← Book details sawun giwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 6

Sashe 6

sawun giwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

A yau kusan kwanan maisoon 12 da dawowa daga saudia kuma suna waya da yaseer jefi jefi kala bata sake mishi harta dawo tana sake mishi, sabida fakewa dayakeyi da hajiyarshi yana samun doguwar magana da ita....daga gefe ɗaya kuma shirye shiryen bikin ƙasarsu maimoun sukeyi sosai domin ansaka amarya lalle kuma yau ne ranar kamu tun safe suna wurin ƙunshi, se yanzu suka fito yamma liss, kowacce anyi mata baƙin zane makyau itada A'isha, gidan suka nufa inda A'isha ke driving maisoon na gefenta. "Sweetheart Inaso zanyi wata magana dake please, cewar A'isha. "Okay inajinki wani abun yafarune? "A'a kawai dai zefarune to Inaso nagaya Miki ne dan kikwanta da shiri. "Okay inajinki minene? "Humm wai kinsan abinda yah fawan yaje yagayawa Abba kuwa? "A'a sekin faɗa minene? "Kedai bari sweetheart wai cewa Abba yayi ai yanasonki keze aura Ni wlh yabani mamaki, shine Abba shikuwa zeje yagayawa Abbey, amma mama tace sam bata yadda ba seya fara neman yardar ki tukkunnah nana ɗauka ma yazo Miki dazancen, taƙarasa zancen tana kallon maisoon da ko ajikinta, bakiji minaceba sweetheart naga babu inda kika damu? "Murmushi maisoon tayi kana tace "to mize damar dani sweetheart nadesan ba yadda za'ayimin auren dole kuma dan yah fawan yace yana sona ba abun mamaki bane domin mazan ayanzu ba kunyace dasuba duk abinda yazo musu arai zasu iyayi sabida Karki wani damu muyi sha'ani kawai. "Ajiyar zuciya A'isha tasauke kana tace "tabbas hakene zancenki sweetheart amma kinsan koda bakiso muddin zancennan yaje gun Abbey wlh se anyi kokin manta waye abbey kuma kinmanta yadda akayi auren anty Zainab ne? Damm gaban maisoon yafaɗi jin kalaman A'isha tabbas maganarta gaskiya ce domin bata manta yadda akayi auren anty zee ba a lokacin ita yah jawwal takeso amma beyi saurin yin maganaba har abokin Abba yazo nemawa ɗan aurenta kuma Abbey yabashi, daga baya dataji tace ita yah jawwal takeso akace sedai tayi haƙuri basataɓa canja magana idan sukayi, tofa hakan anty zee tahaƙura itada yah jawwal bayan sunci kuka har sun gode Allah amma ba wanda ya tausaya musu daga karshe ma dady yasaka yah jawwal yabar ƙasar shiyasa har yanzu beyi aureba, haka akayi auren anty zee kamar takashe kanta...taɓo maisoon A'isha tayi ganin tanata magana tayi shiru domin ita talulu duniyar tunani. "Yadai sweetheart? "Humm ina tuna yadda akayi auren anty zee ne wlh banmanta ba sweetheart shine gabaki ɗaya yarikitani. "To kingani sabida hakan wlh tunwuri idan akwai wanda kikeso kiyi gaggawar kaishi gun Abbey kar ayimiki yadda akayiwa anty zee domin kinganni anan wlh inada wanda Nakeso kawai bazanyi magana bane sabida bansan shi wayakeso ba dudda cewar ina fatar nice domin tabbas idan ban sameshiba wlh zanshiga tashin hankali sweetheart. "Tofa waye wannan yayi Miki mugun kamu hakan sweetheart? Maisoon ta tambaya cikin mamaki..."Humm kinyi mamaki ko? Aibazama kiyi mamaki ba sekinji kowaye? "Please gayaminto wayeshi? Kinsan Bama hakan dake. "Haka ne ai doline zan gaya Miki kodan kitayani addu'ar samunshi. "Okay ina jinki. "Ɗan shiru A'isha tayi kafin tanisa tace *"Yah muhseen* "ƙuttt 😱 yah muhseen dai namu? Maisoon tafaɗa cikin mamaki.."eh shi sweetheart wlh ina mugun son yah muhseen shiyasa alokacinda yace muna yanada yadda yakeso hankalina yatashi amma danaji yace acikinmu take senaji yaɗan kwanta shine naketa addu'ar Allah yasa nice kuma yayi saurin faɗa kar wani yarigashi ayimana katangar ƙarfe domin wlh Allah ina mugun sonshi sweetheart.."tab ɗijam ana wata gawata ashedai yayanmu nada farin jini wlh irin wannan mugunso haka sweetheart Allah yasa kuɗin rabon junane, maisoon tafaɗa cikin farin ciki. (Nikuwa nace tab ɗijam lallai kam shine ake kirada ana wata gawata kokuma nace son maso wani😱 wlh harkinban sausayi A'isha😥) ahakan har suka isa gida suna firarsu.

TALLAH

TALLAH

TALLAH

Mejo najeeb

Labarin isseta yar gidan aljanar ruwa, labari me ban al'ajabi da rikitarwa, gakuma soyayya romantic love story 💋💋💋💋💋💋💋💋💋💓💓💓💓🤭🤭🤭🤭💃💃💃💃💃💃💃💃rikita rikita kenan, dukkansu daga alkalamin taku har kullun mesom farin cikinku wato shaha rarriyar marubuciyar littafin *IZZAR MULKI* labarin daya gigita duniyar ku, AUTAR ALHERI ✍️✍️

Soldier family (labarin mama ƙaramar yarinya me rayuwa acikin aljanu tamkar mutane, wadda daga baya zama koma rayuwa awata ƙasar cikin family me tattare da tantagaryar tsafi da miyagun aljanu, hummm gakuma soyayya da birgewa meban sha'awa romantic love. Soldiers family complete ne game buƙatarshi ze iya tuntubar wannan nomber 👉07037092176.💃

INGARMAM NAMUJI
Labarin suyayya da safna me rayuwa ajeji kamar ba mutunba cikin miyagun haɗurra da kasadar rayuwa, daga gefe kuma tana soyayyar ma'aurata da wani cikakken saurayi jami'in soja a mafalki. Gakuma soyayya yazeed da sumayya abin birgewa, gefe ɗaya kuma da sadeeq da sauratt, suna buga nasu love abin gwanin ban sha'awa..idan kuma koma gefe kuwa ga fitinanniyar kakarsu me abin dariya wato Hajiya nene ikon Allah,,,, gaskiya a wannan family ana buga Ross💃 duk acikin littafin 🐎 INGARMAM NAMIJI 🐎💃 malallakin Autar alheri ✍️.

Humm

My little sister.
Labarin huzda da ahazad yayada ƙanwa uwa ɗaya uba ɗaya amma suna wata irin soyayya meban sha'awa da birgewa daga ƙarshe sun kafema iyayensu akan cewar tabbas su zasu aure juna abinda kuma baze taɓa yuba koya wannan badaƙalar zata kasance🤔🤔🤔 romantic love and 💓💓💓💓 story 💃mallakin Autar alheri ✍️

Misalin ƙarfe 8:30pm suka shirya domin zuwa kamu kamar yadda aka tsara, sunshirya cikin arbian gown pich color tayi musu shegen kyau kamar kasacesu ka gudu, ahakan suka nufi hool ɗin daza'ayi kamun domin kusan sune sukayi na ƙarshe da shiga koda sukaje tuni amarya da angonta na wurin sunacikin fili ana musu liƙi. Suna kunna kai cikin hool ɗin maisoon tafara wata shegiyar rawa me masifar ɗaukar hankali dubada yadda yanayin tsarin jikinta yake se rawar tayi mugun yimata kyau, tanayi tana juya ƙugunta kamar wata tarwaɗa kuma tana dunfaro tsakiyar filin, A'isha nagefe tana mata liƙi tana Murmushi. Ihu kawai wurin ya ɗauka samari se sowa sukeyi ganin yadda albarkatun jikinta ke bada kala Sena fisgar hankalinsu. Wani irin tafi akeyi ana faɗar ga manyan ƙawayena amarya sun isa Big Iadys dan Allah Abasu fili,,,,aiko aka shiga darewa hakan yabawa yaseer damar hango ta alokacinda taƙaraso tsakiyar filin tana yiwa amarya da ango liƙi tana juya ekebe💃wani irin waro ido yayi ganin yadda wani guy keyiwa boom boom ɗinta liƙi batamasaniba. Hakan yasa yataso cikin hanzari yayowurin, jikawai maisoon tayi antsaya bayanta ana zuba mata nera..domin yana zuwa ture guy ɗin kawai yayi yashiga yimata liƙin..ahasale tajiyo domin saukewa koma waye ruwan Bala'i setayi ido huɗu da yaseer yana sakar mata Murmushi... murmushin itama tamaida mishi kana tashiga yimishi liƙin shima sesuka koma su biyu ke rawar suna yiwa junansu liƙi kuma amarya da angonta namusu hakama A'isha da yayyen amaryar, se suka bada kala sosai awurin....yah fawan nacan cikin wasu abokananshi domin yayan angonne abokinshi shiyasa yazo bikin, yana zaune yaji ana faɗar wlh gawata beb can tahaɗu iya haɗuwa domin akwai kayan hutawa ajikinta gayacan se juyasu takeyi cikin salo me ɗaukar hankali..ai besan lokacinda yamiƙe ba domin yazo yaga ko zegwada sa'arshi anan yaɗan huta yau kasan cewar shi mayen mata, sedai yana zuwa wurin yayi fruss ganin maisoon ce gaya se cashewa sukeyi itada yaseer cikin farin ciki duk idanun mutane na kansu,,,wani irin malolo yaji yataso mishi cikin baƙar zuciya yakutsakai cikin filin tareda finciko hannunta kawai yayi waje da ita...amugun ahasale itama tajiyo cikin tsiwa tace

"Wai wanne ɗan renin hankalin ne? akan me zaka riƙoni hakan sekace wata ƴarka..shiri tayi ganin fawan agabanta yana huci, "yah fawan dama kaine? Lafiya kuwa? Tatambeshi cikin mamaki. Wani banzan kallo yatsa mata kana yaja hannunta se cikin motarshi yajefata aciki kana yafigi motar da azabar gudu yabar wurin..wani mugun murmushi yaseer yayi kana yace koma waye kai kagama tsallenka maisoon tawace nikaɗai...!

Tofa 🤔 ko ina fawan zekai maisoon?

Shin ya soyayyar da A'isha keyiwa yah muhseen zata kasance? Ina mokomar yah muhseen da Maisoon ɗinshi? Shin minene nufin yaseer nacewa maisoon tashice?

Yazata kaya tsakanin gimbiya saudat kursum dakuma Sheikh sudais?

Shin miyasa Sheikh sudais ke yawan mafalkin yana love da Maisoon?

Acikin wa'yannan zaratan samarin shin waye gwanin maisoon?? Wace badaƙala za'ataka agaba? Hummm domin jin ansoshin duka wannan tambayoyin kubiyini a SAWUN GIWA book 2 domin ganin yadda zata kaya. Domin ba'ayi Komaiba tukunnah yanzune wasan zefara💃💃💃💃💃💃💃💃💃

Game bukatar biyan kuɗinta nera dubu ɗaya ne zaki ita tura kuɗinki a wannan account ɗin 👉 2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA Bank kana kitura shaidar biyanki awannan nomber 👉 07037092176. 🙏

Autar alheri ✍️
Chapter 6 · 0% Book details