PROLOGUE
A Babban Gida Part 2 Complete Hausa Novel · about 9 min read
*PAGE* 0️⃣3️⃣
Shafin ku ne ƙawaye na
ZAINAB SHEHU UMAR ( ZEELY)
SA'ADATU LAMARA ZULKHAIRAT (Matar mijinta)
RABI'ATU ABDULLAHI HASSAN (matar Ɗan jagade)
FATIMA AHMAD ABDULLAHI (Fatima anatomy)
Ina ƙaunar ku saboda Allah
Barkan ku da Sallah
SHARE AND COMMENT PLEASE!
_______________★★★________________
Sassafiya Mamah ta tashi da aikace-aikacen gida. Sai around 8:00am Zahrah ta fito tana miƙa
“oooooooooooh”
Mamah ce ta kalle ta sannan ta kawar da kai. Wurin Mamah ta taho
“ina kwana Mamah"
“lafiya ƙalau Zahrah kije kiyi wanka sai ki siyo manah ƙosai da koko gidan Mati."
Da “toh Zahrah ta amsa tana wucewa banɗaki. Bucket ta cika da ruwa sannan ta shiga toilet ɗin. Wanka tayi ta fito. Rigar ta ƴan kanti wacce ta ɗan ji jiki ta saka kafin ta shafa mai. Tana gamawa ta janyo hijabin ta da saman shi ya ɗan koɗe saboda dukan rana.
Fitowa tayi ta cewa Mamah
“kawo kuɗin”
miƙa mata 500Naira tayi sannan tace
“ki siyo bread 🍞 Babba guda ɗaya da canjin.
“toh"
Daga haka ta fita zuwa gidan Mati da ke kan kwanar layin su.
Tana fita ƙofar gidan su nan a cike kamar wadda za'a yi taro sun cika rumfar wasu kuma har da kan dandamalin da ke jikin gidan sai ihu suke suna buga uban shewa da gani kaga tataccun ƴan iska. Kallo ɗaya tayi musu ta kau da kanta gefe haɗi da tsaki.
Aljan ne ya hango ta sai wani fara washe baki
“ƴar oga! Ina zaki haka da sassafe"
Bata yi tunani da ita yake ba shi yasa ko kallo bai samu daga gare ta ba. Su kuwa sauran ƴan dabar suka saka ihu nan suka fara tsokalar Aljan.
Da ɗan gudu ta isa gidan sannan ta bada kuɗin ta haɗi da miƙa jug ɗin roba da ta zo da shi.
Ana sallamar ta ta amsa bread wajen Bala Mai shayi daga nan ta wuce gida.
Kamar dai ɗazu wurin a cike yake ammah haka ta wuce abun ta saboda gargaɗin Mamah kan kada ta kuskura ta ce zata kula wani a dabar.
A ɗakin mamah suka karya, Bayan sun karya Mamah ta ɗauƙo wasu kuɗaɗe daga aljihun doguwar rigar da ke jikin ta. Kuɗin zasu kai 15k. Da mamaki Zahrah ke kallon kuɗin, duk da bata da wayo sosai ammah ta san wannan kuɗin da yawa suke
“mamah kuɗin menene wannan?”
“yayan ki Ishaq na da kirki sosai, ya bamu ne mu ƙara a jarin masa”
Ko rufe baki Mamah bata yi ba taga ana shigowa da kayan abinci, shinkafa, taliya, macaroni, indomie da mai har da manja.
Mamaki ne a fuskar su har lokacin da aka ce
“a ina za'a ajiye su?”
Nuna musu ƙofar ɗakin ta tayi don kuwa nan ne wajen da zasu rabauta daga hannun Kawu.
Suna gama shiga da su suka fita. Mamah bata bar mamaki ba ammah tayi shiru abun ta.
Sai wajen 11:00am Kawu ya banko ƙofar ɗakin shi fuskar nan duk yawun bacci alamun ko sallar asuba bai yi ba. Wata shegiyar miƙa da yayi abun takaici Mamah dai jinjina kai tayi tana roƙon Allah ya shirya Yunusa..
Wani kallon banza ya watsowa Mamah sannan yace
“ke ɗan ubanki shine jiya kina ji ina buga gida kika ƙi buɗe min? Gidan na ubanki ne? Nace na ubanki ne gidan?”
Mamah dai bata kula shi ba ta ci gaba da yi wa Zahrah bayanin yadda zasu sauya kasuwancin nasu.
Sheƙa Kawu yayi hakan yasa ya kawo wa Mamah wani uban duka.
Caraf Zahrah ta tare ai kuwa sai a tsakiyar kanta wanda yayi sanadiyar faɗuwar ta ƙasa sumammiya. A firgice mamah ta yo kanta tana jijjiga ta ammah shiru.
Hakan bai ishi Kawu ba sai da ya ƙara kawowa Mamah wani dukan. Bata damu ba saboda hankalin ta da ya matuƙar tashi kada taje ta rasa ɗiyar ta.
Ba tare da ya damu ba ya fice zuwa dabar tasu. Wani ihu suka sa suka fara yi mishi kirari
“Takawar ka lafiya Yunusa BabanMutuwa, kayi yadda kaso da uban kowa, ita kanta mutuwar tsoron ka take, kaga sarki mai cikakken iko”
Dariya yayi jin yadda ake fasa mishi kayi nan da nan majalisa ta fara, ana shan sigari ana gulma tare da kututgumo ashar. Authubillah!
★★★★★★★★
Ta ɗauki kimanin mintuna 20 kafin Zahrah ta ja dogon numfashi wanda lokaci ɗaya ta saki wani irin ihu. Mutanen da ke waje kan su sun tsorata bare kuma Mamah dake kusa da Zahrah, wasu faratu ne zaƙo zaƙo suka fara fitowa daga hannun ta sannan ƙwayar idon ta ta juya baka ganin komai sai farin idon da ya sauya zuwa blue colour ga wani girma da jikin ta ya ƙara tamkar wata aljana da ta fito filin daga.
Mamah ko rasa yadda zata yi da ita tayi, banda ɓari babu abun da jikin ta ke yi.
Miƙewa tsaye Zahrah tayi tana nufar hanyar waje, Mamah bata yi ƙoƙarin riƙe ta ba saboda ita kanta a tsorace take.
Hakan yayi daidai da shigowar Kawu cikin gidan.
Zaro idanuwa yayi cikin kiɗima ya fara ja da baya da niyyar guduwa..
Kirif!! Ƙofa ta rufe kanta yayin da halittar dake gaban shi ta sheƙe da wata dariya maras daɗin ji.
“Hahhhhhhhhh_hhhhhhhhh_hhhhhhhhhhh” dariyar da bata tsaya ba sai bayan minti 10. Kawu kuwa duk rashin tsoro irin nashi yau yaji, ai ance faɗa da aljani ba daɗi.... gabaɗaya zufa ce ke ketowa a jikin shi, bata yi mishi komai ba kawai hannun ta ta ɗaga sama lokaci ɗaya Kawu ma ya ɗago bisa iska.
Gefe ta wulla kawu kafin ta ƙara daga shi can sama a wannan karon, wani irin jujjuya shi take wanda hannun ta ne ke famar yin wannan aiki ɗin, bugawar da tayi mishi sai da ƙasa ta jijjiga, tuni ƴan majalisa suka watse duk da basu san daga ina bane hakan.
Ko motsi Kawu baya yi hakan yasa ta busa mishi iskar bakin ta daga wurin da take.
A wahalce yaja wani dogon numfashi. Bai zata ba bai nufa ba sai ka cinnaku sun kewaye shi, cizo ta ko ina yi masa suke. Babu abinda yake banda susa da kururuwa.
Duk abinda ke faruwa Mamah ta kasa cewa komai. Sai can ta samu bakin magana
“zahrah don Allah kiyi haƙuri ki bar shi haka ai yaji jiki”
“hhhhhh_hhhhh" bayan wani lokaci tayi shiru sannan ta juyo tana fuskantar Mamah
Cikin haɗe fuska take magana
“Madina! Wannan ba Zahrah bace nice!” ta faɗa cikin Muryar ta maras daɗin saurara..
Jikin Mamah ne ya fara tsuma hakan yasa Zahrah hura wa Kawu iska, nan da nan cinnakun suka ɓace ɓat! Jikin shi kuwa duk ya kumbura, ga uban ciwon da yake masa. Banzan kallo halittar ta watsa mishi sannan tace
“Idrisu BabanMutuwa!"
A tsorace Kawu ya ɗaga sannan ya maida kan sa ƙasa
“ka saurare Ni da kyau! Ka gama naka mulkin yanzu lokaci na ne!
Ka daɗe kana cutar da mahaifiya ta da bata taɓa zaluntar ka ba!”
A lokacin mamah ta zube a ƙasa sumammiya. Duk wannan na daga cikin shirin halittar.
“Idrisu Ni na san ka! Ka cutar da rayuwar mu, baka san cewa na san kai ne ka kashe mahaifi naba koh?, Kai ne ka hana Mamah komawa ga dangin ta ta hanyar sihiri koh? Toh wallahi ka kuskura ka ƙara wani kuskure kan hakan zan tona asiri har ƙwayoyin da kake siyarwa”
Kawu dai an rasa bakin magana,kai kawai yake jijjigawa.
“magana zaka yi ba jijjiga kai kamar gwaje ba”
“eh na daina wallahi na daina”
Daga haka ta ɗaga hannun ta lokaci ɗaya shima ya tashi bata direshi ko ina ba sai cikin ɗakin sa.
Tana fitowa ta ɗaga Mamah ma ta kai ta kan katifar ta.
Daga nan ta hura mata iska ita kuma ta faɗi ƙasa kamar matacciya..
Numfashi Mamah ta sauƙe lokaci ɗaya kuma ta tuna meh yake faruwa. Tana juyo wa taga Zahrah kwance kamar gawa..
A hankali ta nufo ganin kamar bata motsi yasa Mamah saurin ɗebo ruwa a cup, addu'ah ta tofa ciki sannan ta shafa mata a fuska.
Numfashin da Zahrah ta ja yasa Mamah jin sanyi cikin ranta. A hankali ta fara buɗe idanuwan ta tana mai tuna abun da ya faru.
“Sannu Zahrah, ina ne yake miki ciwo?” ta faɗa a kiɗimce
“mamah kai na”
“sannu yi haƙuri bari na je na siyo miki magani, ki jira Ni kada ki fita kinji..”
Hijabin ta ta janyo ta fito, karo suka ci da ya Ishaq ƙofar gida ba tare da yan shi bane ta gota zata wuce. Cike da mamaki yace
“mamah meh ke faruwa?” sai a lokacin Mamah ta ɗago
“zan siyo paracetamol me a nan chemist zahrah ce ba lafiya.”
“subhanallah, toh ki koma ciki bari na shigo Mu kai ta asibiti.”
Da kan shi ya ɗauko Zahrah ya saka ta a mota. Babu ƙaƙƙautawa suka isa asibiti. A&E (Accident and Emergency) aka nufa da Zahrah.
Taimakon da ta samu daga wurin likitoci yasa ta ɗan ware.
Sai wajen 5:00pm aka sallame su ammah kafin nan Doctor ya nemi magana da namijin saboda matar kam duk a ruɗe take.
Bayan sun shiga office ɗin doctor, a hankali doctor ɗin ya kalli yaya Ishaq
“bawan Allah garin ya kuka bar ƙanwar taka damuwa ta mata yawa, yarinya ƙarama a ce BP nata na elevating haka tun yazo, gaskiya da matsala ko ma meh take so ya kamata Ku bata”
A sanyaye yaya Ishaq yace “in sha Allah doctor za'a kiyaye”
Daga haka ya fito.
Da kanshi ya ƙara ɗaukan Zahrah suka nufi mota har suka isa babu wanda yayi magana. Bayan sun isa Mamah da kanta ta wanki Zahrah da ruwa mai zafi sannan ta haɗa mata tea Mai kauri da sauran kayayyakin da Ishaq ya siyo musu.
Bayan sallar maghrib yaya Ishaq ya fita sallah sannan Mamah ma tayi. Kallon Zahrah tayi tace “zaki iya sallar?" Kai ta gyada a hankali Mamah ta taimaka mata tayi alwala a zaune sannan tayi sallar ma a zaune.
Bayan yaya Ishaq ya dawo Mamah ta shiga kitchen don girka abinci, ya rage iya yaya Ishaq ne da Zahrah. Kallon ta yayi yace
“cutie, meh ke damun ki haka kike sa damuwa a ranki”
“babu komai yaya Ishaq, meh ka gani?”
Wani kallo ya watsa mata
“baki yadda Ni ɗan uwan ki baneh da ba zaki iya sharing damuwar ki da Ni ba ko?”
Jijjiga kai tayi tace
“aah yaya babu komai fah, Ni mah ban San meh ya same Ni ba kawai dai Kawu ya zo dukan Mamah shine na tare, daga nan ban san ina nake ba”.
Shiru yayi yana nazarin wannan kawun da take faɗa, yana don ganin shi gaskiya.
“shikenan cutie, ki huta kafin Mamah ta gama girki”
Bayan sun ci dinner tukun na Yaya Ishaq ya tafi.
TOH FAH, YA RAI ZA'A KAYA, YAU KAWU ANJI JIKI WURIN ALJANU
KO kAWU ZAI SAUYA HALI?
Duk cikin babban gida.
BA'A FARA WASAN BA, JUST FOLLOW MY INK
[19/09, 10:21 a.m.] 💎Diamond Bhatool 💎: ______________★★★_______________
Typing 📲
🏡 *A BABBAN GIDA* 🏡
_(All in a big family🏠)_
★TAKUN FARKO★
_[Labari/Rubutawa]_
*©Fadimatu Adamu Hassan*
*A.K.A DIAMOND BHATOOL*💎
️
_______________★★★________________️
﷽
Shafin ku ne ƙawaye na
ZAINAB SHEHU UMAR ( ZEELY)
SA'ADATU LAMARA ZULKHAIRAT (Matar mijinta)
RABI'ATU ABDULLAHI HASSAN (matar Ɗan jagade)
FATIMA AHMAD ABDULLAHI (Fatima anatomy)
Ina ƙaunar ku saboda Allah
Barkan ku da Sallah
SHARE AND COMMENT PLEASE!
_______________★★★________________
Sassafiya Mamah ta tashi da aikace-aikacen gida. Sai around 8:00am Zahrah ta fito tana miƙa
“oooooooooooh”
Mamah ce ta kalle ta sannan ta kawar da kai. Wurin Mamah ta taho
“ina kwana Mamah"
“lafiya ƙalau Zahrah kije kiyi wanka sai ki siyo manah ƙosai da koko gidan Mati."
Da “toh Zahrah ta amsa tana wucewa banɗaki. Bucket ta cika da ruwa sannan ta shiga toilet ɗin. Wanka tayi ta fito. Rigar ta ƴan kanti wacce ta ɗan ji jiki ta saka kafin ta shafa mai. Tana gamawa ta janyo hijabin ta da saman shi ya ɗan koɗe saboda dukan rana.
Fitowa tayi ta cewa Mamah
“kawo kuɗin”
miƙa mata 500Naira tayi sannan tace
“ki siyo bread 🍞 Babba guda ɗaya da canjin.
“toh"
Daga haka ta fita zuwa gidan Mati da ke kan kwanar layin su.
Tana fita ƙofar gidan su nan a cike kamar wadda za'a yi taro sun cika rumfar wasu kuma har da kan dandamalin da ke jikin gidan sai ihu suke suna buga uban shewa da gani kaga tataccun ƴan iska. Kallo ɗaya tayi musu ta kau da kanta gefe haɗi da tsaki.
Aljan ne ya hango ta sai wani fara washe baki
“ƴar oga! Ina zaki haka da sassafe"
Bata yi tunani da ita yake ba shi yasa ko kallo bai samu daga gare ta ba. Su kuwa sauran ƴan dabar suka saka ihu nan suka fara tsokalar Aljan.
Da ɗan gudu ta isa gidan sannan ta bada kuɗin ta haɗi da miƙa jug ɗin roba da ta zo da shi.
Ana sallamar ta ta amsa bread wajen Bala Mai shayi daga nan ta wuce gida.
Kamar dai ɗazu wurin a cike yake ammah haka ta wuce abun ta saboda gargaɗin Mamah kan kada ta kuskura ta ce zata kula wani a dabar.
A ɗakin mamah suka karya, Bayan sun karya Mamah ta ɗauƙo wasu kuɗaɗe daga aljihun doguwar rigar da ke jikin ta. Kuɗin zasu kai 15k. Da mamaki Zahrah ke kallon kuɗin, duk da bata da wayo sosai ammah ta san wannan kuɗin da yawa suke
“mamah kuɗin menene wannan?”
“yayan ki Ishaq na da kirki sosai, ya bamu ne mu ƙara a jarin masa”
Ko rufe baki Mamah bata yi ba taga ana shigowa da kayan abinci, shinkafa, taliya, macaroni, indomie da mai har da manja.
Mamaki ne a fuskar su har lokacin da aka ce
“a ina za'a ajiye su?”
Nuna musu ƙofar ɗakin ta tayi don kuwa nan ne wajen da zasu rabauta daga hannun Kawu.
Suna gama shiga da su suka fita. Mamah bata bar mamaki ba ammah tayi shiru abun ta.
Sai wajen 11:00am Kawu ya banko ƙofar ɗakin shi fuskar nan duk yawun bacci alamun ko sallar asuba bai yi ba. Wata shegiyar miƙa da yayi abun takaici Mamah dai jinjina kai tayi tana roƙon Allah ya shirya Yunusa..
Wani kallon banza ya watsowa Mamah sannan yace
“ke ɗan ubanki shine jiya kina ji ina buga gida kika ƙi buɗe min? Gidan na ubanki ne? Nace na ubanki ne gidan?”
Mamah dai bata kula shi ba ta ci gaba da yi wa Zahrah bayanin yadda zasu sauya kasuwancin nasu.
Sheƙa Kawu yayi hakan yasa ya kawo wa Mamah wani uban duka.
Caraf Zahrah ta tare ai kuwa sai a tsakiyar kanta wanda yayi sanadiyar faɗuwar ta ƙasa sumammiya. A firgice mamah ta yo kanta tana jijjiga ta ammah shiru.
Hakan bai ishi Kawu ba sai da ya ƙara kawowa Mamah wani dukan. Bata damu ba saboda hankalin ta da ya matuƙar tashi kada taje ta rasa ɗiyar ta.
Ba tare da ya damu ba ya fice zuwa dabar tasu. Wani ihu suka sa suka fara yi mishi kirari
“Takawar ka lafiya Yunusa BabanMutuwa, kayi yadda kaso da uban kowa, ita kanta mutuwar tsoron ka take, kaga sarki mai cikakken iko”
Dariya yayi jin yadda ake fasa mishi kayi nan da nan majalisa ta fara, ana shan sigari ana gulma tare da kututgumo ashar. Authubillah!
★★★★★★★★
Ta ɗauki kimanin mintuna 20 kafin Zahrah ta ja dogon numfashi wanda lokaci ɗaya ta saki wani irin ihu. Mutanen da ke waje kan su sun tsorata bare kuma Mamah dake kusa da Zahrah, wasu faratu ne zaƙo zaƙo suka fara fitowa daga hannun ta sannan ƙwayar idon ta ta juya baka ganin komai sai farin idon da ya sauya zuwa blue colour ga wani girma da jikin ta ya ƙara tamkar wata aljana da ta fito filin daga.
Mamah ko rasa yadda zata yi da ita tayi, banda ɓari babu abun da jikin ta ke yi.
Miƙewa tsaye Zahrah tayi tana nufar hanyar waje, Mamah bata yi ƙoƙarin riƙe ta ba saboda ita kanta a tsorace take.
Hakan yayi daidai da shigowar Kawu cikin gidan.
Zaro idanuwa yayi cikin kiɗima ya fara ja da baya da niyyar guduwa..
Kirif!! Ƙofa ta rufe kanta yayin da halittar dake gaban shi ta sheƙe da wata dariya maras daɗin ji.
“Hahhhhhhhhh_hhhhhhhhh_hhhhhhhhhhh” dariyar da bata tsaya ba sai bayan minti 10. Kawu kuwa duk rashin tsoro irin nashi yau yaji, ai ance faɗa da aljani ba daɗi.... gabaɗaya zufa ce ke ketowa a jikin shi, bata yi mishi komai ba kawai hannun ta ta ɗaga sama lokaci ɗaya Kawu ma ya ɗago bisa iska.
Gefe ta wulla kawu kafin ta ƙara daga shi can sama a wannan karon, wani irin jujjuya shi take wanda hannun ta ne ke famar yin wannan aiki ɗin, bugawar da tayi mishi sai da ƙasa ta jijjiga, tuni ƴan majalisa suka watse duk da basu san daga ina bane hakan.
Ko motsi Kawu baya yi hakan yasa ta busa mishi iskar bakin ta daga wurin da take.
A wahalce yaja wani dogon numfashi. Bai zata ba bai nufa ba sai ka cinnaku sun kewaye shi, cizo ta ko ina yi masa suke. Babu abinda yake banda susa da kururuwa.
Duk abinda ke faruwa Mamah ta kasa cewa komai. Sai can ta samu bakin magana
“zahrah don Allah kiyi haƙuri ki bar shi haka ai yaji jiki”
“hhhhhh_hhhhh" bayan wani lokaci tayi shiru sannan ta juyo tana fuskantar Mamah
Cikin haɗe fuska take magana
“Madina! Wannan ba Zahrah bace nice!” ta faɗa cikin Muryar ta maras daɗin saurara..
Jikin Mamah ne ya fara tsuma hakan yasa Zahrah hura wa Kawu iska, nan da nan cinnakun suka ɓace ɓat! Jikin shi kuwa duk ya kumbura, ga uban ciwon da yake masa. Banzan kallo halittar ta watsa mishi sannan tace
“Idrisu BabanMutuwa!"
A tsorace Kawu ya ɗaga sannan ya maida kan sa ƙasa
“ka saurare Ni da kyau! Ka gama naka mulkin yanzu lokaci na ne!
Ka daɗe kana cutar da mahaifiya ta da bata taɓa zaluntar ka ba!”
A lokacin mamah ta zube a ƙasa sumammiya. Duk wannan na daga cikin shirin halittar.
“Idrisu Ni na san ka! Ka cutar da rayuwar mu, baka san cewa na san kai ne ka kashe mahaifi naba koh?, Kai ne ka hana Mamah komawa ga dangin ta ta hanyar sihiri koh? Toh wallahi ka kuskura ka ƙara wani kuskure kan hakan zan tona asiri har ƙwayoyin da kake siyarwa”
Kawu dai an rasa bakin magana,kai kawai yake jijjigawa.
“magana zaka yi ba jijjiga kai kamar gwaje ba”
“eh na daina wallahi na daina”
Daga haka ta ɗaga hannun ta lokaci ɗaya shima ya tashi bata direshi ko ina ba sai cikin ɗakin sa.
Tana fitowa ta ɗaga Mamah ma ta kai ta kan katifar ta.
Daga nan ta hura mata iska ita kuma ta faɗi ƙasa kamar matacciya..
Numfashi Mamah ta sauƙe lokaci ɗaya kuma ta tuna meh yake faruwa. Tana juyo wa taga Zahrah kwance kamar gawa..
A hankali ta nufo ganin kamar bata motsi yasa Mamah saurin ɗebo ruwa a cup, addu'ah ta tofa ciki sannan ta shafa mata a fuska.
Numfashin da Zahrah ta ja yasa Mamah jin sanyi cikin ranta. A hankali ta fara buɗe idanuwan ta tana mai tuna abun da ya faru.
“Sannu Zahrah, ina ne yake miki ciwo?” ta faɗa a kiɗimce
“mamah kai na”
“sannu yi haƙuri bari na je na siyo miki magani, ki jira Ni kada ki fita kinji..”
Hijabin ta ta janyo ta fito, karo suka ci da ya Ishaq ƙofar gida ba tare da yan shi bane ta gota zata wuce. Cike da mamaki yace
“mamah meh ke faruwa?” sai a lokacin Mamah ta ɗago
“zan siyo paracetamol me a nan chemist zahrah ce ba lafiya.”
“subhanallah, toh ki koma ciki bari na shigo Mu kai ta asibiti.”
Da kan shi ya ɗauko Zahrah ya saka ta a mota. Babu ƙaƙƙautawa suka isa asibiti. A&E (Accident and Emergency) aka nufa da Zahrah.
Taimakon da ta samu daga wurin likitoci yasa ta ɗan ware.
Sai wajen 5:00pm aka sallame su ammah kafin nan Doctor ya nemi magana da namijin saboda matar kam duk a ruɗe take.
Bayan sun shiga office ɗin doctor, a hankali doctor ɗin ya kalli yaya Ishaq
“bawan Allah garin ya kuka bar ƙanwar taka damuwa ta mata yawa, yarinya ƙarama a ce BP nata na elevating haka tun yazo, gaskiya da matsala ko ma meh take so ya kamata Ku bata”
A sanyaye yaya Ishaq yace “in sha Allah doctor za'a kiyaye”
Daga haka ya fito.
Da kanshi ya ƙara ɗaukan Zahrah suka nufi mota har suka isa babu wanda yayi magana. Bayan sun isa Mamah da kanta ta wanki Zahrah da ruwa mai zafi sannan ta haɗa mata tea Mai kauri da sauran kayayyakin da Ishaq ya siyo musu.
Bayan sallar maghrib yaya Ishaq ya fita sallah sannan Mamah ma tayi. Kallon Zahrah tayi tace “zaki iya sallar?" Kai ta gyada a hankali Mamah ta taimaka mata tayi alwala a zaune sannan tayi sallar ma a zaune.
Bayan yaya Ishaq ya dawo Mamah ta shiga kitchen don girka abinci, ya rage iya yaya Ishaq ne da Zahrah. Kallon ta yayi yace
“cutie, meh ke damun ki haka kike sa damuwa a ranki”
“babu komai yaya Ishaq, meh ka gani?”
Wani kallo ya watsa mata
“baki yadda Ni ɗan uwan ki baneh da ba zaki iya sharing damuwar ki da Ni ba ko?”
Jijjiga kai tayi tace
“aah yaya babu komai fah, Ni mah ban San meh ya same Ni ba kawai dai Kawu ya zo dukan Mamah shine na tare, daga nan ban san ina nake ba”.
Shiru yayi yana nazarin wannan kawun da take faɗa, yana don ganin shi gaskiya.
“shikenan cutie, ki huta kafin Mamah ta gama girki”
Bayan sun ci dinner tukun na Yaya Ishaq ya tafi.
TOH FAH, YA RAI ZA'A KAYA, YAU KAWU ANJI JIKI WURIN ALJANU
KO kAWU ZAI SAUYA HALI?
Duk cikin babban gida.
BA'A FARA WASAN BA, JUST FOLLOW MY INK
[19/09, 10:21 a.m.] 💎Diamond Bhatool 💎: ______________★★★_______________
Typing 📲
🏡 *A BABBAN GIDA* 🏡
_(All in a big family🏠)_
★TAKUN FARKO★
_[Labari/Rubutawa]_
*©Fadimatu Adamu Hassan*
*A.K.A DIAMOND BHATOOL*💎
️
_______________★★★________________️
﷽