Sashe 3
Soyyayar Mutun Da Aljan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin zafin kishi ne ya daki zuciyar Haiman ya mike tsaye hannunsa dafe da kirjinsa ya juya min baya. A lokaci ɗaya wani zazzafan gumi ya fara yanko masa ta ko'ina a jikinsa. "ki yi hakuri Na'eema tsakanin zuciyata da taki da akwai wata dangantaka mai karfi wadda na tabbata kema da sannu zaki santa, kuma kema zaki fara so na a lokacin da wannan dangantakar ta bayyana ga taki zuciyar. Ina son ki Na'eema ba zan iya rabuwa da ke ba. Zan iya zama dake koda bakya so na, zan jira zuciyarki har sai ta so ni koda kuwa lokacin zai kai ga lokacin tsufana ne, zan kasance mijinki har zuwa lokacin. Ni kam ba zan iya rabuwa dake ba. Zan aure ki in kuma baki dama ki ci gaba da zama a gidana har zuwa lokacin da zaki so ni. Zan zama bawa gareki Na'eema ina ji a raina saboda ke kawai aka halicce ni, na yarda da so ɗaya ne tak! Kuma shi nake miki Na'eema."
Yana kawowa nan a zancensa ya bar wurin ba tareda ya koma waiwayen inda nake ba. Wani wahaltaccen kuka ne ya su6uce mini, na shiga rera shi kamar wadda aka ce iyayenta sun cika. Ina cikin kukan ne iyayena suka bayyana a gabana cikin 6acin rai. Na kalle su sau ɗaya na sunkuyar da kaina. Malam wanda dama a cike yake da takaicina ya fara yi mini faɗa kamar zai dake ni.
"Nikam ban san yadda kike so ki maida ni ba Na'eema, da na ɗauka haukar da kike na son Bil'adama kuruciya ce sai gashi abin naki sai gaba-gaba yake, shin me kika maida kan ki ne? Ko dai bakida hankali ne Na'eema? Banda shi a ina kika ta6a ganin an haɗa auren Bil'adama da Aljan? Koko haka kike tunanin zamu zuba miki ido ki kare rayuwarki ta har abada babu aure kina bin bayan Bil'adama?."
Ummy ta kar6i maganar da cewa "Wata kila a kanta za'a fara, banza mara hankali to wallahi tun wuri ki nutsu ki dawo hayyacinki maganar aure babu fashi kuma nan kusa bada nisa ba." a tare suka 6ace rayukansu a 6ace. Hankalina ya koma tashi damuwata ta koma ninkuwa ko kaɗan bana son ran iyayena yana 6aci ta dalilina, na shiga uku ni Na'eema ya zan yi da rayuwata?.
Sai na koma fashewa da Kuka na faɗi kwance bisa shimfiɗar nan ina ayyanawa a raina cewa inama mutuwa zata zo ta ɗauke ni da na huta bakin ciki da kallon kaina a matsayin matar wanin da ba Muhsin ɗina ba.
*Nasmat* ✍
[23/1 17:53] Yar Mutan Arkillah: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*MARUBUCI...*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Soyayyar Mutum da Aljan...* kagaggen labari.
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
Yar'mutan
Arkilla✍
____________
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*Page 4*
Wannan shafin ga baki ɗayansa sadaukarwa ne gareki kawar kirki. *QUEEN HAFSY* aminta ta da ke ta musamman ce, ina yi miki barka da dawowa tawan Allah ya bar zumunci da kaunar juna.
Lokaci mai tsayi na ɗauka ina wannan kukan ganin babu abinda zai kare ni da shi yasa dole na hakura na rarrashi kaina na mike na nufi ɗakina.
Duk tsananin da nake ciki sai da naji saukar ni'ima da sanyi a zuciyata, lokacin da idanuwana sukayi tozali da manya-manyan hotuna na zanen fuskar farin ganina Muhsin. Waɗanda ke makale a kowace kusarwa ta ɗakin. Duk da ba can na nufa ba amma sai naji zuciyata ta jagoranci gangar jikina ta jani zuwa gaban hoton. Na tsaya kikam ina karewa Muhsin kallo wanda yake zaune da kayan aikinsa wato littafi da Alkalami yana son fara rubutu. Nice na zana wannan da hannuna saboda babu inda Muhsin yake min kyan gani kamar in gan shi a karkashin bishiyar nan yana gwada fasaharsa ta rubutu.
Na shafi fuskarsa ta jikin hoton na fara magana cikin shaukin so dan a lokacin ji nake kamar Muhsin ɗin ne a gabana. "Muhsin kasan ina sonka ina kuma kaunarka. Amma gashi ra'ayi na yasha bam-bam dana iyayena. Muhsin bazan iya bijirewa iyayena ba, kamar yadda nake ji bazan iya rabuwa da kai ba. Ya kai masoyina hakika rayuwata tana cikin hatsari, wanda ni kaina ban san makomarta ba. Sai dai ina da buri a kan ka Muhsin. Koda ace ban aure ka ba, ban kuma kasance da kai ba, na so ace na cika maka babban burinka ta yadda har abada zan kafa hujja a zuciyata cewa na taimaki masoyina wajen zama abinda yake so ya zama. Muhsin in dai ban sami ko ɗaya daga cikin waɗannan ba zan iya mutuwa."
Na kifa kaina jikin hoton ina zubda hawaye. Can na ɗago kai na sumbace shi sannan na shiga tunaninsa shin ya tashi daga bacci ya tafi gida ko dai yana nan 'fadarsa'? Karkashin bishiyar nan nake nufi domin nan ne fadar masoyina.
Nan da nan sai naji zuciyata ta kwaɗaitu da son koma ganin fuskarsa. Juyi ɗaya nayi na 6ata sai gani na bayyana karkashin bishiyar nan Amma ban sami Muhsin ba. Wannan yana nufin ya tashi kenan. Ban jira komai ba na nufi gidansu. Kai tsaye ɗakinsa na bayyana nan ma wayam baya nan. Hakan bai sanyayar min guiwa ba na koma 6acewa sai ɗakin mahaifiyarsa gimbiya Suhaima. Wata sassanyar ajiyar zuciya na sauke nan da nan fuskata ta wadatu da kawataccen murmushina. Badan komai ba sai dan ganin zumar rayuwata Muhsin. Yana kwance bisa wani lallausan kilishi wanda ke shimfiɗe a faffaɗa kuma kawataccen ɗakin. Yayi matashin kai da cinyar mahaifiyar tashi tana shafa kansa. farar mace mai farar zuciya.
Can na sami wuri na zauna gefen su ina kallon su kuma ina sauraron maganarsu gwanin sha'awa. Muhsin ya kalli mahaifiyarsa yace "yake ummana shin wai ni babu wata hanya za zan bi in samo maganin wannan lalurar dake damuna?" hawaye ne suka cicciko idon Suhaima, tayi saurin share su tun kafin su fito. Sannan ta kalli ɗan nata mafi soyuwa a cikin zuciyarta tace "koda akwai ta banida sani a kan ta Muhsin, ni kaina da ace na san wata hanya ta samun warakar ka wallahi da na bita na samo maka koda ko zan rasa rayuwata ne." da sauri Muhsin ya kai hannunsa ya rufe bakin ummansa "a'a mahaifiyata, da dai ki mutu kam gwara na tabbata dakiki in yi ta zama a haka har karshen rayuwata." Suhaima ta koma share hawaye tace "kawai dai babu ne ɗana amma wlh da babu abinda zai hana ni binta, Muhsin ina son ganin cikar burin nan naka, ina son ganin ka zama cikakken *MARUBUCI* Amma ban san ta yadda hakan zai kasance ba."
Wata kasalalliyar ajiyar zuciya ya sauke kafin yace "inaga hakan ba zai ta6a yuwuwa bane, inaga ba zan ta6a zama bane wannan shi ne dalilin da yasa Allah ya toshe min kwakwalwa. Amma kam ina son Rubutu Ummana."
Ba umman Muhsin ba ni kaina saida hawayen tausayinsa suka zubo mini. Ta rungume shi cikeda so da tausayinsa "zaka zama ɗana, insha Allahu wata rana zaka zama." gaba ɗaya ɗa da uwar kuka suke yi wannan shine abinda ya kara zaburar da zuciyata kuka nake sosai ina tunani shin ta wace hanya zan iya taimakon Muhsin? Tabbas ya kamata ya zama amma ta yaya?.
6acewa nayi daga ɗakin gimbiya na bayyana gidanmu. A wannan lokacin na gama yanke hukunci babu tsoro ko fargaba a tattareda ni. Na tabbata wannan ita ce damata ta samun abinda nake so daga gare su. Ganin babu kowa a mazaunin mai kama da fada yasa na kutsa kaina izuwa ɗakin baba Malam na shiga da sallama.
Yana kishingiɗe bisa abin sallarsa ya amsa mini sallamar fuskarshi na kallon wani wurin daban. Hakan ya tabbatar mini cewa har yanzu mahaifina fushi yake dani. Na tsuguna ɗan nesa kaɗan da inda yake zaune. Nace "dan Allah baba kayi hakuri, ka sani sarai bana kaunar duk wani abu da zai zo ya 6ata min ranku kaida ummyna." nayi shiru ko zai ce wani abu amma baba bai ce komai ba. Hakan yasa na kara ɗorawa. "Baba dan Allah ina rokon wata alfarma daga gare ka, na yarda da za6in ku zan auri Haiman zan kuma so shi. Amma ni kuma ina bukatar ku cika mini burina kafin wannan auren." sai a lokaci baba ya ɗago ya kalle ni fuskarsa ɗauke da murmushi "dama nace ko canja min ke aka yi ne? Domin ni a nawa sanin Na'eema na bata tsallake umarnina balle ta kai ga bijire mini." "ai har abada ba zan ta6a bijirewa umarninka ba baba." na koma faɗa cike da biyayya da nuna ya isa da ni. Mahaifina ya ji daɗin wannan maganar dan sai da ya tashi daga kishingiɗen da yake ya zauna yana fuskanta ta. Na saci kallon fuskarshi sai na ganta ɗauke da murmushi nima murmushin nayi bakina ɗauke da addu'ar Allah ya taimake ni yasa yau in sami nasara kan mahaifina.
Babana ya katse mini tunani da tambaya. "Mene ne wannan burin naki da kike son cikawa kafin aurenki da Haiman Na'eema?" duk yadda naji na dake d'azu sai da nayi jim kaɗan ina tunanin makomar abinda zan faɗa. Na sake jin muryar baba yana faɗin kar kiji tsoron faɗa min ko mene ne ya' ta, tabbas zan yi miki adalci. Na lura babana ya kagu yaji mene ne burina wanda cika min shi zai sa in kar6i auren mijin da nayi ikirarin bana son sa.
Kaina na sunkuye a kasa na fara magana. "baba, nasan matsayin saninka da yawan shekarunka mawuyacin abune ace bakada masaniya a kan maganin lalurar nan ta Muhsin da na daɗe ina gaya muku. Baba ka dubi Allah da girmansa, ka dubi darajar Ma'aiki (s.a.w) sannan ka dubi daraja da karfin soyayya ka taimake ni in dai har kanada masaniya akan abinda nake tambayar ka baba ka gaya mini. Kar kaji shayin sanar min ko mene ne, idan har na samawa Muhsin waraka ya sami cikar burinsa ta dalilina to zuciyata zata sami nutsuwa zan kuma yi alfahari da soyayyata domin na taimaki wanda nake so. Sannan cikin kwanciyar hankali zan amshi auren za6in ku."
Yana kawowa nan a zancensa ya bar wurin ba tareda ya koma waiwayen inda nake ba. Wani wahaltaccen kuka ne ya su6uce mini, na shiga rera shi kamar wadda aka ce iyayenta sun cika. Ina cikin kukan ne iyayena suka bayyana a gabana cikin 6acin rai. Na kalle su sau ɗaya na sunkuyar da kaina. Malam wanda dama a cike yake da takaicina ya fara yi mini faɗa kamar zai dake ni.
"Nikam ban san yadda kike so ki maida ni ba Na'eema, da na ɗauka haukar da kike na son Bil'adama kuruciya ce sai gashi abin naki sai gaba-gaba yake, shin me kika maida kan ki ne? Ko dai bakida hankali ne Na'eema? Banda shi a ina kika ta6a ganin an haɗa auren Bil'adama da Aljan? Koko haka kike tunanin zamu zuba miki ido ki kare rayuwarki ta har abada babu aure kina bin bayan Bil'adama?."
Ummy ta kar6i maganar da cewa "Wata kila a kanta za'a fara, banza mara hankali to wallahi tun wuri ki nutsu ki dawo hayyacinki maganar aure babu fashi kuma nan kusa bada nisa ba." a tare suka 6ace rayukansu a 6ace. Hankalina ya koma tashi damuwata ta koma ninkuwa ko kaɗan bana son ran iyayena yana 6aci ta dalilina, na shiga uku ni Na'eema ya zan yi da rayuwata?.
Sai na koma fashewa da Kuka na faɗi kwance bisa shimfiɗar nan ina ayyanawa a raina cewa inama mutuwa zata zo ta ɗauke ni da na huta bakin ciki da kallon kaina a matsayin matar wanin da ba Muhsin ɗina ba.
*Nasmat* ✍
[23/1 17:53] Yar Mutan Arkillah: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*MARUBUCI...*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Soyayyar Mutum da Aljan...* kagaggen labari.
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
Yar'mutan
Arkilla✍
____________
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*Page 4*
Wannan shafin ga baki ɗayansa sadaukarwa ne gareki kawar kirki. *QUEEN HAFSY* aminta ta da ke ta musamman ce, ina yi miki barka da dawowa tawan Allah ya bar zumunci da kaunar juna.
Lokaci mai tsayi na ɗauka ina wannan kukan ganin babu abinda zai kare ni da shi yasa dole na hakura na rarrashi kaina na mike na nufi ɗakina.
Duk tsananin da nake ciki sai da naji saukar ni'ima da sanyi a zuciyata, lokacin da idanuwana sukayi tozali da manya-manyan hotuna na zanen fuskar farin ganina Muhsin. Waɗanda ke makale a kowace kusarwa ta ɗakin. Duk da ba can na nufa ba amma sai naji zuciyata ta jagoranci gangar jikina ta jani zuwa gaban hoton. Na tsaya kikam ina karewa Muhsin kallo wanda yake zaune da kayan aikinsa wato littafi da Alkalami yana son fara rubutu. Nice na zana wannan da hannuna saboda babu inda Muhsin yake min kyan gani kamar in gan shi a karkashin bishiyar nan yana gwada fasaharsa ta rubutu.
Na shafi fuskarsa ta jikin hoton na fara magana cikin shaukin so dan a lokacin ji nake kamar Muhsin ɗin ne a gabana. "Muhsin kasan ina sonka ina kuma kaunarka. Amma gashi ra'ayi na yasha bam-bam dana iyayena. Muhsin bazan iya bijirewa iyayena ba, kamar yadda nake ji bazan iya rabuwa da kai ba. Ya kai masoyina hakika rayuwata tana cikin hatsari, wanda ni kaina ban san makomarta ba. Sai dai ina da buri a kan ka Muhsin. Koda ace ban aure ka ba, ban kuma kasance da kai ba, na so ace na cika maka babban burinka ta yadda har abada zan kafa hujja a zuciyata cewa na taimaki masoyina wajen zama abinda yake so ya zama. Muhsin in dai ban sami ko ɗaya daga cikin waɗannan ba zan iya mutuwa."
Na kifa kaina jikin hoton ina zubda hawaye. Can na ɗago kai na sumbace shi sannan na shiga tunaninsa shin ya tashi daga bacci ya tafi gida ko dai yana nan 'fadarsa'? Karkashin bishiyar nan nake nufi domin nan ne fadar masoyina.
Nan da nan sai naji zuciyata ta kwaɗaitu da son koma ganin fuskarsa. Juyi ɗaya nayi na 6ata sai gani na bayyana karkashin bishiyar nan Amma ban sami Muhsin ba. Wannan yana nufin ya tashi kenan. Ban jira komai ba na nufi gidansu. Kai tsaye ɗakinsa na bayyana nan ma wayam baya nan. Hakan bai sanyayar min guiwa ba na koma 6acewa sai ɗakin mahaifiyarsa gimbiya Suhaima. Wata sassanyar ajiyar zuciya na sauke nan da nan fuskata ta wadatu da kawataccen murmushina. Badan komai ba sai dan ganin zumar rayuwata Muhsin. Yana kwance bisa wani lallausan kilishi wanda ke shimfiɗe a faffaɗa kuma kawataccen ɗakin. Yayi matashin kai da cinyar mahaifiyar tashi tana shafa kansa. farar mace mai farar zuciya.
Can na sami wuri na zauna gefen su ina kallon su kuma ina sauraron maganarsu gwanin sha'awa. Muhsin ya kalli mahaifiyarsa yace "yake ummana shin wai ni babu wata hanya za zan bi in samo maganin wannan lalurar dake damuna?" hawaye ne suka cicciko idon Suhaima, tayi saurin share su tun kafin su fito. Sannan ta kalli ɗan nata mafi soyuwa a cikin zuciyarta tace "koda akwai ta banida sani a kan ta Muhsin, ni kaina da ace na san wata hanya ta samun warakar ka wallahi da na bita na samo maka koda ko zan rasa rayuwata ne." da sauri Muhsin ya kai hannunsa ya rufe bakin ummansa "a'a mahaifiyata, da dai ki mutu kam gwara na tabbata dakiki in yi ta zama a haka har karshen rayuwata." Suhaima ta koma share hawaye tace "kawai dai babu ne ɗana amma wlh da babu abinda zai hana ni binta, Muhsin ina son ganin cikar burin nan naka, ina son ganin ka zama cikakken *MARUBUCI* Amma ban san ta yadda hakan zai kasance ba."
Wata kasalalliyar ajiyar zuciya ya sauke kafin yace "inaga hakan ba zai ta6a yuwuwa bane, inaga ba zan ta6a zama bane wannan shi ne dalilin da yasa Allah ya toshe min kwakwalwa. Amma kam ina son Rubutu Ummana."
Ba umman Muhsin ba ni kaina saida hawayen tausayinsa suka zubo mini. Ta rungume shi cikeda so da tausayinsa "zaka zama ɗana, insha Allahu wata rana zaka zama." gaba ɗaya ɗa da uwar kuka suke yi wannan shine abinda ya kara zaburar da zuciyata kuka nake sosai ina tunani shin ta wace hanya zan iya taimakon Muhsin? Tabbas ya kamata ya zama amma ta yaya?.
6acewa nayi daga ɗakin gimbiya na bayyana gidanmu. A wannan lokacin na gama yanke hukunci babu tsoro ko fargaba a tattareda ni. Na tabbata wannan ita ce damata ta samun abinda nake so daga gare su. Ganin babu kowa a mazaunin mai kama da fada yasa na kutsa kaina izuwa ɗakin baba Malam na shiga da sallama.
Yana kishingiɗe bisa abin sallarsa ya amsa mini sallamar fuskarshi na kallon wani wurin daban. Hakan ya tabbatar mini cewa har yanzu mahaifina fushi yake dani. Na tsuguna ɗan nesa kaɗan da inda yake zaune. Nace "dan Allah baba kayi hakuri, ka sani sarai bana kaunar duk wani abu da zai zo ya 6ata min ranku kaida ummyna." nayi shiru ko zai ce wani abu amma baba bai ce komai ba. Hakan yasa na kara ɗorawa. "Baba dan Allah ina rokon wata alfarma daga gare ka, na yarda da za6in ku zan auri Haiman zan kuma so shi. Amma ni kuma ina bukatar ku cika mini burina kafin wannan auren." sai a lokaci baba ya ɗago ya kalle ni fuskarsa ɗauke da murmushi "dama nace ko canja min ke aka yi ne? Domin ni a nawa sanin Na'eema na bata tsallake umarnina balle ta kai ga bijire mini." "ai har abada ba zan ta6a bijirewa umarninka ba baba." na koma faɗa cike da biyayya da nuna ya isa da ni. Mahaifina ya ji daɗin wannan maganar dan sai da ya tashi daga kishingiɗen da yake ya zauna yana fuskanta ta. Na saci kallon fuskarshi sai na ganta ɗauke da murmushi nima murmushin nayi bakina ɗauke da addu'ar Allah ya taimake ni yasa yau in sami nasara kan mahaifina.
Babana ya katse mini tunani da tambaya. "Mene ne wannan burin naki da kike son cikawa kafin aurenki da Haiman Na'eema?" duk yadda naji na dake d'azu sai da nayi jim kaɗan ina tunanin makomar abinda zan faɗa. Na sake jin muryar baba yana faɗin kar kiji tsoron faɗa min ko mene ne ya' ta, tabbas zan yi miki adalci. Na lura babana ya kagu yaji mene ne burina wanda cika min shi zai sa in kar6i auren mijin da nayi ikirarin bana son sa.
Kaina na sunkuye a kasa na fara magana. "baba, nasan matsayin saninka da yawan shekarunka mawuyacin abune ace bakada masaniya a kan maganin lalurar nan ta Muhsin da na daɗe ina gaya muku. Baba ka dubi Allah da girmansa, ka dubi darajar Ma'aiki (s.a.w) sannan ka dubi daraja da karfin soyayya ka taimake ni in dai har kanada masaniya akan abinda nake tambayar ka baba ka gaya mini. Kar kaji shayin sanar min ko mene ne, idan har na samawa Muhsin waraka ya sami cikar burinsa ta dalilina to zuciyata zata sami nutsuwa zan kuma yi alfahari da soyayyata domin na taimaki wanda nake so. Sannan cikin kwanciyar hankali zan amshi auren za6in ku."