Chapter 73
Kufan Wuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 60 min read
Shafi na saba'in da biyu
72
. Awa daya da wasu 'yan tsirarin mintuna suka sauka a garin lagos din,sun sauka cikin yanayi na lullumi harda ma tsarabar yayyafi,tunda suka sauka har zuwa cikin motar hannayensu na sarqafe da juna,tana cikin jikin lamin din wanda hakan yake sake kunnashi,a hakan ya dinga nuna mata wurare,sun wurwuce unguwanni da dama,duk inda suka wuce din kuma sai yayi mata bayanin wajen,ta bude idanu kuwa tana kallon bigiren da bata sanshi ba,xuciyarta cike da mamakin yadda lamin din yasan Lagos har haka.
A hankali suka fada wata unguwa,unguwace mai kyau dai dai gwargwado da kuma tsari,babu cinkoso babu kuma yawaitar jama'a,gidajenta moderate ne masu ban sha'awa,hakanan birji ne a tsakiyar layin,har suka qarasa qofar wani dan madaidaicin plate house mai dauke da qaramin gate.
Lamin dinne ya fara fita ya bude qofar gidan da maqullin da drivern ya bashi,sannan ya dawo ya bude mata murfin motar ta fito,yana riqe da hannun nata dai ya tura qofar gidan suka shige.
'yar madaidaiciyar haraba zaka fara tararwa wadda bata wuce shan iska ba,don ta yiwa mota kadan,saidai qawace take da shuke shuke da kuma marble tiles masu kyau da daukan idanu,da gani kasan baa jima da kammala ginin gidan ba,qaramin balcony ke kallonka,wanda a ciki qofar parlor ne,kana buda qofar falon zaka samu madaidaicin falo da akayi masifar qawatashi kamar ba gobe,a cikinsa akwai qofar kitchen,dining area mai dauke da dining mai kujeru hudu,sai bedrooms guda biyu.
"Zauna ina zuwa" ya fada yana juyawa zuwa waje,a nutse iman ta zauna saman kujerun falon masu azabar kyau,tana sake kallon gidan,ya burgeta qwarai da gaske,komai nashi bai cika yawa ba kamar yadda baiyi qaranci ba.
Tana nan zaune ya shigo da jakarsu,sannan ya duba agogo
"Akwai sauran lokaci,me ya kamata yanzu muyi?,gidan babu komai a cikinsa,zanje na samar mana kayan amfani" rau rau tayi da idanunta,sabida jin cewa zai fita ya barta a baqon wajen dako minti goma cikakke batayi a cikinsa ba,takowa yayi gabanta
"Karki damu, you are safe,zan rufeki ta waje,idan na dawo zan bude da kaina,ga bedrooms nan ki zaba wanda nayi miki" ya sunkuya a tausashe yayi kissing forehead dinta,ya danyi waving mata hannyensa sannan ya fita,ta rakashi da addu'a yana amsa mata.
Duk da atsorace take amma sai dafa dudduba kitchen da dakunan,komai lafiya lau kamar dama can ansan da zuwansu,sai kawai ta janyo jakankuna biyun daya shigo dasu ta bude,ta fara fidda musu kayansu tana jerawa a daya daga cikin bedroom din data zaba,bayan ta gama jera nata a dayan shima ta fara shirya masa nashi a daya dakin,duk kayansa da zata daga sai wani qamshi ya ziyarci hancinta,kamar dama ca kayan da turare aka qirqiresu.
Awa daya da rabi aikin ya dauketa,tana fitowa daga bedroom din yana buda qofar falon,idanunshi a kanta,sai yayi mata nuni data koma ciki,shi da wani yaro ne,tana jinsu suna shiga da kayan store har suka gama ya sallameshi sannan ya cimmata a daki,tana tsaye bakin window tana kallon kyakkyawar harabar gidan.
Ta baya ya rungumota yana axa fuskarsa saman kafadarta,sannan ya zagayo da hannayensa saman shafaffen cikinta yayi mata qawanya
"Ina fata gidan yayi miki?" Kai ta gyada a kunyace
"Anan nake fata zamu axa harsashin tubalin ginin kyakkyawar rayuwar auratayya mai inganci....kin shirya?" Kan ta sake gyada masa murmushi yana kubce mata
"Good" ya fada cikin jin dadi da kuma wani irin shauqi
"Muje ki duba kayan kiga abinda babu a ciki" tana duba kayan tana mamakin yadda yasan kayan amfanin gida haka,kusan shi ya dinga jera kayan a duk inda suka dace,ita din 'yar tayi kawai ta zama,a hakan ma dai a takure take,yana sane sai ya taba wani wajen ko wani sashen daga gareta,amma sai ya narke ya hade hannayensa waje daya yace
"Am sorry" wani abun ta rasa me zatayi,wani kuma kunya ta daureta gaba daya,har suka gama,zuwa sannan lokacin sallar magariba ya shiga,ya buqaci taje tayi wanka tazo suyi sallah.
Ruwa me zafi ta hada saboda yadda takejin dan sanyi sanyi a garin saboda yayyafin da aketa yi tun zuwansu,taji dadin dumin ruwan hakan yasa ta jima a bandakin ba tare da ta ankara ba,ta hade da alwala sannan ta fito.
ta dauki minti kusan hudu tana goge lemar jikinta,sannan ta daga kanta da nufin qarasawa bakin madubi ta samu mai ta shafawa jikinta,saidai wanda ta gani zaune saman madubin harde da hannayensa ya zuba mata idanu yayi matuqar razanata.
Lameen ne,yayi bala'in kyau cikin wani lallausan yadi gray color kamar ba dare ba,baqar hula ce a kansa,kamar yadda qafarsa ke sanye da baqaqen takalma mai budadden sama,fadin irin kyan da yayi ma bata bakine,sexy eyes dinsa a bude tarwai a kanta,da hanzari ta soma komawa da baya da nufin komawa toilet,saidai ina,yana saukowa daga saman madubin,taku uku ya cimmata,batasan ta kaucewa qofar toilet din ba sai data ji ta dunguri bango,cak ta tsaya,ya riga ya cimmata,duk da cewa akwai yar tazara a tsakaninsu amma bata da shaawar motsawa,saboda yadda idanunsa ke yawo a jikinta tun daga sama zuwa qasa,ta tabbatar ko yaya ta motsa akwai matsala,ta gwammaci ci gaba da tsaiwa a haka.
Ci gaba yayi da sauke idanunsa kowanne sashe na jikinsa da idanunsa zasu iya kaiwa,karo na farko tsahon rayuwarsu daya taba ganinta cikin yanayi makamancin haka,kasala ta soma saukar masa tare da wani irin shauqi dake fusgarsa,shuqin da bai taba jin makamancinsa ba,gefe guda kuma yana karantar irin rudewar da tayi,abun sai ya bashi wani nau'i na nishadi sa dariya,baisan me yasa taji tsoron ganinsa ba,yanason sake ganin tsoronta irin haka muraran,ko zamanin quruciya idan iman din ta rude fuskarta kan masa kyau qwarai,don haka ya qara kusancin dake tsakaninsu,har sai daya zamana babu wani sauran space ko na taku daya daya rage a tsakaninsu.
A hankali ya sanya hannunsa saman towel din dake tattare a qirjinta, intentionally yayi hakan da niyyar tunzura tsoronta,amma sai yaji ashe abun ya girmimi tunaninsa,cikin rashin sani ya shafi qirjinta,abinda yasa ta sake razana,ta kama towel din ta riqe tam,tanason ta kalleshi ta roqeshi ya bari amma ta kasa,akwai girma a faruwar lamari irin wannan,ya lameen da take matuqar girmamawa da yi masa kallon yaya a wajenta,koda bassam ba zata iya tuna rana daya data taba bayyana tsiraicinta a gabansa ba,yo inama ta ganshi?.
Sulalewa ta samu tayi,tana kaiwa qasa saita cure waje daya,a boye ya saki murmushi,ya taka da baya ya dauko.kayan da yaga ta ajjiye saman gadon,da alama su zata saka ya ajjiye mata a gabanta,dai dai lokacin da akayi knocking qofar falo,sai ya juya zuwa bakin qofar yana cewa
"Ki saka kayanki" ya buda qofar ya fita,abinda ya bata damar miqewa da hanzari ta koma toilet zuciyarta na bugawa,komai zai fara tsakaninta da ya lameen daga tsammanin mafarki zuwa gaskiya,tana ji a jikinta tabbas zuwa yanzu komai gaske ne,ya kuma gama tabbata.
Da takeaway ya dawo a hannunsa na abinci idonsa na dubanta kamar zata bace masa
"You look so cute my queen" ya fada ta hanyar motsa labbansa kawai,hakan ya sanya furucin ya fita a hankali. Bandaki ya shiga ya sabunta alwalarsa ya dawo sukayi sallah,sannan ya gabatar musu da abincin sukaci a mazubi daya kamar yadda ya sabar musu.
"Ayimin afuwa,fitace ta kamani,akwai saqo da zan karba,banajin zan fita har nan da one week,shi yasa dole a daren nan na fita na karba saqon,sako hijabinki ki rakani,i promise you ba zamu dade ba" itakam dadin hakan taji,sai ta koma ciki,ta laluba kayanta ta samu hijab,ta zura hade da plate takalmi ta fito.
Tunda ta fara takowa ya zuba mata idanu,hannunsa zube a aljihunsa yana qare mata kallo,komai ta saka kyau yake mata,komai ta raba da jikinta sai ya haska ta,ya Allah......" Ya fadi yana lumshe idanunsa,kana ya bude mata qirjinsa ta hanyar wara hannayensa yayi welcoming nata kafin su wuce tana rabe da kafadarsa.
A qofar gidan suka samu mota yana jiransu suka shiga seat din baya ita dashi manne da juna,ko yanzun ma bayani tare da nunnuna mata gurare yaketayi,lallai lagos babban garine da aka ci gaba,har suka je suka dawo,duk da a mota ya barta ya karba saqon amma taji dadin fitar.
Koda suka dawo din shirin barci kawai sukayi,dakin ya dauki wani duhu mai cakude da dim light mai kyau,yadda gidan da garin ya dauki shuru haka dakin,tana a cikin jikinsa idanunsa a lumshe,yanata qoqarin danne zuciyarsa saboda ya bata damar hutawa a daren yau,yana jin dumin numfashinta cikin jikinsa ya gyara mata kwanciya sosai,da qyar ya samu bacci ya daukeshi.
************Washegari garin a lullube da hadari suka tashi,weather din da ya haifar da wani yanayi me dadi a jiki da zuciya,yanayin kuma ya dace da sabbin masoya irinsu.
Tun daga safiyar ya fara bude mata aiki,muraran ya fara bayyana mata waye lameen da irin rayuwar da yake sha'awar yi da iyalinsa,tare suka hada breakfast,suka gyara wajen,wajen wanka ta shige toilet kafin ta gama rufewa ya mamayeta,zatayi magana sai tsintar kanta tayi male male cikin bathtub,bata gama wannan alhinin ba yasa hannu guda ya zare towel din da yayi saura a jikinta,ta qanqame waje daya,sai yayi relax cikin ruwan yana qarewa fuskarta kallo,jikinsa ya saki gaba daya,zuciyarsa na gaya masa ya aikata kawai,daren da yake tunani bazai iya kaiwa ba,saidai akwai sauran abubuwa da yakeso ta fuskanta daga wajensa kafin sannan,idanunsa suka sauka ga duk wata siffa da baiwa ta jikinta da Allah yayi mata ta cikin ruwan da yake garai garai,tsigar jikinsa ta zuba,yaji kamar numfashinsa zai wuce,cikin ransa gana dayanta Allah da idanuwansa basu taba kaiwa ga jikin wata 'ya mace kamar haka ba,sai a yau daya samu halalinsa
"Imaaaannnn" ya ambaci sunanta da wata murya me nauyi,a shagwabe tana shirin sakin kuka ta amsa masa,abunda ya sake tunzurashi kenan,ya zame kadan cikin ruwan,ya kamota zuwa cikin jikinsa sosai ya dorata saman ruwan cikinsa,abinda yaso ta wuce da numfashinsu gaba daya shi da ita,saboda yadda kowanne sashe na jikinsu ya hadu dana dan uwansa,wata ajiyar zuciya me hade da sheshsheqa ya saki kamar wanda numfashinsa ke shirin kufce masa,wani shock mai bala'in qarfi ya ziyarci kowanne sashe na jikin iman din,dukka wata juriya da yakejin yana da ita ta fara kwaranyewa,jikinsa ya fara daukan zafi da chargy,sai ya kamo fuskarta cikin tafuka hannayensa,kiran sunanta yakeson ya sakeyi amma ya kasa,sai kawai ya hade bakunansu waje guda ya kai tsaye ya laluba harshenta ya sanya cikin bakinsa.
Wani zazzafan kiss da ya sake iza wutar da suke ciki ya fara aika mata,cikin salon na ar qwarewa da sanin sirrikan rura wutar soyyaya cikin zuciyar masoyi,salo mai tsafta da kuma tafi da hankali,tuni iman din ta narke masa itama,hakan ya bashi damar sakin fuskarta ya maida hannayensa zuwa wani muhallin na daban cikin sassan jikinta,lokaci guda gaba dayansu suka rude suka kuma fita a hayyacinsu shi da ita,gaba daya ji yake bathtub din yayi masa kadan,sannan he's not comfortable,don haka ya lallaba cikin mutuwar jiki ya dauki iman din cak suka baro toilet din.
Kasa qarasawa gadon sukayi dukansu,suka zube bakin gadon yana ci gaba da charger mata kwanya gaba daya,komai yayi zafi ya kuma kai geji,yakai iya limit din da baya buqatar komai sai kasancewa da ita,duk wani guri dake tsole masa idanu sai da hannunsa yakai,ya gusar da ishirwarsa ya kuma morema wajen son ransa,duk da cikin fitar hayyaci yake amma ya lura da wasu abubuwa tattare da uman din,wadanda suke alamta masa kamar batasan kowa ba cikin rayuwarta,kamar komai bai canza ba daga jikinta,amma bashi da tabbaci saboda yana ganin mawuyacin abune hakan ta kasance,sake hobbasan mai data saman gadon sosai yayi kana yayi mata rumfa,yana ci gaba da aike mata zafafan saqonni masu gusar da hankali tare da neman hanyar da zai maidata mallakinsa ta har abada,sai a sanna iman ta farga.....sai a sannan ta gane cewa lallai game din ya canza salo......sa a sannan tasan komai yana shirin canzawa ne,hankalinta yaso dawowa jikinta,tasa hannu da niyyar dakatar dashi,saidai shima nasa hannun yasa yakauda nata,gami da matseshi sosai cikin nasa tafukan hannayen yana girgiza mata kai alamun a'a,gaba daya kamanninsa sun sauya,farar fuskarsa tayi jazur kamar yadda tata tayi
"Bismillah,Allahumma jannib nash shaidan,w jannibash shaidana ma razaqtana" addu'ar da fiyayyen halitta ya koyarwa ma'aurata kenan yayin da zasu kasance da iyalinsu,saboda koda ubangiji ya qaddara samun qaruwa shaidan bazai iya cutar da wannan abunda aka samun ba,addu'ar data sanya iman fashewa da kuka,kukan kuma daya fita lokaci guda da azabar data fara ratsata.
Daga ita har lameen babu wanda yake tantance halin da dan uwansa ke ciki,azabar daga dinga ratsata da kukan da.takeyi da kuma kalaman neman afuwa da suke fita a bakinta kawai take iya tantancewa,yayin da lameen din kuma ya rasa cikin wacce duniya yake,sama sama kunnuwansa suke jiye masa kukan iman din,amma ya gaza controlling kansa,burinsa kawai ya cimma gaci,gacin da ya daukeshi wasu mintuna kafin yakai inda yakeson kaiwan,ya saki wani sauti mai qarfi yana matse iman gammm a jikinsa kamar zai tsagata gida biyu,kana yayi wani irin laushi gumi na jiqa ilahirin jikinsa kamar wanda aka yiwa wanka da ruwa.
Zare jikinsa yayi yakoma gefan iman din,yanajin yadda bugun zuciyarsa har yanzu bai daidaita ba,a tausashe yaja iman din cikin jikinsa sosai
"Subhana man khalaqal khalqa wa'ahsahum adad,subhana man laisa lahu sharikun fil mulk,subhanal lahil azim...subhana man laisa ka mislihi shai'un" kalama daya dinga fada kenan murya can qasa,wasu hawaye na sauka ta gefan idanunsa,ya tadda abinda bai taba tunanin zai sameshi ba tattare da iman din,lallai wannan hikima da baiwa ce daga ubangiji yayi masa ita,yasa bakinsa a tausashe ya ajjiye mata kiss dake dauke da nannauyan saqo a saman goshinta,sannan yasa hannunsa yana tattare mata gashin fuskarta,fuskarta ta fito sosai,gaba daya tayi jazur,idanuwanta dukka sun tasa alamun kukan datayi masa ba dan kadan bane,take tausayinta ya kamashi,ya soma tuna yadda take neman agajin inna da malam,yasa yatsansa guda daya yana goge damshin hawayen dake kan fuskarta
"Iman" ya kira sunanta a hankali cikin rada,maimakon ta bude idanun nata,sai yaga ta sake runtsesu gam.
Dumin da yaji daga gefen cinyoyinsa yasa yadan ja da baya kadan yana dubawa,jini ne ta wajen daya bata inda suke kwancen,abinda yadan tsoratashi kenan
"Subhanallah" ya fada yana kwantar da iman din tare da janyewa yana duban wajen,sai ya suturta jikinsa sannan ya dawo wajen iman din
"Iman" ya sake kiranta,saidai bata amsa masa ba kamar wancan karon,hakan yasa ya sauko daga saman gadon,lallai dole yasan yayi aikin lallashi,don gaba daya taja bargon daya rufe mata jikinta dashi ta lulluba har saman kanta,zagayowa yayi daga side din data maida fuskarta,ya durqusa gaban gadon
"Iman.....am sorry kiyi haquri don Allah" duk da yanayin azabar da take ciki,da kuma boyayyen kukan da takeyi ta cikin bargon sai dataji kalmar tayi mata girma,yaa lameen da bata haquri?
"Don Allah iman..... please talk to me mana" nan ma kasa bashi amsa tayi
"Ba zaki ce komai ba?" Kai kawai ta girgiza,duk da ciwon da take ji a jikinta,amma babban abinda yafi damunta ayanzu baisan ba zataya iya sake hada ido dashi bane har abada,ta yaya zata iya sake kallon yaa lameen din?,su hada ido dashi har kuma ma suyi magana ko suci gaba da mu'amala.
"Me kakeso?" Tafada da wata dasashiyar muryar dako ba'a gaya maka ba kasan tasha kuka yadda ya kamata
"Ki tashi please na duba barnar da nayi hankalina sai yafi kwanciya,kema kuma ki tashi ki gyara jikinki" tanajin ko sama da qasa zasu hadu ba zata miqe a gabansa ba
"Kaje zan tashi" ta amsa masa tana sake cukuikuye kanta,sam maganar bata kwanta masa ba,ya tabbatar mawuyacine ta iya tashin da kanta
"Zaki iya?" Ya fada damuwa na bayyanuwa saman kanta
"Eh" ta amsa masa,dan jim yayi kafin yace
"Is ok" sannan ya miqe daga tsugunnon da yayi,saidai maimakon ya fita saiya nufi qofar toilet da suka barta a wangale dazun,yadan turota kadan ya labe daga bayanta.
Minti kusan hudu ta bayar,sai data daina jin motsinsa sannan ta yaye bargon,a hankali ta miqe ta zauna tana ciza lebe,a matsayinta name karatun jinya tasan ciwuka taji a gurin ba shakka,saita matso da jikinta gaba a hankali da niyyar tashi.
Wata qara ta saki ta koma ta zauna sanda tayi yunqurin tashin,ya saki murmushi yana fitowa daga maboyarsa,duka saita rude,tana shirin komawa ta kwanta ya qaraso,daukar cak yayi mata tana boye kanta cikin jikinsa,bai damu ko kula da wannan ba ya wuce toilet da ita.
Next Chapter

Leave a comment

Post
Comments

112201018644657456668
Yaa rabb kabawa du wata diya mace musulma damar kai mutuncinta dakin auranta
2 hours ago

dadaummi1
❤️❤️❤️
3 hours ago

Contact Us
Arewa Books Publishers
WhatsApp: 09031774742
Email: [email protected]
Navigation
Home
About
FAQ's
Legal
Privacy Policy
Terms of Service
Social
Facebook
Instagram


Copyright 2021, Arewa Books | ALL RIGHTS RESERVED | Powered by thinkcrypt.io
"
https://arewabooks.com/chapter?id=62d6a0a47fc1109aa6133b68#:~:text=Chapter%2073-,Shafi%20na%20saba%27in%20da%20biyu,ko%20kula%20da%20wannan%20ba%20ya%20wuce%20toilet%20da%20ita.,-Next%20Chapter
[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 73
Wata nutsuwa ce ke sauka a zukatan kowannensu sanda suka kammala sallar azahar,ameen din yaja musu dogayen addu'o'i wanda suke dauke da kalaman yabo da jinjina ga ubangiji da kuma nema tabarrakinsa kan zamantakewarsu,a nutse ya shafa addu'ar sannan ya juyo inda iman ke zaune,kanta a qasa,tana jin nauyi ko yaya ta motsa,idan ta tuna abubuwan da suka faru tun daga zamantowarsu abu daya da lameen da kuma yadda ya tusata a bandaki ya gasata sai taji inama qasa zata tsage ta shige ciki.
Dab da ita ya sake matsowa,ya kama goshinta yayi mata addu'ar nan da annabi ya umarci kowanne ango ya kama goshin amaryarsa yayi mata
"Allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi,wa'azubika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi" ya zare hannunsa daga kan nata,maimakon ya sauke hannun qasa sai ya kamo nata hannayen duka,ya riqesu a tausashe yana kallon tsakiyar qwayar idanunta bayan ya matso sosai dab da ita,har gwiwoyinsu yana gogar juna,cikin wata murya dake cike da taushi zallar shauqi da qauna ya soma magana
"Kin bani komai,kin kuma gama min komai hajar.....ban mallaki abinda zan iya saka miki dashi ba,saidai ina fatan na zamo mafi alkhairin miji,kuma miji na gari da babu tamkarsa,babu sauran abinda ya rage da zan sakawa inna da malam illa addu'ar samun aljanna madaukakiya....sun ingantamin rayuwata,sun maidani cikakken mutum,basu barni a haka ba sai da suka haifamin mata gangariya,wadda zata zamo waje hutu da sanyin idaniya a gareni,duk kalmar da zan fada miki kan irin qaunar dake cikin raina....inajin kamar na ragewa soyayyarki marta bane,fatana ki rayu dani kamar yadda na alqawartawa kaina duk wuya duk dadi zan rayu dake,ki rufemin sirrina iman......banso ko sau daya tak ki kai qarana wajen inna ko malam.....banaso suji shakka ko susa a kaina,ko meye nayi miki ki zaunar dani ki gayan,idan nine keda laifi in sha Allah zan dauki laifina zan kuma nema afuwarki na gyara.....idan kece kuma zan nusar dake cikin salon daya dace wanda zai gamsar dake da kuma zuciyarki da izinin Allah... and lastly......iman" Sai ya sauke numfashi yana sake matsa hannuwanta
"Na'am" ta amsa masa tana sake gujewa kallonsa
"Kalli qwayar idanuna" sosai taji saukar maganar tasa da nauyi a kanta,wannan umarin nasa yayi mata nauyi da yawa,wai me yasa yake acting like babu ma wani abu da yafaru?.
"I said look into my eyes" a hankali kamar mai ciwon wuya ta daga kanta zuwa idanun nasa kamar yadda ya buqata,take kuwa magnet din dake ciki ya jata sosai
"Ni mutum ne dake qaunar caring,inason matata ta soni sosai,kada ta raba kulawa ko soyayyar da takemin da kowa....koda yaran da zamu haifa ne,ki bani soyayyarki ni kuma nayi zan basu tawa soyayyar,nasan zata wadatar dasu in sha Allah.....kinyi alqawari?" Duk da yadda ya aza mata nauyin idanu dana maganarsa,amma haka ta bashi tabbacin da yakeson ji
"Ina fata ubangiji ya qadarta samun rabu a wannan haduwa tamu" ya fada hannayensa asama,maganar data sanyata qarasa dunqulewa waje daya cike da kunya,ya miqe yana dariya ya dagata ya rungumeta cikin dariyarsa yana ci gaba da murmushi,yau dai iman baki ya mutu murus.
Wunin ranar wani wuni ne daya ajjiye dimbin tarihi cikin rayuwar aurensu,ya koma sake kafa wata sassanyar soyayya a zukatansu,ta wani bangaren kuma soyayya me zafi,ta sake sanin abubuwa masu yawa game da ameen din,tarihin rayuwarsa na zahiri tun yana qaraminsa almajirtarsa da fadowarsa hannun malam,hakanan itama ya bata dama a sanda kanta yake kwance saman cinyarsa ta bashi labarin abubuwa da dama da bai sani ba,ciki harda zaman aurenta da bassam.
Shuru yayi abun yana tabashi,hannunsa saman lallausan gashinta yana wasa dashi,komai Allah ke tsarashi ya kuma kawoshi a sanda ya dace,yana can cikin ciwo da zafin soyayya.....ubangijinsa kuma ya dubeshi yana ta yi masa tanadi irin wanda ya dace dashi
"I suffered a lot iman......ban zaci soyayyarki zata barni na rayu ba,amma alhamdulillah,na godewa Allah" shuru tayi tana jinsa,murmushi kwance kan fuskarta,taji tarin kalamai daga bakin lameen wadanda bata tabajin masu zaqi da gardinsu ba,taji irin girman matsayin da take dashi a wajen lameen din,wanda ko kusa bata taba kawoshi kusa cikin ranta kan tana dashi ba,tabbas inda ace ana buda zuciyad mutum aga meke ciki,da bata gujewa lameen din ba,saidai kuma bawa baya taba tsallakewa rubutacciyar qaddararsa.
Washegari tadanji dama dama a jikinta,saboda tabs din data rubuta lameen din ya samo mata su,hakanan shi ya dinha dawainiyar gasata da kanshi,duk da yadda kunya ke dawainiya da ita amma ya murje idanunsa fes,tana kukan shagwaba yana tayata,haka suka dinga yi akai akai,har sai data narke masa da gasken ta gaji.
A hankali take takowa zuwa falon din a daren washegari,tayi masifar kyau cikin wata straight gown data fidda shape dinta sosai,idanunsa na akanta sanda take iskoshi,wani abu daketa motsa masa ya sake motsawa cikin jikinsa,sai ya miqa mata hannu ya mata nuni data taho,bata taba lokacin ba kuwa ta taho ya kuma yi mata kyakkyawan mazauni saman cinyarsa,ya kuma bude qirjinsa ya lullubeta a ciki.
Cikin wuyanta ya cusa fuskarsa yana shinshinarta,launin idanunsa da kuma yanayin saukar numfashinsa yana sauyawa,tun daga wuyanta ya gangaro kunnenta,ya kuma juyo da ita sosai ya cusa kansa tsakanin qirjinta numfashinsa na qara gudu wajen fita da dawowa,a hankali ya soma yawo da hannayensa cikin jikinta,ya fara aike mata sa saqonni,abunda ya rudata ta riqe hannayensa,cikin rudu take girgiza masa kai
"Yaa lameenn...."
"Anty imann......." Ya tari numfashinta shima da sauri kafin ta qarasa fadin abinda zata fada din,yadda taga ya birkice yasa ta kwantar da kanta sama kafadarsa kawai cike da fargaba,tasan laifi da zunubin yiwa miji musu ba tun yau ba,bugun zuciyarta na qaruwa,tana saddaqarwa cewa lallai tata ta qare,har yanzu akwai sauran jinya tattare da ita,hakanan bata manta wuyar da tasha a hannunsa ba.
Sosai yake ya mutsata kamar wani mayunwacin zaki,sai wani numfashi da yake fitarwa kamar gurnani,ita kanta sai daya rudata sosai,zuwa wasu mintuna ya qanqameta kamar zai tsaga cinyarsa ya sakata,sai kuma ya zameta daga saman cinyar tasa ya zaunar da ita yana cewa
"Ina zuwa" a hankali ya taka ya shige daya daga cikin dakunan,da kallo ta bishi har ya bacewa ganinta,saita maida idanunta ta lumshe,ita kanta dukka jikinta ya amsa,duk da cewa a tsorace take da wahalar da tasha a jiya.
Kusan mintuna ashiri sannan ya dawo,da alamu wanka yayi,idanuwanshi a kanta,bai tsaya ko ina ba sai dab da ita,yasa hannu ya shafi saman kanta ya zarce qirjinta,sannan ya maida kansa saman kafadarta ya kwantar,kamar sabon marayan daya rasa mahaifansa
"Queen,inajin sai kinyi haquri da yaa lameen dinki.....bazan boye miki ba,tun ba yau ba nasan ina cikin nau'in mutane mabuqata,abinda ya dinga wahalar dani,saidai na godewa Allah daya dinga bani kariya,har kawo yanzu da ya rabautani da halaliyata" sarqafe hannayensu yayi waje guda
"Kinyi alqawari zaki kula dani....wannan ma zai shiga ciki?" Cike da qwarin gwiwa ga gyada kai
"I will do my best in sha Allah" cikin jikinsa ya sanyata tana mata godiya har taji nauyin hakan.
A daren ya sake koyar da ita wasu sabbain darussa,qaramae akwati guda na wasu irin sexy dresses ya ajjiye,yana daga kwance saman gadon tana saka masa yana gani yana zabar wadanda yake so,wasu idan ta sakasu kamar tayi yaya don kunya,sau tari idan ta gwada wasu duqewa take a wajen ta kasa miqewa,wasu baya ne a kwashe,wasu tsakiyar ciki zuwa cinyoyi,komai a bayyane,bata taba sanin ya lameen din cikakken dan duniya bane sai sannan,ashe kallon kitse akewa rogo,fitina ce fal cikinsa a yanzu yake sauke mata ita.....ni kuwa nace banga laifinsa ba,illar dama kaje baga halalinka na,amma idan halili ne to falillahil hamdu.
Daga qarshe kuwa kasa ci gaba da gwajin tayi,gaba daya kunya ta durqusar da ita,da mabayyanin murmushinsa yataso ya dagata cak dama ya raina daukanta tuntuni
"Idan ina da hali zance kiyimin yawo cikin gidana daga ke sai fatar jikinki,ke kadai Allah ya halastamin iman,kuma dake daya nakeso na rayu" dole dai duk yadda taso masa rowa haka ta bada kai bori ya hau,duk da yayi mata fami qwarai,amma da sauqi akan na jiyan,sannan a yau din tadan dauki haske,ta kuma fahimci wasu abubuwan.
Washegari wajen sha daya na safe tana cikin jikinsa,suna zaune saman kujera yayi relaxing bayansa da makarin kujerar,santala santalan qafafunsa a miqe saman dan table,iman din sanye da wata 'yar fingilar shirt short sleeve,fara ce qal kuma robber,hakan ya sanya ta dameta dai dai size na jikinta,ta kuma fidda kowanne shape nata,wandon jikinta shima haka yake,iyakae tsahonsa gwiwa,ta gyara gashinta cikin farin band jelar ta sauka kafadarta ta hagu,tuntuni ta sani white is favorite color na ameen,don ko a sannan din shima kayan jikinsa farare ne
"Matso ki gani"yayi maganar yana rage sautin tv din dake aiki,kana ya jawo tab dinsa wadda a yanzu da ita yake amfani,tunda ya kashe wayoyinsa,ta maqale sosai kuwa cikin jikinsa tana kallon fuskar tab din daya dauko.
Fasa bude tab din yayi,ya waiwayo ya dubeta,dai dai sanda itama ta daga kanta suka hada idanu
"Fisabilillahi haka akeyi,yanzun kuma nace zan dana asamin kuka?,bayan tun daxu fuska kawai nakeyi?" Da sauri ta dagashi tana turo baki
"To ba kaine kace nazo na gani ba" ta fada a shagwabe tana karya wuya,abinda ya tuna masa da iman din zamm dinta,murmushi ya qwace masa,ya kuma tarota sanda take qoqarin sauka a jikinsa
"Zo mana,zo kiji 'yar qanwata,zo mu sasanta" saiya miqe ya zauna sosai bayan ya ajjiye tab din daga gefansa
"Muyi ban gishiri na baka manda mana,kidan sanmin ko babu yawa kinji" yayi maganar idanunsa cikin nata,launin idanun nasa suna canzawa,da alama da gaske kenan yake,abinda ya tsorata iman ta fiddo idanu
"Yaa....."
"Shshshsh" yayi maganar yana dora yatsansa saman lebansa
"Babu wani yaya....na soke wannan sunan,kiji dani imani ta" kuka ta sakar masa,at least dai yau ai ta huta,ta kuma sanya ran zata huta din,saidai yau dinma tana ji tana gani ya mata wayo ya karba abunsa,tana jikinsa tana masa kuka wanda ke cakude da shagwaba,shi kuwa yana aikin lallashi,hannunsa saman kanta
"Kiyi haquri....kullum sake ninka min qaunarki da sha'awarki ake,babu abinda ke raguwa,keta dabance iman,wallahi da na zauna da wata tabbas dana fada cikin mazan da Allah zai tuhuma,banajin zan iya hadaki da wata mace na kuma yi muku adalci,sonki a jina na yake,bazai taba gushewa ba...." Duk wata tabararta haka ya dauketa sai toilet,tare sukayi wanka sannan suka dawo ya dauko tab din ya fara nuna mata abinda zai nuna mata daxun.
Wasu selective places ne best for honeymoon cikin garin lagos,da pictures dinsu da bayanansu,ya bata daman zaban guri har guda hudu da zasuje,biyu a ciki zasuyi sati daddaya a can,sauran kuma kwana uku uku ne.
Sanda taketa murna binta kawai yake da kallo,farincikinta kadai ya wadatar dashi,inda yana da wani abun da zai sata farinciki sama da haka daya bata,yana jin iman din takai masa ko ina cikin rayuwarsa,hatta fitar numfashinsa ya tabbatar yana fita ne da so da qaunar iman din.
Cikin kwanaki da kuma wuraren da suka zaba din zasuje sun gudanar da gagarumun honeymoon wanda dukkaninsu basa jin zai gushe cikin tarihin rayuwarsu,wata wutar soyayya ce sosai ta kunnu cikin zukatansu da kuma ruhinsu,sun sake dinkewa sun zama abu daya,ta sake sanin waye lamin.....shima ya sake sanin wace iman a badininta,tayi kuka aboye a bayan idanunsa da nadamar gudunsa data tabayi a cikin rayuwarta,tabbas inda tana da qarfin ikon maida lokaci baya ta shafe wancan abun data aikata,ashe wata tarin qoramar zumar soyayya ce take jiranta ta debi kashi ta watsa mata cikin rashin sani da wauta,dukka wani caring da soyayya da take mafarkin samu cikin rayuwarta ta samu sama da haka daga wajen ameen din,ashe ba kudi bane jin dadi?,ashe ba kyau bane soyayya?,ashe ba kudi bane qauna zaman lafiya da kwanciyar hankali?,da gaske duk sanda bawa ya bijirewa zabin Allah,sai Allahn ya barshi da zabinsa yaje yayita wahala,ta godewa Allah daya zabar mata tsayayyun iyaye kuma nagartattu.
Fadin yadda iman ta sake mamaye rayuwarsa ma wannan bata bakine,a kullum ya saka goshinsa a qasa zai roqa musu dawwamammen zaman lafiya da zuria dayyiba,burinsa a yanzu a rayuwa shine ya rayu da iman din har abada,ta kuma tara masa iyali masu yawa,mutum ne shi maison yara qwarai da gaske,kuma ita kanta iman din ta sani.
Suna tsaka da honeymoon din issue na bude kamfanin saida spare parts na motocin da yake shirin yi ya taso, issue din ya taso gadan gadan,dole suka dawo gida,dama kwanaki biyu ne suka rage masa.
A lokacinne suka sake gasgatawa kansu daya bazai iya rayuwa ba saida dayan,fitar da yake da safe ya dawo da yammaci liqis dukkansu shi da ita galabaita suke da kewar juna,dole ba don ya shirya ba ya siya mata layin waya,idan ya fita suna maqale da juna ta waya,duk da haka wataran bai gamsar dashi sai ya yanke abinda yakeyi yazo ya ganta sannan zai koma,aikin me wahala da cin rai,saboda su sona son kafin ya samu license yabar kamfanin a nan Lagos,shi kuma ba wanna ya tsara ba,yanaso kamfanin ya zama a arewa cikin garin kano,bazai bar wannan damar da kuma alfanun da dubba matasa zasu samu na samun aiki ya qare a can ba,bayan ga jama'arsa suna da buqata,ya kashe gida ya raya jeji,yasha wahala dasu sosai kafin ya samu komai ya dai daita,aka kuma sahale masan yayi a gida kanon dabo,cikin qanqanin lokaci komai ya kammala cike da nasara,ya kuma siya dukka wasu kaya da za'a buqata ya aikosu kano,a sannan ya shirya musu qarashen honeymoon dinsu,suka raqashe da kyau,sannan suka fara shirin dawowa gida kuma,iman murna kamar tayi me,kwanaki kadan suka rage su cika watanni uku a lagos din,tayi kewar inna,dole ta haqura kiran gida duk da akwai waya a hannunta,saboda lamin yace yanaso su huce sosai kafin su tunkaresu.
Wani irin kyau iman din tayi,ta sake fari ta cika tayi fresh da ita,duba daya zakayi mata kasan ta samu dukkan wani jin dadi da kulawa da ya kamata diya mace ta samu daga wajen miji,tabbas a yanzu a duniya babu abinda ta nema ta rasa,ko yaushe tattalinta ameen din yake kamar yadda itama ta zage damtse tana tattalin mijinta da dukan wani nau'in kulawa da tasan yanaso,zaiji dadi hakanan ransa zaiyi fari.
Wata mahaukaciyar siyayya lameen din ya dinga mata kamar baisan ciwon kudinsa ba,ta dade da sanin mutum ne shi mai kyauta da abun hannunsa,amma kuma sam bashi da almubazzaranci ko barnatar da kudin a inda bashi da alfanu,anan ya hada mata kayan lefe jimilla na kece raini,ya kuma qara mata da wasu kayayyakin da ita kanta wani abun batasan yadda zatayi dashi ba,soyayyar gaskiya tayi.....babu abinda ke raya soyayya irin kulawa nuna damuwa da masoyi a cikin kowanne irin hali.[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 74
Ana ya gobe zasu tafi ya fidda ita wani eatery mai tsada,yace ta zabi dukka nau'in abinda takeso,bayan ya yiwa wani waiter na wajen magana kan su kawo menu.
Tunda daya daga cikin ma'aikatan wajen mata ta doso wajen idanun lameen a kanta
"Ya fa'alul lima yurid"ya furta can qasan zuciyarsa,idan idanunsa ba qarya sukayi masa ba,ko kuma mantata yayi ba munira yake gani sanye da uniform din ma'aikatan wajen,ta sauke abinci a wani table tana dosu nasu table din dauke da menu din a hannunta,idanunsa ya dauke ya maida ga iman,sam bata lura da tahowarta ba,sai yaja da baya ya miqe
"Ina zuwa queen" sai ya duqa yayi kissing nata forehead sannan ya taka zuwa wani sashe nesa kadan dasu
"Good day madam" muryar munira ta fita cike da girmamawa tana dora menu din kan table.
Da hanzari iman ta daga kai saboda jin muryar da ko a barci ta tashi zata canki ta wacece,munira ce tsaye a gabanta,ta saje da ma'aikatan eatery din,idanu dukkaninsu suka fitar,kowa yana mamakin ganin dan uwansa a wajen,kusan lokaci daya suka ambaci sunan juna,sa munira ta fashe da kuka,abinda yasa iman tayi saurin miqewa kenan ta rungumeta
"Muneera.....kece muneera?zauna" iman ta fada tana gyara mata kujera daya da sauri,zare jikinta tayi da sauri
"Aah,zamana a nan wajen zai jawomin matsala idan har aka ganni....muje tacan baya,akwai labarai iman" miqewa iman din tayi tabi muniran,tana qarewa muniran kallo,gaba daya ta canza ta lalace,idan har kasan asali munira kanka tsaye zaka fadi haka,a haka ma da sauran gayunta tunda babban gidan abinci ne,dole sai da tsafta da kuma gayu,idan ba haka ba korarka ma zasuyi.
Hankalin lameen dake zaune can nesa dasu ya dauko sanda yaga tana jan iman din zuwa can bayan wajen cin abincin,a nutse yake binsu a baya ba tare da sun sani ba,sai dayaga waje suka canza,sannan ya koma can baya yana monitoring nasu ta inda bazaiji sirrinsu ko abinda suke tattaunawa ba,bai matsa daga wajen ba saboda bawa iman din tasa kariya.
"Ba'a yiwa Allah wayo iman,kuma duk sanda bawa ya matsa kan samun zabinsa ba zabin Allah ba,Alla zai barshi da wayonsa ne yayita wahala,kwanaki da muka hadu dake nace miki bikina za'ayi iman,akwai abinda ban gaya miki ba kafin zuwan bikin,nayi saurayi mai dan datawar shekaru,yana bala'in sona,yana kuma da kudi yadda nakeso,saidai matsalar bai cika sharadi biyu cikin sharadaina ba,na farko yana da mata da yara,na biyu kuma yayimin shekaru da yawa,na dinga wulaqantashi qarshema naci masa mutunci muka rabu,ba'a jima ba fallelen yaro ya fito min,ya hada komai irin yadda nakeso,muka shiga soyayya gadan gadan,ya kuma shiga kashemin kudi babu qaqqautawa,kullum mune yawon shopping,gidan cin abinci iri iri,cinema kullum muna a hanya,duk abinda na buqata zan samu saidai idan ban buqata ba,hausawa sukace kwadayi mabudin wahala da kuma wulaqanci,a irin wannan fice ficen da mukeyi dashi a mota,kwatsam ranar mun dawo daga shipping,ya siyomin iphone 13promax,ina cike da murna yace na rakashi gidansu zai karbo saqo wajen mummy dinsa saimu wuce zai siya min wasu set na gold dana gani ana yayi,yace basai na shiga ba,nayi xamana a mota,da murnata na amsa masa da to,muna zuwa ya bude ya shiga gidan,minti wajen goma saiga wayarsa
"Na samu mummy bata jin dadi muneera,tana kwance zazzabi ya kada ita,daure ki shigo kiyi mata sannu saimu wuce" ya fake da qaryar da ko baimin hidima irin haka ba zanji nauyin cewa bazan shiga ga,da kwadayi da qaramar qwaqwalwa irin tawa na saka kai cikin gidan,ashe tarko RUFA'I ya dana min,a ranar ya samu yayimin fyade na rashin imani,yana gamawa saiga alhaji mando ya shigo mutumin da na wulaqanta
"Ba'a tabani a zauna lafiya,wannan shine sakamakon wulaqantani da kikayi,maga waye zai dauki saura,idan kin rasa mai dauka ki dawo zan taimakeki na dauka a haka na qarasa quruciyarki,nine naturo rufa'i,donshi ba kowa bane face yaron dakemin aikace aikace,na bashi dukka kudin da xai isa yayimin wannan aikin,idan kin gama zaman jinyar ki rufe gidan" haka suka tafi suka barni,bayan ya kwashe duk siyayyar da yayimin dama a mota na barta tunda naga shiga kawai zamuyi mu fito.
Na shiga matuqar tashin hankali iman,saidai daga bisani sabbin qawayena da nake tare dasu suka kwantarmin da hankali,suka kuma gayan kada na wani damu,akwai dabaru da ake da magungunan da zaki koma gam kamar yarinya qarama,abinda ya kwantar min da hankalina kenan,na bude sabon shafin rayuwata,naci gaba da zabe da kuma laluben wanda zan aura,lokaci yanata quremin,damarmaki nata zuwa gabana amma idanuna ya rufe,sai daga bisani irin taste dina yazo wato FAISAL.
Faisal yazomin da dukka wasu burika da sharudda nawa da nakeso ya cika,ya cikasu fiye da kima,yaxomin da fuskar babansa wani shahararren attajiri ne da gaba daya ba'a qasata Nigeria suke zaune ba,ya nunan gurare da kamfanoni masu tarin yawa da sunan nasu ne,a gabana yazo da takardun wasu kamfanoni guda biyu ya sauke sunansu ya maida sunana saboda son da yakemin,a ranar naji duk duniya nafi kowacce mace sa'a a rayuwarta,tunda faisal ke zuwa bai taba zuwa da mamaicin mota kaya ko waya ba,hakanan ya sanyani na zabi tsala tsalan motoci har biyu ya shaidan su xan fara hawa daga randa na amsa sunan matarsa,fadi miki irin abubuwan da rufa'i yazomin dasu iman kanki zai daure,don lefe ma cewa yayi ana daura aure zamu dage dubai daga can mu zarce china,acan zan hada duk kayan lefen da nakeso,kayan daki da za'a yimin cewa yayi na karba kudina nayi sabgar gabana dasu,don shi ya saka wani kamfani daga turkey suna mana designs din da ko shugaban qasar nigeria bai taba kwana a kai ba,na jarabtu da wata muguwar soyayya tashi,har bana gane dai dai da ba dai dai ba,hakana bana sauraren duk wanda zaizo min da magana akansa musamman ta suka ko zagi.
Naso na taba kama faisal,na ganshi a hanya yana tafiyar qafa,gaba daya jikinsa ba irin suturar dana saba ganinsa da ita bane,na kira sunansa sai naga bai juyo ba,nasha gabansa ina nuna masa kaina amma sai ya nuna bai taba ganina ba,harshe ha juya ma ya fara yimin yarbanci,ya balbaleni da fada cikin harshen yarbanci har yaso taramin jama'a,abinda yasa jikina yayi sanyi kenan naja baya ya wuce abinsa,har sanda ya wuce din yanata masifa yana nunani da hannu.
Washegari sai gashi yazo a faisal din dana sanshi,maganar dana fara yi masa kenan,amma sai ya nuna zallar mammaki
"Kece mutum ta uku data taba cewa taga wannan bawan Allan,ni kaina da ban taba ganinsa ba mamaki nakeyi sosai,ance sak ni,saidai shi yaren yarbanci yakeyi"
"Exactly" na fada da sauri,zuciyata na gasgata faisal,saboda yadda naga zallar shima mamaki kan fuskarsa
"Ba matsala,zan saka escort dina su lalubomin shi,nima dai naga mekama dani" dariya nayi,na kuma ce
"Ai ikon Allah yafi gaban haka" daga wannan muka shiga wata hirar ta daban.
Bai gane dukka wasu magangu da ayyukan faisal qarya bane,ban gane duk wani magana nashi plan bane,ban gane rami ya shirya min ba sai randa aka kaini gidan faisal,madadin a shiga dani kai tsaye zuwa ainihin ginin tanqamemen gidan,sai akayi boys quarters dani,kowa mamaki da al'ajabi ya cikashi na wannan juyin juya halin,matar gida a boys quarter?,tarin cincirindon qawayena irina 'yan qarya,harda ma wadanda hayarsu nayo su qawar qawa saboda su fidda bikina a duniya,duk haka suka tafi suka barni cikin tashin hankali da mamaki,amma mayaudariyar zuciyata gayamin takeyi wataqila don kada a bata masa gida yasa yayi wannan dabarar,saboda yasha gayan shi mutum ne mai tsafta,amma bai cika son jama'a ba,da wannan na share nayi zamana,ina kallon boys quarter din da yake kamar kango,babu komai sai katifa da labule.
Sanda ango ya iso shi daya kamar maye,da shaddarsa tun ta wajen daurin aure,zan tarbeshi ya matsa
"Dakata.....dakata,opay ce,tanayin squeezing kin jawomin jangwangwama,saina qara dubu biyu akan yadda na karbo aronta,shi yasa tun daxu na kasa sakewa na zauna na sake,sai yawo nake a tsaye kamar wanda ya hadiyi tabarya" uban mamakin daya cika ni yasa na sandare a tsaye,ya zare rigar ya zauna ya bata lokaci ya ninketa tsaf,harda zama akai wai don tafi komawa dai dai,sai daya gama duka sannan ya fuskanceni.yana yaqen baki,zuwa sannan duk wani noti a jikina ya kwance,na gama sallamawa
"Faisal,ka gayamin waye kai"
"Yanzu kuwa,cikakken sunana shine haladu murtala,kuma haifaffen qauyen namuduka ne can iyaka da garin kano,ci rani ya kawoni na hadu da wayyayun abokai wanda suka taba jana zuwa wata dinner,a nan na ganki.na nuna inasonki kika yarfani harda guzurin mari" yana fadar haka fuskarsa ta dawomin tar da kuma abinda ya faru a lokacin,wanda har ga Allah a inda akayi abun s nan na bar batun,na mance da fuskarsa bare abinda ya faru
"Wannan yasa naci alwashin saina rama,kuma saina mallakeki kota halin yaya,nayi bincike a kanki na samo komai,na shigeki.ta yadda kikeso,yanzu gashi na sameki,duk da naji jiki na kashe kudadena sosai,amma babu komai tunda burina ya cika kuma zan fanshe" ina kuka ina komai haladu na sha'aninsa,a daren ya kwanta dani abunsa,babu kazar amarci ko lemon fata na naira 30 ban gani ba,yana gama abinda xaiyi dani ya haureni da qafarsa na fado qasa
"Shegiya tsinanna,girman kan banza ne,ashe fanko ce?,duk wannan wahalar da nasha?,to billhillazi saikin maido min duka abinda na kashe,kuma aure yanxu aka fara bazan sakeki ba" duk da cikin azaba nake amma mamaki ya cikani,saboda nasan anyimin duk wani gyara da zai maidani mace,ko a jikina inajin na matse gam,to amma komai na Allah daban yake,idan ya tafi ya tafi kenan,babu wanda ya isa yayi halitta irin ta ubangiji koshi waye.
Kwananmu uku cikin wannan gida dana fuskanci na uban gidansa ne dake rayuwa a lagos,a kwana na ukun da sassafe naga yana hada kayanmu waje daya,dama nawa kayan da nazo dasu ne daga gida,don ba lefe ba batunsa
"Lagos zamu tafi ci rani,na samo miki aiki a gidan cin abinci,zakiyi aiki harki hadan kudadena dana kashe,na saida gonakina da gidajena na gado duka a qauyenmu saboda ke,to wa billahi bani haqura saikin dawomin dasu" inaji inagani ya kawoni nan,ya kuma danqani a hannunsu yace a sanyamin idanu sosai idan aka ganni da wasu,saboda ni din bin maza ne dani" kuka muneera ta sake sosai,bama ita kadai ba harda iman din
"Inasu mamee,me yasa bazaki sanar musu ba"
"Ya karbe wayata tuntuni,amma na taba satar wayarsa na kirasu,abun mamaki wallahi iman na kasa gaya musu komai,yazo ya sameni a haka yayita dariya,dama nasan zaa rina,shi yasa nayi maganinki,duk wani naki da nasan zaki gaya masa.matsalarki nasa an rufe bakinki,tashi ki ban waje,hakkin mazan da kika zalunta kika ciwa kudi baki auresu bane.....wannan ne abinda ya gayan"
Kukan daya hangi iman din tanayi yasa hankalinsa ya tashi,ya gaza daurewa ya tako a hankali zuwa inda suke,babu wanda yaji zuwansa,sai hannunsa da iman ta gani qasan habarta yana tare digar hawayenta dake shirin sauka qasa
"Meye haka queen?" Maganar data ja hankalinsu,muneera ta bishi da kallo,iman kuwa ta rungume hannunsa tana sake sakin kuka,a hankali ya dagata ya sanyata a jikinsa,a kunne ya gaya mata
"Da nasan kuka zata saki bazan bata damar ganinki ba,muje" da sauri iman ta balle jakarta,ta fiddo dukka kudin ciki ta ajjiyewa munera
"Zan nemeki munira,kiyi haquri" binsu da kallo tayi,har xuwa sanda taga sun bude motarsu sun shige,kanta ya daure matuqa,lamin ne dai haka?,lamin din data rabasu da iman din?.
Cikin mota tana kuka sosai tana baiwa lameen din dukka labarin da iman din ta bata
"Mu taimaketa don Allah honey bee"
"Zan duba" amsar daya bata kenan a taqaice,kafin ya sake waiwayawa yana dubanta
"Amma indai kikaci gaba da wannan kukan,babu abinda zanyi a kai" da sauri tahau goge hawayen,duk da zuciyarta a karye take,munira na cikin masifa qwarai.
************
Jirgin safiya suka bi zuwa gida kanon dabo,cuie da tarin nasarori cikin rayuwarsu ta kowanne fuska ta kuma kowanne fanni,tun a cikin mota iman fake kwance laqwas cikin jikinsa,a hankali ya dora hannunsa saman fuskarta
"Are you okay Baby queen......?" Kai ta gyada masa kawai,saboda cike take da fargabar abinda zai faru tsakaninsu da malam
"Amma duk da hakan kamar jikinki akwai dumi,tun jiya nayi noticing hakan"
"Kaman yanayin weather ne daya juya" dan bata rai yayi cikin wasa yana dubanta
"Kada kicemin haka mana please,ba wani weather,baby ne,ajiyata ce" dariya ce ta qwace mata,ta rasa wanne irin son yara lamin din ke dashi,abinda duka duka satinta uku kenan da ganin period dinta har yake zancan baby?,....gabanta ne yadan fadi data tuna cewa ranar ovulation day dinta sun samu intercourse dashi,kuma lallai komai zai iya faruwa ba,sai tayi shuru tana irgen kwanakin,tare da laluban canje canjen da takeji ajikinta,saidai ta rasa ko guda daya a ciki,bata jin canjin komai,kawai dai daga shekaran jiya jiya zuwa yau dukin jikinta ya qaru ba kamar yadda yake normal ba.
Suna isa gida lameen ya shirya su wuce wajensu malam kai tsaye,itama da wannan zumudin ta iso,saidai tana fitowa a wanka barci yayi awon gaba da ita,ba ita ta tashi ba sai gefin azahar.
A gefanta ta sameshi zaune yanata calculation da lissafe lissafe na wasu kudi,suna hada idanu ya sakar mata murmushi wanda ta kasa fahimtar me yake nufi
"Sannu baby"
"Don Allah ya lameenn.....bafa haka mukayi dakai ba" lumsassun idanunsa ya zaro mata yana dubanta
"Me kuma nayi?"
"Gida fa kace zamuje wajen malam" tana kaiwa nan sai kuka ya qwace mata,ba lameen kadai ba,ita kanta abun sai ya bata mamaki.
A mamakance ya taso ya riqeta sosai ya sanyata cikin jikinsa yana shafa bayanta
"Akan wannan kike kuka?,to ya isa,tashi kisa kayanki mutafi" sai daya dan jima yana lallashinta sannan tayi shuru tana sauke ajiyar zuciya,shi ya taimaka mata ta shirya duk don ya saukar da ita,koma bayan daa da ota ke gaimala masan ya shirya idan zai fita,suyita rigima tana jan gashinsa kan cewa har yau baby ne bai gama iya shirin office da kansa ba,duk gyara daya punishment nasa zai bata hot kisses both kumatunta guda biyun,batasan wayo yake mata ba,shi hakan yafi masa komai dadi a rayuwarsa,shi yasa idan ta gyara masa abu gobe idan yazo bashi zaiyi ba,yana sane zai canza ko kuma yayi ba dai dai ba,moments da suke spending kafin ya fita aiki yana daya daga cikin memorable and sweet moments a rayuwarsa da bazai taba mancewa dasu ba,ya fuskanci zuciyarta a kusa take,ajiyar zuciya taketa saukarwa,don haka ya dinga lallabata har ta gama nata shirin sannan yayi nasa,cikin wani yadin kufta da aka zubawa aiki irin na matasan zamani dake ji da kudi da ilimi,kalar yadin kalar kayan dake jikin iman dinne,sai gasu sun fito fess dasu,best couple ever.
A harabar gidan taga yana yunqurin bude wata sabuwar mota,mamaki ya cikata,saboda batasan da ita ba,hakanan sanda suka shigo gidan bata lura da ita ba,sai da suka shiga sannan ya dubeta bayan ya furta "alhamdulillahil lazi bini'imatihi tatimmus salihat"
"Ma sha Allah,tayi kyau honey"
"Taki ce dama" ya fada yana murmushi,idanu ta zaro cikin mamaki
"Da gaske?"
"Da gasken gaske,na taba yi miki qarya?"
"Ko sau daya yaya na...." Farinciki na wanzuwa saman fuskarta
"ta yaya zan nuna godiyata ma a gareka?"
"Ki haifamin babies masu kama dake da zasu cikamin gidana,sannan ki bani dama naci gaba da kasancewa dake har abada" murmushi ya kubce mata
"Allah ya cika maka dukkanin burikanka,yasa ka gama lafiya,Allah ya kiyayemin kai"
"Ameen uwae yayana,mace ta gari"sunan yayi mata dadi sosai,har sai datayi fari da idanunta
"Amma yaya ka barmin waccan ka dauki wannan kai" motar ya kunna ya fara qoqarin fiddata daga cikin gidan kafin ya amsa
"A sabuwa dal na sameki.....saboda haka baci cancanci kyautar tsohon abu ba,kawai dai idan ina da sha'awar hawa zan ara,kafin komai ya qarasa warwarewa nima na sauya tawa,amma yanzun kam wannan takice,banason ki koma zirga zirgar makaranta rana tana dukarmin lallausan fatarna me tsada" dadi ya sake cikata,kalamai da gaske sune mutum,kulawa itace gishirin zaman aure,kwanciyar hankali da nutsuwa kuma sune jigo,bawai tarin dukiya ko qyale qyale ba.
Duk yadda iman din takai ga zumudin xuwa gidan sai gata tana rabewa a bayan ameen din sanda suke shiga cikin gidan,dariya ya saki ya jawota zuwa gabansa
"Matsoraciya,babu abinda zai faru fa,fada kawai malam zaiyi ni na sani,kuma koda yayi fadan ni zai yiwa bake ba" saita san saki jikinta tana qanqame da hannunsa.
Mufida suka samu a falo tana gurxa danyar citta ginger,da alama lemo zata hada,gefanta wata kyakkyawar black beauty matashiya ce zaune suna hira da mufidan tana tayata kankare bayan ginger din.
Dukka abun hannunta ta watsar ta taso tayo kan iman din tana qwalla qarar murna abinda yaja hankalin inna da Sadiq dake falon malam duka suka leqo da sauri.
Sak inna ta tsaya,wani sanyi yana ratsa zuciyarta,tabi sanyin idaniyar tata wato lameen da iman da kallo,zallar nutsuwa wadata da kwanciyar hankali na bayyana kansu da kansu daga jikkunansu,ba wanda bai qara haske da qiba ba a cikinsu,sai tayi hanzari kau da kai sanda duke gab da hada idanu da ita,saidai kuma murna da farincikin dake saman fuskarta bai canza ba.
Gaba dayansu yau har iman din zubewa sukayi suna gaidata,ta amsa musu cikin kulawa da nuna farinciki,kai tsaye kuma suka wuce wajen malam,kwarjinin nan nan nasa dai yayi musu,saidai shi dinma farincikinsa ya kasa boyuwa,sadiq na gefan lameen din yanata kwasarsa yadda suka saba qasa qasa yadda ba wanda zai fahimta saisu yasu
"Zaku hade da yaagana,tace kun maidata mutuniyar banza,tana zaune zaman jiran gawon shanu ka sace matarka kuka barta gaho" dariya taso qwacewa lamin,ya jima yana tunanin dama yadda zata kaya a tsakaninsu da yaagana din.
Hirarrakin yaushe gamo ne suka barke sosai a rumfar malam,dukka aka tattaru aka dawo nan,harda matar ya sadiq wadda a ranar suka fara ganin juna face to face ita da iman,kuma wani haduwar jini ya qullu a tsakaninsu,saida aka gama hira lamin ya gabatar da bude kamfanin sarrafa motoci malam yasa rana kamar yadda ya saba,sannan ya buqaci ganinsu,hakan yasa matar ya sadiq me yawan kunya da hankali ta janye mufida cikin hikima suka bar dakin.
Fada sosai malam ya dinga yima lameen din irin wanda bai taba yi masa ba kan sakin samha da yayi,ya kuma hada harda iman din kan cewa ita ya kamata ta dinga controlling nasa,shine zata amsa sunan mace ta gari,ya kuma umarceshi da lallai lallai ya tashi a yanzu basai anjima ba,sadiqu ya rakashi biko.
Sosai hankalinsa ya tashi,ya cire hularsa ya aje yana satar kallon iman wadda kanta ke qasa batace komai ba bata kuma motsa ba,duka sun karanci inda hankalinsa ya karkata,sai malam din ya umarci iman din ta tashi tabar wajen
"Ka maida hankalinka ameenu,ka zama tsayayyen namiji bame bin umarnin matarsa ba"
"Kayi haquri malam,kada ka zargi iman ko kawota cikin batun nan,wlh bata da ruwa ko tsaki a ciki"
"Naji,ku tashi ku wuce nace" dolen dole lamin din ya miqe,sadiq ya rufa masa baya
"Ya kamata malam ya haqura haka,shi da kansa fa yaje gidansu yarinyar amma bakaga abinda sukayi masa ba,wai saidai kazo da kanka" kashe motar da yake shirin kunnawa yayi
"Malam din?" Ya tambaya cikin jin xafi
"Eh mana"
"To babu inda zani wallahi,bata kai wannan darajar ba" yayi maganar yana shirin bude motar sadiq ya danqo shi
"Kana qin zuwa laifi zai dawo kaina,ban gaya maka bane saboda kaqi zuwa,na gaya maka ne saboda koda kaje kaga wata fuska ta daban kayi haquri da hakan" da qyar ya shawo kan lameen din,wanda a qarshe yace saidai shi ya tuqasu,shikam baxai kaisu ba,lallabawa akeyi,haka sadiqun ya karba tuqin.
Sun jima sosai suna zaman jiran samhan,daga bisani sai gata ta fito,ta canza gaba daya tadan rame,ta kumayi duhu sai tsaho data qara,kamar wadda aka yiwa dole haka tazo ta zauna hannun kujera tana busa hanci,ita a lallai ba zata nuna masa ta damu dashi ba,ganin haka sai lamin din ya miqe tsaye,ya maida hularsa kanshi
"Malam ne ya aikoni nazo nayi bikonki......" Kafin ya qarasa ta juyo a fusace
"Indai sai ta hannun wanna munafukan tsaffin zan koma wallahi na haqura da aurenka har abada......" Gigitacciyar tsawa daya tabbatar ta isa har cikin gidansu ya daka mata
"Kika kuskura wannan qazamin bakin naki ya sake aibata mutane mafi daraja a rayuwata na rantse da sarin dake busamin numfashi saina zubda miki haqora.........tun daga sanda na sakeki kika fita daga sahun matata saboda dama ban dora miki idda ba,inda akwai sauran iddata a kanki da a yanzu zan cikashe miki sakinki daya da yayi ragowa shashasha,amma na godewa Allah daya sanya ban hada jikina da naki ba........wawiya kawai wanda iliminta bai amfana mata komai ba" daga haka yayi waje da mugun fushi,dole sadiq ya miqe ya bishi,zuciyarsa cike fal da mamakin hali da dabi'a irin na samha,lallai babu abinda zamuce da iyayenmu da suka tsaya tsayin daka suka bamu tarbiyya ganin daraja da kimar mutum sai godiya da fatan alkhairi.
Da kallo ta bishi,tana jin kamar ta dora hannu aka ta zunduna ihu,last chance da hope da take dashi shikenan ya qare?,me yasa batayi controlling fushinta ba?,me yasa bata iya yiwa harshenta waigi ba?,idan yaso in ta koma ayi duk wacce za'ayi ma
_Ni kuwa nace harshe dama mafarin dukkan wata nadama,indai baka iya controlling dinsa ba,Allah ya rabamu da sharrin harasunanmu_
[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 75
Koda iman ta koma falon innan sai tayi qoqarin sakewa tare da mai da komai ba komai ba,duk da cewa taji fitarsu zuwa bikon samha,ta sani cewa duk yadda takai ga so da qaunar lameen bata isa ta hanashi abunda Allah ya halasta masa ba,shi majin mace hudu ne,ko yau ko gobe,da dadi babu dadi,ba dawowar samha ce damuwarta ba,damuwarta ta samu adalci daga wajen ameen tsakaninta da samha,wanda bata haufi ko kadan a kan hakan.
Hirarsu sosai suke da matar ya sadiq wadda ta fahimci ciki gareta dan qarami,duk da hankalinta rabi da rabi ne,har zuwa sanda matar sadiq din ta tashi yin alwala,iman din kuma ta shiga daki wajen inna.
Hira ce ta barke tsakaninta da innar,tanata bata labarin abubuwan da suka faru da bata nan,idan innar ta manta wani abun mufida ta tuna mata,a nan taji zacan auren bushira da dr ahmad
"Aikin yaagana ne wannan,nima bansan yadda akai ta hadasu ba,jiya iyanzu ma bushiran tana nan muna ta hirarku,tana ga qorafin kuyi hijira kun bace bat a qasar nan" inna ta fada har cikin zuciyarta na haduwar auren dr da bushiran.
Dadi ya kama iman naji yadda innarta ke kewarta,a yanzu dukka wata soyyaya ta dawo tsakaninsu,gefe daya kuwa albarka kawai iman ta shiga sawa yaagana,saboda tayi abinda ya dace,an kuma aza qwarya a gurbinta,daga dr har bushira nagartattun mutane ne da suka dace da juna qwarai.
Aiken mufida inna tayi kitchen,sannan ta ajjiye abinda takeyi,ta zauna tana kallon iman bayan ta kirayi sunanta. Nasiha tayi mata sosai kan xaman aure,irin nasiha ta tsakanin uwa da 'ya,ta bude mata abu uwa sosai masu tarin yawa irin wanda basu taba maganarsa ba tsakaninta da innar
"duk yadda maeenu ke sanki akwai sanda zaku bata kiyi rashin dadi,ban yarda ki gayawa kowa ba koda jice,a matsayinki na mace kiyi amfani da hikina da baiwar da Allah ya bawa kowacce 'ya mace ki gyara natsalar,idan kika fuskanci tafi qarfinki ko akwai barna me yawa a ciki a sannan ne zaki nema shawarata,daga kaina kuma ban yarje miki ki gayawa kowa matsalarki ba,koda ya kuke da mutum.......Kada kice zaki dinga amfani da soyayyar da mijinki yakeyi miki ki sake jiki,ki barshi yana aikata ba dai dai ba,ko dorashi akan hanyar da zai tsira ranar gobe,na sani na kuma gani kan fuskarsa,soyayyar da yake miki tana da tarin yawan data wuce ma yadda muke hasashe,kiyi qoqarin amfani da wannan damar ki dinga dorashi kan hanyar data dace" sosai maganganun inna suka shigeta,suka kuma sanyata fidda qwalla,ta kama hannun inna tana mata godiya tare da sake neman gafararta,daga bisani tare suka fito daga dakin sukaci gaba da sabgarsu.
Shuru har yamma lis babu 'yan biko babu dalilinsu😂,abinda basu sani ba tuni mahaifiyar samha ta kira malam da kanta,tace ya jawa lamin kunne,aure babu dole,bashi ba 'yarta,malam baice komai ba har ta gama ta kashe wayar,abinda ya sake sanyayar masa da jiki kenan.
'yar halak bushira sai gata kuwa,iman tasha tsiya tasha tsiya,tun tana ramawa har bakinta yayi shuru,uwa uba kuma ga mayen zazzabin yammar nan da yake yawan rufeta ya fara sako kai,saidai hirar da suka dinga yi tadan rage mata jin zazzabin,ta kuma dauke mata kewar lameen din da take tayi tun dazu,sai takejinta yau duk wani iri,wuni guda bata jita a jikinsa ba rungume cikin faffadan qirjin nan nasa na alfarma dake cire mata duk wani damuwa da fargaba,daga qarshe dai daki dole ta koma saboda zazzabin,tabar bushira da matar sadiq suna ci gaba da hirarsu.
Kwance tayi saman gado,zuciyarta tayi nisa a kewa da tunanin mijinta,cikin hancinta ta fara shaqo qamshinsa,tana bude idanu kuwa shidinne a tsaye,sai ya bude mata hannayensa gaba daya,batayi sanya ba kuwa ta garzayo ta fada,ya maida.hannunsa ya rungumeta tsam yana sansanarta
"How was your day?"
"So boring " ta amsa masa tana yatsina fuska,idanunsa ya fiddo waje
"Beside inna da malam din?" Kunya saita kamata ta boye fuskarta a qirjinsa,abinda ke zuciyarta ne kawai tayi subutar baki ya fito,dariya ya qyalqyale mata dashi kafin ya dagata sama ya juyata,ya kuma ajjiyeta kan madubi yana kalln fuskarta
"Don't be shy.......gaskiyar cikin zuciyarki kenan,nima kuma banajin akwai wani sauran waje a duniya da zanje naji dadin kasancewa a wajen ba tare dake ba.....oya.... pack your stuff mu wuce gidanmu" shi ya tayata suka tattare kayanta,sai gasu a falo da shirin tafiya.
Inna dai dauke kai tayi tayi kitchen tana cewa su tsaya a zuba musu tuwo su wuce dashi
"Kinaso baby?" Ya tambayeta,ta gyada kai,mufida ce ta biyosu dashi,bushira tayo musu rakiya har bakin mota tana yiwa iman tsiya qasa qasa yadda ameen bazaiji ba,don tanajin nauyinsa da girmamashi,ba zataso yaji ba,bushira da bata qyaleta ba saida iman din takai mata duka sannan taja baya tana daga mata hannu.
Yana driving amma yana riqe da hannunta,bai boye mata komai ba kan abinda ya faru gidansu samha
"Allah ya gani dukkanmu munyi iya yinmu,mun kuma fita haqqinsu" ya fadi,saita lumshe idanu kawai,bazatace taji dadi ba,saboda kimar aure,amma ranta bau baci ba,duba da cin kashin data yiwa mutanen datafiso inna da malam
"Allah ya zaba abinda yafi alkhairi"
"Ai yama zaba din in sha Allahu tunda akayi haka"
"Baby,asibiti zamu wuce fa,jikinki yayi zafi da yawa" maqale kafada tayi
"Ka siyon paracetamol kawai ya isa" kansa ya jijiiga
"Ban yarda ba,nifa nafi yarda da cewa cikine Allah" yadda ya dage yasa ta yarda a siyo paracetamol din,sanna ya hado mata da pt strip ta gwada fitsarinta da kanta a gida.
Shuru sukayi dukkaninsu kowa ya zubawa strip din idanu sanda suka fiddoshi daga cikin fitsarin bayan sun idar da sallar asuba,dubanta iman din yayi
"Ki tabbatar fa saikin bani alqawarina indai nine nayi winning cikine" idanunta ta fara saukewa kan strip din kafin takai ga bashi amsa,tar layukan jajaye guda biyu suka bayyana radau,gabanta yadan fadi,ta dauke idanunta ta maida ga lamin,ashe shima ita yake kallo,sai ya dage mata girarsa guda biyun,fararen haqoransa dukka a waje saboda yadda murmushinsa da murna suka gaza boyuwa,ya zuba mata idanu,sai taji wani weakness na yakamata,zuciyarta ta karye,wai itama tahau turbar zama uwa kenan?,nan da wasu watanni zata zama uwa itama?,zata riqe danta ko 'yarta a hannunta?,qwalla ta taru ta cika Blue eyes dinta,saiya bude mata tafukan hannayensa ta shige ciki ya rufe yana sakin qaramar dariya cike da nishadi,hannunsa akan gadon bayanta yana shafawa a hankali yana jero kirari da godiya ga ubangiji,zamewa yayi ya durqusa a gabanta,ya kama dukka tafukan hannayenta yayi kissing tsakiyarsu
"Kin gama min komai hajaru,na yafe duk wani abu da kikace zaki bani,abu daya ne ya rage.....ki haifamin baby girl me kama dake"kai kawai take gyadawa
"Alhmadulillah" bakinta ya furta a sarari,sai suka sake rungume juna,qauna da soyayya abinda ke cikin yana hudasu tun basusan meye ba.
*******Tubali me kyau hadi da kyakkyawan dashe na harsashin kyakkywar mu'amalar auratayya ne a tsakanin lamin da iman,wani irin zama daya zama madubi abun kallo ga kowa,abun sha'awa kuma abun kwaikwayo,duk inda namiji jarumi kuma jajirtacce yake lameen yakai can,banbanci mabayanni iman ke gani,tsayayyen namiji da ya daukewa iyalinsa komai,ya hanasu kuka ko damuwa,ya hana zukatansu jin ciwo kewa ko kuma rashi na wani abu komai qanqantarsa,zallar zama na amana,zama na sanin daraja da kimar dan adam,iman ta sake gani ta kuma sake gasgata kudi da soyayya ba koma suke iya siyawa dan adam ba,daraja kima da dattako gami da sanin kima da darajarka yafi komai tsada da wahalar samu,tayi godiya ga Allah tayi sadaka me tarin yawa kan yadda ubangijinta ya fiddata daga mummunan ramin data afka,tana yima lameen kallon duniyarta koma muce rayuwata gaba daya,qauna ta haqiqa mara misali,wanda ashe a gida rabin rabinta ya fiddo ya nuna mata,a yanzune ya fiddata gaba daya,tsaftatacciyar qauna me cike da tsari da salo na daban.
Ya zame mata aljannar duniya,wannan yasa itama ta zame masa jin dadin rayuwarsa gaba daya,cikinta daya fara fitowa baisa ta gaza wajen yi masa komai ba,ta zame masa cikakkiyar mace ta gari,wadda duk inda hake duk yanayin da yake ciki kallon fuskarta ne kadai ke sauke masa nutsuwa da kwanciyar hankali,duk yadda takeson abu idan lameen bayaso ta barshi kenan,hakanan ko yaya ya nuna yanason abu to ta riqeshi kenan sai inda qarfinta ya qare.
Cikin wata kulawa ta musamman yake tattalinta da kuma rainon cikinta,gefe guda ta koma kan karatunta,ta bada hankalinta akai matuqa,ya bata dukka wani support don ganin ta samu kyakkyawan sakamako ganin suna kan gangara,watannu qalilan suka rage mata,sai Alla ya bata ciki mai sauqi,bata wuce zazzabi ko ciwon kai shine cutarta,sai kuma abincinta wanda kullum tuwone,wannan kuma sai ya zama dutyn inna,kullum sai tayi mata sabon tuwo,yaran dake mata aike a gidan suke jigilar karbowa,duk tuwon daa buqata shi inna zata mata,zaya yiwa lameen girki kala kala na burgewa,amma saidai ta tayashi zaman ci,haka zaici wataran yana tsokanarta,wataran yana tausaya mata sosai,yakam bata lokaci yana lissafo mata nau'in abinciccika ko zataji wanda take sha'awar ci yaje ya nemo mata duk inda za'a samu,saidai kawai ta tabe baki ko tasa dariya,wani lokaci tace....abu kaza ma ni sai naji kamar zanyi amai,wani lokaci yakai mata bugun wasa yace ta rainashi,ya zauna ya zayyano mata abincin yaruka kala kala amma tace masa amai ma taji,saidai tayita dariya ko tayi masa gwalo....haka rayuwarsu take,cike da barkwanci farinciki da girmama juna.
Sannu a hankali wani irin budi yaketa shigowa lameen harda sadiq dinma,kamfaninsu guda biyu kowanne wani irin kudi yake kawo musu naban mamaki,ba komai bane sirrin nasararsu face malam,wanda koda yaushe yake basu shawarwari na yadda zasu kaucewa duk wata hanya da zasu gamutsa halal da haram,duk wanda yayi hulda dasu sai ya dawo ya sake nemansu,saboda komai nasu cikin aminci inganci da amana suka dorashi.
Ameen mutum ne mai hannun kyauta da bayarwa,hakan ya sanya hatta danginsa dake jigawa sukasan lallai fa budi yazo,don kuwa bayan kowanne watanni baya wuce daya zuwa biyu sai yayi rabon kayan abinci kudi da sauran kayan buqatu,iman ta qarfafa masa gwiwa sosai,ta kuma sake dorashi ka wannan hayar,tunda babu abinda suka nema suka rasa a rayuwarsu,kafin kace meye saiga yaa baraka ta zama hajiya,gidanta baya abo da mabuqata da masu zuwa mata fadanci,dama kuma ita din mutum ce mai yawan alkhairi,tun bata dashi abun hannunta bai rufe nata idanu ba,sai kowa ya zama nata,daga dangi har maqota,sosai iman ta samu farinji da karbuwa dari bisa dari wajen dangin lamin,kamar xasu cinyeta saboda qauna da suke gwada mata,hakan kuma ya samo asali ne daga yadda bata qyamar su,tamaishesu kamar nata.
Hankali bai kwanta ba saida iman ta kammaka jarrabawarta gaba daya,ta gama school of nursing,komai ya tafi maya successful saboda taimako gwarzon miji na gari data samu,wanda a lokacin daya fuskanci cikin ya fara mata nauyi sai ya dauko mata usama,shike tuqata ya kaita,ya kuma dawo da ita,sai data kammala sanna usaman ya koma,bai jima a can ba ya sake dawowa nan shima,saboda BUK da lameen din ya samar masa,amma fir yaqi zaman gidan lameen din,ya dawo waje inna yayi zamansa,hakan sosai ya faranta ran inna,ko babu komai ta sake samun mutum a kusa da ita,ga usama ga mufida,gidan sai ya sake mata dadi.
Wata daya da gama makaranta bikin bushira ya tashi da dr ahmad,sosai dr din yayi mata bajinta ta nunawa,tabbas Alla ne yake qulla soyayya,todai ya qullata tsakanin bushira da dr ahmad din,tamkar dama tun da farko sun jima da fara son juna,ko kuma babu wanda suka fara so sai junansu.
Duk yadda iman taso ta gwangwaje a bikin malam al'ameen ya hana,wasi events dinma bai barta taje ba,tayi nacin tayi kukan amma fir yaqi,ya wuni a gida ya sanyata a gaba yana kallon abarsa,taka qararsa wajen amarya bushira amma saita gwaleta
"Kin fara nauyi iman,me zakizo kiyi,kun gama mana komai,sadaki ma ya lameen ne ya biya,ida kika lura ya ameen yana da kulle,yakamata ki saba da hakan ki daina damuwa" haka maganarta take,indai fita bata kama ta zama dole ba lameen din baya qaunarta,ya gwammace idan ya hanata yaga rata ya baci,sai ya zauna ranar ya tayata wuni,yakance
"Shikenan.....munyi one one ko?" Maganar bushira haka take,don haka sai ta saki ranta kawai ta shiga shirya masa dan abun sha da yafiso kafin ta gama girki.
Sanda ta kawo masa drinks din jawota yayi jikinsa ya azata saman cinyarsa
"Zo nan madam.....ki rufan asiri ki rage fushi da saurin kuka,kada ki haifan raguwar baby.....me idon mage" idon magen daya fada a shagwabe ya bata dariya a dole,saboda ya tuna mata zamanin quruciya,ya dinga tsokanarta sai data sake,sai datazo tashi qafa ta riqe
"Bari na baki albishir,ladan fushin da nasa akayi dani...." A kunne ya rada mata,saita zare ido ta kima hangame baki,fuskarta dauke da dariya
"Da gaske ya lamin....kace nayi shirin zama dr"
"In sha Allah" ya fada yana murmushi,gam ta qanqameshi tana masa godiya,sai kuma kukan farinciki ya qwace mata,yasan duk wani burinta wanda ta taba furtawa dama wanda bata taba furtawan ba, he's genius lameen din musamman akan duk wani abu daya shafeta
"Banda kuka queen...... stop it please" ya dinga fada yana shafar bayanta.
[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 76
Randa ta dawo daga raka bushira dakin mijinta,suna hanya ya daukota da kanshi a motarta kamar yadda shi ya kaita da kansa ya kuma jira ta gama duk uzurinta,yake gaya mata ya gama da issue din muneera,yanzu haka auren ya rabu,muneeran tana gida gaban iyayenta
"Zaku iya ci gaba da zumuncinku ta waya,ban hanaki ba,amma ban yarda ko sau daya tasan hanyar gidana bama bare gidana"
"As you wish sir" ta fada tana jin dadin taimakon muneera har qasan ranta,saboda ko babu komai muneeran ta sota da gaske,kawai wata qaddara ce tasa ra ingizata suka yita tafka kuskure,ko bai fada ba dama bata da sha'awar ci gaba da qawancensu,qawance na kusa da kusa,gwara daga nesa nesa,ita a yanzun a duniya qawayenta kuma aminanta guda biyu ne,ta farko innarta,ta biyu kuma busheera.
Lameen da kansa yaje ya dauko mata badi'a daga jigawa saboda ta dinga hutawa,tabbas ta samu hutu,shima kuma ya huta sosai,don sai data ce
"Ni ban gane wayon kawo badi:a ba,kanka ka yiwa aikin nan Allah honey" idanu ya lumshe yana murmushi,iman din ba zata gane yadda ta sake zama cikakkiyar mace ba.
"To nidai abun arziqi da alama bai karbeni ba,fisabilillahi,idan ma na huta to mene" ta motsa ya sake kanannadeta
"Tabbas Allah ya dubi zuciyata,ya kuma soni da rahama da ya hanani hadaki da kowacce mace,dako tantama banayi,zaiyi wuya na tsallake sahun mazan da zasu tashi da shanyayyen barin jiki......wallahi har yanzu iman baki gama sanin yadda nake jinkina a raina ba,abinda zai iya bayyana kawai kika gani,sauran saini da.mahaliccina da kuma zuciyata" duk sanda lameen din yayi mata magana irin wannan jin kanta take a sama,ta yarda da duk maganarsa,saboda tana gani a zahiri,wannan yasa take sakar masa ranta rayuwarta dama gangar jikinta yayi duk yadda yaso da ita.....to sai muce Allah ya raba lafiya hajara aya.
*_BAYAN SHEKARU_*
Tsaye motar tayi a qofar mayalwacin gate din gidan da yake mallakar malam ibrahim khalilu tana danna horn,maroon color ce mai matuqar kyau,yadda kuma take daukan idanu kawai ya isa ya gaya maka cewa sabuwa ce dal.
A hankali gate din ya fara motsawa gaba kafin ya yaye gaba daya,dan matashin yaron da ya doshi shekara goma sha biyu ya bayyana,sak PHOTOCOPY na MUHAMMAD AL'AMEEN mamallakin katafaren kamfanin IB COUTURE daya zagaye qasashen africa kaf sai dai daiku,kyakkyawar harabar gidan ta bayyana,mai tuqa motan ta motsata zuwa ciki,idanunta nakan gilashin mudubin motar tana hangen yaron sanda yake biyo bayan motar bayan ya maida gate din ya rufe.
Shi ya bude mata mota yana fadin
"Sannu da zuwa ummee" takalleshi da kyau,shi yasa koda yaushe yake sake kama ranta,ya debe halayen malam ya cakuda dana babansa,dabi'unsa na dattawa ne,yana matuqar qaunarta da kuma tausayinta,wannan shine first born dinsu
"Yauwa me sunan malam.....ya na ganka a nan?,kun gama musaffar ne?"
"Mun gama ummee,har malam din ma yadan kwanta ya huta" ya amsa mata yana zagayowa daya seat din yana debe mata takardunta da jakar data fita dasu,sannan ya zagayo inda take zaune tana qoqarin daga qafarta data maqale saboda tuqin datayi
"Ko na matso ki dafa ni ummee" ya fada a tausashe,ta kalleshi ta saki mirmushi,ya sani,aikin mahaifinsa ne wannan,wato yau da baya kusa shine zai karba masa
"A'ah,zan iya me sunan malam" sai tayi bismillah ta yunqura ta fito.
Dr iman ibrahim khalilu kenan,cikakkiyar likitar mata,kuma mamallakiyar asibitin nan dake aiki da tsarin addini wato AL_EMAN CHILDREN AND WOMEN HOSPITAL wanda yake duba mata da yara zalla,hakanan tun daga kan nurses da likitocin dake aiki qarqashin asibitin mata ne,tsiraru ne maza suma aikinsu bai shafi duba marasa lafiya ba,kamar masu share haraban asibiti da masu gadi da sauran wasu ayyukan.
Kallo daya zakayi mata kasan ta zama babbar mace,wadda ta gogu da ilimi da kuma wayewa,duk da tulelen cikin jikinta hakan bai hana kyanta da tsarin adonta me burgewa fitowa ba,komai nata classy ne,daga duba daya zaka karanci hakan.
Abinda ya fiddata yau din tana daga cikin ranakun da take zama cikin asibitinta,tana da office nata mai zaman kansa,tana kuma da selective ranaku guda biyu a sati da take zuwa asibitin,duka sauran kwanakin tana zaune a gida,badi'a da bushira na cikin masu kula mata da asibitin,suma kuma suna wasu ayyukan acan,uwa uba usama wanda gudanarwar asibitin ke hannunsa,lameen ne ya gina mata asibitin ya kuma danqa mata shi kyauta halas malak,lokacin data haifa masa yaronsa na uku wanda a yanzu cikin na biyar ne da ita,yara maza hudu reras gareta,cikin da akaci masa burin haifar diya mace kamar su sayo a kasuwa,kada ma lameen din yaji labari,tadan qara lokacin dawowarta akan yadda ta saba,saboda tsayawa da tayi duba muneera wadda itama haihuwa ko yau ko gobe,don sai ta haihu da wajen wata daya ma kafin ita ta haihu,to cikin nata ana tunanin yi mata cs ne saboda yadda babyn yake breech,muneeran ta samu tayi aure bayan shekara kusan uku da mutuwar wancan auren nata,daga qarshe dai tailor da take rainawa ta aura,cikin ma'aikatan dake aiki a IB COUTURE mallakin lameen din,saidai yana cikin ma'aikatan dake daukan albashi mai tsoka,shi kansa bai sani ba sai da auren ya tashi,ya gayyaci lameen din a matsayinsa na ogansa,kuma babban baqo a wajen,ya mata murna sosai saboda mudassir mutumin kirki ne,ya kuma gayawa iman a sanna,har ya barta taje mata yinin biki,daga qarshe bayan sun tare suka matsa ita da mudassir din dai sai da sukeje sukaga gidansu,komai dai dai wadaida,cikin rufin asiri,abun gwanin sha'awa game wadatar zuci.
"Su isma'eel fa?,sun dawo kuwa?" Ta tambayi mai sunan malam wanda ke take mata baya yadda dai lameen keyi mata har kullum,tana kutsa kai zuwa cikin gida wajen innarta
"A'ah basu dawo ba,naji abee ma yayi waya,idan anyi sallar magarib zaizo ya daukemu gaba daya" kai ta gyada don ya kirata ta gaya mata.
Ta samu inna rungume da falle fallen qur'ani tana dubawa,ta daga kanta tana amsa sallamar imanin tata,cike da kulawa
"Sannu" inna ta fada cikin nuna kulawa tana tattare alquraninta,dai dai sanda mai sunan malam ya dawo daga kitchen dauke da ruwa ya miqawa iman din,sai da yaga tasha sannan ya fice abinsu barsu da innar.
Inna da kanta ta hada mata ruwa mai dumi tace tayi wanka,sanna ta tayar da mufida dake bacci wadda zuwa yanzu ta zama budurwa,don zancan karbar kudin aurenta akeyi da usma dan yaa baraka,duk sun tsaya qumbiya qumbiya suna ta yiwa innar boye boye bayan kowa ya gama ganosu,ta shiryawa iman din abincin sannan ta zauna ta tayata ci,don wannan cikin acicine,komai ta samu ci take.
Suna tsaka da hirarsu hayaniya ta fara tashi daga harabar gidan
"To bismillah,da alama su isma'il sun dawo,kuma mawuyacine idan ba dasu maama fatima ta hadomin su ba(yaran sadiq,wanda su kuma su hudu ne,mai sunan inna itace maama kuma babbar,sai lailah....sai hanif,sai aslam shine qarami)" kafin inna ta rufe bakinta kuwa basawan nata suka bayyana cikin falon,isma'il ne mai kado kansu wanda shike bin mai sunan malam,sai Abdallah sajid,sai muhammad da suke cewa mamman,sai kuma yaran sadiq din,fatima matar sadiq tana biye dasu a baya dauke da aslam.
Falon kuwa ya kacame gaba daya,Allah ya taimakesu mai sunan malam ya leqo yace dukka suzo inji malam,basusan malam din yana gida ba,sai kuwa aka fara rige rigen fita zuwa wajen mlam din har ana karo da juna,sunsan kilishi ne ko zuma ko kudi zasu samo,alaqa me mai kyau da matuqar shaquwa tsakaninsu da malam din,yana matuqar ji da jikokin nasa kamar yadda suma sukeji dashi
"Alhmadlh,haba,maji kunnuwanmu,da alama basusan yana gidan ba dama" iman dake zare hannunta daga abinci ta fada.
Indai suka hadu tsakanin fatiman da ima basa jin kunne dama,da inna tayi iya tata hirar saita miqe ta barsu,suka kuwa dasa har sai da aka kira sallar magariba sannan suka wuce sallah.
Basu jima da idarwa ba aka kira cin abincin dare,saboda yau family din ya hadu,can babban falon malam.
Tunda suka shiga idanunta shi suka fara gani,shima nashi idanun ita suka fara gani,anacin abinci ana kuma taba hira cike da raha,harda malam din da inna,family ne mai ban sha'awa da qayatarwa,basuyi boko ba iyayen,amma suna bin tsarin koyarwar musulunci,wanda yafi na boko ban sha'awa tsari da kuma qayatarwa,shi yasa abubuwansu ke burge mutane da yawa.
Wata kulawa ta cikin ido ake bawa juna tsakanin iman da lameen din,amma a haka zaka zaci ita dashi kowa harkar gabansa yake idan ba kana da kula da bin qwaqwafi ba,basar dashi take,tasan sarai me yakeso,abubu biyu ne kuma duk sai taja masa rai a kai.
Shi ya fara janyewa daga cin abincin,ya koma gefe ya tsume yana gayawa yaran su hanzarta zasu wuce gida
"Nayi zaton dana gansu duka nan zasu kwana?sannan shi kansa takwara izifin qarshe na suratul baqaransa bai zauna masa sosai ba,so nake cikin watan nan ayi bikin haddarsa,sai amaisa hakali sosai ga isma'il" Malam ya fada yana dan duban lameen,sai lameen din ya shafa kansa,shi dama hakan yafiso,bayaso ne kawai yabar inna da bari bari shi yasa
"Ba wani abu malam,saisu kwana din,duk yadda kayi da ai ne" nan fa suka hau murna da tsalle dukkansu,don dama haka sukeso,ya zamana ya sadiq zai dauki matarsa da aslam,shima ya dauki iman din su wuce,su babu dan rakiya ma,tunda gaba dayansu babu me shan mama a cikinsu.
Tana hanya zafa wajen inna kiran bushia ya shigo mata,ta daga suka gaisa gaisuwa irin ta aminan juna,suka taba hira suka kuma tsokani juna sannan bushiran ta shaida mata birthday din hamdan danta,next week,ta godewa Allah da yaran basa kusa,da sai sun haukatata,saboda dama birthday din suketa jira,kasancewar lameen bai taba bari an yiwa kowa cikin yaransa ba,ta tayata murna tace kuma za'a kawosu in sha Allah ko su taho ma gaba daya,sukayi sallama tana tsokanarta daa
"A gaida yallabai baban soyayya" dariya tasake
"Zaiji kuwa"
"Ba daga bakina ba pls bama 'yar haka dashi,kada mutuncina ya zube"
"Saiko na fada" ta katse wayar tana dariya.
Kira ya dinga jera mata a waya bayan gama wayarsu da bushira,yana mota yana jiranta,da qyar ta baro cikin gidan ta fito,tana shigowa kuwa ya cukuikuyeta amma a tausashe,ta saki qaramar qara a shagwabe
"Saboda kinsan ke daya nakeson kasancewa dake shine kike jamin rai ko?" Fari ta sakar masa murmushi na kubce mata
"Idan bakai wasa ba wankan gida zan taho wannan karon ma"
"Saiki shirya dakin xaman mutum biyu"dariya ta qwace mata a boye,tasan tun haihuwarta ta hudu yace an daina wannan,ya gaji da zaman tuzunrantakar da yakeyi,ta tsokaneshi kan yayi aure,yace mata saidai tayo masa auren dole idan ta isa
"Ya ake ciki?,kuma ki gayan gaskiya me aka gani?,banda baqin da mukayi yau dama so nayi ayi agabana kada amin rufa rufa" ya tambayeta sanda motar ke fita daga gidan,kanta ta kawar gefe
"Abinda dai aka saba"
"Uhmmm....me kenan?"
"Namiji ne" hannunta dake cikin nashi ya matsa,wanda dama ya saba al'adarsa ce,duk sanda yake tuqi tana gefansa to hannunta cikin nashi yake,qara tadan saki a tausashe
"Macace in sha Allah" lafiyayyen murmushine ya kubce masa
"Yes!....alhamdulillahi rabbil Aalamin,nima na kusa samun photography din me idon mage" ya fada yana dariya cikin nishadi,harara mai cike da qauna ta jefa masa
"Idanun nan na qaramin shauqi a kanki iman,saika tara mutum million da wuya zaka samu daya mai irinsa,yadda kike special haka komai naki yake.....Allah ka san irin son da nakewa wannan halitta,Allah ka bani tsahon rayuwa tare da ita" murmushi ya kubce mata,a kullum kalaman da takeji daga bakin lameen,tana tunanin ko daga yanzu zai daina gaya mata su sun isheta rayuwa.
"Ya Allah.....kaga yadda wannan bawa nake yake kula da baiwarka iman,yake kuma qoqarin cika burikanta da faranta mata ita da iyalinta,ya Allah kada ka barshi haka,kayi riqo hannayensa,ka zama ji da ganinsa,ka zama gatansa,ka yalwata kabarin iyayensa kasa kuma dukka alkhairansa ga jama'ar gari da iyalansa ya zamana sadaqatul jariya ga iyayensa batare daka rage lada ko daya daga cikin ladan da zaka bashi ba"
"Ameen" ya amsa yana lumshe idanu,duk da tuqi yake amma sai daya janyota jikinsa yana buga kafadarta,zai iya cewa babu mace kamar iman duk fadin duniya,addu'ar datake masa ko mahaifiyarsa iyakarta zatayi masa
"Me dame ya faru wunin yau...." Ya tambayeta yana jifarta da murmushin dako yaushe yake saukar mata da nutsuwa.
Wannan kusan al'adarsu ce,duk lokacin da suka wuni da daddare kowa yana baiwa dan uwansa labarin abubuwa masu muhimmanci da suka faru ko ya aiwatar a wunin,sake rage kaifin muyarta tayi,muruar da take wa lameen hira ko bashi labari ta banbanta da muryoyin datake magana da kowa,saita tabbatar ta qwatata yadda zata saukar masa da shauqinta da kuma cikakkiyar nutsuwa,cikin wani irin sanyi ta fara zayyano masa,yana saurarenta yana lumshe idanu,saboda dadin muryar tata tafi labarin dadi,cikin zuciyarsa yana tasbihi ga Allah da kyautar iman da yayi masa halak malak
*ALHAMDULILLAHI RABBIL ALAMEEEEN*👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽
*_Anan na kawo qarshen labarina mai suna BUTULU KUFAN WUTA,,ina fatan kurakuren dake ciki Allah ya yafe mana_*
*_fatan alkhairi a gareku zafafa customers,muna fatan qananun laifuffuka da kura kurai da aka samu a ciki zakuyi mana afuwa,Allah ya qara danqon qauna da zumunci,team zafafa biyar na godiya da jinjina muku qwarai_*
*Inda aka manta ba'ayi conclusion ba ajizanci ne irin na dan adam,Allah ya sadamu da alkhairi,ya kuma hada fuskokinmu da alkhairi a rubutu na gaba*
*Subhanakallahumma wabi hamdika,ash hadu an la'ilaha illa anta,astagfiruka wa'a tubu ilaika*👏🏽👏🏽👏🏽
72
. Awa daya da wasu 'yan tsirarin mintuna suka sauka a garin lagos din,sun sauka cikin yanayi na lullumi harda ma tsarabar yayyafi,tunda suka sauka har zuwa cikin motar hannayensu na sarqafe da juna,tana cikin jikin lamin din wanda hakan yake sake kunnashi,a hakan ya dinga nuna mata wurare,sun wurwuce unguwanni da dama,duk inda suka wuce din kuma sai yayi mata bayanin wajen,ta bude idanu kuwa tana kallon bigiren da bata sanshi ba,xuciyarta cike da mamakin yadda lamin din yasan Lagos har haka.
A hankali suka fada wata unguwa,unguwace mai kyau dai dai gwargwado da kuma tsari,babu cinkoso babu kuma yawaitar jama'a,gidajenta moderate ne masu ban sha'awa,hakanan birji ne a tsakiyar layin,har suka qarasa qofar wani dan madaidaicin plate house mai dauke da qaramin gate.
Lamin dinne ya fara fita ya bude qofar gidan da maqullin da drivern ya bashi,sannan ya dawo ya bude mata murfin motar ta fito,yana riqe da hannun nata dai ya tura qofar gidan suka shige.
'yar madaidaiciyar haraba zaka fara tararwa wadda bata wuce shan iska ba,don ta yiwa mota kadan,saidai qawace take da shuke shuke da kuma marble tiles masu kyau da daukan idanu,da gani kasan baa jima da kammala ginin gidan ba,qaramin balcony ke kallonka,wanda a ciki qofar parlor ne,kana buda qofar falon zaka samu madaidaicin falo da akayi masifar qawatashi kamar ba gobe,a cikinsa akwai qofar kitchen,dining area mai dauke da dining mai kujeru hudu,sai bedrooms guda biyu.
"Zauna ina zuwa" ya fada yana juyawa zuwa waje,a nutse iman ta zauna saman kujerun falon masu azabar kyau,tana sake kallon gidan,ya burgeta qwarai da gaske,komai nashi bai cika yawa ba kamar yadda baiyi qaranci ba.
Tana nan zaune ya shigo da jakarsu,sannan ya duba agogo
"Akwai sauran lokaci,me ya kamata yanzu muyi?,gidan babu komai a cikinsa,zanje na samar mana kayan amfani" rau rau tayi da idanunta,sabida jin cewa zai fita ya barta a baqon wajen dako minti goma cikakke batayi a cikinsa ba,takowa yayi gabanta
"Karki damu, you are safe,zan rufeki ta waje,idan na dawo zan bude da kaina,ga bedrooms nan ki zaba wanda nayi miki" ya sunkuya a tausashe yayi kissing forehead dinta,ya danyi waving mata hannyensa sannan ya fita,ta rakashi da addu'a yana amsa mata.
Duk da atsorace take amma sai dafa dudduba kitchen da dakunan,komai lafiya lau kamar dama can ansan da zuwansu,sai kawai ta janyo jakankuna biyun daya shigo dasu ta bude,ta fara fidda musu kayansu tana jerawa a daya daga cikin bedroom din data zaba,bayan ta gama jera nata a dayan shima ta fara shirya masa nashi a daya dakin,duk kayansa da zata daga sai wani qamshi ya ziyarci hancinta,kamar dama ca kayan da turare aka qirqiresu.
Awa daya da rabi aikin ya dauketa,tana fitowa daga bedroom din yana buda qofar falon,idanunshi a kanta,sai yayi mata nuni data koma ciki,shi da wani yaro ne,tana jinsu suna shiga da kayan store har suka gama ya sallameshi sannan ya cimmata a daki,tana tsaye bakin window tana kallon kyakkyawar harabar gidan.
Ta baya ya rungumota yana axa fuskarsa saman kafadarta,sannan ya zagayo da hannayensa saman shafaffen cikinta yayi mata qawanya
"Ina fata gidan yayi miki?" Kai ta gyada a kunyace
"Anan nake fata zamu axa harsashin tubalin ginin kyakkyawar rayuwar auratayya mai inganci....kin shirya?" Kan ta sake gyada masa murmushi yana kubce mata
"Good" ya fada cikin jin dadi da kuma wani irin shauqi
"Muje ki duba kayan kiga abinda babu a ciki" tana duba kayan tana mamakin yadda yasan kayan amfanin gida haka,kusan shi ya dinga jera kayan a duk inda suka dace,ita din 'yar tayi kawai ta zama,a hakan ma dai a takure take,yana sane sai ya taba wani wajen ko wani sashen daga gareta,amma sai ya narke ya hade hannayensa waje daya yace
"Am sorry" wani abun ta rasa me zatayi,wani kuma kunya ta daureta gaba daya,har suka gama,zuwa sannan lokacin sallar magariba ya shiga,ya buqaci taje tayi wanka tazo suyi sallah.
Ruwa me zafi ta hada saboda yadda takejin dan sanyi sanyi a garin saboda yayyafin da aketa yi tun zuwansu,taji dadin dumin ruwan hakan yasa ta jima a bandakin ba tare da ta ankara ba,ta hade da alwala sannan ta fito.
ta dauki minti kusan hudu tana goge lemar jikinta,sannan ta daga kanta da nufin qarasawa bakin madubi ta samu mai ta shafawa jikinta,saidai wanda ta gani zaune saman madubin harde da hannayensa ya zuba mata idanu yayi matuqar razanata.
Lameen ne,yayi bala'in kyau cikin wani lallausan yadi gray color kamar ba dare ba,baqar hula ce a kansa,kamar yadda qafarsa ke sanye da baqaqen takalma mai budadden sama,fadin irin kyan da yayi ma bata bakine,sexy eyes dinsa a bude tarwai a kanta,da hanzari ta soma komawa da baya da nufin komawa toilet,saidai ina,yana saukowa daga saman madubin,taku uku ya cimmata,batasan ta kaucewa qofar toilet din ba sai data ji ta dunguri bango,cak ta tsaya,ya riga ya cimmata,duk da cewa akwai yar tazara a tsakaninsu amma bata da shaawar motsawa,saboda yadda idanunsa ke yawo a jikinta tun daga sama zuwa qasa,ta tabbatar ko yaya ta motsa akwai matsala,ta gwammaci ci gaba da tsaiwa a haka.
Ci gaba yayi da sauke idanunsa kowanne sashe na jikinsa da idanunsa zasu iya kaiwa,karo na farko tsahon rayuwarsu daya taba ganinta cikin yanayi makamancin haka,kasala ta soma saukar masa tare da wani irin shauqi dake fusgarsa,shuqin da bai taba jin makamancinsa ba,gefe guda kuma yana karantar irin rudewar da tayi,abun sai ya bashi wani nau'i na nishadi sa dariya,baisan me yasa taji tsoron ganinsa ba,yanason sake ganin tsoronta irin haka muraran,ko zamanin quruciya idan iman din ta rude fuskarta kan masa kyau qwarai,don haka ya qara kusancin dake tsakaninsu,har sai daya zamana babu wani sauran space ko na taku daya daya rage a tsakaninsu.
A hankali ya sanya hannunsa saman towel din dake tattare a qirjinta, intentionally yayi hakan da niyyar tunzura tsoronta,amma sai yaji ashe abun ya girmimi tunaninsa,cikin rashin sani ya shafi qirjinta,abinda yasa ta sake razana,ta kama towel din ta riqe tam,tanason ta kalleshi ta roqeshi ya bari amma ta kasa,akwai girma a faruwar lamari irin wannan,ya lameen da take matuqar girmamawa da yi masa kallon yaya a wajenta,koda bassam ba zata iya tuna rana daya data taba bayyana tsiraicinta a gabansa ba,yo inama ta ganshi?.
Sulalewa ta samu tayi,tana kaiwa qasa saita cure waje daya,a boye ya saki murmushi,ya taka da baya ya dauko.kayan da yaga ta ajjiye saman gadon,da alama su zata saka ya ajjiye mata a gabanta,dai dai lokacin da akayi knocking qofar falo,sai ya juya zuwa bakin qofar yana cewa
"Ki saka kayanki" ya buda qofar ya fita,abinda ya bata damar miqewa da hanzari ta koma toilet zuciyarta na bugawa,komai zai fara tsakaninta da ya lameen daga tsammanin mafarki zuwa gaskiya,tana ji a jikinta tabbas zuwa yanzu komai gaske ne,ya kuma gama tabbata.
Da takeaway ya dawo a hannunsa na abinci idonsa na dubanta kamar zata bace masa
"You look so cute my queen" ya fada ta hanyar motsa labbansa kawai,hakan ya sanya furucin ya fita a hankali. Bandaki ya shiga ya sabunta alwalarsa ya dawo sukayi sallah,sannan ya gabatar musu da abincin sukaci a mazubi daya kamar yadda ya sabar musu.
"Ayimin afuwa,fitace ta kamani,akwai saqo da zan karba,banajin zan fita har nan da one week,shi yasa dole a daren nan na fita na karba saqon,sako hijabinki ki rakani,i promise you ba zamu dade ba" itakam dadin hakan taji,sai ta koma ciki,ta laluba kayanta ta samu hijab,ta zura hade da plate takalmi ta fito.
Tunda ta fara takowa ya zuba mata idanu,hannunsa zube a aljihunsa yana qare mata kallo,komai ta saka kyau yake mata,komai ta raba da jikinta sai ya haska ta,ya Allah......" Ya fadi yana lumshe idanunsa,kana ya bude mata qirjinsa ta hanyar wara hannayensa yayi welcoming nata kafin su wuce tana rabe da kafadarsa.
A qofar gidan suka samu mota yana jiransu suka shiga seat din baya ita dashi manne da juna,ko yanzun ma bayani tare da nunnuna mata gurare yaketayi,lallai lagos babban garine da aka ci gaba,har suka je suka dawo,duk da a mota ya barta ya karba saqon amma taji dadin fitar.
Koda suka dawo din shirin barci kawai sukayi,dakin ya dauki wani duhu mai cakude da dim light mai kyau,yadda gidan da garin ya dauki shuru haka dakin,tana a cikin jikinsa idanunsa a lumshe,yanata qoqarin danne zuciyarsa saboda ya bata damar hutawa a daren yau,yana jin dumin numfashinta cikin jikinsa ya gyara mata kwanciya sosai,da qyar ya samu bacci ya daukeshi.
************Washegari garin a lullube da hadari suka tashi,weather din da ya haifar da wani yanayi me dadi a jiki da zuciya,yanayin kuma ya dace da sabbin masoya irinsu.
Tun daga safiyar ya fara bude mata aiki,muraran ya fara bayyana mata waye lameen da irin rayuwar da yake sha'awar yi da iyalinsa,tare suka hada breakfast,suka gyara wajen,wajen wanka ta shige toilet kafin ta gama rufewa ya mamayeta,zatayi magana sai tsintar kanta tayi male male cikin bathtub,bata gama wannan alhinin ba yasa hannu guda ya zare towel din da yayi saura a jikinta,ta qanqame waje daya,sai yayi relax cikin ruwan yana qarewa fuskarta kallo,jikinsa ya saki gaba daya,zuciyarsa na gaya masa ya aikata kawai,daren da yake tunani bazai iya kaiwa ba,saidai akwai sauran abubuwa da yakeso ta fuskanta daga wajensa kafin sannan,idanunsa suka sauka ga duk wata siffa da baiwa ta jikinta da Allah yayi mata ta cikin ruwan da yake garai garai,tsigar jikinsa ta zuba,yaji kamar numfashinsa zai wuce,cikin ransa gana dayanta Allah da idanuwansa basu taba kaiwa ga jikin wata 'ya mace kamar haka ba,sai a yau daya samu halalinsa
"Imaaaannnn" ya ambaci sunanta da wata murya me nauyi,a shagwabe tana shirin sakin kuka ta amsa masa,abunda ya sake tunzurashi kenan,ya zame kadan cikin ruwan,ya kamota zuwa cikin jikinsa sosai ya dorata saman ruwan cikinsa,abinda yaso ta wuce da numfashinsu gaba daya shi da ita,saboda yadda kowanne sashe na jikinsu ya hadu dana dan uwansa,wata ajiyar zuciya me hade da sheshsheqa ya saki kamar wanda numfashinsa ke shirin kufce masa,wani shock mai bala'in qarfi ya ziyarci kowanne sashe na jikin iman din,dukka wata juriya da yakejin yana da ita ta fara kwaranyewa,jikinsa ya fara daukan zafi da chargy,sai ya kamo fuskarta cikin tafuka hannayensa,kiran sunanta yakeson ya sakeyi amma ya kasa,sai kawai ya hade bakunansu waje guda ya kai tsaye ya laluba harshenta ya sanya cikin bakinsa.
Wani zazzafan kiss da ya sake iza wutar da suke ciki ya fara aika mata,cikin salon na ar qwarewa da sanin sirrikan rura wutar soyyaya cikin zuciyar masoyi,salo mai tsafta da kuma tafi da hankali,tuni iman din ta narke masa itama,hakan ya bashi damar sakin fuskarta ya maida hannayensa zuwa wani muhallin na daban cikin sassan jikinta,lokaci guda gaba dayansu suka rude suka kuma fita a hayyacinsu shi da ita,gaba daya ji yake bathtub din yayi masa kadan,sannan he's not comfortable,don haka ya lallaba cikin mutuwar jiki ya dauki iman din cak suka baro toilet din.
Kasa qarasawa gadon sukayi dukansu,suka zube bakin gadon yana ci gaba da charger mata kwanya gaba daya,komai yayi zafi ya kuma kai geji,yakai iya limit din da baya buqatar komai sai kasancewa da ita,duk wani guri dake tsole masa idanu sai da hannunsa yakai,ya gusar da ishirwarsa ya kuma morema wajen son ransa,duk da cikin fitar hayyaci yake amma ya lura da wasu abubuwa tattare da uman din,wadanda suke alamta masa kamar batasan kowa ba cikin rayuwarta,kamar komai bai canza ba daga jikinta,amma bashi da tabbaci saboda yana ganin mawuyacin abune hakan ta kasance,sake hobbasan mai data saman gadon sosai yayi kana yayi mata rumfa,yana ci gaba da aike mata zafafan saqonni masu gusar da hankali tare da neman hanyar da zai maidata mallakinsa ta har abada,sai a sanna iman ta farga.....sai a sannan ta gane cewa lallai game din ya canza salo......sa a sannan tasan komai yana shirin canzawa ne,hankalinta yaso dawowa jikinta,tasa hannu da niyyar dakatar dashi,saidai shima nasa hannun yasa yakauda nata,gami da matseshi sosai cikin nasa tafukan hannayen yana girgiza mata kai alamun a'a,gaba daya kamanninsa sun sauya,farar fuskarsa tayi jazur kamar yadda tata tayi
"Bismillah,Allahumma jannib nash shaidan,w jannibash shaidana ma razaqtana" addu'ar da fiyayyen halitta ya koyarwa ma'aurata kenan yayin da zasu kasance da iyalinsu,saboda koda ubangiji ya qaddara samun qaruwa shaidan bazai iya cutar da wannan abunda aka samun ba,addu'ar data sanya iman fashewa da kuka,kukan kuma daya fita lokaci guda da azabar data fara ratsata.
Daga ita har lameen babu wanda yake tantance halin da dan uwansa ke ciki,azabar daga dinga ratsata da kukan da.takeyi da kuma kalaman neman afuwa da suke fita a bakinta kawai take iya tantancewa,yayin da lameen din kuma ya rasa cikin wacce duniya yake,sama sama kunnuwansa suke jiye masa kukan iman din,amma ya gaza controlling kansa,burinsa kawai ya cimma gaci,gacin da ya daukeshi wasu mintuna kafin yakai inda yakeson kaiwan,ya saki wani sauti mai qarfi yana matse iman gammm a jikinsa kamar zai tsagata gida biyu,kana yayi wani irin laushi gumi na jiqa ilahirin jikinsa kamar wanda aka yiwa wanka da ruwa.
Zare jikinsa yayi yakoma gefan iman din,yanajin yadda bugun zuciyarsa har yanzu bai daidaita ba,a tausashe yaja iman din cikin jikinsa sosai
"Subhana man khalaqal khalqa wa'ahsahum adad,subhana man laisa lahu sharikun fil mulk,subhanal lahil azim...subhana man laisa ka mislihi shai'un" kalama daya dinga fada kenan murya can qasa,wasu hawaye na sauka ta gefan idanunsa,ya tadda abinda bai taba tunanin zai sameshi ba tattare da iman din,lallai wannan hikima da baiwa ce daga ubangiji yayi masa ita,yasa bakinsa a tausashe ya ajjiye mata kiss dake dauke da nannauyan saqo a saman goshinta,sannan yasa hannunsa yana tattare mata gashin fuskarta,fuskarta ta fito sosai,gaba daya tayi jazur,idanuwanta dukka sun tasa alamun kukan datayi masa ba dan kadan bane,take tausayinta ya kamashi,ya soma tuna yadda take neman agajin inna da malam,yasa yatsansa guda daya yana goge damshin hawayen dake kan fuskarta
"Iman" ya kira sunanta a hankali cikin rada,maimakon ta bude idanun nata,sai yaga ta sake runtsesu gam.
Dumin da yaji daga gefen cinyoyinsa yasa yadan ja da baya kadan yana dubawa,jini ne ta wajen daya bata inda suke kwancen,abinda yadan tsoratashi kenan
"Subhanallah" ya fada yana kwantar da iman din tare da janyewa yana duban wajen,sai ya suturta jikinsa sannan ya dawo wajen iman din
"Iman" ya sake kiranta,saidai bata amsa masa ba kamar wancan karon,hakan yasa ya sauko daga saman gadon,lallai dole yasan yayi aikin lallashi,don gaba daya taja bargon daya rufe mata jikinta dashi ta lulluba har saman kanta,zagayowa yayi daga side din data maida fuskarta,ya durqusa gaban gadon
"Iman.....am sorry kiyi haquri don Allah" duk da yanayin azabar da take ciki,da kuma boyayyen kukan da takeyi ta cikin bargon sai dataji kalmar tayi mata girma,yaa lameen da bata haquri?
"Don Allah iman..... please talk to me mana" nan ma kasa bashi amsa tayi
"Ba zaki ce komai ba?" Kai kawai ta girgiza,duk da ciwon da take ji a jikinta,amma babban abinda yafi damunta ayanzu baisan ba zataya iya sake hada ido dashi bane har abada,ta yaya zata iya sake kallon yaa lameen din?,su hada ido dashi har kuma ma suyi magana ko suci gaba da mu'amala.
"Me kakeso?" Tafada da wata dasashiyar muryar dako ba'a gaya maka ba kasan tasha kuka yadda ya kamata
"Ki tashi please na duba barnar da nayi hankalina sai yafi kwanciya,kema kuma ki tashi ki gyara jikinki" tanajin ko sama da qasa zasu hadu ba zata miqe a gabansa ba
"Kaje zan tashi" ta amsa masa tana sake cukuikuye kanta,sam maganar bata kwanta masa ba,ya tabbatar mawuyacine ta iya tashin da kanta
"Zaki iya?" Ya fada damuwa na bayyanuwa saman kanta
"Eh" ta amsa masa,dan jim yayi kafin yace
"Is ok" sannan ya miqe daga tsugunnon da yayi,saidai maimakon ya fita saiya nufi qofar toilet da suka barta a wangale dazun,yadan turota kadan ya labe daga bayanta.
Minti kusan hudu ta bayar,sai data daina jin motsinsa sannan ta yaye bargon,a hankali ta miqe ta zauna tana ciza lebe,a matsayinta name karatun jinya tasan ciwuka taji a gurin ba shakka,saita matso da jikinta gaba a hankali da niyyar tashi.
Wata qara ta saki ta koma ta zauna sanda tayi yunqurin tashin,ya saki murmushi yana fitowa daga maboyarsa,duka saita rude,tana shirin komawa ta kwanta ya qaraso,daukar cak yayi mata tana boye kanta cikin jikinsa,bai damu ko kula da wannan ba ya wuce toilet da ita.
Next Chapter

Leave a comment

Post
Comments

112201018644657456668
Yaa rabb kabawa du wata diya mace musulma damar kai mutuncinta dakin auranta
2 hours ago

dadaummi1
❤️❤️❤️
3 hours ago

Contact Us
Arewa Books Publishers
WhatsApp: 09031774742
Email: [email protected]
Navigation
Home
About
FAQ's
Legal
Privacy Policy
Terms of Service
Social


Copyright 2021, Arewa Books | ALL RIGHTS RESERVED | Powered by thinkcrypt.io
"
https://arewabooks.com/chapter?id=62d6a0a47fc1109aa6133b68#:~:text=Chapter%2073-,Shafi%20na%20saba%27in%20da%20biyu,ko%20kula%20da%20wannan%20ba%20ya%20wuce%20toilet%20da%20ita.,-Next%20Chapter
[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 73
Wata nutsuwa ce ke sauka a zukatan kowannensu sanda suka kammala sallar azahar,ameen din yaja musu dogayen addu'o'i wanda suke dauke da kalaman yabo da jinjina ga ubangiji da kuma nema tabarrakinsa kan zamantakewarsu,a nutse ya shafa addu'ar sannan ya juyo inda iman ke zaune,kanta a qasa,tana jin nauyi ko yaya ta motsa,idan ta tuna abubuwan da suka faru tun daga zamantowarsu abu daya da lameen da kuma yadda ya tusata a bandaki ya gasata sai taji inama qasa zata tsage ta shige ciki.
Dab da ita ya sake matsowa,ya kama goshinta yayi mata addu'ar nan da annabi ya umarci kowanne ango ya kama goshin amaryarsa yayi mata
"Allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi,wa'azubika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi" ya zare hannunsa daga kan nata,maimakon ya sauke hannun qasa sai ya kamo nata hannayen duka,ya riqesu a tausashe yana kallon tsakiyar qwayar idanunta bayan ya matso sosai dab da ita,har gwiwoyinsu yana gogar juna,cikin wata murya dake cike da taushi zallar shauqi da qauna ya soma magana
"Kin bani komai,kin kuma gama min komai hajar.....ban mallaki abinda zan iya saka miki dashi ba,saidai ina fatan na zamo mafi alkhairin miji,kuma miji na gari da babu tamkarsa,babu sauran abinda ya rage da zan sakawa inna da malam illa addu'ar samun aljanna madaukakiya....sun ingantamin rayuwata,sun maidani cikakken mutum,basu barni a haka ba sai da suka haifamin mata gangariya,wadda zata zamo waje hutu da sanyin idaniya a gareni,duk kalmar da zan fada miki kan irin qaunar dake cikin raina....inajin kamar na ragewa soyayyarki marta bane,fatana ki rayu dani kamar yadda na alqawartawa kaina duk wuya duk dadi zan rayu dake,ki rufemin sirrina iman......banso ko sau daya tak ki kai qarana wajen inna ko malam.....banaso suji shakka ko susa a kaina,ko meye nayi miki ki zaunar dani ki gayan,idan nine keda laifi in sha Allah zan dauki laifina zan kuma nema afuwarki na gyara.....idan kece kuma zan nusar dake cikin salon daya dace wanda zai gamsar dake da kuma zuciyarki da izinin Allah... and lastly......iman" Sai ya sauke numfashi yana sake matsa hannuwanta
"Na'am" ta amsa masa tana sake gujewa kallonsa
"Kalli qwayar idanuna" sosai taji saukar maganar tasa da nauyi a kanta,wannan umarin nasa yayi mata nauyi da yawa,wai me yasa yake acting like babu ma wani abu da yafaru?.
"I said look into my eyes" a hankali kamar mai ciwon wuya ta daga kanta zuwa idanun nasa kamar yadda ya buqata,take kuwa magnet din dake ciki ya jata sosai
"Ni mutum ne dake qaunar caring,inason matata ta soni sosai,kada ta raba kulawa ko soyayyar da takemin da kowa....koda yaran da zamu haifa ne,ki bani soyayyarki ni kuma nayi zan basu tawa soyayyar,nasan zata wadatar dasu in sha Allah.....kinyi alqawari?" Duk da yadda ya aza mata nauyin idanu dana maganarsa,amma haka ta bashi tabbacin da yakeson ji
"Ina fata ubangiji ya qadarta samun rabu a wannan haduwa tamu" ya fada hannayensa asama,maganar data sanyata qarasa dunqulewa waje daya cike da kunya,ya miqe yana dariya ya dagata ya rungumeta cikin dariyarsa yana ci gaba da murmushi,yau dai iman baki ya mutu murus.
Wunin ranar wani wuni ne daya ajjiye dimbin tarihi cikin rayuwar aurensu,ya koma sake kafa wata sassanyar soyayya a zukatansu,ta wani bangaren kuma soyayya me zafi,ta sake sanin abubuwa masu yawa game da ameen din,tarihin rayuwarsa na zahiri tun yana qaraminsa almajirtarsa da fadowarsa hannun malam,hakanan itama ya bata dama a sanda kanta yake kwance saman cinyarsa ta bashi labarin abubuwa da dama da bai sani ba,ciki harda zaman aurenta da bassam.
Shuru yayi abun yana tabashi,hannunsa saman lallausan gashinta yana wasa dashi,komai Allah ke tsarashi ya kuma kawoshi a sanda ya dace,yana can cikin ciwo da zafin soyayya.....ubangijinsa kuma ya dubeshi yana ta yi masa tanadi irin wanda ya dace dashi
"I suffered a lot iman......ban zaci soyayyarki zata barni na rayu ba,amma alhamdulillah,na godewa Allah" shuru tayi tana jinsa,murmushi kwance kan fuskarta,taji tarin kalamai daga bakin lameen wadanda bata tabajin masu zaqi da gardinsu ba,taji irin girman matsayin da take dashi a wajen lameen din,wanda ko kusa bata taba kawoshi kusa cikin ranta kan tana dashi ba,tabbas inda ace ana buda zuciyad mutum aga meke ciki,da bata gujewa lameen din ba,saidai kuma bawa baya taba tsallakewa rubutacciyar qaddararsa.
Washegari tadanji dama dama a jikinta,saboda tabs din data rubuta lameen din ya samo mata su,hakanan shi ya dinha dawainiyar gasata da kanshi,duk da yadda kunya ke dawainiya da ita amma ya murje idanunsa fes,tana kukan shagwaba yana tayata,haka suka dinga yi akai akai,har sai data narke masa da gasken ta gaji.
A hankali take takowa zuwa falon din a daren washegari,tayi masifar kyau cikin wata straight gown data fidda shape dinta sosai,idanunsa na akanta sanda take iskoshi,wani abu daketa motsa masa ya sake motsawa cikin jikinsa,sai ya miqa mata hannu ya mata nuni data taho,bata taba lokacin ba kuwa ta taho ya kuma yi mata kyakkyawan mazauni saman cinyarsa,ya kuma bude qirjinsa ya lullubeta a ciki.
Cikin wuyanta ya cusa fuskarsa yana shinshinarta,launin idanunsa da kuma yanayin saukar numfashinsa yana sauyawa,tun daga wuyanta ya gangaro kunnenta,ya kuma juyo da ita sosai ya cusa kansa tsakanin qirjinta numfashinsa na qara gudu wajen fita da dawowa,a hankali ya soma yawo da hannayensa cikin jikinta,ya fara aike mata sa saqonni,abunda ya rudata ta riqe hannayensa,cikin rudu take girgiza masa kai
"Yaa lameenn...."
"Anty imann......." Ya tari numfashinta shima da sauri kafin ta qarasa fadin abinda zata fada din,yadda taga ya birkice yasa ta kwantar da kanta sama kafadarsa kawai cike da fargaba,tasan laifi da zunubin yiwa miji musu ba tun yau ba,bugun zuciyarta na qaruwa,tana saddaqarwa cewa lallai tata ta qare,har yanzu akwai sauran jinya tattare da ita,hakanan bata manta wuyar da tasha a hannunsa ba.
Sosai yake ya mutsata kamar wani mayunwacin zaki,sai wani numfashi da yake fitarwa kamar gurnani,ita kanta sai daya rudata sosai,zuwa wasu mintuna ya qanqameta kamar zai tsaga cinyarsa ya sakata,sai kuma ya zameta daga saman cinyar tasa ya zaunar da ita yana cewa
"Ina zuwa" a hankali ya taka ya shige daya daga cikin dakunan,da kallo ta bishi har ya bacewa ganinta,saita maida idanunta ta lumshe,ita kanta dukka jikinta ya amsa,duk da cewa a tsorace take da wahalar da tasha a jiya.
Kusan mintuna ashiri sannan ya dawo,da alamu wanka yayi,idanuwanshi a kanta,bai tsaya ko ina ba sai dab da ita,yasa hannu ya shafi saman kanta ya zarce qirjinta,sannan ya maida kansa saman kafadarta ya kwantar,kamar sabon marayan daya rasa mahaifansa
"Queen,inajin sai kinyi haquri da yaa lameen dinki.....bazan boye miki ba,tun ba yau ba nasan ina cikin nau'in mutane mabuqata,abinda ya dinga wahalar dani,saidai na godewa Allah daya dinga bani kariya,har kawo yanzu da ya rabautani da halaliyata" sarqafe hannayensu yayi waje guda
"Kinyi alqawari zaki kula dani....wannan ma zai shiga ciki?" Cike da qwarin gwiwa ga gyada kai
"I will do my best in sha Allah" cikin jikinsa ya sanyata tana mata godiya har taji nauyin hakan.
A daren ya sake koyar da ita wasu sabbain darussa,qaramae akwati guda na wasu irin sexy dresses ya ajjiye,yana daga kwance saman gadon tana saka masa yana gani yana zabar wadanda yake so,wasu idan ta sakasu kamar tayi yaya don kunya,sau tari idan ta gwada wasu duqewa take a wajen ta kasa miqewa,wasu baya ne a kwashe,wasu tsakiyar ciki zuwa cinyoyi,komai a bayyane,bata taba sanin ya lameen din cikakken dan duniya bane sai sannan,ashe kallon kitse akewa rogo,fitina ce fal cikinsa a yanzu yake sauke mata ita.....ni kuwa nace banga laifinsa ba,illar dama kaje baga halalinka na,amma idan halili ne to falillahil hamdu.
Daga qarshe kuwa kasa ci gaba da gwajin tayi,gaba daya kunya ta durqusar da ita,da mabayyanin murmushinsa yataso ya dagata cak dama ya raina daukanta tuntuni
"Idan ina da hali zance kiyimin yawo cikin gidana daga ke sai fatar jikinki,ke kadai Allah ya halastamin iman,kuma dake daya nakeso na rayu" dole dai duk yadda taso masa rowa haka ta bada kai bori ya hau,duk da yayi mata fami qwarai,amma da sauqi akan na jiyan,sannan a yau din tadan dauki haske,ta kuma fahimci wasu abubuwan.
Washegari wajen sha daya na safe tana cikin jikinsa,suna zaune saman kujera yayi relaxing bayansa da makarin kujerar,santala santalan qafafunsa a miqe saman dan table,iman din sanye da wata 'yar fingilar shirt short sleeve,fara ce qal kuma robber,hakan ya sanya ta dameta dai dai size na jikinta,ta kuma fidda kowanne shape nata,wandon jikinta shima haka yake,iyakae tsahonsa gwiwa,ta gyara gashinta cikin farin band jelar ta sauka kafadarta ta hagu,tuntuni ta sani white is favorite color na ameen,don ko a sannan din shima kayan jikinsa farare ne
"Matso ki gani"yayi maganar yana rage sautin tv din dake aiki,kana ya jawo tab dinsa wadda a yanzu da ita yake amfani,tunda ya kashe wayoyinsa,ta maqale sosai kuwa cikin jikinsa tana kallon fuskar tab din daya dauko.
Fasa bude tab din yayi,ya waiwayo ya dubeta,dai dai sanda itama ta daga kanta suka hada idanu
"Fisabilillahi haka akeyi,yanzun kuma nace zan dana asamin kuka?,bayan tun daxu fuska kawai nakeyi?" Da sauri ta dagashi tana turo baki
"To ba kaine kace nazo na gani ba" ta fada a shagwabe tana karya wuya,abinda ya tuna masa da iman din zamm dinta,murmushi ya qwace masa,ya kuma tarota sanda take qoqarin sauka a jikinsa
"Zo mana,zo kiji 'yar qanwata,zo mu sasanta" saiya miqe ya zauna sosai bayan ya ajjiye tab din daga gefansa
"Muyi ban gishiri na baka manda mana,kidan sanmin ko babu yawa kinji" yayi maganar idanunsa cikin nata,launin idanun nasa suna canzawa,da alama da gaske kenan yake,abinda ya tsorata iman ta fiddo idanu
"Yaa....."
"Shshshsh" yayi maganar yana dora yatsansa saman lebansa
"Babu wani yaya....na soke wannan sunan,kiji dani imani ta" kuka ta sakar masa,at least dai yau ai ta huta,ta kuma sanya ran zata huta din,saidai yau dinma tana ji tana gani ya mata wayo ya karba abunsa,tana jikinsa tana masa kuka wanda ke cakude da shagwaba,shi kuwa yana aikin lallashi,hannunsa saman kanta
"Kiyi haquri....kullum sake ninka min qaunarki da sha'awarki ake,babu abinda ke raguwa,keta dabance iman,wallahi da na zauna da wata tabbas dana fada cikin mazan da Allah zai tuhuma,banajin zan iya hadaki da wata mace na kuma yi muku adalci,sonki a jina na yake,bazai taba gushewa ba...." Duk wata tabararta haka ya dauketa sai toilet,tare sukayi wanka sannan suka dawo ya dauko tab din ya fara nuna mata abinda zai nuna mata daxun.
Wasu selective places ne best for honeymoon cikin garin lagos,da pictures dinsu da bayanansu,ya bata daman zaban guri har guda hudu da zasuje,biyu a ciki zasuyi sati daddaya a can,sauran kuma kwana uku uku ne.
Sanda taketa murna binta kawai yake da kallo,farincikinta kadai ya wadatar dashi,inda yana da wani abun da zai sata farinciki sama da haka daya bata,yana jin iman din takai masa ko ina cikin rayuwarsa,hatta fitar numfashinsa ya tabbatar yana fita ne da so da qaunar iman din.
Cikin kwanaki da kuma wuraren da suka zaba din zasuje sun gudanar da gagarumun honeymoon wanda dukkaninsu basa jin zai gushe cikin tarihin rayuwarsu,wata wutar soyayya ce sosai ta kunnu cikin zukatansu da kuma ruhinsu,sun sake dinkewa sun zama abu daya,ta sake sanin waye lamin.....shima ya sake sanin wace iman a badininta,tayi kuka aboye a bayan idanunsa da nadamar gudunsa data tabayi a cikin rayuwarta,tabbas inda tana da qarfin ikon maida lokaci baya ta shafe wancan abun data aikata,ashe wata tarin qoramar zumar soyayya ce take jiranta ta debi kashi ta watsa mata cikin rashin sani da wauta,dukka wani caring da soyayya da take mafarkin samu cikin rayuwarta ta samu sama da haka daga wajen ameen din,ashe ba kudi bane jin dadi?,ashe ba kyau bane soyayya?,ashe ba kudi bane qauna zaman lafiya da kwanciyar hankali?,da gaske duk sanda bawa ya bijirewa zabin Allah,sai Allahn ya barshi da zabinsa yaje yayita wahala,ta godewa Allah daya zabar mata tsayayyun iyaye kuma nagartattu.
Fadin yadda iman ta sake mamaye rayuwarsa ma wannan bata bakine,a kullum ya saka goshinsa a qasa zai roqa musu dawwamammen zaman lafiya da zuria dayyiba,burinsa a yanzu a rayuwa shine ya rayu da iman din har abada,ta kuma tara masa iyali masu yawa,mutum ne shi maison yara qwarai da gaske,kuma ita kanta iman din ta sani.
Suna tsaka da honeymoon din issue na bude kamfanin saida spare parts na motocin da yake shirin yi ya taso, issue din ya taso gadan gadan,dole suka dawo gida,dama kwanaki biyu ne suka rage masa.
A lokacinne suka sake gasgatawa kansu daya bazai iya rayuwa ba saida dayan,fitar da yake da safe ya dawo da yammaci liqis dukkansu shi da ita galabaita suke da kewar juna,dole ba don ya shirya ba ya siya mata layin waya,idan ya fita suna maqale da juna ta waya,duk da haka wataran bai gamsar dashi sai ya yanke abinda yakeyi yazo ya ganta sannan zai koma,aikin me wahala da cin rai,saboda su sona son kafin ya samu license yabar kamfanin a nan Lagos,shi kuma ba wanna ya tsara ba,yanaso kamfanin ya zama a arewa cikin garin kano,bazai bar wannan damar da kuma alfanun da dubba matasa zasu samu na samun aiki ya qare a can ba,bayan ga jama'arsa suna da buqata,ya kashe gida ya raya jeji,yasha wahala dasu sosai kafin ya samu komai ya dai daita,aka kuma sahale masan yayi a gida kanon dabo,cikin qanqanin lokaci komai ya kammala cike da nasara,ya kuma siya dukka wasu kaya da za'a buqata ya aikosu kano,a sannan ya shirya musu qarashen honeymoon dinsu,suka raqashe da kyau,sannan suka fara shirin dawowa gida kuma,iman murna kamar tayi me,kwanaki kadan suka rage su cika watanni uku a lagos din,tayi kewar inna,dole ta haqura kiran gida duk da akwai waya a hannunta,saboda lamin yace yanaso su huce sosai kafin su tunkaresu.
Wani irin kyau iman din tayi,ta sake fari ta cika tayi fresh da ita,duba daya zakayi mata kasan ta samu dukkan wani jin dadi da kulawa da ya kamata diya mace ta samu daga wajen miji,tabbas a yanzu a duniya babu abinda ta nema ta rasa,ko yaushe tattalinta ameen din yake kamar yadda itama ta zage damtse tana tattalin mijinta da dukan wani nau'in kulawa da tasan yanaso,zaiji dadi hakanan ransa zaiyi fari.
Wata mahaukaciyar siyayya lameen din ya dinga mata kamar baisan ciwon kudinsa ba,ta dade da sanin mutum ne shi mai kyauta da abun hannunsa,amma kuma sam bashi da almubazzaranci ko barnatar da kudin a inda bashi da alfanu,anan ya hada mata kayan lefe jimilla na kece raini,ya kuma qara mata da wasu kayayyakin da ita kanta wani abun batasan yadda zatayi dashi ba,soyayyar gaskiya tayi.....babu abinda ke raya soyayya irin kulawa nuna damuwa da masoyi a cikin kowanne irin hali.[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 74
Ana ya gobe zasu tafi ya fidda ita wani eatery mai tsada,yace ta zabi dukka nau'in abinda takeso,bayan ya yiwa wani waiter na wajen magana kan su kawo menu.
Tunda daya daga cikin ma'aikatan wajen mata ta doso wajen idanun lameen a kanta
"Ya fa'alul lima yurid"ya furta can qasan zuciyarsa,idan idanunsa ba qarya sukayi masa ba,ko kuma mantata yayi ba munira yake gani sanye da uniform din ma'aikatan wajen,ta sauke abinci a wani table tana dosu nasu table din dauke da menu din a hannunta,idanunsa ya dauke ya maida ga iman,sam bata lura da tahowarta ba,sai yaja da baya ya miqe
"Ina zuwa queen" sai ya duqa yayi kissing nata forehead sannan ya taka zuwa wani sashe nesa kadan dasu
"Good day madam" muryar munira ta fita cike da girmamawa tana dora menu din kan table.
Da hanzari iman ta daga kai saboda jin muryar da ko a barci ta tashi zata canki ta wacece,munira ce tsaye a gabanta,ta saje da ma'aikatan eatery din,idanu dukkaninsu suka fitar,kowa yana mamakin ganin dan uwansa a wajen,kusan lokaci daya suka ambaci sunan juna,sa munira ta fashe da kuka,abinda yasa iman tayi saurin miqewa kenan ta rungumeta
"Muneera.....kece muneera?zauna" iman ta fada tana gyara mata kujera daya da sauri,zare jikinta tayi da sauri
"Aah,zamana a nan wajen zai jawomin matsala idan har aka ganni....muje tacan baya,akwai labarai iman" miqewa iman din tayi tabi muniran,tana qarewa muniran kallo,gaba daya ta canza ta lalace,idan har kasan asali munira kanka tsaye zaka fadi haka,a haka ma da sauran gayunta tunda babban gidan abinci ne,dole sai da tsafta da kuma gayu,idan ba haka ba korarka ma zasuyi.
Hankalin lameen dake zaune can nesa dasu ya dauko sanda yaga tana jan iman din zuwa can bayan wajen cin abincin,a nutse yake binsu a baya ba tare da sun sani ba,sai dayaga waje suka canza,sannan ya koma can baya yana monitoring nasu ta inda bazaiji sirrinsu ko abinda suke tattaunawa ba,bai matsa daga wajen ba saboda bawa iman din tasa kariya.
"Ba'a yiwa Allah wayo iman,kuma duk sanda bawa ya matsa kan samun zabinsa ba zabin Allah ba,Alla zai barshi da wayonsa ne yayita wahala,kwanaki da muka hadu dake nace miki bikina za'ayi iman,akwai abinda ban gaya miki ba kafin zuwan bikin,nayi saurayi mai dan datawar shekaru,yana bala'in sona,yana kuma da kudi yadda nakeso,saidai matsalar bai cika sharadi biyu cikin sharadaina ba,na farko yana da mata da yara,na biyu kuma yayimin shekaru da yawa,na dinga wulaqantashi qarshema naci masa mutunci muka rabu,ba'a jima ba fallelen yaro ya fito min,ya hada komai irin yadda nakeso,muka shiga soyayya gadan gadan,ya kuma shiga kashemin kudi babu qaqqautawa,kullum mune yawon shopping,gidan cin abinci iri iri,cinema kullum muna a hanya,duk abinda na buqata zan samu saidai idan ban buqata ba,hausawa sukace kwadayi mabudin wahala da kuma wulaqanci,a irin wannan fice ficen da mukeyi dashi a mota,kwatsam ranar mun dawo daga shipping,ya siyomin iphone 13promax,ina cike da murna yace na rakashi gidansu zai karbo saqo wajen mummy dinsa saimu wuce zai siya min wasu set na gold dana gani ana yayi,yace basai na shiga ba,nayi xamana a mota,da murnata na amsa masa da to,muna zuwa ya bude ya shiga gidan,minti wajen goma saiga wayarsa
"Na samu mummy bata jin dadi muneera,tana kwance zazzabi ya kada ita,daure ki shigo kiyi mata sannu saimu wuce" ya fake da qaryar da ko baimin hidima irin haka ba zanji nauyin cewa bazan shiga ga,da kwadayi da qaramar qwaqwalwa irin tawa na saka kai cikin gidan,ashe tarko RUFA'I ya dana min,a ranar ya samu yayimin fyade na rashin imani,yana gamawa saiga alhaji mando ya shigo mutumin da na wulaqanta
"Ba'a tabani a zauna lafiya,wannan shine sakamakon wulaqantani da kikayi,maga waye zai dauki saura,idan kin rasa mai dauka ki dawo zan taimakeki na dauka a haka na qarasa quruciyarki,nine naturo rufa'i,donshi ba kowa bane face yaron dakemin aikace aikace,na bashi dukka kudin da xai isa yayimin wannan aikin,idan kin gama zaman jinyar ki rufe gidan" haka suka tafi suka barni,bayan ya kwashe duk siyayyar da yayimin dama a mota na barta tunda naga shiga kawai zamuyi mu fito.
Na shiga matuqar tashin hankali iman,saidai daga bisani sabbin qawayena da nake tare dasu suka kwantarmin da hankali,suka kuma gayan kada na wani damu,akwai dabaru da ake da magungunan da zaki koma gam kamar yarinya qarama,abinda ya kwantar min da hankalina kenan,na bude sabon shafin rayuwata,naci gaba da zabe da kuma laluben wanda zan aura,lokaci yanata quremin,damarmaki nata zuwa gabana amma idanuna ya rufe,sai daga bisani irin taste dina yazo wato FAISAL.
Faisal yazomin da dukka wasu burika da sharudda nawa da nakeso ya cika,ya cikasu fiye da kima,yaxomin da fuskar babansa wani shahararren attajiri ne da gaba daya ba'a qasata Nigeria suke zaune ba,ya nunan gurare da kamfanoni masu tarin yawa da sunan nasu ne,a gabana yazo da takardun wasu kamfanoni guda biyu ya sauke sunansu ya maida sunana saboda son da yakemin,a ranar naji duk duniya nafi kowacce mace sa'a a rayuwarta,tunda faisal ke zuwa bai taba zuwa da mamaicin mota kaya ko waya ba,hakanan ya sanyani na zabi tsala tsalan motoci har biyu ya shaidan su xan fara hawa daga randa na amsa sunan matarsa,fadi miki irin abubuwan da rufa'i yazomin dasu iman kanki zai daure,don lefe ma cewa yayi ana daura aure zamu dage dubai daga can mu zarce china,acan zan hada duk kayan lefen da nakeso,kayan daki da za'a yimin cewa yayi na karba kudina nayi sabgar gabana dasu,don shi ya saka wani kamfani daga turkey suna mana designs din da ko shugaban qasar nigeria bai taba kwana a kai ba,na jarabtu da wata muguwar soyayya tashi,har bana gane dai dai da ba dai dai ba,hakana bana sauraren duk wanda zaizo min da magana akansa musamman ta suka ko zagi.
Naso na taba kama faisal,na ganshi a hanya yana tafiyar qafa,gaba daya jikinsa ba irin suturar dana saba ganinsa da ita bane,na kira sunansa sai naga bai juyo ba,nasha gabansa ina nuna masa kaina amma sai ya nuna bai taba ganina ba,harshe ha juya ma ya fara yimin yarbanci,ya balbaleni da fada cikin harshen yarbanci har yaso taramin jama'a,abinda yasa jikina yayi sanyi kenan naja baya ya wuce abinsa,har sanda ya wuce din yanata masifa yana nunani da hannu.
Washegari sai gashi yazo a faisal din dana sanshi,maganar dana fara yi masa kenan,amma sai ya nuna zallar mammaki
"Kece mutum ta uku data taba cewa taga wannan bawan Allan,ni kaina da ban taba ganinsa ba mamaki nakeyi sosai,ance sak ni,saidai shi yaren yarbanci yakeyi"
"Exactly" na fada da sauri,zuciyata na gasgata faisal,saboda yadda naga zallar shima mamaki kan fuskarsa
"Ba matsala,zan saka escort dina su lalubomin shi,nima dai naga mekama dani" dariya nayi,na kuma ce
"Ai ikon Allah yafi gaban haka" daga wannan muka shiga wata hirar ta daban.
Bai gane dukka wasu magangu da ayyukan faisal qarya bane,ban gane duk wani magana nashi plan bane,ban gane rami ya shirya min ba sai randa aka kaini gidan faisal,madadin a shiga dani kai tsaye zuwa ainihin ginin tanqamemen gidan,sai akayi boys quarters dani,kowa mamaki da al'ajabi ya cikashi na wannan juyin juya halin,matar gida a boys quarter?,tarin cincirindon qawayena irina 'yan qarya,harda ma wadanda hayarsu nayo su qawar qawa saboda su fidda bikina a duniya,duk haka suka tafi suka barni cikin tashin hankali da mamaki,amma mayaudariyar zuciyata gayamin takeyi wataqila don kada a bata masa gida yasa yayi wannan dabarar,saboda yasha gayan shi mutum ne mai tsafta,amma bai cika son jama'a ba,da wannan na share nayi zamana,ina kallon boys quarter din da yake kamar kango,babu komai sai katifa da labule.
Sanda ango ya iso shi daya kamar maye,da shaddarsa tun ta wajen daurin aure,zan tarbeshi ya matsa
"Dakata.....dakata,opay ce,tanayin squeezing kin jawomin jangwangwama,saina qara dubu biyu akan yadda na karbo aronta,shi yasa tun daxu na kasa sakewa na zauna na sake,sai yawo nake a tsaye kamar wanda ya hadiyi tabarya" uban mamakin daya cika ni yasa na sandare a tsaye,ya zare rigar ya zauna ya bata lokaci ya ninketa tsaf,harda zama akai wai don tafi komawa dai dai,sai daya gama duka sannan ya fuskanceni.yana yaqen baki,zuwa sannan duk wani noti a jikina ya kwance,na gama sallamawa
"Faisal,ka gayamin waye kai"
"Yanzu kuwa,cikakken sunana shine haladu murtala,kuma haifaffen qauyen namuduka ne can iyaka da garin kano,ci rani ya kawoni na hadu da wayyayun abokai wanda suka taba jana zuwa wata dinner,a nan na ganki.na nuna inasonki kika yarfani harda guzurin mari" yana fadar haka fuskarsa ta dawomin tar da kuma abinda ya faru a lokacin,wanda har ga Allah a inda akayi abun s nan na bar batun,na mance da fuskarsa bare abinda ya faru
"Wannan yasa naci alwashin saina rama,kuma saina mallakeki kota halin yaya,nayi bincike a kanki na samo komai,na shigeki.ta yadda kikeso,yanzu gashi na sameki,duk da naji jiki na kashe kudadena sosai,amma babu komai tunda burina ya cika kuma zan fanshe" ina kuka ina komai haladu na sha'aninsa,a daren ya kwanta dani abunsa,babu kazar amarci ko lemon fata na naira 30 ban gani ba,yana gama abinda xaiyi dani ya haureni da qafarsa na fado qasa
"Shegiya tsinanna,girman kan banza ne,ashe fanko ce?,duk wannan wahalar da nasha?,to billhillazi saikin maido min duka abinda na kashe,kuma aure yanxu aka fara bazan sakeki ba" duk da cikin azaba nake amma mamaki ya cikani,saboda nasan anyimin duk wani gyara da zai maidani mace,ko a jikina inajin na matse gam,to amma komai na Allah daban yake,idan ya tafi ya tafi kenan,babu wanda ya isa yayi halitta irin ta ubangiji koshi waye.
Kwananmu uku cikin wannan gida dana fuskanci na uban gidansa ne dake rayuwa a lagos,a kwana na ukun da sassafe naga yana hada kayanmu waje daya,dama nawa kayan da nazo dasu ne daga gida,don ba lefe ba batunsa
"Lagos zamu tafi ci rani,na samo miki aiki a gidan cin abinci,zakiyi aiki harki hadan kudadena dana kashe,na saida gonakina da gidajena na gado duka a qauyenmu saboda ke,to wa billahi bani haqura saikin dawomin dasu" inaji inagani ya kawoni nan,ya kuma danqani a hannunsu yace a sanyamin idanu sosai idan aka ganni da wasu,saboda ni din bin maza ne dani" kuka muneera ta sake sosai,bama ita kadai ba harda iman din
"Inasu mamee,me yasa bazaki sanar musu ba"
"Ya karbe wayata tuntuni,amma na taba satar wayarsa na kirasu,abun mamaki wallahi iman na kasa gaya musu komai,yazo ya sameni a haka yayita dariya,dama nasan zaa rina,shi yasa nayi maganinki,duk wani naki da nasan zaki gaya masa.matsalarki nasa an rufe bakinki,tashi ki ban waje,hakkin mazan da kika zalunta kika ciwa kudi baki auresu bane.....wannan ne abinda ya gayan"
Kukan daya hangi iman din tanayi yasa hankalinsa ya tashi,ya gaza daurewa ya tako a hankali zuwa inda suke,babu wanda yaji zuwansa,sai hannunsa da iman ta gani qasan habarta yana tare digar hawayenta dake shirin sauka qasa
"Meye haka queen?" Maganar data ja hankalinsu,muneera ta bishi da kallo,iman kuwa ta rungume hannunsa tana sake sakin kuka,a hankali ya dagata ya sanyata a jikinsa,a kunne ya gaya mata
"Da nasan kuka zata saki bazan bata damar ganinki ba,muje" da sauri iman ta balle jakarta,ta fiddo dukka kudin ciki ta ajjiyewa munera
"Zan nemeki munira,kiyi haquri" binsu da kallo tayi,har xuwa sanda taga sun bude motarsu sun shige,kanta ya daure matuqa,lamin ne dai haka?,lamin din data rabasu da iman din?.
Cikin mota tana kuka sosai tana baiwa lameen din dukka labarin da iman din ta bata
"Mu taimaketa don Allah honey bee"
"Zan duba" amsar daya bata kenan a taqaice,kafin ya sake waiwayawa yana dubanta
"Amma indai kikaci gaba da wannan kukan,babu abinda zanyi a kai" da sauri tahau goge hawayen,duk da zuciyarta a karye take,munira na cikin masifa qwarai.
************
Jirgin safiya suka bi zuwa gida kanon dabo,cuie da tarin nasarori cikin rayuwarsu ta kowanne fuska ta kuma kowanne fanni,tun a cikin mota iman fake kwance laqwas cikin jikinsa,a hankali ya dora hannunsa saman fuskarta
"Are you okay Baby queen......?" Kai ta gyada masa kawai,saboda cike take da fargabar abinda zai faru tsakaninsu da malam
"Amma duk da hakan kamar jikinki akwai dumi,tun jiya nayi noticing hakan"
"Kaman yanayin weather ne daya juya" dan bata rai yayi cikin wasa yana dubanta
"Kada kicemin haka mana please,ba wani weather,baby ne,ajiyata ce" dariya ce ta qwace mata,ta rasa wanne irin son yara lamin din ke dashi,abinda duka duka satinta uku kenan da ganin period dinta har yake zancan baby?,....gabanta ne yadan fadi data tuna cewa ranar ovulation day dinta sun samu intercourse dashi,kuma lallai komai zai iya faruwa ba,sai tayi shuru tana irgen kwanakin,tare da laluban canje canjen da takeji ajikinta,saidai ta rasa ko guda daya a ciki,bata jin canjin komai,kawai dai daga shekaran jiya jiya zuwa yau dukin jikinta ya qaru ba kamar yadda yake normal ba.
Suna isa gida lameen ya shirya su wuce wajensu malam kai tsaye,itama da wannan zumudin ta iso,saidai tana fitowa a wanka barci yayi awon gaba da ita,ba ita ta tashi ba sai gefin azahar.
A gefanta ta sameshi zaune yanata calculation da lissafe lissafe na wasu kudi,suna hada idanu ya sakar mata murmushi wanda ta kasa fahimtar me yake nufi
"Sannu baby"
"Don Allah ya lameenn.....bafa haka mukayi dakai ba" lumsassun idanunsa ya zaro mata yana dubanta
"Me kuma nayi?"
"Gida fa kace zamuje wajen malam" tana kaiwa nan sai kuka ya qwace mata,ba lameen kadai ba,ita kanta abun sai ya bata mamaki.
A mamakance ya taso ya riqeta sosai ya sanyata cikin jikinsa yana shafa bayanta
"Akan wannan kike kuka?,to ya isa,tashi kisa kayanki mutafi" sai daya dan jima yana lallashinta sannan tayi shuru tana sauke ajiyar zuciya,shi ya taimaka mata ta shirya duk don ya saukar da ita,koma bayan daa da ota ke gaimala masan ya shirya idan zai fita,suyita rigima tana jan gashinsa kan cewa har yau baby ne bai gama iya shirin office da kansa ba,duk gyara daya punishment nasa zai bata hot kisses both kumatunta guda biyun,batasan wayo yake mata ba,shi hakan yafi masa komai dadi a rayuwarsa,shi yasa idan ta gyara masa abu gobe idan yazo bashi zaiyi ba,yana sane zai canza ko kuma yayi ba dai dai ba,moments da suke spending kafin ya fita aiki yana daya daga cikin memorable and sweet moments a rayuwarsa da bazai taba mancewa dasu ba,ya fuskanci zuciyarta a kusa take,ajiyar zuciya taketa saukarwa,don haka ya dinga lallabata har ta gama nata shirin sannan yayi nasa,cikin wani yadin kufta da aka zubawa aiki irin na matasan zamani dake ji da kudi da ilimi,kalar yadin kalar kayan dake jikin iman dinne,sai gasu sun fito fess dasu,best couple ever.
A harabar gidan taga yana yunqurin bude wata sabuwar mota,mamaki ya cikata,saboda batasan da ita ba,hakanan sanda suka shigo gidan bata lura da ita ba,sai da suka shiga sannan ya dubeta bayan ya furta "alhamdulillahil lazi bini'imatihi tatimmus salihat"
"Ma sha Allah,tayi kyau honey"
"Taki ce dama" ya fada yana murmushi,idanu ta zaro cikin mamaki
"Da gaske?"
"Da gasken gaske,na taba yi miki qarya?"
"Ko sau daya yaya na...." Farinciki na wanzuwa saman fuskarta
"ta yaya zan nuna godiyata ma a gareka?"
"Ki haifamin babies masu kama dake da zasu cikamin gidana,sannan ki bani dama naci gaba da kasancewa dake har abada" murmushi ya kubce mata
"Allah ya cika maka dukkanin burikanka,yasa ka gama lafiya,Allah ya kiyayemin kai"
"Ameen uwae yayana,mace ta gari"sunan yayi mata dadi sosai,har sai datayi fari da idanunta
"Amma yaya ka barmin waccan ka dauki wannan kai" motar ya kunna ya fara qoqarin fiddata daga cikin gidan kafin ya amsa
"A sabuwa dal na sameki.....saboda haka baci cancanci kyautar tsohon abu ba,kawai dai idan ina da sha'awar hawa zan ara,kafin komai ya qarasa warwarewa nima na sauya tawa,amma yanzun kam wannan takice,banason ki koma zirga zirgar makaranta rana tana dukarmin lallausan fatarna me tsada" dadi ya sake cikata,kalamai da gaske sune mutum,kulawa itace gishirin zaman aure,kwanciyar hankali da nutsuwa kuma sune jigo,bawai tarin dukiya ko qyale qyale ba.
Duk yadda iman din takai ga zumudin xuwa gidan sai gata tana rabewa a bayan ameen din sanda suke shiga cikin gidan,dariya ya saki ya jawota zuwa gabansa
"Matsoraciya,babu abinda zai faru fa,fada kawai malam zaiyi ni na sani,kuma koda yayi fadan ni zai yiwa bake ba" saita san saki jikinta tana qanqame da hannunsa.
Mufida suka samu a falo tana gurxa danyar citta ginger,da alama lemo zata hada,gefanta wata kyakkyawar black beauty matashiya ce zaune suna hira da mufidan tana tayata kankare bayan ginger din.
Dukka abun hannunta ta watsar ta taso tayo kan iman din tana qwalla qarar murna abinda yaja hankalin inna da Sadiq dake falon malam duka suka leqo da sauri.
Sak inna ta tsaya,wani sanyi yana ratsa zuciyarta,tabi sanyin idaniyar tata wato lameen da iman da kallo,zallar nutsuwa wadata da kwanciyar hankali na bayyana kansu da kansu daga jikkunansu,ba wanda bai qara haske da qiba ba a cikinsu,sai tayi hanzari kau da kai sanda duke gab da hada idanu da ita,saidai kuma murna da farincikin dake saman fuskarta bai canza ba.
Gaba dayansu yau har iman din zubewa sukayi suna gaidata,ta amsa musu cikin kulawa da nuna farinciki,kai tsaye kuma suka wuce wajen malam,kwarjinin nan nan nasa dai yayi musu,saidai shi dinma farincikinsa ya kasa boyuwa,sadiq na gefan lameen din yanata kwasarsa yadda suka saba qasa qasa yadda ba wanda zai fahimta saisu yasu
"Zaku hade da yaagana,tace kun maidata mutuniyar banza,tana zaune zaman jiran gawon shanu ka sace matarka kuka barta gaho" dariya taso qwacewa lamin,ya jima yana tunanin dama yadda zata kaya a tsakaninsu da yaagana din.
Hirarrakin yaushe gamo ne suka barke sosai a rumfar malam,dukka aka tattaru aka dawo nan,harda matar ya sadiq wadda a ranar suka fara ganin juna face to face ita da iman,kuma wani haduwar jini ya qullu a tsakaninsu,saida aka gama hira lamin ya gabatar da bude kamfanin sarrafa motoci malam yasa rana kamar yadda ya saba,sannan ya buqaci ganinsu,hakan yasa matar ya sadiq me yawan kunya da hankali ta janye mufida cikin hikima suka bar dakin.
Fada sosai malam ya dinga yima lameen din irin wanda bai taba yi masa ba kan sakin samha da yayi,ya kuma hada harda iman din kan cewa ita ya kamata ta dinga controlling nasa,shine zata amsa sunan mace ta gari,ya kuma umarceshi da lallai lallai ya tashi a yanzu basai anjima ba,sadiqu ya rakashi biko.
Sosai hankalinsa ya tashi,ya cire hularsa ya aje yana satar kallon iman wadda kanta ke qasa batace komai ba bata kuma motsa ba,duka sun karanci inda hankalinsa ya karkata,sai malam din ya umarci iman din ta tashi tabar wajen
"Ka maida hankalinka ameenu,ka zama tsayayyen namiji bame bin umarnin matarsa ba"
"Kayi haquri malam,kada ka zargi iman ko kawota cikin batun nan,wlh bata da ruwa ko tsaki a ciki"
"Naji,ku tashi ku wuce nace" dolen dole lamin din ya miqe,sadiq ya rufa masa baya
"Ya kamata malam ya haqura haka,shi da kansa fa yaje gidansu yarinyar amma bakaga abinda sukayi masa ba,wai saidai kazo da kanka" kashe motar da yake shirin kunnawa yayi
"Malam din?" Ya tambaya cikin jin xafi
"Eh mana"
"To babu inda zani wallahi,bata kai wannan darajar ba" yayi maganar yana shirin bude motar sadiq ya danqo shi
"Kana qin zuwa laifi zai dawo kaina,ban gaya maka bane saboda kaqi zuwa,na gaya maka ne saboda koda kaje kaga wata fuska ta daban kayi haquri da hakan" da qyar ya shawo kan lameen din,wanda a qarshe yace saidai shi ya tuqasu,shikam baxai kaisu ba,lallabawa akeyi,haka sadiqun ya karba tuqin.
Sun jima sosai suna zaman jiran samhan,daga bisani sai gata ta fito,ta canza gaba daya tadan rame,ta kumayi duhu sai tsaho data qara,kamar wadda aka yiwa dole haka tazo ta zauna hannun kujera tana busa hanci,ita a lallai ba zata nuna masa ta damu dashi ba,ganin haka sai lamin din ya miqe tsaye,ya maida hularsa kanshi
"Malam ne ya aikoni nazo nayi bikonki......" Kafin ya qarasa ta juyo a fusace
"Indai sai ta hannun wanna munafukan tsaffin zan koma wallahi na haqura da aurenka har abada......" Gigitacciyar tsawa daya tabbatar ta isa har cikin gidansu ya daka mata
"Kika kuskura wannan qazamin bakin naki ya sake aibata mutane mafi daraja a rayuwata na rantse da sarin dake busamin numfashi saina zubda miki haqora.........tun daga sanda na sakeki kika fita daga sahun matata saboda dama ban dora miki idda ba,inda akwai sauran iddata a kanki da a yanzu zan cikashe miki sakinki daya da yayi ragowa shashasha,amma na godewa Allah daya sanya ban hada jikina da naki ba........wawiya kawai wanda iliminta bai amfana mata komai ba" daga haka yayi waje da mugun fushi,dole sadiq ya miqe ya bishi,zuciyarsa cike fal da mamakin hali da dabi'a irin na samha,lallai babu abinda zamuce da iyayenmu da suka tsaya tsayin daka suka bamu tarbiyya ganin daraja da kimar mutum sai godiya da fatan alkhairi.
Da kallo ta bishi,tana jin kamar ta dora hannu aka ta zunduna ihu,last chance da hope da take dashi shikenan ya qare?,me yasa batayi controlling fushinta ba?,me yasa bata iya yiwa harshenta waigi ba?,idan yaso in ta koma ayi duk wacce za'ayi ma
_Ni kuwa nace harshe dama mafarin dukkan wata nadama,indai baka iya controlling dinsa ba,Allah ya rabamu da sharrin harasunanmu_
[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 75
Koda iman ta koma falon innan sai tayi qoqarin sakewa tare da mai da komai ba komai ba,duk da cewa taji fitarsu zuwa bikon samha,ta sani cewa duk yadda takai ga so da qaunar lameen bata isa ta hanashi abunda Allah ya halasta masa ba,shi majin mace hudu ne,ko yau ko gobe,da dadi babu dadi,ba dawowar samha ce damuwarta ba,damuwarta ta samu adalci daga wajen ameen tsakaninta da samha,wanda bata haufi ko kadan a kan hakan.
Hirarsu sosai suke da matar ya sadiq wadda ta fahimci ciki gareta dan qarami,duk da hankalinta rabi da rabi ne,har zuwa sanda matar sadiq din ta tashi yin alwala,iman din kuma ta shiga daki wajen inna.
Hira ce ta barke tsakaninta da innar,tanata bata labarin abubuwan da suka faru da bata nan,idan innar ta manta wani abun mufida ta tuna mata,a nan taji zacan auren bushira da dr ahmad
"Aikin yaagana ne wannan,nima bansan yadda akai ta hadasu ba,jiya iyanzu ma bushiran tana nan muna ta hirarku,tana ga qorafin kuyi hijira kun bace bat a qasar nan" inna ta fada har cikin zuciyarta na haduwar auren dr da bushiran.
Dadi ya kama iman naji yadda innarta ke kewarta,a yanzu dukka wata soyyaya ta dawo tsakaninsu,gefe daya kuwa albarka kawai iman ta shiga sawa yaagana,saboda tayi abinda ya dace,an kuma aza qwarya a gurbinta,daga dr har bushira nagartattun mutane ne da suka dace da juna qwarai.
Aiken mufida inna tayi kitchen,sannan ta ajjiye abinda takeyi,ta zauna tana kallon iman bayan ta kirayi sunanta. Nasiha tayi mata sosai kan xaman aure,irin nasiha ta tsakanin uwa da 'ya,ta bude mata abu uwa sosai masu tarin yawa irin wanda basu taba maganarsa ba tsakaninta da innar
"duk yadda maeenu ke sanki akwai sanda zaku bata kiyi rashin dadi,ban yarda ki gayawa kowa ba koda jice,a matsayinki na mace kiyi amfani da hikina da baiwar da Allah ya bawa kowacce 'ya mace ki gyara natsalar,idan kika fuskanci tafi qarfinki ko akwai barna me yawa a ciki a sannan ne zaki nema shawarata,daga kaina kuma ban yarje miki ki gayawa kowa matsalarki ba,koda ya kuke da mutum.......Kada kice zaki dinga amfani da soyayyar da mijinki yakeyi miki ki sake jiki,ki barshi yana aikata ba dai dai ba,ko dorashi akan hanyar da zai tsira ranar gobe,na sani na kuma gani kan fuskarsa,soyayyar da yake miki tana da tarin yawan data wuce ma yadda muke hasashe,kiyi qoqarin amfani da wannan damar ki dinga dorashi kan hanyar data dace" sosai maganganun inna suka shigeta,suka kuma sanyata fidda qwalla,ta kama hannun inna tana mata godiya tare da sake neman gafararta,daga bisani tare suka fito daga dakin sukaci gaba da sabgarsu.
Shuru har yamma lis babu 'yan biko babu dalilinsu😂,abinda basu sani ba tuni mahaifiyar samha ta kira malam da kanta,tace ya jawa lamin kunne,aure babu dole,bashi ba 'yarta,malam baice komai ba har ta gama ta kashe wayar,abinda ya sake sanyayar masa da jiki kenan.
'yar halak bushira sai gata kuwa,iman tasha tsiya tasha tsiya,tun tana ramawa har bakinta yayi shuru,uwa uba kuma ga mayen zazzabin yammar nan da yake yawan rufeta ya fara sako kai,saidai hirar da suka dinga yi tadan rage mata jin zazzabin,ta kuma dauke mata kewar lameen din da take tayi tun dazu,sai takejinta yau duk wani iri,wuni guda bata jita a jikinsa ba rungume cikin faffadan qirjin nan nasa na alfarma dake cire mata duk wani damuwa da fargaba,daga qarshe dai daki dole ta koma saboda zazzabin,tabar bushira da matar sadiq suna ci gaba da hirarsu.
Kwance tayi saman gado,zuciyarta tayi nisa a kewa da tunanin mijinta,cikin hancinta ta fara shaqo qamshinsa,tana bude idanu kuwa shidinne a tsaye,sai ya bude mata hannayensa gaba daya,batayi sanya ba kuwa ta garzayo ta fada,ya maida.hannunsa ya rungumeta tsam yana sansanarta
"How was your day?"
"So boring " ta amsa masa tana yatsina fuska,idanunsa ya fiddo waje
"Beside inna da malam din?" Kunya saita kamata ta boye fuskarta a qirjinsa,abinda ke zuciyarta ne kawai tayi subutar baki ya fito,dariya ya qyalqyale mata dashi kafin ya dagata sama ya juyata,ya kuma ajjiyeta kan madubi yana kalln fuskarta
"Don't be shy.......gaskiyar cikin zuciyarki kenan,nima kuma banajin akwai wani sauran waje a duniya da zanje naji dadin kasancewa a wajen ba tare dake ba.....oya.... pack your stuff mu wuce gidanmu" shi ya tayata suka tattare kayanta,sai gasu a falo da shirin tafiya.
Inna dai dauke kai tayi tayi kitchen tana cewa su tsaya a zuba musu tuwo su wuce dashi
"Kinaso baby?" Ya tambayeta,ta gyada kai,mufida ce ta biyosu dashi,bushira tayo musu rakiya har bakin mota tana yiwa iman tsiya qasa qasa yadda ameen bazaiji ba,don tanajin nauyinsa da girmamashi,ba zataso yaji ba,bushira da bata qyaleta ba saida iman din takai mata duka sannan taja baya tana daga mata hannu.
Yana driving amma yana riqe da hannunta,bai boye mata komai ba kan abinda ya faru gidansu samha
"Allah ya gani dukkanmu munyi iya yinmu,mun kuma fita haqqinsu" ya fadi,saita lumshe idanu kawai,bazatace taji dadi ba,saboda kimar aure,amma ranta bau baci ba,duba da cin kashin data yiwa mutanen datafiso inna da malam
"Allah ya zaba abinda yafi alkhairi"
"Ai yama zaba din in sha Allahu tunda akayi haka"
"Baby,asibiti zamu wuce fa,jikinki yayi zafi da yawa" maqale kafada tayi
"Ka siyon paracetamol kawai ya isa" kansa ya jijiiga
"Ban yarda ba,nifa nafi yarda da cewa cikine Allah" yadda ya dage yasa ta yarda a siyo paracetamol din,sanna ya hado mata da pt strip ta gwada fitsarinta da kanta a gida.
Shuru sukayi dukkaninsu kowa ya zubawa strip din idanu sanda suka fiddoshi daga cikin fitsarin bayan sun idar da sallar asuba,dubanta iman din yayi
"Ki tabbatar fa saikin bani alqawarina indai nine nayi winning cikine" idanunta ta fara saukewa kan strip din kafin takai ga bashi amsa,tar layukan jajaye guda biyu suka bayyana radau,gabanta yadan fadi,ta dauke idanunta ta maida ga lamin,ashe shima ita yake kallo,sai ya dage mata girarsa guda biyun,fararen haqoransa dukka a waje saboda yadda murmushinsa da murna suka gaza boyuwa,ya zuba mata idanu,sai taji wani weakness na yakamata,zuciyarta ta karye,wai itama tahau turbar zama uwa kenan?,nan da wasu watanni zata zama uwa itama?,zata riqe danta ko 'yarta a hannunta?,qwalla ta taru ta cika Blue eyes dinta,saiya bude mata tafukan hannayensa ta shige ciki ya rufe yana sakin qaramar dariya cike da nishadi,hannunsa akan gadon bayanta yana shafawa a hankali yana jero kirari da godiya ga ubangiji,zamewa yayi ya durqusa a gabanta,ya kama dukka tafukan hannayenta yayi kissing tsakiyarsu
"Kin gama min komai hajaru,na yafe duk wani abu da kikace zaki bani,abu daya ne ya rage.....ki haifamin baby girl me kama dake"kai kawai take gyadawa
"Alhmadulillah" bakinta ya furta a sarari,sai suka sake rungume juna,qauna da soyayya abinda ke cikin yana hudasu tun basusan meye ba.
*******Tubali me kyau hadi da kyakkyawan dashe na harsashin kyakkywar mu'amalar auratayya ne a tsakanin lamin da iman,wani irin zama daya zama madubi abun kallo ga kowa,abun sha'awa kuma abun kwaikwayo,duk inda namiji jarumi kuma jajirtacce yake lameen yakai can,banbanci mabayanni iman ke gani,tsayayyen namiji da ya daukewa iyalinsa komai,ya hanasu kuka ko damuwa,ya hana zukatansu jin ciwo kewa ko kuma rashi na wani abu komai qanqantarsa,zallar zama na amana,zama na sanin daraja da kimar dan adam,iman ta sake gani ta kuma sake gasgata kudi da soyayya ba koma suke iya siyawa dan adam ba,daraja kima da dattako gami da sanin kima da darajarka yafi komai tsada da wahalar samu,tayi godiya ga Allah tayi sadaka me tarin yawa kan yadda ubangijinta ya fiddata daga mummunan ramin data afka,tana yima lameen kallon duniyarta koma muce rayuwata gaba daya,qauna ta haqiqa mara misali,wanda ashe a gida rabin rabinta ya fiddo ya nuna mata,a yanzune ya fiddata gaba daya,tsaftatacciyar qauna me cike da tsari da salo na daban.
Ya zame mata aljannar duniya,wannan yasa itama ta zame masa jin dadin rayuwarsa gaba daya,cikinta daya fara fitowa baisa ta gaza wajen yi masa komai ba,ta zame masa cikakkiyar mace ta gari,wadda duk inda hake duk yanayin da yake ciki kallon fuskarta ne kadai ke sauke masa nutsuwa da kwanciyar hankali,duk yadda takeson abu idan lameen bayaso ta barshi kenan,hakanan ko yaya ya nuna yanason abu to ta riqeshi kenan sai inda qarfinta ya qare.
Cikin wata kulawa ta musamman yake tattalinta da kuma rainon cikinta,gefe guda ta koma kan karatunta,ta bada hankalinta akai matuqa,ya bata dukka wani support don ganin ta samu kyakkyawan sakamako ganin suna kan gangara,watannu qalilan suka rage mata,sai Alla ya bata ciki mai sauqi,bata wuce zazzabi ko ciwon kai shine cutarta,sai kuma abincinta wanda kullum tuwone,wannan kuma sai ya zama dutyn inna,kullum sai tayi mata sabon tuwo,yaran dake mata aike a gidan suke jigilar karbowa,duk tuwon daa buqata shi inna zata mata,zaya yiwa lameen girki kala kala na burgewa,amma saidai ta tayashi zaman ci,haka zaici wataran yana tsokanarta,wataran yana tausaya mata sosai,yakam bata lokaci yana lissafo mata nau'in abinciccika ko zataji wanda take sha'awar ci yaje ya nemo mata duk inda za'a samu,saidai kawai ta tabe baki ko tasa dariya,wani lokaci tace....abu kaza ma ni sai naji kamar zanyi amai,wani lokaci yakai mata bugun wasa yace ta rainashi,ya zauna ya zayyano mata abincin yaruka kala kala amma tace masa amai ma taji,saidai tayita dariya ko tayi masa gwalo....haka rayuwarsu take,cike da barkwanci farinciki da girmama juna.
Sannu a hankali wani irin budi yaketa shigowa lameen harda sadiq dinma,kamfaninsu guda biyu kowanne wani irin kudi yake kawo musu naban mamaki,ba komai bane sirrin nasararsu face malam,wanda koda yaushe yake basu shawarwari na yadda zasu kaucewa duk wata hanya da zasu gamutsa halal da haram,duk wanda yayi hulda dasu sai ya dawo ya sake nemansu,saboda komai nasu cikin aminci inganci da amana suka dorashi.
Ameen mutum ne mai hannun kyauta da bayarwa,hakan ya sanya hatta danginsa dake jigawa sukasan lallai fa budi yazo,don kuwa bayan kowanne watanni baya wuce daya zuwa biyu sai yayi rabon kayan abinci kudi da sauran kayan buqatu,iman ta qarfafa masa gwiwa sosai,ta kuma sake dorashi ka wannan hayar,tunda babu abinda suka nema suka rasa a rayuwarsu,kafin kace meye saiga yaa baraka ta zama hajiya,gidanta baya abo da mabuqata da masu zuwa mata fadanci,dama kuma ita din mutum ce mai yawan alkhairi,tun bata dashi abun hannunta bai rufe nata idanu ba,sai kowa ya zama nata,daga dangi har maqota,sosai iman ta samu farinji da karbuwa dari bisa dari wajen dangin lamin,kamar xasu cinyeta saboda qauna da suke gwada mata,hakan kuma ya samo asali ne daga yadda bata qyamar su,tamaishesu kamar nata.
Hankali bai kwanta ba saida iman ta kammaka jarrabawarta gaba daya,ta gama school of nursing,komai ya tafi maya successful saboda taimako gwarzon miji na gari data samu,wanda a lokacin daya fuskanci cikin ya fara mata nauyi sai ya dauko mata usama,shike tuqata ya kaita,ya kuma dawo da ita,sai data kammala sanna usaman ya koma,bai jima a can ba ya sake dawowa nan shima,saboda BUK da lameen din ya samar masa,amma fir yaqi zaman gidan lameen din,ya dawo waje inna yayi zamansa,hakan sosai ya faranta ran inna,ko babu komai ta sake samun mutum a kusa da ita,ga usama ga mufida,gidan sai ya sake mata dadi.
Wata daya da gama makaranta bikin bushira ya tashi da dr ahmad,sosai dr din yayi mata bajinta ta nunawa,tabbas Alla ne yake qulla soyayya,todai ya qullata tsakanin bushira da dr ahmad din,tamkar dama tun da farko sun jima da fara son juna,ko kuma babu wanda suka fara so sai junansu.
Duk yadda iman taso ta gwangwaje a bikin malam al'ameen ya hana,wasi events dinma bai barta taje ba,tayi nacin tayi kukan amma fir yaqi,ya wuni a gida ya sanyata a gaba yana kallon abarsa,taka qararsa wajen amarya bushira amma saita gwaleta
"Kin fara nauyi iman,me zakizo kiyi,kun gama mana komai,sadaki ma ya lameen ne ya biya,ida kika lura ya ameen yana da kulle,yakamata ki saba da hakan ki daina damuwa" haka maganarta take,indai fita bata kama ta zama dole ba lameen din baya qaunarta,ya gwammace idan ya hanata yaga rata ya baci,sai ya zauna ranar ya tayata wuni,yakance
"Shikenan.....munyi one one ko?" Maganar bushira haka take,don haka sai ta saki ranta kawai ta shiga shirya masa dan abun sha da yafiso kafin ta gama girki.
Sanda ta kawo masa drinks din jawota yayi jikinsa ya azata saman cinyarsa
"Zo nan madam.....ki rufan asiri ki rage fushi da saurin kuka,kada ki haifan raguwar baby.....me idon mage" idon magen daya fada a shagwabe ya bata dariya a dole,saboda ya tuna mata zamanin quruciya,ya dinga tsokanarta sai data sake,sai datazo tashi qafa ta riqe
"Bari na baki albishir,ladan fushin da nasa akayi dani...." A kunne ya rada mata,saita zare ido ta kima hangame baki,fuskarta dauke da dariya
"Da gaske ya lamin....kace nayi shirin zama dr"
"In sha Allah" ya fada yana murmushi,gam ta qanqameshi tana masa godiya,sai kuma kukan farinciki ya qwace mata,yasan duk wani burinta wanda ta taba furtawa dama wanda bata taba furtawan ba, he's genius lameen din musamman akan duk wani abu daya shafeta
"Banda kuka queen...... stop it please" ya dinga fada yana shafar bayanta.
[7/19, 10:04 PM] Mummyn Yara: 76
Randa ta dawo daga raka bushira dakin mijinta,suna hanya ya daukota da kanshi a motarta kamar yadda shi ya kaita da kansa ya kuma jira ta gama duk uzurinta,yake gaya mata ya gama da issue din muneera,yanzu haka auren ya rabu,muneeran tana gida gaban iyayenta
"Zaku iya ci gaba da zumuncinku ta waya,ban hanaki ba,amma ban yarda ko sau daya tasan hanyar gidana bama bare gidana"
"As you wish sir" ta fada tana jin dadin taimakon muneera har qasan ranta,saboda ko babu komai muneeran ta sota da gaske,kawai wata qaddara ce tasa ra ingizata suka yita tafka kuskure,ko bai fada ba dama bata da sha'awar ci gaba da qawancensu,qawance na kusa da kusa,gwara daga nesa nesa,ita a yanzun a duniya qawayenta kuma aminanta guda biyu ne,ta farko innarta,ta biyu kuma busheera.
Lameen da kansa yaje ya dauko mata badi'a daga jigawa saboda ta dinga hutawa,tabbas ta samu hutu,shima kuma ya huta sosai,don sai data ce
"Ni ban gane wayon kawo badi:a ba,kanka ka yiwa aikin nan Allah honey" idanu ya lumshe yana murmushi,iman din ba zata gane yadda ta sake zama cikakkiyar mace ba.
"To nidai abun arziqi da alama bai karbeni ba,fisabilillahi,idan ma na huta to mene" ta motsa ya sake kanannadeta
"Tabbas Allah ya dubi zuciyata,ya kuma soni da rahama da ya hanani hadaki da kowacce mace,dako tantama banayi,zaiyi wuya na tsallake sahun mazan da zasu tashi da shanyayyen barin jiki......wallahi har yanzu iman baki gama sanin yadda nake jinkina a raina ba,abinda zai iya bayyana kawai kika gani,sauran saini da.mahaliccina da kuma zuciyata" duk sanda lameen din yayi mata magana irin wannan jin kanta take a sama,ta yarda da duk maganarsa,saboda tana gani a zahiri,wannan yasa take sakar masa ranta rayuwarta dama gangar jikinta yayi duk yadda yaso da ita.....to sai muce Allah ya raba lafiya hajara aya.
*_BAYAN SHEKARU_*
Tsaye motar tayi a qofar mayalwacin gate din gidan da yake mallakar malam ibrahim khalilu tana danna horn,maroon color ce mai matuqar kyau,yadda kuma take daukan idanu kawai ya isa ya gaya maka cewa sabuwa ce dal.
A hankali gate din ya fara motsawa gaba kafin ya yaye gaba daya,dan matashin yaron da ya doshi shekara goma sha biyu ya bayyana,sak PHOTOCOPY na MUHAMMAD AL'AMEEN mamallakin katafaren kamfanin IB COUTURE daya zagaye qasashen africa kaf sai dai daiku,kyakkyawar harabar gidan ta bayyana,mai tuqa motan ta motsata zuwa ciki,idanunta nakan gilashin mudubin motar tana hangen yaron sanda yake biyo bayan motar bayan ya maida gate din ya rufe.
Shi ya bude mata mota yana fadin
"Sannu da zuwa ummee" takalleshi da kyau,shi yasa koda yaushe yake sake kama ranta,ya debe halayen malam ya cakuda dana babansa,dabi'unsa na dattawa ne,yana matuqar qaunarta da kuma tausayinta,wannan shine first born dinsu
"Yauwa me sunan malam.....ya na ganka a nan?,kun gama musaffar ne?"
"Mun gama ummee,har malam din ma yadan kwanta ya huta" ya amsa mata yana zagayowa daya seat din yana debe mata takardunta da jakar data fita dasu,sannan ya zagayo inda take zaune tana qoqarin daga qafarta data maqale saboda tuqin datayi
"Ko na matso ki dafa ni ummee" ya fada a tausashe,ta kalleshi ta saki mirmushi,ya sani,aikin mahaifinsa ne wannan,wato yau da baya kusa shine zai karba masa
"A'ah,zan iya me sunan malam" sai tayi bismillah ta yunqura ta fito.
Dr iman ibrahim khalilu kenan,cikakkiyar likitar mata,kuma mamallakiyar asibitin nan dake aiki da tsarin addini wato AL_EMAN CHILDREN AND WOMEN HOSPITAL wanda yake duba mata da yara zalla,hakanan tun daga kan nurses da likitocin dake aiki qarqashin asibitin mata ne,tsiraru ne maza suma aikinsu bai shafi duba marasa lafiya ba,kamar masu share haraban asibiti da masu gadi da sauran wasu ayyukan.
Kallo daya zakayi mata kasan ta zama babbar mace,wadda ta gogu da ilimi da kuma wayewa,duk da tulelen cikin jikinta hakan bai hana kyanta da tsarin adonta me burgewa fitowa ba,komai nata classy ne,daga duba daya zaka karanci hakan.
Abinda ya fiddata yau din tana daga cikin ranakun da take zama cikin asibitinta,tana da office nata mai zaman kansa,tana kuma da selective ranaku guda biyu a sati da take zuwa asibitin,duka sauran kwanakin tana zaune a gida,badi'a da bushira na cikin masu kula mata da asibitin,suma kuma suna wasu ayyukan acan,uwa uba usama wanda gudanarwar asibitin ke hannunsa,lameen ne ya gina mata asibitin ya kuma danqa mata shi kyauta halas malak,lokacin data haifa masa yaronsa na uku wanda a yanzu cikin na biyar ne da ita,yara maza hudu reras gareta,cikin da akaci masa burin haifar diya mace kamar su sayo a kasuwa,kada ma lameen din yaji labari,tadan qara lokacin dawowarta akan yadda ta saba,saboda tsayawa da tayi duba muneera wadda itama haihuwa ko yau ko gobe,don sai ta haihu da wajen wata daya ma kafin ita ta haihu,to cikin nata ana tunanin yi mata cs ne saboda yadda babyn yake breech,muneeran ta samu tayi aure bayan shekara kusan uku da mutuwar wancan auren nata,daga qarshe dai tailor da take rainawa ta aura,cikin ma'aikatan dake aiki a IB COUTURE mallakin lameen din,saidai yana cikin ma'aikatan dake daukan albashi mai tsoka,shi kansa bai sani ba sai da auren ya tashi,ya gayyaci lameen din a matsayinsa na ogansa,kuma babban baqo a wajen,ya mata murna sosai saboda mudassir mutumin kirki ne,ya kuma gayawa iman a sanna,har ya barta taje mata yinin biki,daga qarshe bayan sun tare suka matsa ita da mudassir din dai sai da sukeje sukaga gidansu,komai dai dai wadaida,cikin rufin asiri,abun gwanin sha'awa game wadatar zuci.
"Su isma'eel fa?,sun dawo kuwa?" Ta tambayi mai sunan malam wanda ke take mata baya yadda dai lameen keyi mata har kullum,tana kutsa kai zuwa cikin gida wajen innarta
"A'ah basu dawo ba,naji abee ma yayi waya,idan anyi sallar magarib zaizo ya daukemu gaba daya" kai ta gyada don ya kirata ta gaya mata.
Ta samu inna rungume da falle fallen qur'ani tana dubawa,ta daga kanta tana amsa sallamar imanin tata,cike da kulawa
"Sannu" inna ta fada cikin nuna kulawa tana tattare alquraninta,dai dai sanda mai sunan malam ya dawo daga kitchen dauke da ruwa ya miqawa iman din,sai da yaga tasha sannan ya fice abinsu barsu da innar.
Inna da kanta ta hada mata ruwa mai dumi tace tayi wanka,sanna ta tayar da mufida dake bacci wadda zuwa yanzu ta zama budurwa,don zancan karbar kudin aurenta akeyi da usma dan yaa baraka,duk sun tsaya qumbiya qumbiya suna ta yiwa innar boye boye bayan kowa ya gama ganosu,ta shiryawa iman din abincin sannan ta zauna ta tayata ci,don wannan cikin acicine,komai ta samu ci take.
Suna tsaka da hirarsu hayaniya ta fara tashi daga harabar gidan
"To bismillah,da alama su isma'il sun dawo,kuma mawuyacine idan ba dasu maama fatima ta hadomin su ba(yaran sadiq,wanda su kuma su hudu ne,mai sunan inna itace maama kuma babbar,sai lailah....sai hanif,sai aslam shine qarami)" kafin inna ta rufe bakinta kuwa basawan nata suka bayyana cikin falon,isma'il ne mai kado kansu wanda shike bin mai sunan malam,sai Abdallah sajid,sai muhammad da suke cewa mamman,sai kuma yaran sadiq din,fatima matar sadiq tana biye dasu a baya dauke da aslam.
Falon kuwa ya kacame gaba daya,Allah ya taimakesu mai sunan malam ya leqo yace dukka suzo inji malam,basusan malam din yana gida ba,sai kuwa aka fara rige rigen fita zuwa wajen mlam din har ana karo da juna,sunsan kilishi ne ko zuma ko kudi zasu samo,alaqa me mai kyau da matuqar shaquwa tsakaninsu da malam din,yana matuqar ji da jikokin nasa kamar yadda suma sukeji dashi
"Alhmadlh,haba,maji kunnuwanmu,da alama basusan yana gidan ba dama" iman dake zare hannunta daga abinci ta fada.
Indai suka hadu tsakanin fatiman da ima basa jin kunne dama,da inna tayi iya tata hirar saita miqe ta barsu,suka kuwa dasa har sai da aka kira sallar magariba sannan suka wuce sallah.
Basu jima da idarwa ba aka kira cin abincin dare,saboda yau family din ya hadu,can babban falon malam.
Tunda suka shiga idanunta shi suka fara gani,shima nashi idanun ita suka fara gani,anacin abinci ana kuma taba hira cike da raha,harda malam din da inna,family ne mai ban sha'awa da qayatarwa,basuyi boko ba iyayen,amma suna bin tsarin koyarwar musulunci,wanda yafi na boko ban sha'awa tsari da kuma qayatarwa,shi yasa abubuwansu ke burge mutane da yawa.
Wata kulawa ta cikin ido ake bawa juna tsakanin iman da lameen din,amma a haka zaka zaci ita dashi kowa harkar gabansa yake idan ba kana da kula da bin qwaqwafi ba,basar dashi take,tasan sarai me yakeso,abubu biyu ne kuma duk sai taja masa rai a kai.
Shi ya fara janyewa daga cin abincin,ya koma gefe ya tsume yana gayawa yaran su hanzarta zasu wuce gida
"Nayi zaton dana gansu duka nan zasu kwana?sannan shi kansa takwara izifin qarshe na suratul baqaransa bai zauna masa sosai ba,so nake cikin watan nan ayi bikin haddarsa,sai amaisa hakali sosai ga isma'il" Malam ya fada yana dan duban lameen,sai lameen din ya shafa kansa,shi dama hakan yafiso,bayaso ne kawai yabar inna da bari bari shi yasa
"Ba wani abu malam,saisu kwana din,duk yadda kayi da ai ne" nan fa suka hau murna da tsalle dukkansu,don dama haka sukeso,ya zamana ya sadiq zai dauki matarsa da aslam,shima ya dauki iman din su wuce,su babu dan rakiya ma,tunda gaba dayansu babu me shan mama a cikinsu.
Tana hanya zafa wajen inna kiran bushia ya shigo mata,ta daga suka gaisa gaisuwa irin ta aminan juna,suka taba hira suka kuma tsokani juna sannan bushiran ta shaida mata birthday din hamdan danta,next week,ta godewa Allah da yaran basa kusa,da sai sun haukatata,saboda dama birthday din suketa jira,kasancewar lameen bai taba bari an yiwa kowa cikin yaransa ba,ta tayata murna tace kuma za'a kawosu in sha Allah ko su taho ma gaba daya,sukayi sallama tana tsokanarta daa
"A gaida yallabai baban soyayya" dariya tasake
"Zaiji kuwa"
"Ba daga bakina ba pls bama 'yar haka dashi,kada mutuncina ya zube"
"Saiko na fada" ta katse wayar tana dariya.
Kira ya dinga jera mata a waya bayan gama wayarsu da bushira,yana mota yana jiranta,da qyar ta baro cikin gidan ta fito,tana shigowa kuwa ya cukuikuyeta amma a tausashe,ta saki qaramar qara a shagwabe
"Saboda kinsan ke daya nakeson kasancewa dake shine kike jamin rai ko?" Fari ta sakar masa murmushi na kubce mata
"Idan bakai wasa ba wankan gida zan taho wannan karon ma"
"Saiki shirya dakin xaman mutum biyu"dariya ta qwace mata a boye,tasan tun haihuwarta ta hudu yace an daina wannan,ya gaji da zaman tuzunrantakar da yakeyi,ta tsokaneshi kan yayi aure,yace mata saidai tayo masa auren dole idan ta isa
"Ya ake ciki?,kuma ki gayan gaskiya me aka gani?,banda baqin da mukayi yau dama so nayi ayi agabana kada amin rufa rufa" ya tambayeta sanda motar ke fita daga gidan,kanta ta kawar gefe
"Abinda dai aka saba"
"Uhmmm....me kenan?"
"Namiji ne" hannunta dake cikin nashi ya matsa,wanda dama ya saba al'adarsa ce,duk sanda yake tuqi tana gefansa to hannunta cikin nashi yake,qara tadan saki a tausashe
"Macace in sha Allah" lafiyayyen murmushine ya kubce masa
"Yes!....alhamdulillahi rabbil Aalamin,nima na kusa samun photography din me idon mage" ya fada yana dariya cikin nishadi,harara mai cike da qauna ta jefa masa
"Idanun nan na qaramin shauqi a kanki iman,saika tara mutum million da wuya zaka samu daya mai irinsa,yadda kike special haka komai naki yake.....Allah ka san irin son da nakewa wannan halitta,Allah ka bani tsahon rayuwa tare da ita" murmushi ya kubce mata,a kullum kalaman da takeji daga bakin lameen,tana tunanin ko daga yanzu zai daina gaya mata su sun isheta rayuwa.
"Ya Allah.....kaga yadda wannan bawa nake yake kula da baiwarka iman,yake kuma qoqarin cika burikanta da faranta mata ita da iyalinta,ya Allah kada ka barshi haka,kayi riqo hannayensa,ka zama ji da ganinsa,ka zama gatansa,ka yalwata kabarin iyayensa kasa kuma dukka alkhairansa ga jama'ar gari da iyalansa ya zamana sadaqatul jariya ga iyayensa batare daka rage lada ko daya daga cikin ladan da zaka bashi ba"
"Ameen" ya amsa yana lumshe idanu,duk da tuqi yake amma sai daya janyota jikinsa yana buga kafadarta,zai iya cewa babu mace kamar iman duk fadin duniya,addu'ar datake masa ko mahaifiyarsa iyakarta zatayi masa
"Me dame ya faru wunin yau...." Ya tambayeta yana jifarta da murmushin dako yaushe yake saukar mata da nutsuwa.
Wannan kusan al'adarsu ce,duk lokacin da suka wuni da daddare kowa yana baiwa dan uwansa labarin abubuwa masu muhimmanci da suka faru ko ya aiwatar a wunin,sake rage kaifin muyarta tayi,muruar da take wa lameen hira ko bashi labari ta banbanta da muryoyin datake magana da kowa,saita tabbatar ta qwatata yadda zata saukar masa da shauqinta da kuma cikakkiyar nutsuwa,cikin wani irin sanyi ta fara zayyano masa,yana saurarenta yana lumshe idanu,saboda dadin muryar tata tafi labarin dadi,cikin zuciyarsa yana tasbihi ga Allah da kyautar iman da yayi masa halak malak
*ALHAMDULILLAHI RABBIL ALAMEEEEN*👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽
*_Anan na kawo qarshen labarina mai suna BUTULU KUFAN WUTA,,ina fatan kurakuren dake ciki Allah ya yafe mana_*
*_fatan alkhairi a gareku zafafa customers,muna fatan qananun laifuffuka da kura kurai da aka samu a ciki zakuyi mana afuwa,Allah ya qara danqon qauna da zumunci,team zafafa biyar na godiya da jinjina muku qwarai_*
*Inda aka manta ba'ayi conclusion ba ajizanci ne irin na dan adam,Allah ya sadamu da alkhairi,ya kuma hada fuskokinmu da alkhairi a rubutu na gaba*
*Subhanakallahumma wabi hamdika,ash hadu an la'ilaha illa anta,astagfiruka wa'a tubu ilaika*👏🏽👏🏽👏🏽