Sashe 1
Soyyayar Mutun Da Aljan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[23/1 17:53] Yar Mutan Arkillah: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*MARUBUCI...*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Soyayyar Mutum da Aljan...* kagaggen labari.
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
Yar'mutan
Arkilla✍
____________
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
Page *1*
_Bismillahir rahamanir raheem._
Da sunan Allah mai rahma mai jinkai. Alhamdulillah dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah maɗaukakin sarki. Wanda ya bani dama da ikon fara rubuta wannan takaitaccen labari mai ɗauke da rikicin soyayya. Labarin MARUBUCI labari ne da zai wayar wa masoya kan su domin gane yadda daraja da kuma kimar soyayyar gaskiya take. Da kuma yadda ake sadaukarwa kan soyayya da sallama rayuwa ga biyan bukatar masoyi. Jigon wannan labari shine soyayya darajarta da kimar ta. Da fatan masoya zasu biyo ni sannu a hankali domin kwasar romon dake cikinsa.
Bazan iya kirga ku ba masoyana ko kuma groups da litattafai na suke zuwa, sai dai ina so ku sani sakonnin ku na zuwa gare ni bisa kari kuma ina godiya da kulawa. Sannan ina so ku sani ina kaunar ku ina kuma jin daɗin shawarwarinku gare ni Allah ya bar zumunci 🤝
__________
_______
____
__
_ farkon labari...
Zaune yake bisa wani dutse wanda da yayi sama kaɗan da kasa, karkashin wata bishiya mai yawan ni'ima da yalwar sanyi ga wata ni'mtacciyar iska dake kaɗawa. Wannan bishiyar a bayan gari take gurin da Muhsin ya mayar tamkar fadar sa ko wata majalisa ta zama musamman idan yana so ya jarraba fasaharsa. Yau ma kamar kowane lokaci yana jingine da jikin bishiyar hannun sa rike da farin littafi da alkalamin rubutu. Ya ɗora alkalamin bisa littafin kamar mai yin rubutun sai dai har yanzu ya kasa rubuta koda harafin 'A' a jikin littafin.
Tun yana yi da sauki har ya dawo yi da dukkanin karfin zuciyarshi amma abokiyar gwagwarmaya kwakwalwa ta ki ta bashi haɗin kai kamar kowane lokaci dai. Idanunsa suka cicciko da kwalla jikinsa ya hau kyarma yayi watsi da littafi har ma da alkalamin, tsananin takaici ya kama shi. Ya shiga kuka da takaicin kasancewarsa dakiki mai kunshe da babban buri.
Allah sarki Muhsin. Ni da nake zaune a gefe ina kallon inda ke faruwa na share kwalla, tsantsan tausayinsa ya kara kama ni. Duk da cewa nasan baya gani na amma hakan baya sanyayyar min guiwa ko dakile zuciyata ga jin tausayinsa da kuma kara nutsawa a tafkin kaunar sa.
Kuka yake sosai yana buga kansa a jikin bishiyar nan kamar yadda ya saba yi idan irin hakan ta kama shi. Da sauri na mike domin dakatar da shi tun bai kai ga illata min kansa ba. Cikin dabaru da hikima da kuma kwarewa irin tamu ta sarrafa bil'adama na dakatar da shi ga abinda yake yi. Sai dai har yanzu bai daina kukan ba. Yana yi ina yi an rasa wanda zai rarrashi wani. Ban san ya zan yi ba, damuwar Muhsin na tada hankalina kamar yadda zubar hawayensa ke haifar da fitar nawa hawayen. Tsananin so da tausayinsa na neman hallaka ni, rashin sanin hanyar da zan bi dan in taimake shi na neman illata zuciyata. Yau kimanin shekaru ashirin kenan ina bautar da rayuwa ta ga soyayyarshi. Duk da cewa bai ma san ina yi ba amma na taimaki rayuwarsa ta hanyoyi masu yawa... Muna haɗuwa da Muhsin har ma na labarta masa irin kaunar da nake masa amma cikin mafarkin shi ni kuma zahiri na. Har yau bai ji a ransa cewa da gaske ni ɗin wata ce ta gaskiya ba, ya ɗauki mafarkin da yake yi dani tamkar irin sauran mafarke-mafaken da ake yi a cikin bacci.
*Wane ne Muhsin?*
Tsayayen saurayi kyakkyawa na gaban kwatance ɗan kimanin shekaru ashirin da biyar da haihuwa. Fari sal mai matsakaicin tsayi da faɗi.
Muhsin Al'hussain shine cikakken sunan sa. Ɗa na biyu a gidan sarautar garin gabas wanda yake cikin nahiyar birnin lumai. Garin gabas babban birni ne wanda ya kunshi mutane daban-daban maban-bantan akidu da addinai. Mahaifin Muhsin mai martaba sarki Al'hussain shi ne yake rike da mulkin kasar a yanzu, wanda shima gadon sarautar yayi a gurin yayansa yayan nasa kuma ya gada a gurin iyayensa haka tsarin yake. Mai martaba sarki Al'hussain shi da iyalansa duka ma biya addinin musulunci ne. Yana da mata biyu da ya'ya biyar inda Muhsin ya kasance na biyu a cikin su. Yayansa ɗaya Kabir sai Fatima karamar kanwar su. Su ne yan' ɗaki ɗaya, wato ya'yan uwar gida gimbiya Suhaima. Sai ya'yan ɗakin gimbiya Amrah su biyu Suhaila da Aliyu.
Duk cikin waɗannan ya'yan Muhsin ne kaɗai ya fito daban. Dukkanin su suna da ilmi da kwazon karatu yana shiga kansu sosai, amma shi kam sam kansa baya ɗaukar karatu sau tari a magana ma in yaje wani matakin makalewa yake yi. A wasu lokutan yana magana yana kuka abin tausayi. Akwai kwazon maida hankali da tsare litattafai da ido yana karantawa amma duk abinda ya karanto sai dai ya tsaya iya bakinsa baya kaiwa ga kwakwalwarsa balle ta ajiye masa shi duk kuwa da irin ko'karin da yake na ganin ya saka karatun a kansa.
Hakan ba karamin raini ya ja mishi ga sauran kannensa ba kai har ma da waɗansu ya'yan sarakan idan aka haɗu wawa dolo mai ɗanyen kai babu abinda basa ce masa. Matsalarsa ta gawurta tun iyayen na ɗauka laifinsa ne har suka dawo suka saduda suka fauwala al'amuransu ga Allah.
Sai kuma wani iko na Ubangiji da ya yi a kansa, ya kawo tsananin so da burin zamowa MARUBUCI ya saka mishi a rai, a duniya babu abinda yake burge Muhsin kamar rubuta kirkirarren labari. Kamar yadda babu abinda yafi so kamar ya ga kansa a matsayin MARUBUCI. Lokuta da yawa yakan ji kamar yana tsara labari a zuciyarsa amma idan yaje ya zauna da burin son rubutawa sai kwakwalwarsa ta hargitse ta dagula masa komai. Ya dawo kamar wani zautacce baya kula kowa ba kuma ya shiga kowace irin sabga sai dai ka ganshi yayi lamo yana nazari a kullum Muhsin cikin tunani yake a koda yaushe hawayensa zuba suke yi. Ya rasa abinda yasa ya kasance haka.
* * * * * *
Ni kuwa ikon Allah ne ya haɗa ni da Muhsin, da gani ɗaya naji na kamu da tsananin tausayinsa tun yana yaro ɗan kimanin shekaru biyar a duniya. Tun a lokacin na fara shiga rayuwarsa ina son taimakon sa amma matsalar sa ta sha gaban tunani da sani na.
Alakata da Muhsin tayi girman da duk wani ɗan'uwana na kusa da na nesa yasan ina tare da shi kuma ina matukar kaunarsa. Babu yadda iyayena basu yi ba dan ganin sun raba tsakani na da Muhsin amma abin ya gagara, tun suna jin haushi na har suka dawo suka hakura.
* * * * *
Ni jinsin Alajan ce wadda ta fito daga babban gida mai daraja a can tamu nahiyar. Ni kaɗai Allah ya azurta iyayena da haihuwa kuma mahaifina babban Malamin addinin musulunci ne a can, shi yasa dukkan mu muka zamo mabiya addinin.
Babu irin rokon da ban yiwa mahaifiyata da mahaifina ba kan su taimaka in sunada wani taimako ko masaniya akan lalurar da Muhsin ke ɗauke da ita su taimaka su gaya min amma sun ki. Duk kuwa da cewa inada yakini cewa babana Malam ba zai rasa masaniya akan maganin warakar wannan cutar ba.
Wannan kenan.
Cigaban labari...
* * * * *
Dogon numfashi na koma ja a karo na barkatai, ina karewa masoyina Muhsin da bacci ya sace kallo. Baccinsa yake cikin kwanciyar hankali, yana fidda numfashi slowly. Na rufe dara-daran idona na koma buɗe su a kansa. Ga namiji har namiji amma wananan lalurar zata nakasa shi. Wani irin shaukin son sa ne ka kara ninkuwa a raina yana daɗa mamaye duk wata kafa ta sadar da tunanina. Nan da nan na yanke shawarar tafiya na mika ajiyayyun sakonnin soyayyata ta kafar sadarwar da na shirya mana ta haɗuwa da masoyina ba tareda ya san ko ni wacce ba a cikin mafarki. Dama haka na saba a duk lokacin da shaukin kaunarsa ya motsa mini, nakan zama tamkar inuwa na ratsa jikinsa harma da tunaninsa sai ya ganni kamar yana mafarki ta nan muka saba da Muhsin sosai kuma ta nan ne nake sanar mishi irin son da nake masa. Ta wannan hanyar ne nake farantawa Muhsin ina ɗebe masa kewar rayuwar kaɗaicin da yake. Domin daga ni sai mahaifiyarsa gimbiya Suhaima mu kaɗai ne muke shiga rayuwarsa kuma muke ko'karin faranta masa domin mahaifinsa baya da lokaci koda yaushe yana cikin fada yana fama da talakawa da matsalolinsu.
Na lumshe idona cike da shauki sannan na yunkura da nufin aiwatar da nufina, na shiga jikin masoyina domin sada zumuncin kauna. Kamar daga sama naji an yi gaggawar riko kafaɗata ta baya ana faɗin
"dakata Na'eema"
*Nasmat* ✍
[23/1 17:53] Yar Mutan Arkillah: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*MARUBUCI...*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Soyayyar Mutum da Aljan...* kagaggen labari.
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
Yar'mutan
Arkilla✍
____________
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*Page 2*
*Alhamdulillah ina godiya ga Allah (s.w.a) kuma ina godiya gareku bisa yadda kuka kar6i wannan labarin kuma kuke kara karfafa min guiwa a kan sa. Na gode! Na gode! Masoyana Allah ya bar min ku a duk inda kuke. One love 🤝*
Wannan dakatarwar da aka yi min ba karamin 6ata mini rai tayi ba, na juyo a fusace dan ganin wane ne wannan da yayi min irin wannan katsalandan a cikin rayuwata. "Ummy" na faɗa cike da mamakin ganin mahaifiyata a gabana, wadda ban ta6a tsammanin ta a yanzu kuma a nan ba. Ta zuba min fararen idanunta fuskarta cike da damuwa. Wannan ne ya kara sanyayar mini da ga66an jikina.
*MARUBUCI...*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Soyayyar Mutum da Aljan...* kagaggen labari.
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
Yar'mutan
Arkilla✍
____________
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
Page *1*
_Bismillahir rahamanir raheem._
Da sunan Allah mai rahma mai jinkai. Alhamdulillah dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah maɗaukakin sarki. Wanda ya bani dama da ikon fara rubuta wannan takaitaccen labari mai ɗauke da rikicin soyayya. Labarin MARUBUCI labari ne da zai wayar wa masoya kan su domin gane yadda daraja da kuma kimar soyayyar gaskiya take. Da kuma yadda ake sadaukarwa kan soyayya da sallama rayuwa ga biyan bukatar masoyi. Jigon wannan labari shine soyayya darajarta da kimar ta. Da fatan masoya zasu biyo ni sannu a hankali domin kwasar romon dake cikinsa.
Bazan iya kirga ku ba masoyana ko kuma groups da litattafai na suke zuwa, sai dai ina so ku sani sakonnin ku na zuwa gare ni bisa kari kuma ina godiya da kulawa. Sannan ina so ku sani ina kaunar ku ina kuma jin daɗin shawarwarinku gare ni Allah ya bar zumunci 🤝
__________
_______
____
__
_ farkon labari...
Zaune yake bisa wani dutse wanda da yayi sama kaɗan da kasa, karkashin wata bishiya mai yawan ni'ima da yalwar sanyi ga wata ni'mtacciyar iska dake kaɗawa. Wannan bishiyar a bayan gari take gurin da Muhsin ya mayar tamkar fadar sa ko wata majalisa ta zama musamman idan yana so ya jarraba fasaharsa. Yau ma kamar kowane lokaci yana jingine da jikin bishiyar hannun sa rike da farin littafi da alkalamin rubutu. Ya ɗora alkalamin bisa littafin kamar mai yin rubutun sai dai har yanzu ya kasa rubuta koda harafin 'A' a jikin littafin.
Tun yana yi da sauki har ya dawo yi da dukkanin karfin zuciyarshi amma abokiyar gwagwarmaya kwakwalwa ta ki ta bashi haɗin kai kamar kowane lokaci dai. Idanunsa suka cicciko da kwalla jikinsa ya hau kyarma yayi watsi da littafi har ma da alkalamin, tsananin takaici ya kama shi. Ya shiga kuka da takaicin kasancewarsa dakiki mai kunshe da babban buri.
Allah sarki Muhsin. Ni da nake zaune a gefe ina kallon inda ke faruwa na share kwalla, tsantsan tausayinsa ya kara kama ni. Duk da cewa nasan baya gani na amma hakan baya sanyayyar min guiwa ko dakile zuciyata ga jin tausayinsa da kuma kara nutsawa a tafkin kaunar sa.
Kuka yake sosai yana buga kansa a jikin bishiyar nan kamar yadda ya saba yi idan irin hakan ta kama shi. Da sauri na mike domin dakatar da shi tun bai kai ga illata min kansa ba. Cikin dabaru da hikima da kuma kwarewa irin tamu ta sarrafa bil'adama na dakatar da shi ga abinda yake yi. Sai dai har yanzu bai daina kukan ba. Yana yi ina yi an rasa wanda zai rarrashi wani. Ban san ya zan yi ba, damuwar Muhsin na tada hankalina kamar yadda zubar hawayensa ke haifar da fitar nawa hawayen. Tsananin so da tausayinsa na neman hallaka ni, rashin sanin hanyar da zan bi dan in taimake shi na neman illata zuciyata. Yau kimanin shekaru ashirin kenan ina bautar da rayuwa ta ga soyayyarshi. Duk da cewa bai ma san ina yi ba amma na taimaki rayuwarsa ta hanyoyi masu yawa... Muna haɗuwa da Muhsin har ma na labarta masa irin kaunar da nake masa amma cikin mafarkin shi ni kuma zahiri na. Har yau bai ji a ransa cewa da gaske ni ɗin wata ce ta gaskiya ba, ya ɗauki mafarkin da yake yi dani tamkar irin sauran mafarke-mafaken da ake yi a cikin bacci.
*Wane ne Muhsin?*
Tsayayen saurayi kyakkyawa na gaban kwatance ɗan kimanin shekaru ashirin da biyar da haihuwa. Fari sal mai matsakaicin tsayi da faɗi.
Muhsin Al'hussain shine cikakken sunan sa. Ɗa na biyu a gidan sarautar garin gabas wanda yake cikin nahiyar birnin lumai. Garin gabas babban birni ne wanda ya kunshi mutane daban-daban maban-bantan akidu da addinai. Mahaifin Muhsin mai martaba sarki Al'hussain shi ne yake rike da mulkin kasar a yanzu, wanda shima gadon sarautar yayi a gurin yayansa yayan nasa kuma ya gada a gurin iyayensa haka tsarin yake. Mai martaba sarki Al'hussain shi da iyalansa duka ma biya addinin musulunci ne. Yana da mata biyu da ya'ya biyar inda Muhsin ya kasance na biyu a cikin su. Yayansa ɗaya Kabir sai Fatima karamar kanwar su. Su ne yan' ɗaki ɗaya, wato ya'yan uwar gida gimbiya Suhaima. Sai ya'yan ɗakin gimbiya Amrah su biyu Suhaila da Aliyu.
Duk cikin waɗannan ya'yan Muhsin ne kaɗai ya fito daban. Dukkanin su suna da ilmi da kwazon karatu yana shiga kansu sosai, amma shi kam sam kansa baya ɗaukar karatu sau tari a magana ma in yaje wani matakin makalewa yake yi. A wasu lokutan yana magana yana kuka abin tausayi. Akwai kwazon maida hankali da tsare litattafai da ido yana karantawa amma duk abinda ya karanto sai dai ya tsaya iya bakinsa baya kaiwa ga kwakwalwarsa balle ta ajiye masa shi duk kuwa da irin ko'karin da yake na ganin ya saka karatun a kansa.
Hakan ba karamin raini ya ja mishi ga sauran kannensa ba kai har ma da waɗansu ya'yan sarakan idan aka haɗu wawa dolo mai ɗanyen kai babu abinda basa ce masa. Matsalarsa ta gawurta tun iyayen na ɗauka laifinsa ne har suka dawo suka saduda suka fauwala al'amuransu ga Allah.
Sai kuma wani iko na Ubangiji da ya yi a kansa, ya kawo tsananin so da burin zamowa MARUBUCI ya saka mishi a rai, a duniya babu abinda yake burge Muhsin kamar rubuta kirkirarren labari. Kamar yadda babu abinda yafi so kamar ya ga kansa a matsayin MARUBUCI. Lokuta da yawa yakan ji kamar yana tsara labari a zuciyarsa amma idan yaje ya zauna da burin son rubutawa sai kwakwalwarsa ta hargitse ta dagula masa komai. Ya dawo kamar wani zautacce baya kula kowa ba kuma ya shiga kowace irin sabga sai dai ka ganshi yayi lamo yana nazari a kullum Muhsin cikin tunani yake a koda yaushe hawayensa zuba suke yi. Ya rasa abinda yasa ya kasance haka.
* * * * * *
Ni kuwa ikon Allah ne ya haɗa ni da Muhsin, da gani ɗaya naji na kamu da tsananin tausayinsa tun yana yaro ɗan kimanin shekaru biyar a duniya. Tun a lokacin na fara shiga rayuwarsa ina son taimakon sa amma matsalar sa ta sha gaban tunani da sani na.
Alakata da Muhsin tayi girman da duk wani ɗan'uwana na kusa da na nesa yasan ina tare da shi kuma ina matukar kaunarsa. Babu yadda iyayena basu yi ba dan ganin sun raba tsakani na da Muhsin amma abin ya gagara, tun suna jin haushi na har suka dawo suka hakura.
* * * * *
Ni jinsin Alajan ce wadda ta fito daga babban gida mai daraja a can tamu nahiyar. Ni kaɗai Allah ya azurta iyayena da haihuwa kuma mahaifina babban Malamin addinin musulunci ne a can, shi yasa dukkan mu muka zamo mabiya addinin.
Babu irin rokon da ban yiwa mahaifiyata da mahaifina ba kan su taimaka in sunada wani taimako ko masaniya akan lalurar da Muhsin ke ɗauke da ita su taimaka su gaya min amma sun ki. Duk kuwa da cewa inada yakini cewa babana Malam ba zai rasa masaniya akan maganin warakar wannan cutar ba.
Wannan kenan.
Cigaban labari...
* * * * *
Dogon numfashi na koma ja a karo na barkatai, ina karewa masoyina Muhsin da bacci ya sace kallo. Baccinsa yake cikin kwanciyar hankali, yana fidda numfashi slowly. Na rufe dara-daran idona na koma buɗe su a kansa. Ga namiji har namiji amma wananan lalurar zata nakasa shi. Wani irin shaukin son sa ne ka kara ninkuwa a raina yana daɗa mamaye duk wata kafa ta sadar da tunanina. Nan da nan na yanke shawarar tafiya na mika ajiyayyun sakonnin soyayyata ta kafar sadarwar da na shirya mana ta haɗuwa da masoyina ba tareda ya san ko ni wacce ba a cikin mafarki. Dama haka na saba a duk lokacin da shaukin kaunarsa ya motsa mini, nakan zama tamkar inuwa na ratsa jikinsa harma da tunaninsa sai ya ganni kamar yana mafarki ta nan muka saba da Muhsin sosai kuma ta nan ne nake sanar mishi irin son da nake masa. Ta wannan hanyar ne nake farantawa Muhsin ina ɗebe masa kewar rayuwar kaɗaicin da yake. Domin daga ni sai mahaifiyarsa gimbiya Suhaima mu kaɗai ne muke shiga rayuwarsa kuma muke ko'karin faranta masa domin mahaifinsa baya da lokaci koda yaushe yana cikin fada yana fama da talakawa da matsalolinsu.
Na lumshe idona cike da shauki sannan na yunkura da nufin aiwatar da nufina, na shiga jikin masoyina domin sada zumuncin kauna. Kamar daga sama naji an yi gaggawar riko kafaɗata ta baya ana faɗin
"dakata Na'eema"
*Nasmat* ✍
[23/1 17:53] Yar Mutan Arkillah: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*MARUBUCI...*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*Soyayyar Mutum da Aljan...* kagaggen labari.
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_____________________________________
Wɛ ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucɑtɛ, Mѳtiѵɑtɛ ɑɳɗ ɛɳtɛʀtɑiɳ ѳuʀ ʀɛɑɗɛʀร.
_____________________________________
©
Yar'mutan
Arkilla✍
____________
📚 Zaku iya samun littafan mu a Facebook 👇🏽
Fb.me/ZAMANIWRITERSASSCIATION
📩 Zaku iya aika mana sako ko korafi, Ta email namu 👇🏽
[email protected]
*Page 2*
*Alhamdulillah ina godiya ga Allah (s.w.a) kuma ina godiya gareku bisa yadda kuka kar6i wannan labarin kuma kuke kara karfafa min guiwa a kan sa. Na gode! Na gode! Masoyana Allah ya bar min ku a duk inda kuke. One love 🤝*
Wannan dakatarwar da aka yi min ba karamin 6ata mini rai tayi ba, na juyo a fusace dan ganin wane ne wannan da yayi min irin wannan katsalandan a cikin rayuwata. "Ummy" na faɗa cike da mamakin ganin mahaifiyata a gabana, wadda ban ta6a tsammanin ta a yanzu kuma a nan ba. Ta zuba min fararen idanunta fuskarta cike da damuwa. Wannan ne ya kara sanyayar mini da ga66an jikina.