Sashe 5
Laifin Waye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_AISHA YAHYA TANKO✍️_
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO*
_KASHI NA BIYU_
*PAGE 14*
A can gida kuwa Dr Zahra ce ta gama ƙulluwa ganin irin kiran da takewa Dr Nasir amma baya ɗagawa ta kwanta akan doguwar kujera ta yanke shawarar idan har yana ganin kiranta be daga ba kuma be biyo kiran ba tasan me za tai masa saboda ya fahimci abinda take nufi yake shareta be san ita wace ba, shi yasa yake mata haka ta miƙe tsaye ta nufin toilet tayo alwala ta zo ta gabatar da sallah tare da yin addu'ar neman nasara akan Dr Nasir tashi wayarta tai ƙara da sauri ta ɗauki wayar ba tare da ta duba sunan ba muryar ƙawar Humaira taji akan wayar cikin karfin hali take bata amsa.
"Haba Dr ina kika shiga ne kwana biyu gashi kuma yanzu naji muryar ki kamar baki da lafiya gaskiya akwai matsala.
Wata irin dariya ta ƙaƙaro me ɗauke da sigar damuwa.
"Wallahi Humaira kawai gajiya ce kinsan aikin namu sai a hankali fa, kedai Allah yasa mu dace".
a haka sukai sallama ta ajiye wayar tana bin ta da kallo.
A can office kuwa Dr ne zaune shi da Umar suna ci gaba da tattaunawa akan ciwon Hauwa'u Umar yace.
"Naga tun ɗazu anata waya baka dagawa gwanda ka daga kaji ko lafiya".
Ya dube shi yana murmushi yace.
"Ba ruwanka da ko kira nawa za ai min ni dai fatana ka sanar dani tambayar dana ke ma akan Hauwa'u shin kana ganin zaman ku da ita ya ƙare ko zaka ƙara zama da ita idan taji sauƙi sosai ko yaya?".
Yana maganar ne cikin tsare shi da ido daya yi.
"A gaskiya ina mutukar ƙaunar ta amma bana jin da sauran zaman mu a gaba na gama yanke shawarar tana samun sauki zan sawaƙe mata amma ba'a san raina ba kawai ina ganin hakan shine zaman lafiyar mu".
Inji Umar.
Wata ajiyar zuciya yayi Dr Nasir yayi yace.
"To shikenan Allah yasa hakane ya fi zama alkairi baki ɗaya ina ga tun da mun gama ni zan tafi gida sai kuma gobe in sha Allah nagode bisa haɗin kan daka bani yanzu mun gane _LAIFIN WAYE_.
"Nawa ne ina fatan nan gaba zan ƙara irin wannan kuskuren da a baya ba".
inji Umar.
Suka Miƙe a tare suka fice daga office ɗin Dr Nasir yana gaba Umar yana biye dashi Dr ya nufin wajen ajiye motoci ya fara ƙoƙarin buɗe tasa kenan wayarsa tai ƙara hannu yasa ya ɗauka ya dubi sunan Dr Zahra yayi murmushi sannan ya ƙara a kunnesa yayi sallama cikin natsuwa yace.
"Kiyi haƙuri Dr Zahra inata ganin kiranki amma ba damar ɗagawa na saboda wani dalili yanzu kin ganni sai yanzu nake shiga mota ina ƙarasawa gida zaki ji kirana nagode sai kin jini".
ya kashe wayar yana dariya yace Dr Zahra rigima yana shiga motar ya tayar ya nufi get ɗin fita waje.
Sallama Umar yayi acikin ɗakin jinya ya kalli inda Baba Sa'a take zaune yace.
"Sannu Baba ya jikin nata naga kamar ta koma baccin koh naje na fayyace wa Dr komai game da halin da Hauwa'u take ciki kuma nasan LAIFI NA NE yai min nasihohi waɗanda suka shiga jikina daga ƙarshe na yanke shawara akan Hauwa'u idan Allah ya bata lafiya".
Inji Umar.
"Ɗan nan wacce irin shawarace Allah ya sa ta saki ce,dan ni a yanzu shine burina zan bata dama ta zaɓi irin mijin data ke so ba san raina ba".
Inji Baba Sa'a.
"Hakane dama kuskure ne kuma anyi shi da kuma ƙaddara saboda kowa na duniya akwai irin tasa".
Inji Umar.
Dama gida zan koma idan ta tashi kice ina dubata kafin na dawo gobe.
✍️
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO.*
*PAGE 15*
Wata irin harara ta zuba masa me ɗauke da tuhuma tace.
"A'a kai zamanka ba sai ka dawo ba mun yafe".
haka ya fice daga ɗakin cikin sanyin jiki.
Iskar sa ke da wuya cikin gidan ya buɗe ɗakin ya cikin gajiya wa ya kwanta akan doguwar kujerar dake falon ya zare glas ɗin dake manne a fuskarsa ya lumshe ido yana tunanin abubuwan da suka wakana tsakanin sa da Umar daya tuno Umar yace.
_zai sawaƙewa Hauwa'u yaji wani irin daɗi_ sannan ya mike tsaye ya nufi firij inda ya zaro ruwa me sanyi ya buɗe ya fara sha kenan wayarsa tai ƙara sai da ya gama shan ruwan ya dawo inda wayar take ajiye sunan Dr Zahra ya gani akan fuskar wayar yasa hannu ya ɗaga yace.
"Sannu Dr ya kike yanzu nake shirin cewa sai na gama abinda nake zan kiraki ban jima da shigowa gidan ba ki dan kara haƙuri nan da lokaci kaɗan zan kiraki kinji ya kashe wayar yana ƙoƙarin sake kwanciya saboda irin gajiyar da yai cikin lokaci ƙalilan bacci yai awon gaba dashi be farka ba sai wajen 2: 00 na dare.
Washe gari kuwa haka Dr ya tashi cikin ƙarfin hali yake shirya wa saboda gajiyar data gallabeshi ya gama shirya wa tsaf ya nufo wajen motarsa ya shiga ya tayar tafiya yake a hankali kamar ba'a kan titi yake ba har ya ƙaraso asibitin ya wuce office ɗinshi.
A can ɗakin da Hauwa'u take kwance kuwa Baba Sa'a ce tana zaune a ƙasan gado tana jan carbi taji motsin Hauwa'u ta Baba Sa'a ta dubi inda take tace har kin farka ne sannu.
Daga kai tai alamar Eh tai mata nuni data gyara mata kwanciyar Baba Sa'a ta tashi cikin sauri tana kicikici taji shigowar Dr Zahra.
"Ki dai gyara mata a hankali karfi fama mata ciwonta".
*AISHA YAHYA TANKO*
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO*
*PAGE 16*
Ta gyara mata kwanciya ta koma ta zauna tana sauraron abinda Dr Zahra zata ce game da Hauwa'u
Ta gama yan dube_dubenta ta dubi Baba Sa'a tace.
"Masha Allah jikin Hauwa'u yayi kyau sosai muna sa rai nan da lokaci kaɗan zamu sallameku".
inji Dr Zahra.
Wata irin dariya Baba Sa'a tai tare da yiwa Allah godiya tace.
"A gaskiya naji daɗi sosai burina ya cika kuma Allah ya saka muku da Alkairi yasa ku gama aikinku lafiya nagode sosai".
Dr Zahra ta fice daga ɗakin tana murmushi
Baba Sa'a ta kalli Hauwa'u tace sannu Yarinyar kirki.
Acan office kuwa Dr Nasir ne yake duba files din dake gabansa yaji shigowar Dr Zahra ya kada da abinda yake yi yace.
"Barka da zuwa Dr ashe har kin shigo".
ya umarce ta data zauna.
Taja ta zauna a kujerar data ke dab dashi tana murmushi tace.
"Ai na jima da shigowa har naje na duba Hauwa'u kuma naga wajen ya fara kamewa masan nan da lokaci ƙalilan zata iya dawo normal kaga daga nan ma iya sallamarsu su koma gida taci gaba da shiga ruwan zafi".
"Ƙwarai kuwa dama ranar da muke jira tazo kenan ɗazu naje can dakin naga wata me shigen matsalar ta itama inaso muje tare muga ta ina zamu fara da ita".
Inji Dr Nasir.
Dr Zahra tace to ba damuwa Allah ya bamu ikon sauke nauyin da yake kanmu,jiya bayan na barka a nan naga kayi busy daka koma gida ma haka.
"Wallahi kinsan aikin namu ne sai a hankali Allah dai ya shiga lamarin".
Bayan sun gama tattaunawa ne suka fara ƙoƙarin zuwa duba mara lafiyar.
Acan ɗakin kuwa tuni farin ciki ya baibaye Hauwa'u lokacin data ji Baba Sa'a ta sanar da ita abinda Dr Zahra tace game da ita har ta sami karfin gwiwar cin abinci sosai tana magana.
Suka ji shigowar Umar hannunsa riƙe da ledoji ya ajiye su kusa Da Baba Sa'a yana gaisheta Hauwa'u tuni ta haɗe rai kamar me shirin kuka yace.
"Dan Allah ki saki ranki Hauwa'u ƙaddara ce ta riga ta faru Allah dai ya kiyaye gaba".
Baba Sa'a tace hakane abu dai ya faru ni dai fatana ranar da muka fita daga Asibiti ka bata takardar saki shine abinda nake nema awajenka.
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO*
*PAGE 17*
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah Hauwa'u dai ta sami sauƙi har an salamesu daga Asibiti sun dawo gida
Tun ranar da Dr Nasir ya buɗe yaga ba Hauwa'u a cikin asibiti komai ya dagule masa ya rasa inda zai sa kansa Dr Zahra ta rasa gane inda ya dosa har ta fara sawa zuciyarta haƙuri amma ba dan san ranta ba.
Wata rana Hauwa'u tana zaune a tsakar gida kan tabarma tayi jigum tana tunanin rayuwarta a asibiti ne taji maganar BaBa Sa'a tana cewa.
"ke kuwa Hauwa'u me kikeyi ne haka tun ɗazu na barki anan amma ba abinda kikai sai zaman tunani bayan kuma yanzu ba abinda ya rage miki sai fatan Allah ya kawo miki miji na ba irin Umar ba nazo miki da wani babban albishir amma sai kin min alkawari zaki dena wannan tunanin".
Nan da nan Hauwa'u ta ɗago kai tana dariya ta nuna alamar zaƙuwar taji ko menene.
Baba Sa'a ta zauna kusa da ita tace.
"Umar dai ya sake ki".
Wata irin ƙara da murna Hauwa'u tayi tace.
"Dama wannnan ranar nake jira Baba Allah na gode ma daka bani lafiya ka kuma rabani da mutumin da yake kamar bakin maciji gareni ganinsa ya zame mun masifa".
Kafin su ƙarasa magana suka ji sallama gaba ɗaya suka bi kofar da kallo cikin mamaki suka miƙe a tare Dr Nasir kaine agidan namu .Baba Sa'a sannu da zuwa nabban bako nasan wannan zuwan na Hauwa'u ne ƙaraso mana nan ma gidan ku ne.
Hauwa'u ta kasa cewa komai ta kalli wannan ta kalli wannan shine kawai abinda take yi .
Dr Nasir ya zauna bakinsa ya ƙi rufuwa ganin irin karɓar da akai masa.
Baba Sa'a ta koma daki ta kirawo Malam suka gaisa.
Ta bar Hauwa'u da Dr Nasir zaune a tsakar gida.
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO*
_KASHI NA BIYU_
*PAGE 14*
A can gida kuwa Dr Zahra ce ta gama ƙulluwa ganin irin kiran da takewa Dr Nasir amma baya ɗagawa ta kwanta akan doguwar kujera ta yanke shawarar idan har yana ganin kiranta be daga ba kuma be biyo kiran ba tasan me za tai masa saboda ya fahimci abinda take nufi yake shareta be san ita wace ba, shi yasa yake mata haka ta miƙe tsaye ta nufin toilet tayo alwala ta zo ta gabatar da sallah tare da yin addu'ar neman nasara akan Dr Nasir tashi wayarta tai ƙara da sauri ta ɗauki wayar ba tare da ta duba sunan ba muryar ƙawar Humaira taji akan wayar cikin karfin hali take bata amsa.
"Haba Dr ina kika shiga ne kwana biyu gashi kuma yanzu naji muryar ki kamar baki da lafiya gaskiya akwai matsala.
Wata irin dariya ta ƙaƙaro me ɗauke da sigar damuwa.
"Wallahi Humaira kawai gajiya ce kinsan aikin namu sai a hankali fa, kedai Allah yasa mu dace".
a haka sukai sallama ta ajiye wayar tana bin ta da kallo.
A can office kuwa Dr ne zaune shi da Umar suna ci gaba da tattaunawa akan ciwon Hauwa'u Umar yace.
"Naga tun ɗazu anata waya baka dagawa gwanda ka daga kaji ko lafiya".
Ya dube shi yana murmushi yace.
"Ba ruwanka da ko kira nawa za ai min ni dai fatana ka sanar dani tambayar dana ke ma akan Hauwa'u shin kana ganin zaman ku da ita ya ƙare ko zaka ƙara zama da ita idan taji sauƙi sosai ko yaya?".
Yana maganar ne cikin tsare shi da ido daya yi.
"A gaskiya ina mutukar ƙaunar ta amma bana jin da sauran zaman mu a gaba na gama yanke shawarar tana samun sauki zan sawaƙe mata amma ba'a san raina ba kawai ina ganin hakan shine zaman lafiyar mu".
Inji Umar.
Wata ajiyar zuciya yayi Dr Nasir yayi yace.
"To shikenan Allah yasa hakane ya fi zama alkairi baki ɗaya ina ga tun da mun gama ni zan tafi gida sai kuma gobe in sha Allah nagode bisa haɗin kan daka bani yanzu mun gane _LAIFIN WAYE_.
"Nawa ne ina fatan nan gaba zan ƙara irin wannan kuskuren da a baya ba".
inji Umar.
Suka Miƙe a tare suka fice daga office ɗin Dr Nasir yana gaba Umar yana biye dashi Dr ya nufin wajen ajiye motoci ya fara ƙoƙarin buɗe tasa kenan wayarsa tai ƙara hannu yasa ya ɗauka ya dubi sunan Dr Zahra yayi murmushi sannan ya ƙara a kunnesa yayi sallama cikin natsuwa yace.
"Kiyi haƙuri Dr Zahra inata ganin kiranki amma ba damar ɗagawa na saboda wani dalili yanzu kin ganni sai yanzu nake shiga mota ina ƙarasawa gida zaki ji kirana nagode sai kin jini".
ya kashe wayar yana dariya yace Dr Zahra rigima yana shiga motar ya tayar ya nufi get ɗin fita waje.
Sallama Umar yayi acikin ɗakin jinya ya kalli inda Baba Sa'a take zaune yace.
"Sannu Baba ya jikin nata naga kamar ta koma baccin koh naje na fayyace wa Dr komai game da halin da Hauwa'u take ciki kuma nasan LAIFI NA NE yai min nasihohi waɗanda suka shiga jikina daga ƙarshe na yanke shawara akan Hauwa'u idan Allah ya bata lafiya".
Inji Umar.
"Ɗan nan wacce irin shawarace Allah ya sa ta saki ce,dan ni a yanzu shine burina zan bata dama ta zaɓi irin mijin data ke so ba san raina ba".
Inji Baba Sa'a.
"Hakane dama kuskure ne kuma anyi shi da kuma ƙaddara saboda kowa na duniya akwai irin tasa".
Inji Umar.
Dama gida zan koma idan ta tashi kice ina dubata kafin na dawo gobe.
✍️
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO.*
*PAGE 15*
Wata irin harara ta zuba masa me ɗauke da tuhuma tace.
"A'a kai zamanka ba sai ka dawo ba mun yafe".
haka ya fice daga ɗakin cikin sanyin jiki.
Iskar sa ke da wuya cikin gidan ya buɗe ɗakin ya cikin gajiya wa ya kwanta akan doguwar kujerar dake falon ya zare glas ɗin dake manne a fuskarsa ya lumshe ido yana tunanin abubuwan da suka wakana tsakanin sa da Umar daya tuno Umar yace.
_zai sawaƙewa Hauwa'u yaji wani irin daɗi_ sannan ya mike tsaye ya nufi firij inda ya zaro ruwa me sanyi ya buɗe ya fara sha kenan wayarsa tai ƙara sai da ya gama shan ruwan ya dawo inda wayar take ajiye sunan Dr Zahra ya gani akan fuskar wayar yasa hannu ya ɗaga yace.
"Sannu Dr ya kike yanzu nake shirin cewa sai na gama abinda nake zan kiraki ban jima da shigowa gidan ba ki dan kara haƙuri nan da lokaci kaɗan zan kiraki kinji ya kashe wayar yana ƙoƙarin sake kwanciya saboda irin gajiyar da yai cikin lokaci ƙalilan bacci yai awon gaba dashi be farka ba sai wajen 2: 00 na dare.
Washe gari kuwa haka Dr ya tashi cikin ƙarfin hali yake shirya wa saboda gajiyar data gallabeshi ya gama shirya wa tsaf ya nufo wajen motarsa ya shiga ya tayar tafiya yake a hankali kamar ba'a kan titi yake ba har ya ƙaraso asibitin ya wuce office ɗinshi.
A can ɗakin da Hauwa'u take kwance kuwa Baba Sa'a ce tana zaune a ƙasan gado tana jan carbi taji motsin Hauwa'u ta Baba Sa'a ta dubi inda take tace har kin farka ne sannu.
Daga kai tai alamar Eh tai mata nuni data gyara mata kwanciyar Baba Sa'a ta tashi cikin sauri tana kicikici taji shigowar Dr Zahra.
"Ki dai gyara mata a hankali karfi fama mata ciwonta".
*AISHA YAHYA TANKO*
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO*
*PAGE 16*
Ta gyara mata kwanciya ta koma ta zauna tana sauraron abinda Dr Zahra zata ce game da Hauwa'u
Ta gama yan dube_dubenta ta dubi Baba Sa'a tace.
"Masha Allah jikin Hauwa'u yayi kyau sosai muna sa rai nan da lokaci kaɗan zamu sallameku".
inji Dr Zahra.
Wata irin dariya Baba Sa'a tai tare da yiwa Allah godiya tace.
"A gaskiya naji daɗi sosai burina ya cika kuma Allah ya saka muku da Alkairi yasa ku gama aikinku lafiya nagode sosai".
Dr Zahra ta fice daga ɗakin tana murmushi
Baba Sa'a ta kalli Hauwa'u tace sannu Yarinyar kirki.
Acan office kuwa Dr Nasir ne yake duba files din dake gabansa yaji shigowar Dr Zahra ya kada da abinda yake yi yace.
"Barka da zuwa Dr ashe har kin shigo".
ya umarce ta data zauna.
Taja ta zauna a kujerar data ke dab dashi tana murmushi tace.
"Ai na jima da shigowa har naje na duba Hauwa'u kuma naga wajen ya fara kamewa masan nan da lokaci ƙalilan zata iya dawo normal kaga daga nan ma iya sallamarsu su koma gida taci gaba da shiga ruwan zafi".
"Ƙwarai kuwa dama ranar da muke jira tazo kenan ɗazu naje can dakin naga wata me shigen matsalar ta itama inaso muje tare muga ta ina zamu fara da ita".
Inji Dr Nasir.
Dr Zahra tace to ba damuwa Allah ya bamu ikon sauke nauyin da yake kanmu,jiya bayan na barka a nan naga kayi busy daka koma gida ma haka.
"Wallahi kinsan aikin namu ne sai a hankali Allah dai ya shiga lamarin".
Bayan sun gama tattaunawa ne suka fara ƙoƙarin zuwa duba mara lafiyar.
Acan ɗakin kuwa tuni farin ciki ya baibaye Hauwa'u lokacin data ji Baba Sa'a ta sanar da ita abinda Dr Zahra tace game da ita har ta sami karfin gwiwar cin abinci sosai tana magana.
Suka ji shigowar Umar hannunsa riƙe da ledoji ya ajiye su kusa Da Baba Sa'a yana gaisheta Hauwa'u tuni ta haɗe rai kamar me shirin kuka yace.
"Dan Allah ki saki ranki Hauwa'u ƙaddara ce ta riga ta faru Allah dai ya kiyaye gaba".
Baba Sa'a tace hakane abu dai ya faru ni dai fatana ranar da muka fita daga Asibiti ka bata takardar saki shine abinda nake nema awajenka.
*LAIFIN WAYE*
*© AMAZING WRITER'S ASSOCIATION✍🏽*
*BY AISHA YAHAYA TANKO*
*PAGE 17*
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah Hauwa'u dai ta sami sauƙi har an salamesu daga Asibiti sun dawo gida
Tun ranar da Dr Nasir ya buɗe yaga ba Hauwa'u a cikin asibiti komai ya dagule masa ya rasa inda zai sa kansa Dr Zahra ta rasa gane inda ya dosa har ta fara sawa zuciyarta haƙuri amma ba dan san ranta ba.
Wata rana Hauwa'u tana zaune a tsakar gida kan tabarma tayi jigum tana tunanin rayuwarta a asibiti ne taji maganar BaBa Sa'a tana cewa.
"ke kuwa Hauwa'u me kikeyi ne haka tun ɗazu na barki anan amma ba abinda kikai sai zaman tunani bayan kuma yanzu ba abinda ya rage miki sai fatan Allah ya kawo miki miji na ba irin Umar ba nazo miki da wani babban albishir amma sai kin min alkawari zaki dena wannan tunanin".
Nan da nan Hauwa'u ta ɗago kai tana dariya ta nuna alamar zaƙuwar taji ko menene.
Baba Sa'a ta zauna kusa da ita tace.
"Umar dai ya sake ki".
Wata irin ƙara da murna Hauwa'u tayi tace.
"Dama wannnan ranar nake jira Baba Allah na gode ma daka bani lafiya ka kuma rabani da mutumin da yake kamar bakin maciji gareni ganinsa ya zame mun masifa".
Kafin su ƙarasa magana suka ji sallama gaba ɗaya suka bi kofar da kallo cikin mamaki suka miƙe a tare Dr Nasir kaine agidan namu .Baba Sa'a sannu da zuwa nabban bako nasan wannan zuwan na Hauwa'u ne ƙaraso mana nan ma gidan ku ne.
Hauwa'u ta kasa cewa komai ta kalli wannan ta kalli wannan shine kawai abinda take yi .
Dr Nasir ya zauna bakinsa ya ƙi rufuwa ganin irin karɓar da akai masa.
Baba Sa'a ta koma daki ta kirawo Malam suka gaisa.
Ta bar Hauwa'u da Dr Nasir zaune a tsakar gida.