara ace kece mai bi da abiki.
Allah ubangiji ya bamu ikon aikata alheri da fin karfin zukatan mu Allah ka sadamu da rahamomin sa amin.
Mami ta shigo dakin wurin hjy a lokacin ina zaune ina gyarawa hjy kayan ta da aka wanke don da ta cire kaya zan dauka in hada danawa in wanke tas.
Shine hjy ta tsayar dani in gyara mata jakkar kayanta muna dan hira ina dariya don gareta kadai nake jin dadi a gidan bayan ita sai dan dama anty Aisha duk da yanzu itama akwai sauyi sosai a fuskanta gareni.
Mami na shigowa dakin saidana kadu dan fargaban daya ziyarci zuciyana lokaci guda don yanzu ina tsoron ta sameni a dakin tare da hjy saboda kada ta yi min cin mutunci.
Don haka nake iya kokarina wajen kaskantar da kaina a garesu kamar yadda suke nufi da zancen su gareni.
Ba wai suna takuramin ga hakan bane saidai ko sakin fuska ance rahamane to babu wanan yanzu tsakani da kowa a gidan sai hjy sai ko yan samarin mami jalal da jamal da basu taba nuna min wani canji ba a fuskokin su.
Kamar yadda muka saba hakan ne har yanzu a wurin su do shi jalal sarkin wasa har yakan min ba, a da fadin amaryan mu.
A cikin wasa hakan yasa yanzuma dana fito daga dakin hjy na sameshi zaune tare da yan matan gidan yana cin abinci suna hira nazo zan wuce zuwa kitchen wurin su mama kande.
Muryan shi naji yana fadin a, a ke kuma armaryan mu yau ko dan gaisuwan ban samu ko dai har kin fara amarcin ne mu fara kawo gaisuwa don yanzu ke dan kin zama key a gurin mu sai an murdaki za a bude,
Kai kai haba jalal wanan irin maganan kesa kuna kara hurawa yarinyar nan kai amaryan wa kuma wanan yar kauyen yar aikin kakewa irin wanan maganan.
Sai ta dauka kamar daidai take da kowa a gidan nan yanzu don dan kauye bai iya samun wuri ba.
Wuce daidai yanzu tunda har ta iya halbo zuciyar ya J aiko tafi kowa ke nan dai a yanzu tunda ta doke duk yan matan dake garin nan kai bama garin nan kadai ba duk kasan nan zance.
Ya jamal naci karo dashi da sauri na dan duka ina gaidashi da kwana yadda na saba na shige kitchen haka yasa ban ji sauran maganganun su ba a wurin.
Ashe a bayana har zancen yaso koma masu fada don Rufaida ta dauki zancen da zafi har gaban mami saida maganan ya kaisu.
Mami kan jalal taiwa fada sosai a wurin jamal yace haba mami kina wanan maganan haka gaban kowa bayan yarinyar nan kin sanda cewa itace dai ya jafar ya tsayar zai aure kice kika sanda wanan zancen a yanzu.
Amma shi ya J din ai ya dade da nuna yana kaunar zeey din ki tun muna abuja da kika fara ganin su wurin dinner rantsar daku .
Dalilin kine fa har ya J ya fara kula yarinyar nan yanzu kuma kina fadan wanan irin maganan a kanshi idan bakya son wanan abin ki mayar da yarinyar hannun iyayyenta kowa ya huta idan yana so sai yaje can gurin iyayyenta ya nemeta.
Kai jamal ka rufa min baki da wanan bakar maganan da kake fadi duk yan matan dake garin nan ace baiga wace tayi mashi sai wanan zeey din da bata da asali yar kauye.
Meye to aciki mami ya tambaya da mamaki yana kallon ta tare da fadin itace fa zabinsa mami don me kike kokarin kawo matsala a cikin zancen nan yanzu ?
Jamal ta fada a cikin tsawa tare da fadin ka fita a idona tun kan ranka yakai ga baci dama halin ku daya da Jafar ai don baku san ciwon kanku ba.
Mami don kawai na fadi gaskiya ki barshi mana yayi abinda yake so zaifi ace kin takura kanki akan wanan magana.
Yana fadin hakan ban tsaya sauraren me zata fadaba ya juya wurin jalal yana fadin kai ya mutafi ko ?
Jalal din dakewa mamin su kallon mamakine ya mike yana fadin mami zamu tafi wurin ticket din don a samu da wuri sai dai bamu san na mutum nawa za,a saya ba idan munje.
Ajiyan zuciya mami ta sauke don yanda ranta ya baci da zancen yaran da safen nan tana fadin naku sainawa da hajiya da Aisha Nuriya da yaran tunda shi mamud din ya tafi tun jiya.
Mami zeey din bada ita za, a tafi bane wanan karon ko a nan za a barta ne wanan karon kinsan fa basu haduwa dasu Rufaida a wuri daya ko banza.
Ya za a barta a nan jamal ya fada dole ai da ita za a tafi ko dan taimakawa hjy wa zai iya da lalurar ta idan ba ita ba.
Jin wanan zancen yasa mami ta danyi tunane kafin tace da ita zamu tafi amma mota zatabi wanan karin ita dasu kande da lami da drivobi.
Haba mami ai hakan ba girman ki bane yarinyar nan meye laifin ta dankine fa duk yaja mata koma meye a wurin ku zeey din nan tana da halin kirki gun kowa.
Kallon data watsa masune yasa su fita daga dakin da sauri har suka kai wurin sayar da ticket din suka sayo jamal yace su hada da nawa su saya koma me mami zatace dai sun saya ai.
Hjy kawai zamu fadawa da mun koma gidan zai fi suna wanan maganan ne wayan ya jamal yayi kara ya dauka da mamaki yake kallon wayan daya nuna lamban kasar South Africa.
Waye kuma ya kirani daga south africa ya fada yana nunawa dan uwan nasa dayake tuki a lokacin.
May be wani friend din kane ko ya fada shima yana kallon lamban kafin ya mayar da hankalin shi ga tukin da yakeyi din.
Jamal kuma ya dauki wayan da hello muryan dan uwan shi jafar yaji yana fadin kai jamal ya kuna lafiya ya mami.
Ya Jackson kaine kayi nisa fa ka daga hankalin mami sosai don har yanzu bata koma daidai ba rashin jin inda ka shiga.
No ball kawai nazo kallo don in samu natsuwa a tare dani ya kana gidane ko waje ya tambayi dan uwan nasa.
Wallahi ya gamu nan munzo yankar ticket gobe zamu koma Abuja mami zasu fara aiki monday din nan mai zuwa.
Wanan yarinyar fa ya tambaya sai jamal din yace yanzun haka zancen ta muke a mota don mami tace wai kada mu yanki ticket da ita a mota zasu tafi ita da sauran yan aiki kamar ta.
Yanzun fa ya tambaya No mun yanko da ita zamu hada da hjy saitawa mami magana fine idan ka koma gida kayi flashing layin nan zan yi magana da ita ok ya nagode take care.
Sun dan biya wani guri kafin su dawo sai bayan sallah azahar suka dawo gidan a dakin hjy suka sameta ita kadai a dakin sun gaisa take fadin yau bata gansu ba tun safe.
Jalal yace dazun na shigo da niyar idan nagama karyawa in shigo mu gaisa sai wa yanan yan rainin hankalin suka so raina min wayau suka ja har mami tayi min fada kan yarinyar nan zainab.
Nan dai yake fada mata komai har zancen sayo ticket din da sukayi dani take fadin sun mata daidai don daba haka ba ko ita ba zata tafi ba idan ba wanan yarinyar cikin su don ko taje wa zai kula da ita a can kamarta.
Karbi waya wani ke son magana dake ya fada a dake sai ta watso mai wani irin kallo tana fadin wani wa ka samomin da yake son magana dani.
Wayan ya kara mata a kunne jafar din yana jin rikicin da sukeyi a dakin yana murmushi kafin yace ke tsohuwa kanki nake so nawa zaki sayar min a turo maki kudi gobe nazo na sare.
Dan nema mai muryan turawa ka dauka ba zan sheda muryan ka bane halan ?
Jafari ina ka shige kabar mutane a cikin damuaa haka kan dan magana kankani ka yankewa kanka wanan hukucin.
Ashe kai baka cika jarumi ba kaja fadan da baka iyawa da uwarka na dauka kai cikkaken jarumi ne ashe ba haka ba.
Matsoraci kawai yace lailai tsohuwar nan kin gama sani yau zan ko gwada maku ni jadumine da bai magana biyu.
Ni baka da bakin fadar komai yanzu a gabana tunda kaja fada kabar yar mutane nan da yaki ita kadai.
Hjy wa ya isa ya yakar min mata ban gama dashi ba ai ita mami ta sani tasan bana magana biyu yasa na bata wuri ta sauko daga fushin data dauka.
Yanzun dai ba wanan ba wallahi tafiya ne ya kamani gani nan a kasan africa ta kudu nazo wani abu zan dawo da yardan Allah nan zuwa jibi idan Allah ya kaimu.
Nikan daka ban mamaki sai ince wanan jarumin nawa bai cika jarumin maza ba ashe a duniya.
Yanzu dai hjy ina yarinyar take don nasan nabar sarkin yaki a gida yasa ban daga hankaliba ga zancen.
Yarinya kan na nan tana fuskantar matsi da tsangwama don har tayi niyar guduwa wallahi na dakatar da ita daga hakan.
Kallon juna jamal da dan uwanshi sukayi shikuma yana fadin hjy don Allah kada ki bari ta gudu daga gidan nan idan na dawo zan sake zama na karshe da mami akan zancen.
Bazata ko ina ba a yanzu kan sai dai ban sanarwa gaba ba idan ka kasa shawo kan uwartaka kan zancen.
Ba jamal waya yace jamal din ya karba yake fadin idan mami ta tambaya ka fada mata nine nace a saya da ita.
An gama yaya ya fada yana dariya suka danyi maganan su kafin yace jamal din ya ban wayan.
Ina kitchen abinci lami ke kwasa ina mika mata ledan da take saka tuwon data tuke a cikin sa naji muryan ya jalal na fadin ke zeey karbi waya ana magana dake a bayana..
Sai da gabana ya fadi kanfin in juyo ina fuskanta shi bai tsaya jiran komai ba kawai ya ban wayan na karba.
Tare da karawa a kunnena gami da sallama duk da bansan mai magana ba a lokacin amma sai da nayi sallaman dan koyi da sunan ma,aiki S A W .
Ajiyan zuciya naji an sauke wanda hakan ya tabbatar min dashi ne a layin duk da ban tabbatar da hakan ba lokacin.
Ido lumshi yana maijin wani iri a zuciyar shi ya amsa sallaman tare da fadin ya kike kina lafiya ko kina nan kina aikin kuka da tunane ?
Ko baki maganane ya fada kamar bashine jafar din mami mai yawan daure fuska ga kowa na gidan ba in badon ina yawan zama da hjy ba ina ganin yadda yake sakin jiki a gaban tsohuwar zan iya rantsaewa da baya dariya tunda yake don yawan daure fuskanshi koda yan uwan shi maza.
Sai yau gashi shike min magana mai kama da ba,a a kunnena haka ina jin shi.
Sake maimaita abinda ya fada yayi yana fadin ko bakiji mena fada ba kina nan kin saka kanki a damuwa ko ?
Aa,a na samu kaina da fadi a cikin sanyin murya ina mai girgiza kai kamar yana gabana a lokacin.
To ki daina damuwa don banga laifin ki ba ko kadan a ranan don na gama fahintar dama ke matsoraciyace sosai.
Ko kin fasa taimakawa yan uwar ki da innan kine in sani don in kyaleki in neme wata.
Daga inda nake na dan runtse idanuwa don da ace shidin sa,a nace da zan so haka ya kasance ko dan kyaushi da wayewan shi saidai nasan shirme nakeyi don wutsiyan rakumi yayi nisa da kasa.
Shi din ba ajin irin mu bane yayan talakawa kamar yadda mami ta fada muryan shine ya katse min tunane yana fadin.
Da kun koma abuja zakici gaba da karatun ki don nayiwa mamud magana yanzu ma abinda ya kaishi Abuja ke nan zancen karatun ki don zanfi son sai kin kamala secondary kafin in aure ki mu tafi.
Nagode yaya na fada a dan kunyace danaji zancen karatu Allah yasa dai kina da kokaerin karatun kamar yadda nake zafo ya fada.
Gane bazanyi magana kamar yadda yakeso ba yasa shi fadin ni zan kashe tunda har da magana a hanaki yi dani yanzu.
Sai an jima nace a kage don na matsu ya kashe wayan in huta da wanan bugun zuciyar danake ji a lokacin.
Maimakon naji ya kashe din sai ji nayi yana fadin kingaji dajin muryana ne to idan kin gaji ni ban gaji ba zan iya barin wayan a haka har lokacin dana gama sauran bugun zuciyarki da numfashin ki tunda naga a tsorace kike.
Ban kaiga sani anmsar da zan bashi ba sai muryan Nazira ke fadin ji min yar iska ana aiki kinzo nan kin labe kina waya da maza ko ?
Uban wama ya baki wanan wayan dake hannun ki haka ko sato wayan mutane kikayi kina waya dashi yar iska muga wayan har sata kika fara a gidan nan ashe yau Allah ya tona maki asiri magen banza mai kwanciyar kwanto ayi sake tayi wuf da abin mutum.
Duk abinda take fada a cikin kunnen ya Jafar yana ji bata farga ba don bata kai ga karban wayan ba tana shirin tara min mutane a wurin.
Shigeya yar kauye mara gata da asali watau ke kinzo birni kinsha jan miya har kina kokarin sace zuciyar dan masu gida da kissan ki na yan kauye ko ?
Ki rasa wanda zaki likewa kamar chewing gun sai ya J da kowan mu a nan take zaman jiran shi mutumin da ko ganin shi tsadane a wurin mu.
Ke amma dan bakin tsafin ki da maitar ki har kika iya sanin yadda kika ja hankalinki gareshi yasan da zaman ki gidan nan maza ban wayan naga ko wayan waye kika sace.
Idona ya riga daya ciko da ruwan hawaye a cikin karfin hali nake fadin ni ba barauniya bace kuma bana maita waya kuma ba satan shi nayi ba ya jalal ne ya kawo min shi yanzu da kansa.
Lami daga gefena take fadin haba Naziran hjy yanzu fa jalal ya kawo mata wayan nan muna tsaka da aiki ya miko mata shi.
Karyane wallahi satoshi tayi yar iska watau ke zaki goya mata baya ta dinga muna barna a gidan nan wallahi yau sai kowa yaji sata ta fara muna don kowa ya kankanta kayan shi tunda muna tare da barauniya.
Wallahi ni ba sata nayi ba na fada don ni ko tsinken wani ban taba tabawa a gidan nan na samu kaina da fada cikin sheshekar kuka sai ga Rufaida da salma dake falo sun shigo suna tambaya take fada masu.
Wallahi yarinyar nan na kama ta sato waya tana magana dashi a nan Allah ya kawoni da maishi yau yayi hasara iphone ce kamar ta jamal salma ke fada.
Ba sata nayi ba anty salma yanzu ya jalal ya kawo min wayan inyi magana karya take Nazifa da Rufaida suka hada baki wurin fada.
Satan shi kikayi ke har kina da darajan da zasu baki wayan su shegiya yau Allah ya tona maki asiri don dole sai kin bar gidan nan yau.
Hasken da wayan yayi daga hannuna yasa salma fadin dawa kike waya yar mami a hankali na dago kai na kalleta kafin in mayar da kaina a kasa ba tare dana bata amsa ba.
Dawa ko zatai waya banda munafukan iyayyen tan nan dake mata tsafi a gida.
Nazifa kin san koda ya J take waya kike fadan wanan maganan haka don duk abinda kike fada yana jin ki tun dazun don wayan sai yanzu aka kashe ta.
Sai jikin ta yai sanyi ta juya tana fadin ke ki bari don Allah dama wayan a kunne take ashe salma tace wallahi shi yasa nake fada maki ku fita harkan yarinyar nan ku kyaleta ba kuji.
Zeey yar mami kin gama wayan ki miko min muryan ya jalal ne daya dawo yake fadan haka daga kofa sai kuma yai shiru yana binsu da kallo lokaci guda.
Ina sharan hawaye nake miko mai wayan tare da fadin nagode duk suna tsaye suna kallon mu a wajen lami tace haka kawai kinzo kin dafawa yar mutane sata ba gaira ba dalili kina neman tara mata mutane ki kunyata ta.
Na fada maki shi ya kawo mata wayan yanzu muna aiki a wurin nan amma bakiji ba.
Ba dole in zargeta ba ta fada tana watso min wani kallon tsana daga inda take tsaye Rufaida kuma wani irin kallo mai nuna matukar tsana gareni take jifana dashi kafin tace.
Ya J din kike waya dashi a boye ashe shigiya mai bakin sihiri kin rantse sai kin sace mai zuciya a gidan nan ko to tsaya kiji .
Ya J ba sa, an yin ki bane gaja irin ki yar kauye idan ko ba aikin asiriba me ya gani a jikin ki yake wanan haukan haka akanki .
Jeki ki tambaye sa ai dan uwan ki ne don me zaku ga laifin yar mutane a banza ga mailefin daya nace mata hjy tsohuwa ta fada daga bayan su don layin jalal daya kira yake fada masu hankali tashe abinda suke min a kitchen din.
Hjy bashi keda laifi ba wanan dince mai laifin ita da batar aika mai da asiri ba ke rufaida ki shiga hankalin ki dani kada ki kawo min diban albarka a gaba wurin nan.
Ba kunya har kike maganan asiri haka a gabana yaushe kika san wani aikin asiri can idan ma shi kuke tunane ai da asiri tai masa daba hakan ba.
Da sauri ta dago ido tana kallon hjy din tace eh da idan ya zare a gidan nan baijin assh a kanta wanan ake kira da asiri.
Wanan ko kauna zallasa so da kaunane nata yaja hankalin shi har don sa ya rufe ya gama mutuwa a kanta ta yadda bai iya jin kiran kowa a yanzu.
Mami dake kwance salma ta kirata ta fito da dan saurin ta zuwa kitchen din ta samu hjy na yanka sababi a kofan shiga kitchen din.
Tsaye take bata san abinda ke mata dadi a wurin ba sai faman tunane take a ranta ita kan ta daukowa kanta jidali da hannun ta.
Ita kan dame wanan abin yai kama me jafar dinta ya gani gun wanan yar haka ya mace a kanta ya hanata sakat a zuciyar ta yan kwanakin nan kan wanan magana.
Wai me ya kawo wanan zace mami ta fada daga bayan mahaifiyar nata inda take tsaye.
Mami wanan munafukan ne na kama a kitchen yanzu da wayan su jalal a hannun ta shine na zata satowa tayi take waya dashi nake mata magana hjy ta taso.
Dawa kike waya zeey ya akayi wayan su ma yazo hannun ki har kike waya dashi.
Diyan ki zaki tambaya wanan don su suka bata wayam ba sata tayi ba a gurin su hjy ta fada a hasale ta juya wurina tana fadin fito mu tafi daki ba zan barki a nan ba tunda basu da imani.
Daga mami har yan matan dake tsaye su biyu suka dago ido suka kalli junan su .
Ina tsaye rakube a jikin bango ban ko motsaba don tsoro naji mami tace ba dake ake magana bane kinyiwa mutane tsaye haka.
Na dago matacciyar kafata daya gama sanyi da sarewa na fara dan tafiya nazo na ratsa tsakiyan su na fice daga kitchen din ina jin wani iri a zuciyata sosai.
Nazo wucewa gaban mami dake tsaye a kofan naji tana fadin ku fito daga kitchen din nan kuma da tada zaune tsaye kuke wallahi ina ruwan ku tunda ba wayan ku ta dauka ba.
Da kyat naga dakin don nisan da yai min lokacin ina shiga na zauna daga kofa na fara rera kuka a fili hjy na shigowa dakin tana mitan zancen.
Nace hjy don Allah don so da kikewa Annabi ki roki mami ta mayar dani gidan mu hannun iyayyena .
Ba sai ta rokeni ba ma zeey nima wanan abjn ya fara isata hakana don haka ki shirya gobe a mayar dake gida.
Mudai shirya a maidamu gida zaki fada don ba yar nan kadai zata tafi a gobe har dani yar kauyen uwar yan kauye zamu tafi kafanta kafana a gidan nan goben, har gaban iyayyen ta zan kaita in yaso dan naki yaje gurin iyayyen ta ya nemeta idan yafi maki sauki.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣7️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
FATAN ALHERI GARE KU YAN UWA MUSULMAI ALLAH YA BAMU WUNI LAFIYA AMIN, , , , ,
Jin abinda hjy ke fadi yasa dole na daina kuka don ba zanso nayi sanadin mami da mahaifiyar ta arayuwana ba don na samesu cikin so da kauna iri ta da mahaifi a tsakanin su.
Ni na bar shiri sai ga tsohuwar ita tana hada kayan ta wai ita gida zata bata kara kwana gidan mami.
Hakan ya tayar da hankalin kowa a gidan don mami har kasa take tana ba hjy hakkuri hjy ko sai fada take tana fadin.
Sam bazan zauna inga wanan cin fuskan da yaran ki kewa yar mutane ba haka idan ke kin kasa da ita ni zan tafi da ita can kauyen mu in yaso shi Jafari yazo gurina ya nemi auren ta.
Kin dauko amana dadi dadi kina riko tsakani da Allah ashe rikon naki ga yar baikai ciki ba da har dan ki zaiji shawan hada iri da ita ki fito kina fadin baki yarda ba don ita din ba diyar kowa bane a kasan nan.
Gasu nan birjit a gari dan naki yaje ya zabi daidai dashi a kadarta yau Aisha ce dan tallakawa ya fito nema ashe ba zaki iya bada aurenta ba ga wanda take so ?
Don kawai yanzu kudi ya bude maki ido kowa kuna kallon shi a mutumin banza koko samun abokai yan duniya dakikayi ne yanzu ya sauya maki yanayi.
Idan ma hakan ne sai kije ki aura mashi wacce duk kike son aure mai din ita kuma wanan din zan tafi da ita gurina in sakata karatu idan ina raye wata ran sai kince ba ita bace a gidan nan.
Kuma ki sani koda danki zai mutu ne idan yazo ba zan bashi yar nan ba muddin na bar gidan nan da ita.
Inda nake ta kalla tana fadin tashi muje yar nan nasan dai ko ban san kowa a garin nan bazan kwana a waje ba yau zan samu na Allah da zasu duba tsufana su tausaya min.
Tana kokarin sungumar jakkan kayan ta daga saman gado inda yake ajiye mami tayi saurin dafe jakkar tana fadin hjy don Allah ki rufa min asiri a garin nan kada kije ko ina gwiwa biyu nakai kasa tare da daga hannaye biyu sama ina fadin.
Hjy don girman Allah kiwa mami hakkuri karki fushi da mami ba laifin ta bane laifin zuciyane.
Da yau danta bai bijiro da wanan zancen ba da mami batai fushi dani ba har gobe mami uwace a gareni mai mutunci da kima a idona.
Bazan taba mance mutuncinta a gareni ba don Allah kiyi hakkuri ni in tafi ko mami da yaran ta zasu zauna lafiya.
Hjy ba zan biki ba zan koma gidan ubana in zauna duk abinda Allah yayi min mai kyaune a rayuwata Allah ne shedata wani kalami na soyayya bai taba hadani dasu yaya ba a gidan nan wanan yana daga cikin kaddaran rayuwata.
Don Allah hjy kiyi hakkuri ki zauna a cikin gatan ki kada ki fushi da mami sabodani kada laifin hakan nima yazo ya shafeni watarana.
Ina fadin hakan na fashe da wani irin kuka mai tsanani na mike tare da nufar wardrobe inda kayana yake cikin jakka a jere ina kokarin daukan jakkar.
Takwara ina yanzun kika gama bani hakkuri akan uwarki idan nayi hakkuri ke kuma ina zaki a cikin daren nan .
Ko so kike in fasa hakkuri da uwar taku mu tafi tare kafata kafarki mubar gidan nan a yau din nan basai gobe ba.
Hjy ba Anchau zan tafi yau din ba zanyi kokari in kai kaina gidan anty safiya har kashe gari ta sakani mota in koma gida nufina ke nan muddin barina gidan mami zaisa ta samu sallama tsakanin ta daku.
Ba zaki bar gidan nan ba koda bana raye sai idan aure ya rabaku da uwarki kamar yadda aure zai rabata da yarta Indo.
Muryan mami ke fadin ke zeey mayar da kayan nan ki fice daga nan ki ban wuri da hjy kije gun su kande ko dakin Aisha ki jirani.
Mami ta bani umurni da hakan da sauri na juya na bar dakin nan na barsu tare da mahaifiyar ta na nufi gurin su mama kande na zauna.
Sun dade da mami da hjy a dakin har bayan magariba san nan salma tace dani hjy tana kirana a daki.
Na mike na tafi ina addu,a a raina Allah yasa sun yake hukuncin in koma gidane gaban iyayyena zaifi min wanan zaman rashin yancin kai da banda shi a gidan mami yau har ni zainab Nazifa ta dafawa satan waya.
Hajiya ta idar da sallah har isha,i ina shiga da sallama fuskan tar a kaina tana son ta fahinci halinda nake ciki take tambayana da nayi sallah na bata amsa da nayi tun dazun hjy.
Zauna ki zuba muna abinci ta fada kai tsaye dai umurni ta bani babu daman yin mussu gareta ke nan.
Itama ba wani cika mata nayi sosai ba na dai zuba kadan kadan sai dai nawa din yafi zama kadan don nasan ba zan iya cinye wanda ma na zuba din ba.
Sai faman cakulan abincin nakeyi cikin sanyin jiki itama dai hjyn haka dai take kokari tura abincin a bakin ta can naji tace kada ki yarda in hada nawa baki karasa cinye wanan dan abincin da kika zuba ba kamar za,abawa yaron goye.
Dole na fara tura abincin da sauri ds kyat nake hadeshi gaba daya raina babu dadi a lokacin har na samu na gama kamar yadda ta umurceni dayi.
Ba zancen hira garemu sai kowa yayi shiru a dakin dan dama hjy ma takan dan jefo min magana jefi jefi.
Washegari aka tashi da shirin tafiya kamar in dora hannu akai ince wayo ni Allah don banson inyi nisa da gida kuma.
Dan dama nan na rike sunan unguwar da muke dana su anty safiya don bam manta da sunan unguwar ba har yanzu a raina.
Ina ji ina gani har aka fara fadin a fito da kayan da za a wuce dashi a mota don masu mota zasu rigamu tafiya nake gani.
Jakkunan kayan mu gaba daya an labta su a mota hakan yasa naji raina ya kara baki nasan yanzu kan zuwa ba fashi gareni.
Hjy ta aikeni dakin mami don in tuna mata zancen maganin ta da za a saya mata nan kaduna.
Ina gab da shiga dakin nake jin muryan mami na fadin saida nace kada ku sayo ticket da zeey mota zatabi ita dasu kande baku maganata ba sai da kuka sayo.
Ba laifin mu bane mami ya J yasa mu saya mata kinga ko ba zamu ce masa a a ba tunda kudin sane.
Gulman ku zai ciku daku har jafar din in dai akan wanan yarinyar ne ido na zuba dani da jafar din a gidan nan za,aga waye zai sare a karshe.
Jikina ya sake yaraf kamar kayan wanki inaji kamar in juya kada in shiga dakin a lokacin sai dai na ba zuciyata sanyi na fada dakin da sallama.
Duk suka juyo suna amsa min shigowana ya basu daman sulalewa daga dakin suka bar mami tare dani ina fada mata sakon da hjy ta aikoni.
Naji ki fada mata za a saye na daga don barin dakin sai naji ta dakatar dani ta hanyar kiran sunana.
Da sauri na koma na tsuguna a inda nake tare da dukar da kaina kasa ina sauraren abinda zata fada min a lokacin.
Mami ta dan dade tana kallona na dan wani lokaci kafin ta bude baki ta soma magana dani.
Zeey ina son ki saurareni dakyau kiji abinda zan fada maki kaina gyada ina wasa da yan yatsun hannuna dana hade a wuri daya ina saurenta.
Ba zan taba bari ki bar gidan nan ba koda hjy bata nuna hakan ba don in taimakeki ki taimakeni na raboki da iyayyen ki zuwa nan.
Saidai zanso kiyi nisa da duk wani dana bawai jafar ba kwai a a ina nufin gaba dayan su muddin kina son mu zauna lafiya dake a zaman mu.
Zancen karatu kuma da mun koma abuja zan sa a nema maki wani makaranta gwaunati ki karasa karafun naki a nan.
Saboda haka in kinyi abinda na fada maki kiji dadina idan kuma kinki to ina mai fada maki zeey zaki kwammace dama baki sanni ba a duniyan nan.
Na riga nagiwa jafar mata amma saboda ke yana kokarin ya bijire min kan umurni na don kawai ya nuna min shi dan zamani ne.
Mami kiyi hakkuri in Allah ya yarda zan kiye ni ban taba magana dashi ba kuma bazan taba ko a bayan ki mami.
Shike nan zeey zaki iya tafiya mami ta fada ba sakin fuska a tare da ita zuwa gareni a yanzu haka na mike na fita daga dakin.
Karfe biyun rana muka fito mami tana makale da yan matan ta dake mata sallama mu kuma muna guri daya dasu ya jalal da hjy sai Aisha dake daga gefen mu tsaye tana sana,an ta da waya.
Ba wanda ya kula da yai min sallama kamar yadda suke sallaman su hjy da su jalal dan dama salma dace zeey za a tafi ke nan na danyi dariyan yake ina fadin sai mun dawo anty salma tace ko sai munzo ba.
Haka motar mu ya daga kamar su jawoni su fidani daga cikin motar yadda suke watsa min harara daga sama har kasa kuma kowa ya kula da hakan.
Karfe hudu duk muna cikin gidan mami na Abuja da farko mami taso raba muna daki ni da hjy don tace naje daki daya zamu zauna dasu kande a nan.
Sai hjy tace ni kuma na zauna dawa idan kin kaita can kinsan ko a gida da yaran yayan ki nake zama ai.
Don haka barmin ita mu zauna tare kawatace ko banza tare muke kashewa mu bisa a dakin mu daga ni sai ita.
Haka yasa na koma da zama a dakina dana bari da farko kafin mu wuce kaduna don yanzun ma a nan zamu zauna da hjy din.
Mami bata da lokacin zama gida tare da mu karfe taran safe baya mata a gida don hakane nake tashi da sassafe nai mata aiyukan dana saba mata a dakin ta harta shirya ta tafi.
Kamar yadda mami ta canza min hakan nima nake canza don a gurguje zan karasa aikina kafin ta fita na bar mata dakin sai idan ta gama zata rufo dakin ta kawo makulli gurin hjyn ta ta fice.
Satin mu daya da zuwa wani yammaci muna zaune da dare a falon dukan mu ya mamud ya shigo muka shiga gaida shi da dawo yana amsa muna.
Ina zaune kusa da kafan hjy naji yana fadin mami monday fa yarki zata fara shiga school don na samo mata makaranta a nan garin.
Da bakin wa kayin wanan mami ta fada a daidai lokacin da nake murnan hakan ina kuma gode masu a raina sai naji wanan furcin nata a bazata.
Gabana ya yanke ya fadi lokaci guda naji taci gaba da fadin ko akwai wanda ya kawo min ita gidan nan ne a cikin ku da kuke nuna min gaba gadi game da yarinyar nan.
Meye gaba gadi cikin wana zancen iyami ina taimaka maki yayi kan abinda baki samu lokacin yin sa ba kuma nautin kine kiyi hakan.
Ko haka yar taki zata zauna a gida ita bata karatu ta taimaki rayuwan ta nan gaba tunda a zamanin nan kome ka zama idan ba wanan karatun baka cika cikkaken mutum ba a idon jama,a..
Hjy kikan so tarewa yaran nan fada a kan gaskiyata da zai tafi nema mata ai sai ya nemi shawarata yaji abinda na yanke a kanta.
Fada muna yanzu ai gashi zaune me kika yanke a kan yar nan a yanzu tunda an hutar dake baki ga hakan ba.
Iyami bansan yaushe hali ki ya sauya ya zama na mutanen zamanin nan wajen , , ,
Hjy ba nufina ke nan ba bandai jin dadin yadda yaran nan suke min abu gaba gadi haka kamar banda daraja a gunsu kamata yayi yazo ya fada min kafin ya samo mata din.
Sai kawai yazo yanzu yana fada min magana haka kai tsaye wai mondaya zata fara tafiya wani makarantar ma ka samo mata din.
Mami inda yaran nan suke zuwa a nan na sama mata itama sai su dinga zuwa tare duk da ita a secondary section zata zauna.
What har nawa za a dinga kashewa a kanta ke nan ina kosu yaran nan kana min korafin yayi yawa da farko saidana haneka.
Mami indai zatayi kararun ai karuwan kowa ne nan gaba don haka kiyi hakkuri nayi kuskure ya fada yana dukkar da kanshi kasa alaman ban hakkuri a gareta.
Allah ya kyau hjy ta fada tare da dafani tana fadin yar nan nayi maki murna ubangiji yasa a shiga da kafan dama nace.
Yaya na gode Allah ya karawa arziki albarka yace ba komai ki dai dage da karatu sunce idan sun gwada ki kinyi nasara zasu iya barin ki inda kike a can kaduna.
Allah yasa hjy ta fada tana tattara takardun dake gaban ta alaman zata bar falon ke nan nayi saurin mikewa ina karban kayan daga hannun ta.
Sai naji tana fadin wa zai dinga sauke su a school din kai ko driver zai kaiku ya amsa da fadin.
Dama ai nike saukesu kafin in shiga office yanzun ma nidin dai ne zan dinga sauke su idan zan fita .
Ka nema masu driver daga yanzu da zai dinga sauke su kai ka wuce office din ka kaji abindana fada ta juya wurin hjy tana fadin hjy zan shiga in karasa aiki a daki.
Ni dai na aje kayan na fito daga dakin don babu wani abinda zan mata a lokacin don haka na dawo falon na samu hjy da yaya mamud suna hira Aisha ta shige dakinta ko lokacin.
Har kasa nakai na kara mai godiya yacs Jafar ne ya saka in sama maki nan don haka shi zaki godewa idan ya dawo.
Sai ki mai da hankali ki samu abinda kikaje mema banda wasa ko wani hali na banza don Allah.
Nagode yaya na kara fada kaina yana kasa nake fadin hakan don gabana na faduwa tun lkkacin daya ambaci sunan ya Jafar din.
Suna ta hiran su da hjy ni kuma ina faman tunanen gargadin hjy a raina a wani bangare kuma ina Allah Allah in ga na fara zuwa makaranta ranan monday din.
Rana bata karya saidai uwar diya tayi kunya hausa suka fada don yau gani a class tare da diya manyan mutane don an gwadani na ketare da kyat don su ba wani gata da zaka nuna masu su yarda su kaika gaba saidai idan kokarin kane ya kaika.
Na mayar da hankalina sosai ga karatuna banyi kawa ko aboki ba kamar yadda naga wasu sunayi a school din koda yaushe ni kadai zaka sama a class din ina bitar takarduna da akai mana darasi.
Ranan kwatsan mun dawo daga school tun a haraban gidan idona yayi tozali da bodyguard din shi suna tsatsaye waje suna mazurai da idanu don motan mu daya danno kai gidan.
Gabana ya shiga faduwa haka na daure na shiga cikin part din mu da sanda nayi arziki babu kowa a falon sai tv dake aiki a falon shi kadai babu mai kallo.
Da sauri na shige dakin mu inda na samu hjy zaune ta idar da sallah la,asar a gurin tana zaune.
A gurguje na tube uniform din jikina na fada bandaki ban fito ba saidana shirya a cikin wani dogon riga duk kayan da Aisha ta ban ne nake sakawa a jikinao.
Na fito na o da sallah nacewa hjy zan leka kitchen in fito daga can na zauna abina ina taya su mama kande aiki har muka karasa na dawo don yin sallah lokacin har mami ta dawo tana dakin ta .
Tunda na tun karo wuein kamshin turaren shi ya daki hancina na tsaya na dan saurara ko yana dakin in koma kitchen in zauna har ya fita.
Naji banji wani hayaniya a dakin ba na shiga hjy ne zaune ita kade tana ganina take fadin wai ina kika shiga haka daga barin je in dawo naji shiru sai yanzu.
Har yaron nan ya dawo daga balaguron da yayi yana tambayan ki bai dade da fita daga dakin nan ba.
Wa ke nan na tambaya kamar ban fahince ta ba tace wanan bayahuden mana jafari ai ya dawo tun dazun da ranan nan wai wata kasa yaje kallon ball kawai don barnan kudi.
Shiru nayi don ban san me zan fada ba sai kuma hakan yaiwa hjy zafi take fadin anya yar nan kinko damu da yaron nan kamar yadda ya damu dake.
Don shi da zuwan shi ke ya fara tambayana na fada mai kindan fita sai gashi shiru shiru baki leko ba dakin nan sai yanzu daya fita.
Ko uwar taku tayi nasara a kanki ne tun yanzu nace hjy dan Allah ki daina zancen shi dani kada mami taji ta riga da tayi min kashedi a kanshi tun a kaduna hjy.
Ita iyami din hjy ta fada nace hjy kada kiyi mata magana ko dan karatun nan da yanzu nakeyi kada in rasa sa,ata ta wanan dalilin.
Wai maryama kanta daya kuwa gaba daya yarinyar nan ta rikice min lokaci guda na kasa gane inda ta dosa kan zancen nan.
Haka mukai ta shan bambam dashi ban yarda mun hadu ko sau daya ba a gidan tundaya dawo garin.
Ran ba makaranta ina zaune inawa kaina kitso muna hira da hjy ya fado dakin namu daga sallaman shi ya kutso kai ciki.
Ba daman in gudu in shige koda bathroom ns don ya riga daya ganni ko dole na daure na gaida shi tare damai an dawo lafiya.
Shima yadda ya amsa min naji dadin hakan don ba yabo ba fallasa gareni sai na mike zan bar masu dakin don dai kawai in kaucewa warning din mami gareni.
Ki zauna fita zanyi na leko hjy ya fada daga inda yake tsaye yana magana da hjy gashi ya kara haske sosao yayi wani kyau dashi bakin gashin kanshi yayi lub kwace a kanshi sai sheki yakeyi ga wani saje daya bari a fuska tasa wanda bai saba bari shi a fuska ba.
Yana gama magana ya sa kai ya fita ya bar dakin gabana sai faduwa yakeyi min don abinda idona ya gane min din duk da ban kalleshi sosai ba ma ke nan.
Tun daga wanan rana ban yarda mun kara haduwa dashi ba a gidan don ina ganin shima bai faye zama a gidan ba sosai sai jefi jefi.
Ranan zan fito daki ke nan don hjy na falo mami tafita gurin aiki bata dawo ba ina ganin shi na ruga da gudu na koma daki a zatona ko bai ganni ba ne.
Saida ya dan dade a zaune kafin ya mike ya nufi dakin namu hjy dai tana zaune tana kallon shi tare da tausayi mu a ranta.
Ya tsaya daga bakin kofa dakin bai karasa shigowa dakin ba sai hannun daman shi dayayi amfani dashi wurin rike labulen dakin dashi.
Wa kike gudu haka ya fada a cikin muryan nan nasa mai fida sauti mai dadin saurara kunnuwa suka jiyo min hakan.
A razane na juyo ina kallon shi yana tsaye a kofan yadda yake a wurin wani irin tsoro da damuwane suka ziyarci zuciya sosai take jikina ya fara kyarna ta yadda har ya fahinci hakan.
Hannun ya sauke daya tokare kofa dashi yana gyara suit din dayake sagale a hannun nasa karya fadi.
Takowa naga ya fara yi zuwa inda nake haka yasa gana ya tsananta da faduwa sosai a haka ya iso inda nake rakube ga bango ginan dakin.
Wani abu naji yana taso min wanda yasa na duntse idona a hankali kafin ya kara tako ya cin min a gurin.
Jin kamshin turaren jikin shi gab dani yasa na bude idona na dube shi kadan babu sauran tako a tsakanin mu ko daya a yadda muke tsaye a dakin.
Kokarin ja nayi baya sai dai babu inda zan daga don gaba daya ya tare wurin ya tokare hannayen shi a ginan dakin.
Shiru ya ratsa dakin ba wanda yai magana a cikkn mu kamar babu kowa a dakin lokacin.
Inan tsakiyan hannayen shi har lokacin idanuwa na a rutse kamar naga dodo a gabana.
Ga ba hanyar da zanbi in gudu daga wajen don ya hana hakan gareni ya kankame ko wane gefe da zan iya guduwa mashi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣8️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DON TURA KUDI ZAKI TURO GA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK DARI UKU NE KACAL KATIN WAYA KI TURA GA WANAN LAYIN 08036959257
YAR UWA DON ALLAH KI DAURE KINA BIYAN HAKKIN MUTANE DON ABIN BAN YAFE BA KALMACE MAI NAUYI GA MUSULMI NAGODE.
Har lokacin idanuwana suna a rufe ga numfashinsa ina jin saukan su a kunnuwana idon na kara budewa don jin shirun da yai yawa na dauka nike haukana a lokacin shi baya ko wurin.
Yana nan tsaye a yadda yaken haka yasa na soma kokarin sunkuyawa ta kasan hannun shi in samu in wuce don tserar da rayuwata ga mami dashi.
Ji nayi ya kamoni ya kankame ni a jikin shi tare da mamaye ni cikin wasu irin abubuwan da ban taba tsintar kaina a cikin ba ko a mafalki ban san da wanan nau,in abinba.
Haka kuma ban taba sanin ana wanan abin ba na dauka sai kafiran turawa da nake ganin haka a film danazo gidan mami.
Suma din kuma idan sunayi kawar da ido nakeyi koma na tashi na bar wurin ga baki daya.
Can kasan makogorna na iya furta innalillahi don Allah ya jafar ka bari kada kayi min sanadin da mami zata koreni gidan nan.
Bai kula da abinda nake fadi din ba yaci gaba da abinda yake min kamar ma zancena ya kara mashi kaimi ne .
Babu inda baya karkarawa a jikinsa don abinda yake min din nikan na sadakar sai hawayen da ke zubomin kamar an sake famfo na barwa Allah lamarin sa duk abinda Allah ya kaddara min mai kyaune.
Muryan shi naji a kunne kamar mai rada yana fadin mami kike tsoro yasa har kika fara guduna kina boyewa ?
Idan mami din ta sakaki ki min hakan ko ta hana ki aure ni kamar yadda na bukata ai ba zata hanani wanan bako ?
Abinda mami taji ke nan a karshe wurin da take tsaye ta mutu a tsaye don mamakin ganin halin data same mu a ciki a dakin.
Da sauri mami ta juya kafin ko wanin mu ya ankara mu farga tana gidan a lokacin ta nufi dakin ta da sauri duk maganan da hajiya ke mata a falon bata jita ba.
Karan sakin kofan da mami tayi ne ya farga damu don dai kawai tsoron dake yawa a zuciyana ne daya rufemin ido ban farga da ita ba tun shigowan ta dakin.
Yanzu kan sheshekan kuka na fara mai don na kula in dai ba mami ba hjy tsohuwa ce ta rutsamu a halin da muke ciki.
Ya jafar don girman Allah don ya rasulillahi ka, , , , , shhh yace tare da fufe min baki da hannun sa na kasa karasa abinda nake nufin fadi karshe.
I boldly care da duk wanda zai shigo ya same mu a haka dake dakin nan idan su basu san soyayya yada yake ba wanan ni bai taba damuna tunda sun hana min abinda nake so.
Naji yaya ba zaka taba damuwa ba don kai nan gidan kune bayan hakan kuma kai na miji ne dama mace itace da kunya ai.
Idan mami ne ta bar wurin nan na tabar da yau ban kwana a gidan nan don ta riga da tayi warning dina tun kan muzo garin nan a kanka.
Babu inda zaki tafi matukar ina raye a gidan nan doIn ko kin tafi dawowa zakiyi ita mami tasan halina idan ke baki sani ba.
Ban taba cewa ina son abu har in sashi a raina ban in rasa samu wanan abin don haka ba zan soma shi a kanki ba.
Naji amma don Allah ka barni in bar gidan nan yanzu tun mami bataji wanan maganan ba yau ta kasheni gidan nan.
Don girman Allah ka daga, daga nan in fice na fada cikin wani irin kuka daya zo min mai karfi.
Maimakon ya daga daga wurin saima naji yana kokarin kara matseni a jikin shi.
Kayi ma Allah kaimun alfama na hadaka da girman iyayyen ka ka daina rike ni haka kana hadani da fushin ubangijin mu.
Ka rabu dani ya jafar ka kyale rayuwana hakana ya huta da wanan ukuban daka sakani a cikin sa yanzu.
Ka taimakeni ka taimaki rayuwana da kake shirin rusa min yau karatuna shike nan na rasa shi tunda mami kauye zata mayat dani ina gap da gamawa.
Nima ki taimake ni zainab don ke kadai zan aura a kasan nan in zauna lafiya dake bani na sawa kaina son ki ba Allah ne ya zaba min ke don hakkurin ki da tarbiyan ki.
Abu daya nake so dake shine ki daina cewa zaki bar gidan nan ko karatun ki zai tsaya ba wanda zai faru daga insha Allahu.
A razane na dago kai na kalle shi kafin in mayar da kan kasa don kwarji da nauyin da yai min ga kallon shi.
Ya daga min gira yana fadin nasan mami zata yarda da bukata na idan na kafe a kanki a cikin sauki.
Don farin cikin ta shine nawa itama nawa shine nata bata taba hanani abu nayi shi ba a duniyan sai wanan karon kinga ko zatayi min adalci a nan.
So da sannu mami zata fahinta ta yarde mana muyi aure in dauki mu tafi can inda zaki karatu sai kince kin gaji da karatu a rayuwan ki.
Wani irin takaicin sa da tsanar sa yake tokare min zuciya ga tausayin kaina danakeji nida kaina kamar in dora hannu aka in ta kurma mai ihun a dakin sai anzo an ceceni.
Sai da ya fahinci ya gama hada min zafi akaina don kansa ya janye min daga banga bangan dayi da farko ya tare ko ina da zan iya sulalewa in gudu daga tsayin dayayi a gaba.
Kamar jira nake ya nuna min kofa in gudu aiko yana nunawa na sheka da gudu ina kuka mukai karo da hjy a kofa da tazo shiga kamar.
Duk da nayi murnan ganin ta amma naji haushin da sai yanzu ta zo dakin duk dadewa da mukayi a tsaye tare dashi zuwan ta yai min kama da zuwan yan sandan indiya da sai an gama cin gari suke isowa.
Fadawa nayi a jikin ta ina kuka take ta rude a wurin tana fadin a rikice maikai mata jafari na fadama kabi yarinyar nan a sannu akwai kurciya a tare da ita yanzu sai ka lalabata tukunna.
Ask her idan nai mata wani abin just magana nayi mata kan guduna da takeyi kawai.
Ba dole ta gujeka ba kaida uwar ka kun saka yar mutane a gaba haka wanan hattaran yai wa yar nan yawa a gidan nan.
Ai saika tashi kaje don uwar taku ta dawo har ta leko nan baka sani ba kana nan kana gyara kanka a wurin mace.
Hjy kefa kikace sai na jata a hankali zata fahinceni na fara hakan kuma laifine yanzu hjy ?
Laifine kan indai zaka dinga sakata kuka haka ko wani lokaci murmushi ya sake mai laushi yana kada kai tare da fadin well i know what to do next barin leka mami ya fada yana mikewa har lokacin ina a jikin hjy ina dan sheshekan kuka.
Yana fita daga dakin na dago kai ina fadin shike nan hjy yau zamana ya kare karatun da nakewa murna ya tafi daga gareno don mami korata zatayi yau gidan nan.
Saboda kawai kun kebe dashi a nan zata kore ki hauka tayi kome daga haka sai kora kawai.
Hjy mami tayi warning dina tun a kaduna kada in yarda in tsaya da danta don ta riga da tayi mai mata ko.
Ita iyamin ta fada maki hakan na gyada mata kai kawai ba baki idan ma har ta fadin hakan ai yanzu bake kika bishi ba shi ya biyo ki ko sai tayiwa danta fada shida ke binki.
Dakin mami ya nufa direct ba tare da jin komai a zuciyar shi ba duk da hjy ta fada mai mami ta leko dakin mu yana ciki yasan kuma ta ga halin da muke ciki a lokacin.
Da sallama ya leka dakin ba,a ansa ba haka yasa kai ya shiga dakin mami ya hango a zaune gefeb gado tayi tagumi da hannayen ta dukka biyu kamar wacce ke cikin tsananin damuwa.
Ta rasa abinda ke mata dadi a duniya yaron nan wani abin kunya haka yake son jawo mata ne duk ita a zaton ta ya bar wanan zance ashe shi yanzu yakema ga zancen wata namiji dai sai a barshi ga abinda yake so ya kwallafa rai kuma.
Kallon mamaki yake mata har ya karasa bakin gadon da take zaune a kai yace mami lafiya kuwa na ganki a haka ?
Wani abu ya faru ne ko wani abin kike tunane haka ke kadai a daki kinyi tagumi.
Ido mami ta dago ta gallamai harara da idanuwan ta da suka kade sukai ja tankar zasu fado.
Ji take kamar ta wanka mai mari da tana iyawa a yanzu so yake ya tozarta ta ya kunyata ta a idon kawayen ta tozarta.
Maganan hjy da take tunawa guda biyu shike taka mata burki ga koran yarinyar nan ta koma kauye.
Saidai idan ta tuna da kalamin hjy da take fadin idan ta kori yarnan a gidan ta sai danta yaje gun iyayyen ta a bashi ita ya aure muddin yaje da waliyan shi makusanta ita kuma a barta tana hargowa a gida.
Ga kuma barazan hjy data ita kuma idan ta matsa sai ta dauke yar ta koma da ita wurinta ta inganta rayuwan ta fiye da tsamanin ta to me hjyn ke nufi da hakan.
Hannun ta ya riko don yaga ko a yanzu da take kallon shi hankalinta na ga tunanen da takeyi a lokacin.
Riko hannunta yayi yana fadin haba mami meye zai sakaki irin wanan damuwan haka kinsan fa yanzu aiki na maki ya, , , ,
Baiyi aune ba yaji saukan mari a lafiyayyen fuskan shi lokaci guda ya dago kai da mamaki yana kallonta da kyar ya iya furta mami you slap me ?
Ko zaka ramane tunda yanzu ka girma har bakajin umurnina kake ganin kaika isa har yanzu kake mamakin na mareka ko ?
Allah yasa yanzu da idona na gama ganin ku da kazaman yarinyar nan a dakin hjy ba wani ya tsegunta min hakan ba.
Yanzun kai bakaji kunya ba ace kamarka jafar kamar kafa kamar kake rugumar wanan kazaman yarinyar zainab yarinyar da wani lokaci ma tsami takeyi da wari.
Da sauri ya dago kai a karo na farko tun bayan marin data kwasheshi dashi ya dukar da kanshi bai daga ba yana dafe da wurin cikin mamaki.
Wari mami wari fa kikace yarinyar nan tanayi ban taba jin haka ba a tare da ita asalima ni yau wani kamshin ma naji a wurin ta.
Mami nifa kome takeyi ina sonta hakana da don itace zabina a duk yadda take ya fada yana kokarin mikewa tsaye.
Jikin mami ya sake yaraf kaman ruwan sanyi a gabanta yau jafar ke wanan magana kan mace macen ma wai yar aikin gidan ta wanan wani irin lalacewa ne ya kama dan nata haka?
Ganin ya soma batrin dakin don tafiya don marin ma datayi mai shiko a jikinshi ya yadda nunata take ta soma magana tana fadin.
Yau da uban ka yana raye jafar zakai min haka ince ga wace nake son ka aura kace kai ba hakan ba yaushe ka fara wanan halin banzan na kafi ban sani ba ?
Mami daddy , aiko daddy yana raye ba zai hanani zaban abinda hankalina ya kwanta gareshi don dama daddy yana raye aida yanzun akaiga matsaya ga zancen nan don shi daddy ban taba ganin ya kyamaci wani a rayuwan shi ba
And mami kin san koda daddy yake da rai mun fi shakuwa dake fiye da daddyn mu
Mami kin kasa fahintana ne kin kasa tausa zuciyar ki akan yarinyar nan why mami zaki hanani abinda nake so.
Ba zaka aure ta ba nace bazaka aureta ba ko dole zakai matane mu gani idan zaka iya No mami ba dole amma nasan itama tana sona don naga alaman hakan tare da ita.
Tsoron warning dinki gareta ne take amma ba matsala zan gwada sa, a ta tunda kinban dama a yanzu.
JAFAR mami ta fada da karfi ya fice dakin ba tare daya juyo ya kalleta ba tunda mami take da danta haka bai taba faruwa a tsakanin su ba sai akan wanan dalili.
Me yaron nan yake nufi dani da wanan kalamin nasa tursasa yarinyar nan zaiyi taso shi tunda a yadda ta samemu a dakin da alaman tsoro shi a fuskana don kuka ta samu ina masa.
Ma,ana dai shi jafar din ne ke bibiyan ta a dole meya gani ajikina har ya mace ga son yar nan haka.
Yarinyar da saida tazo nan ma tadan yi wanan clean din da yake rudin shi ta runtse idanunta tana mai fadin kada Allah yasa so ya rudi yaron na ya aikata wani abinda zaija mata kunya ga idon mutane.
Ya zama dole ta jashi a jiki tasan hanyar data bi ta lalashi da lalama ya janye kudirin shi akan yarinyar na don koranta gidanta baida wani fa,ida a yanzu idan tayi amfani da maganan hjy.
Zeey bata da laifi ta sani amma wanan dalilin ya jawo mata tsanar yarinyar ba gara ba dalili taji yarinyar ta fita mata rai ga baki daya ta wanan dalilin.
A dakin mu hjy ta samu ta lalabe ina kwance lamo sai faman ajiyan zuciya nakeyi ga tunanen abinda ya faru tsakanin mu yaki fita a rai.
Duk motsi nayi sai inga kamar a lokacin abin ke faruwa dani uwa uba ga kamshin turaren jikin shi daya dameni a hancina yana kokarin saukar min da kasala a jikina.
Mikewa nayi zubur hjy dake zaune ta kalloni tare da fadin ina zaki ban daki zan shiga inyi fitsari na fada.
Na shiga ta bini da kallon tausayi tana gyada kai Allah kadai yasan yadda take ji a zuciyar ta kan yaranan a yanzu.
Na dan jima a ciki kafin in fito rike da digana dana cire ina daure da tawul a jikina wanda nake kewayawa dashi don a dakin muka same shi wani babba haka dashi fari mai kyau da yan flawer a jikin shi kanana a gefe.
Dogon rigar yar katin da anty safiya ta saya min da zanzo gidan mami na jawo na zauna saman kujera ina dan shafawa jikina mai don kada in bushe.
Au yar nan wanka kikayi gabanin magariban nan kudai yaran yanzu baku da tadan lokacin yin abu.
Hjy na magana tana kallon gashina da har lokacin yana tuke babu kitso a kaina sai fibon dana daure gashin dashi ta bayan kaina.
Kafin ta mayar da kallonta da kyau a inda nake tanaci gaba da fadin yadda kike nan da tsari irin hakane mutanen boye ke so su shige jikin mutum a sauke.
Mutanen boye kuma hjy na fada ina juyowa gareta tace kwarai kuwa yar nan ai su abinda sukw so ke nan urin wanan sakacin da kukeyi a yanzu take sun shigeka suyi maka illa.
Kinga mu a zamanin mu duk irin wa yan nan abubuwan musanshi iyayyen mu na fada muna mukiyaye don tsaron lafiyan mu.
Hjy daga yau na daina ba zan sake kewaya a wanan lokacin ba in Allah ya yarda tace dadai yafi maki kam.
Waini meya hadaki da mutumin naki ne dazun kike ta wanan kuka ina saka riga a jikina da sauri don maganan da tayi naji wanan maganan.
Juyowa nayi da a daidai ina karasa saka rigan na dauki hulan dana dora saman gado na dawo kusa da ita na zauna tare da dan marairaicewa nace hjy ki taimake ni ya jafar yafita daga tsabgata a gidan nan don Allah idan ba haka ba mami zata koreni ta fada.
Kin taba ganin inda aka cirewa mutum rai ga abinda yake so farat daya wanab sai uwarku da take ganin tana iya hakan.
Wai yau dai ki fada min yar nan shin kina son jafarin nan ko bakya son shi inji da sauri na dago kai na kalli tsohuwar sai kuma na dukar da kaina kasa don bansan amsan da zan bata ba.
Ince ina son sa in kaishi ina ko ince banson jinin ta kiri kiri haka a gabanta anya zataci gaba da sona nima duk da nasan tun kan haduwan mu da jafar din tsohuwar take nuna min kauna sahihi.
Sai kuma yanzu da take nuna min kauna tankar itace ta haifi iyayyena ta san zafina fiye da kowa ta yaya zan iya bude baki ince banson jikanta mafi soyuwa a gareta ido da ido haka.
Nasan wani abu yanzu ma saboda shine ta tsaya min take tsare min komai a gidan yadda ya dace.
Murmushi naji tayi tana fadin to ai abu yayi kyau takwara shiya nake kara sonki saboda halin nan naki na alkunya ga kuma girmama mutum saidai iyami taki gane hakan .
Ke din wani baiwace a garesu takwara naso iyami ta gane hakan amma idonta ya rufe ta kasa hangon hakan da kanta.
Nidai har ta gama maganan daidai ana kiran magariba ga agogon dake dakin namu ta mike da sauri zuwa bandaki do bata wasa da ibanda ta kiran sallah kawai ta kan jira ta mike ko wani lokaci.
Bayan kowa ya kammala komai aka fito cin abincin dare kamar yadda aka saba da kyat hjy ta shawo kaina na yarda na fito daga dakin.
Mun samu mami a falon har ta fito tana zaune tunda muka tun karo wurin ta dago kallo daya tayi min ta kawar da idon ta gareni tana fadin hjy kin fito yanzu nake zancen ko lafiya yau baki fito da wuri ba haka.
Muna daki nida mutumiyar ina bata labari mutanen da can yadda suke rayuwan su ga wuri hjy ki zauna tana fadawa mahaifiyar nata cikin girmamawa gareta.
Kafin ta dago kai inda nake tana fadin cikin bada umurni ke jeki aka hijabi a jikin ki baki ganin gidan nan akwai samari ne kike fitow haka dake.
Ya ilahi nikan ko me zanyi mami a yanzu bata ganin haske na na juya naji hjy na fadin zancen banza ke nan yo ai shigarta yafi naki dana yarki mutuntuwa bakiwa wanan mai zama kamar arniya a gida ba haka kai babu hula ko dan kwali sai wanan da jikkn ta yake a suturce.
Hjy mu muharamin si ne ita fa irin shigar da ta dauko yi ke nan har yaro nan ya jefa kanshi a tarkon ta.
Ita yar nan din tasan ta danawa wani tarko da ace hakan take da baki fada ba da bakinki yanzu don da kin gane kabewa ruwane.
Tsohuwar ta juyo gareni tana fadi jeki ki saka hijabin ki dawo muci abinci nikan ina shiga dakin ban kara fitowa ba na neme wuri na kwanta ina sharan kwalla.
Abuja ba kaduna bane don ko sunan uguwanin su ban gama sani ba sabanin kaduna da tun ban shigo shi ba nake jin sunaye unguwanin cikin shi a bakunan mutanen kauyen mu.
Ina barin wurin mami ta mike ta nufi dakin dan lelen ta a karo na farko tun dawowa shi Nigeria don ba dabi,an ta bane zagaya dakin samari nata.
Kofan dakin yana rufe ta murda taji shi a ruwa saidai karan tv dake aiki ana wasan kwallo tana dan iya jiyo hayaniya daga inda take tsaye.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣9️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA YAR UWA DON TURA KUDINSA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN DARI UKU KACAL A WANAN LAYIN 08036959257 NAGODE GA WANDA YASAN ZAFIN ABINDA NA FADA.
Da mamaki ta juya don a zaton ta yana cikin dakin sai dai bataji alaman mutum a part din ba haka ta dawo dakin ta ta nufa direct .
Har ta zauna ta bude system dinta da niyar tayi aiki a cikin sa sai zuciyar ta ba zai barta tayi abinda take so ba a lokacin.
Har dare duk wanda ya shigo gaida ita tana tambaya idan ya dawo sai suce basuga shigowan shi ba kuma security din shi basa nan saidai ga wayan shi na shiga kuma karshe taji wayan a kashe.
Washegari wanan dalilin ya hana mami fita aiki da wuri ni dai nagama mata komai tana bandaki kafin ta fito na karasa na fita daga dakin shiryawa nayi a gurguje kar driver dake kaimu school ya jirani.
Mami ta gane me nake nufi don ta fahinci tun jiyan ina gudinta don ban fito ba ita kuma bata tambaya ba duk ta san banda laifin kan hakan amma zuciyar ta ya kasa daina jin haushina.
Zazzabi mai karfe gaske yake ji a jikin shi tunda ya falka da safe da kyat ya iya shiga bandaki yai wanka ya fito yayi sallah asuba ya koma ya kwanta.
Mami ta fito daga dakinta ta samu hjy zaune a falo ita kadai tana kallo wa,azi da takance kafin mu kai mata kafin mu fita da safe.
Mami ke fadin hjy tun jiya banga shigowan jafar ba ko kinga fitan shi da safen nan da mamaki hjy ke fadin yanzun nake maganan shi a raina ni kadai.
Ko tafiyan yayi babu salma kuma wanan karo ma mami ta dan yi tunanw tare da fadin anya don bai dade da dawowa ba da wuya ya sake fita.