Gabatarwa
Kufan Wuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 541 min read
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 🔥🔥 *_KUFAN WUTA_* 🔥🔥
Free page 01
*TAFIYA DA GWANI ME DADI*
*ZAFAFANKU BIYAR sune suka sake dawo muku da wasu sababbin tsararru kuma zafafan labaransu guda biyar kamar yadda aka saba*
RAYUWAR MACE
rano
NOOR ALB
Mamuhghee
MASARAUTA
miss xoxo
BAK'AR INUWA
Billyn Abdul
KUFAN WUTA
Huguma
Zaku samu gaba daya labaran akan naira
1k kacal
2_400
3_500
4_700
*Zaku saka kudin ta wannan account din*
1487616276
BILKISU IBRAHIM MUSA
ACCESS BANK
*SAI KU TURAWA WANNAN NUMBER SHAIDAR BIYANKU*
09032345899
*KATIN MTN KUMA*
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
_MUJE ZUWA_🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️
Dogon layi ne sosai kamar irin na kowacce unguwa ta masu matsakaicin qarfi,hagu da dama na layin gida jene a jere na masu matsakaiciyar rayuwa,wadanda basu cika mugun kyau ba,kamar yadda kuma basuyi lalacewa da rashin kyan gani ba,duk da cewa wani gidan yafi wani kyau,kamar yadda kowa da irin yadda ubangiji S W T ya tsara masa matakin rayuwar da zai wanzu a kai.
Yawancin gidajen plate ne masu soraye,masu ginin benen daga cikinsu 'yan qalilan ne,haka nan gaban gidajen akwai kwata wadda tabi ta kowanne qofar gida,saidai kuma a rufe take da slap,duk da cewa zakaga daya biyu na wani gurbi da babu slap din,gurbin dake nuni da cewa cirewa yayi ko karyewa,ko kuma an tsigeshi ne bisa qarfi da da yaji,da kuma qiriniya irin ta yara,wanda bisa dukkan alamu ma slap din an hada taro da sisi ne daga mazauna layin an ginashi.
Daga can tsakiyar qarshen layin,wanda zaka iya karya kwana ta shiga dakai wani layin daban,dandazon yarane a tsaye carko carko sunata hargowa,idan daga nesa ka taho,zaka iya hangen yadda qura take tashi a wajen,alamu dake nuna cewa fada ake sosai a wajen.
Idan ka duba tsakiyar wajen sosai,yara ne guda biyu,wadanda gaba dayansu ba zasu zarta shekara goma ba gaba dayansu,'yar baqar dirarriyar yarinyar nata qoqarin kada abokiyar fadan nata,wadda idan kayi mata kallon farko ba zaka zaci zata iya dambe haka da abokiyar fadan nata ba,kasancewar bata kai wancar garin jiki ba,fara ce ba sol ba,kana iya hangen doguwar sumar kanta me santsi yadda ta debi qasa da yashi na wajen,sakamakon cirewar danwakalin kanta,baya ga hijabinta data ci damar dashi tun daga sanda za'a fara fadan.
"Iman.....iman.....ga malam nan" wata yarinya ta qaraso wajen bayan taja birki tana haki,da alama daga wani sashen ta kwaso gudunta ta kuma tuqe a nan.
Sarai iman din ta jita,saita qara himma da hanzarin ganin ta yar da rahama kafin malam din ya qaraso,ta tabbatar matuqar bata gama ba ya qaraso fadan yazo qarshe,hakanan kuma babu makawa itace me laifi a wajen malam din,koda kuwa ta fisu gaskiya.
Saidai bata kai ga cimma burin nata ba taji tsawar malam din a kanta
Dattijon mutum,wanda a qalla shekarunsa sun tasamma hamsin,sanye da fararen kaya qal,riga 'yar ciki da wando,sai babbar riga malum malum,kansa sanye da farin rawani,hannunsa dauke da buzu daya nade wani abu a ciki,daya hannun nasa kuma yana riqene da baqar leda
"Ke hajaru,kinci gidanku!,saketa nace" Ya fada cikin kaushin murya idanunsa duka bisa yarinyar.
Tunkude rahama hajar iman tayi,ta duqa tana kwasar takalmanta da dankwalinta da suka turbude cikin qasa,ranta a bace na rashin samun damar tumurmusa rahama da batayi ba,dai dai lokacin malam ya waiwaya ga yaran yana musu fada,tare da kora kowa zuwa gida,bayan ya bude ledar hannunsa ya fidda alewa ya rarraba musu.
"Muje gida ke kuma,'yar qaniya" ya fada yana tasa qeyar iman zuwa gida,suna tafe yana mata sababi har suka isa qofar daya daga cikin gidajen dake jere a layin.
Tun daga qofar gidan zaka karanci cewa gida ne na makaranta,ma'ana gidan da ake karantar da almajirai,saboda babbar rumfar kwanon da tabarmi dake malale saman simintin dake qasan rumfar kwanon,tun daga malalen simintin,tabarmin dake shimfide din zuwa qasar dake gaban gidan a share wajen yake fesss,kai kace lomar tuwo zata fadi ka duqa ka dauka abarka kaci saboda tsabar tsabta.
Da hanzari almajiran dake zaune a wajen,wadanda basufi biyar ba suka miqe
"Sannu da zuwa malam" duka suka furta,daya daga cikinsu ya matso yana niyyar karbar ledar hannun malam din,sai ya dakatar dashi
"Yi zamanka habu....inasu haladu?" Ya jefa tambayar ga daya daga cikin mazauna wajen,wanda ya fisu girma da wayo
"Basu dawo ba tukunna,amma nasan suna hanya" kai malam din ya jinjina
"Shikenan,ku fara shirin sallar magariba,duk wanda ya dawo kada ya fita,inason ganinku gaba dayanku"
"To malam" suka amsa masa cikin girmamawa,saiya juya ya saka kai zuwa soron gidan.
Faffadan tsakar gida ne mayalwaci sosai,wanda ke dauke da bishiyar mangwaro da babu kamarta a unguwar,wata iriyar bishiya da Allah ya sanyawa albarka,me yawan fidda 'ya'ya masu dadin gaske da kusan kowa yake amfana da ita.
Dakuna biyu ne daga hannun damanka wanda suke falle daya da kuma rumfa da uwar daki,sai wasu da suke kalloka kana shigowa gidan,suma rumfa da uwar daka ne gaba dayansu,baya ga wani babban dakin falle daya dake a soron gidan.
Gab da soron gidan anan rijiyar gidan take,ma'abociyar ruwa me kyau da sanyi,wanda koda da rani ne nata qafewa,anan kusan duka 'yan unguwar ke diban ruwa idan aka shiga yanayi na rani wanda ake yawan samun qafewar rijiyoyi da kuma janyewar ruwan famfo,bandakinsu na daga can wani dan sakaye sai kitchen dake taqi kadan daga dakunansu.
Yadda qofar gidan da sorayenshi suke qal haka cikin gidan yake,komai a killace cikin tsafta a kuma muhallinsa.
Daga qofar kitchen din wata farar macace zaune saman kujera 'yar tsugono,sanye da wata jar atamfa data qara ma haskenta kyau,duka duka matar shekarunta na haihuwa zasuyi arba'in,saidai da alama ita din ma'abociyar tsafta ce da ado.
Kwando ne a gabanta wanda ke cike da alayyahu tana tsinkewa,baya ga albasa data gama yankanta tuntuni,cikin sauri sauri take aikin,da alama bata saba kaiwa dare kamar haka bata gama abincin dare ba.
Sau daya tak ta daga kai ta kalli iman wadda fa shigo tana gursheqen kuka,tabi takalmanta da ta riqo a hannu saboda tsinkewar da yayi,saita maida kanta taci gaba da aikinta,kamar ma batasan da wanzuwarta ba,abinda ya sake tunzura iman din,tayi zaman 'yan bori a waje tana aje takalman nata a gefe,tare da sake bude muryarta tana sakin kukanta.
Ko dagawa ta sake kallon iman batayi ba,saboda irin wannan koke koken da rigimar ta banza da wofi ba yau ne farau ba a wajenta,kusan kowa na gidan yasan da zaman wannan,har zuwa sanda malam yayi sallama ya shigo,sai tayi qoqarin rage sautin kukan nata,ta hau zazzare idanu.
Da malam din ya kalleta dariya ta bashi,amma saiya danne,ya maida kansa ga matarsa safiya da ake kira da inna,wanna tuni ta miqe tana masa sannu da zuwa,bayan ta ajjiye aikin da takeyi ta qaraso ta rusuna ta karbi ledar hannunsa.
"Yanzu ke hajaru.....bakya jin fada kenan ko?" Malam din ya fada yana kama kunnensa da hannu daya
"Sau nawa zan hanaki fada da yara?,.....ina cewa ko sati ba'ayi ba kukayi fada da asama'u....naja miki kunne,shine har kin manta?" Tsuru tsuru tayi tana raba idanu,tsoron yadda malam keta fiddo mata manyan idanunsa irin nata ya shigeta,takan jima har ma ta manta kafin malam yasa hannunsa ya daketa,duk ranar da ya daketa din kuwa lallai ba shakka ta qureshi ne.....kuma fa zata ji a jikinta
"Daga yau bazan sake miki magana ba,amma zan saki a mari idan baki wasa ba" ya qarashe maganar yana sakin kunnen nasa.
Inna da tuni ta koma bisa aikinta tana saurarensu,haushi sosai yake cikata kan yadda malam din bai iya zagewa ya daki iman sosai kamar yadda takeso,saida yakan gaya mata cewa,duka baya tarbiyya,kuma bashi ke gyara yaro ba,saidai ya batashi,nasiha da kuma nusarwa sune suka kamata.
Sannu da gida yayi mata kamar yadda ya saba,yana tambayarta kowa lafiya,ta amsa masa da lpy qalau,wannan kusan dabi'arsa ce,mutum ne shi managarci,wanda yake matuqar kula da iyalinsa dama buqatunsu,bakin gwagwadon ikonsa,abinci abinsha da suttura duka bai yarda sunfi qarfin iyalinsa ba,komai qanqantar abu ya daukewa gidansa,saidai duk da haka bai hana inna sana'a ba,saboda sanin muhimmancinta ga diya mace.
Gangarawa malam yayi ya daura alwala,ya maida rawaninsa yana shaidawa innar zai sake fita,bazai shigo ba sai an idar da sallar isha'i
"A dawo lafiya,Allah ya tsare" tasan ya fadi hakanne don kada ta damu da rashin gamaabincinta akan kari,shi yasa ya fita ya bata sarari don ta samu ta kammala a nutse.
Fitar malam din kamar dama jira hajar take ta sake bude baki da sabon babin kuka,abunda ya qule inna sosai,tayita qoqarin danne zuciyarta don kada ta kaiwa hajar din hannu,amma ko alamun sassauta kukan hajar batayi ba,abinda ya dinga tunzura inna kenan,taji babu makawa saita jibgi hajar din sannan zataji sassauci,don haka ta saki dambun data gama hadawa tana maidashi madambaci hawa na biyu,ta miqe a fusace.
Malam na gyara hannunsa daga qofar fita daga gidan,yana magana da wani babban dalibinsa sahabi,ya daga kansa a hankali sanda ya fara jiyo muryoyinsu,duk kuwa da cewa basu kai ga qarasowa inda yake ba,amma kuma har zuciyarsa ta tafi inda suke.
Su dinne kuwa,matasan yara su biyu ne tafe,suna jere da juna,dukkaninsu shekarunsu basu wuce sha bakwai ba,yanayin fuska da kuma yadda suke tafe cikin raha zai iya sawa mutum yace 'yan biyu ne,saidai kuma kamanni da sukayi matuqar shan bambam a tsakaninsu zaisa ka gane ba twins din bane.
Matashin farko ya dara dan uwansa fari da haske da kuma tsaho kadan,wanda idan baka da lura ma babu lallai ka gane hakan,yana da zagayayyar fuska da madaidaicin hanci mai tudu,siraran labba masu kyau da kwantaccen gashin gira,duk da cewa akwai sauran shekaru masu tarin yawa a gabansa.....amma kuma sai gashi saje ya fara fito masa sosai,alamun dake nuni da cewa mutum ne me yawan gargasa,don sumar kansa ma kawai ta nuna alamun hakan.
Wani irin idanu gareshi kamar na mai jin bacci,saidai idan kuma ya budesu sosai xaka fahimci manya ne suna da girmansu,duk da bai gama girmansa ba,amma kuma zaka fahimci shi din dogo ne,ya fito daga jinsin yaren da sukafi alaqa da fulani,yana sanye da riga t,shirt me kwala mai gajeran hannu,sai wani wandon jeans wanda ya danyi fari kadan,qila saboda yawan morarsa da yakeyi ne,saidai kana kallon jikinsa kasan gwani ne wajen tsafta,domin kuwa.....duk da wuni da yayi wajen aikinsa,hakan baisa koda karin gugarsa ya bace ba bare akai ga yin dauda,muhammad al'ameen kenan.
Saurayi na biyu shima farine,don har yafi dan uwansa fari,hakanan shima ba baya bane wajen kyau duk da cewa shima shekarun nasa basu gama bayyana komai ba,abu gudan da ya sake bambanta su....yafi dan uwan nasa garin jiki,shi kuma shadda ce a jikinsa,duk da cewa ba wata ta azo a gani bace ba,amma shima fes yake,saidai hannunsa da yayi baqi,sabida aikin gyaran mota da yake koya a wani garage,umarul farouq kenan wanda ake kira da faruku.
A ladabce dukkaninsu suka qarasa daura da malam,suna masa barka da yamma,fuskarsa fadade da fara'a,zuciyarsa kuma cike da alfahari dasu yake amsa musu da
"Yawwa.....ya wajen aikin?"
"Alhmdlh" suka amsa masa a kusan tare
"To ma sha Allah" sai suka miqe suka nufi cikin gidan,wanda al'adarsu ce kowacce rana,idan suka dawo gida lokaci irin wannan,basa shiga dakinsu dake soron,wanda shi suke fara tararwa,har sai sun shiga sun yiwa innar sannu da gida sun shaida mata dawowarsu.
A fusace inna ta ciri wayar radio dinta dake a gefanta,wadda ko awa biyu ba'ayi da kawota daga gyara ba,aikin da ya kacame mata yasa bata samu tashi ba bare ta miqa ta daki,sai tayi kan iman cikin fushi tana fadin
"Bari na dakeki da kyau.....sai kiyi kukan me dalili"
"don Allah innarmu" kalmar data ratsa kunnensa kenan,abinda ya sanyata tsaiwa cak daka dukan iman da tayi niyyar yi,ko da bata juya ba tasan waye,ba yau ta fara jin hakan daga bakinsa ba,matuqar yana gidan,matuqar kuma yana kusa baya yarda da adaketan,ya gwammace ya horata ta sassauqar hanya,amma baya qaunar a daga hannu a daketa.
Kafin innar ta gama miqewa tsaye daga durquson dukan da tayi shirin mata....tuni har ita iman din ta miqe da hanzari,ta kuma falla da gudu tayi inda alameen din yake tsaye.
Kafin ta iso ya duqa,ya kuma yiwa jikinsa garkuwa da hannyensa,saboda yasan tana zuwa din jikinsa zafa fada da shagwabar nan tata,abinda ya jima da yi mata shamaki da aikatashi,saboda yadda a kullum take qara girma,shekarunta suna daduwa.
Ilai kuwa tana zuwa abinda ta shirya yi kenan,saidai ya sanya hannayensa ya riqe nata hannuwan,ta sakar masa kuka,cikin sigar lallashi ya fara magana
"Ya isa haka.....ya isa,karki bari aga hawayenki mana" yana maganar ne tare da sanya gefan dankwalinta yana goge mata fuskarta,sannan ya miqe daha durquson da yayi ya kama hannunta suna takawa zuwa tsakar gidan.
Tsaki yaji daga bayansa,ya kuma san ba kowa bane illa sadiqu,wanda ya tabbatar da cewa zuciyarsa yayi matuqar kaiwa nesa,da kuma kara da yayi masa yau,banda haka tabbas ya sani....da tuni ya jima da kai hannu jikin iman din,kamar yadda ya saba duk sanda wani abu irin haka ta faru.
Yana riqe da hannunta har suka qarasa inda inna ke tsaye daura da qofar kitchen,ya russuna yana fadin
"Barka da gida inna" yana kuma ajjiye mata daya daga cikin baqaqen ledoji guda biyun da ya shigo dasu
"Barka kadai aminu,ya wajen aikin?"
"Alhmdlh inna"
"Ma sha Allah,Allah ya qara albarka" ta fada tana ajjiye kallonta kan Ledar da ya ajjiye ya tura gaban innar
"Alhamdulillah inna" ya amsa mata,saidai hankalinsa yana kan iman,wadda har yanzu take kumburi
"Me iman tayi inna?" Lamin ya maida dubansa ga innar bayan ya dauke idanunsa daga kan iman
Sai da innan ta tabe bakinta sannan ta ja ledar ta fara budawa kafin ta bashi amsa,amsar da tasan koda ta bashin babu abinda zai sauya zani
"Fada dai fada dai ita da yara,fadan da kuma kai da kanka sai da ka rabashi amma malam ya ganta da yaran bata haqura ba,ita ba za'a gaya mata ba taji kenan?".
Kansa ya juyar ga iman,wadda ta sake tale baki tana shirin fara wani sabon kukan
"Me yasa iman?,ina cewa ni da malam duka mun raba wannan fadan ko?" Cikin muryar dake nuni da cewa tana gab da sake sakin wani sabon kukan tace
"To ba sune ba.....da na fito sai su fara tsokanata....bayan kuma ni ban kula su ba.....wai idona irin na mage" qaramin murmushin da ya sake qawata fuskarshi ya sake,yana kuma duban qwayar idanun da take magana a kai,tabbas qwayar idanun nata dama eye lashes dinta ba irin na kowa bane,wannan yasa yara da yawa suke tsokanarta,abinda ita kuma ta tsana kenan,yake kuma yawan hadata fada da yaran,tasha sanya kuka kan a cire mata idanun a sauya mata wasu,duk saboda yadda yaran suke tsokanarta,ko kallonta inna batayi,alameen dinne yake tsayawa ya lalace bata haquri da lallaminta,tare da qoqarin yi mata bayanin cewa ba ciwo bane.
Cikin nutsuwa ya tattara hankalinsa a kanta
"Sau nawa zaance ki daina damuwa uhmm?,dukanmu muna son ganinki haka,kuma ke me kyau ce,bakiga duka kin fisu kyau bane?ke ta dabance kinji?,ki daina damuwa da abinda zasu fada" murmushi ta saka kamar kowanne lokaci idan ya yarrasheta irin haka,sai ta gyada kai tana murmushi,abinda ya sanya dimple dinta na hagu da dama lobawa,sai shima ya biye mata wajen sakin murmushin
"aminu.....an kira salla,ka tashi kayi buda baki ka rabu da wanann sakaryar" cewar inna,tana turo jug na ruwan sanyi data jefawa qanqara gabansa,waiwayowa yayi ya dauki ruwan kana ya miqe yana duban iman
"Zanje sallah na dawo...."
"Ina tsarabata?" Ta fada a shagwabe tana langwabe wuya tun kafin ya qarasa maganar da yakeyi,murmushi ya sakamar mata,shi kansa yana yaba rigima irin na iman,shi yasa babu wanda suke shiri dashi kaf gidan saishi kadai,sai kuma malam wani zubin
"Zan taho miki da ita" ya amsa mata yana shirin daga qafarsa
"Qaniyarki....ke me yasa kullum bakya hankali?"
"Idan na iso wajen saina balla mata dan yatsa,laifinsa da yake biye mata" saddiqu daya gama daura alwalarsa a bakin famfo ya fada bayan ya zubda ruwan kuskure bakin da ya guntsa,yana warware dogon hannun rigarsa tare da jefawa iman din harara kamar idanunsa zasu zazzago qasa
"Amma dai ina cewa ba da kai take ba ko?,to ba ruwanka" alamin ya fada yana watsawa saddiqun nashi idanuwan,sanda yazo gab da shi zai fice daga gidan,xuwa qofar gidan don miqawa malam kofin ruwan sanyi suyi buda bakin tare,kamar yadda suka saba,kusan dukansu suna azumin litinin da alhamis,hatta da iman qaramarsu ta fara,yau dinne kawai ya zamana shi da malam ne kawai suka samu damar yi,saddiqu yayi zazzabi na kwana biyu,bai jima da warwarewa ba,abinda ya hanashi yi kenan,ita kuma inna uzuri irin namu na mata,sai kuma iman wadda tun safe al'amin ya daure mata qarqashi kan cewa yau akwai rana,tasha ruwa abinta,ta bari sai ranar alhamis tayi,inna tayita mita har ta haqura ta sanya musu idanu,idan da sabo ta saba da wannan dabi'ar ta al'amin da iman,bama ita ba,duk wanda ya rayu dasu koda na 'yan kwanaki ne sai ya fuskanci haka.
_ina matan dake fama da qaranci ko daukewar sha'awa saboda gajiya qarancin sinadarai ko kuma gajiya a jikinsu?,kina fama da maigida wajen rashin samun gamsuwa fannin auratayya?,dukka matsalarku ta yanke da HILTI UNISEX CHOCOLATE,maza garza kizo ki nema taki_
_CHOCOLATE CE da zaki shata kamar sauran chocolate,saidai kuma aiki a jiki,ba ruwanki da neman tarkacen magunguna mata marasa inganci,AKWAI TA UWAR GIDA AKWAI TA MAIGIDA_
_GAME BUQATA KO KUMA SON QARIN BAYANI,SAIYA TUNTUBI WANNAN NUMBER_
+234 818 401 7452
*Tasted and trusted*👍🏽👍🏽
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: https://arewabooks.com/book?id=628235bbb77ff582983d6c6b
*FREE PAGE 02*
_ina matan dake fama da qaranci ko daukewar sha'awa saboda gajiya qarancin sinadarai ko kuma gajiya a jikinsu?,kina fama da maigida wajen rashin samun gamsuwa fannin auratayya?,dukka matsalarku ta yanke da HILTI UNISEX CHOCOLATE,maza garza kizo ki nema taki_
_CHOCOLATE CE da zaki shata kamar sauran chocolate,saidai kuma aiki a jiki,ba ruwanki da neman tarkacen magunguna mata marasa inganci,AKWAI TA UWAR GIDA AKWAI TA MAIGIDA_
_GAME BUQATA KO KUMA SON QARIN BAYANI,SAIYA TUNTUBI WANNAN NUMBER_
+234 818 401 7452
*Tasted and trusted*👍🏽👍🏽
_____________________________
Basu shigo gidan ba su duka sai bayan sallar isha'i,saboda suna tsayawa daukan karatu wajen malam cikin almajiransa,hannunsa riqe da baqar leda wadda taketa maiqo dauke da awara me zafi da tasha cabbage da yaji mai uban yawa.
Dai dai lokacin da iman din ke zaune gefan tabarma tare da innarmu wadda ke lazumi bayan ta gama tata sallar,abincinta na gefe bata tabashi ba,innar tana ankare da ita amma bata kulata ba,iman din irin yaran nan ne da ko kadan basa qaunar abinci,wani lokaci har sai innar ta ajjiye madoki kusa da ita sannan zata ci abincin,wannan dalilin yasa bata da kumari ko kadan,kusan duka sa'anninta sun fita girman jiki.
Tana jin sallamar alamin ta miqe daga shirin kwanciyar da takeyi,ya qaraso gefanta ya zauna yana ajjiye mata ledar awarar,fuskarta a wadace da murmushi ta janyo ledar ta fara budawa tana cewa
"Na gode yaya alamin" shima murmushi kawai yayi ba tare daya amsa ba,suka bita da kallo sanda ta miqe zuwa kitchen,da alama plate din da zata juye awarar take nema.
Kusan lokaci daya suka dauke idanunsu shi da inna,sai innar ta ajjiyr carbin hannunta gefan daddumarta tana cewa
"Zauna aminu" sabule slippers din qafarsa yayi,ya zauna daga gefa,cikin yanayi na nutsuwa
"Me yasà koda yaushe saidai ka yita biyewa shirmenta?,ta yaya ku da kuke nema ya kasance koda yaushe baka da aiki sai batar mata daa kudi?,yanzu meye laaifin daambu da bazata ci ba,saidai awara?" Murmushi ya saki kawai,sannan a nutse yace
"Inna mu din mune dolen imaan,mu ya kamata ace munyi mata daman,idan bamuyi mata ba waye zaiyi mata,kuma bata roqan kowa a waje saimu da muke yayyenta,kuma ma amfanin neman kenan inna,iman ba wani abu take tambaya ba da ya wuce dan abun marmari" kai kawai innar ta raausayar,dama tasan zaa rina indai lamin ne,wannaan ba shine karo na farko da magana irin wannan ta ratsa tsakaninsu ba,ta rasa wacce irin qauna da kulawa ce wannan da yakewa imaan din,duk da cewa sun kyautata masa matuqa da gaske,kyautatawar da duniya ma ta shaida da hakan,amma kulawar da iman ke samu daga gareshi ta musamman ce.
Koda ta matsa wajen ganin cewa ta hanashi,ko kuma ya rage tasan bata bakinta ne kawai,lamin din bazai sauya ba,a nata hasashen da ganin kamar ya kamata ya rage din,tunda ko babu komai akwai yayarsa dake aure a qauyensu,wadda wasu nauye nauye nata dana yaranta duka ya daukesu bisa wuyansa,kasancewarsa yaro jan gwarxo,mai himma qoqari da kuma neman na kansa,komai dadi komai wuya,kuma komai rintsi,kwata kwata baisan wata kalma ta lalaci,son jiki ko kuma qyuya da ganda ba,dukkan wani aiki da zai samar masa da kudi na halak yana tallafarsa,ya kuma karbeshi hannu bibbiyu yayi,babu girman kai babu ha'inci ko son jiki.
"Shikenan,Allah yayi muku jagora,yasa albarka a nemanku"
"Ameen inna...ameen" ya fada yana jin dadin addu'arta,uwa ce me yawan addu'a ga 'ya'yanta,kome qanqatar alkhairi idan sukayi,bakinta baya gajiyawa da yi musu addu'a dare da rana.
Duk sanda tayi masa addu'ar sai yaji dadi qwarai da gaske qasan ransa,ya rasa mahaifiyarsa tun hankali bai fara riskarsa ba,sai gashi Allah ya musanya masa da wata makwafinta a sanda baiyi zato ko tsammani ba,a lokacin da ya dauke haso ya kuma debe tsammani daga samun dukkan wani tattali kulawa ko kuma jin dadi,cikin tausayi da kuma jin qai na ubangiji ya hadashi da wasu kwafin na iyayensa.
Daga inda take zaune take binsu da kallo,sanda ya karbi awarar da kansa ya juye cikin farantin robar da iman din ta dauko,sannan ya zauna yana gutsutsura mata da daya da daya yana miqa mata tana ci suna hira,kallo daya xakayi musu ka tabbatar da cewa lallai akwai shaquwa me girma a tsakaninsu.
Lumshe idanunta inna tayi,bahaushe yayi gaskiya da yake cewa
"Da da da dukiya babu wanda yasan me morarsu sai Allah" ta Sauke idanunta tana tuna ranar farko da suka fara sanin lamin,ya kuma shigo rayuwarsu ya zama daya daga cikin iyalan gidan.
Malam ibrahim khalili shine cikakken sunansa,haifaffen garin maiduguri,cikakken babarbare wanda ya fito daga gida na ilimi da karatu,asalin gidansu malam khalili gida ne na malamai,da suka gaji karatu tun daga kakanninsu,malam khalili yana daya daga cikin yara uku da suka gaji mahaifinsu,duk kuwa da cewa su biyu rak mahaifiyarsu ta haifa Allah yayi mata rasuwa.
Khalili ya tashi da son karatu da kuma nema tuquru,wannan yana daya daga cikin dalilan da suka sanya yabar maiduguri,ya shiga duniya neman karatun qur'ani dama na addini haiqan,daga gari zuwa gari,har ma wasu qasashen da muke maqwabtaka dasu.
Sosai karatu ya daukewa khalili hankali,bai samu yin aure da wuri ba,har zuwa sanda ubangiji ya nufeshi da zuwa qasar niger.
A canne ya hadu da fatima buzuwa,tana zuwa daukan karatu makarantar wani abokinsa,yarinya ce a sannan me qwazo da kuma hazaqa,don lokacin ma ta kusa kammala haddar qur'ani,tana izifi na hamsin da biyar,tun daga baqara take rubutawa a allo ta haddace sannan ta wanke a sake yi mata qari,ta samu tarbiyya me kyau da kuma kulawa,duk da cewa mahaifinta ya rasu,amma mahaifiyarta batayi sakaci da tarbiyyarta ba,saboda ita daya Allah ya basu.
Lokaci daya soyayya da shaquwa ta shiga tsakaninsu,suka fahimci juna da kyau,manya suka shiga maganar aka tsaida maganar aure,ba dadewa suka angwance,ya kuma daukota ya taho da ita garin kano,inda anan ya bude tsangayarsa shima,yana karbar almajirai daga kowanne gari ko qasa.
Almajirancin makarantar malam khalili ba kamar sauran almjirci bane da muke gani ayanzu,wada aka watsar da duk wani mutunci da kuma kimarta a yanzu,yara suke wahala da sunan neman ilimin alqur'ani me girma,wanda sam hakan bashi da tushe bare asali sam cikin addininmu.
Dukka yaron da zai karba sai ya kasance makusancinsa ne ya kawoshi,zaa rubuta adreshinka da lambar wayar wanda ya kawoka,sunan gari dana qauyenka da kuma inda za'a iya samunka,sanna bai yarda a kawo masa yaro babu haka ziqau ba babu abinda zaici,abun kwanciya da kuma kayan baqatun yau da kullum,saboda shi din bai yarda da fita bara a makarantarsa ba,karatu aka kawo yaran shi sukeyi,yakan baka zabi idan ka soma hankali,kana da sha'awar karatun boko?,idan kana dashi zai shaidawa iyayenka ya sanyaka a makaranta,idan baka buqata kuma zaka kama sana'a ne,don bai yarda da zama babu sana'ar yi ba,saidai kowacce sana'a kake kana yinta ne bisa sanya idanunsa da kulawarsa,da kuma tabbatar da cewa sana'ar da kakeyi din bata sabawa addini da kuma al'ada ba.
Wannan dalilin ya sanya makarantarsa ta kasance mai tsari,mutane da dama sukeso kawo yaransu karatu nan wajensa,saidai duk shekara akwai adadin da yake dauka,idan suka cika kuma baya sake dauka sai wata shekarar.
Zamansa da fatima wani irin zama ne me matuqar dadi da kuma ban sha'awa,khalili wani irin mutum ne managarci,mai halaye da kuma dabi'u masu kyau,tsayyen akan harkar gidansa da kuma sauke nauyin iyalinsa,idan kaga fatima zakayi tsammanin tana auren wani me halin ne,saidai ko daya,tsabar kula da take samu ne da kuma tsaiwar mijinta wajen sauke nauyinta,babu abinda ta nema ta rasa,tana matuqar jin dadin xama dashi,kamar yadda shima yake yaba mata,yake kuma matuqar jin dadin xama daa ita,saaboda ita din macace ta gari,mai tarin biyayyawa mijinta,wadda tasan dai dai ta kuma san akasin hakan,bai taba cewa tayi ta musa ba,kamar yadda bai taba cewa ta bari taqi ji ba,Shi yasa shima yake qaunarta,da kuma qoqarin ganin ya hidimta mata iyakar iyawarsa,bata nema komai ta rasa ba cikin gidanta,cikin wannan yanayin,shekara biyu da aurensa Allah ya albarkaceta da samun haihuwar santalelen da namiji,aka sanya masa abubakar saddiq.
Daga kan saddiq tayita haife haife suna mutuwa wato WABI,makusanta da wasu cikin dangi sukayita so malam khalili ya qara aure,amma yace sam baiga dalili ba,yanajin dadin zama da matarsa,bai nema komai ya rasa ba,idanma ta hahuwa ce,kana iya haifar yaro guda daya amma ya zame maka me albarka fiye da masu tarin yaran,indai yana da rabo a haihuwa zata qara,ita kanta a sannan ta bashi dama amma yace bazaiyi ba,Cikin ikon Allah kuma sai Allah ya basu haihuwar hajar iman,haihuwar da duka fidda rai da ita,zuwan iman a daidai wannan lokacin ya janyo mata soyayya mai tarin yawa,saboda tazo a sanda basu zata ba,ta kuma zo a dai dai lokacin da suke marmari da buqatar qaramin yaron cikin gidan.
Shekarar iman daya a duniya da watanni biyar lamin ya shigo rayuwar cikin gidan a lokacin.
Yadda jama'a keta yabawa malam khalili kan yadda makaranta da kuma dalibansa suke a tsare ya sanya malaman wasu tsangayun dake unguwarsu da kuma wasu unguwannin suka shiga adawa da kuma takun saqa dashi,suke kuma matuqar jin haushinsa,ganin cewa ya fita daban da sauran malaman tsangayu,babu bautarwa ko azabatarwa ga dalibansa,kamar yadda bai yadda ya zama cima zaune me matacciyar zuciya ba,sai abinda iyayen yara suka dauko suka bashi,aah,shima kamar kowa,duk sanda ya tashi dalibansa shima yana tafiya neman kudinsa,ya dawo kuma lokacin da aka kusa sake zama ci gaba da karatu,komai nasu na tafiya a tsare ne,kana ganin dalibansa da yadda yake tafi da komai dole ya baka sha'awa.
Daren wata jumma'a ne,tana zaune tsakar gidanta daya kasance sai ita daya,sai hajar dake kwance a gefe saman wani abun shinfidarta me hade da katifa maras tudu,duk kuwa da cewa akwai motsin almajirai da hayaniyarsu daga qofar gida amma cikin gidan ba kowa,saboda babu wanda ke shigarwa malam gidansa gaba gadi don suna almajiransa,idan kaga yaro cikin gidan,to qaramine wanda shekarunsa basu wuce wanda shari'a ta wanzar da hani na shigarsa gidajen matan aure ba,tana da mai mata aike da maiyi mata wanki ana biyansa duk a cikinsu,bai yarda suyi mata aiki ba tare daya biyasu ba,saboda yace su din mutane ne suma kamar kowa.
A hankali hayaniyar tasu ta fara raguwa,da alama an gama rabon abincin dare ne,wanda ake auna cikin abincin kowa a hada,manya a cikinsu su dafa a rabawa kowa,a wani gida da suke zaune wanda yake daura da gidan malam din,gida ne da wani bawan Allah ya bayar kyauta su dinga kwana,hankalinta bai wajen sosai,yana can ga tunanin abinda ya tsaida malam da din bai dawo yadda ya saba ba,shi da saddiqu da yayi masa rakiya.
"Taho a hankali....riqeshi sadiqu" ta jiyo maganar malam din tun daga soro,abinda yasa ta ajjiye allon da take rubuta fasayakfika humullah ta maida hankalinta ga qofar shigowa gidan.
Malam dinne da sadiqu da wani dan farin yaro da bata sanshi ba,ta miqe tana masa sannu da xuwa,ya amsa hankalinsa yana kan yaron
"Maza dora ruwan zafi innar saddiqu" malam din ya fada yana tsugunnawa a gaban yaron,yana yage ragowar rigar jikinsa,da hanzarinta ta koma madafa,ta hada ragowar itacen data gama girki ta kunna ta dora masa ruwan,sannan ta dawo tsakar gidan,inda malam ke tsugunne gaban yaron yana masa sannu,sadiq na tsaye a saman kanshi yana kallonsu.
Kujera 'yar tsuguno ta jawo ta zauna,idanunta akan yaron da yake cikin hali na galabaita ta yiwa malam sannu da zuwa
"Yauwa binta" ya amsa da alamun rashi na a bace ne
"Ki duba maganin zafi don Allah idan akwai,idan ruwan yayi zafi ki juye sadiqu ya tayashi gasa jikinsa,bari naje na dawo" daga haka malam din ya miqe ya fita.
Duk yadda malam din yace tayi haka tayin,ya gasa jikinsa da kyau,sauran ta sakashi ya shiga bayi yayi wanka dashi,cikin kayan sadiqun ta zabo wasu ta bashi ya sanya,don xasuyi kai daya dashi,yana gamawa ta zuba masa abinci,ta koma ta dauki iman data tashi ta fara rigima ta fara bata nono,daga inda take din tana kallon yadda sadiqu ya sanyashi a gaba yana kallo,tun dazun shima zuciyarsa a karye take fuskarshi ta nuna hakan.
Malam ne yayi sallama,ya qarasa gaban yaron yana duban yaron daya ambata da lamin,ya bashi paracetamol din daya shigo dashi da kuma ruwan tea me zafi a leda,yace idan ya gama yasha yasha maganin,sai saddiqu ya kaishi daki ya kwanta.
https://arewabooks.com/book?id=628235bbb77ff582983d6c6b
Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.
*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*
_____________________
*KUFAN WUTA*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_
*YADDA AKE BUDE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form din kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 03
https://arewabooks.com/book?id=628235bbb77ff582983d6c6b
🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ZAFAFA BIYARRRRR*
*_INGANCIN LABARAI_*
*_FASAHA NUTSUWA DA IYA SARRAFA ALQALAMI_*
*_TSARI DA TSANTSAGWARON HIKIMA_*
*_SOYAYYA MAI RATSA ZUKATA DA NARKAR DA ZUCIYA_*
*_JIGON LABARAI DA YASHA BAMBAM DA NA SAURA MAI SANYA ZUCIYA MAMAKI DA TUNANI_*
*_YIN LINQAYA CIKIN DUNIYAR LABARI KAJI KAMAR DAKAI AKEYI DA GASKE NE_*
*DUKA SAI CIKIN GAMAYYAR LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*_ADADE ANAYI SAI GASKIYA_*
*_HIKIMA KASHIN KWANCE_*
*ABOKAN HIRA NE GA WANDA KE CIKIN KADAICI!*
*ABOKAN TAFIYA GA WANDA KE CIKIN NISHADI*
*WARWARAR MATSALA GAME NEMAN MAFITA*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
______________________________
Ajjiye iman inna tayi sannan ta nufi daki,ta dauko babbar tabarmar malam din da yakan zauna a kai ta shimfida masa,sannan ta gabatar masa da abinci da ruwan wanke hannu,ta zauna nesa kadan dashi tana ci gaba da shayar da iman wadda ke rigima saboda bata qoshi ba,ta sakeyi masa sannu da xuwa
"Yauwa sannu binta,ya hidima ya gida"
"Alhmdlhi" ta fada tana dan murmushi,duk data saba da irin wannan kulawar tashi,amma duk sanda ya tambaya din hakan yana mata dadi,saboda tasan cewa mata da yawa ne suke neman hakan basu samu ba
"Wannan yaron da kike gani sunansa lamin,na tsinceshi ne a can unguwar da naje nida saddiqu dubiyar abokina,abinda ya bani mamaki yaro qarami yashe gaban famfon tuqa tuqa,jikinsa duka tabo na duka,yasha ruwa yanata amansa,wadda ina tsammanin babu komai ne a cikinsa,yayimin kama da almajiri don haka na matsa kusa dashi,sai daya dan rage aman na tambayeshi sunansa da kuma inda yake,yamin bayani,ashe almajirin makarantar malam dan lami ne,sai na tuna kwanaki uku da suka wuce tabbas naji ana neman wasu cikin daliban,na tambayeshi me yakeyi to a nan,kansa tsaye ya shaida min guduwa yayi,na masa fada na kuma nemi dalilin da yasa yabar makarantarsu,shi baya jin tsoron wani abun kada ya sameshi,a yadda na fahimta tsoron malamin da makarantar yafi tsoro akan duk abinda zai sameshi,abun takaicin kudi malamin yake sanya musu duk ran laraba,kowa sai ya kawo wadan nan kudaden,idan kuma ba haka ba,zai ma yaro duka mai tsananin da zai gwammace koma ta yayane ya samo ya kawo masa,to shi kusan duk sati sai an dakeshi,saboda baya iya kawo komai,don yace bazai iya yadda sauran sukeyi ba,don cikinsu harda masu sata don kawai su kawo,lamarin ya dagamin hankali,na daukeshi na maidashi gaban malamin,duk da inajin tausayinsa,amma babu gatan da xanyi masa da ya wuce hakan,saidai abun mamaki abun takaici kuma abun haushi,sanda naje ga malamin,tunda ya tambayi waye ni ya fara yimin wani kallo,nasa ma'anar kallon,tunda sarai nasan waye malam dan lami,yana daga cikin masu adawa da tsarina,amma ni hakan bai dameni ba,burina da fatana shine kowa ya gyara,tun kafin nakai ga cewa komai ya soma dakawa lamin tsawa,tare da jifansa da miyagun sunaye da kuma kalamai,ya kuma fara hanqoran neman manya cikin dalibansa su dauke lamin su saka masa shi a mari,abinda bai jima da fita daga ciki ba,a nan na nuna masa nima ainihin xafina,na hana kowa yaxo wajen ya taba yaron,a nan malam dan lami ya tada husumar cewa dalibinsa ne,kuma babu wanda ya isa ya hanashi yi masa duk hukuncin da yaga dama,tunda a hannunsa aka danqashi,indai kuwa bazai hukunta laminu ba,saidai yabar masa makarantarsa,ya koreshi,ya kori yaron ba tare daya tsaya yaji meye zance ba,bai tsaya yaji me yaron shima zaice ba,bai kuma sanar da magabatansa ba bare susan ina yaronsu ya koma"
"Na fuskanci tijara yake ji,don haka bance komai ba na tattaro al'aminu,na wuce dashi chemist saboda yanayin ciwuka da raunin dake jikinsa na tabon bulalai da duka da kuma mari daya dade a qafarsa ya zame masa ciwo. A hanya nake tambayarsa wayeshi da kuma qauyensu,ya shaidamin shi din dan birnin kudu ne,mahaifiyarsa ta jima da rasuwa tun yana qarami,yayarsa da ita ta riqeshi har zuwa sanda ya tasa,mijin yayar yace bazai iya daukar nauyinsa ba saboda shima bashi da komai,yayarsa bata da yadda zata riqeshi saboda shi da itan duka marayu ne,hakan ya sanya mijin yayar ya kawoshi bara,ya damqa shi a hannun malam dan lami,tunda kuma ya tafi bai waiwayoshi ba,duk da cewa bai wani jima a makarantar ba,azaba ba wacce bai gani a waie malamin ba,don kusan karatun ma dana tuntuba ba wani mai yawa bane,azabar da suke sha tafi karatun yawa,wanna dalilin ya sanya na yanke shawarar kawoshi makarantata yayi karatu,zuwa sanda zai warware kuma mu nemi ita 'yar uwar tasa ko mijinta mu gaya masa inda yake a yanzu".
Kai inna ta gyada idanunta na kan lamin,zuciyarta cike da tausayinsa,tunda malam yake kawo almajirai bata taba ganin yaron da taji ya kwanta mata ba kamar lamin din,a dan awannin da yayi dasu wanda bai wuce awa daya da rabi ba,ta fuskanci nutsuwar dake tattare da yaron,komai nashi a hankali yakeyi cikin nutsuwa
"Allah ya rufa asiri,ya gyara mana xukatanmu" shine abinda inna ta fada,suka kuma fara rayuwa da lamin din,wanda cikin kwanaki biyu ya sake da sadiqu,wani irin sabo sukayi sosai dashi,saika zaci sun dade tare.
Tun farko dama aminu din bai soma kwana cikin almajirai ba,cikin dakin saddiqu suke kwana,hakanan hatta da suttura ta saddiqun yake sanyawa,kafin daga bisani malam ya bayar da kudi inna ta samo musu gwanjo masu kyau shida saddiq din,sosai sadiq ke murnar samun dan uwa,lokaci kadan lamin ya shiga jiki da zukatan su inna,saboda yarone haziqi,duk wani aiki da saddiq keyiwa inna da malam alamin din ya daukeshi,sai malam da inna na hanashi suna raba musu kowa ya dauki nasa.
Kusan tare sukayi rainon iman da inna,idan inna tana aiki tofa iman tana hannunsa,yayita tiri tiri da ita kenan,tun tana masa qyuya har ya zamana duk cikin gidan babu wanda take yarda dashi Kamar yadda take yarda da alamin,wani lokaci idan aiki ya kacamema innan idan ya dauki iman sai tayi da gaske ta korashi makaranta sannan zai tafi,sannu a hankali sai sabo da shaquwa suka shiga tsakaninsu,baya son kukanta,baya son abinda zai taba iman din,da a daki iman din gwara a dakeshi,koda malam ya sanyasu makaranta sai ya zamana sai ya fara kai iman sannan shi zai wuce,koda kuwa shi xaya makara,kudin break dinsa kuwa badai yaci a cikinsa ba,komai ya gani shi zai kwasowa iman din ya kawo mata,idan kaga yadda yake matan sai ka rantse da Allah ciki daya suka fito.
Kamanni ne kawai zasu tona asiri,saboda kowa a cikinsu kamanninsa daban,hasken fata ne kawai ya hadasu,tun iman na qarama ta fita daban,tana da kyan fuska qwarai da kuma yalwar suma,wadda ta gajeta daga wajen inna.
'yar lele iman take a wajen alamin tun tana da qananun shekaru,zai iya hana cikinsa ya bata,duk abinda tace tana so to matuqar yana dashi sai ya bata,idan babu kuwa zai nema mata,abinda yasa ya tashi kenan da zuciyar nema,zama da madaukin kanwa inji hausawa sukace shike kawo farin kai,tun saddiqu bashi da ra'ayi har zama da lamin ya sanya ya zama mai neman na kanshi kamar alamin din.
Kusan duk kudin daya samu wajen nemansa fiye da rabinsa siyawa iman wannan ne siya mata wancan,tun bata isa ado ba yake mata siyayyar kayan kwalliya da qyale qyale,tun malam da inna na fada,har suka fahimci a jininsa yake kulawa da iman,bazai iya dainawa ba,dole suka haqura suka sanya masa idanu,saidai innan tayi masa fada da kuma dabarar ya dinga aje wani abu saboda yayarsa,wadda a yanzu shekaru ke sake jaa nauyi na dada hawa kanta,tana kuma da buqatar taimako ko yaya ne.
Alamin shine kewa iman komai,itama duk abinda take da buqata alamin din take durafafa kanta tsaye,bata ko kallon sadiqu dan uwanta,saboda yana da zafi shi din,hakanan yanzu yanzu ba wani abu bane yakai mata bugu idan tayi ba dai dai ba,sabanin alamin.....wanda bashi da daukan zafi a kanta,hasalima yana tare duk wani abu da yasan xai bata ranta ko ya cutar da ita,idan tayi ba dai dai ba cikin ruwan sanyi zai nusasheta ya kuma gyara mata,tana kuma daukan maganarsa fiye data kowa cikin gidan.
Dinki dashi lamin yafi qwarewa,ya iya dinkin mata kamar masifa,har zuwa yanzu da yake kan shekara ta kusan goma sha shida,wannan yasa iman dake da shekaru goma sha daya cikin rayuwarta tun a sannan ta zama abun kallo,indai tayi kwalliya kowa sai ya yaba,tana da kyau sannan kuma alamin din yana fitar da ita da dinkuna sai kace wata qatuwar budurwa,don idan kaga dinkunan da take sanyawa saika tambaya waye yayi mata,sau tari idan yayi dinkuna ya samu kudi sosai,yakan je kasuwa ba tare daya gayawa kowa ba,ya samo mata atamfa falle bibbiyu masu sauqin kudi ya mata skert da riguna tsala tsala,saboda bata iya daura zani ba har yanzu,abinda yake hadata da inna kenan,kullum fama take amma har yanzu iman din bata iya ba,koda yaushe saidai ayi mata riga da skert ko kuma doguwar riga.
Idan kaga iman din saika dauka diyar wani ce,saboda bata rasa komai ba,kullum tsaf zaka ganta cikin suturu masu kyau.
Amin Abubakar haifaffen garin birnin kudu ne dake jahar jigawa,bafulatani ne uwa da uba,abinda yasa ya gaji kyau kenan shima tun quruciyarsa,tun shekarunsa basu fara nuna ba,yaro ne da tun a halittarsa Alla ya masa baiwa masu tarin yawa,yana da nutsuwa qwarai da gaske wadda ta hade masa da miskilanci,miskilancin da tun zamanin quruciya ya sanya ba kasafai zaka ganshi cikin wasanni irin na yara ba,yafi ganewa yana zaune daga gefe yana kallonsu,idan abu ya burgeshi ya saki murmushi kawai.
Kafin rasuwar mahaifiyarsa ya samu tarbiyya qwarai daga wajenta,wannan tasa ya zama wani na daban,idan yana wasu abubuwan saika dauka wani babba ne me shekaru.
Yadda malam da kuma inna suka riqeshi abune da bazai manta dashi kafatanin rayuwarsa ba,sun masa wani gini sun kuma zame masa garkuwa kuma ginshiqi cikin rayuwarsu,ya fahimci daga inna sadiq da kuma malam dukkaninsu suna qaunar iman,suna dannewa ne saboda yanayi irin na tarbiyya,shi kuma baiga abinda zaiyi ya faranta musu ba fiye da kula da abinda sukeso,hakan yasa ya sanyawa kansa bawa iman din dukkan kulawa,sannu sannu kuma sabo da shaquwa suka shiga tsakaninsu.
Wani lokaci har mantawa yakeyi,yakan kallo iman din a matsayin 'yar uwarsa ta jini,har sai idan wani abun ya gitta da zai sanya ya tuna cewa ba jininsa bace.
_shimfida kenan......muje zuwa_
_ina matan dake fama da qaranci ko daukewar sha'awa saboda gajiya qarancin sinadarai ko kuma gajiya a jikinsu?,kina fama da maigida wajen rashin samun gamsuwa fannin auratayya?,dukka matsalarku ta yanke da HILTI UNISEX CHOCOLATE,maza garza kizo ki nema taki_
_CHOCOLATE CE da zaki shata kamar sauran chocolate,saidai kuma aiki a jiki,ba ruwanki da neman tarkacen magunguna mata marasa inganci,AKWAI TA UWAR GIDA AKWAI TA MAIGIDA_
_GAME BUQATA KO KUMA SON QARIN BAYANI,SAIYA TUNTUBI WANNAN NUMBER_
+234 818 401 7452
*Tasted and trusted*👍🏽👍🏽
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 🔥🔥 *KUFAN WUTA*🔥🔥
NA
*HUGUMA*
Free page 04
*_MASOYA 'YAN QASAR NIJER,ZAKU TURA KATIN WAYA(AIRTEL/MOOV) TA WANNAN NUMBER_*
+22795166177
Zaune take saman kujera 'yar tsugunno,sanye da uniform na makarantar primary din da take zuwa,tana ta qoqarin daura takalmin sandal a qafarta,komai nata tsaf kuma fes,karin guga ya kama uniform din jikinta sosai,shaidar cewa suna samun kulawa yadda ya kamata,hatta da takalmin sandal din qafarta qyalli yake,kamar yadda farar safarta take qal kamar baa sakata.
Wannan kusan duka aiki da horon lamin ne,idan baiyi mata da kansa ba,to ya riga ya koyar da ita,iman din akwai tsafta kamar yadda lamin din yake,bare ma kafin ta yiwa kanta wani abu sau daya yayi sau goma,wankinta da nashi duka suna wuyansa,kama daga uniform dinsu zuwa kayansu na zaman gida.
Lamin din na tsugunne gefan kitchen yana shirya mata abinci a wani dan qaramin kwando me kyau,wanda shi da ita sukaje ta zaba ya siya mata,tana ta masa surutu yana biye mata,wanda duka akan jarrabawar common interence da zata zana ne a yau,inna na daga cikin kitchen din tana zubawa shi yana shiryawa har ya gama,dai dai sanda ta gama sanya safa da kuma warin takalmi daya,dayanne ya gagara,don haka lamin din ya qarasa wajen ya tsugunna ya kama takalmin yana daura mata,sannan ta miqe tana diban takardunta sabon pencil biro har ma da cleaner dasu sharpener da lamin din ya siya mata.
Suka miqe suna yiwa inna sallama,saboda lamin din ne zai kanta har can inda zasu zana jarabawar da kansa,daidai lokacin malam ya shigo
"A'ah,har kin gama shiryawa kenan,to ai Allah yasa motar bata tashi ta barki ba" malam ya fada yana danna wayarsa Tecno keypad dake hannunsa saboda yaga lokaci
"Dama ba tare zamu tafi ba,ya lamin ne zai kaini" iman ta fada tana duban malam
"A'ah,wanne irin sakarci ne wannan,ya ga motar makaranta zaki ce saidai laminu ya kaiki?,ki wuce ki shiga cikin 'yan uwanki dalibai ku tafi"
"Ai malam kada ma ka bata bakinka,babu yadda bayi dasu ba,tun jiya nake sababi,amma dole ne naja bakina na tsuke,saboda shine yake goya mata baya,wai kada ta shiga cikinsu uniform dinta ya cukurkude......sai kace tafi kowa" jin inna ta sako baki ya sanya iman ta fara narai narai da ido kamar me shirin sanya kuka tana duban lamin din,so take ya sanya baki,kada su malam su hanashi ya rakata.
Zahiri ita tsoro takeji,saboda yadda taji wadanda suka gama primary wancan shekarar suke fadan wahalar jarabawar,duk da yadda lamin din ke qarfafa mata gwiwa tare da nuna mata cewa ba wani abu,suma sunyi fa,iya karatu tasan ta yishi,don a rana suna kwashe awanni masu yawa lamin din yana mata lesson,tana da matuqar qoqari da fahimta,saboda haka duk karatun da yake mata tana daukeshi,wannan dalilin ne yasa lamin din yaci burin tayi karatu mai zurfi,duk sa'ilin da suka zauna suna hira kuwa rabin maganarsa kenan,wannan abu yayi tasiri itama cikin ranta,bata da burin daya wuce ta ganta ta gama qaramar makaranta ta shiga jami'a,ta zama likita lawyer ko 'yar jarida,cikin ukun nan takeso ta zama daya.
"Malam kasan wannan shine karonta na farko da zata fita wani waje tayi jarrabawa irin wannan,rakatan kuma zai qara mata qwarin gwiwa,tunda makarantar basu hana ba malam ka bari na kaita" da qyar lamin yasha kansa ya barsu suka fice.
A soron gidan ya dakata yana cewa
"Bari na tada sadiq ya rakani,tafiya bibbiyu tafi dadi"
"Yaaya,Allah bazaije ba koka tasheshi" iman ta fada tana jan tunga,sai ya waiwayo ya kalleta,taso bashi dariya yadda ta tsuke dan qaramin bakinta ta marairaice,ya fuskanci so ne batayi yaje din,don tabbas idan suka tafin tare bazai barta ta sake ba,duk kuskuren da tayi saiya taso mata da fada hantara ko kyara.
"Ina zuwa dai" ya fada yana saka kansa cikin dakinsu.
Saidai duk yadda yaso tada sadiq din ya rakashi ya qiya,sai ya cusa kansa ma qasan filo yana cewa a dawo lafiya,Allah ya bada sa'a,dole ya fito daga dakin ya barshi.
Dadi iman din taji,ta dinga boye dariyarta har sai data fito ta dara,harara lamin din ya watsa mata da lumsassun idanunsa
"Ni kikewa dariya saboda ya yarfani ko?" Sake qyalqyale masa tayi da dariyan
"To ai yaa lamin kai kam baka iya harara ba,hararaka irin ta masu jin bacci ce" fara'ar fuskarta kadan ta ragu
"Ya lamin,ni dakai me yasa dukanmu bamu da lafiyar ido?" Ta tambayeshi sanda suka kusa ficewa daga layin nasu tana dubansa,da alamun damuwa cikin muryarta.
Murmushi ya sake wansa iyakarsa saman lebansa,duk da qarancin shekarunsa amma yanayinsa kamar wani babban matashi,akwai wani iri kwarjini na daban dake fita saman fuskarsa.
Duk da cewa a shekara ta sha bakwai yake amma hankalinsa tabbas yafi na iman din nesa ba kusa ba,kasantuwarsa namiji ita kuma diya mace
Cikin harshen da yake ganin zata iya fahimta ya fara mata magana
"Lafiya lau idanunmu suke ni dake,ba kina gani sosai ba?,ko akwai wani abu da bakya iya gani" saifa girgixa kai alamun a'ah
"To kin gani ba.....nima ina gani sosai,har daga nan ina iya ganin wanda ke tsaye gaban rumfar malam dalha" ya fada yana nuna wajen da yatsa,abinda ya sanyata tada kai ta kalli wajen,kawai tazarar nisa a tsakaninsu,don haka abun ya bata mamaki,har ta fidda idanu,sannan ta waigo gareshi
"Yaaya" kai ya jinjina mata,bata sake kokwanto ko tantama ba,saboda tasan halin lamin din tunda ta fara wayo,qarya itace abu na qarshe da baya kusantarta a rayuwarsa kaf,koda ya gaya mata waye a tsayen,da suka isko wajen saita ga shi dinne kuwa,abinda ya sanyata sakin dariya
"Na yarda Allah yaya,lafiyarmu qalau" murmushi ya kuma saki a maimakon dariya
"Na gaya miki dama,yanayin halitta ce,kowa da yadda Allah ya halicceshi,kamar yadda yayi wani dogo,wani gajere,wani fari wani baqi,wani me kyau wani akasin haka"
"Wani me suma me kyau irin taka,wani kuma tashi irin ta yaya sadiqu ko?" Wannan karon dariya ta bashi,har haqoransa suka bayyana
"Zaki bayani duk randa kika fada a gabansa,shima sumarsa me kyau ce sosai iman....,amma taki tafi tasa kyau sosai" murna ta cikata,tadanyi tsalle kadan
"Don Allah yaya ba na fishi kyau ba?"
"Neeeesa ba kusa ba" ya fada yana duban fuskar dake cike da quruciya,murmushi na fita daga kan tata fuskar
"To amma me yasa yake cemin me idon mage,mummuna?" Ta tambayeshi tana tura baki,saiya sake sakin murmushi,indai yana tare da iman din bata bari fuskarsa da bakinsa su huta
"Ki rabu dashi,kishi yake dake" ta saki qaramar dariya cikin nishadi,tana jin dadin zama da ya lamin fiye da kowa cikin gidansu,duk sanda zai bata amsa,yana bata amsa ne ta yadda zata dace da ra'ayinta da kuma abinda takeson ji,indai yana nan baya bari bacin rai ya zauna saman fuskarta,da irin wadan nan hirarrakin sannu a sannu har suka samu abun hawa,ya kaisu inda daliban shekarar daga makarantun wannan qaramar hukumar zasu zana jarrabawar.
Sai daya tabbatar da shigewarta exam hall din sannan ya juyo zuwa gida,a qafa ya zabi ya tako zuwa gidan,saboda kudin dake gareshi su isa kawosu gida shi da iman din zuwa la'asar idan an gama jarrabawar.
Yana gab da isowa qofar gidan nasu ya hangi yarinyar na tahowa,ubaida 'yar layinsu ce,ya fuskanci duk sanda xasu hadu da yarinyar saita dinga wani sinqe sinqe,idan sukayi clashing kuwa haka zata gaidashi cikin girmamawa,duk da cewa kwata kwata shekarun da ya bata basu wuce biyu ko daya ba,saidai yanayin garin jiki da kuma kwarjinin da yake dashi,zaka zaci cewa wani babban yayanta ne.
Yanzun ma yana kallonta tayi wuf ta shige soron wani gida ta buya,saidai taci gaba da leqensa har ya wuce ta sannan ta fito.
Yana da yawan gumi,don haka sanda ya isa dakinsu ya jiqe da zufa,ya samu sadiqu ya fito a wanka daga bandakin da ba'a dade da yi musu ba cikin dakin nasu,wanda suka hada kudi abinsu shi da saddiqun aka musu,saboda girma da sukaga sun fara,lamin ne ya kawo wannan shawarar,kuma ta kwantawa saddiq din,da yake dakin ma sha Allah yana da girma,don ya dauki katifunsu guda biyu bayan leda me kyau dake malale a dakin,da yake ba wanda yake shigar musu kuma wuni suke wajen sana'a ledar lafiya lau take,sai kujera guda daya doguwa da kuma kwabet ta katako mara tsaho amma kuma tana da fadi,anyi mata bangare biyu kowa da sashen kayansa,kusa da kujerar akwai wani dam teburin na katako da talabijin ta zaune,da receiver a kanta,wadda suka jona daga maqota,dama ba wani kallon arziqi suke ba,sunfi kallo sanda ake ball da wani waje,shima kusan sadiq ne me wannan nacin,lamin din yafi ga sauraren news a redio.
Suna hada ido ya harari sadiq din wanda yake daura tazugen gajeran wandonsa
"Baka kyauta ba wallahi,abinda kake sam bai kamata ba"
"Allah ya sani bazan iya irin rayuwarka ba,yarinya sai shegen fi'ili da shagwabar banza da wofi,kamar wata yayayya,ayita riritata,yarinyar da an kusa bude mata littafin ayyukanta nan da wasu shekaru kadan" sadiq din ya amsa masa yana zura riga a jikinsa,harararsa lamin ya sakeyi
"Idan bamu kula da ita ba da waye ne zamu kula?,ita kadai ce fa a gabanmu?,kuma ma ina wani shagwaban yake?,kaidai matsala ce dakai kawai,kuma idan baka canza ba bazamu taba dai daitawa ba" daga haka yaja towel dinsa dake hannun kujerar ya shige bandaki,yana jiyo sadiq yanata qananun maganganun indai iman bata canza ba shima bazai canza ba.
Kansa kawai ya kada cikin takaici,dukkaninsu har yau sun kasa karantar iman,kamar shi daya shi da.malam ne suka fuskanceta,ba shakka tana da sakalci da shagwaba wani lokacin da gabunta irin na yaran da ake haifa daga qarshe,to amma fa tana da hankali da wata irin nutsuwa,haka kuma tana da fikira da saurin fahimtar abu,ko yaya ka zauna da ita zaka san cewa uwa ta gari ta taka muhimmiyar rawa wajen nutsuwarta da dabi'unta,yarinta kuwa har yanzu bata wuce lokacin ba,so dole sai an dinga mata uzuri ana nusasheta harta wuce lokacin.
Sanda ya fito lallausar sumarsa mai santsi da zaka zaci relaxer yake sanya mata tanata digar ruwa,zuwa sannan har sadiqu ya shiga cikin gida ya karbo musu abun karyawa,kunu ne me zafi sai qamshin lemon tsami yake,sai kuma fanke da qosai wanda ya tabbatar qosan nashi ne,saboda shi fanken bai dameshi ba,qosai ne koda ya huce zai cishi a haka yana jin dadinsa,koshi ko alala,sau tari sadiq na tsokanarsa da cewa
"Wai lallai saika nuna kai cikakken bafullaci ne,qauna ce shadidiya tsakaninku dama da qosai" wani lokaci yayi dariya ya barshi,wani lokaci kuma ya rama.
"Yauwa,daga kan plocker dinka akwai saqo gashinan an bani,ka duba" sadiq ya fada yana qoqarin kai cup din kunun bakinsa,ajjiye towel din da yake goge kansa dashi yayi ya qarasa gaban locker din,wadda take dauke da tarkacen kayan shafa na maza,kai kace wani zabgegen saurayi ne,tarin turaruka ne kala daban daban,kama daga roll-on, sure,body spray,body mist masu sanyi,da turaruka na kaya shaving cream,da body cream masu sauqin kudi,man wanki baki da mayukan gashi na maza,sai kuma man saka takalmi yin qyalli.
Hannu yakai ya dauki farar takardar da aka nannadeta four corners,ya ware a hankali,sannan ya zuba mata sleepy eyes dinsa da suke a lumshe,yana bin yadda aka zane takardar da zanen furanni da kuma tsuntsaye,sannan ya sauka ga saqonnin soyayyar dake rubuce a tsakiyar wani lafcecen heart (zaku iya tunawa da wasiqar soyayya da ake rubutawa zamanin quruciya?,ya kai zunzurutun zinaren mazirarin zuciyata?😂).
Maida wasiqar yayi sama a qasa yana lalubo sunan marubuciyar,sunan ubaida ya bayyana,saiya linke takardar,sannan ya waiwaya ya dubi sadiqu
"Yaushe ka mayar dani dan iska ka fara karbo wadan nan abubuwa kana kawomin?,bari to na ajjiye na kaiwa malam,kada wataran ya kamaka ya zaci bakinmu daya,ko kuma ni nake aikenka" da hanzari sadiq ya tashi yana danne dariyarsa yasha gaban lamin dake zura jallabiyarsa ta barci
"Kaga.....ni kada ka yimin sharri,ni ina ruwana?,ina zaune ta aiko qanwarta ta kawomin,kaga kenan bani na janyota ba ko bare kace" tsayawa yayi yana duban sadiq din,ya sanshi qwarai da rawar kai,saboda yawancin lokuta idan yaga ana tashi daga aiki lamin din ya biyo masa ya sakashi a gaba sunyo gida,suna isowa anyi magariba sunyi masallaci,saga can sun zauna karatu da malam,ana tashi hira cikin abokansu lamin din baya bari su zarce awa daya zai takura sadiq din kan su shiga gida,ko su zauna a dakinsu suyi wata hirar,ko suyi karatu,ko su kalli ball idan nepa sun agajesu da wuta,ko kuma su zauna tare da inna kafin malam ya shigo,yakan yi qorafin
"Waikai.....sai kace wasu mata da Allah,kai ko dan 'yammatan nan da akeyi na layi bamu da,kana gani su buhari fa,yarinyar nan ta bayan layinmu har dan wasiqa suke aikawa junansu" kallonsa kawai lamin yakanyi
"Shekararmu nawa ne?"
"Sha bakwai mana,ni harda watanni ma"
"Tabdijan,a shekara sha bakwan har mukai wannan matakin?,meka ajjiye?,me kake dashi?,wanne mataki ka taka a karatu?"
"Mtseeww,ka gane mana,bafa wai aure zamuyi bafa,kawai irin dai soyayyar nan da kowa ke tabawa ce,ai abun kunya ne a yadda mukafi dukka samarin unguwar nan kyau amma ace mune bamu da budurwa"
"Nidai a wajena ba abun kunya bane,amma tunda kai a wajenka haka yake,kaje Allah ya bada sa'a" daga haka ya maida hankalinsa ga qaramar tvn dake gabansa,wanda suke hasko wasan da ake bugawa ta gasar nahiyar turai,tsakanin Manchester da Barcelona.
Yana jin sadiqun yana mitar yanzu kallon qwallon ma sudanje gidan kallo suyi cikin mutane amma abu ya gagara,kowa yana can ma su suna cikin gida kamar mayu.
Shi sam irin wadan na shirmen na tashen girma Allah ya tsameshi,baya bashi sha'awa ko kadan,yadda yake gudanar da rayuwarsa yafi masa dadi,shi mamaki ma yake idan yaga sa'anninsu suna soyayya,tome zasuce a wadannan shekarun nasu?,dariya suke masa idan ya fadi hakan,sau tari sukance
"Dama mune muke da kyau irin naka?,kai don bakasan yadda 'yar mata matan nan ke sonka ba,miskilancinka kawai yasa suke shakkar yi maka magana".
Hannu lamin ya sanya kan locker din tasa bayan ya gama wannan tunanin,ya ciro wani man fito da saje da qasumba da sadiq din ya siyo tun rannan,wurgi lamin yayi dashi saman kujera
"Shi yasa dama ka siyo wannan saboda kayi sauri ka hada gemu kai dole gaka babba ko?" Yadda lamin yayi maganar cikin jin haushi ya sanya sadiq qyalqyalewa da dariya dole
"To wai kai din da kaketa haka waliyyi ne kai?,girman nan fa yana tahowa na gaya maka gaskiya,don ko a yanzu haka habarka ta fara gemu,toni kuma saina zauna a haka a rainani?,ko kai rannan ina ganinka kanata matse matse?,waye yayi wankan asuba shekaran jiya?" Ya qarasa fada qasa qasa saboda kar a jiyosu.
Kafin sadiq ya ankara lamin ya kwada masa wani comb da yake taje sumarshi,a baki yaso ya sameshi Allah ya taqaita masa ya goce ya samu kafadarsa,sai yayi qofa yana sheqa dariya
"Kaga kenan gwara ni,kiran girman kawai nake,kai kuwa ya fara samunka,idan ka gama shiryawa ina jiranka a wajen inna" saboda wajen sana'arsu zasu wuce,don suna hutu ne saboda sun kammala rubuta jarabawar qualifying,suna jiran wucewarsu S S3,bugu da qari ma kuma weekend ne.
Yana shiryawa maganar sadiq na dawo masa,a ranar ya faki idanun sadiq yayi wankansa ne baisan yana ganinsa ba,bayason sadiq din ya sani,saboda yana kunyar abinda zaice masa,duk da cewa daga shi har sadiq din ba jahilai bane,tun kafin zuwan wannan lokacin malam ya musu bayanin xuwan nasa,saidai shi abun naso yazo masa da wani yanayi na daban,yana jin cewa halittarsa ta dabance,don kusan bai taba ganin ko ji daga sadiq din ya shiga yanayi irin nasa ba.
A nutse ya shirya,kamar ko yaushe tsaf dashi,cikin wani yadi mai sanda sanda me sauqin kudi,yayi kyau,dai dai da matashi mai qananun shekaru.
A tsakar gida ya samu inna da sadiq din,ya miqe suna yiwa inna sallama,ta rakasu da kyakkyawar addu'a da kuma fatan alkhairi,ta bisu da kallo tana jin alfahari da 'ya'yan nata,wanda tsakanin sadiq din da lamin bata banbace wanda tafiso a cikinsu,tun bayan shigowar lamin din rayuwar gidan.
Tun qarfe uku ya katse dukkan ayyukansa bayan ya dauki uzuri waje ogansu ya koma daukar iman din.
Baifi jiran minti talatin yayi ba daliban daga makarantu daban daban suka fara fitowa,yana tsaye harde da hannayensa ya hangota,ya zuba mata idanu yana murmushi ganin yadda take waige waige,ya tabbatar da cewa shi take nema,yadan sake sakayewa kadan don ya gani ko zata iya ganoshi,saidai batayi wani nisan zango ba golden eyes dinta ya hango mata shi,saita taho da dan gudunta ma gauraye da quruciya tana dariya,tana zuwa ta daneshi.
A hankali yasa hannunsa yana zareta daga jikinsa,ita kuma tana sake maqaleshi tare da fadin
"Ya lamin mun gama...."
"Imaannn" ya ambaci sunanta yana dan dagewa kadan
"Sakeni mana" turus tayi bayan ta sakeshi tana kallonsa,baki a tabe alamun shagwaba
"Yaya me nayi maka?"ganin yadda fuskarta ta nuna rashin jin dadinta saiya duqa a gabanta yana duban golden eyes dinta
"Iman.....daga yau kin girma fa,kin zama babba,ko baki gani bane?,kin zana jarabawar fita daga primary,zaki tafi secondary,duk wanda yaje secondry kuwa ya girma.....wadda ta girma kuma ba'ason tana taba maza kinji?" Saita tura baki gaba
"Ni bana kula kowa Allah ya lamin,ko mazan ajimu ma Allah,kaine kawai,kuma kai ba yaya na bane?" Kansa ya gyada yana sake fidda murmushi
"Yayanki ne,amma ko nidinma daga yau na hana kinji?saboda kin zama big girl" Kanta ta gyada,saidai da alama har cikin ranta bata gamsu ba,yana ankare da ita yadda tayi kicin kicin da rai,duk yadda yake janta da hira kan yadda taji jarabawar taqi sake masa ta bashi labari,bai gaji ba yaci gaba da janta da hirar har suka iso bakin titi don su tari abun hawa.
Dalibai ne birjik da masu daukarsu,daga gefansa wata 'yar matashiya ce riqe da hannun wata daliba,da alama qanwarta ce,tunda ya shiga wajen dauko iman ya lura da yadda taketa satar kalloshi,dauke kai yayi yanzun ma kamar dazu,ya sanya hannunsa cikin aljihunsa ya fito da baqin glass dinsa da yakan sanya lokaci lokaci.
Sanyawar da yayi saita sake haska kyanshi cikin farar fatarsa,ya miqa hannu yana tsayar musu da adaidaita sahu,gaba kadan dasu ta tsaya,ya taka ya tsaya yana masa bayani inda zai kaisu.
Yana shirin shiga yarinyar ta qaraso tana fadin inda zata itama
"Shiga muje" mai adaidaitan ya fada mata jin hanya daya ce,abinda yasa fasa sanya qafafunsa,ya kuma dauke kwandon iman da ya zura a motar yaja baya yana cewa
"Kuje kawai" binsa ta danyi da kallo
"Dukkanmu qannenmu muka dauko,kowa gida kuma yakeson zuwa,kuma tunda yace muje ai hanya dayace ko?" Ta fada tana dan fara'a,kai ya gyada
"Ga wasu 'yan uwanki can daga gaba,idan hanya daya zaku shikena sai ya cike dasu" yanayin fuskarta ya nuna bataso ba,amma haka ta saka qanwartata itama ta shiga.
"Yaya sun tafi fa,dama shiga kawai mukayi" sosai ya kalleta sannan ya amsa mata
"Babu kyau hada maza da mata guri daya,nima bazanji dadi ba idan kika shiga keda wani" tadai jishi ne,amma bata fahimta abinda yake nufi ba.
Basu dade ba suka sake samun wani abun hawan,a hanya ya siya mata tarkacen alawoyi,abinda ya sanyata sakewa kenan,ta dinga bashi labarin jarrabawar,da kuma yadda ta amsa kowacce tambaya,don kusan duk abinda ya karanta mata shi taga ya fito.
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 🔥🔥 *KUFAN WUTA*🔥🔥🔥
NA
*HUGUMA*
*ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥
*LAST FREE PAGE*
*_GA WADDA KE BUQATAN BIYAN KUDINTA,ZATA IYA TUNTUBARMU TA WANNAN NUMBERS DIN_*
09032345899
KO
09166221261
Tun bayan zana jarabawarta ya soma mata tanadin tafiya zuwa makarantar gaba ba tare da kowa ya sani ba,ya siya duk abubuwan da yasan zata iya buqata da kadan da kadan,zuwa lokacin ya fara canza yanayin kusancinsu,sabida girma daya fara zuwan mata,a sannan ta shiga shekara ta goma sha uku,duk wasu abubuwa daya kamata ace ta sani yana koyar da ita cikin dabara da kuma hirarsu,abubuwan da ya kamata diya ta sani a shekarun fara girmanta,bugu da qari innarta itama ba baya bace,sau da dama idan ya gaya mata wani abun takan ce inna ta gaya mata,saidai bata fiya daukarsa serious ba kamar idan shine ya gaya matan,tafi maida hankali idan shine ya fada mata da kansa.
Cikin sa'a jarabawarsun ta fito,taci wata government school da basu da nisa da ita,ba bata lokaci malam ya fara mata shiryen shiryen komai,saidai ya tadda amin yaci rabin aikin,shuru malam yayi cikin mamaki tare da qara qaunar amin din har cikin jininsa,irin kulawa da iman ke samu a wajensa ko dan uwanta da suke ciki daya sadiq bata sameta ba.
Bashi da abinda zaice masa banda godiya,godiyar da take saka amin din jin nauyi da kunya,saboda shikam har yanzu a nasa ganin bai sakawa su malam din da komai ba,don har kwanan gobe arziqinsu yakeci,sun sanyashi cikin iyalinsu,yana kwana ya tashi muhalli daya dasu,kuma har kwanan gobe malam din bai daina ciyar dashi da dauke masa wasu buqatu irin na uba da dansa ba.
Duk da haka malam din ya kwakkwafeshi kan ya dinga adani da tanadi,ya daina qarar da duka nemansa akan iman din kadai,ya shaida masa yana taru,bai nutsu ba sai daya samu tabbacin hakan daga bakin sadiqu.
Bangaren inna ma saidai addu'a da fatan Allah ya jiqan mahaifansa,amin din hannun kyauta gareshi,abun duniya bai rufe masa idanu ba sam,kulli yaumin baya taba shigowa hannunsa rabbana cikin gidan,wannan dabi'a tasa har sadiqu ya koyeta,hakan kuma bai sanya ya manta da yayarsa dake garinsu ba wadda tasha dawainiya dashi ba,duk sanda zaije ganinta yakan riqe wani abu me kauri yakai mata.
Cikin nasara iman ta fara zuwa makarantar,yarinya ce mai hazaqa da kaifin basira,gefe daya kuma ga alamin,ya soke hirar dare saidai karatu,idan sun gama karatun ayi hirar kafin inna ta korata ta kwanta,cikin qanqanin lokaci tayi suna cikin makarantar.
Sannu a hankali rayuwa keci gaba da tafiya musu cikin nasara,iman ta gama js 1 ta tafi js 2,har ta tafi zuwa js 3,a sannan tuni yammatanci ya fara zuwar mata,duk wani baiwa da surar kyau na 'ya mace ya fara bayyana a jikinta,wani irin sassanyan kyau wanda hatta da inna ya sanya take sake saka hankalinta da kulawarta akan diyartata,don ko ita duk da tashen kyau da tayi zamanin quruciya bata kai iman din ba,inda Allah ya taimaketa iman din nada wani irin nutsuwa da kuma kamun kai,bata da hargagi ko hayaniya,ko rawar kan yaran da suke tashen girma.
Ta bangaren alamin ma ya sanya kulawarsa sosai akan iman din,bama shi ba harda sadiqun da suke ganin kamar bai damu da al'amuranta a baya ba,saboda lokacine na sabbabin qawaye,kuma lokacine da qananun samari da suma suke tashen girma suke iya shiga rayuwar yarinya,su sauya ta tare da koya mata dabi'u kala daban daban.
A sannan Allah ya fara sanyawa nemansa albarka,don cikin shagon nasu da suke dinki a yanzu haka shima ya mallaki keke nasa ma qashin kansa,idan bashi da makaranta zama yake ya wuni yana dinkinsa,idan kuma yana da lectures sai ya bada haya wani ya hau,da kudin dinkinsa yake sponsoring karatunsa da komai na rayuwarsa,ya taimaki yayarsa da a yanxu babu abinda zatace dashi sai hamdala,hakanan daga inna har malam gajiyar alamin din sukeci sai godiya.
Yana da tsari da kuma bin komai a sannu,bai dauki rayuwarsa da zafi ba,bai kuma dauki kansa a wani ba,komai nashi moderate yake yinsa tsaka tsaki,babu qarya a ciki,baya kallon wai collage yake,dole sai yayi abinda wane da wane sukeyi,idan ka ganshi baka isa ka aibatashi ba ko kai waye,yana da tsafta da sutura ta zamani bakin gwargwado,saidai duk abinda yasan zai zame masa wahala baya kawoshi cikin rayuwarsa,hatta da wayar hannunsa mai matsakaicin kudi ce,bai damu da sai ya riqe babba ba,tunda wannan din zatayi masa komai da babbar zatayi masa,yakanyi tunanin gwara ya sanya kudin cikin sana'ar dinkinsa,don a yanzu wani keken yakeso ya sake siya banda wanda yake dashi.
Dukkan wani rufin asiri da kuma kyautatuwar rayuwa ya sameshi,iya shi da sadiqu a qananun shekarunsu sun tsayawa gidan,sun saukewa malam abubuwa da yawa su sukeyi,don hatta da harkar karatunsu,kama daga kudin registration da sauransu su sukewa kansu da kansu.
**********Kamar yadda al'adar gidan ranar kowacce juma'a tuwon shinkafa akeyi miyar taushe,wannan juma'ar ma hakan take,gefin magariba IMAN ta gama komai,ta kuma killace gidan kamar yadda ta koya daga mahaifiyarta,saboda a yanzun da shekarunta suke goma sha biyar,dukkan wani aiki da ada yake wuyan innar yanzu ya dawo wuyanta,ta horu da wannan tun tana da shekara goma a duniya,don haka sam komai baya bata wuya a yanzu.
Tsaye take gaban dogon madubin dake jingine,wanda ya kusa rabin qofar dakinta,gefe da gefansa sama da kuma qasansa an zagayeshi da katako mai kauri saboda ya bashi kariya,tare da samun damar tsaiwa sosai a muhallin da aka ajjiyeshi.
Daure take da zanin data fito daga wanka dashi,sai tasa hannu ta zare dan qaramin hijabin da take xurawa duk sanda zata shiga wankan,take jiqaqqe gashinta daya kwanta har gadon bayanta ya bayyana,yasha ruwa sosai,saboda wankan tsarki da tayi na al'ada data gama.
Sai data sanya qaramin towel ta sake goge gashin nata sarai,tadan fifitashi kadan yasha iska,sannan ta shafeshi da mai,ta kuma sanya cumb ta tajeshi,take ya dauki sheqi,cikarsa kuma ta bayyana,taja kujera ya qarama da takan zauna akai idan zatayi kwalliya,ta fara mulke jikinta da mayukanta da take amfani dasu.
A nutse ta gama shafa manta,ta shafe fuskarta da powder,tana yi tana duba dan qaramin agogon dake manne a saman mudubin nata,wanda lamin ya siya mata,saboda tashi tafiya makaranta.
Gaban akwatinta dake shaqe da kaya ta zauna tana duba kayan da zata sanya din,batason ta saka wadanda zasu dameta,saboda zafi da akeyi,uwa uba ma kuma ba jimawa zasuyi a jikinta ba zata cire ta saka na kwanciya barci.
Garin daga kayan idanunta suka sauka kan wasu kaya baqaqe masu adon farin zare,da sauri ta sanya hannu ta daukosu tana waresu,sai yanzu ta tuna dasu,kayan da inna rabi ta bata(yar uwar innarta),kaya ne na buzaye masu kama da saqin fulani,saidai shi plain zani ne da kuma riga mai kama da buba,wadda iyakarta cinya,kala biyu ne kayan,akwai jajayensa,dukansu ta ajjiyesu da zummar zata saka kuma bata saka din ba,sai yanzu data binkito wajen ta gansu.
Miqewa tayi ta fara gwada rigar,ta isa gaban madubi,tar kamanninta suka fito,baqaqe kayan sun kwanta saman farar fatarta sun qara mata wani irin kyau,sun kuma tafi da qirar jikinta,duk kuwa da cewa a sake suke,sai ta dan soma jujjuyawa kadan tana sin ta sake ganin yadda suka amsheta,tana qiyasta ranar da zata sakasu.
Qwalla mata kiran da inna tayi ya dakatar da ita daga abinda takeyin,tana daga dakin ta amsa tana duba agogi,tasan ba shakka ta gota lokacin da take kaiwa su ya saddiqu abinci,don haka ta rarumi zanin kawai ta daura,ta yafa dankwalin kayan saman kanta.
Innar bata tsakar gidan,tabbacin cewa daga rumfarta take mata wannan kiran,bata kai ga shiga rumfar innar ba ta jiyo muryarta tana fadin
"Ki dauki abincinsu aminu ki miqa dakinsu,ashe tun yammaci ya dawo bashi da lafiya,bai qaraso ciki ba ya shige dakinsu ya kwanta abinsa,sai yanzu da abubakar ya shigo yake gayamin" har cikin ranta taji wani rashin dadi jin cewa baijin dadi,bai kuma gayawa kowa ba,bayan ita idan bata da lafiya bai barinta tayi jinya ita kadai,tun daga zamanin quruciya har yanzu data fara sanin ciwon kanta,sai ta amsawa innar da to,ta juya da sauri zuwa kitchen,ya debi kayan abincin data riga ta shirya musu,wanda dama ba kasafai take kai musu ba,sunfi shigowa su dauka da kansu,ta nufi soron tana takawa a hankali,cikin ranta tana fatan samun jikin nasa da sauqi.
Tana dab da bakin qofar dakin nasu sadiq ya daga labulen ya fito
"Ki zubamin a plate ya dan sha iska,yanzu zan dawo" ya fada yana sanya takalminsa,ta amsa da to kana tayi sallama ta saka kanta zuwa cikin dakin.
Babu kowa a dakin,sai motsin ruwa daga toilet din nasu,ko ina fes yake,sai qamshin tsintsiyar turare da kuma turarukan da suke amfani dasu daya gauraye dakin,tanason dakin tun ainihi,saboda yafi kowanne daki dake gidan sanyi da kuma dadin zama,a zamanin quruciya,tasha shiga dakin ayita nemanta,har bacci yayi awon gaba da ita.
Table din da tasan suna ajjiye karikicen kayan abincinsu ta qarasa kai ta dora a nutse,sannan ta bude fa fara zuba lafiyayyen tuwon farar shinkada,da miyar taushe wadda aka sakawa tantaqwashi,cikin mintuna qalilan qamshi ya bade dakin.
Plate biyu ta zuba harda lamin din,saita koma saman doguwar kujerar dake dakin ta zauna,tana dakon ya fito tayi masa sannu,duk ranta babu dadi sosai,dama kusan sati guda suna sabani dashi,basa haduwa sam,inna ta gaya masa yana wasu dinkunan biki ne,shi yasa yake fita da wuri ya kuma dade bai dawo ba,ga kuma makaranta.
Tana tausayin yadda yake nema tuquru,ya dauki sana'arsa da muhimmanci,fiye da yayanta sadiq,don shi wasu lokutan yakan zauna a gida yace bazai fita ba,musamman idan lectures suka hade masa ranar yasha wuya,amma bata taba ganin lamin din yana hutu ba,idan tayi magana sai ya saki murmushin dake qarawa idanunsa lumshewa yace
"Babu wani hutu a nan duniya,namiji kuma da struggling aka sanshi".
Yana da dabi'ar jimawa yana wanka,don haka sai ta tura hannunta cikin gashin kanta tana dan warashi saboda ya sake samun iska,a hankali har dankwalinta ya zame daga kanta,saita kamo gashin ta rabashi biyu ta fara kitsa kalba wai ko zaifi saurin shan iskan.
Sai da ya sanya hannu ya sake sharce gashinsa da kyau,sannan ya kama murfin qofar bandakin ya murdata ya bude a hankali cikin rashin qwarin jiki.
A hankali idanunsa suka fara sauka a kanta,tayi nisa da kitsa jelar kalbar,kayan jikinta sun haskata ainun,har suna canza mata yanayi zuwa ainihin bafulatanar niger kuma shuwa zam.
Bin jelar da take kitsawar yayi da kallo,zuciyarsa ta wani buga,sai ya lumshe idanunsa kana ya budesu duka lokaci daya,maimakon dauke idanunsa da yayi niyyar yi daga kanta,haka sai ya gagara,ya maida idanun nasa yana ci gaba da kallonta
"Anya ko zaka iya ci gaba?,zaka iya daurewa?,zaka iya cika alqawarin daka daukarwa kanka?" Jerin gwanon tambayoyin da ya jefawa kansa kenan,sai ya sake lumshe lumsassun idanuwansa da zazzabi ya sake sanyawa suka rusuna suka kuma janye,ya budesu lokaci guda yana qoqarin hadiye wani abu,kana yayi qoqarin jan qofar bandakin ya rufe,lokaci guda kuma yana takowa zuwa cikin dakin,yana qoqarin daure fuskarsa.
Motsin nasa yaja hankalin iman,bata damu da rashin walwalar dake fuskarsa ba,saboda tasan cewa bashi da lafiya,qila shine abinda ya kawo qarancin walwalar.
"Sannu ya amin" ta fada cikin nuna tsantsar kulawa
"Yauwa" ya amsa mata a dan dake,saita sake zubawa fuskarsa idanu,yau kadai sai take ga ya canza mata,wani girma da kwarjini da tsahon rayuwarsu tare bata taba gani saman fuskarsa ba a yau take gani,kodon yaune ta fara yi masa kallon qurilla?,ko don yaune kadai ranar da zata iya tunawa ya hade mata rai haka?
"Ina dankwalinki?,me yasa zaki bude kanki gaban abincinmu?,ko so kike ki haramta mana ci?" Yayi maganar still a dake,hannunta ta sanya ta baya ta janyo dankwalinta ta lulluba saman kanta,tun daga sanda ya horar da ita zama da dankwali,mawuyacine ka sameta babu shi,maimakon ya zauna sai ya nufi inda kayan shafarsa suke,ya janyo turaren da yake mulke singalalin hannayensa dasu ya fara shafawar,wannan dalilin yasa komai nashi qamshi yake,komai nasa kana iya ganeshi saboda qamshinsa na daban da yake yawan amfani dashi,abu guda daya cikin rayuwarsa da bai daukeshi da sauqi ba,yana kuma iya sanya ko nawa ne ya siyeshi wato TURARE.
Bayan ya gama ya dauki na jikin ya fara fesawa,cikin lokaci qanqani sassanyan qamshinsa ya budade dakin,iman dake zaune ta lumshe idanunta tana zuqar qamshin har cikin zuciyarta,tana mutuwa da mayatar son wannan qamshin tun ba yau ba,tayi tayi ya siya mata ko ya san mata nashi amma ya gaya mata turaren maza ne,mata kuma basa sanya turare maza,dole ta haqura,take amfani da wanda ya zaba mata,har kawo yau.
Bata ankara ba taga ya iso gaban flask din,ya bude flask din data zuba dan farfesun busashen kifi datayi musu da sauran kifin da malam ya siyo musu tun shekaran jiya waccar,basu iya cinyeshi ba saboda basu da yawa a gidan
"Ka kawo na zuba maka ya amin" ta fada tana kai hannunta da sauri kan kwanukan,saidai cikin rashin sa'a sai hannayensu suka hadu waje guda,saboda ya kawo nasa hannun ne shima don ya zuba,itama takai nata.
Da sauri ya janye nashi hannun,zuciyarsa na wani irin lugude cikin qirjinsa,karon farko itama a rayuwarta data ji wani shock har cikin jijiyoyinta,shuru ya ratsa na second guda,kafin ta rigashi sake maida hannunta tana yunqurin zuba masa,tare dayi masa sannu da jiki,ranta da zuciyarta yana bata cewa yau miskilanci ne ya hadu da ciwo hala,abinda ta jima bata gani ba tattare dashi.
Idanunya ya sauka kan jelar kalbar datayi guda daya,wadda keya reto gefan kunnenta saboda tsahonta
"Da sauqi alhmdlh" ya amsa yana janye idanunsa,tare da lalubar kansa,wai yau din me yake damunsa ne?,kamar yau ne ya fara ganin iman din.
Sosai yayi qoqarin hana idanunsa sake maida idanunsa kanta,saboda ya tabbatar a yau din akwai wani sabon al'amari dake shigarsa wanda baisan dashi ba
"Shikenan yaya?" Ta fada tana sake nannade jelar kalbar cikin yatsanta guda daya tana kuma kallonshi
"Eh" ya amsa mata a taqaice
"Allah ya qara lpy" ta fada tana juyawa zuwa hanyar fita,don ta karanci da gaske yau 'yan miskilancin ne a kusa,ta kuma fi kowa sanin halinsa idan suka motsa masa,idan ya sauko da kansa zai nemi inda take,ita kuma tayita qorafi kenan a sannan,saidai yayi murmushi kawai yace baisan sanda shi hakan ta faru ba.
Baisan ita yabi da kallo ba sai da ta fita a dakin,idanunsa suka sauka kan labulen dake lilawa,saiya dauke idanunsa da sauri,ya zamo daga gefan katifarsu ya sauka qasa sosai yaja abincin gabansa,yanata qoqarin ganin yaci,saidai duk da hakan tunani ne fal ransa.
Yana tuna maganar da sukayi da malam tun yana ajin farko a collage,malam din ya masa kyautar da har duniya ta nade bazai taba mantawa dashi ba,ya shaida masa ya bashi iman din halak malak,ya bashi ita a matsayin matar aure.
Sosai alamin yaji girma da nauyin kyautar malam din,bazaice baya son iman ba,kamar yadda bazaice yanajin soyayyarta a ransa ba,soyayya irin ta aure ba,yana mata soyayya irin ta 'yan uwantaka,saidai shi kansa yasan cewa matsayi ya bata a zuciyarsa bana wasa ba,matsayin da take dashi a wajensa ba na nan kusa bane,saidai koma mene a sannan yana ganin tayi matuqar qanqanta ya tunkareta da maganar soyayya,tunda yaci mata buri da kuma tanadi nayin zuzzurfan karatu,ya karba hannu bibbiyu kuma ya samu zuciyarsa tayi na'am da hakan,saidai ya barma ransa akwai ajiyayyen lokaci da zai fara tunkarar iman din da dasa mata soyayyarsa ta hanyar data dace,ta hanyar da bata kaucewa shari'a tsari da kuma al'ada ba,saboda haka ya nemi alfarmar malam din bayan ya gabatar masa da qudurinsa,ya shaida masa babu komai,shidai fatansa Allah ya sake hada kansu,sai gashi a yau rana tsaka ya soma jin wani baqon lamari game da iman din,tun lokaci bai kai masa Target din da yayi ba.
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM_*
*_DUK WADDA TASA HANNUNTA TAYI MAN SHARING LITTAFI NA ZUWA WANI WAJE ALLAH YA BIMIN HAKKINA DON ISARSA DA BUWAYARSA_*🤲🏽🤲🏽🤲🏽🤲🏽
*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,ZAKI IYA TUNTUBARMU TA WANNAN NUMBERS DIN*
09032345899
Ko kuma
09166221261
06
Daki ta wuce kai tsaye don cire kayan,tana tafe tana hangen fuskarsa cikin idanuwanta,bata taba ganin wanda miskilanci yakewa kyau ba irinsa ba,ba tun yau ba,tun shekarunta basu kai haka ba tasan da wannan.
Sake shanshana hannunta tayi karo na barkatai tana sheqar qamshinsa data dauko wajen saurin bude masa Flask din abincin,saita saki ajiyar zuciya,haka kawai yau din take jin zuwan nata dakinsu wani iri,cikin kasala ta qarasa cire kayan,sai ta zumbula doguwar rigarta kawai,ta dauki littafanta ta tafi dakin inna,saboda yau ta tabbatar babu zancan karatu,tunda amin din baya jin dadi.
Sanda ta shiga dakin innar ta fita dubo amin din nata,babu jimawa ta dawo,tana ta mitar yadda ya dawo ya shiga daki ya kwanta da ciwo a jikinsa bai gayawa kowa ba,motsi kadan sai tambayo sadiqu jikin nasa,bata samu sukuni ba sai data tabbatar da sauqin.
Wani abu daya tsayawa iman din a rai,yadda ta dinga juyi wajen bacci tana hango fuskar ya amin din,sai zuciyarta ta dinga raya mata kodai laifi tayi masa,qamshinsa daya nacewa hannunta ya dinga shiga hancinta,a ranar ta jima tana juyi kafin ta samu bacci yayi awon gaba da ita.
Washegari abokansu na unguwa da wajen aiki daidaiku suka dinga zuwa dubashi,abinda zai baka tabbacin yana da kyakkyawar mu'amala da jama'a,dole inna tasa bayan ya dawo daga makaranta,da zata dora sanwar dare ta qara mudu,ta kammale komai kafin magariba kamar yadda ta saba,ta shiga bandaki tayi wanka saboda zafin da ake dan tabawa,sannan ta shirya ta dawo falo wajen inna sukayi sallar magariba.
Tana saman abun salla tana dakon baqin da suka shiga dakinsu ya sadiq din su fita ta shiga ta dubashi,don da safe da zata wuce makaranta ta samu yana barci,data dawo tanata aiki ga kuma 'yan dubiya,abinda yasa wunin yau gaba daya bata ganshi ba kenan,duk sai takejin babu dadi,take kuma ji wani iri,kamar akwai nisa distance dake shirin shiga tsakaninsu kenan,ta lura tun daga sanda ta shiga js2 yayi bala'in sauyawa,ko wasa da dariya da zaman hira da suke ada yanzu babu kaso casa'in cikin dari,saidai kulawar da yake bata babu abinda ya sauya
"Naji hayaniyar ta ragu,ki leqa kikai musu abincin,nasan halin amin,indai yana ciwo bason abinci yake ba" tsam ta miqe tana gyara yafen mayafinta data yi sallah dashi,sannan ta nufi kitchen ta debi abincin tayi soro.
Da sallama ta cusa kai soron,wata baqauwar murya ce ta amsa mata,matasa ne guda biyu da zasuyi shekaru kusan daya dasu sadiq,daya na zaune saman daddumar da aka shimfida masa saman ledar dakin,dayan kuma na zaune gefan katifar sadiq.
Dan daburcewa tayi kadan saboda yadda taga sun zuba mata ido,sam bata saba cudanya da maza ba,uwa uba kuma ta zaci lamin da sadiq ne kawai a cikin dakin,saita taras da akasin haka
"Yana bandaki,yanzu zai fito" daya daga cikin samarin ya fada ganin yadda tayi turus,saita duqa a hankali ta ajjiye kwanukan,tana samun waje gefe daya ta tsugunna don jiranshi ya fito bayan ta gaidasu.
Shuru yadan ratsa a tsakani,daya daga cikin samarin da tun dazu yake satar kallonta ya fara janta da hira,da qyar take amsa masa tambayoyin da yake mata,qasan ranta haushinsa na kamata,don me zai dameta da wata hira,bayan ita ba itace ta kawota ba?.
Minti kusan takwas sannan ya bude toilet din ya fito,jikinsa da lema sosai,har jallabiyar daya sanya tana mannewa a jikinsa.
Da ita ya fara hada idanu,kowannensu ya janye idanunsa daga na dan uwansa,wani nauyi yau daya taji idanun nasa sunyi mata,rashin fara'arsa ta kwanakin nan gaba ta sauyashi,ta sanya tana jinsa kamar wani baqo a wajenta.
"Ya amin....barka da dare,ya jikin naka?" Sai daya gyada kai yana hadiye wani abu daya tsaya masa na haushi da takaicin junaid,saboda ya lura da irin kallon da yake binta dashi
"Da sauqi alhmdlh..... I hope kinje makaranta?" Yayi mata tambayar dai dai sanda sadiqu ke shigowa da lemukan fanta masu sanyi a hannunsa,sai maltina ta gwangwani guda biyu,dama abinda yaje siyo musu kenan,da zummar idan ya dawo yaje ya dauko musu abincin
"Naje yaya"
"Ma sha Allahu,qanwar saddiq ce da alama?" Junaid ya tambaya idanunsa a kanta yana washe baki,bata amsa ba saiya gyada kai,ta maida idanunta tana kallon yadin mayafin dake jikinta kamar ba bata ba
"Tubarakallah......kina aji nawa yanzu?"
"Js 3"
"Kune 'yan placement na bana ko?" Sai ta sake gyada masa kai kawai,don ta ankara da yadda ya lamin din yayi dif kamar baya dakin,hasalima man shafawarshi yake budewa zai shafa,saidai fuskarshi a dinke take tsaf
"Muje ki lalubi cokula ki bani" sadiq yayi saurin fada sanda junaid ke qoqarin jefa mata tambayar,abinda ya sanyata miqewa sadiq yabi bayanta,duk da hakan sai da junaid din yace
"Kaje ka dawo muyi magan.....ko mu fara da amin kafin ka iso" ya fada yana dariya dariya,daya dan saurayin yana tayashi,suna dan duban amin da suke zaton zai tanka,saidai baice dasu komai ba,hakanan yanayin fuskarsa na nan a dinke,abinda yasa ya musu kwarjini ya kasa maganar dashi,don dama tuni sun dade da sanin halinsu,tun suna 'yan qasa da shekara sha takwas,lamin din ba kowanne yayin magana da shirmen magana yake tankawa ba.
Har sadiq ya dawo da spoon din ya zuba abincin suka fara ci yanayinsa bai koma dai dai ba,yanajin sanda junaid din ke neman izini daga wajenshi ko sadiq din ya gana da iman,domin yace shikam ta gama yi masa,yadda yaketa kodata da yabata yasa wani abu yayi masa tsaiwar mashi a wuya,ya dinga jin kamar ya kai masa naushi a fuska,abinda ya sanyashi miqewa ya fice zuwa qofar gidansu ya zauna saman dakali.
Fayau yau qofar gidan yake,saboda kusan dukkan almajiran malam sun tafi ganin gida,sau biyu dama yake barinsu suje duk shekara ganin gida,su kuma dawo lokaci daya sanda ya sanya musu.
Iskar zafi na kadawa sosai ta wajen,sai ya jingina bayansa da ginin qofar gidan,ya lumshe idanunsa yana sakin ajiyar zuciya,saman harshensa yana jin wani daci daya tabbatar bayan na rashin lafiyar da yayi,harda mugun kishin iman din daya tsinci kansa a ciki.
Baisan ya akayi haka ba,daga jiya zuwa yau gaba daya iman din ta birkita zuciyarsa,sonta ya taso masa da wani irin qarfi da a baya bai taba jin makamancinsa ba,daga jiya zuwa yau kuma da abokansu wajen mutum hudu ke taya iman din sai yaji ya kasa sukuni,shigowarta na qarshe da daddare kawo musu abinci ya sanya yayi mata kallon qurillar daya tabbatar da cewa eh tabbas ta girma ta kuma fara zama budurwa.
Bai dauka cewa girma zai zowa iman din haka gadan gadan ba,duba da yanayin jikin fulani da take dashi,to ashe duk ganinta da yake cikim hijabi yasa yake wannan hasashen,girma da murjewa take ta ciki ba tare da an ankara ba,har ga Allah bazai iya fadan yadda ya dauki bashi itan da malam yayi da matuqar qima da daraja ba,saboda kima da mutuncinsu da yake gani,to amma ya sakawa ransa cewa bazai tunkari iman din da wata magana ta soyayya ba a yanzu,zaici gaba da bata kulawa ne kamar yadda suka saba a baya,har sai ta shiga ajin qarshe ko na kusa da qarshe na kammala secondary dinta.
Tun ba'ayi nisa ba ya gane akwai gyaran daya kamata yayiwa tarayyarsu,kamar yadda suke kusa da juna koda yaushe din nan ya kamata ya janye,ta dinga kallonsa a matsayin yaya da gaske,don tun farkon girmansa ya fuskanci cewa yana da wata dabi'a a halittarsa a matsayinsa na da namiji na yawan sha'awa,inda Allah ya taimakeshi me yawan kamewa ne shi,banda hakan......yadda 'yammata ke mutuwar sonsa.....iya cikin matan dake kawo musu dinki kawai,banda na 'yan ajinsu a makaranta,gefe guda kuma ga 'yan unguwa da sauransu,wannan ya sanya ya sake janyewa iman din,abinda yaketa bata mamaki kenan da taraddadin shin me tayi masa ne?,duk da cewa qasan ransa shima baijin dadin hakan,saidai hakan shine dai dai,kuma zai sanya nutsuwa a zukatan malam da inna,koda basu nuna masa hakan saman fuskarsa ba.
Tsakiyar tunaninsa yaji hayaniyarsu junaid suna fitowa,suka masa sallama ya amsa musu sama sama,ya bisu da kallo sanda sadiq ke taka musu zuwa bakin titi sunata hayaniyarsu irin ta samari,sai ya bisu da kallo har suka dan kaucewa ganinsa.
Ba jimawa yaga dawowar sadiq din,ya qaraso inda yake zaune ya dafa kafadarsa
"Tashi mu koma ciki,wajen na akwai sauro,ko gama warkewa bakayi ba kazo ka zauna ka baza masa jikinka yanata gutsira a banza" yunqurawa yayi ya miqe cikin qarfin hali yabi bayan sadiq din zuwa cikin dakin nasu.
Sunwa wajen kaca kaca kamar yadda akasan yanayin cin abincin maza samari yake,yana jin sadiq din ya buda murya ya fara kwadawa iman din kira,yasan kuma cewa zaiyi tazo ta gyara wajen ta kwashe kwanukan,sai lamin din ya dakatar dashi
"Dakata malam,kuturu ne kai da bazaka iya kai kwanuka ba?,ni idan na gama zan gyara wajen,daga yau ma banason ta sake kawo abinci indai akwai baqi a ciki,saidai idan kaine a ciki" waiwayowa yayi ya zubawa lamin din ido,ya karanci tsabar gaskiyarsa yake fada saman fuskarsa,sai ya saki murmushi ya dawo ya zauna gefan lamin din
"Duk da cewa bani na kar zomon ba....amma zan baka shawara,kada ka tsaya kallon ruwa kwado yayi maka qafa,diya mace duk yadda kake raina girmanta tasha kan tunaninka,kana mata kallon kamar tayi qanqanta da soyayya,ka gwada mata bayani kaga idan bata dauke karatun ba gaba daya,ni na rasa abinda ma kake jira,an maka kyauta an kuma baka dama amma ka tsaya wani tsari naka?,ka saka kai kawai,Allah ya bada sa'a" sadiq ya qarashe yana dukan kafadar lamin.
Yana cin abincin yana tattauna zancan shi da zuciyarsa,akwai kunya soyayya da yarinya tsakanin mahaifinta da mahaifiyarta,mutanen da yake musu kallon mahaifansa,abu daya ya yankewa ransa,zai fara bata kulawar data banbanta da irin wadda yake bata a baya,zai fara dafa zuciyarta da soyayya ba tare da ya furtata gareta ba,ta yadda da kanta zatayi dako ta kuma zaqu da ranar da zaya furta mata din,saiya saki wani murmushi wanda ya qawata fuskarsa data dan qara haske kadan sabida zazzabin da yasha.
*********Kamar kowacce rana da bata da makaranta asabar ko lahadi,yauma haka ta tashi tayi dukkan wasu aiki na gidan,kama daga shara wanke wanke da kuma dora karin safe.
Ta gama komai tas inna na daga rumfarta tana sallar walha,ta debo kayan data bata din zuwa bakin famfo nan tsakar gida,sannan ta koma kitchen tana goge duk inda ta bata din.
A nutse yake takowa zuwa cikin gidan,sanye da jallabiyyarsa da yake amfani da ita yawancin lokuta idan ba fita zaiyi ba,hannunsa riqe da ledar da mlam ya bashi ya kawo cikin gidan bayan sun gama karatun da sukeyi duk safiya da wurwuri bayan an tashi almajirai.
Kai tsaye ya isa rumfar inna da sallama,ya cire slipper dake qafarsa ya shiga.
Tana zaune saman abun sallah tana jan carbi,fuskarta ta wadata da murmushi sanda ya tsuguna a gabanta yana gaisheta,cike da kulawa ta amsa masa tana sake tambayarsa qwarin jikinsa,duk da cewa ya warware
"Alhamdulillah na warware ai inna,yau ma zan fita aiki in sha Allah"
"Ma sha Allahu,Allah ya qara lafiya"
"Ameen inna...ga wannan ledar,malam ne yace na kawo a dafa masa"
"Tana kitchen ai,saika miqa mata,kace kada ta cika masa yaji da yawa" innar ta fada bayan ta bude taga meye a ciki,ya amsa da to ya miqe tsam da ledar ya nufi kitchen din.
Ta bada hankalinta ga aikin da take sosai taga kamar inuwar mutum cikin kitchen din,abinda ya sanyata zabura kenan,ta waiwayo da sauri,har tsummar hannunta tana faduwa a qasa.
Idanu suka hada dashi,yana tsaye jingine da jikin qofar,ya zuba mata idanu yana binta da kallo,gabanta yayi wani mugun faduwa,kamar karo na farko kenan data taba ganinsa,cikin sanyin jiki ta duqa don ta dauke tsummanta tare da cewa
"Ya lamin.....ka bani tsoro" kusan a tare suka duqa din,shine ya samu nasarar dauke mata tsumman,suka dago a tare,idanunsu ya fada cikin na juna,yadan ja baya kadan saboda sunyi kusanci da yawa,ya miqa mata yana ci gaba da kallonta tare da cewa
"Dama can matsoraciyar ce" idanunta ta janye daga nasa,saboda nauyin da taji zuciyarta nayi,qamshin turaren jikinsa yana busowa zuwa cikin kitchen din,kai bakace baiyi wanka ba,tsabar abotarsa da turare ne kawai,yayi wani fresh 'yar cutar da yayi kwana biyu,sai sumar kansa dake adan hautsine saboda bai gyara ta ba,daga sallah makaranta suka zauna kawai,hakan kuma sai ya qara masa kyau.
"Yaaa banfa zata ba" ta fada da salon shagwabar data saba masa magana a baya,sautin muryarta yaji ya tabashi,ya kuma saukar masa da kasala,ya sauke boyayyar ajiyar zuciya,tare da dora ledar hannun nasa kan kantar da take gogewar
"Barka da safiya yaya,ya jikin naka?" Ta furta tana kaucewa kallonsa,saboda wani yanayi da takeji duk sa'ar data kalleshin
"Alhamdulillah,na warware.....gashi nan,malam yace adafa masa,inna tace karki cika yaji da yawa" a marairaice ta waiwayo
"Yaaya,na gama komi fa,Allah saura wanke wanke,kwanciya nakeso nayi" yadda tayi masa maganar ya sake tafiya dashi,sai ya harde hannayensa a qirji ya zuba mata idanu harta gama,duk da bashi take kallo ba,amma tanajin idanunsa a kanta
"Yanzu idan mijinki yace yanason ki dafa masa abu kamar haka hakan zaki ce?" Banbarakwai taji maganar tasa,fa waiwayo da sauri sai taga ita yake kallo,fuskarsa ta wadata da murmshi
"Inna na miki haka ne saboda tanason ki gina gidanki da kulawa,ki shagwaba mijinki da soyayyar da zatasa ki tsaya masa a zuciya" wata irin kunya ce ta rarrafo ta rufeta,saboda yanayin yadda yake mata maganar kawai ta sanya taji kamar qasa ta tsage ta shige,wannan kuwa ya lamin dinta ne?,magana yake mata da wani irin sound da bata sanshi dashi b,wani irin kallo na daban da sexy eyes dinsa,gaba daya taji kaman ya zare mata laka,sai ta juya tana ci gaba da aikin a hankali,kunya na nuqurqusarta.
Bata ankara ba har ya dauki kwanon dake kusa a ita ya juye kifin a ciki yana cewa
"Tunda raguwa ce ke bari na tayaki" tare suka dawo tsakar gidan,tana wanke wanke,shi kuma yana gyara mata kifin,gaba daya sai ta jita cikin wata takura da bata taba jin irinta ba tsakaninta da lamin din,saboda duk wani motsi ko daga kai da zatayi saita samu tagomashin wani kallo da ta kasa farrasa na meye?,saidai yana sanya zuciyarta karyewa da kuma yin laushi.
Ya sakankance sosai abinsa,yanata aikata mata da kallon da yake da tabbacin zai wuce kai tsaye zuwa cikin zuciyarta ne yayi masauki me kyau,koda bai furta komai a gareta ba,baya da fargaba saboda inna tace zata shiga tadan kwanta,malam kuwa yayi baqi a waje,wanda yasan yawanci idan sukazo sukan dauki awa biyu tare kafin su tafi,sadiq kuwa baida matsala dashi,shi ba baqonsa bane bare yaji kunyarsa.
Kusan tare suka gama komai da ita,sannan ya wuce dakinsu bayan ya sanyata ta saka masa ruwan wanka.
*HILTI UNISEX CHOCOLATE*
*_chocolate ce ta musamman daga qasar TURKEY_*
*_Maganin matsalarki hajiya keda mai gida cikin tsari babu yane yamen magunguna_*
*Ki tuntubi wannan number don k'arin bayani*
08184017452[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 07
*_ZAFAFA 5 NA MIKA GAISUWAR TA'AZIYYA ZUWA GA MARUBUCIYA UMMY AISHA, TA KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION, BISA GA RASHI NA MAHAIFIYAR TA DA TAYI. MUNA FATAN ALLAH YA JIKANTA DA RAHAMA, YA GAFARTA MATA, YA KUMA BASU HAKURIN WANNAN BABBAN RASHI AMIN._*
__________________________________
_SAKINA VENDIBLES_
_SAKINA VENDIBLES_
_SAKINA VENDIBLES_
_(INDE HARKAR TURARUKA NE MASU KAMA JIKI DA GIDAH KAI HARDA TSUGUNNO. SAKINA VENDIBLES ITACE KAN GABA)_
_SUNA DA KAYA INGANTATTU MASU MATUKAR KYAU AKAN FARASHI MAI RAHUSA.)_
_KINASON ASAN KIN ISA MACE? WADDA ZAKUYI GOGAYYA DA MASU SAKA DESIGNER TURARE AMMA KI FUSU KAMSHI? DUK INDA KIKA GIFTA ASAN EH. KEDIN TABANCE , KIN ZARCE SAURAN MATA)_
_AKWAI KHUMRAH WHITE AND BLACK_
_KULACCAM BLACK (FOR HAIR( AND WHITE FOR BODY_
_WASU DAGA CIKIN KAYAYYAKIN MU SUN KUNSHI👇_
Turaren wuta list*
Queens special
Kajiji mix
Kajiji whole
Gabgab
Brown Hawiii
Special Halut
Sandal balls
Sandal strips
Sandal flakes
Dubai oud
White Hawii
Classy Dufr
Black bange
Black bange
Musky Dorrot(Na tsuguno)
Cous cous
*_DA SAURAN SU DA YAWA_*
*_Handles_*
*Instagram* @sakina_vendibles *Facebook*
@Sakina vendible *Tiktok*
@Sakina vendibles_
Tsaye take gaban mudubin nata tana karanto addu'o'i,bayan ta gama shirinta tsaf na tafiya makaranta don zana jarabawar placement,kamar kullum,tayi kyau cikin uniform din da a kullum idan ta saka zaka dauka ta sanyashi ne da nufin gayu ko ado,saidai sam ba haka bane,qirarta ce,haka Allah ya yita,fatarta na daukar kowanne irin nau'in dressing.
Lokaci daya gabanta ya dan fadi,ta kuma lumshe idanunta sanda ta jiyo muryar ya al'amin yana tambayar inna bata fito ba,wannan wani baqon yanayine da bata jima da tsintar kanta a ciki ba,a duk sanda zataji murya ko motsin ya al'amin din.
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana wara idanunta da suka dauki mintuna a kulle sanda ta tsinci muryar inna tana kiranta,cikin yanayi na me kama da me alhini ko tsoron haduwa da ya al'amin din ta zura takalmanta half cover masu kyau,wanda al'ameen dinne ya siya mata,kamar yadda fiye da rabin komai nata da take amfani dashi na rayuwarta.
Dashi suka fara hada idanu sanda ta fito tsakar gidan,saita sauke idanunta daga kanshi da hanzari saboda yanayin kallon da ya jefeta dashi,wanda shi kansa baisan yayi ba,tayi masa kyau sosai yau din,duk da ya saba ganinta amma yau din kamar an qara mata girma da shekaru,itama cikin ranta take tadinshi,yayi wani kyau cikin shadda light blue daketa qyalli,bisa alamu sabuwa ce kar,yau ya fara sanyata,hakan kuma baya rasa nasaba da daurin auren dan abokin malam din da zashi,wanda malam dinne ya wakiltashi yaje,saboda a jiya shi ya wuce Niger,can dangin inna da akayi mata rasuwa zai musu gaisuwa.
Ko kadan bata zargi kanta kan yadda takejin sauyi da baqunta tattare da ya al'amin din ba,saboda ita kanta tana ganin kamar shima ya sauya,kallo da yanayin firarsu gaba daya ya canzata,bata saba jin nauyinsa ba idan suna hira a baya,tana hira dashi kamar yadda takeyi da ya sadiq,amma a yanzu tanajin akwai wani banbamci a tsakaninsa da ya sadiq din.
Tana qoqarin gaidashi inna ta fara mata fada
"Kinsan yana jiranki zaki shiga ki zauna....."
"Innaaa.....bansan lokaci yayi bafa....girkin nan shi ya cinyemin lokaci" ta fada a shagwabe kamar yadda ta saba,boyayyen murmushi ya kubce masa,abun ya zame mata cikin jininta,ta saba maganarta a haka,abinda ke sake daukan hankalinsa dangane da ita kenan,duk da yana qoqarin boyewa da kuma dannewa
"kaima duk da kai aminu,da tafiyarka,tasan hanya ai,ta tafi da kanta"
Baice komai ba,yadan saki sassanyan murmushin nan nasa,sannan ya matsa inda ta hada komai nata ya sanya hannu ya dauka yana fadin
"Mun wuce inna,daga wajen daurin auren shago zan wuce"
"Ba zaka dawo ka karba abin karin naka ba" sumarsa irinta buzaye daketa qyalli ya shafa da hannunsa
"Ina da ayyuka da yawa ne inna.....akwai dinkin wata amarya da nake,nace mata tazo jibi ta karba,banaso tazo ban gama ba" kai inna ta gyada,ta sanshi da matuqar qoqari wajen cika alqawari,mutum ne shi kaifi daya,mai matuqar qoqarin ganin ya cika alqawari,sam bashi daga cikin jerin layin teloli
"Haka ne,to Alla ya dafa ya tsare mana ku,sai kun dawo"
"Ameen inna" suka amsa gaba dayansu,sannan ya sanya iman a gaba suka fice.
Cikin jikinta take jin kunya nauyi da kuma wani irin yanayi,yayin da shi kuma tunaninsa yayi nisa game da yadda zai tafiyar da koma a tsakaninsu bisa tsari da tsafta,tafiyar sai tazo da sabon salo,saboda ba haka ya saba rakata zana jarrabawa ba,sau biyu tana satar kallonsa,ya ganta sarai,amma sai yayi kamar bai ganta din ba,har zuwa sanda sukayi tsaye a bakin titi suna jiran abun hawa,daga layin cikin layin da yake facing dinsu,wata mata dake sanye da uniform fari da ash,wanda hakan ke alamta ma'akaciyar jinya ce wato (nurse) take tunkaro bakin titin,dukkaninsu sun ganta,har zuwa sanda ta iso titin daga daya tsallaken ta tsaya
"Kamar haka nakeson ganinki.....ina miki sha'awar karatun jinya,ina miki sha'awar ilimi me zurfi"muryar al'ameen wadda ta fara cika da amo na mazantaka a 'yan watannin nan ta ratsa kunnen iman din.
A hankali ta daga kanta ta sanya dubanta ga matar,tun ba yau ba dama ta sani wannan shine burin al'amin din a kanta,ta dade da haddace hakan,kusan kowa a gidan ya sani,don haka sau tari idan suna irin wannan hirar ma babu me ce musu uffan,tsakaninsu ne
"Kiyimin alqawarin zaki cikan wannan burin" cikin mamamki kalamansa ta daga idanu kamar zata klalleshi amma kuma ta kasa,saboda tuna yadda take ji,da kuma yadda idanuwansa ke mata nauyi yanzun a jiki da zuciya
"Bake da kula kowanne irin saurayi,bake ba soyayya" lafazin nasa ya ratsa ta tsakiyar tunaninta ya katse mata shi shi wani sauti mai taushi kuma qasa qasa.
Wata irin kunya ce ta dirarta mata,ire iren maganganunsa kenan da suke caza mata kai,da kuma sake sanyata jin kunya da nauyinsa,maganganun da a baya baya mata su,tadan sadda kanta qasa,qaramin murmushi yana qwace mata
"Eh,wannan ce hanya daya da zaki taimaki cikar wannan buri nawa,ki bari,idan lokaci yayi,ni zan zaba miki ɗanɗasheshen miji da zai dace dake" qarasa rufeta kunyar tayi,sai ta kare fuskarta da hannunta tana cewa
"Ni ban kula kowa ya al'ameen,kuma ma waye zai kulani nima?,dubeni fa?" Murmushi ne ya qwace masa sanda ya saka hannu yana tsayar musu da wata adaidaita sahu sannan ya bata amsa
"Kina da kyau imani....ke kyakkyawa cw ta ajin qarshe ko farko zance,irin kyan dake jan hankalin kowannw namiji....wanda ke ba zaki gane hakan ba,amma a taqaice,ke sarauniya ce" wanda tun daga ranar ta samu sunan queen daga wajen al'amin,sunan da ya koma kirata dashi lokaci lokaci,musamman idan ya zamana babu malam ko inna a wajen,don ta sadiq dama ya maidashi kamar wani kakansa,ba wai kunya ko nauyinsa yakeji ba,yayin da sunan ya tsayewa iman,yake kuma matuqar yi mata dadi,zuciyarta nata mata saqe saqe akan al'amin din,me yasa ya canza?,me yasa yanzu yake tsaye mata a rai?.
Cikin guntar karatun litattafan hausa data fara a boye ya samu amsoshi da dama,saidai kuma har yau bai furta mata ina sonki iman ba,to hakan meyake nufi?.
*******. ******. ********
Tun dazun data zauna a wajen hankalinta yake rabi da rabi,daya a wajen,daya kuma ya karkata kan jinkirin shigowar al'amin gidan yau,sau biyu tana tura almajiran gidansu suna gano mata rumfar karatu ko yana wajen malam sai ace mata baya nan,tunda ta gama ayyukanta tayi alwalar magariba ta shimfida musu tabarma ita da inna a nan wajen sukayi sallah take saka ran shigowarsa,amma shuru kakeji,gashi har qarfe tara na dare na haramar yi,har sadiq ya shigo yaci abincinsa ya sake fita.
Ta gwada kiransa ta wayar inna kuma sau uku ana ce mata a kashe wayar take,har inna dake jin radio ta rage sautinta tana jajjabin rashin shigowar tasa,wanda bata sauke ba sai ga sallamarsa.
Wani boyayyar ajiyar zuciya da batasan daga inda ta taho ba iman din ta sauke,shi dinma koda ya shigo idanuwansa suna kanta,ta miqe a kunyace a kuma nutse tana gyara daurin dankwalinta tare da qoqarin yi masa sannu da zuwa tana yunqurin karbar ledojin hannunsa
"Yauwa Queen" ya furta qasa qasa yadda innar ba zata jiyo ba,saita saki murmushi tana dora kayan saman daddumar data tashi a kai,inda shi kuma ya qarasa yana zama a kai tare da yiwa inna barka da gida,ta miqe daga kwanciyar da take tana amsa masa tare da tambayarsa dadewar da yau yayi,har tana shirin tura sadiq ya dubosa.
Murmushi yayi yana jin dadin yadda har kullum inna ke nuna masa qauna da soyayya irinbya da da uwa
"Aiki ne yau ya riqeni inna,ban gama musu ba,kuma gobe zasu shigo da safe su karba,na katse ne na shiga kasuwa,shi yasa dinkin ya kaini har dare" jinjina kai inna tayi,tana sake jin qaunar al'ameen din cikin rai da zuciyarta,har kullum shi mutum ne dake sanya cika alqawari gaba da komai a rayuwarsa,ya tsani saba alqawari
"Sannu da qoqari,Allah yayi jagora"
"Ameen inna" .
Iman na daga kitchen tana qoqarin hado masa abincinsa tare da dora masa ruwan wanka take jiyo hirar tasu,ta hada komai a nutse a kuma tsaftace kamar yadda inna ta horar da ita ta fito dashi zuwa inda yake zaunen.
"Sannu da aiki autar inna" ya furta cikin kulawa,ta saki murmushi bayan ta duqa ta aje a gabansa
"Kinga bar abincin nan,zo kiga.....siyayyarki ta tafiya nasreen memorial academy" sosai maganar tayi mata ba zata,makarantar da inna ta kusa dukanta a kanta,saboda yadda ta nace ta kafe tanason makarantar,ita kuma inna ta haneta da zancanta,saboda private school ce da duk term ake biyan kusan dubu goma sha biyar,innan kuma tasan matsawar alamin din yaji tofa sai ya kaita,shi yasa ta sanyata a daki ta ja mata kunne,koda ta sanarwa malam murmushi yayi
"Bansan ko tabarar auta ke damu hajar ba,banda haka.....yaci ace wasu abubuwan zuwa yanzu tafara ragewa,yaron nan hidima da kuma bautar da yake mata ko ciki daya suka fito iyaka kenan,kinyi dai dai,taci gaba da zuwa ta gwamnatinta yadda ta saba,tunda ita takeyi tun tasowarta,kuma tana da basirar gane abubuwa,gashi lafiya lau komai ke tafiya"
Laqwas jikinta yayi sanyi sanda yake fiddo siyayyar da yayi mata yake kuma shaida mata sati me zuwa zata fara zuwa,an gama koma,idanunta suka ciko rau rau da qwalla tana satar kallon inna,tana tsoron kada tace itace ta tusashi gaba ka dole sai ya kaita,ko kuma ita ta gaya masa zabinta.
Ta bangaren innar ma jikinta sanyin yayi,wane irin yaro ne al'ameen din?,ta tabbatar yinin da yayi har dare a shago kudin wannan siyayyar ya hada ya kashewa iman din gaba daya,tabi kayan da ya zazzage din da kallo,litattafai ne tari guda, school bag,takalmi me kyau da 'yan makaranta,biruka da pencils,hatta da uniform din makarantar gashinan a dinke a goge sai sanyawa kawai.
Fada sosai inna ta rufe iman dashi,wannan karon harda al'amin din,kan me yasa zai dinga biyewa iman din da duk abinda tace tana so,ita din 'yar wace da bazata ci gaba da zuwa makarantar gwamnati ba,kamar yadda saura suke zuwa?.
Sosai yaji babu dadi saboda kukan da yaga iman din tanayi,saida inna ta soma sassauta fadan sannan ya mata magana cikin kwantar da kai,yana mata bayani zafa fahimta banbamcin karatun makarantun gwamnati da kuma da na kudi,tare da nuna mata shima yana sha'awar ya canza mata makaranta dama,bawai ita ta sakashi ba,ya dade yana wannan tanadin.
Saida inna ta tabbatar ba iman ce ta tursasashi ba sannan ta fara saukowa,saidai duk da haka bata bar mita ba
"Yanzu kai da kake da nauyin 'yar uwarka a ka,ga naka karatun,sanna kuma ka dauka duk wata lalurar iman ka rungume?" Murmushi kawai ya sake
"Ba komai inna,Allah zaiyi,mudai aci gaba da yi mana addu'a.....sannan don Allah inna karki sake cewa komai sadiq yaji" ya fada da sauri,saboda jin muryar sadiq din dake shigowa da sukayi,kuma yaga reaction na fuskar iman,yasan sadiq din dan hada waje ne,maimakon ya gyara saidai ma ya bata,saidai duk da hakan daya shigo shima sai daya tofa albarkacin bakinsa,magana dai bata mutu har shigowar malam,shine ya yayyafawa abun ruwa,ya sanya albarka a ciki,ya kuma ja kunnen iman,sannan ya kebe da al'amin din bayan kowa ya tashi ya basu waje.
"Yanzu kai malam al'ameen haka za'ayi dakai?" Cikin fargabar ko wani laifi ya yiwa malam ya daga kai ya dubeshi,malam din ya fahimci abinda ke yawo saman fuskarsa,sai ya saki murmushi
"Kai da zaka zama magidanci nan gaba,haka zaka zauna sai abinda takeso zakayi mata?,shifa namiji kullum so ake ya zama tsayayye,yana da kyau a dinga bawa mata dama kan raayi da zabinsu,amma kuma bafa akan komai ba,qarqashinka zata zauna nan gaba kadan,to dole tun yanzu ka dinga azata akan tsari da tafarkin da kakeso ta kasance akai" cikin hikima malam din ya dinga nusasheshi,daga bisani kuma suka fada hira,wanda wannan ba sabon abu bane dama tsakaninsa da malam din ba,sunawa juna kallo da da mahaifi ne.
Ya jima yana nazari kan maganganun malam,su suke ganin kamar yana biyar son ran iman dinne,wanda sam shi ba haka bane,duk abinda yakewa iman....tun kafin ya soma jinta da wani matsayi daban a cikin zuciyarsa kawo yau,yana mata ne saboda ta cancanta ta kuma dace yayi mata hakan,sau tari kuma zabu da ra'ayinsu ana samun arashi yana zuwa daya,iman din ta dabance cikin rai da rayuwarsa,duk da yana ganin abubuwa sosai tattare da ita,ita dinma kamar ta canza,amma nan gaba kadan zai qarasa bude mata komai,yana son yabi komai ne bisa tsari na hankali da dacewa,da wannan ya kwanta a ransa.
*ZAFAFA BIYAR 2022*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKANFARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA_
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 08
*_LITTAFIN KUDINE,ZAKI IYA TUNTUBAR WADAN NAN NUMBERS DIN DON SIYAN NAKI_*
09032345899
Ko kuma
09166221261
_______________________________
Misalin takwas da rabi na safiyar ranar litinin din,zaune take saman doguwae kujerar dake falon principal din nasreen memorial academy,tayi neat cikin shigar uniform din makarantar da shima ya karbeta fiye da makarantar data baro,idanunta sunyi narai narai tana kallon al'amin daya miqe yana sallama da principal din,bayan sun gama komai shi da sadiq sun damqata ga hannun hukumar makarantar,baqunta take ji sosai cikin wannan makarantar,tamkar yau ne rana ta farko data fara zuwa makaranta,al'ameen ya waiwayo a nutse ya sanya hannunsa a aljihun wandon lallausan yadin jikinsa da iya tsahon rigar ya tsaya a gwiwarsa,ya ciro 200 ya miqa mata
"Idan ba zaki iya komawa gida ba ki jirani na dawo,sai na maidake" hannu tasa tana amsa
"Zan iya yaaya" ta amsa mishi a tausashe,principal din yayi murmushi
"Wannan qanwar taka da alama kana ji da ita" ua fada cikin salon barkwanci,sai al'amin ya waiwaya ya dubeshi sannan ya saki murmushi
"Auta ce"
"Oh....i see" ya sake sakin murmushi ya musu sallama yabu bayan sadiq suka fice.
Tana zaune nan tana rarraba idanu,har principal din ya kira daya daga cikin masu goge goge dake aiki a makarantar,tayi masa kiran Assistant monitor din ss 1,ba jimawa ya dawo yace tana zuwa.
Ba'a rufa minti biyar ba tayi sallama,cikin nutsatsiyar muryarta,tana sanye da uniform irin na iman din,iman din ta bita da kallo,tana da haske saidai baikai nata ba,tana da madaidaicin kyau,a qiyasce shekarunsu zasuyi daya da ita
"Ga new student nan,ayi mata seat,sannan a shigar da sunanta cikin register"
"Okay sir" ta amsa a ladabce,sannan ta waiwaya zuwa sashenbda iman ke zaune.
Suna hada idanu ta sake mata murmushi,saita soma takawa zuwa inda take din tana dubanta,har yanzu kuma murmushin bai bar kan fuskarta ba,ta duqa ta dauki hand bag din iman din tana cewa
"Taso muje" saita miqe tana dan jan rigarta tabi bayan yarinyar.
Tare suka jera cikin yanayin baqunta,saita waiwayo ta sake sakar mata murmushi
"Sunana munira hasan......nice assistant monitor na ss 1,monitor dinmu namiji ne.....kefa,meye sunanki?"
"Hajar ibrahim khalil"
"Yadda kike da kyau haka sunanki yake da dadi" munira ta fada tana sakin murmushi gami da kallon iman.
Martanin murmushin iman din ta maida mata tana cewa
"Na gode" sukaci gaba da takawa,maganar muniran na maimituwa a ranta,sai ta sanya hannu ta shafi fuskarta a fakaice,an jima ana fadin ita me kyau ce,saidai ita bata taba ganin kyan ba a karan kanta,hakanan bata taba baiwa maganar wani muhimmanci ba.
Kai tsaye munira ta kutsa kai cikin ajin,wanda ya dauki shuru,kowa ya bada hankalinsa ga allon da malamin dake tsaye yaketa cikashi da rubutu daliban suna kwafa suna mayarwa zuwa ga litattafansu. Sallamarsu sai taja hankalin kowanne dalibi dama matashin malamin dake tsaye gaban allo,ta qarasa daura da malami tana cewa
"Sir,sabuwar daliba ce inji principal,yace a saka sunanta cikin register" kai ya gyada gami da cewa
"Okay"idanuwansa nakan fuskar iman,wadda ta fara jin wani iri,saboda yadda idanuwa sukayi mata caa na dalibai maza da mata,musamman ita da banda primary data yi da maza lokacin bata da wayo, junior dinta ajinau mata ne zalla,kasancewarta government school
"What is your name?" Malamin ya jefa mata tambayar da harshen nasara,cikin sassanyar muryarta data sake janyo mata idanuwa ta amsa masa,sai ya jawo register din kusa dashi ya rubuta sunan,sannan ya bawa munira umarnin tayi mata wajen zama.
Kai tsaye seat dinta ta matsa mata,saboda tsarin zaman duk seat daya mutum biyu yake dauka,da su biyu ne akai ita da qawarta,to bayan an shiga sabon term sai aka canzawa qawartata makaranta,hakan ya sanya take zaune ita daya,saboda ba da kowa ita din take jurar zaman ba.
Ranar farko a makaranta ga duk sabon dalibi rana ce dake cike da baqunta da rashin sabo,kusan hakan taso faruwa ga iman,saidai kuma kirkin munira ya hana hakan faruwa,saboda janta data dinga yi da hira,koda aka fita break tare sukayi break din,aka dawo suka zauna a seat dinsu,tana ta bata labaruka da suka danganci makarantar da yadda take,har zuwa lokacin da aka kada bell an tashi kenan,iman din ta saba jakarta tana nufi qofa bayan ta yiwa munira sallama.
A qafa ta fara takawa sabida tadan qara gaba inda babu cunkoson dalibai sosai,tana tsaka da tafiya taji muryar munira na kiranta,saita dakata ta kuma waiwayo suka hada ido,kowa ya sakarwa dan uwansa murmushi,ta dakaci muniran har ta qaraso inda take,suka jera sukaci gaba da tafiya tare,kafin daga bisani muniran tace
"Ya na ganki kina takawa a qafa?" Waiwayawa iman tayi tadan dubeta cike da mamakin tambayar tata,to ame takeson ganinta?,kamar taji tambayar da ta yiwa kanta sai ta dora
"Ko mai daukarki ne bazai samu zuwa ba?,ranar farko a makaranta kuwa ai bai kamata ya barki kiyi tracking ba". Sai yanzu ta fahimci zancanta,saita murmusa
"Dama can motar haya nake hawa,saidai wataran idan hanya ta biyo da yaa al'ameen ta qofar makarantarmu ya jirayeni mu koma gida tare" kai munira tadan jinjina,tana cike da mamaki,saboda kallon farko data yiwa iman,ta mata duba ne na yaran da suka fito gidan hutu,sam kyan qira da dirin da Allah ya bata tayi zubin gidan yaku bayi ba,ta tsammaci zata ga wata shimfidediyar mota tazo daukarta ne,saita aje tunanin nata tana tambayar iman din unguwar da take.
Sanda ta gaya mata idanu ta fiddo
"Ai bamu da nisa da juna,abun hawa daya zamu hau,tunda nima yau shuru ba'azo daukata ba" ta fada tana saka hannu tana tsayar musu da adaidaita sahu,suka masa bayani suka shige,iman din na qoqarin neman ragi kan kudin da ya gaya musun,amma sai taga muniran bata damu da price din da ya fada ba,don haka itama sai tayi shuru kawai.
Suna tafe muniran na jan iman da hira,a dan zamansu na awanni iman din ta fuskanci muniran kamar daga gidan masu dashi ta fito,koma ba haka ba to tabbas gidan data fito sunfi nasu wadata,tadan saki jiki kadan da ita tana biyewa hirar tata,har aka kawo inda muniran zata sauka,wanda daga nan zuwa gidansu iman baifi naira 20 ba kudin mota.
Kudin da ya buqata munira ta ciro ta biya musu,iman zata doje tayi gaba abinta bata tsaya ma sauraren qorafinta ba,mai adaidaita yaja sukayi gaba,cikin ranta kafin su qarasa gida tana ta yaba kirkin muniran da karamcinta,azamansu na wasu taqaitattun awanni.
A dan gajiye ta shiga gida,saboda akwai qaerin lokacin tashi kadan a wannan makarantar kan makarantar data baro.
Da sallama ta kutsa tsakar gidan nasu qarfe biyu da rabi da minti biyar,inna dake duqe tana baza masarar data wanke don ta samu tasha iska akai niqa ta dago tana amsa sallamartata,idanunta akanta,ta sabule jakar bayanta ta zauna saman kujera 'yar tsuguno tana dan goge zufar goshinta tare da yiwa inna sannu da gida
"Yauwa,an taso kenan?" Ta fada tana juyawa zuwa ga aikinta
"Wlh inna,duk na gaji,makarantar tafi waccan nisa"
"Ah to,aishi sa kai yafi bauta ciwo" tasan mita sarai inna zata dorar,don haka ta saki dariya kawai ta miqe tana daga jakarta
"Amma inna karatun da ake mana a waccar makarantar baiko kama qafar rabin na wannan makarantar ba"
"To Alla ya taimaka" ta amsa mata.
Kamar zatayi gaba sai kuma ta dakata
"Inna ya al'ameen bai dawo ba?"
"Tunda ya fita dai bai shigo ba" saita daga hannunta duban fuskar siririn agogon silver dake hannunta tana duba lokaci,wanda yau ta fara sakashi,kuma al'ameen dinne ya siya mata saboda makarantar
"Amma dai inna ba tuwo zakiyi ba"
"Zanyi ko zakiyi?" Kai ta gyada cikin salo na zaquwa da son jin amsar innar
"To zanyi inna"
"Bashi bane maqiyar tuwo.....dambu nakeso wai nayi" sai fuskar iman din ta dan saki,don ita gaba ce tsakaninta da tuwo,tunda taji batun dambu kuwa,tasan saboda malam da al'ameen za'ayishi,don haka tayi damarar zagewa tayishi yayi kyau yayi dadi ko don al'ameen din,tana matuqar jin dadin yadda yake yaba mata idan tayi girki,da yadda yake nuna jin dadinsa,koma bayan sadiq dake kusheta,wani lokaci har sai malam ya shiga sannan zai qyaleta,duk da shima yana yine kawai saboda tsokana,bawai don bata iya din ba,don ta fannin girki inna ta yarda da ita dari.bisa dari,tun tana da shekara takwas innar ta fara shiga madafa da ita,tana da shekara sha biyu kuwa ta sakar mata girkin,saidai ta dinga tayata ko duba mata,zuwa yanzu kuwa da ake magana fa gama zama cikakkiyar qwararriya.
Ruwa kawai ta watsa tadan tsakuri abincinta kamar yadda ta saba ta fito ta kama aikin,yau dama babu islamiyya,anyi bikin yaye wasu dalibai da suka sauke alqur'ani,don haka aka basu hutu,wanda ida an koma su iman dinne 'yan babban aji,duk da ita dama already tana biyo bayan duk inda aka biya matan da hadda wajen malam,wani lokaci kuma idan abubuwa sunwa malam din yawa al'ameen ya karba mata.
Cikin karsashi da kuzari take aikinta,tana yi tana yiwa inna surutun makarantar,wanda ada al'ameen din ta tarawa labaran,saidai tasan ba lallai ta sake ta bashi labarin sosai ba,sabida kaifi da nauyi da idanuwansa a yanzu suke mata,ta rasa dawa kuma zata tattauna wannan,qawarta daya a unguwarsu,to itama takan jima basu hadu ba saboda yanayi na karatu da kuma tsarin tsaron fita a gidan kowannensu,saidai tanata timing da sanya lokacin da zata fita taje susha hira da ita.
Ganin ta kammala hada komai,dambun ya hau wuta,kuma tsakar gidansu babu kowa,saita debo 'yan qananun brassier dinta da ta fara amfani dasu a boye ta zuba a botiki ta zauna daga bakin famfo,wanda yake daura da qofar shigowa ta fara wankesu.
Ta jima tana ajiyarsu,tun wani lokaci da sukaje nijer,anty raheena 'yar uwar inna ta bata tace ta ajjiye zasuyi mata amfani,bata aminta da hakan ba sai sanda amfaninsu ya taso mata,ta rasa wanda zata gayawa tana buqatarsu.
Babu irin wannan hirar tsakaninta da innarta tun farko,ya alameen din nata kuma koda wasa ba zata iya tunkararsa ta gaya masa tana so ba,sai ta tuna da ajiyarta, doon haka ta debo abunta ta fara amfani dasu hankalinta kwance,amma tanata boye boye,don sai irin haka gidan babu kowa take wankesu ta shanyasu a bayan qofar dakinta,ko idan ta shiga wanka.
Tana wankesu tana dan rera karatun qur'ani da tausashiyar muryarta mai cike da sanyi nutsuwa da kuma tashen 'yammatantaka.
Daidai lokacin da al'ameen wanda kansa ke ciwo ya shigo cikin gidan,tun daga soro yayi sallama kamar yadda ya saba,saidai muryarsa bata da wani qarfi me yawa saboda gajiya da kuma ciwon kai,wanda ya tabbatar stress ne na dinki.
Sam bataji shigowarsa ba,kamar yadda shima ya ganta bagatatan a farkon qofa,don sam bai kawo samuwar wani mutum zaune a wajen ba.
Saman fuskarta ya fara sauke ganinsa,ta langabe kanta gefe guda,qaramin bakinta me dauke sa jajayen labba yana motsawa a hankali,sautin karatunta yana fita da kadan da kadan,gefan da kanta ya karkatan jelar manyan kitso guda hudu dake kanta sun kwanto ta nan har saman qirjinta.
Tayi masa kyau ainun,fuskarta da maqerin budurci ke aikinsa a kanta tayi wani fresh tare da annuri na daban,saiya lumshe idanunsa qirjinsa yana bugawa,wani abu mai sanyi da qarfi da girma ya tsaga qirjinsa ya sauka saman zuciyarsa,ya tabbatar wani feeling ne me cike da soyayya da kuma qauna ya saukar masa,sai ya bude idanun nasa yana saukesu zuwa ga abinda take wankewar.
Idanu ya qurawa brasssier din nata yana mamakin yaushe ta fara amfani dasu,qaramin murmushi ya qwacewa fuskarsa,ya sani tunda can tana da yawan zama da hijabi cikin gidan,to amma kwanaki yaji yadda inna ke qorafin bata cirewa ko cikin daki tasha iska,wala'alla yana da nasaba da hakan?.
A firgice ta dago sanda taji sallamar mutum saman kanta,a zabure ta miqe saboda ba zatan ganinsa,har tana fatali da ruwan wankin da abebaden dake ciki tayi dakinta da gudu,sai ya bita da kallo,dariya ta qwace masa,ya duqa a hankali ya kwashe mata abubuwanta da hannu daya ya maida ga botikin,sannan ya tako zuwa cikin gidan yana aake jaddada sallamarsa,inna dake can uwar daki ya fito zuwa rumfarta tana amsa sallamar,saiya taka a hankali zuwa rumfar innar yana cire takalman qafarsa,rabin hankalinsa na ga dakin iman din data turo qofar ya murmusa ya shiga rumfar innar.
*_HILTI UNISEX CHOCOLATE STILL AVAILABLE, GRAB YOURS NOW,DAB TAKE DA QAREWA_*👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽
08184017452
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 09
*Game buqatar biyan kudin zafafa biyar,zai iya tuntubarmu ta wannan number*
09032345899
Ko kuma
09166221261
__________________________________
"Tunda ta shigo ta fara tambaya da cigiyarka,nasan kuma labarine kawai cike taf da bakinta zata baka na makaranta" inna ta fada mishi bayan sun gaisa,tana ninke abun sallar data bari a wajen ta gashi ta shiga ciki,murmushi ya sake yana dan shafo kansa,yana funa dramer dinsu ta yanzu yanzu
"Aiki take tayi ai inna,na dauka yau zata huta sabida gajiyar sabuwar makaranta" dan satar dubansa kadan inna tayu,duk sanda ya nuna wata kulawa kan iman din hakan namata dadi qwarai,kuma dama shi ba baqon abu bane a wajensa,tana da tabbaci da yaqinun diyarta qwaya daya tilo ta dace da mijin aure,namijin da yasan abinda yake,mai yawan tausaya mata da qaunar farincikinta
"Diya macace al'aminu,gwara taci gaba da sabawa akan hakan,na gana nauyun iyalinta ne zai hau kanta,mace bata da wani hutu da ya wuce tayi abinda ya dace a matsayinta na mace,to daga baya saita huta din" dan nauyin innar yaji ya kamashi,saiya gyada kai sannan ya miqe yana yiwa inna sallama.
Koda ya fito tsakar gidan babu ita har yanzu,hakanan babu motsinta,ya gifta inda ta tashin idanunsa nakan botikin wankinta,ya sake sakin murmushi ya wuce soro,ya saka key ya bude dakinsu ya shiga.
Saman kujera ya zube yana furzar da iskar daya zuqota tun daga hunhunsa,hannunsa yana saman kansa yana shafa sumarsa daga gaba zuwa baya a hankali,yanajin yadda kansa ke sarawa,gefe guda kuma yana qarewa dakin nasu kallo,yasan hargitse kadan yana buqatar gyara,kwana biyu bashi da isashen lokaci da zai zauna ya gyara din,dinki yake na jama'a tuquru saboda gabatowar azumi,yanason ya samu isashen kudi a hannunsa da zai yiwa gidan siyayyar kayan azumi,ya yiwa iman kayan sallah sannan yaje ya gano yayarsa itama da nata kayan azumin dana sallah,inna tasha hanashi saboda sadiqu da malam duka suna tasu siyayyar,amma sam yaqi yarda,inda daga qarshe yace baya jin dadin hakan a ransa,sai yaga kamar innar ta warshi ne shi,wannan furucin yasa ta qyaleshi,bata sake magana ba.
Ruwa ya fara diba ya shiga wanka ko zaiji dadin jikinsa,bayan ya fito ya murzawa qofar dakin nasu key,duk da yasan babu me shigo musu kai tsaye,ya sanya boxer da singlet ya koma ya kwanta saman doguwar kujerarsu yayi rub da ciki.
Idanunsa ya runtse gam,tunanin iman na dawo masa,surorinta na bayyana cikin idanunsa,wani yanayi na mamayar ilahirin jikinsa,tsigar jikinsa na tashi,sai ya sake gyara kwanciyar tasa yayi rub da cikin da gaske,ya sake rufe idanunsa a hankali yana ci gaba da dulmiya cikin tunaninta,murmushi na qwace masa saman fuskarsa lokaci bayan lokaci,sai daga bisani yaso dakatar da kansa saboda ganin yadda tunanin ke neman qara ta'azzara ciwon kan nasa,don haka ya haqura da kwanciyar,ya miqe ya balli paracetamol biyu cikin magungunansa yasha,ya sanya jallabiya ya jawo qofar dakin nasu ya fito zuwa qofar gida.
Yaci sa'a malam yana nan,an gama karatun yamma yana shirin sallamar yara,ya cire takalmansa yayi tattaki cikin girmamawa zuwa gaban malam din,yayin da shima malam ya bishi da kallo wanda ke nuna tsantsar kulawa.
Gefansa ya zauna,bai kuma yi magana ba har ya gama sallamarsu
"Al'ameenu.....lafiya kake kuwa?" Malam ya jefa masa tambaya,sai ya daga kansa cikin murmushi ya dubi malam,yana yabawa da jinjina qoqarin bayin Allahn,yadda suke iya hakaito damuwar daje tattare dashi,ta ciwo ce ko akasin hakan
"Kaina ne yake dan min ciwo"
"Subhanallahi.....matso nan" malam din ya fada,saiya matsa gabansa kadan,ya sanya hannu saman kansa ya kama masa shi da addu'o'i,ya matsa bayan ya gama yana masa godiya,wanda babu jimawa yaji ya fara sauka,daga bisani ma suka shiga tattaunawa,har zuwa sansa sadiqu ya dawo dava wajen aikinsa shima ya zauna nan wajensu yana cewa
"Na biya ta wajen aikinku mu taho tare,saina taras waika taho"
"Kaina ne ya fara ciwo,saina yanke na dawo gida na huta" cikin yanayin nuna alhini da damuwa yace
"Subhanallah,sannu"
"Yauwa,da sauqi ai,malam ya kamamin ya sauka" ya fada ganin yadda fuskarsa ta nuna damuwa
"Kaine ma man,ka dinga kwanciya wasu kwanaki kana hutawa,kana stressing kanka da yawa wallahi" murmushi kawai ya sakar masa ba tare da yace komai ba,shi a karan kansa a jikinsa yakejin akan struggling bai fara komai ba,namijin duniya dan gwagwarmaya ne,abinda ya saba gayawa sadiqu kenan.
Basu shiga gida ba anan suka yada jam'in sallar magariba su da sauran jama'ar dake salla a wajen duk sanda malam ke kusa,aka idar suka sake zama hira,irin zaman da ba kasafai lokaci ke basu damar yinta ba,saboda baqi da kuma yanayin aikinsu,daga bisani malam din yayi baqo,suka shiga tattaunawa,hirar sauta koma ysaka insa da sadiqu,sunaga qus qus dinsu saboda kada malam yaji,saboda hirar irin tasu ce,yana bashi labarin yarinyar datace tana sonshi,al'ameen din nata sukar abun,saboda shi sam yana qalubalantar mace tace tanason da namiji a irin wannan zamanin,daga qarshe malam ya tura daya daga cikin almajiransa su sanya a fito da abinci,wanda dama da wuya kaga anyi girki a gidan dai dai cikin masu gidan,saboda baqin da malam din kanyi lokaci zuwa lokaci,sadiqu yacewa yaron ya gayawa iman ta hado da nasu.
Cikin gidan babu kowa sai ita,don haka inna ta tsaida yaron malam din,ta taya iman shirya abincin,yaron ha daukar mata wani ita kuma ya dauki wani suka fito dashi.
Tunda ta doso wajen idanuwansa na kanta,cikin lullubin hijab har qasa,duba daya zaka yiwa hijabin kasan tsafta ta wadaceshi,don harda karin guga,idan kuma ta kusanto inda kake zaka iya jin qamshin body mist din da take amfani dasu,'yan 300 ne,saidai suna da sanyin qamshi,tana da maitar son qamshi da turare,don haka tun kafin ma takai haka ta iya zaben turare, training din al'ameen dince,tun daga tsafta zuwa son qamshi,girki ne kawai aikin inna.
Har zuwa sanda ta fara isa gaban malam ta ajjiye musu nasu abincin bayan ta duqa ta gaidashi shi da baqonsa idanunsa na a kanta,girma da 'yammatancinta yana sake cika sosai,ta zama budurwan gaske,saita qaraso gabansu a hankali,daidai sanda baqon malam ya furta wata magana data dauke hankalin al'ameen daga wajen kwata kwata ta maidashi kan hirar su malam din.
"kada dai ace hajarunka ce ta girma haka?" Murmushi malam din yayi
"Itace mana" kai ya gyada
"Ikon Allah,girman dan mutum babu wuya"
"Ka kwana biyu baka ziyarcemu bane shi yasa" malam ya amsa masa gana wanke hannunsa cikin kwanan wanke hannu dake gabansa wanda inna ta hado dashi
"Lallaifa an kwana biyu" sai yadanyi shuru kadan sannan yace da malam
"Ni kuwa malam khalilu,da zaka amince ai da mun qulla wani alkhairi" daga kai malam yayi ya dubeshi sanda yake qoqarin bude kwanonin abincin
"Ina saurarenka malam basiru"
"Me zai hana yaron wajena ilyasu yazo yaga hajaru,bamusan me Allah zaiyi ba,kaga idan Allah ya daidaita tsakaninsu ai mu shikenan,kakarmu ta yanke saqa,tuwona mai na"
Saura kadan maganar tayi tafiyar yaji da numfashin al'ameen,idanunsa suka fara laluben iman dake duqe a gabansu tana ajiye musu nasu abincin sabida bacewa ganinsa da take neman yi,zuciyarsa tayi wani bugawa tare da qara adadin gudunta.
Ajjiye murfin hannunsa malam yayi yana duban baqon nasa
"Zanfi kowa jin dadi matuqar hakan zata kasance,inama ina da wata diyar bayan hajaru da na baku,kuyimin aikin gafara,tuntuni na bayar da hajar,lokaci kawai muke jira a zartar da komai nan kusa in sha Allahu".
Nannauyar ajiyar zuciya alameen din ya saki,yana share gumin dake goshinsa tare da duban tsakiyar blue din qwayar idanun iman din dake haske cikin dan hasken dake kewaye da wajen,kamar tasan ita yake kallo saita daga kai suka hada idanu,ta sakar masa da murmushi tana sadda kanta qasa cike da jin nauyi da kunyar abinda ya faru dazun,abinda ke alamta masa cewa bataji maganar dasu malam ke tattaunawa ba,nauyin numfashin ajiyar zuciyar da ya saukar ne ya sanyata daga kai suka hada ido da ita.
Kusan baici wani abincin kirki ba ya tattara ya koma cikin gidan,dakinsu ya fara shiga saidai ya kasa zama,yanason yin magana da iman din,ba kasafai ya fiya son kebewa da ita ba saboda kare haqqin sharia sa kuma gujewa shaidan,amma dole ya zaqulo dalilin da zai sanya su zauna suyi magana da ita,don haka ya dauki sabuwar wayarsa daya siyo a dazun ya juya da niyyar fitowa,dai dai sanda sadiq ya shigo ya wuce cikin gidan ya barshi a dakin yana amsa waya.
Dakin malam da ya gani a bude ya tabbata malam din ya shigo cikin gida,kuma idan ya shigo din inna na tare dashi,hakan ya sake bashi qwarin gwiwar isa ga rumfar inna.
Cikin saa ya sameta zaune tsakiyar litattafanta,ta bajesu tanata qoqarin gwada assignment din da aka basu a yau din,wanda zasuyi zanen zuciya ne tare da fitar da kowanne chamber na cikinta.
A hankali ta daga kanta tana amsa sallamar tashi,sai kuma ta maida kan nata ta duqar tsakanin qafafunta tana juya abun zanen dake hannunta,ya sake sakin murmushi,ya qarasa a hankali kan kujerar dake daura da ita ya zauna saman hannun kujerar,cikin lallausar muryarsa daya ragewa kaifin sauti yace
"Hajar 'yammata" ji tayi tamkar zata lume a wajen,sautin muryarsa a yau din ya zama na da an cikin kunnuwanta,uwa nauyinsa da takeji ya ninku cikin ranta daga sanda yaga abinda taje wankewa dazun
"Ina fatan kin kwashe wankinki,saboda banason kowa yazo ya gani" saita saki abun rubutun ta juyar da kanta ta sanyashi saman kujerar tana boye dariyarta cikin jin nauyi,ta tabbata zaiyita tsokanarta ne idan batace wani abu ba,don haka cikin siririyar muryarta tace
"Don Allah ya alameen....don Allah" yasan me takeson fada,saiya saki qaramin murmushi me dan sauti kadan,ya zamo ya zauna sosai saman kujerar yana cewa
"To shikenan....duk da dai an boyen.....shikenan dai,ungo wannan,sakamin a charge" a hankali ta juyo tana avoiding hada idanu dashi,tasa hannu biyu ta karba wayar da yake miqo matan
"Laaaa yaya,taka ce?" Kai ya gyada mata tana juya wayar a hannunta
"Tawa ce" saita narke kadan,duk da bata bari sun hada ido ba
"Don Allah yaya yaushe zaka siyamin nima,kaga fa na shiga senior" ya santa qwarai da son waya,saidai a yanzu bashi a ra'ayin ta riqe qaya torching kwata kwata saboda wasu dalilai
"Wannan bata ishemu ba?,abuna ai naki ne"
"Yaaya,idan ka fita fa da abarka zaka dinga fita"
"Zan dinga bar miki ita duk weekend kina danawa,shikenan?" Cikin murna tace
"Yauwa yaya,na gode"
"And....idan naga yanayin performance naki a wannan term din,zan siya miki qaramar keypad indai inna da malam sun bari" sosai ta nuna murnarta,ta tashi ta fara qoqarin saka masa a chargyn
"Idan kin gama kizo zamuyi wata magana" ya fada yana saukowa tare da buda takaddan data fara zanen yana kallon zanen nata.
Tana gama sanya chargyn waigowar da zatayi taga ita yake kallo bayan hannunsa na riqe da zanenta,wani weakness ya saukar mata,duk kuzarinta na daxu ya gudu,batasan wane irin power da magnet ne a idanun yayan nata ba,wanda a baya da babu su sai a yanzu
"Zauna a nan" ya mata nuni da wajen da yake buqatar ta zauna din,inda zai zamana suna fuskantar juna ne,ta zauna ta lanqwashe qafafunta
"Wa kikeso a zuciyarki?" Ya jefa mata tambayar kai tsaye,abinda ya sanyata daga kai ba tare da tako shirya ba ta dubeshi saboda jin saukar ba zata da tambayar tashi tayi mata,idanunsa cikin nata ya jinjina kai
"Yes.....zuwa yanzu kin girma queen,ke din ba yarinya qarama bace kamar yadda kike kallon kanki,zuciyarki zata iya fadawa soyayya at any time.......wa kikejin kina so" sosai ya jefata cikin nazari,kafatanin rayuwarta batasan kowa ba bata saba da kowa ba sama dashi,bata taba kallon kowa ba taji wani abu na daban a kanshi ba sai shi,inda tasan soyayya ko alamominta,ba shakka zata iya cewa wala'alla shi takeso,amma yanzun batasan shaquwa ko ganin girma bane,duk bata sani ba.
Maganarsa me nauyi ce,don haka ta girgiza masa kai kawai
"Uhunnn..... talk to me mana,ki gaya min" sake girgiza kai tayi da qarfi,murmushi me qarfi na son qwace mata,wanda ya cakuda da kunya
"Don Allah yaya,babu kowa fa" kamar yace
"Harda ni?" Sai kuma ya danne wannan a ransa,ya saki nannauyar ajiyar zuciya,ya sake cooling muryarsa sosai
"Bani aron hankalinki iman" sau daya ta daga kai ta kalleshi ta mayar qasa tana sake gada nutsuwarta kamar yadda ya buqata
"Inaso ki bani dama guda daya tak a rayuwarki iman,ina da wani tanadi na musamman cikin rayuwarki"
"To yaya" ta fada a sanyaye.
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 10
*_Wannan littafin na kudi ne,game buqata zaki iya tuntubar wadan nan numbers din_*
09032345899
Ko kuma
09166221261
"Imannnn" ya danja sunan nata,ta amsa da na'am,har yanzu idanunta suna qasa
"Bana so ki kula kowa,banason kiyi soyayya da kowa..... infact ma,na miki zabin mijin aure wanda zai dace dake in sha Allah.....kin yarda?" Kai fa gyada tana sake saukar da kan nata qasa
"Kinyimin alqawari?" Saita sake jinjina masa kan,ya sauke numfashi mai nauyi daga qirjinsa yana furta
"Alhamdulillah".
Shuru yadan ratsa dakin,yana ci gaba da kallon zanen nata,saidai zuciyarsa ta rarrabu kashi kashi wajen tunani iri daban daban
"Zanen nan yayi kyau,ina tunanin yadda kika iya zanen zuciya har haka.....soyayyarki zata kasance me kyau haka" da sauri ta daga kanta suka hada idanu,wadanne irin manya manya kalmomi ya al'ameen ke mata amfani dasu ne haka,gashi ya ritsata da idanu yana kallonta,sai ita ta janye nata idanun tana sake qunshe fuskarta waje daya,ya saki murmushin nasarar da yake hangowa,yana iya hasashen yadda yake samun ci gaba da kuma galabar narkar mata da zuciya kowacce rana idan ta bullo kafin ta fadi.
Shi ya zauna ya tayata aikin gaba daya kasancewar science yayi shima,banda rashin zamowarsa dan wani shi din mutum ne me matuqar qwaqwalwa daya kamata ace ma zuwa yanzu yayi nisa a karatun likita da yake jarabar so,suna aikin yana dan janta da hira don ta saki jikinta,tadan sake amma ba kamar yadda suka saba ba,bai bar cikin gida ba saida inna ta fito daga wajen malam,sannan ya wuce dakinsu ya barta da tarin tunani cikin kwanyarta.
********WASHEGARI******
Bayan tasowarta daga makaranta wanda shima tare da munira suka taho,ta kuma sake biya mata kudin mota,bayan tayi wanka ta sauya kaya taci abincinta inna ta bata dakan garin kunu wanda akewa malam,tace takai bayan layinsu ta tsaya a daka ta taho dashi
"Don Allah inna zan leqa gidansu bushira" bushiran ba boyayya bace a wajensu,nutsatsuyar yarinyace da suke taba qawance da iman,wanda tun quruciya itace kadai ta dauke halayyar iman din,duka sauran irinsu rahama abokan fadanta ne,banda yanzu da girma da hankali yazo ake gaisuwar mutunci a wuce wajen.
Tana kaiwa mai dakan kudin ta zarce gidansu bushira,wanda gidajen dake tsakaninsu da gidan dakan bai wuce gida shida ba,tayi sa'a fa sameta a gida,dama kuma ba inda take zuwan,islamiyya ce,kuma makarantarsu daya,anyi musu hutun sauka sai wani satin xasu koma
"Wata sabon gani" bushira dake cire lallen data yiwa yatsu hannunta ta fada tana tabe baki bayan sun shiga dakinta da suke kwana da qannenta,murmushi ima tayi suka shiga tsokanar juna da hirar duniya,kafin daga bisani iman din fa budewa bushira abinda ke tafe da ita.
Shuru iman din tayi na kusan minti goma tana juya bayanan da bushira tayi mata,baya ta gama bata labarin komai,ta dauke hannunta daga kumatunta
"Amma bushira,ta yaya yaya al'ameen zai soni,bayan yayana ne?"
"Yayanki,ciki daya kuka fito?,ko yaya sadiqu ne?" Kai ta girgiza alamun a'ah
"To kuwa kinga ya halatta kuso juna ku kuna qaunaci juna,dama kuma abinda yafi dacewa kenan,don kusan dama ke din rainonsa ce......kuma ko ke qarya kike kice baki sonshi munafuka" bushira ta qarashe maganar tana ɗakawa iman duka a cinya gami da sakin dariya wadda ta sanya uman din dole ta tayata
"Ya al'ameen ya gama haduwa iman,idan ma bakiso wata ce zata daukeshi,yana cin list na sahun farko na kyawawan unguwan nan wanda babu na biyunsu,duk yadda zan gaya miki yadda 'yammatan unguwar nan ke sonshi da fatan ya sosu ba zaki gane ba,abu daya ya rage miki....ki jira sanda zaice kawai yana sonki ki karbi tayinsa hannu bibbiyu.....idan ma yayi nauyin baki ke ki furta kawai a wuce wajen" duka iman ta kaiwa bushira a gadon bayanta
"An gaya miki bani da ajine,duk yadda muka taso tare dashi bazan bari ajina ya zuba ba"
"Gaskiya ne tawan,kema a unguwar yayinki ake,kawai shakkar malam dasu ya al'ameen din ya hana a fara tareki ko sallama dake,amma ni kaina masu kamun qafa dani a kanki suna da yawa,harda masu motoci wallahi" miqewa iman tayi tana daure gashinta mai santsi da ya ware wanda dama babu wuya ya warware din,ta maida hijabinta saman kanta tana fadin
"Su riqe motocinsu.....kinga na manta shaf da aiken daya fito dani ma"
"Muje na taka miki" bushira ta fada itama tana janyo hijabinta suka yiwa ummansu sallama suka fito tare.
*******SANNU SANNU******
Kwanaki ke shudewa sa iman cikin makarantar nasreen,zuwa sannan bata da wata qawa ko aminiya data wuce munira,shaquwa me qarfi ta fara shiga tsakaninsu,duk da banbancin halaye da kuma dabi'u dake a tsakaninsu,gami da sukunin rayuwa.
Cikin sati uku ta fahimci wace munira,'ya mace guda daya tilo da mamanta ta haifa bayan yara maza qannenta guda hudu,tana ji da ita ainun,tana bata kulawa da gata,kusan mafi yawa daga cikin familyn su munira masu arziqi ne masu sukuni,saidai shi mahaifin muniran rufin asirin Allah gareshi,mamarsu muniran ta fishi kudi,hakan ya sanya komai na gidan take tafi dashi yadda takeso idan ma maigidan yayi wanda baiyi mata ba,tana ji da munira sosai,hakan yasa ta daukaki rayuwarta,tanason rayuwa me tsada sosai,hakanan takan kutsa kanta inda Allah bai kaita ba,gidajen 'yan uwan mamanta masu dashi ainun babu inda bata sani ba,wani lokaci idan ta shilla ta debi kayanta ta tafi daya daga cikin gidajen nasu,takan jima bata dawo nasu gidan ba,har ma sai kayi zaton 'yar gidan ce.
Da yake fara ce hakan sai ya sake qawata fuskarta,ya kuma ja hankalin samari a kanta,tana da samari sosai,kuma dukkaninsu 'ya'yan manya ne,wayar hannunta kuwa a lokacin babbar iPhone ce,dukkan abinda take ta'ammali dashi,tun daga sutura zuwa cima masu tsada ne,komai zatayi saita siya me tsada,saboda mamanta ta tsaya mata,batason sam taga muniran tata ta shiga cikin danginta an raina ta,hakan ya sanya take kashe mata kudi tuquru.
Saidai kuma muniran nada kirki daidai gwargwado,hakan shi yake taimakawa wajen boye da yawa daga halayyarta da basu dace ko kamata ba.
Ba komai na halayenta iman ta sani ba,tunda iyakarsu makaranta,da an rabu shikenan,sai kuma washegari,iya abunda ta sani muniran tana da kirki da kuma yawan kyauta,duk da tana zillewa duk wani abu da zaisa muniran ta kashe mata kudinta,kamar tafiyarsu tare,da yawan lokuta zillewa take tayi tafiyarta saboda kada muniran tace zata biya mata kudin motar.
*MONDAY MORNING*
Cikin clean uniform dinta da suka dauki karin guga kyakkyawar matashiyar hajar Ibrahim Khalil ke takowa tana nufar ajinsu,kafadarta daya saqale da jakarta,daya hannun kuma dan madaidaicin flask din abinci ne a ciki.
Kana duban fuskarta zaka karanci ranta a bace yake,saidai hakan wani kyau ya qara mata na musamman,sandin bacin ran nata makara datayi,aka kuma shanyasu a bakin gate har na wajen awa daya cikin rana,wanda wannan shine irin punishment din makarantar tasu.
Kamar ance ta daga kanta saman varander dinsu,ta daga kyawawan blue eyes dinta,idanunta sauka ga malamin,sir arabi,malamin daya takurata tun zuwanta makarantar,da shegen kallo naci da kuma shishshigin shiga harkarta,shike daukarsu darasin turanci wato English,yammatan makarantar da yawa suna yinsa,saboda motar da yake hawa,kana kallonsa kasan ba talauci ko babu suka sanyashi koyarwar ba,saidai ita sam imani hakan bai dameta ko ya dadata da qasa ba,don sam jininsu ita bai hadu dashi ba,ya fiya jin kansa saboda yaga yana tashen samartaka,yana sanya shaddodi da hawa mota,ita sam a rayuwarta batason mutum me jin kansa ma,izza da fadin rai,shi yasa tako ina ya al'ameen yake burgeta.
Yana da wani irin kwarjini gami da aji,uwa uba miskiline naqin qarawa idan baiso ba,hakan yasa baya daukar raini ko izgili,amma sam baida girman kai ko dagawa.
Ta sauke nata idanun tana jan tsaki qasa qasa,gami da qare hade ranta gab da zata shiga cikin ajin nasu,sabida yadda yawanci lokaci irin wannan sanda tazo a makare mazan ajin ke binta da kallo,abinda ta tsana ita kuma kenan,don haka a dake ta shiga ajin.
"keda mutumin naki ne?,na hangeshi tsaye upstair" munira ta fada tana danne dariyarta sanda iman ke zama kusa da ita,tana duba littafin subject din da akeyi
"Shine mana,me shegen kallon tsiya,banason mutum me kallo"
"Tsaurin idanu dai,kwata kwata baki dace irinsa bama,shi bai gani ba kedin kalar matar manya ce" waiwayowa iman tayi sanda take dora littafin saman table dinta
"Kamar yaya?" Murmushi munira tayi tana ci gaba da copying note dinta
"Kamar har yanzu bakisan baiwar kyan da Allah yayi miki ba,ai kyan kyau irin naki ki morewa babban gida,inda zaa jiqaki da kudi da mota,fita qasashen waje babu kama hannun yaro,shine kika mori kyanki,amma ba kowanne irin kalar namijine zaizo ya tsaya gabanki da sunan yana sonki ba" tsaki iman taja,saboda ta dauki maganar munira a matsayin shirme,ta bude littafinta ta fara kwafar note din da sauri da sauri don ta fuskanci ya kusa dawowa ya goge wanda ya fara.
"Am telling you fa,kina ganin kamar wasa ce maganata?,to Allah koni da ban kama rabin qafarki a kyau ba,zakiga kalar mijin da zan zaba"
"Don Allah ki shiru ki barni da bacin ran da yake damuna" dariya muniran ta saki tana ci gaba da rubutun,har zuwa sanda malamin ya kammala yayi musu explanation ya sallamesu.
"Me ya hanaki zuwa makaranta Friday ne?" Iman ta tambayi munira tana maida littafinta jaka,sai data juya manya idanunta,da alama amsar da zata bayar amsa ce da take mata dadi cikin ranta sosai sannan tace
"Kinsan biki muke na wata cousin dita,so ran Friday muka tafi garinmu acan zaa daura aure,kuma ina cikin wanda aka siyawa ticket zasubi flight,kinga ko bazan bari nayi missing ko damata ta wuceni ba,nayita neman number dinki na gaya maka,sai dana fara checking wayana naga ashe bamu taba exchanging numbers ba......ki bani number dinki saboda irin hakan,kinga nama canza sabuwar waya,ranar aka bani gift dinta" munira ta fada tana saka hannunta a aljuhun rigarta.
Kallo daya zaka yiwa wayar kasan cewa bata qananun kudade bace,hakanan sabuwa ce fil sai sheqin sabunta take,munira tabi wayar da kallo sannan ta amsa mata
"Nikam ai bani da waya,ta ya al'ameen nake ara duk weekends nayi game ko browsing" kallon mamaki qarara munira ta jefi iman dashi,harda dan ja baya
"Kina ss 01 amma ace baki da phone iman, jokes apart please,wasa kikemin ko number dince ba zaki bani ba?"
"Tunda baki yarda ba ai babu amfani na dage saina gamsar dake,duk yadda kika dauka hakane"
"Am sorry my friend,Allah na dauka wasa kikemin....amma kuma,ba sani ba wallahi,da dana canza na baki dayar,sai qanina na bawa wanda yake bin me bina" idanu iman ta fidda
"Ni shegiya kaza,ya al'ameen bazai bari ba,amma ina saka ran muna gama wannan term din zai siya min keypad sabuwa in sha Allah,yayi alqawarin idan nayi abun kai zai siyamin" dariya sosai munira ta saki tana kallon iman
"See you don Allah,wani irin keypad?,to ko 'yan aikin gidanmu banjin akwai me keypad,don Allah karma ki fada wani yaji,sai ajinki ya zuba,mazancan da kike jawa aji saisu rainaki,su dauka qaramar yarinya ce ke".
Rai sosai iman ta bata tana dubanta
"To sai me?,ni ina farinciki da duk abinda nake dashi,kuma iya abinda yake ganin ya dace dani kenan,kuma ina farinciki da hakan"
"Wait mana iman" munira tayi saurin dakatar da ita ganin kamar taji haushi
"Nifa ba abinda nake nufi kenan ba,ki fahimceni.....ina nufin yanzu budurwa kamarki,ai ya kamata a sakar miki mara a siya miki waya me kyau saboda gudun raini daga wajen tsararrakinki.....na tabbatar yana da kudin da zai iya siya miki babbar waya,ko yaya ne kaima kayi dan abun xamanin nan da kowa yakeyi" duban munira kawai take,tabbas ya al'ameen idan tace tana so zai siya matan,amma a hakan ma babu lallai su malam su yarda ba,sai tayi shuru bata sake cewa komai ba,saboda isowar wata 'yar ajinsu da tata wayar,tazo munira ta tuttura mata pics da wasu videos,da kadan kadan sai ga masu wayar suna zuwa,sunata sending ma junansu abunda kowa keson sawa a wayarsa.
Tana daga gefe tana kallonsu,kowacce wayar hannunta babbace,wata daga gidansu wata kuma saurayine ya siya mata,ba shakka tana bala'in son waya da maitarta,amma ba zata takura ya al'ameen din ya siya mata sama da wadda yace zai siya matan ba.
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 11________________
*_Huuuuuum! Idan kaji hanci a sama yayin gittawar mata ƴan ƙwalisa ko shiga gidajensu kasan maganar ta ƙamshi ce_*
*_Ina magana ne aka kayan ƙamshi ƴan gaske ba saka iska ta hure maka ba_*
*_Ina mata ƴan ƙwalisa ma'abota so da ƙaunar ingantattun haɗin turaruka ƴan gaske? To kuzo maza ga dama a tafin hanunku cikin sauƙi da sauƙaƙawa._*
*_Ana siyarda Turarukan Wuta na yan Maiduguri Set na amare. Ana bada sari kuma._*
*_Sannan akwai kayan gyaran jiki. Akwai zumar qiba result cikin 1 week. Turaren daki, jiki, kaya, tsuguno, humra, colacca, turaren wanka, mopping scents, air freshener._*
_Address Kano, Mariri Maiduguri Road. WhatsApp number 07068145252_.
*Sai kunzo🤳🏻*
___________________________________
Tare suka jero da muniran bayan an tashi kamar yadda suka saba,suna tafe suna dan hira munira na tsokanarta
"Nikam kullum aka tashi daga makaranta dalibai basa gajiya da kallonki iman?" Tsaki taja,itama abun yana damunta,don har ta yanke shawarar fara sanya niqabi
"Sai suyita ai,kamar kai dayane mutum,su ba bil'adama bane 'yan uwanka"
"Kin fita daban seriously,shi yasa kike shan kallo" munira ta fadi sanda take nufan wata mota ash jaye da hannun iman,dakatawa iman din tayi tana qoqarin kuma zame hanunta daga na munira
"Ina kuma zaki kaini ga hanyar titi?" Waiwayowa tayi tana dubanta,fuskarta dauke da murnushin nan
"Oops,sorry,na manta in gaya miki,me daukana ya dawo da daukata,dama shike maidani gida indai naje gidan uncle jibril,yawanci ina bin motar haya ne idan ina gidanmu" kai iman ta jinjina tana saita hanyarta zuwa titi
"To sai gobe,Allah yabamu alkhairi" da sauri tasha gabanta
"Ban gane ba,bayan ta hanyar unguwarku xamu wuce,ki shigo don Allah,yana da kirki,zai ajjiyeki unguwarku,cousin dina ne sadam,lokacin tashinmu lokacin ne shi kuma yake komawa gida cin abinci,shi yasa yaje biyowa ta nan ya daukeni mu wuce tare" kai iman ta jinjina
"A'ah fa,zanbi adaidaita kamar yadda na saba" dambu taliya ta kada iman amma taqi,har sau da na cikin motar ya fara mata horn,dole ta haqura tace da ita
"Shikenan,bani number wayar to"
"Idan kin kira amma kice ni kike nema,don ya al'amin ko inna cikinsu wani zai daga,saboda numbers dinsu ne" dariya munira ta saki
"Allah ya sawwaqe,yanzu inda saurayi kikayi haka zaki gaya masa kenan?"
"Ke kika sani,ni bani da wani saurayi ma" da wani mamakin take duban iman din,saidai ta share ta soma karanto mata digit's din tana lodawa a wayar tare sa serving,sukayi sallama tana jajata mata Allah yasa ta samu mota da wuri,saboda sadam ya gaya mata ana wuyar abun hawa yau din,sakamakon taadar da man fetur yayi,da yawa wasu masu ababen hawan sun haqura sun ajjiye abun hawan nasu a gida.
Ta samu tulin dalibai kuwa masu jiran abun hawa,haka nan tabi sahunsu itama,tana fatan su samu da wuri kodon ranar da ake dasawa.
Kusan duk motar da zatazo ta wuce a cike take,wata kuma kafin ta qarasa inda ta tsaya wasu sun shige sun cikata,tana nan a tsaye tsayin wasu mintuna ta hangi kamar gilmawar motarsu munira,sai kuma taga ta tsaya taja da baya ta dawo dab da ita
"Why not ki qyaleta....ba'a dole wajen taimako fa" sadam daya dan hada rai ya fadawa munira
"Qawatace,banason ganinta tana sha ranar nan,kayi haquri minti daya"
"Ok" ya amsa qasa qasa yana jona wayarsa a chargy,munira ta bude murfin motar ta fito ta nufi inda iman take.
Da farko musu taso ta sake mata,sai da taga muniran taji haushi,sannan kuma me motar ya fara buga musu horn sannan ta bita,sanyin ac ya ratsata sanda jikinta ya shige motar,ta maida murfin ta rufe sanda munira ke mita
"Haka kawai ki tsayar da kanki a wannan ranar babu gaira babu dalili,bayan ga abun hawa,ai tsaiwa a ranar nan sai dole"
"Ina yini" tayi qoqarin gaida matuqin motar ba tare data amsa mitar da munira ke mata ba
"Laf....lafiya qalau.... 'yammata" harshensa yadan sarqe,bayan idanunsa sun sauka a fuskar iman dake ciro jakar bayanta zuwa saman cinyarta ta glass din gaban motar,gabansa yadan fadi,ya zuba mata idanu na wasu sakanni ba tare daya iya dauke idonsa daga kanta ba,tunda yake bai taba ganin halittar mace da komai yaji.....ta kuma tafi da imaninsa irin wannan ba,wani irin kyau mai cika idanun me kallo,abinda yasa yadan daburce har ya qara mata da kalmar 'yammata kenan ba tare da ya sani ba,kalmar kuma data dan ja hankalin munira tabi sadam din da kallo,don tasan ba dabi'arsa bace hakan.
Haka kawai ya samu kansa cikin rashin nutsuwar da yake da tabbacin ya fada kogin soyayyar iman ne farat daya,ya dinga satar kallonta lokaci bayan lokaci,har sai da iman din ta ankara,ta kuma tsargu,tare da tuhumar kanta na meye xata shiga motar wasu,koda rana zata kasheta?,sai ya basar,ya fara soko musu hira,yana kuma jan iman din din
"Wanne layi zamu shiga?" Ya tambayi iman din kai tsaye,idanunsa na kanta ta cikin mirror
"Ya isa,anan ma zan sauka" ta fada tana sake gyara jakarta
"A'ah,ai da kin barmu mun cikasa ladanmu ko?" Ya fadi yana dan saki murmushi,munira ma ta saki nata tana gyada kai
"Aikuwa dai"
"A'ah na gode,babu nisa,zan qarasa da qafata" bai sake cewa komai ba ya fara qoqarin faka motar,sannan ya saka hannunsa a aljihun gaban motar ya budeshi,ya ciro wrapper din 'yan dari dari sababbi ya miqa munira
"Bata,tasa kati a waya"
"Ina taga waya,saidai tasha chocolate" munira ta fada cikin sigar zolayar iman tana miqa mata kudin.
Kememe iman taqi amsar kudin,saima ta soma takawa tayi gaba abinta tana cewa sai gobe
"Ni nasan ba zata karba ba,amma ka barni da ita,zan kai mata gobe" tace da sadam,saiya sauke ajiyar zuciya,cikin kasala ya tada motar
"Ban taba ganin yarinyar data yimun ba irin qawarkin nan ba,ki shigemin gaba don Allah na mallaketa" dariya munira ta saki
"Karka damu,indai zaka saki kudi duk ba zaya gagara ba"
"Mayyar kudi,bansan ina zakikai son kudi ba muni" dariya ta sake
"A'ah ya sadam,kudi fa abun sone,babu meson wahala ko talauci,ko aikin nan da kake yanzu ba kudin kake nema ba?". Murmushi yayi kawai,don yasan wajen magana badai a kada muniran ba,gaba daya shi yanzu hankalinsa ya tafi ga iman.
Koda washegari taje mata da kudin makaranta cewa tayi ba zata karba ba wallahi,harda qarin handset daya siya ya dora mata akai,kusan fada sukayi da iman din akan hakan,ita ta dage saita karba,dan uwanta ne,kuma babu dadi maida hannun kyauta baya,yayin da iman din tace sam batasan wannan zance ba,kawai daga haduwa da mutum sai ta karbi abun hannunsa?,tace waye ya bata ma a gida?. Wani kallo muniran tayi mata
"Au daman duk yammatan da samari ke musu kyauta nunawa suke a gida suce wanene ya basu?,kowacce boyewa take tayi amfani dasu abunta,ki karba kawai,don gaskiya bazan iya maida masa ba,don bansan bayanin da zanyi masa ba"
"Ki riqe na baki kyauta tunda ba zaki iya mayarwa ba"
"Bani ya bawa ba,amma zan ajjiyesu har zuwa randa zaki amsa" ta fada cikin bacin rai tana zuge handbag dinta ta jefasu ciki,zancan bikin qawayensu guda biyu dake matsowa da aka zauna yi shi ya raba gardamar,duk da haka muniran bata sauko ba.
Koda aka tashi tun daga bakin gate ta lura da motar jiya ce tazo daukan muniran saita zame ta gudu,ta canza hanya ta shiga motar haya tayi gida,washegari ta dinga mita da qorafi iman din tace da ita
"Kada ma ki soma batawa kanki rai,don Allah bazan sake shiga motar wani a gida baa sani ba" tasan da gaske take idan tayi magana,don haka bata sake cewa da ita komai ba,sai kumbure kumbure da take mata alamun tashi fushi,dariya ta saki
"Kyayi ma ki sauko" amsar da iman din ta bata kenan.
********. ******. ********
A nutse ya ajjiye almakashinsa saman keken da yake kai,sannan ya miqe ya nufo inda iman ke zaune saman wani stool tana fuskantarsa.
Ganin ya dosota saita dauke idanunta a hankali,ya saki qaramin murmushi da ya sake qawata fuskarsa,ya zauna saman wani keken dake daura da ita,ya dora qafarsa daya saman wata kujerar roba da babu kowa akai.
Shagon nasu yanzu babu kowa sai wani dan matashi guda daya daketa faman dinki,da alama masu kayan suna hanya ne,koma bayan sanda ta shigo din da yake cike da matasan,sunata shirin fita wata ball ta abokinsu,shi dinne yace ba zashi ba,don ba wani abokinsa bane na kusa,saboda dama ba mutum ne shi me tara abokai da yawa ba.
"Banfiyason zuwanki shagon nan ba,kina ganin dai yadda kullum yake cike da mutane" dan turo baki gaba tayi
"To ya alameen,idan ka dawo gida inna ba zata bari muyi magana bafa.......kuma lokaci yana qurewa,bikin gaba daya saura uku" idanu ya zubawa lips din da take turowar,kamar ya kama ya tsotse haka yakeji,saiya dauke idanun nasa yana tattara kansa waje guda
"Me yasa baki kirani a waya ba?" Saita fidda idanunta duka a kanshi
"Ka manta ne,inna ta hanani taba wayarta,tace ina qarar mata da kati"
"Haba da Allah haba,ya zaayi ace budurwa kamanki aron wayar inna kike?,ai kinfi qarfin haka,wani idan ya ganki zai zaci babbar iPhone ki manya manyan Huawei kike riqewa" ya fada da salon tsokana.
Kallon da al'ameen ya jefeshi dashi yasanya shi jan bakinsa yayi shuru,kafataninsu sunsan halinsa baya daukar wargi,hatta da ogansu me shagon wani lokaci kamar shakkar al'ameen din yake saboda kwarjinin da Allah ya zuba masa,uwa uba kuma mutum ne shi mai tsaiwa akan gaskiya,idan kaga ya dage kan abu,to idan akayi zuzzurfan bincike shine me gaskiya
"Bani mu gani" ya fada yana miqa mata hannu,sai tabi hannun nasa da kallo daya nannade hannun rigarsa zuwa gwiwar hannu saboda yaji dadin kallo,cike yake da gargasa da jijiyoyin da zasu shaidamaka cikin jikinsa a murde yake,kuma qaqqarfan namijin duniya ne.
Kunya ta kamata sanda ta miqa masa yankin atamfofin guda biyu taga ya janye hannunsa yana jan hannun rigarsa yana rufe hannayen nasa,idanunsa kuma na bisa fuskarta,da alama yaga kallon data bishi dashi kenan.
Murmushi ya saki sanda taja hijabinta ta kare fukarta,yana qoqari yaga ya gujewa duk wani abu da zai sanya taji wani abu tattare da ita,bayason ya raba mata hankali tun yanzu ko yayi cikakken wasa da hankalinta,saidai lokaci yana nan zuwa da zai mantar da ita kowa cikin duniya saishi kadai.
Tana miqa masa ta sauka daga kan kujerar don ba zata iya ci gaba da zama ba
"Qawata zata kawo dinki yaaya don Allah,kada kace aiki ya maka yawa"
"Karta damu,indai ta wajenki ta biyo"
"Saika dawo" ta fada tana masa sallama,bai amsa ba illa binta da yayi da kallo,kominta a nutse kuma a tsare Allah yayi mata shi,yana jin sara qiris ya fara tilastata sanya niqab,yana jin ciwo cikin qirjinsa da zuciyarsa duk sansa ta fita koda makaranta ne,yafi jin dadi da samun nutsuwa udan ya dawo gida ya sameta cikin gidan.
Wani irin shauqinta yakeji yana fusgarsa har ta bacewa idanunsa,ya sauke ajiyar zuciya yana sauka dubansa ga qyallen atamfofin data bashi,ya daga kai a hankali ya dubi matashin daketa aikinsa
"Yahaya......ka dubamin atamfar nan don Allah ka gaya min kudinsu gobe ko jibi"
"An gama" ya fada yana miqewa tare da miqa hannu ya karbesu.
*********. *******. ******
K'arfe hudu da minti ashirin da hudu wayar inna ta kada,iman data kai jug din data hadawa munira lemo kitchen ta dire da sauri ta dawo ta daga tana amsa kiran,munira ta tsammata,kuma ita dince,saita aje wayar tana jan babban hijabinta ta dora saman atamfar dake jikinta,wadda al'ameen ya zauna ya bata lokaci sosai ya tsara mata dinki na gani na fada
"Inna zan leqa waje na shigo da ita"
"Saikin dawo" inna dake zaune tana qoqarin gyara saitin radio dinta ta fada,tana son ta kamo freedom radio don jin shirin mu qyaqyata kafin biyar na yamma tayi. Slippers dinta ta zura ta tako zuwa soron gidansu.
Gab da zata fita shi kuma yana qoqarin shigowa,saura kadan suyi gware,taja da baya tana yarfe hannu tare da yamutsa fuska,abinda ya taimaka qwarai wajen fitowar dimple dinta duk sanda ta motsa fuskarta,yayin da shi kuma yaja da baya yana qare mata kallo.
Yana iya hangen yadda tayi wani kyau duk da cikin hijabi take,yana jin shi daya ne a duniya yake iya ganin kyanta koda cikin lullubi take,kuma a kanta kadai yake da wannan baiwar
"Ina zakije?"
"Qawata din nan da zata kawo maka dinki zan shigo da ita"
"Koma ciki" saiya koma da baya ya qwalawa daya daga cikin almajiran gidan kira,yace ya duba layin,idan yaga wata baquwa tana neman gidan nan ya shigo da ita,ya dawo ya zarce dakinsu sannan tuni iman ta kona ciki,duk da taso ya barta taje da kanta ta shigo da ita,saidai ba zata iya yi masa musu ba.
Ba jimawa saiga sallamar munira,iman ta fito da sauri,suka rungume juna cikin murna,kamar wadanda suka jima basuga junansu ba,kai tsaye suka fada dakin inna.
Cikin girmamawa ta gaida inna,innan ta amsa mata,sannan ta miqe ta fice zuwa dakin malam da tun daxu dama takeson shiga ta gyara masa kayan sawarsa ta barsu su biyu cikin rumfarta.
"Hajar ibrahim khalil" munira ta fadawa iman wadda keta qoqarin zuba mata lemo da abinci bayan ta qarewa falon nasu kallo
"Munira sulaiman"
"Yaudai gani a gidanku,naga randa zakizo nima namu gidan" hararta tayi cikin wasa
"Aiba zuwana kikayi ba,kawo dinki ne ya kawoki ko?"
"Eh duk da haka,inda hakanne ma ai da shagon zan tambaya nakai musu direct,da qyar mafa yaron da kika aika ya ganoni" ta fada tana daukan lemon takai bakinta
"Nazo fita mukaci karo da ya al'ameen,shi yace na koma ya tura sa'idu" ajjiye lemon tayi
"Yaudai zanga ya alameen da zancansa ya cika mana kunnuwa aka hanamu sakat,ya al'ameen din nan me shegen tsauri da takura,hala ku biyu inna ta haifa kawai" kai ta girgiza mata tana murmushi
"Mu uku ne,kawai yaya sadiq"
"Amma ban taba ji daga bakinki ba" zamanta fa gyara saman kujera
"Barshi wannan,bamu cika shiri dashi ba" dan dariya muniran tayi suka ci gaba da casa hirarsu,har ta soma bata labarin bikin wata cousin dinta da zasu fara,wanda tsiran kwana ukune dana qawarsu amina,wadda ta kawo dinkin ankonta yanzun.
Yadda taketa bawa iman labarin bikin da yadda aka tsara komai ya tabbatar mata tana matuqar ji da bikin,har ta zolayeta da haka
"Keee,ba dole ba,kinsan manyan mutanen da zasu halacci bikin?,inda naji dadi ana ya gobe dinner din amina zaayi kamu,ran dinner din amina ranar event din gidansu ango za'ayi ba namu bane,so babu lallai naje,washegari ne zaa tashi bikin gadan gadan"
"Wai ita aminan dinner zatayi?"
"Eh mana,wannan atamfar ai ita zaa saka ranar" tabe baki iman tayi,saboda ita duk wata harkar dinner ba zuwa take ba,bata damu da ita ba,koda ta damu dinma tasan ba dabi'ar gidan bace,babu me barinta
"To inajin babu ni a zuwan"
"Saboda me?,ya al'ameen zai hanaki ko?" Dariya ta kubcewa iman
"Au,sharri zaki masa?har kinyi tafsiri ma?" Itama tana dariyar ta amsa mata
"Eh to ai nasan qarshen zancan kenan,nidai badon yayanki bane Allah cewa zanyi da wata a qasa,wannan tsanani da boyo haka?,barima dai ya shigo inga ya yake ya alamin din" maganarta saita dan shigi iman,duk da haka tana dariya ta miqe
"Yama fa shigo gidan amma kin jishi shuru,bari na duba koya gama na masa magana" ta fada tana ficewa,ta manta bata dauki hijab din nata ba.
*LITTAFIN NAN NA KUDI NE,KI TUNTUBI WADAN NAN NUMBERS DIN DON BIYAN KUDIN NAKI*
09032345899
KO KUMA
09166221261
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 12
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
____________________________________
Tun daga bakin qofar dakin nasu qamshin turarensa ke karakaina,ya cika soron gaba daya,taja numfashi sosai ta sheqi qamshin,tana matuqar son qamshin turarensa,har yau kuma bata taba jin kowa da irinsa ba,babu abinda yake kashewa kudi sosai wajen siyansa irin turare.
Knocking tayi yace a shigo,ta tura qofar a hankali,idanunta suka sauka a kanshi,yana tsaye gaban mudubi yana ajjiye kwalbar turaren da ya gama fesawar yana qoqarin dora hula saman kanshi,yayi kyau cikin shadda ruwan makuba,dinkin zamani daya fidda samartaka sa zallar kyan da Allah ya bashi.
Ta cikin madubin ya kafeta da idanu,abunda bataso,sai ta kauda da kanta tana cewa
"Yaaya,ta iso tun dazu tana jiranka"
"Ganinan fitowa,wani waje zani na tsaya ne na shirya gaba daya kar na saba alqawari" ya fada yana daura agogon hannunsa,saita gaza tafiya yaci gaba da satar kallonsa har ya fuskanci haka,ta basar da sauri,sabida wani iri takeji da ganin kwalliyar da yayi din
"Yaa ina zaka da yammar nan" sai daya gama daura agogonsa tsaf sannan ya amsa
"Akwai wani da muka hadu da yace nakai takarduna,wala'alla idan da rabo zan samu scholarship,tunda suna da hanya"
"Allah yasa a dace" tayi masa addu'ar da har cikin ranta haka yake
"Ameen qanwata,na gode" tadanyi murmushi sannan ta miqe ta nufi hanyar waje.
Cikin tattausar muryarsa yayi sallama cikin falon,munira ta daga kanta daga danna wayarta da takeyi tana amsa sallamar
"Wow"bakinta ya motsa ta furta kalmar qasan zuciyarta,ta gyara zamanta sanda suke magana da iman
"Karbomin fura wajen inna" ta amsa da to sannan ta miqe ta fita zuwa wajen innar,dakin ya danyo shuru,saiya qarasa kujerar dake daga bakin qofa ya zauna a hannun kujerar.
Cikin fara'a gami da mutuntawa munira ta gaidashi,ya amsa kadaran kadaham,sanda iman din ta dawo da furar a cup ta miqa masa itama ta koma ta zauna.
Sai daya fara kurbar furar a hankali cike da nutsuwa sannan yace
"Muga kayan" saita dauka ledar ta aje masa a gabansa ta fidda kayan tana masa bayani,baice komai ba harta gama yana shan furarshi,sai data kammala dai dai sanda ya gama sha ya miqe da cup din a hannunsa
"Imani....ki dauka ki aje wajenki,idan zan fita jibi ki tunamin"
"To yaya" ta amsa masa sanda yake fita.
"Wow....wow,wannan shine ya al'ameen?,badan wani abu ba da na saka kai wallahi" harara iman ta balla mata
"Ba zaki yaudararmin yayana ba,saboda nasan baida kudin da zaki tsaidashi takara" dariya ta saki,tabbas abinda ke cikin zuciyarta kenan,saidai ba zata iya fitowa kai tsaye ta gayawa iman din ba,tako ina al'ameen yakai namiji,abu daya ya rageshi rashin 'ya'yan banki masu yawan gaske da zasu maisheshi wani,amma banda haka tabbas gawurtacce kuma isashen namiji ne.
"Yanzu haka maganar ci gaba da karatunsa ce ta futar dashi" iman tadan bata labari
"Allah sarki yayanmu,Allah ya bada sa'a"
"Ameen" iman ta amsa mata,daga haka suka fada wata hirar.
********. *******Tana daga zaune gefan katifar dake shimfide dakin iman,bayan ta karbi dinkunanta da sukayi kyau sosai wanda al'ameen din yayi mata,wayarta na hannunta tana ta danne danne,da yake gwana ce qwarai ita din wajen danna waya,shi yasa babu inda ke mata wahalar shiga loko da saqo na kowacce irin waya
"Kiyi sauri don Allah muje kada mu samu layi" munira tace da iman wadda ke shiryawa zasu wuce gidan qunshi,saboda gobe zaa fara bikin qawartasu
"Na gama ai,hijabi kawai xan saka" ta fada tana ware gogaggen hijabinta me kyau
"Kiwa Allah ki aje hijabin nan,wallahi wajen 'yan gayu ne sai kisa a dinga mana kallon tara saura kwata,ko kamar nawa mayafinne ki saka,tunda kinga dai babba ne,kuma bashi da shara shara" inan din ta buda baki zatayi magana munira ta dakatar da ita
"Nasan yanzu zaki kawo karatun ya Alameen,goben ma kenan haka zakiyi?" Murmushi kawai iman tayi,don kamar ta shiga zuciyartata,maganar al'ameen din ya hanata saka mayafai zatayi mata,saita aje hijabin,ta bude ma'ajiyar kayanta,ta ciro daga cikin sabbin lafayar da yagana ta bata,wata 'yar uwar mahaifinta har guda biyar masu azabar kyau da tsada.
"Kai kai kai,ke kinga kyan datayi miki kuwa,ma sha Alla,da ana musayar kyau Allah da tuni na karba naki na hadaki da nawa" munira ta fada cikin nuna santi da yabawa da kyan iman din tayi,wanda zahirin gaskiya gaskiya ta fada,wani kyau lafayan tayi mata,idan ka kalleta kamar ba zaka dauke ido ba,ita kanta dai data juya ta sake kallon kanta a madubi ta gasgata hakan.
Tana tsaka da sanya halfshoe dinta da ya alameen ya siya mata 6k wanda ya dace da lafayar jikinta wayarta da ya alameen din ya bata tecno ta dauki tsuwwa,munira ta kalli sashen da wayar take,ta tuntsire da dariya tana cewa
"Ana kiranki a rakani kashinki?' sai data manna mata harara sannan ta isa inda wayar take
"A haka nakeson kayata"
"Amma dai wallahi ba girmanki bane,dressing dinki sam bai kamaci wannan wayar ba" ta saba da jin wannan lafuzzan daga bakin muniran,don haka tayi banza da ita ta isa inda wayar take ta daga abunta.
Sai data gama wayar ta dubi muniran
"Su hamra ne,already wai suna wajen,har an fara yiwa wasu,mu kadane bama nan"
"Nasan zaa rina dama,munyi delay da yawa" munira ta fada tana daukar ledar kayanta.
Saida suka biya wajen inna,munira ta yiwa innan sallama da kuma godiya,ita kuma iman ta karbi kudin qunshin sannan suka fito suka wuce.
AMARYAR KB BEAUTY PARLOR,katafaren wajen gyaran amare da uwayen gidaje,yammata harma da zawara,waje ne na alfarma wanda ya kasance iya kudinka iya shagalinka,wajene daya amsa sunansa,duk sanda kaje haka zakaga manyan hajiyoyi suna karakaina,suna dukkan wani nau'in gyaran jiki da kuma kayan magunguna na gyaran jiki da aka warewa waje na musamman a ciki.
Amarya sakina itama iyayenta da danshinsu,hakanan wanda zata aura din shima ba baya bane,tun asali gidansu basu damu da karatun boko ba,kasuwanci sukafi bawa qarfi,don haka sanda miji ya fito mata ya kuma tabbatar musu zai siya mata dukkan wani certificate,basu wani jinkirta ba aka cireta daga karatun aka fara shirin auren nata.
Tun daga shigarsu wajen iman tasan waje ne na matan da suka isa,dukkaninsu qawaye ne,saidai bata wani saba can dasu kamar yadda suka shaqu da munira ba,don haka bayan 'yan caftarsu ta qawaye da murnar shigowarsu,sai ta samu waje saman kujerun da aka tanada a wajen tayi zamanta,tana sauraren hirarrakin dake tashi a wajen,da kuma shige da ficen 'yan gayu mazansu da matansu.
Hira suke irin ta matasan yammatan dakeji da tashen quruciya,dukkansu babu wadda ba daga babban gida ta fito ba,kusan ita daya ce ma kawai zaa ce iyayenta ba wasu masu kudi bane,saidai ita din ma shigarta fes take,kai bakace hakan ba.
Abu daya ne idan ka lura dashi zaka gane banbamcinsu,manya manyan wayoyin dake hannun kowaccensu,da kuma irin kudaden dake jakarsu,kowacce ta fito da tata tana harkar gabanta.
Mutum uku cikinsu saida samarinsu sukazo har qofar wajen suka basu kudin lallaen da gyaran gashi,kowanne cikin babbar mota,hakan kudin da suka basu sababbin ne a rafarsu.
Kafin zuwan nasu suka saka gasa,duk wadda kudin da aka bata yafi na sauran yawa ita zaa fara yiwa,daga qarshe fahima ita ta cinye,dole ita aka saka za'a bari a fara yiwa.
Ita dai nata idanu,sai wata matashiya dake kusa da ita wadda batafi sa'arsu ba da aka sawa lalle,tun dazu ake kiranta babu me daga mata,don haka iman din ta matsa kusa da ita
"Bari na daga miki"
"Yauwa na gode" ta fada a yagance tana murmushin jin dadin hakan da iman din tayi mata,ta riqe wayar da kafadarta ta fara amsa kiran,murya can qasa,wanda da alamu saurayinta ne ya kira,don sunyi doguwar waya sosai,har aka gama yiwa amarya sakina qunshinta da qawarta da sukazo tare,ango yazo daukarta,dukka suka tashi mata takiya,munira na cewa sai sunje sun gaisa.
Ko alamar motsawa iman batayi ba,amma munira ta finciki hannunta,dole ta bisu.
Yana jingine jikin fara qal din motarsu,wadda da alama sabuwa ce,su biyune shida wani matashin saurayin kamarsa,cikin fara'a da barkwanci irin na angwaye da qawayen amarya,tana tsaye daga gefe tana kallonsu,don ita komai ma sabo ne a wajenta,saboda wannan shine karonta na farko na bikin qawa a waje,ko cikin dangi ma ba kasafai take zuwa ba saboda nisa da suka dan mata,daga na uwa har na uban,sai dai daiku dake nan garin da suke.
Kowa cikinsu ta fara gabatar masa da kanta da kuma sunanta,har aka gama,munira ta waiwayo
"Matso mana iman" abinda yaja hankalin angon da abokin nasa kenan"
Idanu abokin ya zuba mata sosai,ya furta
"Subhanallah" har zuwa sanda ta iso idanunsa yana kanta
"Itama cikin qawayenku take?" Saurayin me suna hashim ya tambaya bayan ta gama gaidasu
"Eh....iman,ba kasafai ta fiya son shiga jama'a ba ai"
"That's good" ya fada yana gyada kai,still ita yake kallo,abinda yasa ta takura kenan,taja da baya tana fadin
"Bari naje kafin ku gama,kada azo kanmu babu kowa"
"Wait iman....ki tsaya ki karba kudin liqi mana" kafada ta daga
"A'ah,na gode sosai wallahi" daga hakata qara sauri tayi ciki tana mita cikin ranta,gaba daya batasan me yasa mazan yanzu suke da shegen kallo ba.
Basu jima sosai ba suka dawo,sauran su uku kenan da suka rage ba'a yiwa ba
"Haba iman.....haba da Allah,me yasa kike abu kamar baki waye bane,ke dan samarin nan ma na yayi da akeyi ki kasa yi,guy iya haduwa amma ki yarfashi ki taho,ke kinga yadda ya rude da zancanki bayan kin taho,Allah annabi a hadaki dashi?,at last dai dole muka bashi number dinki" idanunta ta zaro
"Me yasa zaku bashi don Allah,me yasa zakuyimin haka?" Ta fada adan rude,dukkaninsu suka sanya dariya
"Seriously da gaske nake,yanzu me zance da ya al'ameen idan yaga wani ya kirani?"
"Waima.....wai.ya al'ameen,to meye a ciki?,shi kansa yasan kin isa a kirakin,waima idan bai bari an kirakin ba,jiqaki zaiyi yasha?,a yadda Allah ya halicceki iman saidai idan ba zaki dinga fita ba a gida zaki boye kanki" munira ta qarashe bayanan suka kuma goyi bayanta
"Gaskiya kam,koni da za'a bani dama yaya na zan yiwa kamu" budurwar da ta taimaka mata dazu ta sanya baki a hirarsu,kowa ya sanya dariya.
Ko a jikin munira ta qara gaba ta cire dan kwalinta don a fara yi mata gyaran gashi,yayin da iman ta dinga binta da harara tana gasa mata ita.
Daidai sanda aka gama musu wayar muniran ta dauki tsuwwa,ta daga da hanzari
"Ina zuwa.....Allah bazanyi missing ba,gani nan zuwa" shine abinda muniran ta fada tana maida wayarta jaka
"Don Allah don annabi qawalli ki rakani kamun nan,ban zaci abun haka aka shiryashi ba sai yanzu da batula ta kirani,ba zamu jima ba in sha Allah zamu taho,kinga hanya daya zamuyi,gida zan koma zan debo kayana,sai gobe zan wuce gaba daya" da farko uzuri ta bata kan yamma tayi sosai,kafin suje ma magariba tayi,kuma malam yana fada idan tayi dare a waje,haka ya al'ameen,da qyar munira tasha kanta,tace zata rakata har gida ta yiwa inna bayani,zannan ta aminta,nan cikin kayan data amso dinki ta zabi daya daga ciki ta sauya,ta kuma biya aka mata lite makeup,tayi tayi iman ta dauki wani a ciki itama ta sauya tace aa,kayan jikinta sun isheta.
Tun daga shigansu wajen iman ta tabbatar lallai bikine na manya,wadanda sukaci suka tada kai,wani mahaukacin gida ne mai dauki da tafkekiyar haraba,wanda ama qawata ta da decorations irin na biki,duk yawan jama'ar dake wajen ta daukesu tsaf,harda ragowar sararin da motocin gidan ke fake abinsu basusan anayi bama.
Tunda suka shiga din iman ta samu seat ta zauna,daga inda take din tana iya hango yadda komai ke wakana,amarya tayi kyau iya kyau tare da angonta,sai gudanar da komai ake cikin fariya boko da kuma nuna wadata.
A hankali ta daga kanta ta kalli yadda sama ta fara duhu,alamu suna nuna anyi kira sallar magariba zuwa yanzu,duk da bata iya jiyo kiran ba saboda tashin kidan daya karade wajen. Kome take kuma ko a ina take bata wasa da salla,haka aka tarbiyyantar da ita,don haka ta laluba wayarta ta fara kiran munira babu qaqqautawa,wanda sai a kira na biyar ta samu ta daga,tace mata gatanan zuwa,ba jimawa kuwa sai gata,da alamu biki yayi biki
"Nifa zan wucw gida gaskiya,gashi har anyi sallah mu bamuyi ba"
"Don Allah ki bani minti goma kacal,ummi ce zata bani saqo na tafi dashi" mahafiyace,ba zata iyace mata karsu jira ba,saita rausaya kai
"Idan na koma gida malam ya koroni kyasan inda zakiyi dani,kaini wani wajen nayi sallah" dariya ta saki
"Ba korokin da zaiyi,ya kori auta ai babu wannan maganar,muje na rakaki" tare suka jera da ita,saidai duk inda suka gifta sai an kalli iman din,yawanci kallo ne na baqunta da kuma tsarin surar da Allah yayi mata,wadda ta fita daban data sauran mata.
Ganin yadda hanyar shiga gidan ke cike da mutane sai iman din ta dakata da bin munira
"Gaskiya ki samarmin wani gurin inda zan kebe ni kadai nayi sallata,cikin gidan nan da alama a cike yake,kuma ni babu wanda na sani" tayi qoqarin nuna mata babu komai ta shiga amma tace a'ah,don haka ta jata can bayan gidan,inda garden din gidan yake,wanda ke wadace da grass carpet,da kuma famfunan da ake bawa lambun ruwa
"Yauwa,yanzu naji daidai" iman din ta fada tana ware idanunta cikin wajen saboa yadda ya birgeta,wata iska ta daban wajen yake fitarwa,bugu da qari shuru yake kamar ba cikin gidan dake cike da hayaniyar biki yake ba
"Ki kirani idan kin gama saimi wuce,ni hutun sallah nake"
"Baki da matsala,amma dana gama zazu zamuyi gida"
"In sha Allahu" ta fada tana juyawa da sauri zuwa ciki,iman ta bita da kallo,cikin ranta tana mamakin yadda muniran ke bala'in son alaqa da masu kudi,take kuma qaunar bikinsu,saita dage kafada,qila don ta taso taga haka danginsu yake.
A hankali take takawa zuwa wajen wani famfo daketa zuba shi kadai yana aika ruwa zuwa sasannin shuke shuken dake fadin lambun,ta tsaya a gabansa cikin nutsuwa,ta waiga ta tabbatar babu kowa,sai ta fara ware lafayar dake jikinta don kada ta jiqe,ta ajjiyeta gefe,ta daura alwalar,sannan ta dauketa ta yafata a matsayin mayafi kawai ta tada sallarta,sai data idar sannan ta miqe,ta zameta daga kanta ta fara daura abarta a jikinta.
Sau uku tana nadata tana jin batayi mata dai dai a jikinta ba,karo na hudu taja tsaki ta fara warewa da xummar sake daurawa
"Kawo na tayaki tunda kin kasa" sautin muryar daya daki dodon kunnenta kenan wanda ya razanata,ta kuma rude gaba daya,ta damqe lafayar tata da hannayenta gaba daya,a kuma matuqar tsorace sannan a razane ta waiwaya don ganin waye?,daga ina kuma ya shigo ko ya fito?.
*ZAFAFA BIYAR*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*13
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
____________________________________
Matashin saurayi ne tsaye a bayanta,fari qal,wanda har wani yellow yake saboda haske,ma'abocin kyau na gaske,wanda fuskarsa ta cika da baqin gemu da kuma sumar kai,ba siriri bane kamar yadda yake ba mai qiba ba,jajayen lips dinsa dauke suke da murmushin da ya bayyana fararen haqoransa,yana sanye da wata muguwar shadda daketa faman zuba qyalli da maiqo,ruwan hanta wanda ta dace da fatarsa da kuma fitar da kyansa muraran,hannayensa na goye qirjinsa,wanda hakan ya bayyana muqullin motar dake soke cikin daya daga cikin 'yan yatsunsa.
Tsoro ya sanya ta sake ja da baya ganin yadda yake ci gaba da kallonta,murmushi shimfide saman fuskarsa,cikin wata murya mai zaqi ya sake cewa
"Gashi nadin yayi miki kyau sosai da sosai,saidai kuma kuma baki iya daurawa ba,halan mama ce ta daura miki kafin ki fito?" Rasa amsar bashi tayi sai idanu da take rarrabawa
"Wannan auta ce da alama" ya sake fada yana komawa da baya a hankali ya zauna saman kujerar concrete dake wajen,har yanzu bai janye idanuwansa daga kanta ba,hakanan murmushin da yakeyi baibar kan fuskarsa ba
"Iman.....iman" sautin muryar munira ya fara shigowa wajen,da alama ita take nema
"Uhunnn.....da alama ke suke nema,abokan tafiyarki ne ko?" Ba tare daya jira amsarta ba ya dora
"ki daura abarki,lemme close my eyes" ya fada yana lumshe qananun kyawawan idanunsa.
Ta tabbatarwa kanta ba zata iya fita a haka ba,saboda al'ummar dake harabar wajen sun ninka shi a yawa,saita leqa a hankali,ta tabbatar da gaske idanunta a rufen suke,don haka cikin sauri ta fara daurawa.
"Are you finished......an min izini na bude idanuna?" Ya fada a tausashe
"Eh" ta amsa cikin sanyi,ya bude idanun nasa tarwai saman fuskarta
"Wow.....wow I didn't realize yadda ta miki kyau kamar yanzu da nake kusa dake, please ke wanne yare ce?......i think kanuri ne suke amfani da ita ko?" Yadda yayi maganar har saman fuskarsa ya nuna da gaske so yake ya sani,don haka ta gyada kai
"Eh sune"
"It means ke din kanuri ne?" Kafin tace komai munira ta iskota
"Canza waje kikayi kenan inata bul......" Maganarta fa maqale a maqoshi sanda idanunta suka sauka a kansa,saita rusuna da sauri cikin girmamawa
"Yallabai barka da yamma" cikin wata dakiya wadda bada ita yanzu yanzu suke magana da iman ba yace
"Barka" kafin wani a cikinsu ya sake magana wata muryar ta sake cika wajen da kiran sunan
"Bassam.......bassam"
"Hey guys.....wannan kiran fa?" Ya fada yana daga sautun muryarsa dake da zaqi,wanda har sai da iman tadan sake kallonshi.
Mutum biyune suka qaraso wajen,dukkansu samari ne da kana musu kallo daya zakasan sunaji da jini da ajiki da kuma tashen samartaka,kowannensu kalar shigar dake jikinsa zata fallasa maka wadatar da yake ciki
"Shege....baka da mutunci wallahi,na dauka da gasken kayi tafiyarka" daya daga cikinsu ya fada yana cika yana batsewa,tare da jifansa da harara,baki ya tabe kamar yadda mata kanyi
"Gab nake da tafiyan ai,rabo yasa na ratso ta nan" yayi maganar kansa tsaye yana nuna iman da yatsan hannunsa,dukka suka waiwaya suna kallonta,abinda ya sanyata gaba daya taji ta tsargu ta kuma takura,
"Rabon samun matar aure" kamar saukar tsawa iman taji maganar,wanne irin magana ce wannan yakeyi,bayan har yanzu basu zarce mintuna ashirin da fara ganin juna cikin rayuwarsu ba,batasanshi ba bai santa ba,har yanzu ko kalma daya tak bata furta gareshi ba,saita rutsashi da kallon mamaki,ganin haka shima ya tsareta da nasa kallon tare da murmushi mai qawatarwa
"Yes,da gaske nake" ya tabbatar mata yana lumshe idanunsa tare da budesu a lokaci guda
"Muni......qawarki ce?" Daya daga cikin wandanda suka shigo wajen ya tambaya,cikin murmushi tare da madaukakin farincikin da muniran keta qoqarin dannewa tace
"Eh yaya ahlan,aminiyata ce......"
"Zaku iya bamu waje mu tattauna?" Matashin da aka kira da bassam ya fada still bai iya dauke dubansa daga kan iman ba,sai ahalan din yaja da baya
"Baka da matsala,but kada ka dade da yawa"
"Alright" ya amsa a taqaice,dukkaninsu sai suka juya suka fara barin wajen,yayin da iman ta bisu da kallo cikin taraddadi,tamkar ta bisu amma ta gaza daga qafarta daga wajen.
"Have a seat please" ta tsinci muryarsa yana tsaye daga bayanta kamar wani bodyguard da uban gidansa,ya tashi daga mazauninsa ya bata daman zama,bata da abun cewa illa qarasawa da tayi,a hankali ta zauna kamar yadda ya buqata,saidai bata wani saki jikinta ba kamar wadda ke dosane saman garwashin wuta.
Qarasowa yayi a hankali,ya shimfida handkerchief a gabanta qasa saman grass carpet din yayi xaman dirshan,tazarar dake tsakaninsu ba me nisa bace,saidai bai kusantota da yawa ba,ya aza mata dukka idanunsa sannan ya fara magana da ita.
"sunana bassam balarabe madaki....." Kai tadan daga kadan ta kalleshi,kamar tasan sunan,kamar tana dan jinsa cikin kafafen yada labarai
"Nine da na uku a wajen mahaifina,da na farko a wajen mummy na,shekarata ashirin da da takwas,'yan kasuwane mu duk da muna karatun boko me zurfi,hasalima nine jagoran dukka kamfanonin madaki general enterprises,ban taba aure ba,saidai for now zan sanya damba,domin kuwa naga matar aure,sai kuma inda qarfina ya qare,ki daga kanki ki kalleni da kyau kiga nayi miki ko banyi miki ba,saboda ni din mutum ne kaifi daya,banason boye boye kuma ban iyasa ba....."shuru ne ya ratsa tsakani,bata ko motsa ba bare ta daga kai ta kalleshi,sai wani bugu da zuciyarta keta famanyi,saboda tsayin rayuwarta bata taba tsaiwa da wani da sunan saurayi ko soyayya ba saishi.
Duk yadda yayi kan ta dubeshi ko tace wani abu taqi,har wayarta ta dauki tsuwwa,sunan inna ya bayyana,abinda ya sanyata miqewa zumbur kenan
"Innata ke kira,tun daxu muka fito,kuma tacemin kada nakai dare a waje" tayi masa bayanin tana qoqarin bin bayan kiran inna daya katse.
Wayar ya zubawa idanu har zuwa sanda kiran ya shiga,a dan rude takewa innar bayanin gata nan a hanya,bata saurareta ba sai fada da taketa tsula mata kamar xata rufeta da duka ta cikin wayar,dai dai sannan munira ta sake shigowa.
"Kije xan rakota zamu fito" amsar daya hawa munira kenan,saidai kafin ya miqe iman har tabi bayan munira,cikin azama ya cimmata suka jero.
Sai gaba daya ta duburce saboda yadda idanuwa suka dinga yawo a kansu,suka dinga jan hankalin mutane,ta lura sam ko a jikin bassam,sai hira da yake janta dashi cikin lanqwashashiyar murya,idanuwansa a kanta duk bayan sakan uku zuwa biyar,har suka qaraso parking lot na gidan.
Milk color din wata jibgegiyar mota ya bude mata yana fadin
"Bismillah" baya taja,idanunta na nuna alamu na tsoro
"Xan qarasa titi nahau napep" waiwayawa yayi ya kallo munira
"Ke baki gaya mata anguwarnan ba'a samun abun hawa na haya ba?"
"Bata sani ba" munira ta amsa masa cikin wani salo na yauqi irin na 'yammatan da suke ji da kansu
"Ok,muje na fitar dake titi a motar,amma bisa sharadi daya......idan ba'a samu abun hawa ba,zan kaiki unguwarku" a jikinta takeji zaa samu,don haka tace masa ta yarda,saiya gyada kai yana murmushi
"Allah kasa nayi winning", ya fadi harda daga hannayensa sama,tadan dauke kai kadan yana son bata dariya ganin yadda ya haqiqance bilhaqqi.
Wani sassanyan qamshi ke tashi cikin motar,ko ba'a gaya maka ba kasan turaren da yake amfani dashine ya hadu da qamshin freshener na mota da kuma sanyin ac ya bada wani yanayi me mugun dadi,tun daga waje dama zakasan motar sabuwa ce,cikin motar kuma shi xai qara tabbatar maka da hakan.
Addu'ar bassam itace taci kuwa,don sun jima suna tsumayin samun abun hawa saidai babu shi,dole hakanan tana ji tana gani suka dauki hanya zuwa unguwarsu,zuciyarta ta dinga bugun uku uku,ranta cike fal da tsoro da kuma fargabar kada ta hadu da wani dan gida.
Tunda suka soma tafiya yake janta da hira,cike da nuna tsantsar kulawa da wani salo dake nuna zallar shauqi,baiji kunya ko nauyin ganin idanuwan munira ba ya dinga fayyace mata zuciyarsa,kalamansa suka dinga yi mata nauyi aka,har kunya tasa ko cikakken motsi ta kasa,karo na farko da wani ya zauna yana shirya wasu manyan kalamai wai duk don saboda ita,ta yadda lallai kamar yadda ya gaya maya ne,shi din bashi da boye boye ko kuma rufa rufa,a haka har suka iso dab da layinsu,tasa ya ajjiyeta daga baya baya.
Har tasa hannu zata buda murfin motar da hanzarinta,ya danna mata Lock
"Ya zaki tafi ki barni haka?,babu gamsashshiyar amsa,sannan kuma babu madafa,so koke gobe ayi jana'izata?"
"Me kake buqata?"
"Phone number dinki" ya amsa mata kai tsaye,so take ya barta ta wuce don haka ta fara karanta masa yana serving,duk da haka bai barta ba har sai daya kira yaji ta shiga sannan yace
"Thank God" ya furta yana fitowa shima da sauri dava motar,ya zagayo inda take ya bude mata cikin girmamawa.
Waiwayowa tayi ganin ya fara take mata baya yana biye da ita kamar wani bodyguard,ta buda baki zatayi magana,ya ritsata da kallon nan nasa
"Tattaki zan miki angel...."ya amsa mata tambayarta tun batakai ga yinta ba
"A'ah,don Allah ka bari,wallahi na gode,zan qarasa,munira zata rakani" hannayensa ya sanya ya rufe fuskarsa kadan yana furzar da iska
"Banso kika dakatar dani ba....but,ba yadda zanyi,abinda zuciyarki keso ya zama kamar umarni ne a gareni.....munira" ya kira sunan muniran da tayi mutuwar tsaye a gefe
"Ki kulamin da ita,har ku isa gida banaso ku quda ya tabata.....deal" tunda ya fadi hakan tasan me yake nufi,ko banza yau za'ayi mata yayyafin kudi,tasan a zaune take wannan,haka suka jera da iman din zuwa cikin layinsu,bassam ya bita da idanu,yana jin kamar ya hadiyeta,wani wawan kamu soyayyarta tayi ma zuciyarsa,irin kamun da ba'a taba yi mata irinsa ba,bayajin zai iya haqura da yarinyar ba tare da ya mallaketa ba.
*ZAFAFA BIYAR*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 14
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
_____________________________________
Cikin wani irin zumudi da zakwadi munira tayi hanzarin kamo iman suka jera
"La'ilaha illallahu,wallahi kin cika 'yar baiwa iman.....dama ni jikina yana bani ke matar manya ce,da alama ke zaki zama tararuwar gidanku.....iman,kinsan kuwa waye bassam a karan kanshi kafin akai ga mahaifinsa?,kinsan yammatan dake layi da kai kawon kama qafa dashi?,bakya amfani da social medias ne,amma da basai na gaya miki waye bassam ba" hankalinta duka yayi gida,saidai tana saurara gami da fahimtar kowacce magana ta muniran ke magana akai
"To sai akayi yaya?"
"Don girman Allah kada kiyi mana baqulu da baqinciki,don wallahi bake kadai ba,hatta ni na warke,na kuma sake zama babbar yarinya,don Allah kada ki qauron baki,kada kice baki sonshi,saboda bassam irin mazan da kowacce mace ke buri da qauna ce" munira ta fada tana marairaicewa
"Nifa tsaya kiji,na yiwa ya al'ameen alqawarin bazanyi soyayya da kowa ba" idanu munira ta fitar kafin ta maidasu
"Kamar yaya?"
"Eh,yace idan lokaci yayi zai fitarmin da miji" dariya ta saki sosai cikin nishadi
"Dalla can,ashe ke baki da wayo,ya fadi hakane fa a sannan saboda qananun shekarunki,kada farinjinin da kike dashi maza suyi amfani da kya da kike dashi su yaudareki,amm kawo yanzu ai kinkai munxalin fara zance ma,tunda dukkanmu zance muke,ga wasu ma an fara aurarwa,koshi yaga bassam zai miki sha'awarsa,zai kuma so ya zama surukin gidanku" kai iman ta kada
"Duk abinda ya al'ameen ya fada yana nufin abinda ya fada din"
"Ikon Allah,nifa ban ganewa wannan dagiyar ta ya al'ameen ba,banda yayanki ne ai da sai nace ko kansa yakewa tanadi ne?" Waiwayawa kawai tayi ta kalli muniran,saita dauke taci gaba da tafiya batace komai ba,kunnuwanta na sauraren magiyar muniran kan kada ta tankwabar da soyayyar bassam kamar yadda ta yiwa dan uwata sadam
"Ke kamar bakisan rayuwa ba iman,wasu har rubutu da maganin farinjinin samun mai kudi ake musu,ke kuma kin samu daga Allah amma zaki wofantar da damarki,ki godewa Allah wallahi,koda bakison sadam ko qawance kukayi wallahi saikin tserewa sa'a a cikin dangi da qawayenki,saikin wuce kallon raini,ke ba zakisan haka ba,amma ni naga abubuwa da dama kuma ina kan gani cikin dangin umma na,saboda mahaifina ba kowa bane,mahaifiyata tana auren mutumin da ba wani ba" wannan hirar ita ta kaisu ga qofar gidansu iman,wanda babu mutane sosai,sai dai daikun daliban malam da suka dawo daga gurare daban daban akayo gida kuma,wasu na cin abincinsu na dare wasu na hira,saboda yau din ba ranar karatu bace,uwa ba kuma alamu na nuna malam din baya kusa ma.
Kallon da inna ta watsa mata sanda ta shiga shi ya sanyata ta shiga taitayinta,munira ta qaraso ta rusuna gaban inna
"Don Allah inna kiyi haquri,wallahi gidan qanwar umma ta rakani,ummance kuma ta tsaidani zamu amshi saqo mu taho mata dashi,don Allah inna kiyi haquri,laifina ne"
"Allah ya tsare gaba,amma ku kiyaye,kada ku bari ku dinga yin dare a waje,'ya'ya mata ne ku"
"In sha Allahu inna,ayi haquri,na gode" munira ta fada tana miqewa,suka qarasa dakin iman din
"Don Allah qawa na roqeki,nasan zai kiraki,koda baki sonshi ki tsaya ki saureshi a rabu lafiya" munira tace da iman cikin lallabawa sannan ya fito bayan sunyi sallama.
Kayan jikinta ta fara cirewa ta sanya na zaman gida,sannan ta daura alwalar sallar isha'i,ta dawo dakinta ta tayar,data idar tayi zaune saman abun sallar,tana jin gajiya na nuqurqusarta,ta daga kai ta dubi agogo,bataji duriyar alameen ba,da alama bai dawo bane,da tuni ya nemeta.
Idanunta suka sauka kan ledar da munira ta ajjiye mata me kayan takeaway na bikin data hadota dasu,ta janyo ta bude ta gani,su souvenir's ne kala kala harda na banza da rashin sanin ciwon kudi,sai kuma kayan ciye ciye.
Jakarta ta zaro cikin kayan ta bude don ciro wayarta,hannunta ya sauka kan wasu abubuwa,ta zazzagesu da hanzarinta. Sabbin kudade ne fil a miqe,yan 200 bandir guda,idanu ta fiddo waje cikin tsoro da mamakin yadda akai kudin suka samu,sai kuma tayi tunanin na munira ne,tunda jakar na hannunta,don haka ta dauki wayarta ta cire lock din ta fara qaqarin nemanta,saita ga alamun tex,ta buda don duba daga ina yake.
Ta zaci daga kamfanin mtn ne,don su kadai ke tura mata saqo,saidai a yau din akasin hakanne,don kuwa wata tsararriyar number ce dauke da wani zazzafan saqo,wanda ke cike da wasu shiryayyu kuma tsararrun kalamai dake nuna zallar shauqin soyayya da ma'abocin saqon ya tsinci kansa a ciki.
Sau uku tana karanta saqon tana komawa farko,sai daga qarshe idanunta suka kai kan sunan bassam,ta maimaita sunan sannan ta goge saqon da sauri,zuciyarta na bugawa,ta fita ta kira munira
"Kinyi mantuwar kudinki cikin jakata fa"
"Ba nawa bane,naki ne,bassam yace a baki" kicin kicin tayi da ranta
"Amma me yasa zayimin haka?,kinsan dai bana karbar kudin kowa ko?ko sadam da yake dan uwanki ban karbi kudinsa ba kin sani,bare wannan da bansan kowa nasa ba"
"iman.....wai me yasa kike haka ne?,kinsan dai babu kyau maida hannun kyauta baya ko?,ya zaa dinga miki alkhairi kina qin karba?"
"Na karba idan an gani a gida nace me?"
"Dama ni bance ki nuna ba,idan kinsan za'ayimiki fada ki ajjiye abinki ki dinga zara kina amfani dashi"
"Banaso munira,kizo kawai ki karba abinda ki maida masa" dariya taji ta qyalqyale dashi
"Toni ina zan ganshi yanzu?,bayan kin fita daga motar naji yana waya,a taqaice dai a abuja zai kwana ba'a kano ba,sannan na riga da nayi masa alqawarin zame masa jagora wajen samunki,kinga idan kina tsoro ma kina iya bashi dama yazo gida yaga malam......hakan zaisa kuyi tarayyarku babu tsoro ko shakku,kiyi amfani da kudinki kawai malama,sai da safe" munira ta katse wayarta abunta ta barta da waya a hannu.
Karar shigowar kira ya sanyata zabura,saura kadan wayar ta subuce a hannunta,tayi qoqarin saka wayar a silent sannan ta nutsu ta duba me kiran,idan har idanunta dai dai suke nuna mata number dazu ce data tura mata saqo,saita samu kanta da latsa ok,ta kara wayar a kunneta.
Zazzaqar muryarsa ce ta fara dukan kunnenta,a hankali ta amsa masa sallamarsa
"Kin tafi kin barni da kewarki,inajin kamar ba awannin da suka shude bane muka rabu,kamar wasu shekaru ne suka raba tsakaninmu....." Yayi maganar cikin salon iya jan hankalin diya mace,da kuma zallar qwarewa wajen sace zuciyar diya mace
"Don Alla kice wani abu kafin zuciyata ta fashe imani......zuciyata ta kamu da mahaukacin sonki,wanda har ta fara hasashen yadda rayuwa zata kasance mata babu ke". Wata ajiyar zuciya cw ta subuce mata saboda nauyi da kalamansa suka fara yiwa zuciyarta
"Me zance maka to?" Ta samu kanta da furtawa
"Koda bakice komai ba ki saki jiki ki bani dama,don koda baki fada ba na samu labarin nine mutum na farko da zan fara bude zuciyarki,so inason ayimin alfarma a kuma bani dama,nayi dashe me kyau,wanda zai bada kyakkyawar yabanya......don Allah beauty" ya qarashe maganar cikin marairaicewa.
Murmushi mara sauti ya subucewa fuskarta,ashe itama watace,ashe takai a gaya mata kalamai har haka anema soyayyarta,itama ashe takai,kalaman baqine ga kunnenta,saboda haka nan da nan ta sake ta bashi kunnuwanta,yayi amfani da wannan damar ya dinga mata hira me matuqar dadi,yana kodata gami da yabata takowanne fanni,tare da kuranta matsayin data samu cikin 'yan daqiqu,da kuma yadda zuciyarsa ta mato mata.
Kiran sunanta da taji inna nayi daga tsakar gida ya dawo da ita daga nisan kiwon da tayi,cikin hanzari ta katse wayar,ta kuma kasheta gaba daya ta tura qasan filo,cikin yanayi rashin gaskiya ta kwasa ta yiwo waje da sauri ta tsaya kan inna
"Gani inna" kallo ta bita dashi a nutse kafin daga bisani tace
"Me kika shiga daki tun dazu kika zauna kinayi ko abincinki baki dauka ba?"
"Sallah nake inna?"
"Qara'insu kikeyi?" Da sauri ta girgiza kai
"A'ah inna,isha'i ce kawai,gajiya tasa dana gama nadan kwanta,kinsan munsha zaman lalle"
"Yayanki ya shigo,bakiji shigowarsa ba?" Tayi mamaki,don har ga Allah bataji shigowar tasa ba da gaske,karo na farko da irin hakan ta faru,don babu wani abu dake shagaltar da ita ta kasa jin shigowar al'ameen din
"Banji ba inna,gyangyadi ya saceni" ta fada tana istigfarin qaryar data sharara
"Dauki abincinsu kikai musu,daga nan ki cewa sadiqu yazo ina kiransa"
"To inna" ta fada tana daukar babban farantin kayan abincinsu tayi dakin.
Kamar ko yaushe sai data tsaya tayi sallama aka bata izini sannan ta cusa kai,dashi idanunta suka fara karo,hannunsa riqe da wayarsa yana kallon wasu styles na dogayen riguna daya dora a account dinsa na Instagram,wanda bai jima da budeshi ba bisa shawarar sadiqu.
Sexy eyes dinsa da suka sake lumshewa saboda gajiya da yunwa ya buda a hankali ya sauke a kanta,ta qaraso a nutse ta ajjiye farantin
"Sannu da zuwa yaya"
"Yauwa queen.....ya gida?"
"Lafiya lau yaya,ya aiki"
"Alhmdlh,zubamin abincin" ya fada yana zamowa daga saman kujerar zuwa qasa,hankalinsa akan lallenta baqi da ja wanda yayi masifar zanuwa saman farar fatarta me haske sosai
"qunshin yayi kyau sosai queen" ya samu kansa da fadi sanda take qoqarin zuba masa abincin,saita daga kai suka hada idanu,cikin jin nauyinsa tace
"Na gode yaya"
"Amma garin yaya kikayi dare haka?" Dan raurau tayi da fuskarta
"Allah yaya munira na raka wajen event din cousin dinta,kuma ta yiwa inna bayani"
"Ki kiyaye please,kinga ke Queen ce,bai kamata sarauniya guda a dinga ganinta a araha a waje ba har dare" murmushi ya sake subuce mata,ta gyada kai tana murza yatsun hannunta,daidai sannan sadiqu ya fito daga bandaki
"Zubamin nima ina zuwa,abu me sanyi yau nake sha'awar sha" ya fadi yana nufar qofa
"Inna tana kiranka ma"
"Tom" ya qarashe amsa matan yana ficewa.
Yana cin abincin yana satar kallonta,sake kyau da zama cikakkiyar budurwa take,hatta da fuskarta ta nuna hakan balle gangar jikinta,kamar ma so take ta haura shekarunta,tana dagowa suka hada ido,sa ya mata nuni da wata leda
"Ga mayafinki can" cikin murna ta tashi ta dauko tana dubawa
"An gode yaya,Allah ya qada budi,amma yaya kala biyu ne fa"
"Wannan zai hau kowanne kaya cikin ankon,kiyi amfani dashi,daga baya saina sama miki dayan" kai ta gyada kawai,amma bataso hakan ba,saboda anyi duka qawayensu kala daya zasu saka.
Tana maidashi cikin ledar sadiqu ya shigo da lemukan a hannunsa,ya miqa mata wasu
"Ki dauki daya ki kaiwa inna sauran" ta karba tayi godiya sannan ta fice.
A wajen inna abincinta ta karba tace zataci a daki,hankalinta da tunaninta duka ya koma kan wayarta,koda ta shiga dakin,kunna wayar shine abu na farko data fara yi,tana gama kunnuwa saqonni suka fara rigen rigen shigowa a jere kusan guda biyar,saita koma ta zauna,murmushi na subuce mata tana qoqarin budawa ta karanta.
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 15
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
_________________________________
Dukkan saqonnin nasa suna tafe da kalaman dake nuna rudun da ya shiga kan katsewar wayar da kuma jinta a kashe da yayi bayan ya sake kira,magiya yake mata kan ta taimakeshi ta buda wayar tata,ta daure tayi kiransa,murmushi ta kuma saki,yanzu kashe wayarta kawai ya sanyashi a damuwa?,wanne irin so ne wannan?,har ta dannan kiransa ta fasa ta katse,ta ajjiye wayar ta jawo abincinta tahau ci,saidai tana ci gefe guda kuma zuciya da qwaqwalwarta suna dawo mata da abubuwan da suka faru wunin yau,tun daga haduwarsu kawo yanzu,duk kyanta da yake fadi gani take ya fita,saita miqe ta isa gaban mudubi tana qarewa fuskarta kallo,kalamansa a kanta na dawowa kanta turyan turya,sai ta kuma sakin murmushi,ta juya ta dauki kwanon abincinta da kayan ciye ciyen bikin da muniran ta hadota dashi don ta kaiwa inna ko zata iya cin wani abun a ciki.
***********Washegari*******. Da saqonsa tayi karin kumallo,wasu irin shiryayyun kalamai dake dauke da dandasa dandasan kalaman zallar soyayya,dolenta murmushi ya subuce mata bayan ta kammala karantawa,yakansa ta shiga mamakin wai ita din me muhimmanci ce har haka?,itama ashe watace data cancanci samun qauna maqura?,tana wannan tunanin saiga kiransa,ta sake yin sauri wajen saka wayar a silent.
Sai data katse ya qara kira sannan ta daga
"Beauty.....girmanki ne,amma kuma so kike na haukace na kasa aiwatar da abinda ya kaini abuja?kinsan kuwa samun hadin kanki shine kawai abinda zai bani nutsuwar aiwatar da abinda naje yi din?" Murmushi ta saki a boye
"Ni wacece da hakan zata faru da kai?"
"Kina mamakine ko kina tantama?,lallai da alama har yanzu bakisan irin matsayin da kike dashi a wajena bane,kinsan tunanin kina da wani masoyin da ranki keso kadai daga jiya zuwa yau ya sanyani nayi zuru zuru,zakiyi mamakin yadda na koma,please beauty......kicemin ni kadai ne wanda ya fara yaqin neman soyayyarki,duk nasan mafarkine kawai nakeyi,amma mace kamarki lodi lodin maza nasan ke gware a kanta" yadda yake maganar cikin laushi da sanyi ya bata dariya,har batasan tace dashi
"Kai kadai ne" ba,wani qaramin ihu ya saki,wanda yake nuna zallar farincikin da zuciyarsa ke ciki
"Yes.....kice na sanar da mommy a daidai" idanu ta zaro
"Me?" Ta tambayeshi cikin mamaki da fargaba
"Eh, already labarinki yaje wajen mommy,tun a jiyan ban iya barci ba sai dana gaya mata komai dana sani game da ke,infact ma ita harta matsu taga beautyna,na gaya mata,ta qara haquri har na shawo kanki tukunna"
"Bassam" ta kira sunanshi a karon farko
"Nifa na yiwa yayana alqawarin bazanyi soyayya da kowa ba, already ma yace shine zai zabarmin miji" wani mummunan faduwa gabansa yayi,take ya rikice mata,har abun yayi matuqar bata mamaki,da gaske yake kan duk abinda ya fada,da gaske ne yadda yake kururuwar sonta
"Please give me a chance beauty,ki bani dama....na miki alqawari indai na kasa sace zuciyarki da samun soyayyarki zan amshi sunan looser,zan kuma rabu daki,amma na tabbata yayanki baya nufin abinda ya fada" sai data ce ta bashi damar sannan taji salama da sukuni cikin muryarsa.
Da hanzari tayi masa sallama tana katse wayar,ganin ya kusa cinye mata lokacin aikinta,ta cusa wayar qasan pillow,sannan ta janyo dankwalinta ta daure sassalkan gashinta ta futo tsakar gida,qirjinta cike fal da bitar kalamai da al'amuran da suke gudana tsakaninta da bassam,tun daga haduwarsu kawo yau.
Tana tsaye a kitchen tana dama kunu,tayi nisa cikin tunaninta,a hankali ya qaraso bakin qofar kitchen din,idanunsa suka sauka a kanta
"Assalamu alaikum" yayi sallama cikin tattausar muryarsa dake cike da wata irin nutsuwa ta halitta,ta waiwayo a hankali suka hada ido,sai ta saki murmushi tana dan motsawa kadan
"Wa'alaikumussalam,ina kwana ya amin"
"Lafiya qalau queen,ki tashi lpy?"
"Lpy qalau....."
"Ma sha Allah,na godewa Allah da queen ta tashi lpy" murmushi ta sake,sai taji kalamansa na mata kama dana bassam
"Zan samu ruwan dumi?" Tunda taji haka tasan daga motsa jiki ya dawo,shi yasa suk safiya bata rabo da ruwan dumin saboda shi,matuqar tana kitchen din,tasan yana shigowa zai nema
"Eh yaya" ta fada da sauri,tana juyawa zuwa inda ta ajjiye flask din ruwan zafi,ta fara zuba masa,idanunsa na biye da ita.
Daidai yadda tasan zai iya sha ta zuba ta miqa masa,hannu biyu yasa ya karba
"Na gode" murmushin da ya sake fidda dimple dinta tayi,tana jin kunya ta masa abu ya gode mata.
Ta zaci fita zaiyi a kitchen din,amma sai taga yaci gaba jingina da qofar,yana kurban ruwan yana binta da kallo,yana monitoring duk wani motsinta,wutar qaunarta tana sake ruruwa cikin ransa,yana jin cewa lokaci kadan ya rage komai yazo qarshe,banda ma delay da ya samu naci gaban karatunsa yadda yaso,da tuni zuwa yanzu komai yayi nisa,saboda ya riga ya tsara ci gaba da karatun iman din a gidansa,hankalinsa sai yafi nutsuwa da hakan
"Akwai wani abune yaya?" Ta tambayeshi cikin jin kunya da kuma nauyinsa,miskilin murmushinsan nan mai cike da nutsuwa da wata izza izza ya sake,ya tashi daga jinginar da yayi ya tako zuwa kitchen din,ya dora mata cup din kusa da ita
"Babu komai.....kawai ina kallom queen dita yadda take qara girma kullum tana zama 'yar budurwa"
"Kai yaaya" ta fada da sauri tana sunne fuska,shi kuma ya saki 'yar qaramar dariya mai sauti kadan,ya taka ya fita a kitchen din.
Wunin ranar gaba daya bassam bai barta ta huta ba,kowanne motsi nashi sai ya gaya mata ga abinda yakeyi,duk wani schedules nasa daga safiya zuwa dare tsaf sai data sani,tamkar tare suke aiwatar da komai.
Ko wajen kamun surayya haka tayita fama da saqonninsa,yayin da munira ta hanata sakat da zancansa,batasan ya akayi ba sai ji tayi qawayenta sun fara tsokanarta da MRS BASSAM,kowacce a cikinsu cewa take
"Gaskiya ba qaramar sa'a kika taka ba,yaro ne matashin saurayi da jini ke zagayawa a jikinsa,yaro ne da kudi amma hausawa sukance abokin tafiyar manya, friend dina ne a insta,kije kiga yadda 'yammata ke rushing a kansa,daya daga cikin qawayensu ta fiddo wayarta,ta shiga account dinsa na Instagram ta buda mata hotunansa ta miqa mata.
Ta jima riqe da wayar a hannunta tana bin duk wani abu nashi daya dora a can,ta yadda da duk abinda suka fada din,daga kan hotunansa dake kan shafin nasa zakasan ba qananun kudi yake riqewa ba,kowannw hoto sutturu na alfarma ne a jikinsa,rabu da matan social media da kyakkyawan namiji,tarin followers ne dashi jingim maza da mata,abun ba'a cewa komai,kowanne hoto nasa ko wata magana da zaiyi,zaka tadda tarin comments da likes rututu a qasanta,ta sake gyara zama tana bin wallafar tasa.
Ba qarya bane,komai yaji tattare da bassam din,ta sauke ajiyar zuciya tana sakin murmushi sanda wata 'yar ajinsu da ba wani magana suke da ita can can ba ta shigo tana tsokanarta itama da mrs bassam
"Ya hadu guy din,bazan boye miki ba,nayi iya qoqarin na sameshi,to amma nasan ni ba type dinsa bace,shi din sai kyawawa dama irinku,ina tayaki murna gaskiya iman" murmushi kawai iman din ta bita dashi tana sake maida idanunta kan fuskar bassam.
Kwana biyu sukayi suna casar biki,tana zaune qawayenta nata liqi wa amarya,saboda tasan ita din bata da kudin da zatayi liqin,sai daga bisani ta bude jakarta dauko wayarta don duba lokaci,batason ta sake dare kamar na rannan idanunta suka sauka kan kudin da bassam din ya bata,bata taba komai ba a ciki banda kudin transport datayi musu ita da qawayenta,saita zari masu yawa a ciki,itama ta isa saman stage t fara liqawa ango da amarya,take taji kanta daidai da sauran qawayenta dake wajen,suka dauki ihun sai mrs bassam,abinka da zuciya da kuma aikin dan adamtaka,sai taji kata yana fasuwa a hankali,sannu sannu sai datayi liqi me yawa da ya sanya mc kama sunanta sannan ta sauka ta kona gurin zamanta,cin maganinta ya sanya samari da yawa dakeson kawo mata caffa suka kasa qarasowa inda take.
********Washegari**********
Wunin sakina,ranar ne kuma za'a kaita,saidai dukkaninsu basuje ba sai yammaci,dukka qawayen suka hadu,cikin daya daga cikin lafayoyinta da bata taba sanyawa ba ta shirya kanta,duk tafisu tsada shi yasa ta zabi ta sanyata,milk color ce me haske,sai adon gold a jiki,takalmin qafarta me tsini ne kuma mai tsinin dunduniya,ta ciki wani lace ta sanya mara nauyi,wanda ya amin yayi mata dinkin straight skeet da riga me dogon hanu,ta tara gashinta tayi masa nadin alkaki ta qasan daurinta samfurin ture kaga tsiya.
Fadin kyan da tayi a lokacin bata bakine,saika rantse da Allah daga gidan wasu hamshaqan ta fito,saboda kulawa da take samu gami da sutura me kyau,kowa kaffa kaffa da dama dama da ita yake cikin qawayenta,abinda ta lura dashi ya fara faruwa tun sanda munira ta shaida musu bassam shine masoyinta
"Komai yaji,wanka iya wanka,amma wallahi kika fito da wayar hannunki sai naji kamar zan nutse" munira ta fada dai dai yadda iman dince kadai zata iya ji.
Sauke wayar tayi tana duban munira,wanda dama ta dauko wayarne saboda jin qarar shigowar saqo,wanda kuma take da yaqinin ba daga kowa yake ba illa bassam
_"Kinyi kyau iya kyau baby.......,yanzu na shigo gida daga tafiya,amman bazan iya daurewa ba.....sai nazo naga wannan kwalliyar beautyna"_ wannan shine saqon da taci karo dashi,wanda mamaki ya kamata kan ta ina ya hangi adonta.
Maimakon ta bawa munira amsar maganarta saita buge da tambayarta
"Ya akayi bassam yaga kwalliyata?" Idanu munira ta wara
"Wallahi ban sani ba,shida baya nan yana abuja?"
"Ya dawo gida yanzu,kuma yana zancan zuwa ya ganni ba tare daya nemi address ba,bari naga gudun ruwansa,ta ina zai lalubo ni?" Ta fada tana gyara zamanta gami da gyara rufin lafayarta.
Murmushi munira ta saki
"Har yanzu bakisan waye bassam ba,mai kudin da idan yaso zai iya sanin duk wani motsi naki,amma bari mu gani,da rabon muje gidan amarya a lafiyayyar mota" munira ta fada cikin murna,batabi ta murnar munira ba,don tasan babu lallai yazo din,tunda baisan ina suke ba,saita dan goce kadan ta jingina da kujerar dake daura da ita.
A hankali zuciyarta da qwaqwalwarta suka shiga tunani,suka shiga hasko mata fuskokinsa data gani cikin hotunansa na ista cikin mabanbantan yanayi da shiga kala daban daban,tarin tulin 'yammata daketa commenting akai,da kuma qoqarin jan hankalinsa zuwa private chat,a hankali taji shauqin son ganin fuskar tasa na saukar mata,saita lumshe idanunta tana bitar lausasan kalamansa da suka zame mata abokai cikin kwanakin nan,dasu take kwana dasu take tashi,ta kuma hadasu da fuskarsa iya shiga da tsari na jikinsa,take taji komai yayi mata dari bisa dari,sai ta lumshe idanu tana sauraren hirarrakinsu,tare da kasa kunne taji xai kirata ko zai turo saqo ya nema address?.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM_*
16
Taji mamaki sosai sanda yake shaida mata yana qofar gidan,ta dubi munira duban tuhuma,ta daga hannayenta sama alamun ba ruwana.
A matuqar darare fa shiga motar sanda ya bude mata da kansa ya mata izinin shigar,shima saboda idanuwan yammata dake qofar gidan ana shirye shiryen daukar amarya da sukayi musu caa kamar zasu cinyesu.
Nannauyar ajiyar zuciya ya saki yana shafar qirjinsa
"Thank God,sai yau dana ganki sannan naji kamar an ciremin qaya, beauty,i really missed you" kunya ce tadan saukar mata,taja lafayanta ta sake boye fuskarta ta murmushi
"I liked it baby,inason kunyar nan taki,amma dai ya kamata adan fara rageta,a nunamin soyayya ko?".
Hira yake janta da ita sosai cikin wani salo da yasan yana tafi da zukatan 'yammata,ya hada mata abubuwan sha da ci duka cikin motar saman dan wani abu da ake janyowa me kama a table,saidai taqi taba komai saboda bata saba ba,ba zata iya cin komai a gabansa ba,uwa uba kuma a takure take jinta,ga kalamansa daya cikata dasu wadanda suka yiwa kanta nauyi,taketa jin kunyar yadda yake marairaice mata kamar zai kwanta aka ta soshi don Allah,yayi alqawarin zai mallaka mata komai.
Abinda bai sani ba tuni ya fara barin burbushin wani abu a cikin zuciyarta,ya sanya zuciyarta ta fara narkewa da kadan da kadan,hakanan tanajin wani abu na tabata duk sanda ta kalleshi,ta kuma tabbata kowacce mace ma dole taji irin wannan,saboda dan gayu ne iya gayu,wanda gayun ga hade da kyau da kuma ilimi quruciya da kuma wadatar arziqi.
Kafewa yayi kan shi zai kaita gidan amarya,bazai barta tahau motar kowa ba,nan kuwa ta samu qawayenta 'yan tayi,kowacce tace a motar itama zata,a haka suka dibi mutum hudu daga cikinsu suka wuce.
Ko a hanya ma bai barta ba,hira yake mata qasa qasa cikin kalaman da zasu iya wafce ko sace zuciyar kwacce irin mace,idam yaji tayi shuru cikin murya me kama da rada zaice
"Uhmmm baby......baby kice wani abu mana,don Allah karki haukatani" wani abun ko bataso saita amsa masa.
Da suka isa ma hanata fita yayi yaci gaba da dasa mata dashe me wuyar cirewa,su sauran suka shige ciki,sai da yaga an ragu sannan ya mata tattaki har qofar gidan ta shiga,sannan ya daw jikin motarsa ya jingina yana jiranta.
Tana shiga kamar dama jiranta sukeyi kowacce ta shiga ihu da kuma zolayarta
"Ku keshan soyayyarku,amma nice nake sumewa" inji zee qawarsu
"Gaskiya gaskiya kika bar wannan guy din kin tafka asara,keee.....me tsada be wallahi wannan,samun namijin da komai yaji a tare dashi kamarsa ai abune me wahalar gaske,tabdi,gaskiya kin shiga sahun mata masu sa'a a duniya" daga daga cikinsu ta sake fada
"Banda zaman amana ake ai ni zanyi wufff dashi" batasan ta jefa mata harara ba sai da suka kwashe mata da dariya
"Almura,ashe ya fara sace zuciyar da akaqi bawa kowa dama". Haka suka hadu sukayita yi mata cari.
Duk yadda taso ya barta ta samu abun hawa na haya ta koma gida yaqi ji bare gani,duk ta gama tsurewa,yayi parking qofar wani babban store ya fita bayan yace tazo su shiga tare amma taqiya.
A qalla kusa minti talatin ya barsu cikin motar ita da qawayen nata kafin ya dawo,siyayya yayi mata mai ubansun yawa data sanya iman din tsurewa,ya dubi su munira yace su shiga ciki su karbo sauran kayan duka nasu ne.
Sai da suka fita ya fidda wasu qananun leda guda biyu,daya daya bude wani dan qaramin akwati ne me azabae kyau,zobe ne a ciki me bala'in kyau da daukar idanu ya miqa mata
"Saka,so nake naga yadda zaiwa kyawawan hannuwanki kyau" ya fada yana murmshi,yadda ya tsareta da kallo ya sanya dole ta saka zoben,ko don ta tsira daga kallon da yake jifanta dashi
"Ma sha Allah,da dama da nayi kissing wannan kyawawan yatsu,Allah ya mallakamin su" tsananin kunya ya hanata magana,sai kawai ta janye hannun nata ta boye cikin mayafi.
Leda ta biyu still shima wani kwalin ne,wanda ke dauke da wata santaleliyar wayar hannu,wanda ko ba'a gaya maka ba kasan cewa ba qaramar wayar bace,bawai a girma na jiki ba,a'ah,kudaden da aka zuba kafin a mallaketa.
Miqa mata wayar yayi,ta janye hannunta taqi karba tana dubansa
"Na siyeta ne saboda ke,an saita komai da komai nata,akwai layi a ciki,na siyeshi ne saboda ni kadai,nafison duk sanda na kiraki na sameki available" babu jan dogon bayani tace mishi ba zata karba ba,yaji babu dadi har saman fuskarsa,saidai a nata ganin haka shine daidai,don batasan inda zata sanya wayar ba.
Wannan dalili yasa ta kasa musanta masa sanda ya bata gift na ledar daya loda mata siyayya,suna tafe munira na mata rakiya kamar kowanne lokaci,saidai jikinta asabule yake
"Munira,nufar gidanmu fa kike da wadan nan kayan"
"Na sani,ki tsaya ki gani mana" ta bata amsa babu alamun damuwa a tattare da ita.
A bakin famfo suka samu inna tana tarar ruwa a buta,da alama bandaki zata zagaya,ta daga kai tana amsa sallamarsu,cike da ladabi kamar kullum munira ta gaida innar,ta amsa mata tana tambayarta mutanen gidan,ta soma gajiya da ganin yarinyar tare da iman,bata fiyason mu'amalar iman din da baqin fuskar qawaye ba,duk da dama silar bikin sakina ne ya kawota gidan.
"Inna wai kaya ne da sakina ta bayar a rabawa tsakaninmu qawayenta da muka yi mata hidiman biki,shine nace ta ajjiye mana a wajenta,idan yaso in an tashi sai a raba,sai iman din ke tsoron kada ki fada,shine nace bari na roqeki don Allah"
Idanu innar ta sauke kan ledar da muniran ke nuna mata,kowaccensu tayi shuru tana jiran jin amsar da innan zata bayar,kamar ba zatae komai ba sannan ta amsa
"Ba damuwa,amma karsu jima,banason ajiyar abinda ba naka ba"
"In sha Allahu inna" daga haka ta miqawa iman ledar,sukayi sallama ita ta juya ta fice.
Cikin kwanakin gaba daya bassam ya sanya wuta wajen nema soyayyar iman din,ya kuma ci galaba da gagarumar nasarar da bai taba kawowa kansa zai samu ba,ita kanta iman din ta fada wani muguwar soyayya da bata taba tunanin zata fada ta ba,sannu a hankali ta dinga ganin kyan da bassam da kuma sauran jama'a ke kururutawa tata,ta kuma hango dacewar da sukayi da bassam din. Da kuma dacewarsa da zamantowarsa miji a gareta.
Ta samu sakewa da dukka kaya da siyayyar bassam sanda taje maiduguri ta dawo,saita sanya dukka kayan cikin tsarabar da yagana tayi mata,a zuwan ita ta bata su,ta fidda fella fellan laces din ciki ta bawa al'ameen ya dinka mata.
Haka kawai yaji jikinsa yayi sanyi sanda ya bude laces din xai dinka,tailor ne shi da yasan aikinsa,ya kuma san kudin kaya masu tarin yawa,a idanu kawai akace ka yiwa lace din kudi kasan ba qarami bane bare aje ga ainihin kudinsa,kusan guda uku ne kuma dukka haka suke.
Yagana 'yar kasuwa ce,tana kuma samu sosai da kasuwancinta,to amma kuma laces din sunyi tsada da yawa,saidai daga bisani ya gargadi kansa,yakuma share maganar cikin ransa,tunda ya riga ya aminta da wace iman din,rainonsa ce,ta kuma tsotsi tarbiyya daga inda suka tsotsa,wato wajen inna da malam,ya budesu yayi mata dinkuna masu kyau,da suka sanya ta dinga murna sanda ya kawo mata su,ta kuma ajjiyesu,batayi amfani dasu ba sai da bikin murjana,daya 'yar ajintasu.
Ta fita sosai cikin qawayen nata,ta kuma fita daban,ta haska yadda ya kamata,ta dinga jin kanta yana fasuwa cikin qawayenta,saidai tayi qoqari matuqa wajen hana kanta jin izza ko girman kai.
Kasancewar bassam ma'abocin tafiye tafiye ne,baya nan akayo bikin murjana,yaji babu dadi sosai,saboda yaso su kasance tare a lokacin,don har yanzu abu na gaba da yake buri da buqata shine ta gabatar dashi a gidansu,ya samu 'yancin zuwa ganinta kai tsaye a duk sanda yaso.
Saidai ita a nata bangaren cike take da tsoro da kuma fargaba,tsoron yadda zatayi bayani wa malam inda ta sanshi,a inda suka hadu,da kuma yadda akai har suka saba babu wanda ya sani,ina zatace ta samu lasisi ko kuma umarnin sauraronsa,uwa uba kuma ta sani,burin ya ami tayi karatu,basuyi cewa zata gabatar da mijin aure a dai dai wannan gabar da take aji biyar a makarantar secondary ba.
Duk da baizo ba amma tuni wayarsa ta samu baquncin hotunanta tsala tsala ta hannun jakadiyarsa munira,wanda suka sake haukatashi tare da susutashi,suka kuma sanyashi qara daura damara da cin burin kasancewa da iman din,da kuma maidata ta zama matarsa kuma mallakinsa,ko me zaya kashe kuwa.
Tafiyar al'ameen zuwa jigawa garinsu ya sake qulla wani sabon kusanci da kuma shafin soyayya tsakanin iman da bassam,saboda wayarsa daya bar mata aro kafin ya dawo,ita kuma tayi amfani da wannan damar,ta bude account na Instagram WhatsApp da Twitter,yadda zata samu damar ganin bassam din yadda ranta yakeso.
Ta kuwa kalleshin,babu wani hoto nasa data tsallake ba tare data masa kyakkyawan kallo uku ko sama da haka ba,gayu iya gayu,kudi iya kudi ta gansu,gefe guda kuma ga ilimi kamar yadda take da sha'awa,daya qyalla idanu ya sameta ta WhatsApp kuwa kamar zaiyi me saboda murna,hakan ya sanya ta sake zama mayyar waya,kullum tana manne da ita a daka,Allah Allah take ta gama abinda take ta dauki wayarta su kasance tare.
Tuni inna ta fara lura da canje canjen dabi'u da kuma halaye tattare da iman din,abinda yasa ranar da amin ya dawo daga qauye,suna tsakar gida,inna na saman babbar tabarma,shi kuma yana kan kujera 'yar tsuguno yana bawa inna labarin ci gaban da qauyensu keta samu,iman din na saman tabarma daban,ta tattara hankalinta gaba daya saman wayar,abinda yaso jan hankalinsa kenan,duk da suna hira da inna,amma kusan bayan kowanne minti sai ya daga kai ya kalleta,yasan cewa ba haka suka saba da ita ba a lokaci irin wannan daya dawo daga tafiya,tana nuna kewarta sosai a kanshi,abinci na musamman take masa,ta hada da ruwan zafi na wanka takai masa,yana cin abincin tana damunsa da hirar abubuwan da suka faru bayan baya nan,shima kuma tana tambayarsa abubuwan daya gani da sauye sauye da aka samu.
Miqewar da tayi yasa inna tace
"Ina zuwa?" Fuska tadan ya mutsa kadan
"Kwanciya zanyi inna,na gaji" idanu ta kafeta dashi
"Me yake damunki ne kwana biyu da kika koyi kwanciyar wuri?"
"Kawai inna,saboda makaranta ma,da shirye shiryen qualifying da mukeso mu fara" sam maganar bata shigeta ba bare al'amin,wanda ya maida kansa ga qaramar keypad din daya tafi da ita,yana serving station din da yake yawan sauraran labarai a cikinsu
"Wannan wayar ke daukan hankalinki iman......" Maganar da taso tadan tsoratata,amma saita dake,saboda tasan halin innar da matuqar bin qwaqwaqwafi
"Games ne da yawa na dauko inna,kuma inajin dadin yi"
"Dole ki maida masa wayarsa,tunda tana neman canzaki" saita marairaice cikin tsoro da faduwar gaban kada a yanzu yanzu innar tace ta miqa masa abarsa tunda ya dawo,kafin kuwa ta gama tunanin nata abinda ta zata din ya afku,innar tace da ita
"Bashi wayarsa maza,tunda Allah ya dawo dashi lpy alhmdlh,aikin mori abinda kika mora,dama kullum malam cikin fadan me yasa ya barta a hannunki yake"
"Don Allah inna........"
"Karki min magiya"
"Zan karba gobe inna,ki qyaleta" al'ameen ya shiga maganar,saboda ko waye mutum komai qanqantarsa bazaiso irin wannan titsiyen ba,zuciyarsa kuma fes take kan iman din,baya shakka ko zargin zata aikata wani abu ba dai dai ba,ko kuma ya saba da tarbiyyan gidan,yadai bata uzuri kan cewa rashin sabo ne,da kuma daukin wayar tunda ta jima tana sonta.
_________________________________
*mg's skincare*
Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩
Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️
Shin kinafama da
Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata?
Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫
Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind
Bridal kit:18k
Beauty kit:11k
Student package:7k
Herbal whitening soap:3k
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Facebook: mg's skincare
Instagram:glow_with_mgs
Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝
Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩
Then @mgs skincare gat you covered 💯
Now is time to glow😍
Pamper ur skin🦵
Shine like bride👰🏻♀
Glow🧖♀️
💯 tested nd trusted🤝
Guarantee
Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 17
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
__________________________________
Washegari bai karba wayar ba kamar yadda yace din,saboda sabgoginsa na dinki da kuma neman samun damar ci gaba da karatunsa da yaketa fafutuka,saidai a ranar yanajin yadda inna ke mitar yadda iman din fa tashi a makare ta fara ayyukan gida,wanda saboda quracewar lokaci bata samu gama aikin ba,inda daga qarshe ta shirya ta wuce makarantar a makare,innan kuma ita ta qarasa sauran aikin da ya rage din.
Washegari qarfe takwas saura minti biyar na safe ya fito a shirye zashi su hadu da mutumin daketa masa fafutukar ganin ya samu tallafin karatu,ya gaida inna dake dauraye flask din malam na kunu sannan ya tambayeta malam,tace yana qofar gida,ganin takalman iman na makaranta yasa ya tambayi inna iman dun bata wuce makarantar ba?
"Ina zata wuce,ta zama abunda ta zama,babu abinda ta iya sai kasala da sakalcin banza" sai yaji a ransa indai waya ce take sanyata hakan bai kamata ya barta da ita ba,don ko a jiya da daddare yana jin bambamin sadiqu kamar zai bugeta kan yace fa.kiqo masa abinci ta shantake,dama kuma can sadiqun zafi gareshi,bai cika haquri ba,don haka sai ya qarasa rumfar inna da kansa.
Sallamarsa da shigowarsa gaba daya yayita,tana zaune a qas tana saka farar safarta,ta daga kai tana murmushi gami da amsa sallamar tasa,gabanta yadan fadi da fari,saboda ganin da tayi ya danyi mata zubi da bassam saboda adon da yayi
"Ina kwana yaya?" Maimakon ya amsa mata sai ya maida mata da tambaya yana dan tsuke fuska
"Me kike har yanzu baki tafi makaranta ba?"
"Yaya makara nayi wajwn tashi"
"Kin fara wasa da karatunki ko?" Saita girgiza kai
"Aah yaya,bacci ne......"
"Is ok,idan na dawo zan karbi wayata,ki sakamin a charge idan sun kawo wuta tayi full" a sanyaye ta gyada kanta,sam batason ya karba wayar,saidai......wayarce ta shiga ranta ko kuma alaqarta da bassam ce bataso ta yanke?.
Tare suka fita shi da ita,sai daya sanyata a abun hawa ta tafi sannan ya tari nasa yahau,kasancewar ba hanya daya zasuyi ba.
Tun a makaranta ta turawa bassam saqon maida wayar,ta kuma goge duk wani account da wani abu daya shafeshi,kama daga hotunansa daga tuttura mata,da kuma saqonnin sms,sai data tabbatar bata bar komai akai ba sannan ta maida wayar tata jaka,saidai rabi da rabi na karatun ranar ba shigarta yake ba,tana can ga tunanin yadda zasuyi kewar juna ita da bassam din,ta saba chart dashi,kuma yafi.mata dadi akan kiran ways,a chart dinne take sakewa sosai ta gaya masa sirrikan zuciyarta.
*********Goma da rabi na daren ranar,wanda tayi dai dai da kwanaki biyu da amsar wayar daga hannun iman din,har ya gama shirin kwanciya saboda sammakon da yakeson yi gobe zuwa shagon dinki don kammala dikunan wasu amare,sai kuma ya miqe ya jawo locker dinsa sake jikin katifarsa,ya dauko wayar ya sanyata a charge,saboda tunaqa da yayi zai turawa wani mutum photon wasu takardu nasa.
Gefan katifar ya koma ya zauna yana jiran charge din yadan hau,saboda bashi da tabbacin akwai charge akai,ya bata mintina goma sannan ya koma gaban socket din ya zauna yakunna wayar,bayan ta daidaita ya shiga gallery dinsa ya fada laluben hotunan takardun,tunda already yana dasu,saidai sama ko qasa ya rasasu,ya dinga kaikawo bai gansu ba,har zai haqura ya sake sabbin dauka,duk da yasan ba zasuyi kyan wadancan ba,saboda wadancan din anyi scanning dinsu a computer,sai kuma ya tuna,ya wuce zuwa recycle bin na wayar.
Tun daga farko ya fara cin karo da hotunan da baisansu ba,bai kuma waye mai su ba,sa'an nan baisan mutumin dake jikin hoton ba rututu masu yawan gaske.
Sosai kansa ya daure,ya dinga bin hotunan da kallo daya bayan daya,mamaki na sake cikashi ta yadda hotunan suka shiga cikun wayarsa.
Sannu a hankali ya gangaro kan hotunan iman,iman dinsu dai,cikin salo na gaye da kwalliya,hotunan da sukayi masifar kyau suka kuma fidda duk wani kyau da Allah ya bata,duk da cewa shigarta bata bayyanar da tsiraicinta ba,amma kyan da tayi cikun hoton,kyau ne da bai taba ganin tayi irinsa ba a zahiri.
Gaba daya qwaqwalwarsa so tayi ta tsaya da aikin yin kowanne tunani bare ta bashi hint na abinda ke faruwa,saboda yadda ta dode gaba daya kamar bata taba wani tunani ba,sai ya koma ya zauna dirshan sanda kwanyarsa ta taimakeshi ta tuna masa cewa iman itace mutum ta qarshe da wayarsa ta jima a hannunta.
Wani mummunan faduwa gaban al'ameen yayi,har yaji kamar an samu wani abu an buga masa akai,gudun zuciyarsa ya dadu sosai,sai ya sauka da sauri,ya koma binciken wayar,bakinsa cike da addu'o'i cikin rudewa.
Duk inda ya shiga babu komai an share,manhajar WhatsApp itace abu na qarshe daya duba,ba tare da yana da wani yaqini na samun wani abu ko hujja ba.
Ga mamakinsa yana shiga WhatsApp din ya bude sarai,da alamun account din da akayi amfani dashi shine har yanzu kan wayar ba'a shareshi ba.
Suna da hoton dake kan number farko kuma qwaya daya dake kan account din gaba daya ya sanyashu furta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" dukkan wata dakiya da jarumta tasa ta fara zagwanyewa lokacin da ya fara bin chart history din,yana karanta hirarrakin da akayi cikin inbox din,wani irin gudu zuciyarsa taci gaba dayi kamar zata faso qirjinsa ta fado waje,kunnuwansa sukayi dummm wanda ya dauka har tsakiyar kansa,a hankali cikin wani salon sanda feeling na daina gane abinda ke kewaye dashi ya fara kutsawa cikin jikinsa,yana aikawa kowanne sashe na jikinsa,a hankali ya daina gane komai da kowa sai zallar tashin hankalin daya tsinci kansa a ciki,tashin hankalin da yayi masa ba zata,tamkar zuwan ajali ga dan adam.
A hankali sai wayar ta gagara riquwa a hannunsa,ya zameta a hankali ya saketa gefansa,ya koma ya zauna sosai yana son fahimtar da kansa abinda ke faruwa,kamar bashi da idanunsa ya gani ba,saidai kuma wani sashe na kwanyarsa na gaya masa,ba iman dinsa ba,ba iman dinsa bace,hala ta bada aron wayar itama ga wani,idan ma ita dince ko dai wasa take?.
A sannan ji yayi babu abinda yake da buqata banda yaga iman a gabansa ya tambayeta abinda ke faruwa,yana da burin idan ta tashi amsa masa ta amsa da cewa wasa take,ba da gaske take ba. Ba tare da la'akari ko kuma duba da cewa dare ya fara yi ba ya miqe da hanzar ya nufi qofar fita,yana so ya sadu da ainihin cikin gidan.
Garam sukayi karo da sadiq dake shirin shigowa da ledar balangun da ya tafi siyo musu,saboda dukkanins mutane ne masu son cin dadi a bakunansu,hakan bai basu matsala ba,saboda kowannensu neman kudi yake tuquru
"Haba mana master......saurin me kake?,gani na dawo,wajen ne akwai layi,kasan ya iya gashi" ja baya yayi yana duban sadiqun da yake mulmula goshinsa,wanda shi sam bai ma damu da nasa goshin da ya buge ba,saboda rudanin da yake ciki,gaba daya ma ya manta wai sadiq din ya tafi siyo musu nama.
Idanu sosai sadiqu ya zuba masa yana masa wani baqon kallo
"Amin.....lafiya kuwa?,wani abu ya faru ne bayan na fita?" Qafafunsa dake a mace kamar lawashin da yasha rana ya fara janyewa da baya da baya,bayan hankalinsa a sannan yakai kan agogo,ya kuma tabbatar bazai iya shiga cikin gidan a yanzu ba,sabosa bai taba shiga din ba idan ba wani abu bane ya taso
"Babu komai" ya amsa ma sadiqu yana zubewa gefan katifarsa,tare da yin hobbasa na ganin ya saisaita mood na fuskarshi
"Koda naji" sadiqun ya fada yana cire takalmansa ya dorasu saman abinda suke dora takalma dake bakin qofar dakin sannan ya shigo,ya bude musu naman yana bawa amin din labarai kamar yadda suka saba duk dare kafin su kwanta.
Idan yace yana gane abu daya da sadiqun ke fada to tabbas ya zabga qarya
"Ya baka cine?,wai anya lafiya kake kuwa?" Kalmar da sadiqun yace dashi kenan yana rutsashi da ido,abinda yayi silar daya ringa miqa hannu ya a zaqular naman yana hadiyewa ba tare da ya tsaya cikakkiyar taunawa ba bare ya gane wanne irin taste gareshi,haka ya dinga tsaya masa a maqoshi kamar wanda ke cusa dan wake,abinda yayi sanadiyyar qwarewarsa kenan yahau tari,wanda ya sarqafeshi sosai,sai da yasha ruwan sanyin da sadiqu ya bashi sannan ya lafa,da wannan ya fake yaje ya kwanta,saboda qirjinsa da ya dauki zafi,sadiq yace may be ko ulcer dinsa ce ta motsa kuma.
Tunda ya kwanta idanuwansa a rufe suke gam,ko qwaqwaran motsi baya qaunar yaji a kusa dashi bare magana ko surutu,lokaci bayan lokaci yana bude idanunsa ya sauke ga agogo,yana qididdigar mintunan da suke gabansu kafin wayewar gari.
Zuciya da tunaninsa sunkai sun komo,ya kuma rasa a wanne bigire zai ajjiye tunani da zuciyarsa,karafkiya qaryata juna da sa'insa babu kalar wadda ba'a samu ba tsakanin sashe biyu na zuciyar dake qirjinsa,wata zuciyar na rinjayar da qaryar cewa ba iman bace,haka ba zata faru ba,yayin da wara zuciyar ke tabbatar masa da iman dince,saidai ta aikata komai ne bisa rashin sani,koma meye ya riga ya yankewa kansa hukunci kawo qarshen komai,koma meye zai faru ya faru,qirjinsa bashi da qarfin daukar zuciyar da zata rasa iman haka cikin sauqi,saima ya korewa kansa wannan tunanin da yake kallonsa a baqi kuma mummunar fata cikin rayuwarsa.
Dai dai lokacin da iman din take can kwance saman tata katifar a zahiri,a badini kuma tayi matuqar yin nutso kuma me zurfi cikin kogin qaunar bassam,wanda ta ara masa daqiqa masu dama yana sake karanta mata yadda qaunarta ta tashi zuciyarsa a aiki,irin girma da kuma matsayin da take dashi,abinda ya sake sawa taji kanta ya fasu,alfahari da samun bassam da kuma soyayyarsa ta shigeta,ta bude masa tata soyayar sosai wadda ta narkar da ilahirin zuciyar bassam,ya kuma dauka mata alqawura masu matuqar nauyi a mizani,girma kima da kuma martaba cikin duniyar soyayya,wanda daga qarshe sukayi tarayya kan alqawari guda,duk rintsi.....duk wuya.....suna tare,babu gudu kuma babu ja da baya,dukkan wanda ya sauka daga kai ko kuma ya sauya,la'ana da kuma hukuncin cin amana yahau kansa.
Wannan kusan itace hira mafi dadi da sukayi da bassam a wajenta tsahon tarayyarsu,domin kuwa ko bayan ya sauke wayar sun rabu kasa runtsawa tayi,murmushin dake kan fuskarta cikun duhun dakin yaqi barin fuskarta,hirarraki muryarsa da gwala gwalan kalamansa sukaqi barin qirji da zuciyarta,ta dinga tariyarsu tana jin wani dadi qauna da shauqi yana sake kamata,zuciyarta jaririyar zuciya ce,wadda ta fara soyayya ta zahiri a karon farko,don haka komai baqo ya kasance mata,sai daga bisani fa samu baccin yayi awon gaba da ita,cike da mafarkan bassam,wanda a ciki har ya zama miji a gareta.
Kwata kwata baccin da yayi tsahon daren dukansa bai wuce na awanni uku ba,suma din a tsitstsinke,a kunnuwansa akayi kiran asubahi,yayi alwala suka fice masallaci tare da sadiqu,wanda hakan al'adarsu ce,kuma acan suke tadda malam.
Miqewa sadiqu yayi ya dubeshi bayan an idar da sallar,wasuma har syn fara watsewa
"Nikam yauma idan zaman azkar dinkan nan zakayi saidai mu hadu a gida,don wallahi jiya kwata kwata bacci bai isheni ba" ya fada yana miqa
"Shikenan,saina taho" ya amsa masa yana sake maida kansa qasa,don bayason sadiq din ya fahimci bai samu bacci ba.
Yana kallon sadiq ta qasan idanunsa har ya fice,hakanan yaji bazai iya komawa cikin gidan ba,ya kintata wani lokaci ne da zai cimma iman,duk da cewa yau tana da makaranta alhamis ce.
Cikin wani nishadi da walwala take zuba kunu da awarar data soya cikin cup da plate don taci ya wuce makaranta,ta gama shirinta tsaf,kana duban fuakarta zakasan wani nishadi takeji,bassam ya raya darenta ya kuma qawata mata safiyarta da kyakkyawan saqon barka da safiya.
Ta juyo zata fito kenan yayi sallama bakin qofar kitchen din,idanunsu suka shiga cikin na juna,sai ta hangi baqon yanayi tattare dashi,saidai bata kawo komai ba cikin ranta ta zarce da gaisheshi,ya amsa mata yana nazarinta
"Akwai ruwan dumi?" Ya tambayeta yana jingina da qofar kitchen kamar yadda ya saba,tsaiwarsa kwnan duk sanda zai karba ruwan,duk da yawanci a gajiye yake shigowa dama saboda exercise da yakeyi,sabanin yau,da babu execise din da ya iya fita,saidai zuciyarsa a jigace take qwarai,wanda hakan yayi tasiri har zuwa gangar jikinsa,ya matsu ya kuma damu ya fidda abinda yake zuciyarsa da ransa komai da komai ma ya huta
"Yaaya...gashi" ya tsinci muryarta tana masa magana,da alama tun daxu ta zuba ta miqa masa,sai ya karba ya fara kurba a hankali,bayan ya matsa mata hanya
"Idan kin gama ki dauko litattafanki ina jiranki" har tadan dakata sai kuma ta amsa da to tayi gaba,kasancewar ta saba lokaci lokaci yakan rakata,koda ba har makaranta ba to xai kaita bakin titi,saidai a kwanakin nan abun yaja baya.
*_LITATTAFAN ZAFAFA BIYAR_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 18
Jerawa yayi da ita kafada da kafada sanda suke takawa a hankali,idanunsa qur saman hanya,zuciyarsa na taraddadi da fargabar abubuwan da zayaji.
Satar kallonsa ta sakeyi a karo na barkatai,ganin sun nufi hanyar makarantar tasu kai tsaye ba tare da ya tsaidan mata da abun hawa ba
"Yaya,a qafa zumuje?,ka manta?,kawai dan nisa fa?,naga munbi ta layin nan" lokaci ya kalla a hankali kafin ya sauke hannunsa ya kuma sake rage speed na tafiyar,ya zaro wayar dake aljihun hagunsa ya miqawa iman idanunsa cikin nata
"Karbi ki dubamin" cikin rashin fahimta ta miqa hannu ta karba wayar,ta kuma bude kamar yadda ya umarceta.
Abinda ta gani din shi ya birkita kwanyarta cikin sakanni,duk da tasan da wanzuwarsa,amma bata tsammaci yaci gaba da wanzuwa cikin wayar ba,take rudewa suka bayyanar mata,saidai tayi qoqarin bawa kanta dakiya da qwarin gwiwa,tunda babu wani na sabo ko rashin tarbiyya kaf cikin charts dinsu,bugu da qari ma tana jin lokaci yayi da zata bayyanawa duniya bassam dinta
"Waye wannan?" Amin ya fada yana kallon wayar kafin ya maida dubansa ga fuskar iman. Har cikin ranta taji tambayar kamar tazo mata a dai dai,don saboda dama ya amin dinne kawai take tunanin zatayi maganar dashi,ya kuma fuskanceta har ya kai zancan gaban malam,to saidai shima duk sanda ta yunqura zata yi masa maganar sai taji ya mata wani mugun kwarjini,amma yanzun komai zaizo da sauqi.
Sunne kai tayi irin na alamun jin kunya
"Saurayina ne ya amin"ta fada tana rufe fuskarta da tafin hannu.
Hasbunallahu wa ni'imal wakil,ita yayi qoqarin zuqowa saga mafitar maganarsa zuwa saman harshensa,sannan yayi azamar dafe wata bishiya da tafiyarsu ta ratso dasu ta gefanta don neman agajin tsaiwa sa qafafunsa.
Kasancewar sautin addu'ar tashi bai samu fitowa ba illa maqalewa da yayi saman harshensa.......wannan ya sanya sam batasan me yake faruwa ba,cikin wani irin tashin hankali yaci gaba da kallon iman duk da fuskarta a rufe take da hannunta
"Iman......ina alqawarin da kika yimin ba zakiyi soyayya da kowa ba?,ina alqawarin da kika yimin na bani damar zabar miki miji na gari?" Yanayinta ya sauya kadan cikin boyayyar fuskarts,duk da bata kalli tasa fuskar ba amma ta fuskanci sauyun sauti sosai fiye dana dazu
"Yaaya.....kayi haquri,na saba maka wannan alqawarin,amma shima ina da tabbacin irin mijin da kakeson zabarmin dinne,kuma zaka yaba da zabina yaya,ya shiga rayuwarta ne katsam" qara dafe bishiyar yayi da kyau saboda jin jiri na dibansa da yayi,babu sauran kwana kwana ko boye boye
"Iman......nine mijin da na yi miki tanadi,ni ya amin dinki nine mijin dana zaba na kuma killace kaina saboda ke,iman.....ni amin nike sonki iman,zuciyata ta girma da sonki ta kuma rayu da sonki tsahon shekaru masu yawa". Kamar wadda aka jibgawa wani abu a saman kanta haka taji,ta yaye fuskarta da sauri da kuma hanzari don tana da buqatar tabbatarwa kanta ba shirin film akeyi a wajen ba,tana son ta gani da gaske ya amin ne?,kuma ba wasa yake mata ba?.
Saidai kuma.....kallon farko ta karanci zallar gaskiyar dake fitowa tun daga zuciyarsas shimfide saman fuskarsa muraran,abinda ya sake firgitata,ta danyi baya kadan tana jin tashin hankali yana rufto mata,ta yaya haka zata faru?,ta yaya zaice wai da sonta ya rayu?,me yasa bai gaya mata tun da can ba sai a yanzu data riga tayi alqawari da wani,data riga tayi nisan kiwo cikin duniyar soyayyar wani?,ta yaya zata gane yaren da yakeson koya mata bayan bashi ta iya ba?,meye yake shirin faruwa?.
"Ya ameen,da gaske kake?,nice fa iman dinka?"kai ya gyada mata yana kallon tsakiyar idanunta kai tsaye
"Na sani,iman dita ce,shi yasa nake gaya mata halin da zuciyata take ciki,ina sonki iman......burina kuma na aureki,in fact,malam ya jima da bani ke!" Maganarsa ta qarshe saura kadannta wargaza kwanyarta
"Me?!" Ta furta da wani sauti me kauri da amo
"Eh,malam ya bani ke tuntuni" ya fada yana gyada mata kai tare da tabbatar mata.
Kanta ta soma girgizawa,sam sam kwanyarta ba zata dauki wannan batun ba,wacce iriyar magana ce haka mara dadin saurare?,ta yaya zaizo mata da wannan maganar?,tsahon zamansu da rayuwar da sukayi a muhalli guda bai taba tunkararta da maganar ba sai yanzu?sai daidai wannan lokacin?.
Ci gaba tayi da gigixa kanta tana koma da baya,kafin ta juya cikin wani irin hanzari ta nufi hanyar gida,ya miqe da sauri yabi bayanta yana qwala mata kira,saidai ko waiwayawa batayi ba bare ta saurareshi,har ya fara rufa mata baya,sai kuma ya tsaya cak bayan ya yiwa kansa birki ya kuma gayawa kansa gaskiya kan bai kamata ya bita ba din,jama'a suna kallonsu,sannan kuma gida zata shiga a hakan,shigarsu tare cikin wannan yanayin su duka biyun bai kamata ba,kuma yana biye da ita,sai ya dawo a hankali cikin wata kasala da mutuwar jiki ta gaske,ya duqa ya dauki jakarta data sulale a wajen ya soma takawa a hankali shima zuwa hanyar gidan,kwanyarsa na juyawa,tunaninsa yana hautsinewa,yaya iman ta dauki maganar?,me ya sanyata firgicewa haka?,wadan nan sune tambayoyin da ya dinga maimaitawa kansa su wanda bashi da amsoshinsu.
A hanya komai kama kamar iman bai gani ba,hakan ya alamta masa ta jima da isa gida kenan?,wannan yasa daya dawo shima bai shiga gidan ba,dakinsu ya wuce kai tsaye,ya zame saman katifa yayi rub a ciki,bayajin akwai wani abu da zai iya tabukawa,saboa ya jin kamar qafafunsa ba zasu iya daukar gangar jikinsa ba.
Yadda batasan a gida ya wuni ba itama shima baisan tana kwance cikin dakinsu ba,dukkaninsu wani irin yini sukayi mai wahala qunci da kuma takura,tunanin dake qirjin kowannensu ya nauyayar masa,wani irin yanayi mara dadi na zulumi da kuma fargaba,fargabar data kasance mai tarin banbamci a tsakanin iman da ameen.
Sai magariba da ya shiga cikin gidan inna keta mamakin dama yana ciki?,saboda sadiqu nada aiki da yawa a ranar a garejinsu,abinda ya sanyashi fitar wuri sannan kuma har zuwa lokacin bai shigo ba
"Banajin dadi ne inna,kuma banaso na gaya miki nasan zakiyita damuwa ne" amsar daya bata kenan
"Ikon Allah,don iman bata jin dadine itama,nasan da dole zata bincikoka,nayi mamaki nima da banji motsinka ba ashe jikinne.....don Allah aminu ka daina zama da ciwo baka fada,babu kyau,a qalla ya kamata ko leqaka a dinga yi ko ana ganin yanayin jikin naka,baka zauna a daki kai kadai ba kamar babu kowa cikin gidan uhmmm"
"In sha Allah inna,kiyi haquri" ta amsa masa sa babu komai,yanayin sanyi da yanayinsa ya koma saita azashi da cewa don bayajin dadin jikinsa ne,daga bakin qofar dakin iman din ya tsaya yayi mata sannu saboda wanzuwar inna a wajen kada taga ya wuce,ya jiyota can qasa sosai ta amsa masa,sai ya sake wucewa zuwa dakinsu.
********. ****. ********
Munira ce rike gam da hannun iman din sanda suke zagayawa zuwa bayan ajujuwansu,bata sakar mata hannu ba sai da suka dangana saman wani dan tudu wanda asalinsa tarin qasa ne saboda jimawa a wajen ya koma kamar dutse.
"Tunda kika shigo na tabbatar ba lafiya ba,gashi jiya na dinga zura idanu an bani saqo na baki amma baki shigo ba" munira ta fada tana duban iman dake zaune ta rungume qafafuwanta a qirjinta.
Ajiyar zuciya me nauyi ta sauke,a.hankali ta fara magana cikin sautin da sai ka dauka wani babban ciwo tayi
"Rayuwata na neman fadawa garari munira......na shiga rudani me zurfi daga jiya zuwa yau,irin wanda ban taba hasasowa ba" matse fuska munira tayi tare da sake tattara hankalinta waje daya
"Rudanin me?,me ya faru?rabuwa kukayi da bassam?" Kai ta girgiza
"Muna gab da rabuwarne wala'alla"
"Karki gayamin wannan mummunar kalmar mana iman,kina haukane?,bassam din zaki bari ya subuce miki?"
"Munira.....ya ameen ke sona" saita firfitar da idanu waje
"Yayannaki da kuke ciki daya?,wanne irin hauka ne wannan?"
"Ba ciki daya muke ba,riqonshi inna tayi,kuma almajirin malam ne,dalibinsa ne" sak munira ta tsaya tana kallon iman,tarin mamaki ne fal saman fuskarta,sai iman ta gyara zama ta gaya mata duk yadda akayi.
Fuska munira ta yatsina
"To don yana sonki shine me?,kawai saiki zauna a rabaki da wanda zuciyarki takeso?,wanda zai zama hutun rayuwa a gareki matuqar kika aureshi,karki manta,'yammatan wannan zamanin SHI SUKE BURI" Kai iman ta girgiza tana jin tashin hankali na sake ninkuwa cikin ranta
"Munira.....bakisan halin malam ba,na tabbatar baya magana ta tashi,kuma wallahi wallahi indai ya ameen ya tabbata yana sona malam ya sake fahimtar hakan babu wanda ya isa ya hanashi bashi ni duk duniya" murmushi munira ta saki,sai ta matso kusa da iman din sosai
"Kinga,ayi me baro baro kawai a wuce wajen......ki bude bakinki malama,karki cuci kanki,ki gayawa kowa kina son bassam,kuma shi kike da burin aura,ki gayawa ameen bassam kikeso kanki tsaye,idan kikace zaki tsaya kunya ko kara,to wallahi kina ji kina gani za'ayi babu ke,ni dama na dade ina zargin sonki yake,shi yasa ya tajura rahuwarki ya hanaki sakewa kamar kowacce diya,abu daya ne ya ciremin zargina da kika gayamin cewa yayanki ne.....amma Allah na tuba,me na sama yaci ballantana ya baiwa na qasa,ki duba surarki da kyau....banda ma yiwa kai kasada me zaisa yace yana sonki a irin wannan lokacin da arziqi ya qwala muku kira?,me yake dashi da zai riqeki iman?,ina cewa makarantar da zaici gaba ma kokawa suke shi da ita da fafutukar ganin ya sameta,idan kika auri bassam.....bashi kansa ba,hatta da abokansa dana kusa dashi.....danginsa na qauye rankatakaf sun huta,amma shikenan saboda ya dankwafe rayuwarki sai yace wai yana sonki saboda cuta da mugunta,yana da kyau yana da kwarjini na daukar hankali,amma magana ta domin Allah bashi da sinadarin riqe mace kamarki.......da dinki zaici da ke?,koda karatun da bashi da tabbacin samunsa?ke rabu da gaibu fa ki kama dahir,kuma shima matuqar yana sonki ai zaiso ci gabanki ne,bawai ya aureki ku dankwafe waje daya babu ci gaba ba" ire iren maganganun munira kenan data ci gaba dayi,kamar zata ari baki.
Iman tana saurarenta tsaf,ita ba wannan bace damuwarta,babbar damuwarta soyayyar bassam da zuciyarta ta saba da ita,kuma batajin zata iya jurewa rasashi.
"Gashi inji bassam......,jiya ya aiko yaranshi ya kawo min da daddare saboda ya kikkiraki jiyan bai jiki ba,ya damu sosai,shi kansa yaron nasa idan kinga motar da yake hawa ko......hmmmm" tayi zancan sanda take fidda waya sabuwa dal tana miqa mata.
Wannan karon batayi musun karba ba,jiki a sanyaye ta amsa,saboda tana jin wannab shine lokaci mafi dacewa da su kasance tare da juna da bassam din.
Nan da nan labari wayar ya karade cikin qawaye da classmates dinta,tanajin mazan ajin suna fadan kudin wayar,mamaki ya kamata,ta jujjuya wayar a hannunta tana mamaki yadda mutum zai iya narka kudi kamar haka ya siya waya qwaya daya jal.[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 19
Cikin jiki zuciya ruhi da kuma idanu ya tabbatar akwai matsala,irin matsalar da duk sanda zuciyarsa ta gaya masa akwaita yana qoqarin qaryata kansa da tunaninsa,komai da komai din na iman ya canza kuma ace ya janye daga muhalli da bigiren da ya santa ada,duk dacewa ba mazaunin gida bane shi.....amma kuma gaba daya iman din ta yiwa idaniyarsa qaura,ya daina ganinta,walau da safe koda dare,tamkar wasan buya ta tsiro dashi a tsakaninsu a tsanake,yasha ganin wucewarta wuf a duk sanda ta karanci motsinsa a waje ki tahowarsa izuwa wajen.
Iman din dake tiri tiri da dukkan wani abu da ya shafeshi a yanxu ba ita bace,iman din dako yaushe take shiga kokwanto da wasi wasi duk sanda wasu awanni suka shude bataji motsinsa ko gilmawarsa ba,dukka a yanzu sun kau,kwanaki biyar din da suka biyo bayan maganarsu bai sake sanyata a idanunsa ba,koda muryarta zai iya cewa baifi sau uku ya jiyota ba tsayin kwanakin.
Wata iriyar rayuwa yake a kwanakin wadda shi kansa baxaice ga inda ta dosa ba,saboda rashin gane ainihin abinda iman ke nufi,ina tasa gaba?,meye alqiblarta?, Duka bai sani ba,tarin damuwar dake danqare cikin zuciyarsa ta bayyana cikin ayyukansa na yau da kullum,ada idan gana dinka riga goma a wuni daya,a yanzu biyu yake iyayi,sauran duka tunani ya cinyeshi.
_wannan kenan_
K'arfe takwas na dare bayan kammala sallar isha'i ya shigo gidan,wanda direct daga masallaci gidan ya nufo,tunda dama can shi ba ma'abocin zaman majalissa bane,koda ya zauna din baya wuce minti goma zuwa ashirin zai sallama dasu ya wuto gida yaci gaba da sabgoginsa.
Sanda yake sanyo kai cikin gidan tare da sallama a bakisa yaga kamar wani abu ya gifta wuf zuwa daki,inna ta daga idanunta tabi iman da kallo wadda ita dince tayi hakan,cikin mamaki tana amsa sallamar amin din,ta fuskanci wasu sauye sauye sosai game da alaqar ameen din da iman,yau dinne kuma idanunta suka ganeta real,zuciyarta tadan tsinke kadan,tana fatan kada ubangiji ya sanya wata matsala ce ta afku tsakaninsu komai qanqantarta,don basa fatan hakan,saboda ko a jiya sun jima ita da malam suna tattauna batu akan aminu da iman din
"Barka da dare inna" amin ya fada cikin murmushin sannan me sanyi da akullum yake fuskantar innar dashi,fuskantar da da zai yiwa mahaifiyarsa cikin girmama a tarin ladabi.
Cikin nata salon kulawar da kuma nuna qauna ta sakar masa fara'a
"Yauwa aminullahi,sannu da qoqari,an samu shigowa?" Ta qarashe maganar tana tura masa kujerar tsuguno,sai ya zame ya zauna kan shimfidar abun sallar da iman ta tashi yanzu akai,ya zauna sosai akai ya tanqwashe qafafunsa yana gaidata kamar wanda ba tare suke gida daya ba.
Cikin kulawa ta amsa masa,sai 'yar hira ta shigo kan wajen aikin nasu,aduk sanda wata matsala ko ci gaba suka sameshi kam aikinsa,da ita yake shawara,da ita yake tattaunawa,su kashe su binne,inna takanji matsalarsa dari yayarsa dake jigawa bataji guda daya ba.
Duk wannan hirar fiye da rabin hankalin inna yana kan dakin iman,tana zuba idanu tare sa saka ran ganin fitowar iman,tana fara'a gamida nuna kulawa dayi masa sannu da zuwa,ta kuma debo abincinsa ta gabatar masa kamar yadda suka saba,sabanin haka shuru kakeji.
Hankalin inna ya dan daga kan,ranta kuma sosu,ta kasa jurewa sai data daga murya cikin sauti mai qarfi ta qwalawa iman din kira.
Kai tsaye kuwa kiran ya isa kunnuwan iman,wadda ke kwance rub da ciki kan katifarta,ta nutsa cikin duniyar chart da bassam,wanda har bata iya jin hirar dake gudana tsakanin inna da bassam dake zaune daga qofar dakinta.
Da hanzari ta danna wayar qasan pillow,tunda dama babu wanda yasan da zaman wayar,koda yaushe kuma a silent take,ta tashi da wani irin reaction na rashin gaskiya ta fito waje tana gyara daurin dankwalinta.
Tamkar batasan ya shigo gidan ba,tamkar ba dalilin shigowarsa yasa tabar tsakar gidan ba ta gaidashi,duba daya yayi mata yasan lallai mawuyacine abinda zuciyarsa keta gujewa ba shine ya afku ba,iman din dake marmarinsa a yau ita ke gaidashi babu wani doki babu komai,fara'a da ya santa da ita babu kaso casa'in cikin dari.
Da wani mugun bin qwaqwafi inna ke karantarsu gaba dayansu,saita danne tace da iman
"Wanne irin sakarcine wannan,ki wuce ki dauko masa abincinsa,kin kama kin wani qule daki?,haka kawai kin koyi nunqufurcin banza da wofi na zaman daka?,inacewa baki jima da fitowa ba?,me kika koma yi a ciki ko wutar nepa babu?" Gabanta ya fadi saboda tasan halin inna sarai,tana matuqar qoqari wajen kiyayewa duk wani abu da zaisa inna ta zargi akwai wata a qasa amma a banza,mutum ce ita me mugun kula da kuma tsantseni
"Inna kayana na fito dasu na manta zan gyara na barsu a waje" ta fada cikin marairaicewa
"Saiki wuce ki debo masa abincin" ta sake maimaitawa tana miqe qafafunta da sukeso su fara mata ciwo,dama kwana biyun daurewa kawai takeyi
"Zan fara watsa ruwa,kamar nan da minti ashirin sai a kawomin"
"To shikenan....,idan zaki hada masa ga kwadon xogale can ragowar na malam da yayi buda baki dashi saiki hada masa dashi" da to ta amsa tana nufar kitchen,saidai ranta a bace yake sosai,kawai saboda amin din innan ta sakata a gaba take mata fada,yadda innar ke nuna masa kula da tattalinsa koda yaushe ko ya sadiqu bata yi masa haka,abincinma sai an wani hada masa kulli yaumin kamar wani magidanci,rana dai daine zai shiga kitchen ya dauko da kansa yaci.
Tunda take dashi bata taba ganin aibun hakan ba sai yau,sai yau da zuciyarta ta karkata zuwa wani hanya daban ba wadda a baya take kai ba.
Kwata kwata bata qaunar su kebe da amin din baki daya,wannan shine babban dalilin da haduwarsu cikin gidan ma ta haramatata,saboda batason ya sake dauko.mata magana makamanciyar wadda yayi mata a rannan,shurunsa da rashin nemanta da baiyi ba shima a kwanakin ya sauqaqa mata dukkan wani tsoro da kuma zulumi nata,koda bata buda baki tayi magana ba tana kyautata zaton ya zuwa yanzu ya gane inda ta dosa.
Tana hada abincin tana mita qasan ranta,fuskarta a hade,hakanan bakinta yana ta motsawa,tasan yayi hakkanne kawai don ya samu damar magana da ita,kuma batajin zata sake bashi wannan damar.
Data gama hadawar saita koma daki dauko hijabinta,hasken wayarta dake alamta shigowat saqinnin bassam ya zaunar da ita,ta saki murmushi sanda ta fara bin saqonnin nasa,saita manta da aikin da zatayi ta shiga maida masa amsa.
Ya jima tsaye gaban mudubi gana sharce kansa yana kuma duban fuskarsa,kwanyarsa na masa bitar tarin maganganun dake cunkushe daga zuciyarsa zuwa bakinsa,mamakin yadda komai yake qoqarin sauyawa cikin qanqanin lokaci yakeyi.
Cikin jallabiyya ya shirya bayan ya feshe jikinsa da turarensa kamar yadda ya saba,hatta da boxer na ciki bai tsira ba,sai ya koma saman kujerar dakin ya zauna yana duba lokaci,tayi delay sosai,amma sai ya bata uzuri,kamar hadda hali da dabi'ansa yake,mutum ne shi mai yawan bada uzuri,zaiyi wuya karon farko ya kamaka da laifi,sai ya dora hannunsa saman sumarsa da har yanzu danshin ruwan dake jikinta bai bushe ba,yana shafata a hankali daga gaba zuwa baya,yana jin yadda damuwa ke sandar jiki da zuciyarsa.
Wayarsa ya maida gefe ya ajjiye yana furzar sa zazzafar iska daga bakinsa sanda yayi kiran layinta yaji busy,wani abu ya tsaya masa a maqoshi ya kuma tokare masa maqogaro,a hankali yaci gaba da shafar sumarsa yana lallashin kansa da kansa,sai ya lumshe idanunsa yana sake fitar da iska mai tsaho wai ko zata rage masa nauyin da yakeji cikin qirjinsa.
Kiran wayarsa da akayi shi ya dauke masa hankali,ya kuma zuqe yawan mintunan data dauka bata kawo masa abincin ba.
"To ba damuwa,bari zan kira idan na duba" amsar da ya bayar kenan sanda yaji motsinta,da kuma sallamarta a bakin qofa cikin zazzaqar muryarta,ya bata izinin shigowa yana qoqarin sanya wayarsa a silent,wanda kafin ya gama ya daga kansa harta ajjiye abincin ta juya
"Iman" ya qwala mata kira,ta waiwayo tana jin ba dadi a zuciyarta kan tsaidatan da yayi
"Zo ki zauna......magana zamuyi"
"Yanzu zan dawo" ta amsa masa a taqaice,saiya gyada kai lumsassun idanunsa suna zube saman fuskarta,yana ganin sauyi muraran daga iman dinsa zuwa wata iman din ta daban,ta juya da hanzarinta ta fice,cikin ranta tana jin saidai suyi maganar da wata amma ba ita iman din ba.
Amma kuma tana saka qafarta a tsakar gida inna dake fitowa daga daki ambaci sunanta
"Wai wanne irin baqin hali kika koyo imani?,wannan zobon da kika ajjiye ya gama hada sanyinsa babu mesha ba zaki kai masa ba,bawan Allah azumi yakai fa?" Kamar zata dora hannu aka ta zunduma ihu haka ta dauki jug din zobon ta nufi soron dashi,bata taba jin inama tana da qanne ba irin yau,da babu shakka saidai fa ta tura daya daga cikinsu ta samu ta dawo,domin har a jikinta tana jin bassam nacan yana jiranta,haka fa tura qofar dakin ranta a bace sallamarta a ciki,daidai sannan nepa suka kawo wuta,hasken farin qwan lantarkin dake dakin ya mamaye ko ina,ya kuma taimakawa ameen qwarai wajen ganin yanayin fuskar iman din.
Can nesa ta samu ta zauna bayan ta dire masa jug din,kanta a qasa kamar wata surukarta tace gani.
Baiko motsa ba sabda tayi maganar,sai kafeta da yayi da lumsassun idanunsa na wasu daqiqu,sannan ya miqe cikin nutsuwar nan tasa,ya taka a hankali ya rage tazarar dake tsakaninsu,a hankali ya zame saman carfet ya zauna saitinta,ta yadda zasu iya ganin juna yadda ya dace.
Dakakkiyar muryarsan nan me cike da amo na mazantaka ta fara fita,yau din cikin wani irin yanayi na sany da laushi,duk da cewa dama can ita iman din wannan amon ta saba ji daga gareshi,bai fiya kausasa mata a magana ba
"Iman.....a duniya idan akwai wanda zai fadi halayyata bayan inna da yayata to kece ta ukunsu,banajin ko sadiqu ya sanni yadda kika sanni" sai ya sanyi shuru yana sauke numfashi gami daci gaba da kallonta sannan ya dora
"Kwanaki biyar da suka shude,munyi magana dake.....na bayyana miki komai,saidai kuma har yau na kasa karantar me wannan iman din take nufi?,ina ta fuskanta?,ina ta sa gaba?iman baki sona ne?,ko ya amin din naki bai miki ba?,idan banyi miki ba iman ki fito ki gaya min,saboda ni ba baqonki bane......"ga fada maganar cike da qwarim gwiwar samun akasin abinda zuciyarsa ke raya masa,saida amsar da iman din ta bashi tayi matuqa girgizashi,ta motsa masa zuciyarsa fiye da yadda ya zata ko kuma ya tsammata......amsar da bai taba kawowa koda cikin mafarkansa zai jita daga bakin iman din ba,bai taba zaton zata iya furtata ba
"kayi haquri ya amin........bassam nakeso" ta amsa masa,tamkar dama jira take a bata wannan damar.
Dukkan wata jijiya dake kai saqo jini da kuma iska a jikinsa zuwa muhallansu sai da ta tafi hutu na sakanni,kafin ya samu nasarar zuqo numfashinsa,bayan ya tabbatar numfashin ya koma saman qirjinsa yadda ya dace,sai ya fara kokwanton duniyar zahiri ce ko ta mafarki,saboda haka yayi qarfin halin motsawa kadan
"Iman.....sake maimatawa naji". Yayi maganar sautin muryarsa na fidda wani amo wanda zai alamtawa mai sauraron da kunnensa da kuma qirjinsa ya cika da hikima cewa lallai akwai wani abu mai tsananin nauyi da yake shirin danne zuciyar da wannan sautin ya fito daga gangar jikinta......
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: .20
"Kayi haquri ya amin......basai na maimaita maka ba,abinda na fada din,hakan nake nufi har tsakiyar zuciyata" wannan karon shigar da maganar tayi masa tafi wadda tayi masa dazu,domin kuwa a take launin fari dake qwayar idaniyarsa ya juye zuwa ja,saukar wasu abubuwa masu kama da mãsu yakeji tako ina a jikinsa.
Bai taba hasashen rashin samun nasafa kamar wannan a rayuwarsa ba,bai taba tunani ko hangen failure irin haka ba kafa rayuwarsa,sai gashi kalar tashi faduwar tana son ga riskeshi kan yanayi mafi muni,kan iman.....iman din da duk duniya babu wani abu da yakejin yana da lasisi qwarin gwiwa da tabbaci a kansa kamarta,saboda rainonsa ce,halittar da yaso yake kuma qimantata cikin kafatanin rayuwarsa.
"Zuciyata da gangar jikina ta rayu dake a matsayin wata makusanciya,kuma halitta mafi da kima a idanuna,sannan daga bisani dukka wadan nan suka narke suka koma soyayya me nauyi da kuma qarfi,irin qarfin da zai iya fasa zuciyar duk wanda ya kama......ima,daga ranar da malam ya bani ke daga ranar na laluba zuciyata,sai na tarar ashe yarin sonki ne zallah shimfide a cikinta,dashi ta rayu tsahon zamanta cikin gidan nan,ban fahimci haka ba saboda kallon qanwa ta jini da nake miki kuma muharramata,sai ranar da malam ya tunsar da ruhina halaccin abun sannan na tabbatar da haka.......iman" ya kira sunanta da wani irin taushi da ya sanya gangar jikinta zubawa
"Ki yarda ki soni,ki karbi soyayyata iman,ina miki albishir din cewa,zaki sameni a matsayin cikakken miji GARKUWA INUWA KUMA MAJINGINA ga matarsa,zan maidake abar kwatance cikin mata,zan gatantaki da dukkan wani nau'i na gata da alqaluma suka rubuta aka kuma adanashi da sunan GATA".
Tabbas jikinta yayi sanyi da jin fitar wandan nan kalaman daga bakin ya amin din,tunda bata tana jinsu daga bakinta ba,saidai kuma idan fa waiga ta waigo....zuciyarta ta maimaita mata kabar amin dai dai yake da rasa bassam muddin ranta,sai wani rauni na musamman ya lullubeta,taji ba zata iya ba,ba zata iya barinsa ba,ba zata iya rayuwa babu shi ba,jaririyar zuciyarta ta saba da soyayyarsa,kunnuwanta na iya sake tariyo mata kalaman da ya gama gaya mata yanzun nan,tamkar yasan abinda ke shirin faruwa kenan,cikin karyayyar murya dake nuna karyewar zuciyarsa,baya ya gama roqonta ta barshi yazo gidansu haka nan,ta barshi yazo ya gabatar da kansa wajensu malam,amma tsoro ya sanyata tace aa
"Karki yaudareni iman don Allah,ki soni yadda nake sonki koma fiye da haka,duk randa kika kwatanta rabuwa dani,ba shakka sunana gawa" yayi maganar kamar zai fashe mata da kuka.
Kai take girgizawa a hankali tana dubansa
"Kayi haquri ya amin,bazan iya ba,inason bassam,ina son bassam,zuciyata tana sonshi ya ameen,ka taimaka ka mara min baya mu samu cikar burinmu" sosai yaji hankalinsa ya sake tashi,ya sake kawo kusanci tsakaninsu yana dubanta sosai
"Look iman.......kinsan me kike fada?,ya ameen dinki kike cewa ya barwa wani ke?,bazan iya ba iman.....ki bani dama na wanke wancan daga ranki nayi miki sabon dashe me kyau da ma'ana" ji tayi kamar ya kwara mata ruwan zafi,saita miqe da sauri,wani abu me kama da tsoro da kuma fusata suna cudanya cikin ranta
"Bazanyi maka qarya ba,bazan iya ba......inason bassam.....ina sonshi" wannan kalaman data furta su suka sanyashi runtse idanunsa katamau ya gaza budesu har tabar dakin,fitarsu daga bakinta zuwa kunnuwansa sun aikawa sa zuciyarsa wata irin guba me tasiri da saurin illata dan adam
"Iman....iman" ya dinga maimaita sunan cikin kwanyarsa,kamar sunan baqo ne a wajensa,mamakin yadda iman din ke magana dashi haka kai tsaye,babu haufi......babu kara ko alkunya,iman dinsu ce wannan?,idan itace me ya canza ta?,meye ya sauyata haka?,tabbas akwai abinda ke faruwa ko kuma ace ya riga ya faru,waye wannan bassam din?,yaya akayi yayi nasarar canza iman din gaba daya?.
Wadannan sune abubuwan da suka taru sukayi masa rubdugu,suka saukar masa da wani matsanancin ciwon kai cikin mintuna qalilan,wanda hakan ya tilasta masa kwanciya,yana sauke numfashi a hankali,tafin hannunsa daya dafe da goshinsa.
Abu kamar wasa ciwon kan ya zaunar masa sosai ya kuma sanya masa jinya,kusan kowa na gidan ya damu da yadda alamin din ya kwanta ciwo haka lokaci guda,babu ma kamar inna data tabbatar ranae lafiya lau ya shigo,abunda ya tsaya mata a rai,haka kawai taji bata yarda da iman din ba,musamman da taga qarancin damuwa kan ciwon alamin tattare da ita,abinda bau taba faruwa ba tsahon rayuwarsu tare,ita tafi kowa shiga damuwa da dimuwa duk sanda bashi da lafiya,tafi kowa zamantowa kusa dashi,ta kumafi kowa sake maida hankali da kula da al'amuransa,amma dukka yanzu babu wannan.
Kasa daurewa inna tayi,saboda lokacine da suke gab da cika burinsu ita da malam,lokacine da suke son fahimtar juna da shaquwar dake tsakaninsu tafi tada,amma sai ga wani baqon lamari na kuma shirin bullowa a sanda bai kamata ba,bai kuma dace ya bullo din ba.
Kiran iman tayi ta rufeta da fada kan halin ko in kula data lura yana faruwa,duk da cewa sai mai tsananin kula da sanya idanu zai karanci hakan
"Inna,shirin zana jarabawar qualifying muke fa,kuma ina da buqatar nayi karatu sosai,shi kansa da kansa yake korata yace na dinga zama waje daya ina karatu" salon qaryar data shararawa innar kenan,haka kawai taji bata gamsu ba,kuma hujjar bata ratsata ba,don haka batace mata komai ba ballantana ta amsata.
Misalin qarfe takwas na dare ne,yana zaune qasan ledar din,ha jingina bayansa da doguwa kujera guda daya dake dakin,qafafunsa na miqe sambal,wanda hakan ya sake bayyana baiwar tsayi da Allah ya bashi,sambala sambalan qafafunsan yayi crossing nasu waje guda,yadan daga kansa sama kadan,saidai idanunsa a runtse suke.
Idan ka sanshi kallo daya zakayi masa kaga yadan fada,ba kamar yadda yake ada ba,dakin babu kowa saishi kadai,sai tv daketa faman yi,albarkacin wutar NEPA da ake da ita.
A mintunan da suka shude dazu shida sadiqu ne,wanda ya zauna ya sanyashi a gaba cike da damuwa kan sai yaji mene ne damuwarsa?,amsa daya yake bashi
"Bani da wata damuwa sadiqu,na gaya maka,ciwo ne kawai daga Allah" kansa ya girgiza masa gana dubansa alamun bai yarda ba
"Haka dai ka fada,amma kuma ban yarda,saboda bani kadai ba,duk wanda ya sanka idan ya kalli fuskarka yasan akwai damuwa qasan ranka" murmushin qarfin hali ya sakar masa
"Mutumin da bashi da lafiya har a tambayeshi batun damuwa dama?,ina damuwa ne kada na mutu na barka kai kadai" dariya ya sanya ta qwacewa sadiq din,duk sanda yayi masa irin wannan zolayar a sanda bashi da lafiya dariya yake bashi
"Kaga.....ka samomin abun sha me sanyi mana please kaji?" Yace da sadiqun,saboda yadda zuciyarsa ke masa zafi,wala'alla idan wani abun me sanyi yabi ta maqogaronsa ya ratsa qirjinsa ya samu sassauci,dalilin fitar sadiqun kenan,shi kuma ya lula duniyar tunani,dason warware tarin tunane tunanen da suke cunkushe a kansa.
Sallamarta ta sanyashi bude idanunsa da sauri cike da mamaki,yau kwanaki biyu kenan rabonta da dakin,saidai ya jiho muryarta daga tsakar gida,ko kuma idan zata fice.
Daga sallamae bata sake cewa komai ba,ta wuce tana ajjiye abincin,shima sai ya maida idanunsa ya rufe,amma yana iya gani da kuma bibiyar motsinta ta qasan idanunsa,yadda idan ka shigo ma zaka tsammaci idanunsa a rufen suke,koma bacci yake.
Sosai ya lura da yadda taketa tsutsuke fuska da kuma bata rai,dukkan alamu suka nuna dole akayi mata ta kawo abincin,sai data gama shirya komai ta juya da zummar ficewa,cikin zafin nama ba tare da duba yanayin jikinsa ba ya miqe da hanzari ya tareta.
Kallon kallo suka yiwa junansu,kowa yana duban dan uwansa cikin mabanbancin emotion,ita ta fara kauda idanunta daga kansa,ta kuma ja da baya sannan a hankali tace
"Fita zanyi,inna tana jirana" ba
"Iman,idan har da wasa kikemin......kiyi haquri ki janye maganarki,idan har gwadani kike iman,ki sani wallahi bazanci wannan jarabawar ba" kan nata yana can daya bangaren ta amsa masa,batason ta dubeshi don kada taji nauyi ko rashin kamata
"Wasa kuma?,ka taba yimin wasan furtamin kana sona?" Kansa ya girgiza
"Yadda baka taba min ba.....haka nima da gaske nake bassam nakeso,kayi haquri shi nakeso,shi nakeso,na riga na kamu da sonsa" ta qarashe maganar tana zuba masa qwayar idanun nan nata da a shekarun baya zamanin quruciya yara ke tsokanarta dame idanun mage.
Cikin jikinsa yaji ya kamata ya kauce ya bata hanya,hakan kuwa yayi,yaja jikinsa gefe a hankali,hakan ya bata dama ta daga labulen,ta kuma tura qofar ta fice,zuciyarta na ganin baiken ya amin da yake sake tararta da wannan maganar,maganar da take ga ya isa ya barta hakanan,tunda dama tun asali babu irinta a tsakaninsu.
Yadda ta wuce fuuu zuwa dakinta ya sanya inna dake daura alwala bakin famfo ta saki abunda take ta miqe ta bita da kallo,lallai ya kamata ta tambaya,ta kuma sanya tuhuma tsakanin bassam da iman din.
******Yana zaune daga gefan malam din,saman babbar dardumar dake malale a babban falon malam din,wanda babu komai sai dardumar da labulaye,da filalluka sample din tuntum.
Karin safe malam din yakeyi suna dan taba hira da sadiqu da amin din,yayi matuqar qoqari wajen ganin ya sake jikinsa ta yadda ba zasu fahimci komai ba,amma shi kadai yasan me yakeji a zuciyarsa.
Tashin muryar inna suka fara ji daga tsakar gida cikin tsawa,abinda ya sanyasu su dukka yin sak suna sauraro izuwa tsakar gidan,saboda gaba dayansu baqon abune a wajensu tattare da innar,basu taba jin wani abu makamancin haka daga gareta ba
"Me yake faruwa ne?" Malam yayi tambaya a fili,kamar yana buqatar ansa daga wajensu sadiqu
"Leqa sadiqu,me ya samu binta haka" malam din ya sake fada cikin jimami da mamaki,sai ya miqe yabi bayan sadiqu saboa kasa zama da yayi.
Duk muryarta da suke jiyowa tana daga cikin dakin iman ne,malam ya qarasa a hankali ya sanya kansa cikin dakin,abinda ya manta rabonsa da yayishi,sai ya samesu cirko ciro a tsaye,hannun sadiq riqe da waya yana juyata
"Lafiya binta?" Malam ya sake tambayar inna,wadda ke tsaye a kan iman,ranta a mugun bace,bata amsa masa ba,sai wayar hannun sadiqu data karba ta miqa masa,yasa hannu yakarba shima ya shiga juyata
"Ta waye wannan?" Malam din ya tambaya
"Ta iman ce" sadiq ya amsa masa
"Iman kuma?" Malam ya maimaita cike da dimbin mamaki
"Ita" inna ta amsa with confidence wanda ke cakude da wani irin zallar bacin rai,maida dubansa ya sakeyi ga iman da kanta ke qasa
"Ya akayi kika samu wannan wayar?" Tambayar data fadarwa da iman din gaba,saboda bata shirya amsata ba kwata kwata
"Tambayarki nakeyi" malam ya sake fada
"Malam,tun kafin ka shigo na tambayeta bata cemin komai ba,kamata......" Hannu malam ya daga mata,sai tayi shuru tana saukar dakai,abinda bata taba yi ba iman din ta sanyata yinsa yau
"Iman,karo na qarshe....ina kika samu wannan?"
"Wanine ya bani" dukkansu sai da maganar ta daki kowa a cikinsu,ta kuma sanyasu a cikin rudani
"Wani fa kika ce iman?,wayeshi?"
"Saurayina ne" ta fada da low tune cike da fargaba,saidai zuciyarta na gaya mata wanna shine last option da take dashi.
Shuru dakin ya dauka,kowa yayi dif a cikinsu,malam yana ci gaba da juya wayar,yayin da kansa ha daure,mamaki kuma yake sake nuqurqusarsa
"Muje rumfata" ya basu umarni yana yin gaba da wayar a hannunsa,suka mara masa baya,sadiqu na satar kallon iman din,yana jin kamar a bashi dama ya zabga mata mari ko sau daya ne,saurayinta?,a gidansu kuma wai?,iman din?.
Sallamar malam tasa amin dake zaune a waje bai motsa ba bai kuma tashi ba tunda suka fita,ya daga kansa yana amsawa,tunda suka fitan jikinsa ya bashi akwai wani abu dake shirin faruwa,duk da bayajin abunda suke fada daga can din.
Shiru ne ya ratsa falon na wasu sakanni,har zuwa sanda malam ya jefawa iman tambayar
"Waye saurayin nata?,a ina suka hadu" tambayar data qular da inna da kuma sadiqu,ta kuma sanya amin ya sake saukar da kansa,abubuwa da yaketa qoqarin boyewa da kuma dannewa zasu fasu kenan.
Sosai ta bawa kanta qwarin gwiwa,da kuma jin yaqinin cewa ba zasu tilastata kan abinda bata ra'ayi ko kuma bata so ba,tiryan tiryan ta fayyace musu waye bassam din,da kuma lokacin da suka dauka a tare
Wani abu ya yiwa sadiqu tsaye a wuya tunda ta fara amsawa malam tambayoyinsa,huci yake fitarwa yana jin kamar ya tashi ya rufe iman din da duka,idanunta har sunyi soyewar da zata yi wannan bayanin a tsakankaninsu su hudu?,ameen kam ko motsawa bai yi ba,saboda wani nauyi da yaji qirjinsa yayi.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" malam ya fada qasa qasa,saiya miqawa iman wayar
"Ki kirashi kice inason ganinsa,yazo yau yau din nan,daga yanzu zuwa magariba,idan kin gaya masa ki dawomin da wayar" dukkansu sai sukai saroro da jin maganar da malam din yayi,banda amin da babu wani abu da yaji,saboda yasan waye malam,duk wani hukunci da zai yanke tafe yake da hikima a cikinsa,kuma yana da manufa,sadiqu da inna duka suke zaton zaya rufeta dashi,amma sukaga akasin hakan....saidai koma meye zasu zuba ido suga meye matakin da malam din zai dauka.
Wayarta ta karba ta miqe ta fice tana qoqarin aiwatar da abinda malam din umarceta,tana ji cikin ranta akwai nasara tattare dasu.
K'arfe takwas saura na dare bassam ya iso qofar gidansu iman,bayan ya samu cikakken kwatance daga iman,cikin shiga yake ta alfarma da nuna irin dukiyar da Allah ya bashi,hakanan motar da yazo cikinta,tafi kowacce mota da yake hawa tsada.
Yana tsaye daga jikin motar bayan ya bude Boot na motar,ya kira wasu daga cikin daliban malam dake rumfar gidan suna daura alwalar sallar isha'i dake gabatowa ya sanyasu suka fara kwashe kayan ciki suna shiga cikin gida dasu.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: ''21
Saidai kuma ko sakanni goma ba'ayi ba,sahun farko na yaran da suka fara shiga gidan da kayan suka sake fitowa dauke dasu a kawunansu,kai tsaye suka nufoshi,ya tsaya cak yana dubansu
"Inna tace malam din baya nan,a ajjiye kayan a a waje har sai ya dawo" yasan sunan inna a bakin iman,ya tabbatar ummanta ce,sai ya ciro wayarsa don kiran iman din yayi mata bayanin cewa shine ya aiko,saidai kuma koda ya kira wayar a kashe take,don haka dole ya maida wayar aljihun nasa,ya kuma sa aka lode kayan cikin rumfar.
Ya bude motar yana shirin shiga ya zauna ya jirayi malam din saiga bullowar malam din,ya fahimci hakane saboda yadda daliban nasa keta masa sannu da zuwa,dawowarsa kenan daga wajen saukar qur'ani da akayi na daliban wata makaranta.
Kallon farko yaji malam yayi masa wani mugun kwarjini,dama kwarjinin malam din ba sabon abu bane ga duk wanda ya sanshi,saboda yadda qur'ani da tsoron Allah ya ratsashi,saiya qarasa ya russuna yana gida malam din,ya amsa gana binsa da kallo saboda baisan waye shi ba
"Dan samari daga ina?"
"Bassam ne" ya amsa yana shafa qeyarsa
"Ma sha Allah,to yayi kyau,ka qarasa masallaci muyi sallah,idan an idar sai ka sameni a qofar gida" kira malam din yayi yasa aka kawo masa ruwan alwala.
Sam sadiqu da suke shigowa layin a lokacin shi da amin bai lura da canzawar salon tafiyar al'amin din ba,tunda suka shigo layin yake hangen baquwar motar,zuciyarsa na gaya masa bassam ne,ilai kuwa ya hangi fuskarsa sanda yake alwala daga tsaye,duk ya rikice ruwan nata dawo masa yana bata shaddar jikinsa
"Ina zuqa sadiqu,nayi mantuwa" amin ya fada yana juya ya koma da baya,sam bazai iya hada numfashi da bassam din ba,bazai iya kallon fuskarsa ba,yana jin wani kishi na sukar zuciyarsa,hakan yasa ya yanke shawarar ya kauce daga wajen.
"Ina aminu ne?" Tambayar da malam ya yiwa sadiqu kenan sansa sadiq din ke zama gefan malam,wani side din ba wanda bassam yake zaune ba
"Tare muka shigo dashi,amma yayi mantuwa a shago ya kuma tun dazun" sai kawai malam ya gyada kai,ya gabatarwa da bassam ruwan randa me sanyi da aka kawo masa a kwanon sha,saidai bassam din yace ya qoshi,ba kuma komai ya kawo hakan ba,saboda sam bazai iya shan ruwan daba na roba ba.
"Malam bassam.....naji dadi da amsa kirana da kayi,ni din nan nine mahaifin iman,kuma a yadda al'ada ta tanadar.....da kuma addininmu,a duk sanda saurayi yaga yarinya yana so,zai fara turo magabatansa ne,saboda kiyayewar mutunci kima da kuma daraja ta kowanne gida,idan an bawa magabatansa dama.....zasu sanar masa yazo yaga yarinya,to a taka tarayyar da hajar duka babu wannan,banga laifinka ba,saboda bansan waye kai ba,ban kuma san daga inda kake ba,na tattara laifin na dorashi ga hajar,saboda ita tafi kowa sanin irin gidan data fito da kuma waye mahaifinta,kayi kusakurai da yawa,ka yita hidimawa diyata ba tare da sanina ba,wanda hakan kansa ya sabawa qa'ida da tsari,saidai nata laifin a idanuna yafi naka ...to duka ba wannan ba,abinda yasa nace maka kazo shine,inason shaida maka na dakatar dakai daga mu'amala da hajar,saboda nayi mata miji tuntuntuni,ko ita kanta bana jin ta sani,da haka ba zata faru ba,don haka nake baka haquri....wadan nan" ya janyo ledar gefansa da sadiqu ya shigo da ita
"Duka abubuwan daka taba bata ne,ciki harda wayar hannu,ka duba idan akwai abinda ka taba bata da babu shi a nan wajen kayi magana".
Wani gumi ne yake yankowa bassam,saboda bai taba tsammani ko kawo cew maganar da ta sanya malam ya kirashi kenan ba,wato rabasu zaiyi?,cikin tashin hankali ya motsa baki ya fara roqar malam din kan kada ya aikata haka,ya bashi daman gyara kuskuransa ya kuma bashi iman din ya aura
Murmushi irin na cikakkun dattijai malam ya sake,koda babu al'ameen bayajin zai iya baiwa iman bassam din,aure yakeso yayi mata na mutunci da siyawa kai daraja,auren qwarya tabi qwarya,kini sai kininsa
"Kayi haquri samari,na riga na bada hajar kamar yadda na gaya maka,kuma bama magana mu tadata,saboda shi alqawari abun tambaya ne ranar gobe......idan ka tashi tafiya ga kayanka nan,bama buqatar komai cikin abinda ka kawo din,ka sauka lafiya" daga haka malam ya miqe yayi cikin gida,sadiqu ya mara masa baya ransa fari qal,wannan abinda malam din ya aikata shine dai dai.
Sai da malam din ya gama duk abinda ya saba yi bayan shigarsa gida sannan yasa innar ta turo masa masa iman,wadda ta kasa ta tsare dama tana ta jiran jin abinda ga faru bayan xuwan bassam gidan,tunda a yanxun duka wayoyinta suna hannun malam,ana kiran nata kuwa kamar na tsikarinta ta miqe ta fito.
Cikin kwantaccen harshe malam yayi mata bayanin komai,ya kuma gaya mata cewa ita din an bayar da ita ga aminu tuntuni,shi ya nemi abar abun a hannunsa shi yasa suka qyale
"Nasan lamarin xai iya zamar miki mai wahala,to amma matuqar kika maida komai ba komai ba,zakiga komai din yazo miki da sauqi,tunda dai aminu ba baqonki bane,shaquwa sãbo da kuma fahimtar junan dake tsakaninku yasa mukayi sha'awar hakan ma,saboda haka ki tattara hankalinki waje daya,ku sake fahimtar juna,aminu kamar dan uwanki na jini yake,hakazalika bana jin zaki samu mijin aure tamkarsa,munsan halinsa ciki da bai,hasalima kusan fiye da rabi na halayyarsa rainonmu ne" kai inna ke kadawa cike da gamsuwa,itama sai yanzu hankalinta ya kwanta da hukuncin da malam din ya zartas
"Banason na sake ganin wani shirme ko kuskure makamancin wanda kikayi a yanzu ya sake maimaituwa,tunda na gama magana da yaron,na kuma fahimtar dashi,Allah ya sake hada kanku,ya tabbatar mana da alkhairi,tashi kije,ki kuma yita addu'a".
Da qyar iman ta iya riqe kanta sai data shiga dakinta,wani irin kuka ta saki mai sauti da amo,wanda saura kadan su malam din su jiyota,ta yaya zata iya fara rayuwa da bassam?,ta yaya zata iya rabuwa dashi?,yaya akayi bassam ya amincewa rabuwa da ita?,ina dukka tarin alqawuran da sukayiwa junansu shi da ita, just recently,me yasa malam zai mata haka?,me yasa ya amin za'a hada baki dashi a rusa farincikinta?,me yasa ya dage sai ya aureta?,wadan nan up ta kwana tana yiwa kanta,gefe daya sai ta samu kanta dajin matsanancin haushin amin,shine ya jawo komai,banda ya nuna yana sonta....banda ga karba kyautarta da malam yayi masa da za'a barta ta zabi wanda takeso,ta tabbatar da hakan.
Ta gefan al'ameen kuwa shima daban malam yayi kiransa
"Kayi saken da wani ya shiga gurbinka ya fara yiwa kansa aiki,yanzun dole sai kayi aikin gogeshi,duk da inaji a jikina cewa akasi ne aka samu,saboda haka aikin bazaiyi maka wani wahala ba......,ka sake kula da kyau,banda ka roqi alfarmar abarta ta qarashe makarantarta saboda watanni ne suka rage,da bana jin zaa rufa watan nan ban daura aurenku ba,ko a yanzu babu tabbacin hakan ba zata faru ba,Allah ya sake kiyayewa,ya hada kanku". Da wadan nan maganganun malam yayi tunanin cewa ya gyara komai,kuma komai zai hau kan hanya da kuma tsari,saidai ina.......akwai guguwa a gaba mai tarin qura,guguwar data jirkita gidan da duk wani tsari nasa gaba daya.
WASHEGARI.....kamar ba zataje makaranta ba don har qarfe shida da rabi tana kwance tana share hawayen da tun daren jiya ya gaza tsaiwa,daga bisani taji damuwa kamar zata fasa mata zuciya,ko banza idan taje din zata samu koda aron wayar da zasuyi magana da bassam din,taji ya akayi aka haihu a ragaya,sannan kuma tana da tabbacin samun shawarar wari daga munira,don haka ta sauko daga kan gadonta,ta fita zuwa tsakar gida,taja ruwa a rijiya,ta cika botiki takai bandaki,bata ko damu da tsaiwa ta kashe sanyinsa ba.
Sanda ta cewa inna ta wuce makaranta ba tare da tayi dukka ayyukan data saba ba ba kuma taci komai ba inna batace da ita komai ba,saboda tasan dole damuwa zata biyo baya,amma suna hange da hasashen tarin alkhairin da zai dorarma rayuwarta,damuwar tadan lokaci ce qanqani.
Cikin sa'a suka hade a bakin gate na makarantar kowa na shirin shiga,suna hada idanu kawai kuka ya qwacewa iman din,abinda ya tashi hankalin munira kenan,ta kama hannunta da sauri ta jata bayan ajujuwansu.
Kuka sosai take mata muniran tana kallonta bata ce mata komai ba,kamar yadda bata tsaidata ba,har sai data yi me isarta ta fara tsagaitawa sannan muniran ta magantu
"Ya kamata koma meye ki daure zuciyarki ki gayamin,saboda bazan taba sanin yadda zan kamo bakin zaren ba idan baki gayamin matsalar ba"
Handkerchief din data fito dashi daga aljihunta ta sanya ta share fuskarta,wadda ta hada ja sosai saboda kukan data kwana tanayi,kaf ta kwashe duk abinda ya faru ta shaida mata.
Tsaki munira taja,ranta yana suya da sake baci,haushin ameen ya kamata matuqa
"Babu wanda ke miki maqarqashiya da son ganin koma bayanki face amin,shine kanwa uwar gami,haka kawai mutum ya shigo gidanku ya muku kane kane ya rabaki da iyayenki,duk soyayyar da suke miki,ni ban yarda zasu iya tirsasaki ki auri wani haka kawai bisa radin kansu ba,sai don su faranta masa,idan zaki zage ki karta masa rashin mutuncin da zai cire duk wata soyayya taki dake zuciyarsa ki zage" kai iman ta girgiza
"Ni duka ba wanna ba,mafita kawai nake nema,banason na rasa bassam"
Gyara zama munira tayi cikin seriousness tace
"Akwai plan guda uku....,zamu bi kowanne a ciki,idan na farko baiyi aiki ba zami tsallaka na biyu har zuwa na uku.....na farko,zaki sanya bassam ya turawa malam iyayensa kai tsaye,su roqarma bassam ke,wala'alla girma da kimarsu yasa su cika mishi idanu ya kasa musa musu......idan wannan biyi aiki ba.......zaki je ki roqi ameen ya shaidawa malam ya janye,ki kwantar dakai sosai,ki masa dukkan wata kala ko kama ta ban tausayi......idan wannan baiyi ba,babu wani sauran option sai guda daya" ta furta tana daga yatsarta,idanunta akan iman
"Wanne ne?" Iman din ta tambayeta tanason jin qarashen bayanin muniran
"Maganata da na fara yinta a farko,ki rufe idanunki ki karta masa rashin mutuncin da zai tsigeki daga zuciyarsa,yaji bayason koda hada inuwa dake bare har igiyar auratayya ta hadaki dashi" kai iman din ke girgizawa
"Ba za'a kai nan ba in sha Allahu,kiramin bassam" ta fada tana tattara hankalinta kan jakar munira da take kyautata zaton wayar tana ciki.
Wayar ta miqa mata bayan ta cirota ta cire mata password din,da sauri da sauri ta zuba numbers din bassam din ta danna masa kira.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 22
Fitar sautin muryarsa cikin sallama kadai ya tabbatar mata ya kwana cikin damuwa ne,saboda yadda muryarsa tayi can qasa sosai,amsa masa tayi cikin nata laushin,ya kira sunanta da dan qarfi,abinda ya sanya zuciyarta ta qara karyewa,sai ta miqe ta matsa kadan daga inda munira take,hawaye na qoqarin silmiyo mata.
******BAYAN KWANA HUDU*********
Lokaci mai tsaho take batawa suna hira da bassam a wayar munira duk sanda taje makaranta,hakan ya rage mata damuwa sosai,a nan suka gama shirya ranar da zai turo mutanensa wajen malam,ta saka masa lokacin data tabbatar idan sunzo din zasu malam.
Ranar tun yammaci ta kasa sukuni,tana tsakar gida tana yankan alayyahun miyar taushen data dora,mahadin alkubus da sukayi a daren amma hankalinta gaba daya baya jikinta,inna da suke aikin tare tana lure da ita,tana mamakin yadda gaba daya iman din ta sauya kamar wadda aka yiwa juyen qwaqwalwa,har yanzu ta fuskanci babu alamun gyaruwar mu'amala tsakanin iman din da lamin,abun yana damunta sosai,saiai ta duqufa da addu'a,tana ta gayawa Allah,koma meye Allah ya kawo qarshensa,ya warware cikin sauqi.
Zuwa sanda ta kammala sallar magariba kuwa kamar sabuwar sojar dake koyon parade a karon farko,taji shigowar malam,ta kuma ji fitarsa,amma daga nan bata sakejin kowanne motsi ko kuma tashin wata maganar ba har zuwa wayewar gari.
A washegari a gurguje ta dinga komai,so take ta isa makaranta ta kira bassam din a wayar munira taji me ya faru?,ko baqin basu zo ba?,saidai sanda ta jefa masa tambayar ya tabbatar mata sunje,amma babu wata nasara,domin kuwa,kalar bayanin da yayi masa shi dashi irinsa ya maimaita musu.
Hankalinta ya tashi qwarai,amma ta danne ta dinga kwantarwa da bassam din hankali,inda daga qarshe yace sunyi shawara da abokinsa ya sake turawa dai kamar bayan kwana bakwai.
Hakan kuwa akayi a karo na biyu,abinda ya faru wancan lokacin yanzun ma shi ya sake faruwa,still dai malam ko kiranta baiyi ba bare yayi mata wata magana,daga bakin bassam din taji sunzo,a ranar kusan qaramin hauka sukayi ita da bassam din,daga qarshe suka sake yankewa cewa zai sake dai turawa a karo na uku.
A ranar ne tun bata tambayi bassam ba tasan lallai sunzo,wani qaton kuskure suka tafka a wannan karon,siyayya suka shirgowa malam.din ta fitar hankali kamar za'a bude shago,abinda yayi matuqar bata ran malam din,bashi kadai ba.....harda sadiqu,yayi musu fata fata 'yan aiken,sannan ya dawo ciki ya sanya aka kira mishi iman din,jikinta a sabule ta shiga rumfar malam din,saita taras da al'amin a zaune a gefansa,kanshi a qasa.
Dauke kanta tayi daga inda yake,tana jin wani abu me kama da haushinsa yana kamata,shine sila,shine ya jawo komai,yanzun kuma me yakeyi a wajen malam din?,saita samu waje ta zauna a hankali itama kanta a qasa.
"Tsahon zamanku dashi baki shaida masa waye ibrahim khalilu ba?,to idan bai sani ba ina fatan saqon dana aike masa dashi ya riskeshi,hajar.....idanma abun duniyarsa yake rudarki gwara ki fiddashi daga zuciyarki,ni khalilu ba makwadaici bane,kima da darajata itace gaba da komai,daga yau........indai nine mahaifinki na soke makarantarki.......sannan kuma na sanya ranar aureku keda aminu wata biyu masu zuwa,sati takwas kenan,sadaki kawai nakeso kaje ka hada,daga dubu ashirin zuwa abinda Allah ya hore maka".
Malam din yana kaiwa nan ya miqe cikim bacin rai yana gyara malum malum dinsa,taju daya yayi baiyi na biyu ba iman ta miqe hadi da sakin qaqqarfan kuka,sannan ta sulale a wajen,ko waiwayota malam din baiyi ba yaci gaba da takawa ya fice a rumfar,hakan ya baiwa inna damar yunqurowa,hannunta dauke da murfin samira data sakawa malam abinci,wanda ko kusa iman din bata ankara da tahowarta ba bare abinda ke hannunta ba sai qarar saukar murfin a hannun amin da yayi hanzarin tare bugun da hannunsa bayan ya ankara da tahowar innar,daidai qashin tsintsiyar hannunsa,ya hadu ya bada wani sauti qwalll!.
Idanunsa ya runtse saboda yadda zafin bugun ya ratsashi,sai a sannan iman ta ankarata,cikin azama tayi bayansa saboda samun mafaka ta tsaya tana rarraba idanu tare daci gaba da kukanta,wanda ya hasala inna,ta sake yunqura ta wurgawa iman din murfin,ya kuwa daki kanta
"Gafara aminu ka bani waje.....banason abinda bai shafeka ba na hada dakai,matsa ka bani waje,imani......ashe ke BUTULU CE KUFAN WUTA?,sakayyar da zakiwa aminu kenan?,kukan auren aminu kike saboda tsantsar butulci?" Inna ta fada cikin tsananin bacin rai,hankalinta a tashe kan hannun amin data buga
"Don girman Allah kiyi haquri inna,bada zafi za'a fahimtar da ita ba" da qyar ya lallaba inna ta fita daga rumfar malam din,saidai fada take sosai kamar zata ari baki,abunda basu saba gani daga gareta ba.
Shuru dakin ya dauka bayan ficewarta,babu komai sai sautin kukan iman din,a hankali ya matsa gaba ya bada space a tsakaninsu sannan ya waiwayo insa take tsayen,kuka take sosai kamar zata hadiye da zuciyarta,suna hada idanu ta sulale ta durqusa gabansa,cikin madaukakin kuka harshensa yana hadewa tace
"Don girman Allah ka janye ya amin,don Allah ka gayawa malam ka fasa,ka barmu mu auri juna nida bassam" suka sosai kalamanta sukayi masa qasan zuciyarsa,ya lumshe lumsassun idanunsa sannan ya budesu,bayajin zai iya zuwa ya tunkari malam yace masa ya fasa aurenta,bazai iya wannan aikin ba,amma kuma a yanzun baisan ta yadda zai lallabata ta daina wannan kukan dake ci masa zuciya ba
"Ya isa iman,ki daina kukan haka,kije zamuyi magana" wani abu ta hadiye tana dan jin relief yana saukar mata,sai ta tashi a hankali kamar yadda ya buqaceta ta fice daga dakin,yayin da shi kuma ya bita da kallo.
Idonsa ya runtse gam tare da kama gashin kansa ya riqe da qarfi,wani radadi ciwo da zafi yakeji tsakiyar qirjinsa,bai taba yarda da cewa son maso wani azaba gareshi ba sai yanzu,bai taba yarda da wannan maganar ba sai a yanzun,inama zai iya,inama zai yiwu,da tabbas ya cire wannan bassam din daga zuciyar iman din ya dasa kansa,bai taba kawowa ko a mafarki iman din zata gujeshi ba.
Cikin kwanakin gaba daya gidan ya zama wani iri,da sadiqu da inna gaba daya fushi suke da iman din,yayin da malam keta qoqarin ganin abubuwa sun daidaita ta hanyar nusashshe da ita da kuma janta a jiki,ta bangare daya kuwa ita gaba daya bata wannan take ba,tanata qoqarin komawa ne kamar da tsakaninta da amin din saboda ta samu yayi mata abinda takeso,ya tausaya mata ya janye ya barta da bassam,tana da tabbacin furtawa janyewarsa ce kadai abinda zai samu dama da kuma lasisin kasancewa tare da bassam a matsayin miji da mata.
Koda yaushe idan ta tada maganar yana cewa ta bari zasu tattauna,dawo da kusancinsu da take ta qoqarin yi ya masa dadi,saboda ya sanya a ransa ta wannan hanyar zai sanya kansa cikin zuciyarsa a sannu a sannu,sannan idan tafiya ta fara nisa zata haqura haka yake fata,don haka ta bangare daya ma tuni ya sake dawowa da aikinsa haiqan na dinki,duk da malam yace sadaki kawai yake buqata,amma bazai qyale iman dinsa babu sabbin sutura kamar kowacce amarya ba,uwa uba yana son ya samar musu gidan da zasu zauna da kanshi bawai malam din ya basu ko ya samar musu ba,don haka ya fidda ajiyarsa da yaketa yi,wadda yake saka ran amfani da ita idan ya samu gurbin karatun da yaketa fafutuka,daya duba kuwa kudade ne masu yawa sa zasu isheshi yayi abubuwa masu yawa dasu.
Sam iman bata gane wasa kawai yake mata da hankali ba sai da ya shigo da wasu atamfofi ya kirata yace ta zaba guda biyar a ciki.
Atamfofin ta kalla sannan ta sake dubansa gabanta yana faduwa
"Na menene kuma had biyar?" Murmushi ya saki yana dubanta
"Ta ya zaayi ina tailor guda nabar amaryata babu sabon kaya?" Zumbur ta miqe hawaye na cika idanunta,hankali take take dubansa
"Ashe dama yaudarata kakeyi?,ashe ba zaka iya yimin abinda nakeso ba?" Zaiyi.magana cikin daga murya tace
"Kada ka sake kacemin komai kaji malam" daga haka ta juya da gudu zata fice,sukaci karo sa sadiqu,saita gewayeshi ta fice,ya qaraso dakin a fusace
"Me yarinyar nan take gaya maka?".
Ganin a zabure sadiqun yake,sanna ransa a bace yake,zai iyayi mata komai sai yace
"Ina ruwanka?,zancan miji da matarsa?" Kai ya girgiza ba alamun wasa a fuskarsa
"Tsawa fa naji tayi maka daga shigowata tun dahga farkon soro"
"Koma meye babu naka a ciki" amin din na kaiwa nan sadiqu bai saurareshi ba yayi cikin gidan,amin ya miqe yabi bayansa,saboda ya tabbatar yadda ran abubakar ke a bace kwanakin akan iman din,dama kawai dama yake buqatar samu a kanta lallai akwai abinda zai faru.
Dai dai sanda ya isa kuwa tuni ta samu marin farko daga wajen sadiqu,yana shirin qara mata na biyu amin din ya riqe masa hannu,yana zuwa dakin dama ya saka kanshi da sauri,abinda ya mata rabonsa da aikatawa,saboda sam babu wanda ke shiga dakinta sai inna.
Qarar data qwalla ita ta fito da inna dake uwar dakanta,dafe da kuncinta amin ya sameta hawaye wani nabin wani,zai sake kai mata mari na biyu amin ya riqe hannunsa cikin bacin rai,sadiq din na qoqarin qwacewa yana sababi,tsaiwar inna kadai a wajen ta fahimci abinda yake faruwa
"Ka barshi aminu yayi mata dukan tsiya,shashasha BUTULU,koda baikai ga dukanta ba ni gab nake da na saka ua daketan dama ai,duk irin takunki ina sane dashi,idanuwa kawai na zuba miki" inna itama ta dora da nata sababin,da qyar ya fiddasu daga dakin kowa ya koma nashi ranshi a bace,sannan ya tsaya bata baki,amma ko kallonsa batayi ba har ya gama ya fita,yana fitan ta sakawa qofarta sakata ta koma ta kwanta,tana kin haushi da tsanar amin na shigarta,ko babu komai shine yayi silar dukanta da ya sadiqu yayi,sabida ta manta rabon da ya sanya hannu a jikinta ya daketa.
A daki ya cimma sadiqu yanata huci
"Baka kyautamin ba sam sadiq"
"Nikai baka kyautamin ba,dama irin abinda take maka kenan baka taba gayamin ba?" Kai ya girgiza
"Bata taba yimin ba,kuma kota taba din ma meye naka a ciki?,ina ruwanka,tun asali dama baa shiga tsakaninmu ai kafi kowa sani" kansa ya kada
"Wannan abun ba irin tarayyarku ta baya bace amin,ka daina maida wannan abun ba komai ba"
"Wannan ai ba dabara kayi ba,duka babu abinda zai gyara saidai ma ya lalata,zaka sake dasa mata qin abunne a zuciyarta maimakon ta sassauto"
"Tayita qin mana,ina ruwan wani,aure ne dai sai anyishi,ko tanaso ko bataso,ko gawarta ce sai an kai"
"Subhanallah" amin ya fada yana jin babu dadi har cikin ransa
"Kada ka sake fadin haka,ita zata zauna zaman auren ba wani ba,dole idan taci gaba da qi a haqura a qyaleta,ko cikin addini babu auren dole"
"Eh,amma akwai auren cancanta ko?,kai kana tunanin malam zai janye maganarsa ne?,daga gurinka take samun fuskar yin dukka wadan nan iskace iskancen wallahi" daga haka sadiq din ya miqe abunsa ya tura toilet dinsu ya shige.
Zazzafar iska ya fitar daga bakinsa,gaba daya kansa ya daure,zuciyarsa babu dadi,komai ya daure masa waje daya,iman din tayi sauyawar dako a mafarki yaga hakan za qaryata,wai dukka soyayyar waninsa ce data danne tasa a zuciyarta ko kuwa akwai wani abu na daban da baisan dashi ba?.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 23
MATAKI na sauyawarta ta dauka, option na qarshe da take ganin tana dashi,tun daga lokacin ta soke gaisuwa tsakaninta da ameen,ko magana bata bari ta hadasu saidai idan a gaban malam inna ko sadiq ne,bai taba gayawa kowa ba,sai yama tsiri fitar wuri wajen dinkinsa,ya wuni har dare a can yanayi sannan ya dawo gidan,hakan ya aake qaranta haduwarsu,ya kuma zame masa alkhairi,saboda nan da nan yayi dinkuna masu tarin yawan gaske,kudi kuma suka dinga shigo masa.
Duk wata hidima da take masa a yanzu ta sabule hannunta,babu abinda yake hadata dashi,hatta da abinci ta daina kai masa,babu irin abunda inna batayi mata ba kan batun kai abinci amma ta qeqashe,ita kanta innar kallon iman din take kamar an canza mata ita,saidai bakinta bai fasa addu'a akan iman din ba.
********Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana ajjiye kwalbar turaren da ya gama fesawa a jikinsa,sai yanzu yaji dadin jikin nasa bayan yayi wankan,saboda gajiyar da ya hadawa kansa yau din tana da yawa.
Da baya ya koma yana shirin zama yaga an dage labulen,iman ce dauke da kwanukan abincinsu guda biyu,bazai iya tuna ranar yaushe bane rana ta qarshe da ta shigo dakin har ya ganta kamar haka,amma ko a yanzun idan ka dubi fuskarta da kyau zakasan cewa tilas akayi mata.
Tana ajjiye kwanukan ta juya abinta zata fice ba tare data ce masa kanzil ba,kusan ha saba da wannan sabuwar dabi'artata,gaaba take dashi sosai,don ko kallon inda yake batayi,to amma ayau din yanason suyi magana ta qarshe kuma ta fahimta dashi,don gaba daya salon rayuwar da takeso su shimfida batayi masa ba,don haka cikin zafin nama irin ta zaratan maza yayi wuf ya isa gabanta,ya kuma sanya qafarsa ya tura qofar dakin,ta kuwa rufe ruf,jamlock ya shige
"Meye haka?" Ta fada cikin wata iriyar tsiwa tana dubansa kai tsaye
"Ta yaya zaki tafi kibar angonki?,bayan kwana da kwanaki bai samu kun kebe ba,kuma koda kun hadu a tsakar gida ba'a kallonsa ko a gaisheshi?"
"Wai gaisuwata dama kake zaman jira?,aiko wallahi zaka bushe baka sameta ba,ka matsamin na wuce" wadan nan ba baqin kalamai bane a wajensa,saboda tuni ya saba jinsu,amma a yanzun shi ba wannan bace a gabansa
"Ni ban taba ganin inda ake soyayya dole ba,duk inda aka ce ba'a sonka ya kamata kayi aiki da hankalinka ka gusa daga wajen tun lokaci bai qure maka ba,naci babu abinda zai haifar maka,wanda bai sonka kawai bai sonka,saika qara gaba ka lalubi wata ai ko,ka matsan na wuce ina da abunyi". Sosai yagi qoqarin hadiye maganganunta,tare da danne duk wani reaction da zasu bada saman fuskarsa
"Babu inda zaki,amaryata nakeso gani da gaske" wata irin harara ta watsa masa kamar idanunta zai fado
"Wace amaryar taka?" Saita zubda yawu gefe
"Allah ya kiyaye ya tsareni,ni in aureka?,na aureja nace na auri meye?,wallahi da na aureka gwara na mutu,kai koda an daura an kaini saina caka mana wuqa dani dakai din duka mu mutu" dummn kansa yaji yayi da kalamanta ba qarshe,ya lumshe idanunsa ya furta
"Ya salam,Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla" a fili,saidai muryarsa can qasa,wai dama haka mata suke?,haka suke canza alqibla lokaci guda?,iman ce fa wannan,iman din da ya gama sanin quruciyarta,ya koya mata ababe masu yawa cikin rayuwarta,yau ita take iya tsaiwa a gabansa ta gaya masa wadan nan maganganun.
Wani irin matsawa yayi da baya cikin fushi da hanzari,ya sanya hannunsa ya dauko kakkaifar wuqar da yasha lemon fata da ita tunda safe,ya dawo gabanta ya lalubi hannunta ya sanya mata wuqar a zafafe
"Bismillah,ki fara aiwatarwa tun yanzu,ga wuqar nace,ki nunawa duniya ke cikakkiyar mara hankali ce mara qwaqwalwa ta gaske" ya fada cikin wata irin tsawa data kada hanjin iman din,ya ritsata da idanuwansa da suka sauya launi saboda bacin ran maganarta da yadda zuciyarsa ke tafasa,jikinta ya dauki kyarma,sai ya sanya hannu ya fisge wuqar ya kuma yi jifa da ita,taku uku ya qara zuwa gabanta,tazarar dake tsakaninsu tayi qaranci qwarai,har suna iya shaqar numfashin juna
"Ko a yau aka daura mana aure dake zan iya datse igiyar aurena dukka ukun dake kanki.......tunda har zaki iya daukan rai lallai ba shakka na tabbatar wancan mutumin ya cire dukka imanin dake zuciyarki tausayi da kuma jin qai.....ba abun mamaki bane tunda tuntuni ya cire miki ganin girman maganar iyaye. Tun farko bani da sha'awar auren macen da bata sona koda kuwa wanne irin so nake mata,rashin zarrar da zan bijirewa maganarsu malam saboda su din iyayena ne ya sanya na haqura da tsarina na dauki nasu......badai saboda ina sonki ne ya sanya kike dukkan wasu abubuwa da kike ba?,ki bude kunnenki.....daga yau,ni muhammad amin,na rabu dake har abada,idan kinso kije ki auri billgate" daga haka ha kewayeta cikin wani irin zafi da har tan jin wani irin huci sanda ya giftatan.
Cikin daren juyi ta dinga yi tana hango abinda ya faru tsakaninta dashi,wani irin fushi da bacin rai data hanga daga gareshi
Washegari da safe saiga kiran malam,a lokacin ta samu bacci ya dan dauketa bayan ta shaidawa bassam duk abinda ya faru,ya bata qwarin gwiwa tare da kwantar mata da hankalin lallai nasara tana zuwa.
Tun kafin takai ga zama da dogon hijabinta malam din ya fara sauke mata ruwan bala'in fada,fadan daya rudasu gaba dayansu ita da amin dake zaune a wajen
"Idan ma ita ta tursasaka ko ta sakaka kazo ka fadi cewa ka janye a bata wanda takeso.....to inamai shaida maka daga kai har ita baku isa ba,bazan kuma fasa abinda nayi niyya ba,dakai da ita din gaba daya mu zuba nida ku,tunda haka kuka zaba,ku tashi ku bani waje shashan banza" wannan itace magana ta qarshe da malam din yayi dasu.
Sati guda a tsakani suka wayi gari da baquncin yaa gana,yayar malam kenan,dukka gidan babu wanda baiyi mamaki ba,banda al'ameen da yasan da zuwan nata,hasalima yasan maqasudin zuwan nata,tunda shine sila,rabonta da garin kano an jima,a qalla ba'a qasara an kusa shekara biyar ko shida.
Daga inna har iman data rame ta fada saboda damuwar da take ciki suka tashi haiqan wajen tarbarta da abinci da sauran abubuwa,hira sosai suka sha da inna harma da iman din mutuniyarta,saida la'asar bayan iman din ta zuba mata ruwa a buta tazo ta sanar mata sai ta dubeta
"Wai duk meye silar wannan ramar ta hajar?" Ta jefawa inna tambayar,tabe baki innar tayi
"Gatanan,ki tambayeta" maida dubanta tayi ga iman,saita sunkui da kai hawaye suka fara tsatstsafo mata,tana jin ranta yana suya
"Ke na tambaya ai ba hajar ba"
"Dan uwanta za'a bata,aminu,wanda suka taso gida daya,cikin mutunci da girmama juna,wanda yasan darajarta,tayi tsallen albarka ta dauko wani bare,wanda dukiyar da yake da ita ko ubanta baida rabin rabin rabinta tace shi takeso,ban sani ba ko abun hannunsa ke rudarta" inna na kaiwa nan iman din ta juya da hanzari ta fice a dakin,hawayen da take riqewa suna sauko mata,wato kallon da suke mata kenan?,babu wanda ya kalli cewa soyayya ce sila a cikinsu?.
Batasan yadda suka qare da inna ba,don bata fito daga dakin ba kwata kwata sai da zata daura alwalar magariba,shima tanayi ta koma dakin,sai wajen qarfe goma na dare har tana shirin kwanciya taji anyi knocking qofarta daga tsakar gida
"Ki fito inji malam ki sameshi a rumfarsa" muryar ya sadiqu ta ratsa kunnenta,take ciwon da kanta yake ya sake hauhawa,haka ta miqe a daddafe ta zura hijabinta ta fito zuwa rumfar malam din,gabanta na wani irin faduwa.
Daga gefe guda ta rakube jikin yagana,kamar wadda zata shige cikinta,dukka al'ummar gidan ce cikin fakon,kallo daya malam din yayi mata ya dauke kansa,sannan ya fara magana
"Allah ya sani nayi dukkan iya bakin qoqarina don ganin na baki ingantacciyar rayuwa,na kyautata gobanki amma ban samu hadin kai ba kwata kwata daga gareki ba,kin sanya kwalli kin murje idanunki,kin kuma gaza gane ko fahimtar abunda mu muke hangar miki........shikenan,zan miki yadda kike so din saboda darajar yagana dashi kansa aminun da yakai qarata wajenta yakuma jajibota ta taso ta taho,zan baki yaron da kikeso,amma ba bisa zabi ko son raina ba......zan bashi aurenki amma bisa sharadai kamar haka,sharadi na farko,aurenki dashi babu yaji,babu saki,sharadi na biyu,idan kika saka qafa kika bar gidan nan banason ganin wulqawarki a gidan nan bare naga kina zirga zirga da sunan ziyara,mun yafe masa ke,na uku babu ruwanmu da duk wata matsala da zata taso miki ko ta tunkareki,idan ma hakan ya faru to ki nemi wani gidan amma dai ba nan ba......."
"Amma malam....." Amin yayi qoqarin datsar malam din,saboda jin girman sharadin da yaketa yankowa iman din,da sauri malam ya dakatar dashi
"Idan kace wani abu sau ranka ya baci,tunda kun gama naku kun tursasani saiku barni nima nayi nawa" maganar ta sanya alameen komawa yayi laqwas,saboda bai taba jin malam din ya gaya masa hakan ba sai yau,karo na farko kaf tsahon rayuwarsu tare,yagana.batace komai ba,duk da.sharuddan sunyi tsauri da yawa,tana fatan iman din taji girma da.nauyin sharuddan tace ta janye,wannan dalili yasa batace komai din ba.
"kin yarda kin amince?" Malam ya tambayeta da kakkausar murya,dukka sai idanu ya koma kanta,kowa fatansa a wajen tace a'ah,kowa addu'ar da yakeyi cikin zuciyarsa kenan.
A hankali zuciyarta ke wassafa mata tare da tariyo mata kalaman bassam,irin soyayya da Zai nuna mata,kulawa da kuma qauna tare da daukaka darajarta a cikin mata,ta tuna yadda suke begen juna ita dashi,saita daga kanta a hankali zuwa sama alamun
"Eh" wani irin runtse idanu amin yayi wanda ta saukar masa da ciwon kai lokaci guda,saboda yadda jijiyoyin kansa suka harba sanda ya tsinkayi amsar da iman ta bayar,yana iyajin wani zazzafan huci da sadiqu dake kusa dashi ya fitar,alamun zuciyarsa zafi kawai takeyi,kamar anyi ruwa an dauke haka wuta ta daukewa kowa dake dakin,kalaman malam suka sake ratsa shirun
"Ki kirashi ki shaida.masa cewa......rana ita yau yazo da sadaki a daura muku aure,yazo da shaidunsa biyu sun isa,daga nan ya daukeki ku wuce" ba iman ba,hatta da ya gana saida maganar malam din ta girgizashi,wanne irin hukunci ne haka tsattsaura bayan wanda ya furta kuma dazu,a rude iman take bin malam din da kallo,tana jin maganar tasa kamar a mafarki,a sadaka malam zai bada ita kenan?
"A'ah malam,ba za'ayi haka ba,don bakason mijin data zaba hakan ba shine zai sa ka bada diyarka baka binciki waye shi ba,sannan ka dauketa haka ziqau ka bada ita babu komai kamar sadaka,ba lefe babu dukka wasu kayyayaki da al:ada ta tanada" duban ya gana yayi
"Me zan aikata kuma bayan wannan?,kina tunanin a yanzu akwai wanda zaka tunkara kan neman sanin sahihiyar halayyar me kudi ya gaya maka gaskiyarsa tsakaninsa da Allah?,abune mai wahalar gaske,kaya kuma ya gana da kike magana a kansu,keda kanki kikace al'ada,al'ada kuma ba addini bace,dama a addinance shine zai bata wajen zama,wajen zama kuwa ya hada harda kayan daki"
"To amma ita binta ai zata sanarwa danginta zata aurar da diyarta ko?"
"Babu wanda zan gayawa,yadda ta zabarwa kanta kenan,don haka bazan dagawa kowa hankali ba,tunda shi ta zaba kuma an bata me yayi saura?,wanne muhimmanci muke dashi?,me zamu tsinana mata" inna ta fada tana miqewa tsaye,ta fara takawa tana barin falon,batason taci gaba da zama bare hawayen da takejin suna tsatstsafo mata su samu zubowa,tun dazu take dannesu,batason su zubo bare su zamewa iman din bala'i cikin rayuwarta,tausayin iman din takeji na yadda soyayya ta rufe mata idanu,tun bata gama sanin duniya ba,na yadda tabar lu'u'lu'u ta dauki jan qarfe,bata jin a duniya iman din zata samu mijin da yakai amin nagarta da komai da komai,tabbas diyartata ta tafka babbar asara,a yau kuma a karon farko cikin zuciyarta taji ta buraci inama ace tana da wata diyar bayan iman,da babu ko shakka koda batakai munzalin aure ba ta wanketa ta bawa amin ita,kallon fuskarsa da tayi sau daya bata qara marmarin kalla ba,tabbas dukkan abinda yayi yayi shine saboda tsabar juriya da qarfin hali irin nasa,amma idan kayi nazarinsa da kyau zaka karanci zallar tashin hankali da gigita da ya tsinci kansa a ciki.
Inna na fita sadiqu ya miqe ya mara mata baya,al'ameen ya miqe a daddafe shima yana lalubar hanya malam ya zaunar dashi
"Duk da irin qiyayyar da hajar ta nuna maka.....amma ko sau daya baka taba nuna bakason auren nan ba,baka taba musu damu ba,hakanan baka taba bijirewa umarninmu ba,kai da kake bata tsatsonmu ka fito ba,babu abinda zance dakai saidai nace Allah yayi maka albarka,ya baka mace ta gari wadda zakayi alfahari da samunta" kansa a qasa ya amsawa malam din,sannan ya miqe a hankali yana ficewa,ya gana tana binsa itama da addu'a,ranta duk babu dadi,saboda duk wanda yasan iman a dangi yasan al'ameen,yasan kuma nagarta irin tashi da halin dattakonsa.[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 24
Ba qaramin kai ruwa rana akayi da malam ba kafin ya amince ya saurari ya gana,ya qara bikin zuwa sati uku masu zuwa,don ya rantse ya maya cewar ba zata qara masa wata guda a gida ba,saboda shi kam bazaici gaba da zama da yarinyar da tafi qarfin umarninsa ba,wannan furuci shike daga hankalin iman,bataso ko sau daya taji malam ya fadi hakan.
Munira da tasan yadda komai ya wakana da sauran qawaye da basu sani ba duniya sabuwa,duniya ta samu,nan take aka soma shirin biki gadan gadan,bassam ya sakar musu komai,yace su tsara komai,su fadi dukkan abinda suke buqata kada suji shayi ko wani abu,ya sakar musu bakin aljihu iyaka, events events sai da suka tsara na kwanaki bakwai curr,kuma kowanne kudi za'a kashe ba qarami ba,saidai duk wannan abun malam yace ba cikin gidansa ba,hakanan ya gana ta dauki ragamar komai ta maida gidan wani dan uwansu dake daura da unguwarsu,ya bawa iman din daki guda,sai data koma gidanne ma taji tadan ware,saboda ta daina ganin mugun kallo daga inna,wanda take aika mata dashi duk safiyar duniya har zuwa faduwar rana,suka kuma zame hannunsu daga duk wani abu daya danganci bikin,don malam ma yace bashi da kudin da zai siya mata kayan daki a lokacin bare kayan kitchen,yadai siya katifa botiki buta tsintsiya da labule,ya kuma siya mata fulasai da tukwane.
Munira ce ta tseguntawa bassam abinda ake ciki,ranar saiga kira daga bassam din cikin sabuwar dalleliyar iPhone 13 pro max
"iya abinda suka siyamin din ya isheni,dashi kuma zan tafi" amsar data bashi kenan ta katse wayarta abunta,ranta ya baci sosai kan me yasa muniran zatayi mata haka?,koda tazo take mata maganar cikin bacin rai sai tayi dariya
"Wallahi wallahi ya zuba miki komai a gidanki,kuma ina da yaqinin babu wanda yasan shine yayi miki,to meye a ciki wai?,ai shima yasan basuson auren ne shi yasa akayi miki haka,amma ki kwantar da hankalinki,komai zai wuce" kai iman din ta gyada,duk da cewa wani lokaci idan shna hidimarsu takan manta ta yadda za'ayi auren nata,amma duk sanda ta tuna sai taji jikinta yayi sanyi
"Inajin kamar na fasa auren nan munira,gaba daya daga inna har malam sun jingine ni,kamar ma basa sona" idanu munira ta fitar
"Ashe baki da hankali?,don fa zaki aura,to idan baki sani ba bari na gaya miki,kudi sune qare magana,idan kana da kudi zaka iya siyan komai,zaka iya mallakar komai,ciki harda soyayyar mutane da farinjini,ke har mutunci a yanzu a wannan zamanin kudi suna saiwa mutum shi,bari ki gani,wuyarta ki shiga gidan,sukaga kuna zaune lafiya qalau,kuma abubuwa na shiga da fita daga hannunki komai zai canza,zai zama tarihi kamar ba'ayi ba"
"Na yadda lallai bakisa waye malam ba......babu abinda ke iya canzashi a duniya idan ba gaskiya bace" ta maidawa munira amsa tana kallonta
"Kinga,kada fa ki damu,yau da gobe bata bar komai ba,matso kiga kayan da bassam ya zabar muku,tunda ke kinqi sakin jiki aje a zabi komai dake" ta bude wayarta tana nuna mata kayan masu azabar tsada daya tilar mata da sunan lefe,gefe guda kuma ga kayan dukka events din guda bakwai din,kowanne anko sukayi ita da bassam din,kuma a dinke suke,kana gani kasan anci mutuncin naira a wajen.
Kudi sosai ya ajjiyewa iman din na gyaran jiki da sauransu ta hannun muneera,da kudaden tazo a hannunta tana nunawa iman din
"Yanzu ina zamu ayi miki gyaran jiki sharp sharp na kwanakin nan da suka rage,yadda zaki sake fita"
"Amaryar kb global enterprises"
"Inane haka?" Muneera ta tambayi daya daga cikin qawayensun da tayi magana
"Ai babu inda zamu samu fiye da yadda mukeso irin kamfanin AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISES"
"Babu wasa fa,kinsan mrs bassam ce,duniya zata daukaki bikin nan,dole ne mukaita inda zaa fita kunya,wadanda suka san abinda sukeyi"
"Haba malama,kinfa sanni,ita ta yiwa sakina gyaran jiki?"
"Yes.....nafa tuna,sakina tasha kyau gaskiya......anyita maganar yadda jikinya yayi kyau wallahi cikin qawaye,ga yadda jikinta ya dinga ya dinga fidda wani irin qamshi,ni kaina sai da na tambayeta wanne turare ne,amma kamar tana saida kayan amarya set na kayan qamshi ko?"
"Abubuwan da suke samarwa fa suna da yawa,kinga suna da
Turaren wuta from chad
Sandal flakes
Kajiji
Yellow sandal
Mufaddal.
Senegalese Kajiji
Couscous.
Green sandal.
Sudanese mix.
Shek Bakhur.
Sandal coconut.
Dorot
Hadut.
Gabgab.
Sandal rose.
Green fruity.
Sandal bange.
Kajiji balls.
Sandal balls.
Aroosa.
Khumra
VIP Khumra
Royal princess oil perfume ne
Hair kulacca
Sudanese kulacca na jiki
Sudanese scrub and dilka
Bath fragrance (turaren wankan)
Carpet and curtains perfume
Wardrobe balls
Sai kuma kayan gyaran mata kamar
Maganin infection
Maganin mata 👇🏽
Tsimi
Tula syrup
Tabaje
Kurman namiji
Pussy dessert
Silky syrup
Bata gaban kishiya
Hatsabibin gari
Zumar Chad
Tsimin tula
Tula juice sweetener
Ciccibi
Kaza
Zumar bita zaizai
"Kai,amma matar ta hadu,duk ina kikasan wadan nan kayan nata?"
"Kai kayanta ai dar ne,auty na duk wani qamshi ko gyara da zakiga tayi a maryar kb takeyi,duk sanda mijinta zai dawo daga spain acan ake mata gyaran jiki,karkiso kiga gift din da mijn ke bata idan ya dawo" shewa suka sanya,muneera tace
"Bani number dinta,can zamu kai tamu amaryar a hada mana ita"
"Ok,08067558902". Nan take muneera tayi serving.
Sanda yagana ta tashi komawa maiduguri taje ta dawo kafin satittikan bikin su cika,da kanta ta kira iman din ta sakeyi mata jirwaye da kamar wanka,don sanyi jikinta yayi sanyi,amma kuma babu alamun zata janye daga auren bassam
"Karki dauka kamar na daure miki gindi ne kije ki auri wanda kikaga dama,a'ah....nayi hakane saboda yadda na tsani auren dole,saboda shi yagi sanadiyyar rasuwar jikata balaraba,babu abinda yafi bin umarnin iyaye dadinkoda kuwa ka fisu gaskiya" da wanna kalaman ta tafi tabar iman.
**********Katafaren falone wanda idan ka kirashi da aljannar duniya bakayi kuskure ba,saboda yadda ya wadata yaji dukkan wani kayan alatu na rayuwa,wani abunma idan ka kalla kasan harda nuna fariya a cikinsa,duk kuwa da cewa arziqinsu yakai suyi koma meye,amma falon sak samfurin irin falukan da masu kudin qasashen larabawa ke ginawa kansu.
Babbar macace mai tsaho da kuma kauri,sanye da wani dandatsetsen lace da yasha ruwan stone tun daga sama har qasa,qafafuwanta sunsha jan lalle har zuwa yatsun hannunta,tana zaune saman kujerun alfarma dake falon ta dora qafa daya kan daya,'yan aikine keta hidima da ita,saidai babu wadda ta daga idanu ta kalla,ta bada himma kan canza channel tv daga wada take kai zuwa wata,fuskarta kwata kwata babu annuri ko kadan.
Kyawawan labulayen parlor din aka daga gami da sallama cikin muryarsa me zaqin nan,zaqin da har yaso yayi yawa ta fita daga ta maza zuwa sigar muryar mata irin masu dan babbar muryar nan.
Bassam ne sanye da qananun kaya,idanunsa sanye da qwabjejen baqin glass daya haska farar fatarsa,ya doso inda matar take zaune yana sallama.
Ciki ciki ta amsa masa,yana zama dukka masu aikin suka watse,suka barsu su kadai cikin falon
"Barka da hutawa" ya fada cikin sigar dake nuna boko tayi matuqar ratsashi,sai data ajjiye remote control din a gefanta,sannan ta tattara dubanta a kanshi,cikin wata murya dake nuna a ciki take dashi tace
"Ashe abinda kaje ka jajibo mana kenan?" Ta jefa masa tambayar tana qanqance idanu
"Kamar yaya mom?"
"Yanzu bassam ka rasa yarinyar da zaka auro sai 'yar gidan almajirai?,'yar matsiyata,masu ci da allo da tawada?,wadda iyayenta basu ajjiye komai ba?,duk tulin 'yammatan da kake dasu,babu irin jinsin yaren da qabila da kuma 'yan qasar da babu?babu kalar matsayin da iyayensu basu dashi?, recently 'yar gidan commissioner of finance tazo gidan nan takanas saboda kai,ringidi ringidi ina murna kamar gaske,ashe kai idanunka wata suka hango maka?" Kansa ya shafa yana bata fuska
"Munafukan nan su fahima da sukaje kai lefe ne suka gaya miki,wallahi dama nasan za'a rina" tsawa ta daka masa
"Kai dalla banza shashasha,wanda baisan ciwon kansa ba,su kishin dan uwansu suke idan kai baka kishin kanka,wannan 'yar gidan matsiyatan dama tuntuni kaketa yiwa ruwan kudi,kake rawar jiki kana barnatar musu da kudi,kudin da basusan darajarsa ba,kudin daka zubar musu inda da tabbacin har ubanta ya mutu bazai hada jarin da yakai yawansu ba,wallahi wallahi banda magana tayi nisa ko zaka mutu ba zaka aureta ba,so kake kawai ka tozartani cikin qawaye da abokan gaba 'yan baqinciki da mahassada?" Ciki ciki yace
"Am sorry mom,amma yarinyar ai tayi,nasan zata fiddaki kunya shi yasa na zabeta,don kaf cikin wadanda kike lissafawan babu wadda ta kama qafarta a kyau,kawai talakawa ne dai,amma shi kansa babanta da qyar ya bada ita"
"Kai dalla can matsa,au da qyar ya bayar?,to ai daya riqe abarsa,kada Allah yasa ya bayar din,saboda Allah ya taimakeshi ma zai hada jini damu?" Sake hasala hajiya hafsatu tayi wadda suke kira da mom,da qyar bassam yasha kanta kafin ta sauko
"Wannan gidan naka ka bata ta zauna ba?" Kai ya jinjina mata
"To ban lamunta ba.....me zasu iya zubawa a wannan gidan har ya cika?,matuqar kanason aurenta duk uban abinda suka jera din,a kawoshi nan part din hajj a shareshi a jera" idanu ya fitar
"Haba mom,why?,nifa gaskiya inason sakewa da matata" haiqan ta sake taso masa,saboda tasan halin bassam din,zuma ne saida wuta
"Gidan ubanta yakai parlour daya dake part dinka kima ne?,idan kanasonta ta dawo ta zauna damu,idan kuma ba haka ba,to saidai ka fasa auren nata,wannan gidan sai ka tashi sake auren abokin burmin qwaryarmu sannan za'a shigeshi,amma ba zaka saka min diyar almajirai a ciki ba" daga wannan ta miqe abunta ta nufi stairs ta haye abunta.
Abunda ya sanya inna ta kasa riqe hawayen da taketa qoqarin tsaidashi,ranar da al'ameen ya sauke motoci guda biyu shaqe da kayan gado da kuma kayan kitchen na ban mamaki,dukka wani tanadi nasa da yayi don kansa ya qarar dashi akan iman din kamar yadda ya saba,babu yadda baiyi da sadiqu ya siya mata freezer,home theater da sauran kayan wuta ba amma fafur yaqi,yace sisinsa bazai kashe mata ba,tunda mai kudin duniya zata aura,shima da yasan haka zai qarar da komai nashi lallai da bazai bari ya siya mata komai ba,shikam.kamar bashi da zuciya,ya manta abinda iman din tayi masa ne ko kuwa?.
Murmushi kawai yayi ya kada kai,cikin nutsuwarsa da muryarsan nan mai dauke da wani irin sound yace
"Ko a lahira wani yana cin albarkacin wani bare gidan duniya,diyar data fito daga tsatson inna da malam tafi qarfin na rama mata sharri da sharri,koda abunda tayimin yafi haka girma da muni,aurenta ne bataso nayi.....kuma na yiwa kaina wannan alqawarin yadda bataso har abada aure tsakanina da ita,Allah ya tabbatar da ita gidan mijinta,ya basu zaman lafiya me dorewa" binsa kawai da kallo sadiqu yayi,yanajin kimar amin din tana daduwa cikin ransa da idanunsa.
Daga ita har malam din rasa bakin magana sukayi,saboda ko su ba zasu iya yi mata kayan da suka kama qafar haka kyau da tsada ba,kunya duk ta cikasu,imanndin ta qishi,shi kuma ga abinda ya saka mata dashi nan,daga qarshe yaa gana ce tasa aka yiwa bassam magana kan za'a zo ayi jere,yace ya gama komai,sam ya gana tace sai an jera mata,ya debe wasu daga cikin nashin,hakanan aka kai kayan gidansu bassam,inda mom tace anan zata zauna.
Duk da cewa kayan sunyi iya qurewar gatan yarinyar da iyayenta ke da matsayi irin nasu malam,amma su fahima da suke qanne ga bassam da kuma yayunsa tabe baki sukayi sanda sukaga zatin kayan,saidai kuma sauran da bassam din yayi wanda basusan shine yayi ba shi ya hanasu tankawa.
Biki aka shiga gudanarwa gadan gadan,irin bikin da yake burin 'yammatan yanzu,bikin da ya dauki hankula,yaja magana a social media qwarai da gaske,hotunansu suka dinga shiga wayoyin jama'a,loko da saqo,biki bassam din yayi na kece raini,yayi barnar kudi kamar baisan ciwonsu ba,abinda ya bata ran momy qwarai,tsana da kuma haushin iman ya cikata tun bata kai ga shigowa gidan ba,ta yaya yarinyar da bata isa ba,bata kai komai ba bassam din zai xauna ya dinga kashe mata kudi haka?.
K'arfe tara na dare ya samu ya kutso zuwa dakinsu dake soro,hannunsa riqe da baqar leda,wadda ke dauke da dinkin riga da wando da 'yar ciki na dakakkiyar shaddar da ya zuba kudade masu nauyi ya siyeta,ya kuma kashe kudade masu yawan gaske akayi mata aikin hannu gabanta da bayanta.
Duk yadda inna taqi taro amma hakan bai hana gida samun baqi ba,saboda wasu da yawa sun rugi sun taho bikin ne saboda labarin irin mijin da zata aura da ya kai musu
#zafafabiyar
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: *25 A*
_AM SORRY,ASHE AN SAMU TSALLAKE,GA MISSING PAGE DIN NAN,AMMA NA YAU DANA GOBE NA BAKU KENAN,ASHA KARATU LAFIYA_
25
Cikin matuqar dauriya da juriya yaketa attending baqin da sukazo domin malam,da yawa mutane sunata yi masa Allah ya sanya alkhairi,ga zatonsu shine angon,ya buga kyau babu qarya,don dole idan kazo wajen ka zaci shine angon da gaske din.
Kusan a idanunsa tawagar bassam suka iso,cikin tawagar motoci na kece raini,hadi da tarin dubban al'umma,wanda hakan zai tabbatar maka ba qaramin gangami angon yayi ba,ya dauke idanunsa daga sashen da suke,zuciyarsa na qara yawan adadin bugawarta.
Shuru yayi yana jin tamkar ana dura masa hayaniyar jama'ar dake wajen cikin kansa sanda lasifiqar dake wajen ta yada muryar mutumin dake sanarwar cewa an biya sadakin hajar ibrahim khalil wato iman din naira dubu dari da hamsin da kuma galleliyar sabuwar mota,daga nan liman ya zarcw da sigar daurin aure.
Kamar wasa yaji qafafunsa sun gaza daukarsa,a hankali yaji kamar yana sulalewa,duhu ya soma sauka a idanunsa,abu na qarshe da ya iya gani fuskar sadiqu daya taroshi yana qwala masa kira,daga haka komai ya tsaya masa cak......
********Tunda suka fito daga gidansu take wani irin kuka,bayan ta gama kukan da saika tsammaci wa'adin rayuwarta ne ya qare,har zuwa sanda ta zame tana roqon inna ta gayawa malam ta fasa auren,don sam bata samu ganin malam din bama,saboda yana can asibiti wajen al'ameen,ita kanta innar
"Allah ya bada sa'a" kalmar data gaya mata kenan,tana qoqarin yafa mayafinta don wucewa asibiti wajen al'ameen da aka kwantar tunda safen.
Ko a cikin motar kukan take kamar babu gobe,gaba daya komai yafita a ranta,hakanan hankalinta a tashe yake,saidai dukkan wanda zasu bata baki sunyi iya abunda zasu iya,basusan dawar garin ba,saima suka hau mata shaqiyanci kan gobe iwar haka inda zakaje gidan ragal da ita,su bazasu iya ba,angon ya qarasa rarrashinta.
Babu wanda bai gigita da irin kyau girma da tsaruwar gidansu bassam ba,don duk yadda suke hasashe ya wuce nan,kai tsaye suka nufi part din mom da ita,kamar yadda yake a al'ada,kaiwa uwar miji matar danta,matuqar basu da nisa da juna ko kuma cikin gida daya kamar haka.
Saidai kuma dab da zasu qarasa qofar sashen aka taresu kan su wuce da ita sashenta,basai an kawo mata ita ba.
Kallon kallo aka hauyi,kowa da abunda ya fahimta,hakanan kowa da abinda yake saqawa cikin ransa ko kuma shifa abokin tafiyarsa,haka suka juya da iman din zuwa sashenta kamar yadda mom ta buqata.
*_BAYAN AWANNI UKU_*
A hankali hawaye keci gaba da sauka daga idanunta,wani irin mutuwar jiki da bacin rai dukka sun mamayeta,musamman idan ta tuna irin sallamar da sukayi da inna,malam kuwa dama bataga idanunsa ba bare ya sadiqu,uwa uba kuma lamin dake asibiti batasan a wanne hali yake ciki ba,saidai kuma ta wani sashen ranta yakanyi mata sanyi,musamman idan ta tuna da irin alqawuran da bassam yayi.mata da tanadin kulawa a irin wannan daren.
zuwa lokacin sashen nata yayi tsit,saboda kowa ya watse ya kama gabansa,babu qarar komai saita babban engine da ake zubawa disel wanda shike bawa dukkan gidan wuta,tana
Tun tana sharar hawayen tana kuma dakon shigowarsa,har hawayen suka kafe,tsoro kuma ya mamayi shurun,saita sake curewa waje guda tana sake sakin wasu sabbin qwallar.
Tun tana daga idanu tana duba lokaci har idanun nata suka fara nauyi,sabida gajiyan data tara a jikinta na kwanaki bakwai,a hankali baccu ya rinjayu juriyarta yayi galaba a kanta,ta sulale nan gefan lallausan gadonta ta fara bacci ba tare data sani ba.
Can cikin barcinta taji kamar ana taba qafafunta,abunda ya zaburar da ita kenan ta farka a firgice,suna hada idanu da bassam dake kanta saita sunkui da kai qasa,yana tsaye riqe da babbar rigarsa ya zuba mata idanu,saidai akwai yanayi a launin idanunsa,kamar wanda yayi barci ya farka
"Bacci zakiyi baki sauya kaya ba,hala kin gaji da jirana ko?,abokaina ne suka hada wani dinner iya mu imu,ga wannan,nidai bacci nakeji,saida safe" yayu maganar yana ajjiye mata ledar daya shigo da ita ya nufi saman gadon ya fada akai.
Waiwayawa tayi da kanta gefan da ya kwanta din,yayi dai dai saman gadon,da alama da gaske yake bacci zaiyi,don har ya cusa kansa qasan pillow abinsa ya fara sauke numfashi d'ai d'ai.
Mamakine ya cikata sosai,wanne irin ango ne haka?,ko 'yar sallar nan ta daren farko ma bai damu yayita ba?,ta maida dubanta ga ledar da ya shigo da ita din,sai ta matsar da ita kawai gefe,ta miqe ta lalubi toilytayi fitsari sannan ta daura alwala,ta dawo saman gadon tankwanta daga ca daya gefan.
Ta jima zuciyarta tana mata saqe saqe kafin bacci yayi awon gaba da ita.
Koda ta farka da asuba saita taras har yanzu baccinsa yake,tayita qoqarin tashinsa yana sake juyi yana kwanciya,daga qarshe fincikota yayi cikin jikinsa ya matseta,tayita kiciniyar qwace kanta amma ta kasa,haka ta haqura,tana ji tana gani daga shi har ita sallar asuban ta wucesu.
11:02 AM
Ko ina na gidan tabi tadan kakkabe inda yayi qura ta kuma badeshi da turaran wuta bayan tayi wanka ta kuma sabunta kwalliyarta cikin atamfa,ganin har sanda ta gama din babu wani abu da zasu karya dashi saita shiga kitchen,ta soya qwai ta dafa ruwan tea,tana jerewa saman dining ne bassam.ya fito yana amsa waya,daga shi sai singlet da gajeran wando,tadan waiwaya ta kalleshi,sai ta dauke idanu taci gaba da abinda take,da alama bai jima da farkawa ba sannan yayi salla.
Inda take ya qaraso,ya jata jikinsa ya rungume yana ci gaba da amsa wayar,wannan ya bata damar jin muryar wanda suke wayar dashi,muryar macace,saidai bata iya jin me take gaya masa,suna a haka har ya vama wayar,ya ajjiye nan saman table din da suke tsaye daura dashi
"Amarya bakya laifi"
"Ina kwana" ta gaidashi cikin girmamawa
"Lafiya lau,me aka dafa mana" yayi maganar yana miqa hannu ya bude kwanukan
"A'ah,ba'a kawo abinci daga cikin gida ba?"
"Eh gsky,ban sani ba ko ina ciki an buga anji shuru" daukar wayar tasa ya kira mom.
Ciki ciki ta amsa gaisuwar tasa,ba tare data bari ya dora da maganarsa ba tace
"Ku ba'a isa ku shigo ku gaida mutane ba kenan"
"Yanzu muka tashine mom,na tambayeta ma an kawo abinci tace a'ah"
"Waye bawanta?,idan zata tashi ta girka ta tashi ta girka da kanta" saita datse wayarta abunta
"Oh shit" ya fada yana cije baki,ya sake aje wayar sannan ya saketa ya zagaya ya zauna yana cewa ta hada mishi tea din.
Kadan kadan take kurba cike da baqunta,shi kuma wanda zai sanyata ta saki jikin tunda suka zauna yake amsa waya kala daban daban,har sai daya kusa gamaw sannan ya sauke wayar,ya dubeta yana murmushi
"Saifa kinyi haquri,nidin mutum ne mai jama'a,mai kuma busy sosai,mutane na ne na Media suke congratulating dina" dan qaramin murmushi kawai ta saki tana gyada kai.
To a yanayin gidan amarya da yake da farinjini banda gidan iman din,don kuwa babu kowa a sashen nata,koda kuwa 'yan cikin gidansu bassam din,shi kansa daga bisani kiransa akayi daya daga cikin abokansa,ya shirya cikin dakakkiyar shaddarsa,yayi kyau sosai kamar kowanne lokaci,tana dubansa bayan ta gama tayashi ya shirya tana fesa masa turare
"Ya kamata mu shiga ciki kafin ka fita mu gaida mom ko?"
"Sai na dawo tukunna"
"Zaka biya ya wajensu inna ne?" Ta tambayeshi,don tana zaton zasu gaisuwar surukai ne kamar yadda al'ada ta tanada
"Kai,bana jin haka gaskiya" da wannan amsar yayi gaba bayan ya danyi kissing bayan hannunta,tayi masa a dawo lafiya,saidai tana mamakin me yasa bazai qarasa gidan nasu ba.
Shuru ita daya a sashen,sai tv dake aikinta,duk da cewa gidan sabone a wajenta,amma ko sau daya batayi sha'awar bari ta tashi ta zagaya taga ya gidan yake ba,haka kawai takejin jikinta a mace,sam babu wani karsashi ko walwala tattare da ita,ta dauki waya ta kira inna ya kusa sau biyar amma bata daga ba,so take taji dama yaya jikin lamin,ganin bata dauka ba saita maida akalar kiran wayar sadiqu,shi wayar tasa ma a kashe take,malam shine na qarshe data kira,cikin sa'a kuwa ya daga,saidai daga gaisuwa bai sake barin wani abun ya hadasu ba ya kashe wayarsa.
Tana cikin wannan yanayin su munira ita da qawayenta suka iso,abunda yadan motsata kenan,har ya rage mata damuwar da take ciki,cikin lokaci kadan suka cika gidan da hira,sunata tsokanarta gami da zolayarta kamar dai yadda akasan qawayen amarya kanyi idan sunzo gidan qawarsu sabon aure.
Su munira ne kan gaba,aka shiga kitchen aka shiga dafe dafe,lafiyayyen abinci sukayi,aka fidda kula aka zubawa bassam nashi,daya daga cikin qawayen nasu ce tace
"Amma dai ki dinga saka sanwa da mamansa,duk da suna da wadata da dadi ki dafa ki aika mata" harara munira ta jefa mata
"Kinjiki da wani abu,su masu kudi ina sukasan wannan,babu ruwansu,dadin auren gidan wadata kenan,nasuma basi gama cinyewa ba bare su saurari na suruka".
Ta sake sosai taci abincin a cikinsu muniran,ta sake wanka tayi kwalliyarta dakyau,wanda hakan yayi masifar fidda kyanta,kamar ka saceta ka gudu,ga kyan quruciya da halitta ga na amarci.
"Kannensa sun shigo kuwa?,suna da kirki ko?"munira ta tambayi iman sanda suka kebe,abinda yaketa bawa iman din mamaki kenan tun dazu,babu wanda ta gani daga cikin gidan,ko don itadin bata shiga bane
"Ko fuskan mamansa ban sani ba har yanzu"
"Karki damu tunda zaku shiga anjima,kinsan su masu kudi basu danu da rayuwar kowa ba,surukutar ma ba kasafai ake yinta ba,musamman aka hadu da 'yan boko,su kuma duk sun hada" amsar muniran tadan kwantar mata da hankali.
Suna tsakiyar hirar bassam ya shigo,ya zuba mata idanu saboda yadda tayi masifar yi masa kyau,ya bude mata hannayens babu ko kunyarsu munira,hakanan itama ta isa gareshi saboda kada ta kunyatashi,ya rungumeta tsam a jikinsa yana fadin
"Kinyi kyau beauty,kina da kyau baby" ba shiri su munira suka fara lalubar jaka zasu tafi,kudi masu tsoka ya basu wanda ya sake gigitasu,ya kuma sanya driver ya maida kowaccensu gida.
Ita taimaka masa yayi wanka kamar dazu ya kuma shirya yaci abinci,a lokacin ta sake matsa masa su shiga ciki su gaida mom,yace ta dauko mayafi suje.
Tun daga shigarta ta tadda qannensa kafin fitowar uwar gayyar wato mom tasan cewa bata karbu ba,ba'a kuma maraba da ita,'yammata hudu ta samu a parlor din suna kallo,saidai kaf dinsu babu wadda tayi mata duba biyu bare ta saka ran zasu gaidata,hakan baisa ta kasa gaidasu ba,saboda ta lura biyu daga cikinsu zasu girme mata,biyun ne zasuyi sa'anni.
Sama sama suka amsa kamar wadanda aka yiwa dole,bassam din ya jefesu da harara
"Wanne irin iskancin banza ne wannan,kunaji ana gaidaku" daya daga cikinsu ce wadda ke riqe da tab tana ta faman danne danne ta waiwaya ta masa wani irin kallo
"Tunda mun amsa ai fine"
"Shut off......" Yadan fada mata a tsawace,sai kawai ta miqe ta sauko daga saman kujeran da take kai tana quna quni tayi ciki abinta,sauran ma sai suka fara binta daya bayan daya,kafin daga qarshe mom ta fito.
Kallo daya zakayi mata kasan cewa hamshaqiyar macace da taci ta tada kai,takeji da izzar kudi da kuma isa
"Sai yanzu kuka ga damar zuwa gaisheni?" Mom ta fada tana zama cikin luntsuma luntsuman kujerun da ta kusa nutsewa a ciki
"Tunda na fita ban dawo bane sai yanzu" ya amsa mata hankalinsa nakan wayarsa
"Ita 'yar mulkin ba zata iya zuwa da kanta ba saika sanyota a gaba kamar 'yar gidan sarakai?" Tayi furucin bata ko dubi sashen da iman din ke zaune na,mummunar faduwa gaban iman yayi,fargaba ta saukar mata,jin bassam baice komai ba saita motsa,cikin girmamawa ta qarasa gabanta ta duqa tana gaidata cike da surukuta da girmamawa,wani kallo ta debo tayi mata shi sama da qasa,duk da cewa a zaune take,kana ta amsa mata da amsawa guda daya tak,sannan ta dauke kanta ta tattara hankalinta kan danta suka shiga hirarsu abinsu,kamar ma sun manta da ita,kamar ma Allah baiyi wanzuwarta a wajen ba,sai data gaji don kanta qafafuwanta suka fara tsami sannan ta nemawa kanta wajen zama.
Awa daya babu wani abu a ciki sannan mom ta waiwayo inda take
"Da Allah dan kauce daga nan,muna magana" jikinta a mugun sanyaye ta dan dubi bassam,sai taga hankalinsa yana kan wayarsa,ta miqe a hankali cikin girmamawa tace
"Sai anjima mom" ci kanki batace mata ba,saima dogon tsakin data bita dashi sanda take fita daga falon,don kyau yarinyar tana da kyau,saidai kuma ta samu tawaya ta fuskoki biyu,na farko gidan data fito din bai cancanci ace kamar bassam ya auri diyar gidan ba,na biyu kasancewar mahaifinta malami,batason ya zamana bassam din ya auri matar da zata mallake mata d'a,wanan dalilan yasa gaba daya taji iman din batayi mata ba.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 26
Kwanciyarta tayi daga gefe guda na dakin bayan ta gama addu'o'inta,tana jinsa yanata motsi har zuwa sansa ya jawota jikinsa
"Wai fushi ma kikeyi?"kanta ta girgiza
"Idanma nayi fushi nima ban kyauta ba dana daga maka waya,kayi haquri,amma maganar hijabi,bazan iya daina sakashi ba,dashi aka tarbiyyanceni" tsaki taji yaja
"Su tarbiyya manya,nidai indai kinason farantamin ga abinda nace dake nan" abinda ya fada kenan,daga haka dukansu kowa yaja bakinsa yayi shiru. Daren ranar jagwalgwalan da ake matan ma ba'a yishi ba,itama hakan sai yafi mata dadi,saboda ko babu komai ta kwana cikin salama.
To tun daga waccar ranar ya koyi yawon dare,idan ya dawo daga aikinsa,yaci abinci wanka kawai zai sakeyi ya fice,bashi zai shigo gidan ba sai qarfe daya na dare wani lokacin har biyu yakan iya kaiwa,wani lokaci ko sallar isha'i sai ya dawo zaiyi.
Abun ya shiga cikin jerin abubuwan dake dagula mata lissafi a rayuwar gidan,ta kuma rasa inda yake zuwa,tayi masa duk abinda ya dace don tasan inda yake zuwa amma amsa daya ce,aikine yake riqeshi,daga baya ma data dameshi sai ya daka mata tsawa,ya kuma ce mata shi ba danta bane,kada ta sake gigin masa wannan banzar tambayar,sanda yake gaban mom ba ba'ayi masa wannan sanya idanun ba bare yanzu da yake da 'yanci
"Ni banason takura da sanya idanu,wannan ne yasa na auroki tun kina sha takwas bakikai ashirin ba" wannan maganar tasa ta tsaya mata a wuya,me yake nufi?,me maganarsa take nufi?,bata da wani abokin shawara duk duniya sai munira,amma a wannan karon sai ta gaza furtawa muniran abinda yake damunta cikin gidan nata,koda yaushe idan suna chart gaya mata take komai lafiya
"Shegiya iman,an samu duniya,muma Allah ya sanyamu a danshinku,Allah yasa kada ki canza qawaye nan gaba matan manya a manta damu,inason zuwa amma jarabawa ta hanani,umma ta dage sai na fidda result masu kyau idan inason aure bayan candy" sai a lokacin taji wata kewa ta makaranta ta kamata,ya akayi tayi sakacin da maganar karatunta tasha ruwa?,ta tuna irin yadda ya al'ameen yasha gwagwarmaya akan karatunta,gwagwarmayar da ko nashi karatun bai maida hankalin ya yiwa ba,ta sauka daga chart din,ta lalubo number wayar inna a karo na barkatai ta kirata.
Daf da zata tsinke aka daga,don har ta fitar da rai da za'a daga din,satinta biyar da xuwa gidan,amma sau daya tak ta taba kiranta ta amsa sai wannan karon.
Tanajin sallamar innar hawaye suka sauko mata,cikin rawar murya ta fara gaidata,innar ta amsa a dake kamar anyi mata dole,daga haka shuru ya biyo baya
"Sai anjima" inna ta fada tana datse wayar,saidai can wani saqo na zuciyarta taji yana matsewa,muryar iman dinta ba haka take ba,tabbas ta canza.
A lokacin suna tare da al'ameen wanda ya ajjiye takardun daya shigo dasu gaban innar
"Amintacce......da alama bakinka akwai labari" inna ta fada cikin fara'a sosai,saboda ta hangi wata walwala mai yawa a fuskar al'amin din,abubuwan da suka farun sai suka sake zama kamar wani mabudi na qarin kusanci da fahimtar juna tsakanin alameen din da inna
"Allah yayi inna....na samu tallafin karatu zuwa qasar dubai" idanu inna ta fitar sosai,gaba daya bakinta yaqi rufuwa
"Kaiii....Alhamdulillahi,Allah mun mun gode maka,Allah kaine Allah,Allah ka qarawa annabi muhammad daraja,aminu?,abun ya tabbata?" Kai ya gyada murmushi cike fal fuskarsa
"Wallahi inna,don har na haqura na fitar da rai"
"Rabon kwado ai baya taba hawa sama aminu,kuma ita addu'a babu abinda ta bari" sai taja takardun ta dudduba iya abinda zata iya ganewa a ciki,tayi masa addu'a sosai.
Sun dan jima suna tattaunawa shida inna kafin ya dauki takardun ya wuce daki,saboda yace tun yanzu zai fara shiri,don tafiyar tasu ba zata wuce sati hudu masu zuwa ba in sha Allah.
Iman ce mutum ta farko data fara fado masa a rai sanda scholarship din ya samu,amma yayi gaggawar tsigeta daga ransa ya ajjiyeta a gefe,saboda ya riga da ya yiwa kansa alqawarin sake sabuwar rayuwa da zai shafe babin iman kwata kwata daga cikinta,tun sanda aka sallamoshi daga asibiti bayan baqar wahalar da yasha ta sati daya,ya kuma dawo gida yayi jinyar sai biyu.
*******jaye take da trolley dinsa tana biye dashi a baya,yayin da shi din kuma yake sanye da wasu rantstsun suits masu bala'in kyau da daukar idanu.
Tana biye dashi tana mamakin yadda sam hankalinsa bai kanta,a matsayinsa na magidanci kuma sabon aure wanda bai dorar da komai cikin rayuwar auren ba,zaiyi tafiya ta wata guda cur,amma babu ko alamun damuwa tattali ko nuna kulawa saboda zai tafi yabar amaryarsa agida,sai faman amsa waya ma da yakeyi,har suka isa inda motar da zata kaishi airport ke jiransa.
Sai daya shiga motar kafin ya rufe sannan yadan dage wayar daga kunnensa
"Allah ya kiyaye,ya bada sa'a,Allah ya kaika lafiya"
"Ameen.....ba wata matsala ko?"
"Eh to,waye zai tayani kwana,shine maganar da tun jiya nakeyi maka ita baka amsamin ba"
"Ki shiga cikin gida ki roqi fahima ko fairuza wata tazo ta dinga tayaki......idan akwai wata damuwan kada ki damu,ki bude locker din cikin dakina ta gefan gado,key din na jiki,ki dauki adadin abunda yayi miki,saina dawo" daga haka yaja murfin motar ya rufe.
Kasa daga qafafunta tayi daga wajen,sai hannyenta data goya tana bin motar da kallo kawai,inama yadda yake sakar mata kudi farinciki yake bata haka?,inama ace nutsuwar zuciya da ruhi take samu har haka gurinsa,sam kwata kwata batajin wannan ruhin na matan aure cikin jikinta,tana jinta wani salaf tamkar tana gida,kai......akwai tarin bambance bambance ma a yanzun kan zamanta a gidansu da kuma wannan gidan,saidai kuma.....ta yaya zata daidaita wadan nan al'amuran?,ta yaya zata koma tana jin kanta da ruhinta kwatankwacin yadda kowacce mace takeji cikin gidanta,kamar yadda takejin matan aure na hira cikin group nasu na WhatsApp?.
Sai data shiga sashen nata sannan ta tabbatarwa kanta mawuyacine ta iya kwana ita daya kamar yadda ta kwatantawa ranta,saidai kuma.....ta yaya zata tunkari wadancan mutanen,wadanda suka kaita gefe daya suka ajjiye,sam basa tuna ma akwai wata halitta me rai ta dan adam a wajen?.
Tana tsaka da wannan tunanin sallamar munira ta katseta,taji matuqat mamakin ganinta,suka saki juna bayan sun gama murnar ganin juna,muniran na qare mata kallo
"Me zan gani haka?,ke ko 'yar qibar nan ta amare da akeyi ke babu ke?,sai kyau kawai da fatarki ta qara" baki kawai iman din ta tabe tana miqewa
"Me zan kawo miki?"
"A'ah muje,yau saina zaba na darje,sai nayi qara'in abinda na dade banci ba" tayi maganar tana miqewa,dariya dukka sukayi suka rankaya kitchen.
Tsaye tayi kawai daga gefe tana kallon yadda muniran ta rude,taketa santin babu ce kawai babu cikin kitchen din,ita batasan ko sau daya daga alatu har cimar dake cikin kitchen din ba dai dai da rana daya bata taba ci ko amfani dashi ba taji ya tsarga mata ba ko yayi mata dai dai
"HANGEN DALA FA BA SHIGA BIRNI BACE(huguma) munira" cikin rashin fahimta ta waiwayi ta dubeta"
"Kamar yaya?" A wannan gabar taji ta kawo maqura kuma iyakar da dole kwanyarta ita kadai ba zaya iya wannan ayyukan ba,don haka ta fayyace mata komai,illa ta suturta maganar rashin iya yin komai a gado da bassam din bayayi.
"Mtseww,ni wallahi idan nice ke wannan ba matsala bace a wajena,indai zanci nasha na qoshi,nayi wadaqa da kudina duk su suka jiyo,ke kuwa cikin wadan nan abubuwan dana lissafa babu wanda kike da matsalarsa,yawon daren bassam,yawan mu'amala da waya fiye dake,rashin baki isashen lokacinsa,wannan duka damuwoyin kansa ne ba naki ba,wasu danginsa sa sauransu ba case dinki bane kowa yayi ta kansa,tunda babu abinda kika waiwaya kika rasa" girgiza kai iman dake goye da hannuwanta tayi
"Ba zaki gane bane munira,zaman ya wuce ya baki abinci sutura da kudi,wannan duka wani tunaninmu ne ashe na rashin sanin ciwon kai da kuma quruciya,kinsan da miji ya baki naira dubu gwara ya baki minti dayansa?,ya kalleki duba na so qauna da soyayya?,ya saurareki saurare na girmamawa da jin qai.....amma fa,duka wannan ga macen datasan ciwon kanta ne,wai kuwa kinsan har yanzu bazan iya banbance miki mene bassam yakeso ba da kuma abinda bayaso?,saboda har yanzu ban samu wani isashen zama dashi da zai kaini ga fahimtar hakan ba?,ya tara kudin amma har yau nema yake,ya kasa zama ya huta ko qaqa"
"Gwara yayita nema muku ai keda yaran da zaki zazzago masa" munira ta amsa mata tana tura qatuwar lomar shinkafa wadda fiye da rabinta naman kaza ne data masa gutsi gutsi.
Amsar da muniran ta bata yasa ta qare mata kallo a fakaice,saita gane cewa muniran ba fahimtarta take ba,ba kuma zata gane ba,saboda ba'a cikin system din take ba,don haka ta sakin zancen kawai,ta qyale muniran.
Sanda zata tafi ta bata kyautar dubu biyar,sosai muniran taji dadi
"Kai.....dadin auren me kudi kenan,yanzu irin wadan nan kina dasu nasan bila'adadin,kiyita tara abinki kina aikawa dasu gida a sarrafa miki,kiyi kiyi kema nan da nan ki kama qasa" munira ta fadi tana danna kudinta a jaka,murmushi kawai iman din tayi,suka fito tana taka mata.
Da zasu wucw tayi tayi muniran ta rakata su shiga wajen mom fa tambayo fahima ko fairuza tayin kwana munira tace bata shiga,saboda idan ta shiga suka mata kallon banza ba zata bari ba,haka ta barta ta wuce,data dawo daga rakiyar saita wuce sashen mom din ita daya.
Tana kutsa kai cikin falon gabanta na tsananta faduwa,saboda yau kuma batasan da wacce fuskar zasu tarbeta ba,wacce magana zasu yayyaba mata,a haka dai ta daure tayi sallama cikin lallausar muryarta tana saka kai cikin falon.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 27
Taci sa'a za'ace ko rashin sa'a,ta samesu su dukka hudun suna nan,uku fahima,fairuza da nasma suna can saman dining suna cin abinci,ikram na zaune qasan carpet cikin falon tana aiki cikin system,da yake ita din ta fara aiki a babban kamfanin gidansu,momi ma na daga gafe tana fama da kallon news,idanunta saye da glass din da iman din tafi kyatata zaton medical ne.
Kamar ko yaushe d qyar ta amsa sallamarta ta dauke kanta,ikram ma dake aiki kallo daya ta mata taci gaba da aikinta bayan ta amsa sallamar,a haka duk cikinsu ta fisu sauqi,kuma itace babba cikin matan,su kuwa sauran dake saman dining suna kaiwa ciki suna hirarsu kamarma basusan ta shigo ba.
Ikram din ta fara gaidawa,ta amsa babu yabo babu fallasa idanunta akan aikinta,saita qarasa ta gaida mom,ta amsa tana kallon tv abinta.
Shuru ya biyo baya kamar babu wata baquwar halitta a wajen,tamkar kaya suka aje ko kuma kashi,bakajin komai sai sautin tashin hirar su fahima.
Sai data gaji da zaman kuramen sannan cikin yanayin dari dari da kuma tsoro tace
"Amm....mom dama zuwa nayi na roqi alfarmar fahima ta dinga zuwa tana tayani kwana kafin ya bassam ya dawo"
"Wait!....wait.....me nake jiyowa?" Muryar fahiman ta ratso tun daga inda take zaune,sai iman din ta dubi sashen cikin mamaki,saboda ta zaci tun shigowarta basusan ta shigo ba,ashe sunajinta.
Da wani irin taku fahiman ta sauko daga wajen,ta qaraso gaban iman ta tsaya tsam a kanta,ta jefeta da wani irin kallo na raini da qasqanci sannan ta fara magana cikin fada
"Lallai na yarda ni kadai kika raina cikin gidan nan,yanzu don Allah ki dubeni daga sama har qasa......" Tayi maganar tana nuna kanta
"Kamar ni.....in tafi gidanki tayaki kwana?,ko don kina ganin kanmu daya?,to ai hausawa sunce abanza wai talaka ya girmi sarki,ni ba tsararki bace,sunanki ya fita daga bakina" hannu mom ta dagawa fahima
"Yafi da Allah" sai data ja mata dogon tsaki sannan tayi gaba taba gunagunan maganganu
"Ke kalleni nan" mom ta fada tana duban iman din sosai
"Ina cewa a gidanku ke kadai kike kwana a dakinki,dakin da babu cikakkiyar qofa ma,kinga nan gidan" ta fada taba nuna falon da yatsanta
"Kaf katangunsa dogaye ne masu qwari,babu inda ya zaizaye ko ya cinye,baya ga haka akwai guards a gidan nan,sabida haka idan zaki wuce ki bawa mutane wake kije ki koyi kwana ke kadai ki koya,don bassam ma bai fara tafiye tafiye ba idan shine,banason wani iyayin banza da kwainane" jikinta babu laka ko kadan ta miqe,tana takawa a hankali ranta a bace jikinta a matuqar sanyaye,tana iya jiyo dogon tsakin mom din,sannan tace
"Gayyar tsiya arna a idi" kalmar data sanya hawaye suka silalo mata masu zafin gaske.
Hakanan kuwa ta kwana ita daya a sashen kamar mayyar,fargaba tsoro da kuma baqinciki sukayi mata qawanya,wani abu me kama da nadama ya fara sauko mata,har yanzu har kuma kawo yau ba zata iya dorar da wani abu guda daya da zata ce ta samu naci gaba ba a gidan farinciki ko walwala,banda tarin kudi da yake ajjiye mata wanda batajin dadinsu ko kadan,sannan bata da abunyi dasu.
A haka a haka bassam ya kwashe sati biyu da yin tafiyar tasa,wanda tsahon sati biyun nan idan tace sunyi cikakkiyar waya sau uku to qarya takeyi,kwata kwata kiran da yayi matan ma sau ukunne,idan kuma ita ta kirashi sai yace mata yana wani aikin,ko kuma yana kan hanya ko kuma zai kirata,kiran da bazaiyi mata shi kenan ba,idan ta gashi ta online kuwa,ta tura saqo,sai iya kaiwa kwanaki biyu bai buda ba,hakanan zai gama zamansa online baisan ko sallama ya turo mata ba,amma haka ta dinga danne ranta tana gayawa kanta da gasken ne aikinne yayi masa yawa.
Ashe motsin mutum ma awaje koda ba zakuyi magana ba rahama ne,batasan da wannan ba sai a yanzu da bassam din baya nan,su mom ta fuskanci ba kallon cikakkiyar 'yar adam sukeyi mata ba,don har tafiya sukayi ta kwanaki hudu bata sani ba,randa zasu dawo ta fita tadan tattaka cikin gidan saboda gajiya da tayi da zaman waje gudan taga shigowar motarsu ana mata sannu da zuwa,batayi qasa a gwiwa ba ta qarasa itama ta siga cikin 'yan sannu da zuwan,saidai ko kallon tsiya bata samu ba bare tasaka ran samun na arziqi,haka ta juya ta koma sashenta gwiwa a sanyaye.
Sati na hudu da tafiyarsa gaba daya ta sake zabgewa,ta kuma rame,sai fari data qara da kuma kyau da sheqi da fatarta keyi,a sannan ya turo wani mutum da zai dinga zuwa yana koya mata mota duk yammaci cikin gidan,haka kuwa akayi,sati biyu kacal iman din ta qware sosai,hannunta yafada,har ta fara hawa saman titi tana shawagi titunan gefannin unguwarsu ta dawo,hakan shi ya fara rage mata kadaici da kuma dauke mata hankali,saidai kuma tana shan kallo,abinda yasa tasa aka maida mata gilasanta tint.
Ranar ta gwada kiran bassam tace masa zataje gida,domin zuwa lokacin haqurinta ya qare ya gaza,innarta kawai takeson gani,tana shiryawa amma kuma fargaba ce fal ranta,saboda batasan irin tarbar da innar xatayi mata ba,hakanan fa shirya tsaf cikin wani lafiyayyen lace na alfarma,ta debi kudi masu dama ta zuba ajakarta.
Tana tafe tana duba hanya,harta riski wannan babban store,anan ta tsaya ya loda siyayya me yawa ta kayan abinci me yawa,da kayan maqulashe,irin abubuwan da tasan malam da inna naso sannan tayi hanyar gida.
Tun daga nesa ta fahimci yau ba'a zauna karatu ba,saidai kuma akwai dalibai dai daiku cikin rumfar gidan nasu suna harkar gabansu,a hankali ta sako motarta cikin layin nasu,ta daidaita motar daidai qofar gidan,sannan ta bude ta fito.
Da murna daliban malam din sukayo wajenta,musamman wandanda suke dan dasawa dasu suke mata wanki da sauransu,ta fidda jakarta tayi musu rabon 'yan 200 sababbi fil,sannan tabar musu booth din motar a bude,tace su debo duka kayan ciki su shigo mata dashi ciki.
A hankali idanunta suka sauka a qofar dakin dake garqame da muqulli,ta tsurawa qofar dakin idanu har zuwa sanda tazo zata gifta qofar dakin,ta lumshe idanu gabanta ya fadi saboda wani qamshi data shaqa,qamshin turaren ameen ne da ya kama dakin fiye dana ya sadiqu yake ratsowa ta labulen window din dakin dake bude,taci gaba da saka kai zuwa cikin gidan gabanta naci gaba da faduwa har ta bayyana a tsakar gidan.
Fes tsakar gidan yake kamar kowanne lokaci,tsahon watannin yana nan yadda yake,babu wani abu daya canza,don ko lokacin bikinta ko fenti ba'a yiwa gidan ba bare wani abu makamancin wannan.
Sallama biyu tayi,ana ukun ta jiyo inna daga rumfarta tana amsawa,taci gaba da tafiya har zuwa bakin rumfar,ta sabule takalmanta,ta saka kanta ciki bakinta dauke da sallama.
Sak inna dake saka ruwan pure water a sabuwar qaramin fridge dake kusa da qofa ta tsaya tana duban iman din,da alama tayi mamakin ganinta,sai kuma ta share,ta hade fuskarta waje guda taci gaba da abinda takeyi,kamar bata ganta ba,babu wani reaction najin dadi akan fuskar innar.
Har ta qaraso ta zame tana gaida innar bata bar abinda take ba,ta amsa mata dai taci gaba da saka ruwan,dakin ya dauki shuru,sai motsin yara dake shigo da kaya a tsakar gidan,wanda inna batace komai ba tunda tasan muryoyinsu,ta dauka wani abun suka shigo yi.
Tana gamawa fa rufe fridge din,ta dawo saman daya daga cikin kujerun ta dauki carbinta,sai tayi hanyar fita abinta ta fita daga dakin zuwa kitchen ta kama ayyukanta.
Wasu zafafan hawaye ne suka tsattsafowa iman tana daga zaunen,yanzu innarta ce tayi mata wannan shakulaton bangaron?,innarta da suke zama suyi hira da ita?,innarta dake bata kulawa?,innarta dake gaya mata yadda zatayi kewarta?.....kece sila.....ke kika ja. Wannan itace amsar da zuciyarta ta bata,saita miqe cak tabi baya innar.
"Kawo inna na wanke miki" ta fadi tana qoqarin amsar kwanukan dake hannun inna
"Ni shegiya.....rufamin asiri,barni da kayana,ina ni ina saki aiki hajar?" Kalaman sai suka yiwa iman din girma a kanta,gaba daya saita kasa ci gaba da riqon kwanukan,ta samu gefe ta sulale ta zauna.
Sam inna bata lura da kayan ba sai data gama zata koma kitchen
"Ke meye haka?waye ya kawo wadan nan kayan?"
"Nice inna" ta fada bakinta nadan rawa,tana addu'ar Allah yasa kada innar ta wofantar dasu taqi karba
"Maza maza kafin ma malam ya shigo ya sabar miki kisa a fita dasu daga gidan nan,don bamu da gurbin ajjiyesu,jiya jiya aminu kafij ya tafi yabar mana abincin rabin shekara,babu abinda muke buqata,shida sadiqu sun ishemu rayuwa"
"Ina ya ameen din ya tafi?" Tambayar data fara zuwa mata ka kenan,bata ta sababin da innar keyi,sai daga bisani da fadan innar ya tsananta hankalinta ya dawo kai
"Don Allah inna kuyi haquri,don girman Allah" wani kallo ta watsa mata
"Haqurin me?,me kikayi mana?" Kasa bata amsa tayi,sai qas datayi da kanta hawaye na sauka,lokaci daya gaba daya duniya ta daina mata dadi,ta daina jin wani dandano ko dadi nata.
Duk sababin da inna keyi hakan bai sanya ta tashi tasa an kwashe kayan ba,har zuwa sanda ta jiyo muryar malam yana sako kanshi cikin gidan,mummunar faduwa gabanta yayi,ta ambaci sunan Allah tana daga kanta a gigice sanda taji ya ambaci sunanta,kafin ya iso ta miqe tsaye tana dakon isowarsa.
"Zoki wuce ki koma gidanki,can ne wajen zamanki,mu basai kinzo kin gaishemu ba,wadan nan kayan da kika zo dasu kuma bamu da wajen ajjiyesu,abunka da gidan talaka me nema,uwa uba kuma ya hadu da yaro me hazaqa daya cika masa dan rumbunsa da abincin watanni shida,don kada ya tafi ya barshi da yunwa.....ungo wannan" ya fadi yana miqa mata 'yan 200 din tari,wanda tana ganinsu ta gane wadanda ta rabawa almajiran ne,kenan karbosu yayi
°°"200 ce babu a ciki,wadda kika bawa habu,ya fita aiki,amma ga wata madadinta,saidai ita din tsohuwa ce,idan kuma bakison tsaffin kudi kiyi haquri,idan ya dawo zan karba na ajjiye miki sabuwarki,duk randa Allah ya hadamu saiki karba" sulalewa tayi a wajen tana sakin kuka tare da roqon malam ya barta ko azahar ne ta qarasa kaiwa,amma baibi ta kanta ba,hasalima yaran ya kira,yasa suka dinga jidar abincin suna maida mata boot din nata,inna na kitchen,yadda batace tak ba,hakanan bata waiwayosu ba,har ta gama roqarsa,ta sanya mayafinta da takalminta ta fita.
Tana tuqin tana sharar hawaye,har taso ta tafka shirme,sai da tayi parking gefan titi tadan daidaita kanta sannan taci gaba da tafiya.
Koda taje gida kwance kawai tayi taci gaba da kukanta,ba wanda ya damu da ita bare ta saka ran zaiyi cigiyarta,hasalima sanda tacewa mom din zataje gidan cewa tayi me zatayi mata,kudine?....idan shi take buqata ta tabbatar danta ya ajjiye mata su,tunda tasan dama nan sukafi kauri,maganar data sanyata cikin alwashin ba zata qara gayawa mom din ba din zata fita zuwa gida.
hatta da kayan cikin motar ta barsu batabi ga kansu baba ita ta tashi ba sai gab da magarib,tunda dama tana fashin sallah ne.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 29
Lokacin da bassam din ya shaida mata dawowarsa tayi dukkan wani shiri na tarbarsa,kama daga gyaran jiki qunshi da kuma gyaran gashi,hakanan ranar daya shaida mata cewa jirgin qarfe hudu xasu sauka ta shirya lafiyayyen abinci kala kala duk na taryarss,saidai tun sanda ya shigo din,banda qarar shigowar motocinsa babu abinda ta sake ji,tun tana duban hanya har ta sare,don da alama sashen mom ya wuce direct.
A hankali abincin data jera zafinsa ya zagwanye,kwalliyarta ta fara sulalewa tana yin nata guri,har bayan sallar isha'i,tayi kwance lamo saman doguwar kujera ita daya tana hadiyar zuciya.
Sha daya saura na dare taji ya turo qofar ya falon,tana daga kwance ta daga kai kawai ta dubeshi,bacin rai ya hanata mata motsawa bare ta tarbeshi,sai taci gaba da kwanciyarta kawai,har zuwa sanda ya qaraso kanta ya tsaya
"Ke!" Ya kirayi sunanta da kakkausar murya,a mamakance ta daga kanta ta dubeshi
"Kina jin mutane,su dawo daga doguwar tafiya irin wannan amma ki kasa zuwa ko sannu ki musu,me kike nufi?" Gani tayi ya gama raina mata hankali ma,daya shigo baiko kula da yanayin daya sameta a ciki ba zai dirar mata da fada,saita miqe ta zauna sosai saman kujeran
"A ina na gankan banda yanzu?"
"Ok....amma kinsan ina sashen mom ko?,ba zaki iya shiga can ba ki sameni,da gaske mom take kenan da tace baki qaunar rabarsu,don baqin halima tsahon watannin da nayi amma ace ke daya kike kwan?" Kanta ne ya daure sosai,maganar ta bata mamaki,wanne sabon salo ne haka kuma aka fito dashi cikin gidan,me dame mom ta shirya masa na maganganu,sai zuciyarta ta bata shawarar ta sauko ita,saboda batasan me dame ta gaya masa ba wanda zai iya tunzarasu shi da ita
"Ba haka bane,tunda naga kayi can nasan kana da buqatar ku kebe,ban kuma dauka zaka dauki tsahon wannan lokacin baka shigo ba,duba can abincinka ne har ya huce" dubansa yakai ga dining din,ya hangi kwanukan a jere,tabbas yana da buqatar girkinta,don tunda ya tafi yayi missing taste din abincinta,ko daya dawo ma da zumudin yazo yaci girkinta ya dawo,saidai kuma ya samu tarba daga mom,da kuma nau'ikan abinciccika kala kala,ta kangeshi kuma da nau'in hirarrakin da suka jima basuyi ba.
Saukowa yayi ya sassauta fusatar da yayi,ya miqa mata hannu
"Is okay.....muje ki bani abincin naci,ince dai shikenan ko?" Itama qoqari tayi ta sake danne nata fushin,ta bashi hannun ya dagata,suia qarasa dining din,tayi serving nasa,ta zauna opposite dinsa,yana ci yana bata labarin tafiyar da yayi,mutum ce ita mai zurfi da kaifin gabe abu,ta fuskanci akwai wani abu guda daya behind tafiyar tasa da yaketa ciccirewa yana sauya masa lamiri.
Ruwa ta hada masa me dumi yayi wanka,sai daya shirya ya kwanta sannan ta dawo gyara wajen,zuciyarta na raya mata wala'alla yau wani abu ya wakana a tsakaninsu,ta gama gyara wajen ta shirya itama.
Saidai ko data je bedroom din already ma bacci yayi awon gaba dashi,saita zauna daure da bedside drawer tana addu'o'inta,dai dai nan wayarsa ta kada alamun kira.
Idanunta taka kan screen din wayar,sunan linda ya bayyana,sai hotonta dake blinking,ko bakaga sunan ba hoton kawai ya isa ya gaya maka qabila ce kuma ahlil kitabi wato kafura,kiran yadan dauki hankalinta,saidai kafin takai ga yin komai taji ya motsa,ya kuma kai hannunsa ya dauki wayar da sauri ya kara a kunnensa
"Goodnight,am tired" abinda taji ya fada kenan ya kashe wayar gaba daya ya jefata qasan pillow dinsa,ya koma kwanciyar rub da ciki yaci gaba da barcinsa.
Sosai kiran ya tsaye mata a rai,ta lura ko sati daya ba'a rufa ba da aurensu ta gane yadda 'yammata ke yawan kiransa a waya,iya abinda idanunta suka gane mata kenan,don bata taba daukar masa waya ba bare tayi bincike,tun ranar da abokansa sukazo tsautsayi yasa ta dauka,hakan kuma ya haifar musu da sabani.
To ashe wasa farin girki,tunda ya dawo sai abubuwan suka sake rikicewa,daga bangarensa har zuwa bangaren mom,ita mom tunda ya bata kyautar danqareriyar mota wadda kudinta ya tasamma miliyan goma shikenan suka sanyata gaba ita dasu fahima,ada basa shigowa bangarenta,amma a yanzu sai suka tsiri shigo mata,kai tsaye zasu fada mata bedroom dressing room ko kuma kitchen dinta,duk abinda sukaga dama zasu dauka,su tafi dana tafiya,su barnatar dana barnatarwa,duk da cewa Allah ya wadatasu da komai,babu abinda suka nema suka rasa,bata taba daga idanu ta kallesu ba,amma duk da haka bata tsira da baqar magana da kuma habaici ba,abinda ta lura dashi shine. sun dauki aqidar qwarya tabi qwarya,gaskiya ne da ake cewa idan kaga diyan talaka na aure gidan masu arqizi to ba shakka rabone ya rantse,ko kuma su din irin mutanen nan da ake cewa daya cikin million ne,don zaiyi wahalar gaske kaga hakan,kowa irinsa yake aure,sun maida abun jari hujja.
Bata sake gasgata hakan ba saida matan yayun bassam din sukazo gidan su biyu,dukkansu gudajen iyayensu masu maiq ne kamar gidansu bassam din,haba haba mom take dasu,babu raini tsangwama ko wulaqanci irin wanda suke mata ita,tsakaninta da faccalolin nata dai baina baina,babu yabo hakanan babu fallasa.
Ta bangaren bassan kuwa,tun tana kawaici da yadda mata ke yawan kiransa harta qosa ta fara qorafi akai,abinda ya sanya kenan yake yawaita saka wayansa a silent.
Abun sai ya zame mata biyu,ga lalurarsa da bai taba tsayawa yayi mata wani gamsashen bayani akai ba,ga kuma wannan dabi'a tasa,hasalima kamar ma damuwar da yakeyi a baya akan al'amarin yanzu taja baya sosai,kawai da ya kasa yake tashi yayi wanka yaci gaba da sabgarsa.
K'arfe sha daya saura na dare take takowa zuwa parlor dinsa na musamman dauke da butar shayi mai hade da tray da qananun kofunansu,sanye take da kayan bacci masu kauri riga da wando da suka saukar mata ash color marasa turuwa,sai gashin kanta mai santsi data matse waje daya yanata sheqi a hasken qwan lantarki,duk inda ta gifta sai tabar sauran qamshinta a wajen.
Da sallama ta shiga,yana saman kujera a zaune yana ta aiki da system,kansa ya daga ya kalleta,ya zuba mata idanu,tayi masa kyau sosai a idonsa,iman din badai kyau ba,wani irin kyau ne da ita da baya dusashewa,ko don yanzunne take kan tashen shekarun quruciya da kyan nata?,komai nata daban yake,komai nata na musamman ne.
Sake maimaita sallamar tata tayi sanda ta iso gabanshi,duk da cewa ba wannan ne karon farko,ta saba da halinsa na rashin damuwa da amsa sallama,idanunsa ya lumshe yana amsa mata,yana da feelings sosai akanta wanda har yanzu bai kasheshi ba,saidai kuma ya rasa abinda yasa duk sanda yazo gareta haka tae faruwa dashi,ita kadai.....baisan daga ina matsalar take ba,tun yana damuwa har takai ma ya rage damuwa akai.
"Wannan kwalliyar tayimin,ya kamata na biya farashinta" murmushi ta sake,tana jimawa bataji kalami mai dadi daga bakinsa ba,har takan manta da cewa akwai wasu kalmomi masu dadi da sukayi saura a tsakaninta dashi da zasu iya furtawa juna
"Na gode" ta ambata tana ajjiye masa shayin.
System din taga ya ajjiye ya laluba wasu takardu ya ciro cheque,rubutu yayi akai sannan ya miqa mata
"Na biya kudinta" ya fada yana miqa mata cheque din.
"Na gode" ta ambata tana karba,ta juya tana duba abinda ya rubuta ajiki,naira dubu dari ce.
Gefanta ta ajjiyeta tana tatara hankalinta akansa,don ba wannan ne a gabanta ba,sam yanzu ire iren wadan nan kyaututtukan nashi basa damunta balle ma su burgeta,saboda ta rasa dukkan wani abu daya kamata ace ta samu daga gareshi,kulawarsa da kuma lokacinsa dukka samunsu sun zame mata wani kayan gabas,tana yunqurin bude baki ta fara magana kira ya shigo wayarsa,kamar kowanne lokaci tabi wayar da kallo,bacin rai da baqinciki suna cikata,bata da wani sakewa dashi matuqar wayarsa zata kasance a bude.
Shima kamar wasu lokuta da dama haka ya daga wayarsa abunsa a gabanta,briefly yace zai kira idan ya gama abinda yakeyi,ta bishi da kallo ranta yana quna,bayajin kunyar daukar wayar duk wadda ta kirashi a gabanta,yau din dai ta kasa cinyewa
"A gabana bassam.....a gabana kake daga wayar wasu?" Fuskarsa yada tsuke,saboda ya tsani tayi masa qorafi akan hakan Ai bai kamata ace kina damuwa ba,tunda dai kinsan mutum kamata bazai rasa masu tayawa ba,suna nan jingim da yawa,a cikinsu kuma na zaboki" ranta je taji ya sosu da abinda ya fada,sai kawai ta miqe,yana yawan fadin magangun da bai kamata ace ya gaya mata su ba
"Na godewa Allah da bani na taya ba,nice wadda aka taya" daga haka tayi gaba abinta,tana jiyosa yana faffadar maganganu amma tayi banza dashi,daga baya bayan wasu mintuna data koma dauko wayarta,saita sameshi ya bararraje abinsa yanata hirarsa,kana masa duba daya zakasan da mace yake waya,wani abu ya tokare mata wuya,tana komawa sashensa ta shige toilet tasha kukanta sannan ta wanke fuskarta ta fito.
Tana da tarin matsalolin da batasan dawa zata tattauna ba,waye zai bata shawara,a yanzun bata buqatar shawarar munira,saboda abinda ta fuskanci madubin hangen nesarsu a yanzu ya bambanta dana juna,kowanne a cikinsu da irin abinda yake hangowa daya saba dana danuwansa,a yanzun munira na cikin rudu da gushewar gano abinda gobe zata iya haifarwa kamar yadda itama ta tsinci kanta a ciki watannin baya,wanda sai a yanzunne hijabin daya rufe kwanya da idanunta yake yayewa sannu a hankali,wani baqin gani mara kyau da kuma dimuwa yake bayyana a gareta.
Al'ameen shine sunan daya fado mata a rai,saita lumshe idanunta hawaye suna saukar mata,tana da yaqinin idan da ace aurenta kamar kowanne irin aure ne.....shine mutumin da zaiyi ruwa yayi tsaki wajen shiga matsalolinta da damuwarta,ta tabbatar da babu yadda za'ayi ya tsinci kanta a kadaici irin haka,ba zata rasa mafita ba,ba zata rasa abokin shawara ba,tun ranar daurin aurenta bata sake ganinsa ba,bata sake sanin a wanne hali da yanayi yake ciki ba,hasalima bata san ina hake ba,don kusan zuwanta gidan uku bayan aure da daddare,duk da ba jimawa take ba amma bataga koda gilmawarsa ba,taga sadiqu kuma yaci ace shima ta ganshi,zuwanta na farko taji anyi xancen ya tafi wani waje to ina yaje?,bata sani ba,bata kuma dame amsa mata.
Bai shigo dakin ba sai wajen qarfe daya saura na dare,har a sannan tana kwance kanta na mata wanu matsanancin ciwo saboda tunane tunane da suka cika mata kwanya,a hakan zaka tsammaci bacci take,saidai idanuwanta biyu,har ya gama abinda zaiyi ya haye gadon yaja bargonsa abinsa,ba jimawa taji tashin munsharinsa.
Idanunta ta runtse,wasu hawaye masu dumi suka gangaro mata,a haka munira take cewa ta share tayi sabgar gabanta?,ta dauka cewa samun kudi da sutura da cima kadai sune dadin aure kamar yadda a baya dukkaninsu qwaqwalensu suka basu?,ba shakka tana kan kuskure,wanda bata fata yayi mata jagoranci zuwa rayuwar data tsinci kanta yanzu ita a ciki.
Watansa guda da dawowa ya sake shirya wata tafiyar,wadda zai dauki a qalla wata biyu acan kafin ya dawo,tafiyar data zama mabudin budewar komai,da kuma wani irin rikici daya sake sanyo rayuwar aurenta a gaba.Ya tafi ya barta kamar kowanne lokaci,babu kulawa daga kowanne sashe,sai azabar kadaici da zaman shuru,wata daya da sati biyu da tafiyarsa safiyar wata lahadi30 safiyar lahadi
Tunda gari ya waye tana kwance bata tashi ba,tunda ta idar da sallar asuba,saboda tasan cewa babu wani abu da zatayi koda ta tashin.
Ciwon ka take fama dashi matsananci sosai,wanda ta kusa a qalla wata daya tana fama dashi,tun bayan tafiyar bassam din,koda ba'a gaya kata ba tasan yana da qaqqarfar alaqa da yawan tunani da kuma damuwa da take kwana ta wuni a cikinta.Babbar damuwarta yanzu a rayuwa yadda zata dai daita da inna da kuma malam,ta sani cewa mutum daya ne a rayuwa a yanzu zai iya daidaita tsakaninsu AMEEN,wanda shi kuma a yanzun batasan a wacce duniyar yake ba,ko giyar wake tasha tasan bata isa ta fuskanci ya sadiqu ba,tana da yaqin ranta sai yayi matuqar baci fiye da abinda inna da malam zasuyi mata,dukka danginta ba'a kusa suke ba bare taga wasu,wadanda ke a kusan basu wuce su biyar ba,su dimma babu sa'anninta ko masu qananun yara yammata da zasu kawo mata ziyara bare su rage mata kewa.
Da qyar ta sauka daga saman gadonta,kanta kamar xai fado,ta shiga kitchen ta hada ruwan tea ta riqo a mug ta dawo dakin,gefan gado ta zauna,ta jawo wayarta ta fara laluben number munira,saboda shekaran jiya tace mata zata zo,tanaso ta tabbatar zata zo din.
A kashe wayar tata take,sai ta bude data taba fatan samunta online,tunda wani lokaci akan sameta ta WhatsApp,koda layinta bai shiga ba.
Ta sama take kallon notification na wayarta,saqonni keta shigowa,idanunta suka fada kan wata baquwar number,wadda ta turo jerin hotuna har guda shida,batasan number din ba,hakan ya sanyata ta fara bude saqonta.
Rubutune kamar haka daga farko
hi me gadin gida,ina fatan wadan nan hotunan zasu debe miki kewar wuninki na yau,asha kallo lafiya_
Mamaki ya cikata,ta dannan hotunan cikin sakanni suka bude mata,tarwai kamar gilashin madubi.
Mummunan faduwa gabanta yayi,Har mug din hannunta yana subucewa daga hannun nata,ya fadi a qasa ya tarwatse shida ragowar tea din dake ciki,innalillahi wa inna ilaihi raji'un ta shiga furtawa hannayenta na rawa,zuciyarta na bugawa da gudu kamar zatayi tsalle ta faso qirjinta ta fito waje,tuni ta dade a tsaye tana bin hotunan da kallo daya bayan daya,duk da yadda hannunta ke rawa amma bata fasa binsu daya bayan daya ba,saboda tana jinta ne kamar a duniyar mafarki ba a gaske ba.
Wasu irin qazaman hotunane na bassam shi da wata qedara wadda babu alamun digon musulunci tattare da ita,hotuna ne da babu abinda suka boye na tsiraicin dake jikin dan adam,wasu hotunan suna kwance saman katafaren gadon da dakin yafi kama da hotel,wasu a bakin beach harda wadanda akayi a toilet cikin bathtub,abun babu ko kyan gani.
Jiri ne ya debeta yana shirin kayar da ita,tayi hanzarin komawa ta zauna,wayar ta sulake gefe,sai ta saka duka tafukan hannunta saman fuskarta,ta lullube fuskar,sannan ta fashe da wani matsanancin kuka,nadama da dana sani tana cin zuciyarta.Kuka take haiqan cikin tashin hankali,babu me rarrashinta ko bata baki,tunda take a duniyarta bata taba ganin abinda ya daga mata hankali irin wannan ba,ashe dama haka bassam din yake?,neman mata yakeyi?,kenan lafiyarsa qalau?,ita yake rainanawa hankali ko kuma me?.
Cikin matsanancin hali ta wuni ranar,zuwa dare saiga wani saqon da yafi wancan muni,gajeran video da yasanya numfashinta wucewa,bai dawo ba sai bayan wasu sakkanni,ta dauki wayar tayi wurgi da ita tana gunjin kuka mai sauti,kamar ta tsaga qirjinta ta fidda zuciyarta haka ta dinga ji.Kwananta uku cikin wannan halin ita daya,ta fede ta rame ta lalace ta kuma zabge,depression ya fara kamata,kamar wata mai matsala a qwaqwalwa wani lokaci,ita kadai zata tsaya gaban madubi tana zantuka da kanta tana kuka.
A kwana na hudu munira tazo,ba zata iya gaya mata komai da komai ba,tsairaicin mijinta ne,kai batajin ma muniran zata iya bata shawarar da ta dace,don daga isowarta gidan ta fara surutu kan motar da aka yiwa iman din kyautarta,motar da tunda ta hauta sau daya bata qara hawanta ba,hasalima bata ita take ba,ta kanta takeyi a yanzun,bata buqatar dukkan wani abu daya fito daga hannun bassam din,komai nashi a qazanta take kallonsa,tadai gayawa muniran abunda ke faruwa sama sama,sai ya dan tabe baki
"Shine kika zauna kika fige haka?,to don Allah ta yaya zaki raba mutum irin bassam da yammata da matan waje?,kina ganin yadda Allah yayishi,bai rasa komai ba,su sauran matan dake gidan wadata an gaya miki haka suke zaune basu da matsala,tunda dai.baki rasa komai ba ki barshi yayi sabgarsa kema kiyi naki sha'anin,tunda ya sakar miki mara,bai takuraki ba,wadda take miki ture turen aurenki takeson kashewa kawai" shuru tayi tana mamakin munira,lallai wanda Allah ya ganar dashi ya huta,saita rabu da ita ita da banzan tunaninta.Cikin rahama da jin qan ubangiji,da wani yammaci tana kwance a bushe kamar wadda ta shekara jinya,ubangiji ya aiko mata da bushira,qawarta tun zamanin yarinta.A gigice ta miqe ta nufi bushira,suka rungume juna
"Bushira,ya akayi kikasan gida na?,yaushe kika dawo?" Tambayar data fara jefa mata kenan tun kafin ta zauna,murmushi tayi tabi iman da kallo
"Amarya hala laulayi kika fara,irin wannan dashewa haka?" Maganar sai ta taba zuciyar iman din sosai,har rauninta ya bayyana saman fuskarta,duk.yadda takai ga dannewa saiga hawaye suna ambaliya kan fuskarta,rudewa bushira tayi sosai
"Subhnallah,meye haka iman?,daga magana?,ko na miki ba dai dai bane?" Kai ta girgixa ta qanqame bushira tana fashewa da kuka
"Ina cikin tashin hankali bushira,tunda nayi auren nan ban taba jin dadinsa na kwana uku ba,Allah ya mallakamin abinda na nace akansa,amma kuma sai ya barni da iyawata"
"Zauna muyi magana a nutse" bushira ta fadi tana zaunar da ita saman kujera hankalinta a tashe,babu haufin komai ta shaidawa bushira duk yanayin da take ciki,saboda a duniya a yanzu cikin ranta tana jin babu qawar data kai qawar quruciya,qawar islamiyya,qawar da aka tashi a unguwa tare,qawar kusa da gida wadda ta fito daga gidan tarbiyya,ki qaraci tara sabbin qawayenki,daga makarantu ko ma'aikatu,qasashe da garuruwa,mawuyacine ki samu irinsu,sun saki kin sansu ciki da bai.Bushira ta jina jinjina tarin matsalolin da suka dabaibaye iman din watanni kadan da aurensu,ba shakka akwai wata a qasa,saita daga kai ya dubeta
"Me ya kawo rashin aurenki da ya amin,don na tabbatar nayi imanin yana sonki,sonki yakeyi kamar yadda nayi miki hasashe" kai tsaye ta amsa mata da furucun dake fita daga bakinta cike da tarin nadama qarara
"Ya ajjiye duk wani abu a gefe ya kalleni ya gayamin yana sona,amma nasa qafa na shure,na shaida masa bana sonshi bassam nakeso,saboda a lokacin soyayya ta rufemin idanu,ina ganin bassam ya fishi cancanta Duk abinda ya biyo baya ta gaya mata tsaf
"Subhanallah" bushira ta maimaita sau uku sannan ta dora
"Dukkan wata matsala da kika ci karo da ita,kece kika kirawa kanki ita,tun inaca na fara jin wai wai 'yan gidanku basuson aurenki,na tabbatarwa kaina akwai abinda yake faruwa iman,bakisan ba'a musu da iyaye ba?,bakisan bayan bautar Allah kada ka hadashi da abokin tarayya babin iyaye shine abu na biyu da Alla yake fadi ba?,saboda girmansu ya hada haqqinsu da bautarsa?,bakisan koda kin fisu gaskiya da hujja qarara mabayyaniya mawuyacine Allah bai jarrabeki ba?,abar ta batun ya alameen tunda yanzu wani kike aure amma inason na gaya miki,kin tafka babbar hasarar da bazaki maida gurbinta har abada ya alameen?,kusan shi ya raineki,baya ga inna da malam yafi kowa sanin ciwonki,yafi kowa sanin me kikeso da kuma abinda bakiso?,yafi kowa tattalinki?,shine karatunki suturarki da duk wata walwalarki,koda qiyayya kike masa azuciyarki haiqan....iyaka wadan nan abubuwan basu isa su tsaidashi a mizanin wanda ya cancanci aurenki ba?.iman.....ina tunaninki ya tafi da har kika zaci samun wani makwafin ya alameen a duniyarki?" Fuskarta ta kifa gaba daya saman pillow,tana jin tsakiyar kanta kamar ana yamutsa mata kwanya ko ana mata hajijiya a tsakiyar kanta.
Yanayin yadda ta shiga rudu da yawa ya sanya bushira sassautawa,ta fara kwantar mata da hankali da kalamai masu taushi,bayan ta sanyata ta sauke dukka wani social network dake wayarta,ta kuma shaida mata ta jirayi dawowar mijinta,ta bibiyi maganar a nutse,kada tayi hanzarin yanke hukunci gudun nadama ko dana sani,saboda zai iya yiwuwa sharrin mace ne da kaidinta,muhimmin abu kuma na qarshe da taja hankalinta shine,ta nace ta kuma dage ta dai daita tsakaninta dasu malam
"A yanzu babu abinda nake da buri sama da na ganni a tsakiyar mala da inna,saidai abunda nake fuskanta a duk sanda naje ganinsu da sunan ziyara ya tursasa min zama gefe guda,abunda ke cikin idanuwansu da irin kallon da sukeyimin,sun gaza fahimtar ba dukiyar bassam bace ta jani ga aurensa,koda akwai tasirin dukiyarsa wallahi bushira bame yawa bace,amma rannan inna cemin tayi,wai na matsa da zuwarmusu gida,ta zaci zan canza wasu iyayen ne ai masu wadata,tunda sudin basu da komai,basu kuma ajiye komai ba Kai bushira ta jinjina
"A irin wannan situation din ba kowa ne zaki gaya masa haka ya yarda ba,amma hakanan zaki ci gaba da zuwa kina fuska tarsu da dukka maganganun da xasu gaya miki,yawan maganganun da zasu gaya miki yawan dafi da tsatsar dake wankewa daga zukatansu a kanki kenan,a haka a hankali a hankali komai zai dinga wankewa daga zuciyarsu" kai ta gyada,qwarai taga hikimar hakan,hasashen bushira yayi dai dai
"Amm sannan kuma" bushira ta fadi baya tayi gyaran murya,da alama maganar da zatayi tadanyi mata nauyi
"Maganar matsalar mijinki,ya kamata ki tuntubeshi ku tattana,zama haka bazai yiwu ba,duba da cewa haqqinki ne a kanshi" ta qarashe maganar tadan murmusawa kadan. Dan qaramin tsaki iman taja
"Manta da wannan bushira,ana ta kai wa yake ta kaya?,a wannan yanayin da nake ciki?, infact ma gaba daya Allah ya zaremin abun daga zuciyata,sau tari ka nakan tambayi kaina ko bani da cikakkiyar lafiya ne?,ko romance din da muke na gaza jin wani cikakken wani abu akansa......ni bushira ban ma yarda baida lpy ba zuwa yanzu,idan har hakane,me yakewa ita wannan karuwar data turomin hotunansu cikin qazamin yanayi?,jagwalgwalon da yakemin itama yake mata?" Tayi maganar wani abu me daci da tauri yana tsaya mata a maqoshi.
Girgiza kai bushira tayi
"Kada ki zargi haka,karuwa ce,indai yana da kudi koda bashi da mazantaka zata iya zama dashi,matuqar zai kashe mata abinda yake dashi,dama ba abunda sukeyiwa kenan ba?" Kai iman ta gyada mata,tana dan samun relief cikin zuciyarta,ita kanta bushiran tasan ta gaya mata hakanne kawai saboda ta kwantar mata da hankali.
Cikin yanayin quncin da take ciki kaso dari kaso hamsin ya zagwanye,bushiran ce ta tada girki da kanta ta shiga kitchen,ta shirya lafiyayyar jalop rice,ta zuba musu tare,ta hilaci iman din sai data ci mai dan dama,saidai har zuwa sannan kanta na mata ciwo,tana daurewa ne,sannan ta danji qwarin jikinta abincin da taci.
Ya kamata shima kije kiga likita,bai kamata kita zama da ciwo me naci irin haka baki nema magani ba" bushira ta bata shawara sanda ta shirya zata tafi,kamar ta hana bushiran tafiya haka taji,zuciyarta ta dinga yi mata rashin dadi,batasan tayi missing childhood friend dinta ba sai a yanzu. Haka ta rakata har qofar gate,bayan ta saka mata kudi masu yawa a jakarta,wanda sai da tasha qwarbai da bushiran sannan ta karba,a take ta hangi bambamci qarara mai kuma tarin yawa tsakaninta da muneera.
"Anya da bushira ce muneera zata barni na auri bassam na qyale ya ameen?" Tambayar data dinga yiwa kanta kenan sanda take dawowa zuwa sashents
"Muneera qaunata take ko kuma qina?" Tambaya ta biyu da tazo kanta kenan,wadda ta kasa tantance ta.
Tana sanya kai a parlor din nata taga shigar fahima dressing room dinta,cikin mamaki tabi bayanta,duk da tuni zuciyarta ta gama gaya mata abunda ya shigo da fahiman,tunda ba yaune karonsu na farko da suke mata irin hakan ba.
Dai dai sanda ta shiga fahiman tayi nisa a dudduba laces dinta dake rataye jikin hanger,sau daya ta juyo ta dubi iman din taci gaba da abinda takeyi,kai bakace gidanta kuma dakinta ta shigo mata kanta tsaye ba tare da saninta ba.
Daya daga cikinsu ta ciro daga hanger din,ta kalli jikinsa sosai sai ta ninkeshi,ta matsa sashen takalma ta fara dubawa suma.
A yau din ranta a matuqar bace yake da rainin hankali da kuma iskancin da suke mata,abun ya fara wuce makadi da rawa,sun kuma fara wuce iyaka,don haka ta bude bakinta da dan qarfi tace
"Wai lafiya kiketa yimin dauki dai dai cikin kayana?" Juyowa tayi ta watsa mata wani kallon banza
"Kayanki ko kayan yayana?,ins kukaga arziqin da zakizo da wadan nan kayan daga gidanku" maganar ta sake tunzura iman,a fusace ta qarasa cikin dakin,bata tsaya wata wata ba ta fusge lace din dake hannun fahiman
"Duk da yayan naki ne ya siya na hana bazan bayar ba,matuqar da sunana yayan naki ya siya to babu wanda ya isa ya dauka ko ya tabamin kaya babu izinina,ki fita ki bani waje tun zuciya bata debeni na miki matsiyacin dukan da za'a sake ganeki" tabbas a yadda taga idanun iman din sun sauya kala tana kuma bubbudesu da kyau,furucinta ke nuna tsantsar tunzurarta,tunzarar da bata taba ganin tayi makamanciyarta ba tabbas zata iya aikata abinda take fadi,don haka ta saici hanya tana dubanta Zakisan dani kike,sai kinyi nadama
"Na jima banyi nadamar ba,wacce nadamar ce ta ragemin banda wadda nake ciki,yi waje!" Sai fahiman ta juya tana ficewa daga dakin,iman din kuma ta zube a wajen dafe da kanta da takeji kamar zai tarwatse[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 31
Da qyar ta kawo lanta parlor dafe da kan nata da yake sara mata kamar xai fado,tana zaune anan taji anata fama knockin
"Madam ki bude.....hajiya ce take kiranki" abinda 'yan aikin da mom din keta aikowa taxo suke fada kenan ta window dun parlor,saidai babu wanda ta saurara a cikinsu bare ta bude musu qorar.Muryar mom dince daga qarshe ta bayyana da kanta a qofar falon,saidai a sannan sama sama ma take iya jin abinda take fada,saboda yadda kunnuwanta sukayi dimm gaba daya,ta daina gane komai kamar wadda ta suma,irin suman nan na ido biyu,kamar kuma wadda ta tafi duniyar mafarki Sanda ta koma normal data duba agogo awanni ta diba a hakan,ta miqe da qyar ta koma bedroom tana kiran sunan Allah.
Wannan ya sanya a washegari dole ta miqa kanta asibiti,dr ahmad Abdullahi shine likitan da take gani,yayi mata gwaje gwaje sosai,bayan ya kammala dubata,sakamakon da ya bayyana shine ta kamu da hawan jini,don jininta yakai 190,mamaki sosai ya kama dr ahmad,ya sake daga kansa ya kalleta,sannan ya duba shekarunta dake rubuce jikin file dinta na asibitin.hajiya aqananun shekarunkin nan bai kamata ace jininki ya hau har haka ba,ya kamata ki sakawa ranki nutsuwa da salama.....ko meye yayi zafi maganinsa Allah,kiyi qoqarin kwantar da hankalinki ko domin lafiyarki,hawan jini mummunan ciwo ne dake da hatsari da kuma barazana ga dukka sassan jikin dan adam" wani abu me nauyi taji ya sake saukowa saman qirjinta,ta kwantar da fuskarta saman hand bag dinta,tana jin kamar ta gayawa dr Ahmad matsalolinta,mutum ne mai bala'in nutsuwa haiba da kamala,wanda tun farkon zuwanta asibitin ta zabi ta dinga ganinsa,saboda alamomi na riqo da addini dake damfare dashi
"Kiyi haquri hajiya,at younger age naki irin wannan. ko 20yrs baki kai ba bai kamaci kibar wani abu ya gadar miki da ciwon da zai tarwatsa lafiyarki ba" bai nemi sanin halin da take ciki ba,amma yayi aikinsa na likita ya kwantar mata da hankali da kalaman da suka dace.Sosai tayi masa godiya,ta kuma sawa ranta zatayi qoqarin bin komai a sannu kamar yadda bushira da dr ahmad suka bata shawara.Daga asibitin gidansu ta wuce,ta dauki aniyar yau koda zasu koreta kamar yadda suka saba ba zata ko ina ba,yadda innar ta saba tarbarta haka yau dinma tayi mata,saidai yau din da sassauci bata nemi ta koma gida ba,qarin wani ci gaban yau din bata raba wajen zama da ita ba,saidai babu ruwanta da ita,kamar ma babu wata halitta a dakin sai ita daya.Ko iya hakan ma ya yiwa iman din dadi,tayi kwanciyarta kan doguwar kujerar dake falon tana bin innar tata da kallo,abinda yadan sake mata dadi,yadda kusan sau uku suna hada ido da innar sanda innar take satar kallonta,addu'a take cikin ranta,ubangiji ya sassauta mata,ya sauko mata da zukatan iyayenta ko zata samu salama ta wani bangaren.Shima malam din daya dawo yau data je ta gaidashi babu abinda yace da ita,sai da yana alwalar sallar magariba sannan yace idan ta idar da salla ta wuce gidanta,kamar ba zata tafi ba,kamar tayita zamanta da iyayenta,kamar ta dawo da rayuwarta ta baya haka taji,saidai bata da wani zabi,bata kuma da yadda zatayi,tunda ita ta siyawa kanta ta kuma biya,tafiya ta kamata dole.Daga ranar ta samu.nayi,duk sanda taje asibiti checkup saita zarce gida,ba zata koma gidansu ba sai magariba,wannan ya sassauta mata damuwarta qwarai da gaske,sai taji duka sauran matsalolin dake tsakaninta da bassam minus ne,duk da suna qasan ranta suna cin zuciyarta,bacin rai yakan dawo mata a duk anda ta tuna da munanan hotuna da videos din da aka tura mata.
A wannan karon batasan bassam din zai dawo ba saboda ta ajiye wayarta gaba daya,a yanz ta sake tsanar wayar kwata kwata,ta fita daga kanta Ranar bayan ta idar da sallar azahar,ta dama yoghurt na L&Z da lallausar furar data debo daga wajen inna da ko ci kanki batace da ita ba sanda tasa hannu ta diba furar,ta damata da yoghurt din tasha,bata fiya girki ba,saboda a yanzun sam bata da appetite,kome zata dafa ba dadinsa zataji ba,ta fidda hijabin kanta ta koma saman doguwar kujerar falonta ta kwanta rigingine,hannunta daya saman kanta,idanunta a lumshe,qira'ar shaik shary al_afasy data kunna jikin tv na ratsa falon a hankali,tana bin qira'ar da boyayyen sauti,saidai kuma kana iya ganin yadda qaramin bakinta yake motsawa.
Alamun bude qofar falon bai sanyata ta bude idanunta ba,don bata raba dayan biyu su fahima ne,duk da cewa tun ranar da abun ya faru babu wadda ta sake shigo masa sashe,saidai yadda taji alamun ana tahowa inda take ya sanyata ta bude idanun nata,ta zubesu saman guskar bassam dake sanye da suit ash colour,blue din qwayar idanunta suke fitowar ta saboda rashin kwalli da kuma kodewa da idanun nata sukayi.
Fuskarsa a matuqar murtuke,ta danne zuciyarta ta miqe daga kwanciyar datayi sanda taga ya iso kanta ya tsaya,ta dauki remote ta rage sautin karatun ca qasa sannan ga furta masa sannu da zuwa.
Ciki ciki ya amsa mata yana ajjiye trolley dinsa idanunsa nabin parlor din da kallo.yana sassauta tie dinsa,kamar me neman wani abu
"Me ya samu wayarki?,inatason in sanar miki dawowata amma ba'a samunki"
"Matsala ta samu" ta amsa masa a taqaice tana kaucew kallon qwayar idanunsa,saboda wani tsanarsa data ji ta saukar mata lokaci guda sanda yayi mata zancan waya,wani baqi take gani yayi mata a idanunta,dukk wani kwarjini kyau da qaunarsa da takeji ta laluba taji.babu ko guda daya
"Meye amfanin kudin dana bar miki da bazaki iya dauka ki sayi wata ba" haushi tambayar tabata qwarai,idan kuma tace zata bude baki ta bashi amsa maganar ba zata fita da dadi ba,don haka sai ta miqe kawai a maimakon ta amsa masa,tasa hannu taja trolly din nasa zuwa dakinsa,dakin da tunda yasa qafa ya tafi bata sake shigarsa ba,dakinta da aka zuba mata kayan ameen tafi jin dadin xama cikinsa sau dub
Dukka motsinsa tana ankare dashi,sai wani ciccin magani yake da bata fuska kamar wadda tayi masa wani abu,abunda ya sake bata mata rai da dugunxumata yadda wayarsa ta fara harbawa da kira don masifa,ko awa guda biyu da shigowa cikin gidansa ba,kiran yana shigowa yana katsewa.
Banason hauka..just two hours?,ba haka mukayi dake ba,karki sake kirana,ki barni na huta" sune kalmomi na qarshe da taji daga bakinsa sanda take fitowa daga bandaki bayan ta gama hada masa ruwan wankan da ya buqata.Maganganun da suka tsaye mata a rai kenan,suka kuma sake fama mata mikin dake ranta,ta dinga hadiyar yawu da qyar,ko baya data gama hada masa abincin gaggawan data shirya masa takai masa daki parlor ta dawo tayi zamanta,bata tashi daga wajen ba saida lokacin sallar la'asar ya gabato,sannan ta koma dakin.
Bacci ta sameshi yana yi haiqan kamar wanda yayi tafiyar qasa,kamar ya shareshi ta wuce sai kuma taga bai kamata ba,a qalla akwai hakkin salla a wuyansa,don haka ta qarasa ta fara qoqarin tadashi,saidai juyin duniya yaqi tashin yace ta rabu dashi,ba tun yau ba,bai cika damuwa ba da lokacin sallah saboda ya kubce masa.
Kwarai taso dauke kanta daga wayarsa daketa blinking,da alama a silent ya sakata,saita dawo da baya,zuciyarta na rinjayarta kan ta duba wayar ko zata samu haske kan abinda yaqi gushewa daga zuciyarta,yake kuma kai komo.
Sofa din dake dakin can wata corner ta koma ta zauna akai,hannunta na rawa zuciyarta tana bugawa ta bude wayar,babu nambobin sirri,hakan ya bata damar wucewa kai tsaye zuwa WhatsApp dinsa.Charts ne burjik da 'yammata iri iri,wasu hausawa wasu yare,harda 'yan wasu qasashen,dukka hirace dake nuna qauna da soyayya tsakaninsu,sai kuma receipt na kudaden da yake turawa wasu daga ciki.Harta gota sunan ta dawo da baya,tabbas yayi kama da sunan wadda ta tura.mata saqo wancan watan,ba tare da bata lokaci ba ta danna ta shiga.bata tsaya duba saqon qarshe ba tayi scrolling zuwa sama,saboda tana son sanin meye tsakaninta dashi tun daga farko zuwa yanzu,sai data je qarshe sannan ta fara bin saqonnin,wanda suka fara ne ran uku ga wata,data duba date yayi dai dai da kwananta guda a gidan bassam din,saqon farko shine ya fara tura mata shi kamar haka
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 32
_Baki da hankali ashe jessica?, Da gaske kike dama sai da kika aikata din?,ta yaya zaki haramtamin matata ta sunna?_
Emoji na dariya ta fara aiko masa sannan tace
_mahaukatan ai biyu ne,wato ni da kaii,ta yaya kake da tabbacin bazan aikata abinda na niyyata din ba?,ta yaya kake tunanin zan sake barwa wata diya mace kai?,shekara biyar?,cikakkun shekaru biyar kana yaudarata kan zaka aureni,to na gaji da alqawarin banza,daga yau din kai nawa ne ni kadai,naga macen da zata sake morarka bayan ni_
Bayan wasu sakanni da basu da yawa ya maida mata amsa
_karkiyimin haka?,ki fadi ko nawa ne zan biyaki_
_banason komai daga gareka,aurena nakeso kawai kayi_
_kinsan me kike cewa?,addininmu ba daya bafa?_
_eh,kowa sai yayi addininsa ai ko_
Sauran maganganun da suka biyo baya gaba daya ciki bacin rai yake mata su,da kuma barazana,daga qarshe saqonnin suka yanke,suka shiga wani kwanan watan na daban.
Hoton passport dinta ne da aka bugawa visa ta qasar daya ce mata zaiyi tafiya a sannan,idanu iman ta fitar tana jin wani tashin hankali,dukka saqonnin sun bayyana mata cewa dukka tafiye tafiyen da zaiyi da Jessica yake tafiya,ita ta zame masa madadinta.
Tashin hankalin da ba'a saka masa rana,wato daman watace tayi masa sihirin da bai iya aikata komai idan bada ita ba garin biye biye da neme nemen matansa?,wannan wacce irin masifa ce,dama tafiyar da yakeyi tare suke tafiya,ashe shi yaba samun abunda yakeso shi yasa ya jingineta,ya daina damuwa da situation dinsa,ashe ba lalura gareshi ba?.
Kamar yasan meke faruwa yayi juyi cikun barcinsa da zummar gyara kwancinyarsa,idanu suka hada tana riqe da wayarsa hawaye sun mata face face saman fuska,sai yadan miqe da hanzari ya zauna saman gadon
"Me kikemin da waya?,miqo min wayata" yayi maganar yana hade rai,cikin sautin kukan data kasa controlling dinsa ta fara magana
"Ashe dama haka kake bassam?,ashe kai din baqin kumurcin maciji ne?,ashe dafin da yake tattare dakai kenan?,manemin mata ne kai wata kake dauka kuyi tafiya nisan duniya wata da watanni kabar matarka ta sunna a gida?baya ga tulin yammatan da kakewa hidima bassam,har wata ka ajiye?,dadironka......." Tsawa ya daka mata
"Dalla malama dakatamin mana,ni zaki saka a gaba kamar dan cikinki kinamin wanna titsiyen?,ko uwata bata isa ta bimin qwaqwaqwafi haka ba bare ke,abinda yasa tun farko banson aure saboda banason bin diddigi da takura,kema da nake ganinki me mitsi mitsin shekaru har kinsan bin diddigin spouse dinki?,yaushe kikayi wannan wayon?" Cikin bacin rai ta fara maida masa amsa
"Ko yau nafado duniya matarka ce ni,kuma ka dade kana wasu abubuwan a gabana ka manta?"
"And so what?,eh matatace ke......me kika rasa?,ci sha suttura ko kudi?"
"Basu nake buqata ba,don ba don saboda su na aureka ba" wata dariya ya saki yana zuro qafafunsa qasa idanunsa cikin nata
"Zuqi ta malle inji bahaushe,shi yasa naga kinqi dan uwanki ko.....ke,bari na gaya miki,tarrr idanuna suke kallo kowacce mace,a zamanin nan dama mace tana maka soyayyar gaskiya ne?,duk wadda tace tana sonka saboda Allah qarya take maka,shi yasa nake amfani da damata,in kashe miki kudi nima na amfana dake,na sakar miki komai......saboda haka banason takura ko kuma sanya idanu,ki barni nayi rayuwata yadda na saba,banason takura" cikin xafi da tsananin fushi ta miqe
"Amma ka shayar dani ruwan mamaki bassam...."
"Bakiga komai ba,abinda kika gani kika maqalen shi sauran suka gani suke tare dani,kalleni sama da qasa......wanda bai kaini komai da komai ba ya tara yammata bareni da babu abinda Allah ya rageni dashi, relax 'yammata,kici arziqi kibar arziqi a inda yake,idan kina tunanin zan zauna nayita lallabaki yanzun kina batawa kanki lokacine kawai,i already won the election.......so no need naci gaba da campaign,kin gane?"
"Amma ka zalunceni,ka cutar dani,kakuma cutar da zuciyata......".
Dif wuta ta dauke mata saboda saukar wani zazzafan mari saman kuncinta,wanda ta manta a duniyarta rabonta da irinsa saboda gata da kulawa da take samu
"Stupid kawai........don kinga na qyaleki bayan iskanci da wulaqancin da kikayiwa mahaifiyata?,ina da labari fa amma na dage miki qafa,ko kin dauka nima bansan kima da darajarta ba kamar yadda bakisan kimar naki ba?to ki kiyayeni wallahi, you worth nothing to me,ni mace ba kayan gabas bace a wajena,yanzu yanzu ina iya wullar da ita na canzata da wata" Kalamansa sun matuqar girgizata tare da taba mata tunani,ta kasa koda qwaqwaran motsi bare ta aiwatar da komai,hannayenta saman kuncinta har ya zura slippers dinsa yana jan tsaki bayan ya dauki wayarsa ya fice daga dakin.
Komai tsaya mata yayi cak,ta daina gane komai ta kuma daina fahimtar komai,batasan me zatayi ba,kamar yadda batasan meye abu na gaba da zai sameta ba,saida jikinta ya bata amsa ta hanyar daukar rawa,wanda a take zazzabi yayi mata kirif,jikinta gaba daya ya fra shaking,qafafuwanta suka gaza daukarta,ta sulale a wajen ta cure waje daya.
Wani mugun zazzabi mai uban huci ne ya rufeta,ta jima zaune a wajen kafin taja jikinta zuwa nata dakin,tayi curewar alkaki tsakiyar gadon.
Maganarma ta hana kanta kuka bata taso ba,duk da yadda takejin kanta yana barazanar rabewa gida biyu,ji take kamar duniyarta zata tashi,nadama iya nadama,dana sani mara iyaka wadda ta ninka wadda takeyi a baya tun 'yan kwanaki da aurenta da bassam,ashe ita din banza ce?,ashe ita din wawuya ce?,ashe itadin bata da hankali?,dukka a ture abubuwan da suka faru gefe,a dauko maganar sanin ya kamata dangane da iyaye,tabbas ta tozarta su malam da inna,ta kuma ci amanar ya alameen,ta tabbata BUTULU KUFAN WUTA kamar yadda inna ta kirata dashi,kallonta kawai bassam yakeyi?,amma yayi mata shuru tun a sannan bai gaya mata gaskiya ba saboda burinsa na aurenta?.
Ya tabbata bassam fasiqi ne........haka dabi'arsa take ko daga baya ya sauya,sam sam wannan ba bassam din data sani bane,ba shine bassam din da tayi soyayya dashi a waje bane,shi kadaine hakan?,ko dukka maza haka suke?.
Kafin wani lokaci yanayin da take ciki ya ta'azzara,taji kamar ranta na shirin fita ta numfashinta ne,ta tabbatar taci gaba da zama a haka komai zai iya faruwa da ita,asibiti yafi kamata taje,to amma waye zai kaita?,waye xai tallafeta,bushira da munira sukazo kanta,bushira bata iya tuqi ba,munira ta fita wayewa ta wannan fannin,duk da a yanzun bataso ko qaunar alaqarta da munira taci gaba,amma dole ita din xata kira.
Tana tsaka da yi.mata bayani numfashinta ya fara seizing,wayar ta sulale mata,ta runtse idanunta tana ambaton sunan Allah.
Sanda munira ga qaraso tuni ta fara ficewa daga hayyacinta,haki take sosai,muniran ta kamata bayan ta duba key din motarta,suka fito ta sanyata a motar suka fice ba tare da kowa ya sani ba.
Cikin sa'a suka taras dr ahmad ne on duty,cikin gaggawa ya karbeta ya shiga bata taimakon gaggawa,hankalinsa yayi matuqar dugunzuma da ganin yanayin da take ciki,at her age bai kamata ace tana shiga mummunan yanayi haka ba,shekarunta sunyi qanqanta da yawa,don haka bayan ya daidaita komai ya shaidawa munira yana buqatar ganin iyayenta ko mijinta.
Washegari ta tashi jikinta da dan dama dama,saidai kuma babu qarfi sam,
"Tun jiyan na gayawa bassam kinga har sha biyu na rana na shirin yi bai shigo ba" inji munera dake danne dannen waya,kai ta kada,sam batayi mamaki ba,saboda gaba daya tasan cewa bassam ya sauya,ba shine bassam data sani ba,abun tambayar ina tulin soyayyar da yake mata?,ina tulin soyayyar daya dinga nuna mata?,ina tayi
"Bani waya na kira inna" shine abinda tace da ita maimakon tsayawa su tattauna batun bassam din,ta miqa mata,ta saka numbers din inna data dade da haddacesu ta soma kira.
Bugu biyu ta daga,cikin raunanniyar muryarta ta fara gaidata,innar ta amsa
"Inna bani da lafiya,ina asibiti"
"Allah ya sawwaqe,ya baki lafiya" ta amsa mata kai tsaye,sai shuru yadan biyo baya,iman din tayi ta maza tace
"Inna,ba zakizo ki ganni ba?" Maganar tadan taba innan,amma sai tayi kamar bata jita ba,qarshe ma dif ta yanke kiran.
Hawaye ne ya biyo kuncin iman din,ta tabbatar lallai tana neman taimako,tana neman sanya hannun wani babba cikin al'amarinta,idan ba haka ba za'a wayi gari a samu baqinciki ya kasheta.
Ba bassam ne yazo ba sai dare,koda yazo dinma fada ya fara yi mata wai kan me zata saka qafarta ta fice daga gidan bata shaida masa ba?,ai ba zaman kanta take ba,abun ya daure mata kai,don haka ta bawa banza ajiyarsa,ana tsaka da haka dr ahmad daya dawo zaiyi night round ya taras dashi
"Banda abinka,ai kone patient irin wannan yayi ba'a masa fada a yanayin da take ciki,gaskiya ku kula da.lafiyarta,saboda matuqar za'a bar irin wannan abun na yawaita faruwa da ita zai iya tana zuciyarta,ko ya sanyata ta shiga mummunan yanayi" sake duddubata yayi ya rubuta mata sallama da magunguna,tare da yi mata jan kunne kan ta kula da lafiyarta.
Ko a cikin mota babu wanda ya kula dan uwansa,tuqinsa yake ita kuma ta maida kanta saitin window,hadiyar zuciya kawai take tana qoqarin hana kanta shiga bacin rai saboda warning din da dr ahmad yayi mata.
Suna isa gida ta bude motar ta fice abinta,dakinta ta shiga,ta cire kayanta ta fara shiga ta watsa ruwa,ta hado da alwala tayi sallar magrib data kubce mata ta hada da isha'i,sai taji nutsuwa 'yar kadan ta saukar mata,sannan ta miqe ta fara laluben wayarta.
Batayi duba me yawa ba ta ganta,ta koma gefan gadonta ta zauna tana lalubar number wayar ya gana,ta tattara dukka nutsuwarta. Wayar na ringing zuciyarta na dade karyewa,rauni yana cikata,tana sake qwararawa kanta gwiwa,cike da fatan ya gana zata shiga lamarin nata,ta kuma samar mata da mafita.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 33
Ba jimawa muryar yagana ta bayyana da sautin sallama,muryarta na rawa ta amsa mata sallamar tata,da fari ya gana bata fahimta komai ba cikin muryar iman din ba,saima fara tsokanarta da tayi da cewa
"Ja'ira,tunda na miki haji da ummara kika manta dani sai yau da kika gama sheqe amarcin watannu shida?"
"Uhmmm" kawai iman tace,don idan tace zata bude baki ta bada qwaqwarar amsa kuka ne zai kece mata
"To ya gidan,ya angon naki?,ina fata anata biyayya ko?" Tamkar wannan tambayar kukan yake jira sai kuwa ta fashe dashi,a rude ya gana ke tambayarta lafiya,saidai ta kasa cewa da ya gana komai,sai sautin kukan dake fita daga bakinta,wanda ya faro ne tun daga qasan zuciya,yana bayyana tsantsar quncin da zuciyarki ke ciki.
Bata hanata kukanta ba,sai da tayi mai isarta sannan ta fara labartawa yagana komai,babu abinda ta boye mata a ciki.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" wannan kalmar yagana ta dinga maimaitawa cikin rudewa,hankalinta yayi matuqar tashi
"Kiyi shuru hajar,ya isa" ya gana keta fada
"Wannan shine abinda su malam ke guje miki, shine abinda muke guje miki gaba dayanmu" ta fada feeling her guiltiness,tana ganin kamar itama me laifi ce, da nata kason da ta sanya baki malam ya sauka daga qudirinsa,duk da cewa haka yaran sukaso,duk da cewa babu wanda yasan gaibu,ba wanda yasan hakan zata kasace sai Allah jalla wa 'ala.
Kwantar mata da hankali ta dunga yi da kalamai masu taushi,tare da nuna mata illar saka damuwa a ranta a situation din da dr yace tana ciki a yanzu,daga bisani ta bata shawarwari da kuma jan hankali
"Kowanne gidan auren akwai nashi qalubalen hajar,ki zama jajirtatta ki aiki tuquru ki gyara gidanki,zanzo kanon zan zauna da malam da binta din,suma dole zuwa yanzu su sauki ai su tayaki da addu'a,idanma sunqi na tabbatar cikin zukatansu babu wanda zai kaisu dakuwa da halin da kika shiga" ba maganar data sake sa mata nutsuwa irin wadda yagana din ta gaya mata na zata sasanta tsakaninsu dasu malam din.
Sun jima kan waya tana bata addu'o'i da shawarwari,har sai data tabbatar da ta samu nutsuwa.
Ta sake kiran bushira ta shaida mata,itama ta shiga damuwar,saidai shawarwarin data batan sunyi kusan kamanceceniya dana yagana,duk abinda suka fada ya dace kuma dai dai ne,saidai abu daya da takeji cikin ranta,bassam da aurensa gaba daya sun fice mata fit a rai,kamar fitar kibiya daga cikin baka,wannan ya bata salama,ta tattara hankalinta wajen shan maganinta,tsakaninta da bassam saidai kallo,sai kuma idan sun hadu a parlor,wannan yasa ya dauka fushi take dashi shi yaaa ta watsar dashi,shi kuma sai ya dauki aniyar quntata mata,hakan yasa ya sake fidda ainihin halayyarsa,yake baje kolinsa na hira da 'yammata barkatai,da kuma fiya joint joint dasu yana musu barin kudi,bata duk wani chart bare ta gani ranta ya baci,whatsApp kawai takeyi,shima kuma already tayi mute na status din nasa.
A yanzu kallon kanta take a matsayin me gadin da gaske cikin gidan bassam din,komai nashi ya daina damunta,hakanan ta tattara rayuwarta waje daya,kama daga suttura da dakin kwana ta koma amfani da wanda tazo dashi daga gidansu,sai abunda ya kama dole zatayi amfani da nashi.
A hankali ta fara samun sauqi da nutsuwar rai da ruhi,musamman data maida alqur'ani abokin hirarta,gaba daya ta zama wata iri,wani irin sukuku,ba hirar nan ba kuzari me yawa,babu kuma wani ado na azo a gani,saidai bata yada tsafta da kuma qamshi ba,saboda dashi aka raineta.
Bata damu ba sam,tunda yanzu ta samu matsayin kiran malam da inna su daga,ta kuma gaishesu,hakanan idan taje sun daina korota gida,iya wannan ya isheta.
Bushira na dan zuwa mata,itama idan taje unguwar takan qarasa gidansu susha hira sosai,ta janye jikinta sosai da munira,idan tazo kadaram kadaham,ta daina gaya mata kowanne yanayi da take ciki,hakanan ta daina shawara gaba daya da ita.
*_WATA SABUWA......inji 'yan ca ca_*
Da yammacin ranar litinin,bayan ta idar da sallar la'asar ta fito parlor zuwa kitchen don samarwa kanta abinda zata sanya a cikinta,don rabonta da abinci tun breakfast da tayi da tea da two slices na bread.
Rasa me zata dafa tayi,saboda cikinta ne ita daya,tuntuni ta sauke dafa abinci da bassam,don baya shigowa gidan sai dare ya tsala,sha biyu da rabi daya har biyuma wani lokaci.
Busashen kifi ta gyara hade d wake,ta tsaida sanwar jalop din taliya da wake da busashen kifi,saita koms parlor sanye da hijabin sallarta,hannunta maqale da carbun nan counter wanda a yanzu bata rabo dashi.
Ta gama lazuminta zaman shurun ya mata yawa,saita kunna tv,abinda yakan jima batayi ba kenan,ta fara kallon wani film na tarihin sahabbai daga wata tashar da pure larabci,saidai kuma akwai subtitle na turanci.
Film din ya dan dauki hankalinta,saboda ta kwana biyu bata saka tv a idanunta ba,har sai da sanwar ta jima tana tafasa sannan ta farga,ta miqe da hanzari ta koma kitchen din,ta hada komai sannan tayo hanyar parlor din.
Cak ta tsaya ganin baqin da bata barsu a parlor din ba amma ta dawo ta taras dasu,wasu a tsaye wasu a zaune,wasu kuma daga bakin qofa.
Mom ce ita da fahima fairuza da nasma,sai kuma anty billy wadda take qanwa ce ga mom,shahararriyar mara mutunci ce,wadda bata dauki talaka a bakin komai ba,tunda suka taba haduwa da iman sau biyu iman din bata sake bari sun gamu da ita ba,saboda zallar kallin qasqanci da take jifarta dashi,ta lura ma kusan anty billyn tafi mom zaqewa akan auren iman din da bassam.
Cikin dakiya da sanyawa ranta nutsuwa ta qaraso falon
"Sannunku da zuwa" ta fada a nutse,babu wansa ya kalleta ko ya tanka mata a cikinsu,saima tsaki da Anty billy taja,tana mata wani irin kallo kamar zata sheqa mata mari.
Batabi ta kanta ba tunda ita din ba dolenta bace,saita dubi mom
"Mom ku zauna,ga guri"
"Rasa wajen zama nayi tun daga cikin gida na da zanzo nan na zauna?......kai.....David" ta qwala kira,saiga wasu daga cikin qattan ma'aikata maza na gidan su hudu sun shigo
"Ku shiga store din gidan nan,ku fiddomin dukka wani kayan abinci da abinsha dake ciki ku kawo min shi nan" tak iman din bata ce ba,sai ta koma gefe ta basu hanya kawai tana kallon ikon Allah,gami da tambayar kanta abinda yake faruwa.
Kusan mintuna goma suka kwashe suna fidda kayan,hadda buhun shinkafar da aka bude aka fara amfani dashi,matsowa tayi gaban kayan,ta nuna shinkafar da aka fara amfani da ita tace a maida store din,amma dukkan wasu sauran abubuwan amfani da kayan alatu,kama daga waken gwangwani,kifin gwangwani,indomie,madara lemuka ruwan roba kai hatta da kifi da nama dake cikin fridge tasa an fiddasu,duka aka tattare mata su tace akai sashenta.
Dubanta tayi sosai bayan sun fice
"Nasan zaki ta yiwa kanki tambayar dalilin da yasa na aikata haka ko?,to ba komai bane illa gajiya da nayi da ganin ana ciyar da banza wofi,wata shida da aure amma banga alamun samun qaruwa ba,dan tofe tofen yawu da amai da zazzabin dare duka babu,to meye amfanin ci dake?,dadin ai yayi miki yawa,ki kwana a ac,kici me kyau kisha mekyau,ku saka suttura me tsada amma baby wanu alfanu da kike kawo mana........"
"Wallahi ya hafsa sakar mata maqoshin da kukayi ne ma yasa kwanaki can ta fara yunqurin soma rashin mutuncin nan" kai mom ta girgiza tana kallon billy
"Ai ni ba'a haifi matar da dana zai auro ta rainani ba,kosu mimi da ake gani muna zaune lafiya bina suke su da iyayensu suke wasu,wanda idan ama fadi sunansu ansan da zamansu,idan ita ban isa da ita ba ai na isa da dana ko?......saboda haka" ta fada tana maida dubanta ga iman
"Ki kwana da sanin bassam aure xaya qara,yarinyar da zai aura din tana nan zuwa cikin gidan nan don su fahimci juna,wannan satin ko kuma sati na sama" daga haka suka juya suka fice daga sashen nata.
Shuruuuuu tayi bata iya tanka musu da komai ba,bakinta ya riga da yayi nauyi,idan ma tace zata tanka din me zatace musu?,kowa ya siya rariya yasan zata zubda ruwa,kome ya faru da ita ta jawa kanta,idanunta keta radadin yajin tara hawaye amma ta daure ta hana kanta,bata dawo saiti ba saida hancinta ya fara jiyo mata qaurin girkin data dora,kamar wadda babu laka a jikinta ra nufi kitchen din,ta kashe gas din gaba daya ba tare data damu ta duba ya dahu ko bai dahu ba,illa dai ta bude tukunyar,tabi abincin da kallo kamar wata shashasha,so take taga meye abinda bata ci a gidansu?,meye malam bai ciyar da ita ba?,meye yayyenta basa siya mata idan tace tana da buqata?,wacce cima ce sabuwa a wajenta cikin abinciccikan dake cikin gidan?malam da 'yan uwanta ba ragwage bane,basu yarda taga wani kalar abincin a wani gida tayi sha'awarsa ba'a girka shi a gidansu ba,saita saki murfin tukunyar,ta sulale a wajen,ta kuma saki kukan da taketa faman hana kanta yi,abincin da bata ci ba kenan.
A kwanakin ta fahimci abinda mom din ta aikata da sanin bassam,tunda gaba daya duk wani abu na buqata idan yanaso sassan mom din yake tafiya abinsa ya dauka yayi sha'anin gabansa dashi,idan kuma na amfanin koda yaushe ne,sai yake zubawa cikin freezer na falonshi yake amfanin da abunsa.
Koda wasa bata taba daga kai kota nuha ta damu ba ko ta gane abinda yake aikatawan,a yanzun saukowar iyayenta yafi komai dadada mata rai,hakanan ta fannin abinci dama a yanzun ba wani shiga cikinta yake sosai,so duk abinda ta samu ci take ta kwanta,idan bai mata ba kuma tana fiddawa cikin kudinta tayi magana da masu gadi su siyo mata,ko kuma ita din idan ta fita,musamman ranakun ganin likitanta,ganin likitan da babu abinda ya shalli bassam dashi,komai ita ke kashewa kanta cikin abinda yake ajjiye mata ada,don a yanzun ya daina ajjiye mata komai,tasan kuma duka daga umarnin mom ne,da kuma shima halinsa da ya bayyanar mata qarara a yanzu.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 34
Tun tana bedroom dinta take jiyo motsi da kai kawo cikin falonta,da fari tayi tunanin bassam ne,to amma jin motsin na sake matsowa dakunan kusa da ita ya sanyata ta zura gyara zaman hijabinta,ta ajjiye alqur'anin data qulla qawance dashi ta leeqo don ganin abinda ke faruwa.
Mamakine sosai ya cikata ganinsu fahima na wucewa da kayayyaki dakin dake bashi da tazara da nata,sai ta jinjina kai,batace musu komai ba ta juya zuwa ciki,don dama basu ganta ba,saidai kuma har yanzu tana tunanin abinda zasuyi cikin dakin,dawowa sukayi part dinta ko kuwa?,saita aje tunanin a gefe guda,ganin cewa bazai amfaneta da komai ba,ita dake lallaba lafiyarta a yanzun.
Ta jima tana jin motsi da buruntunsu amma duk da haka bata tashi ba,taci gaba da zarafin gabanta,har zuwa sanda ta gama abunda takeyi din,ta fita zuwa kitchen don ta laluba ko zata samu abinda zata iya ci.
Ta qofar dakin tabi,an jashi an kulleshi,saidai kana iya jiyo qamshin freshner dake tasowa daga cikin dakin,saita kauda kai ta qarasa kitchen din.
Dube dube ta tsaya yi,sai a sannan ta tabbatar lallai bata da wani sauran abinda zata iya ci cikin gidan,shinkafar data rage itama a yanzun babu ita,duk kyau girma da qayatuwar kitchen din dama gidan gaba daya amma babu abincin da dan adam zaici?,wani abu ya tsaya mata a wuya,tsahon rayuwarta a gidansu,bata taba bude ido a ma'ajiyar abincinsu taga babu shinkafa sama da kwano biyar ba,sai gashi yau a gidan aurenta,gidan da kowa yakema kallon ta samu aljannar duniya,gidan da ake ganin koda da dawisu da talo talo taso zata ciyar da kanta,a yau shinkafa gwangwani daya ta gagareta,ruwan famfo shine ruwan shanta musamman idan tayi saken da pure water dinta ya qare,ita kanta batasan suna ko ma'anar auren nan nata ba,saidai kawai tana so tayi biyayya ga abinda yagana tace,ko Allah zaisa ta zame mafa hujja kuma shaida a nan gaba.
Ruwan Lipton ta hada da kuma bread ta dawo dakinta,tana lissafa kwanakin da suka rage da zata koma ganin likita,daga can zata siyo abubuwan da suka samu kafin ta samu ganin bassam ta shaida masa,sabida a yanzu bata da guarantee na lokacin ganinsa.
Abunda yake bata mamaki yadda sam mom bata damu da irin daren da yake kaiwa ba kafin ya kawo cikin gidan,abinda ta fuskanta shine,hakan yana yiwa mom dadi saboda kawai a cusgunawa iman,bata damu da illar da hakan take dashi ba,bata damu da me sakamakon hakan zai haifar ba.
********. *******. *******
K'arfe biyu na rana tana zaune a falon tana yankan farcenta,sanye take d wasu blue black material wanda aka yiwa dinkin doguwar riga bubu,saiya yane kanta da babban dankwalin rigar,ta zauna anan dinne saboda tadanyi kallo fa ragewa kanta kewa da zaman kadaici,wanda dr ahmad ya gargadeta da hakan,baisan cewa zaman kadaici ya zama wani bangare na rayuwarta ba.
Kamshin turarensa daya fara busowa sosai cikin falon ya sanyata dago da kanta,bassam dinne yayi kwalliya sosai cikin qananun kaya,yayi kyau babu qarya,kasancewar yana da wannan baiwae ga daukar ido duk sanda yayi ado,rabonta da ganinsa idan bata manta ba zata iya cewa yau kwanaki bakwai ko takwas kenan,saita dauka kanta taci gaba da abinda takeyi,yayin da shi kuma ha qaraso inda take zaunen,idanunsa a kanta.
Sosai tayi masa kyau,duk biye biyensa har yau bai taba haduwa da mace me sassanyan kyau haka me tafiya da hankali ba irin iman din,duk da cewa ba wata zuzzurfar mu'amala bace take shiga tsakaninsu amma yayi missing skin nata mai taushi da wani irin qamshi,yasha kwatanta yadda zai tsinci kansa idan ya shiga duniyarta ta zahiri.....yanaji a ransa lokaci ya kusa da zai sanya jessica koda bata qaunar Allah ta kawo qarshen abindata aikata masa.
Wannan sharetan da yayi yanaji a ransa shine hanyar da zaibi kawai ya hukuntata,ya kuma nade tabarmar kunyarsa tsaf da hauka,sannan ta yaya kamar shi,shi din da mata ke Rububi mace kamar iman 'yar tsakuwa a cikin 'yammatansa,sabida tayi fushi ya zubda ajinsa ya lallasheta ko ya bata haquri?,yayin imanin dole tata zata kawota,a nan zai jata a qasa ya kuma nuna mata iyakarta,ta yadda nan gaba ko kara ya sanya ba zatayi sha'awar tsallakewa ba,shi yasa yaji dadin kwashe kayan abincin da mom tayi,ko iya su zasu ta kawo kanta gareshi.
Ya zaci zata furta wani abu,amma sai yaga ko sashen da yake ma bata kalla ba,har ya qaraci tsaiwarsa da gyara tie da kuma hannun rigarsa ya soma ganganrawa zai fice,mamaki fal ranshi,wanne irin miskilanci gareta,ya zaci kawo yanzu zatayi laushi tazo ta nema sulhu kamar yadda abokansa ke bashi labarin yadda sukeyi da matansu idan suka kamasu da laifi makamancin haka,sai gashi ita sake dauke masa wuta ma tayi gaba daya.
Karamin tsaki taja sanda ya fita,tana jin yana sake sire mata a rai,ji take kamar ta tattara kayanta tabar gidan,saidai kuma bataso tayi kunnen uwar shegu da maganar yagana,abinda ke sake taka mata burki kenan.
Tana nan zaune a wajen tana ta so ta tashi,amma wani film da ake haskawa ya tsaidata,ta dauke idanunta daga kan tv zuwa bakin qofar falota sanda taji hayaniya,ana kuma qoqarin shigowa falon.
Fahima ce kan gaba dauke da trolley,tanata faman zuba hira da mutanen dake bayanta,don har waiwayawa take,sai fairuza daga bayan nata,da kuma wata baquwar fuska na wata fara qal din matashiya.
Dukkansu sun hada ido da ita,amma sai kowa yayi kamar bai ganta ba,suna takowa zuwa cikin falon tare da ci gaba da hirarsu,wanda rabinta cikin harshen turanci sukeyinta.
Dab da zasu giftata matashiyar cikinsu wadda itace baquwar fuska a cikinsu a wajen iman ta sake kallon iman din sosai,sannan suka wuce,qofar dakin dataji motsinsu a jiya taga fahima tasa key ta bude sun shiga gaba dayansu.
Ko zama basu gama yi ba ta sake jin motsi,saiga bassam ya shigo,tabi hannuwansa da kallo,yana riqe da wata qaramar jaka mahadin trolley din dasu fairuza suka riqo,daya hannun nashi kuma babbar leda ce,wadda duk da baka iya ganin abinda yake ciki xaka fahimci takeaway ne,walau na abinci ko na kayan maqulashe.
Duk da dakewar da yayi amma yanayinsa yadan sauya,kamar bai danji dadin ganinta a wajen a zaune ba,kafin ya qaraso ma saita miqe abinta tana daukar hijabinta dake aje gefe ta wuce dakinta tabar musu falon.
Aqalla awa wajen uku tana ci gaba da jin hirarrakinsu da darunsu daga can dakin,tun tana jurewa har suka fara cikata,saita qarasa bakin qofarta ta rufeta ta murza key,abinda yasa gaba daya ta daina jiyo motsinsu.
Duk yadda taso kauda tunani da mamakin abinda ke faruwa cikin gidan amma hakan yaqi yiwuwa,ta gaza fahimtar komai,idan banda jahilci ta yaya za'a sauki baqo cikin gidanta amma a gaza gaya mata?,wanne irin tsarine wannan.
Ranar gaba daya a dakinta ta qarar da wuninta,har zuwa dare,ta gama karatunta da sallolinta ta kashe fitila ta kwanta,bayan ta saita alarm saboda tanaso gobe ta tashi da dan wuri zata asibiti ganin dr ahmad.
********Karfe goma na safiya ta gama shirinta tsaf cikin abaya,wanda mafi yawa tafi sanyata idan zata fita,duk da yada ta sauya,duk kuma da yanayi na rashin kwanciyar hankalin da take ciki amma hakan bai hanata yin kyau ba,kamar wata balariya haka ta fito,ta murza key din da tun yammacin jiya ta sanyashi bata bude ba sai yanzu.
Tana isowa falon qamshi ya daki hancinta,koda ba'a gaya mata ba tasan cewa daga cikin kitchen dinta qamshin yake fitowa,idanunta suka sauka a qofar dakin,qofar a bude take,saidai ba gaba daya ba,an dan sayata ne,labule kuma ya qara rufe sauran gurbin da qofar bata rufe ba.
Tana iya jiyo sound na murya na tashi daga cikin dakin,sai ta dinga jiyo kamar muryar bassam,amma zuciyarta taqi aminta da hakan,saboa bataga abinda zai kaishi dakin ba ida ana magana na abinda ya kamata,tayi qoqarin dannen zuciyarta,ta qara takawa zuwa gaba tana duba gurbin data ajjiye milkshake dinta jiya tana fatan Allah yasa bai lalace ba,sabida shi kadai ya rage mata a gidan.
Balle murfin tayi takai bakinta,dai dai lakacin da qofar dakin ra motsa,labulen ya daga,tana shirin dauke idanunta bassam na fitowa daga dakin,bai kuma lura da ita ba yayi gaba zuwa kitchen,saiga yarinyar jiya na biye dashi,sanye da kayan bacci masu sulbi,wadanda suka bi jikinta suka kwanta,sumar kanta kuma a bayyane saboda rashin saka dankwali.
Saura kadan ta qware Allah ya taimaketa ta dawo dashi zuwa bakinta,sai ta dire kwalin kanta yana sarawa,ta daure a hankali ta juya tana laluben hanya ta fita daga parlor din.
Sai data kusa minti talatin zaune cikin motarta tana qoqarin daidaita kanta,kuka take sonyi amma kuma ya kasa zuwa,sai zafi da zuciyarta keyi,cikin zafin nama ta kunna motar ta kuma tasheta ta figeta da gudu.
A minti talatin take zuwa asibitin dr ahmad,amma a yay minti ashirin ne ya kaita,tana zuwa mutum biyune a gabanta,saita zauna kawai tana bin kowa da idanu har zuwa sanda akayi kiran sunanta.
Kallo daya dr ahmad din yayi mata ya tabbatar bata rabu da matsala ba
"Lafiya kike kuwa hajjaju?" Kamar jira take dama ya tambayeta,sai kawai ta fashe masa da kuka,ta gaza riqe wajjaj damuwar,abun yana neman fin kwanyarta.
"Subhanallah......subhanallah" ya dinga maimaitawa cikin nutsuwarsa,idanunsa na kan yatsun hannayensa yana dubansu,saboda babu tayadda zai kalli fuskar matar wani,duk da taja mayafin abayarta ta lullube fiye da rabin fuskarta.
Sai daya tabbatar ta rage dafin dake cikin zuciyarta,sai ya miqe ya qaro gudun acn dake office din,sannan ya isa bakin fridge dinsa,ya debo ruwa da lemo da cups,ya dawo bakin table din,ya zuba kowanne a cup ya ajjiye mata a gabanta,sannan ya koma kujerarsa ya zauna yana cewa
"Bismillah,dauki kisha" tabbas tana da buqatar ruwa saboda yadda maqogoronta ya bushe tas,duk da cewa bataci komai ba,amma sai ta dauki ruwan ta kurba,har sai data ji bushewar maqogaron nata ya ragu sannan ta ajjiye.
"Nasha gaya miki,indai kinason lafiyar zuciyarki ki guji abinda zai bata miki rai"
"Bani nake batawa kaina rai ba dr" a wannan karon kasa boye masa komai tayi,ta bashi labarinta gaba daya,tana ji a ranta kamar ya al'ameen dinta ne a gabanta take gaya masa matsalolinta.
Da farko fada ya sakeyi mata akan kuskuren data tafka tun farko kamar yadda duk wanda yaji yake mata
"Iyaye ba wasa bane,saba musu da bujire musu shine kuskure mafi muni da dan adam zaiyi a rayuwarsa,kome zaki gani yanzu cikin rayuwarki sakamakin bata musu ran da kikayi ne,amm alhmdlh,tunda sun fara saukowa ki sanya ran samun raguwar jarrabobinki.......inda ace ni isasheshene da zai iya yanke hukunci kan al'amuranki,da na haramta aurenki da mijinki saboda bayyanar fasiqancinsa,amma bani da wannan hurumin,shawara daya ce zan baki,ki tsananta addu'a babu ji babu gani akan ubangiji yayi miki mafita mafi alkhairi,amma damuwa bata warware damuwa saidai ta qara maka damuwa,ta kuma gadar maka da cututtukan da zasu iya naqasa rayuwarki" kalamai masu kyau da ma'ana ta samu daga bakin dr ahmad,wanda hakan ya sanya ta qara ganin kima da mutuncinsa a idanunta,yayi checking nata sosai,ya sake dorata akan magunguna sa shawarwari,kafin tabaro asibitin ta samu relief sosai,sai kawai ta wuce gidansu,ko banza idan taga inna zata sake samun wani sassaucin.
Bata koma gidan ba sai dab da isha'i,tana shiga suna cin karo dasu,suna zaune dashe dashe a parlor dinta,yarinyar da har yau batasan sunanta ba,cikin dressing din da bai kamata wani wanda yake ba muharraminta ba ya ganta da irin wannan shigar ba,babu kowa a sahen daga shi sai ita suna kallo.
Sam ba tabarmar kunyar da bassam din ke nadewa ne ke damunta ba,ko kuma yadda tazo ta samesun ba,don a yanzun ta sanya bassam din a ajin BABU,dashi da babu duka daya haka ta saka a ranta,ita din kamar mai zaman jiran wa'adinta ne........yadda mom ta bada dama aka kebance da danta na cikinta,aka basu dama suka kadaice,bata ko kishin tarbiyyarsa,ama ture ta tata da suka raina,suke ganin bata kai komai ba......wanda tana da yaqini da kuma tabbacin babu matar auren da zata lamunci ayi mata haka,saidai ita din bassam ba shin a gabanta ba,shi da babu duk daya take kallonsu,don haka ko kallon tsiya basu samu ba bare na arziqi,ta sanya kai tayi ciki abunta,yayin da bassam.ya dage yana aika mata da miyagun maganganu cike da fada da rashin daraja.
"Calm down baby..,..karka bari ta bata mana jin dadinmu mana" yarinyar wadda ake kira da seema ta fada,saidai zuciya nata tunzurashi akan kada ya qyale iman din,sai ya miqe
"Ina zuwa baby" yabi bayan iman din cikin fushi da jin cewa iman din ta wulaqantashi.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 35
Towel ta daura ta kuma zura hijab,tana shirin shiga wanka bassam din ya shigo,saidai kuma suna hada idanu kaifin abinda ya shigo dashi din ya ragu
"Ke.......kina jina ina miki magana saboda kin rainani kika shigo kika barni?wato ga banza shasha mahaukaci ko?" Maimakon ta tanka masan kamar yadda yakeso dinndai ,sai ta sake bawa banza ajiyarsa,ta qarasa ta dauki man wanke gashi ta sakeyin gaba.
Sake fusata yayi sosai,ya daka mata tsawa yana cewa
"Na yarda da gaske kin rainani kamar yadda mom tace,saboda kinga kin dan fara riqe kudade,kina cin mai kyau kisha me.kyau ki kwana a ac"
"Kul!" Ta fada itama cikin daga murya,abun sai ya bashi mamaki,ya buda idanunsa yana kallonta,itama sosai ta bude nata idanun cikin nashi
"Karka kuskura ku zarme cikin maganganunka,shurun da nakeyi bawai yana gwada bansan ciwon kaina ko bani da wayo ba,ina sane da komai,hakanan a shirye nake da faruwar kowanne abu,ina cin me kyau?,ina abun yake?,ina qudan yake ballantana romonsa?,na tabbatar sanda ka daukoni daga gidanmu ba haka nake ba,hakanan ba dusa muke ci ba,maganar kwana a ac kuma kai kanka kasan ka fada ne don kaji dadin bakinka,ac ba shine arziqi ko kuma kyau ba,inda shine......ni hajar bazanyi kyan da ka gani a tattare dani ka nace sai da ka auroni ba......ka rabani da kowa nawa,kazo kana gasani kuna nunamin baqin halayen da babu arziqi ko dattako ko kadan a cikinsa,na rantse da Allah daga yau duk wanda ya sake takani saina takashi ko wayeshi,ka gayawa sauran" tasowa yayi kamar xai daketa,wani jarumta tazo mata,ta dauki fitilar gefa gado ta daga sama
"Duk randa ka sake ka kwatanta dukana,koda da wasa ne,wallahi wannan abar bata da muhallin da zata fashe ta kuma tarwatse illa kanka" sake birkicewa yayi da maganganun tabarmar kunya,ta bawa banza ajiyarsa ta shige bandaki ta murza key.
Famfo ta kunna saboda batason yaji sautin kukanta,ta dinga kuka sosai tana kiran sunan Allah,daga nan tana jiyo yadda yake bin duka lockers dinta yana kwashe kudaden da suke ciki yana fadin
"Zanyi maganinki,zakisan cewa bani da kyau,saboda kinga na sangartaki shi yasa kike dukka iskancin da kikaga dama".
Cikin ikon Allah kafin ta baro bandakin zuciyarta tayi sanyi,data fito din saita kulle dakinta,ta shirya ta jawo takeaway din data shigo dashi ta fara ciba wani da yawa taci ba ta ture saboda yaddaa taste din bakinta ya dauke gaba daya,ta ballo maganinta tasha ta kashe fitila ta haura gado ta kwanta,don ta hana kanta tunani saita janyo wayarta,cikin karatuttukan malamai da take download ta ajjiye ta buda daya ta fara sauraro,a hankali ta sake samun nutsuwa,ta tattara dukka hankalinta akan karatun tana fahimtar kowanne lafazi dake fita daga bakin malamin.
Wata irin rayuwa ake gudanarwa cikin gidan musamman sassan iman din,kamar wasu maguzawa ko kuma wadanda basusan addininsu ba,seema diyace ga tsohon ambassador din nigeria a England,kuma 'yar qawace ta kurkusa a wajen mom,cikin manyan qawayenta makusantanta,an dauko cancankat an kawota gidan da sunan su saba da bassam kafin maganar aurensu,an kawota sashen iman din ba tare da neman yarda ko amincewarta ba,basa yiwa iman din kallon komai face qasqantacciya wadda bata da wani daraja ko kima saboda bata fito daga gidan nau'in mutane da suke da abun duniya ba wato kudi.
Dukkan abinda suka ga dama yi suke a sassan nata,idan ka shigo zaka tsammaci seema ce matar gidan,saboda gaba daga iman din ta tattara tabar musu gidan,tayi qaura zuwa dakinta tana aiwatar da al'amurata,idan kaga ta fito tofa saidai idan wani dalili me qarfi ne ya fiddota,tana gamawa kuma zata koma,bama kasafai zaka ganta din ba,tunda babu kayan abinci bare tace xatayi girki,kayansu lemuka da madara kawai data tara a dakinta sune abincinta,wanda suma suna kan hanyar qarewa.
Hausawa sukace ba'a bawa kura ajiyar nama,a nan kuwa na bawa bassam,gaba daya bassam ya ja iman ya ajjiye gefe,ko cigiyarta baya yi bare nemanta,domin kuwa ya samu dukkan abunda yake buqata daga wajen seema,tsula tsiyarsa yake,ya samu lasisin fiye da yadda yayi tunani,don zuwa lokacin ya samu makarin lalurarshi ba tare daya bari jessica ta sani ba,babu abinda ya banbanta seema da matarsa,dukkansu basu da wata damuwa ko tunanin ranar nadama.
*_KOMAI NISAN DARE gari zai waye_*
Tunda gari ya waye yau sashen nata shuru yake,babu motsin bassam bare na seema,ko ba'a gaya mata ba kuma tasan sun fita ne tare,don wannan din ba wani baqon lamari bane tattare dasu,hakan ya bata damar fitowa parlor ta dan zauna,saboda ta rage muguwar kewa da zaman kadaicin dake damunta,zuwa yanzu ta fara qosawa,ta kuma fara gajiya da abinda idanuwanta suke gani,sau tari zuciyata tana gaya mata ta gudu,ko tayi yaji,saidai dukka haqurin da take tana yine saboda ta kafa hujja ya kuma zame mata hujja,ba'a wajen yagana kadai da kullum take sake tausarta ba,a'ah.....har sauran al'umma da duk mutumin da zai qalubalanceta a duk sanda ubangiji yaga damar zartar da hukuncinsa akan zamanta.
"Salama alaikummm" sautin muryar dake dauke da gurbatacciyar hausa ya samu mazauni a kunnuwan iman,cikin mamaki ta daga kai don jin daga inda sallamar ta fito.
Zabgegiyar macace sanye da mini skirt wanda inda zatayi kyakkyawan tsuguno ba abinda zai hana bayyanar tsiraicinta,sai armless chiffon shirt v neck shape daya bayyana kusan rabin qirjinta,kanta yasha lodin attach,yayin da hannunta yasa fixing na faratan kanti,takalmin qafarta me igiya ne,mai azabar tsinin dunduniya kamar wadda ta shirya tsokane idon duniya,tafkeken sun glasses din daya kusa cinye rabin fuskarta na riqe a hannunta tana kallon iman,kamar yadda iman ke kallonta,tana son tuna a inda ta taba ganin fuskarta,da kuma abinda ya kawo wannan halittar cikin gidan
"Zan iya shigowa?" Ta tambayi iman tana ci gaba da kallonta,bata da zabin daya wuce ce mata
"Bismillah" tana nuna mata wajen zama,saita qaraso cikin taku kamar zata karye saboda tsinin takalminta,ta zauna saman kujerar tana ajjiye jakarta gefe,har yanzu kuma idanunta yana kan fuskar iman,wanda har kallon ya soma sanyata ta tsargu.
Kaf sashen nata bata da wani ruwa bare lemo na roba da zata iya bata,don haka ta gyara zamanta tana duban matar
"Kene matar bassam ko?" Ta tambayeta tana dage girarta
"Eh nice"
"Woww......a fili kafi kyau akan hoton daya nunamin" turus iman din tayi,kada dai ace kwashe kwashen bassam ne har yakai suka fara biyoshi har cikin gida,lallai zai kai gabar da kuma ba zata iya ci gaba da zuba masa ido ba"
"Am jessica.....oh....sorry ....ya taba gayamin baki karatu ba,ko secondary school baki kammala ba ko,bari nayi magana da ausanku" sosai maganar ta daurewa iman kai,saidai kafin ta gama wannan tunanin ta sake jefata a wani
"Da fariko......nazo wajenki ne da kyakyawan zuciya,zuciyana babu haushi a kanki,abinda yasa nayi shawaran zuwa na fitar dake daga duhu shine,na farko ke yarinya ne,bakasan komai akan duniya ba,na biyu kuma baka taba tsokanana rigima ko wani abu ba mara dadi tsakanina dakai......ba kamar matan bassam na baya ba"
"Mata kuma?" Iman din fa fada a bayyane cikin mamakin daya fito fili ya bayyana qarara saman fuskarta.
Kai Jessica ta kada tana dan qaramin murmushi
"Yes,wives na bassam ba,nasan baki sani ba......but keep calm,zan miki bayanin komai .......idan zaki iya tunawa watanni da suka wuce an taba toro miki da pics na mijinki shi da wata,to nice wannan din" zumbur iman ta miqe cikin bacin rai
"Tashi ki fitarmin a gida annamimiya arniyar banza,me kikazo kuma yimin?,saboda kinga wancan lokacin na qyaleki ban kulaki ba,shine kikayo tattaki har cikin gida?" Hankali kwance Jessica ta dubeta
"Karki tashi hankalinki mana,koda na tashi na tafi,tafiyana babu abinda zai canza,saima wargaza miki naki rayuwan,ki tsaya ki saurareni,daga qarshe koma meye saika fada" wani sashe na zuciyarta taji yana umartarta ta bata dama,saita koma ta zauna tana huci,saidai ba cikin kujerar ba,a hannun kujera ta zauna wannan karon,da shirin kota kwana,ko zata kawo mata rainin hankali,idan seema ta samu daurin gindin mom tana abinda taga dama.....ita kuma jessica fa?,na meye zata sakewa sauran?.
"Kamar yadda na gaya miki sunana,ni din ba 'yar garin nan bace,abinda ya kawo nan din karatu ne,shekarata goma tare da bassam muna soyayya dashi,asalin fara soyayyarmu kuwa ya nuna min zai aureni ne,nayi masa tuni da bambancin addininmu yace babu matsala,shi wannan ba matsala bane a gidansu,tun a sannan mahaifinsa yana da rai,ashe bassam ya fada ne kawai saboda ya samu kaina ya lalatani,ni kuma a sannan ban sani ba,na bashi amanar kaina da rayuwata sai yadda yayi dani,na sani tu a lokacin bassam yana da farinjinin 'yammata,wanda yawancinsu kudi da kyau da yake dashi yake rudarsu,to ban damu ba sosai saboda ban zaci yana nemansu bane kamar yadda yake nema na,sai daga bisani na gane hakan,mukayita tashin hankali dashi,daga baya na haqura na qyaleshi saboda na fuskanci a jininsa ne,bazai daina kulasu ba,naci gaba da biye masa tare da nace masa kan maganar aure na,amma har muka dibi shekaru biyar bassam yaqi yarda da maganata,a haka muka shiga shekara ta shida,a sannan ne na samu ciki,wadda na tabbatar da cewa bassam ne yayimin shi,tunda a sannan babu wanda nake kulawa saishi,qememe yace a zubar dashi ko na rabu dashi,ni kuwa naqi,saboda a tamu al'adar mu ba abun ku ya bane don kina tare da saurayinki kinyi ciki kin haihu,kina iya tara yara hudu biyar har fiye da haka da saurayi,sai daga bisani idan kuna tare a daura muku aure da yaranku.
Barazanar daya shiga yimin yasa na tattare na koma qauyenmu,ya daina jin duriyata da labarina gaba daya,acan nayi rainon cikina na haifi yarinya mace,sai data isa yaye shekara daya da rabi na dawo rayuwar bassam,nayi gyara na musamman saboda nasan lagonsa,ina dawowa kuwa ko takan cikina baibi ba aka dora da sabgogi,abinda bai sani ba lamfo nake masa ina bibiyar duka rayuwarsa,saidai ashe nima lamfo yayimin,sanda na dawo masa da maganar aurenmu yace shi Allah ya tsareshi,me zaiyi da ragowar wasu,maganar ga batan rai,tunda ko ragowar wasunne ni ai shine ya fara nunan hanya,a sannan munyi bacin rai dashi irin wanda bamu taba yi ba,na tattare komai nawa muka rabu,amma a raina akwai shirin daukan fansa,saboda haka na fara binciken abubuwan da suka shafeshi da yake boyewa,wanda idan suka bayyana zasuyi destroying dinsa.
Cikin abinda na gano kuwa harda aure da yayi na mata uku,daya ya saketa,biyu yana zaune dasu ba tare da kowacce tasan da 'yaruwarta ba,sannan mamanshi ma batasan da auren ba,saboda auren sirri yayi abunsa na watanni,idan ya gama morar yarinya saiya rabu da ita ya koreta.
A sannan daya daga cikinsu nada ciki,kishi yasa na dawo rayuwar bassam,na fara nunawa matansa cewa akwai wata fa tare dashi,sai muka shiga gwabzawa dasu,inda daga qarshe basu cimma nasara ba,lokacin daya diba na sakinsu yayi ya rabu dasu.
Unfortunately ba'a dauki dogon lokaci da rabuwarsu ba na tsinci labarin xaiyi aure,dana tareshi da zancan kansa tsaye yacemin eh aure zaiyi,abun ya girgizani ya kuma bani mamaki,na dinga son insan wacece wannan data sauya ma bassam ra'ayi lokaci daya,ya kuma aminta zai aureta?,saidai ban samu wannan damar ba,saboda gida dana koma can garinmu,'yarmu da bassam baisan da ita ba bata da lpy,inacan kuma ban dawo ba har ya rage saura kwana uku daurin aure,wannan shi ya wargazamin duka plan dina,amma dana bawa sister na labari,saita kawo shawarar na kassara mazantakansa,tunda dai shine taqamar kowanne namiji,ta yadda babu wata mace da zai iya tsinanawa komai indai bani ba,a wajena ne kawai zai iya kasancewa namiji,wannan itace hanya guda daya da zata mallakamin shi,tasa ya dawo tafin hannuna"
"Sosai shawarar ta yimin,ta kuma faranta min rai,ana ya gobe daurin aure na tura masa Tex,na tayashi murna,nayi masa kuma albishir din abinda ke shirin samunsa,ya kirani ya zazzageni,yace shi zan yiwa barazana,ni kuma nace masa maji ma gani.
Bayan yaje ya tabbatar da abinda na gaya masa,wannan shine abunda yayi sikar dawowarsa wajena,muma sake zama kamar miji da mata ni dashi,yaso kasancewa tare dake qwarai da gaske,saboda yadda zuciyarsa ta cika da sha'awarki tun sanda ya fara ganinki,don ko lokuttan da yake tare dani ke yake ambata......yaso yayi mu'amala dake da farko kamar yadda yakewa kowacce mace,bansan me ya gamo ya kasa aiwatar da wannan ba,ya juya manufar zuwa ta aure a kanki,amma daya daga cikin dalilan da na sani shine......ya aureki ne don ya bunne barnar da yake aikatawa,saboda kedin kina da qananun shekaru akanmu,ba zaki takurashi ko hanashi yayi yadda yakeso ba.
At last saqon da nazo dashi gareki na ceton rai ne,saboda ni na riga na fada,no way out......bassam ya fara harka da wata yarinya serah,yarinyar da nake da dukkan tabbaci da yaqinin tana da cutar HIV,ban kuma ankare da hakan ba saida suka fafa nisa a mu'amala,zuwa sannan kuma me afkuwa ta afku......anan ne kuma na fahimci cewa ya warke ya samu makarin sihirin da nayi masa,idan kinsan har yau bai nemeki ba......to ki kubutar da kanki.....ki tseratar da quruciyarki,idan kuma an riga an gamu......sai nace miki ina miki jaje,ni ban damu ba da kaina,saboda ko babu komai na hada iri dashi......." Saita miqe tana maida glass dinta
"Dukka cikin kalamaina babu qarya ko daya,idan akwai ubangiji ya hukuntani,na fada miki ne sabida nayi ceto ga innocent soul,na barki lafiya".
Zata iya cewa inuwar jessica itace abu na qarshe data iya gani,sai bude idanunta tayi taga daya daga cikin ma'aikatan gidan mata a gefanta[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 36
Sai data sake bude idanunta sosai taji tana yi mata sannu sannan ta fahimci suma tayi a wajen,a hankali qwaqwalwarta ta fara tariyo mata abunda ya faru zuwan Jessica da kuma abubuwan data shaida mata,kuka sosai ta fashe dashi,sannan ta miqe da sauri ba tare data kalli matar dake gefan nata ba,tsanar gidan da tsanar duk wani abu da kuma duk wani mutum dake gidan tana darsuwa a ranta,bassam?,bassam.......ashe shidin furen kan juji ne?,ashe baqin maciji ne shi mai dauke da mugun dafi?,irin dafin da idan ya tsartu ga gangar jiki yake ɗai ɗaita jiki,ya kuma haifar da mummunar illar da bata warkewa.
Takai ta kawo yafi sau shurin masaki,ta rasa wacce shawara ya kamata ta yanke?,meye abu na qarshe daya kamata tayi?,don dai tabbas indai ya tabbata dukka abinda jessica ta fada haka yake.....babu wani sauran zama tsakaninta da bassam har gaban abada.
Fitowa na ukun da tayi zuwa falon kamar me neman wani abu,yayi dai dai da shigowar bassam da seema,saidai wata irin shigowa sukayi,tana gaba fuuuu yana binta a baya
"Haba mana seema....tun a hanya nake fama dake ki tsaya ki saurareni.......na rantse miki babu wani abu da yake tsakanina da ita fa?" Ko juyowa ta kalleshi seema batayi ba ta shige dakinta,kana ta fito ta sake wuceshi,ya soma takawa zai bita yana kiran sunanta,saidai tuni ta fice abinta.
"Damnit" ya fada yana yarfar da hannuwansa,da alama abun baiyi masa dadi ba,wasu hawaye masu dumi suka saukowa iman tana kallon fuskarsa ba tare da ya sani ba,babu abinda take hangowa sai lokacin da ya yaudareta,ya kawota duniyarsa bisa kyakkyawan zaton zata samu dukkan wata kulawa data dace da diya mace,ta miqa masa dukkan yardarta,ta zama butulu kufan wuta ga ya ameen dinta,mutumin da ya sota fiye da kowa a duniya
"Ke kuma meye kika wani tsaya kina kallon mutane kamar baki sansu ba" cikin muryar kuka ta fara magana
"Ina kallon mayaudariya kuma maha'inciyar fuska,azzaluma wadda bata damu da gobenta ba bare na wani,fuskar da take iya fuskantar kowanne zunubi,take iya mu'amala harda kafirai maqiya Allah da ma'aiki irinsu Jessica" sosai taha reaction na fuskarsa ya sauya sanda ta ambaci sunan Jessica din
"Ke!,banason hauka da rashin hankali fa?,kisan me bakinki yake fada,to sai meye?,sai mene?,babu abinda zan nema ban samu ba cikin rayuwata,sai na kasa jin dadin rayuwata?,sana ragi kaina?,bazai yiwuwu ba,kinga....ni ba kalar mazan da suke daukan raini daga matayensu bane"
"Raini shine abu mafi sauqi da zaka samu daga gareni idan na yarda na zauna dakai......"
"Ba sai....." Maganarsa ta tsaya sanda yajiyo muryar mom tana qwala masa kira,hankalinsa ya tashi,saboda ya tabbatar seema qararshi takai wajen mom,ba'a cika sakanni ba mom din ta bayyana cikin parlor din,kamar kullum cikin takun qasaita take takowa cikin falon,taku dai dai kamar qasa ba zata iya daukarta ba,saboda jin izza da kuma isa
"Me ka yiwa seema?" Tambayar da tayi masa kenan tana cika tana batsewa,gami da jefa harara ta musamman ga iman,wadda take tsammanin kamar tana da hannu kan bacin ran seeman data hada kayanta tana iqirarin tafiya
"Bab....ba komai fa mom....kawai......"
"Bassam" iman ta kirashi a kaurare,saboda a yanzun idanunta basa ganin kowa,bacin ranta kuma yana ninka na baya ne
"Wuce muje sassa na daga kai har seeman" mom ta fada tana tsareshi da idanu,da hanzari iman tasha gabansa ganin yana yunqurin fita
"Dakata malam.....yau zamana dakai ya qare a gidan nan,bazan iya zama da fasiqin namiji ba"
"And so what?.....ga hanya nan ki tafi,ke kika rasa bani ba,don na taimakeki,na miki gata,na kawoki rayuwar wadata shine zaki dinga fiffiqemin kina min wannan fitsarar" ya fada a tsawace.
Baya tayi tana girgiza kanta,zuciyarta kamar zata fado,sai kuma ta juya da gudu tayi dakinta,duk da gunjin kukan da take amma tana jiyo muryar mom tana cewa
"Ko bata fada ba zamanku ya qare,a gabana saboda ita din ba 'yar gidan mutunci bace?,dama ni na gaji da wannan auren,gwara ayi komai a gama tsakaninka da seema,nima sai hankalina yafi kwanciya"
Ma'ajiyar jakankunanta ta nufa ta fara hargitsosu tana dubawa ko zata dace da wadda keda kudi a ciki,saboda ta tabbatar a yau din ta tashi bata da komai.
Saidai har ta gama bincikenta bata samu kudin da takejin zasu kaita inda take lissafa zata je din ba,abu daya ta sani,koda a qafa ne.....koda me zaya faru ba zata sake kwana cikin wannan gidan ba,gidan da dashi da maqabarta a wajenta bashi da maraba.
Hijabin da take sala ta janyo ta zura,sannan ta sanya slipper din da take yawo dashi tsakanin bedroom dinta zuwa parlour,taku daya biyu sai ta tsaya cak,ta kuma sauke ajiyar zuciya,ta dawo da baya da hanzari ta buda wata locker ta sanya hannu,saiga atm ta fito dashi,tsahon xamanta a gidan ta manta dashi,saboda koda yaushe akwai kudi available kuma cash,qaramar purse da batayi niyyar dauka ba ada ta koma ta dauka,ta jefa atm din da wayarta a ciki,cikin wani irin hanzari da kuma sauri kamar wadda za'a kama ko ace dawo ta qara gaba.
Karo na farko a rayuwarta data doshi tasha da sunan tafiya wani gari,kai tsaye ta nema motar dake lodi zuwa maiduguri,bayan ta tsaya a wani atm machine ta cira kudaden da tasan zasu iya kaita duk inda ta nufa,tun cikin napep akan hanya tasan cewa bata da wani qwarin gwiwa da zata doshi inna malam ko uwa uba yaya sadiqu da wata matsala data shafi aurenta,matuqar ba dan saukowar da sukayi bane takeso ta rushe wannan sassaucin a tsakaninsu,a yanzu bata da kowa.....bata da wanda zata dosa idan ba yagana ba,ita kadai ce madafarta,ita daya ce takejin zata tallafi wannan raunin nata.
Tafiya mai cike da wahala da quncin zuciya tayi,don tunda suka tashi daga kano har suka isa maiduguri......tsahon awannin batakai koda ruwa bakinta ba,a hakan a lexirouse taje......saidai yadda takeji kanta dama jikinta kamar wadda ta tafi a kori kura ko kuma 'yar qurqura,wahala tako ina,don ko bayan sun sauka da qyar ta samu me abun hawan daya amince zai kaita unguwarau yagana sabida dare da yayi,uwa uba shi daya ne ya gane kwatancen da taketa yi masa da qyar,ya tsula mata kudi kuwa sosai,amma bata damu ba,don ba wannan bace matsalarta,burinta shine ta ganta gata ga ya gana,ta kuma karba mata 'yancinta,ta rabata da auren bassam a kanta.
Tsoro ne ya kama yagana sanda taga iman din,daga bisani mamakin ya maye gurbin tsoron
"Hajaru.....daga ina haka a wannan daren?" Maimakon ta bata amsa saita fashe da wani irin kuka,tamkar rarraunan marayan daya rasa uwa da uba duka a lokaci guda.
"Subhanallahi,hajar wani ne ya rasu acan kanon?" Kai ta girgiza mata alamun a'ah saboda ganin yadda hankalinta yayi mugun tashi
"Ki lallabata a hankali" alhj bukari mijin yagana ya fada bayan ya gama tausar iman din,ya fice ya basu waje.
Sai data rama sallolin dake kanta,ya gana ta gabatar mata da abinci duk da cewa dare yayi,amma sai ta kasa ci,abinda yasa ta hada mata abu me ruwa ruwa da kuma zaqi wanda take ganin zata iya sha.
Ba wani da yawa tasha ba ta ture,bata matsanta mata ba ta dauka ya rufe,sannan cikin kwantar da hankali ya gana ta sake tambayarta.
Kamar wancan karon.....babu abinda iman din ta rufewa yagana,cikin matuqar tashin hankali take tafa hannaye tare da dauko dogon salati
"Allah mun gode maka daya kare mana ke,Allah abun godiya,wato shi yasan manufarsa da tun farko yaaa farkarsa tayi masa sihirin da ya zama hoto,da tuni yanzu wani zancan ake akanki kenan iman ba wannan ba?" Yagana ta fadi tana dafe kanta cike da zallar kaduwa da kuma tsoro.
Kai iman din ta jinjina hawayen mai radadi da zafi suna sake sauka akan kuncinta
"Ki kwanta kiyi bacci,kada ki sanya wata damuwa cikin ranki,aure kamar an rabashi an gama,ai zama ya kuma qare,babu wani zancan gyara ko sasanci,da wannan cutar?,mu godewa Allah daya tsayar ma iya nan,yanzu zanje mu tattauna da alhaji,don musan ya za'a bullowa abun,dole khalilu ya sani shima,tunda abune daya shafi jininka" sai data tabbatar iman ta kwanta sannan ta yunqura ta miqe ta fice zuwa dakin mai gidanka.
Idan tace tayi cikakken barci a daren tayi qarya,juyi kawai ta dunga yi tana tariyo rayuwarta,tun daga sanda ta fara mallakar hankalinta har zuwa yanzu,abubuwan da suka dinga faruwa,musamman lokacin aurenta da bassam,da yawa gangancinta ne ya janyosu,ta runtse idanunta tana jin wani ciwo a qirjinta tana hango kanta tsaye gaban ga ameen tana zazzaga masa rashin kunya dukka akan bassam,ta fashe da kuka mara sauti bayan tayi qoqarin rufe bakinta,tana jin wani irin kaico da muguwar nadama suna shigarta,jikinta ya dinga kakkarwa,kadan ya rage hawan jininta ya dawo da mugun qarfi,cikin taimakon Allah ta dinga ambatar sunan Allahn,yakawo mata dauki komai ya daidaita,gab da asuba wani wahalallen bacci mai mafarkai barkatai marasa dadi yayi awon gaba da ita.
Lokacin data farka don yin sallar Asubar kanta yayi wani mugun nauyi,ta lallaba cikin toilet din dake dakin ta daura alwala tazo ta bada farali,ta dan jima saman abun sallar tana addu'o'i na tuba neman rahama gafara da yafiya da kuma sauqi a dukkanin rayuwar da zata risketa a nan gaba.
Sai data tabbatar ta gaji da zaman sannan ta janyo wayarta don duba lokaci,sai idanunta suka fada kan envelope dake fuskar wayarta,wadda ta fado da sunan bassam,tasa hannunta ta bude wayar sannan ta bude envelope din ta fara duba saqon
*_Ni Bassam balarabe madaki,na saki matata iman saki daya_*
Sau biyu gabanta ya fadi lokaci guda bayab ta gama karanta gajeran saqon,ta duba da kyau tabbas number bassam dince,saita lumshe idanunta tana sakin wani numfashi me nauyi daga qirjinta,wanda bayan fitar numfashin......sai taji kamar ya fita ne tare da dukkan wani nauyi daya jima a qirjinta,nauyin da taji ya saukar mata tun ranar da aka daura mata aure,watanni tara baya kenan cikin na goma,bata ji kuma ya sauka ba sai a yau din,maimakon taji dimuwa ko kuma damuwa,a'ah ,sai ta jita sakayau,a nan taja pillow ta maida kanta ta kwanta,tana lumshe kyawawan blue eyes dinta,cikin zuciyarta da kuma labbanta dake motsawa tana fadin
"Alhamdulillah....alhamdulillah,Allahumma salli ala sayyidina muhammadin wasallim" tun tana fada da qarfinta har wani irin bacci ya rinjayi qwayoyin idanuwanta suka rufe ruf,ta lula duniyar bacci.
"iman.....iman" taji ana kiran sunanta sama sama,saita buda idanunta,suka sauka kan yagana dake tsaye gefanta,qarasa bude idanun nata tayi ta miqe ta zauna tana ambaton sunan Allah,sai a sannan yaagana ta samu waje ta zauna tana dubanta
"Inata tararrabin baki samu barci ba,yanzu kuma na koma tararrabin baccin lafiya kuwa kikeyi?,tun daxu ko motsawa bakiyi?,kayan abincinki tunda duminsu har sun huce" gefanta taga jeran kwanukan abincin,mamaki ita kamta ya kamata,saboda bata da wani nauyin bacci,amma kuma ace har an shiga an fita sau nawa bata ji ba
"Alhaji ne zai fita,ni kuma banason ya fita ba'a tsaida matsaya ba" ba kasafai iman din ke magana ba idan ta farka daga barci batayi brush ba,saboda haka ta cewa yaagana tana xuwa,ta shiga bandaki,ta wanko bakinta sannan ta dawo
"Ya sauqaqewa kowa wahala yaagana,da asuba ya aiko da sakin ma ta saqon waya" duk da cewa yaagana taji haushin hakan sabida rashin mutunci ne da rashin kima,a rasa ta yadda zaa saki mace saboda son a wulaqantata saita saqon waya,amma kuma jin dadinta yafi yawa,jin cewa komai yazo qarshe,batayi qasa a guiwa ba ta shaidawa alhaji,saidai ya girgixa kai
"Dole sai an kirashi anji ta bakinsa,saboda haka ina ganin zuwa gobe ko jibi,ku shirya sai mu wuce kanon tare,akwai wasu kayana da sukazo dama,suna kasuwar kantin kwari" da wannan maganar suka tsaida matsaya,ta kuma shaidawa iman din,kai kawai ta kada kana tace
"Allah yasa muna da rai".
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 37 Kwana biyun da tayi gidan yaagana sai taji kamar an canzata ne,duk wani takura da quncin zuciya da takeji babu shi,abu daya ne yake sanyata faduwar gaba zuwa biyu,yaya malam da inna zasu kalli abun?,zasu karbeta kuwa?,idan sun karbetan alaqarsu zata koma kamar yadda take da?,ko kuma ta tabarbare kenan?,wadan nan tambayoyin suke cin ranta,suke kuma takurata lokutta da dama idan ta tunasu Randa suka tasamma kanon sammako sukayi,saboda haka goma na safe acan tayi musu,basu sauka gidan malam ba,sai da suka fara biyawa gidan kawu muntari,gidan alwalin iman din,wanda ta koma gidansa da zama lokacin aurenta da bassam din,sannan suka qarasa gidan malam din.
Kamar wata baquwa haka ta zama,ta kasa sakewa gaba daya,motsi kadan sai ta kalli inna,ita kanta innar tayi mamakin ganinta tare da yaagana da kuma alhaji,saidai bata ce komai ba,ganin harda kawu muntari Basu xauna gidan kawu muntari ba,don haka a gidan inna suka karya aka kuma dora abincin rana,zuwa lokacin mazan suna rumfar malam din,da alama kuma tattaunawa sukeyi,daga bisani ne malam din ya leqo yayi kiransu su dukka suka isa rumfar tasa.Hajaru..inason ki sani cewa duk abinda ya samu bawa muqaddarine daga ubangijinsa,yanzu yanzu muka gama magana da mijinki,mun kirashi kuma ya tabbatar mana da sakin da yayi miki,to amma kuma shi malam mahaifinki ya kafe kai da fata kan bai aminta da abinda kika zo dashi ba.munaso ki bude baki ki gaya mana,tsakaninki da Allah meye ya hadaku dashi?" Kanta a qasa,hawaye ya cika mata idanu,tanajin quna da zafi a ranta,ta gaji da zancan bassam da tarin matsalolinsa,tunda dai har ya sahale mata ya kamata a rufe babinsa hakanan,to amma hakan ba zata yiwu ba,dole saita gaya musu abubuwan da suka wakana. A nutse ta labarta musu komai,ya gana data zame mata kamar shaida itama ta gaya musu duk abinda ta sani,parlour din ya dauki shuru,sai sheshseqar kukan iman din. Gyaran murya malam din yayi
"To yanzu yaaya mu me xamuyi?,muda bamu isa komai ba?,ai saidai muce Allah ya kyauta na gaba,riqon hajar kuma yanzu ai yafi qarfinmu,bamu da muhalli da irin abincin da take ci,saidai ko a cigita cikin dangi ko akwai inda zata iya zama dasu" sosai maganar malam din ta girgiza iman,sautin kukanta ya qaru,hankalinta ya sake tashi fiye da yadda take a da,ta waiwaya tana ruqon inna,sai innar itama taja jikinta gefe tana cewa
Wa?,ni binta,yo zantukan malam dukka akan hanya suke" tausayin iman ya kama alhaji da yagana,ran yagana ya baci sosai,ta kalli iman
Tashi ki shiga ciki" ta miqe tsam tana jin jiri yana dibanta,har sai data bace sannan yaagana ta dawo da kallonta kansu
Duk wannan zantukan da kuke kai da binta zancan banza kuke,wai ku dole saikun nunawa duniya bakwason imani,fushi kuke da ita,zancan banza ne kuke,wallahi wallahi kuka sake na tafi da hajaru maiduguri saikun manta kalarta" alhj mijin yaagana ne ya karba
Malam ni a tunani na kaine zaka yi mana wannan fadan bamu xamuyi maka ba,ka taba ganin inda hannunka ya rube ka yanke kayar?,bayan haka kuma.a yanzu dai inajin babu sauran kalar nadamar da ta rage hajar bata yita ba,babu ita,kuma dama ance ba'a qwace garma a hannun yaro ko?,idan ya gaji yaji wuya da kansa zai cillar da ita,saboda haka,ina mai aron bakinta nima,kuyi haquri ku manta da komai,kalar tata qaddarar da kuma jarrabawarta kenan,Allah yasa kuma ta cinyeta Kiranta yaagana tayi,kowa da kalan nasihan da zaiyi mata,cikin kuka da zubda hawaye ta sake duqawa ta nema gafarar inna da malam,dukka suka amsa da cewa sun yafe mata,saidai malam yace aje ayi mata gwaji a ranar,don a sake tabbatar da lafiyarta,haka kuwa akayi,result ya fita cewa bata tare da wani ciwo banda hawan jinin data samo a can,shima kuma likitan ya bada tabbacin indai zata samu kwanciyar hankali da nutsuwa zata rabu dashi, tension ne ya kawo mata shi. Ya saddiqu kuwa har yanzu jiya iyau,mu'amalarsu sam bata koma kamar ta baya ba,har sai da malam ya kirashi ya masa fada sannan ya sauko,ya rage daure mata fuska. Batasan cewa sabawa umarnin iyaye koda kai keda gaskiya ba indai ba sabon Allah suka umarceka ba babban bala'i bane sai yanzu,ranar da sadiqu yasa motoci a gaba akaje aka kwashe kayanta rankatakaf daga gidan bassam.a ranar tayi wani irin ni'imtaccen bacci,baccin da rabonta da irinsa tun ranar data sanya qafa tabar gidan nasu,bacci harda makara,a ranar data sake tabbatarwa da cewa babu ita babu bassam kenan,sunyi hannun riga har abada. Iya furniture din da taje dasu gidan da kuma motar hawanta data zo cikin sadakinta kadai ya sadiq din ya dauko,banda wannan tsinke nasu bai shigo cikin kayan ba Shawara yayi da ita ya tarkata kayan furniture din aka saida,motar kuma tace a ajjiyeta,don ko son ganinta batayi,don haka sai ya jata ya kaita garage dinsa,don shima yanzun ya bude nasa qaramin garage din gyaran motocin,har ma ya dauki yaran unguwa su hudu suna koyon aiki a wajen,suna kuma taimaka masa
bayan wasu watanni Sanda ta samu nutsuwa abu na farko daya fara zuwa kanta shine karatu,a yanzu bata da burin daya wuce ta dawo da karatunta,ta shaidawa malam,ya aminta da hakan,saboda tun farko yasan burin ameen kenan a kanta, ya sadiqu ma yayi murna sosai da har yanzu karatun bai bar kanta ba,kuma shine ya shige mata gaba,ta samu takardun qualifying da secondary School certificate,sannan ta samu damar zana jamb dukka cikin shekara guda,komai nata ya hadu yadda ya kamata,ya sadiqu ya daye tuquru wajen sama mata makaranta,har ta dinga mamakin yadda ya maida kai,saboda har yanzun 'yar tsama suke,saidai katsam sai gashi makaranta ta samu,muma course din data nema,murna kamar tayi me? Tun ana saura kwana bakwai ta fara zuwa din babu irin fada da hudubar da bataji ba kan qawaye,daga bakin inna ne,daga bakin malam ne uwa uba kuma daga uban gayyar ya sadiqu. Zuwa yanzu itakam aita gurzu,ta kuma gane duniya,ba sai an mata ma magana aka qawaye irinsu munira ba,munirar da suka jima suna gaisawa amma bata taba gaya mata aurenta ya mutu ba,sai ranar data wanki qafa taje gidan da sunan ziyara sannan ta samu labari,daga nan kuwa tayo gida wajen iman din cikin tashin hankali. Saidai kuma yadda ta samu iman din qalau cikin walwala yasa jikinta ya danyi sanyi,ganin munira a gidan sam bai yiwa iman dadi ba,don ita yanzu bata qaunar dukkan wani abu da yake da alaqa da bassam,ko kuma zai tuna mata dashi,a yanzu rayuwarta dadi take mata,tana jin kamar an tariyo mata da rayuwarta ne,saidai akwai abu daya da tasan ta rasashi,akwai abu daya da takeji cikin zuciyarta cewa tayi missing,tana jin akwai wani babban bangare abu mai muhimmanci kuma jigo cikin rayuwarta data rasashi wato ameen..abunda ke daure mata kai kuma shine,babu wanda ya taba yin zancansa a gabanta..da kunnenta dai bata taba ji ba,babu wanda ya taba yi mata maganarsa,tunda tazo gidan bata taba ji anyi labarinsa ba,ita kuma bata taba tambaya ba,inaaaa .ina ta isa tayi zancansa ita din?,bata da wannan qwarin gwiwar sam,saita tattara komai ta ajjiyeshi gefe guda,bawai don ta manta ba. Tun munira na zuwa iman nayi mata hannunka mai sanda.tana daure mata fuska da rashin sake mata,har takai ga ta fito gaba da gaba da gaya mata
Tunda na fito munee ban taba zuwa gidanku ba nikam.inaga ba.me zai hana mu haqura da wannan ziyarar,muci gaba da gaisawa kawai a waya idan da yiwuwar hakan?" Sosai taga rashin dadi qarara samn fuskar munira,saidai ya zamar mata dole tayi mata hakan,saboda ta fuskanci abinda ya sameta munira ce ta bada gudunmawar afkuwarsa kaso saba'in cikin dari,shi yasa ta gwammace su nesanci kuna gaba daya ita da ita,a yanzu mutum daya take tare da ita,suke kuma shawara wato bushira,saboda ta tabbatar ita din qawa ce ta arziqi,data fito daga gidan dattako da sanin ya kamata. Fara zuwan iman makaranta taci qwal ubanta ba kadan ba,taji jiki ta jigata,saboda shi karatu ko yaya ka barshi,to shima saiya maka nisan da baka taba tunani ba,saidai naci da jajircewa sune tushen dukkan wata nasara,haka ta sakawa ranta himma naci da kuma jurewa,da kadan kadan sai gashi ta fata ganewa,ana kuma dan tafiya da ita babu laifi,saidai ba kamar sanda take kafin aurenta ba,bata damu da hakan ba,ta sama ranta tafi tafi wataran zata dawo da kanta wannan matakin da ikon Allah.
bayan shekara biyu Turare shine abu na qarshe data fesa saboda cike kamalar kwalliyar tata,ta maida turaren saman madubi ta ajjiye tana kallon fuskarta jikin madubin dake dakin. Kyakkyawar fuskar hajar ibrahim khalilu iman fuskar da a yanzu tafi cikar kamala fiye da shekara biyu baya,fuskar data cika da tarin annuri da kuma alamu na qarin shekaru,alamun da suka qara ma fuskar tata cikar kamala,kyau da kuma haiba,sai cikar haduwar hankali da kuma sanin ciwon kai da suka bayyana akan fuskarta,a hankali ta gyara daurin kanta hagu da dama ta tabbatar yayi,ta murmusa har dimple dinta ya lotsa daga dukkan kumatunta
Alhamdulillah.ta fada a bayyane,kamar yadda ya zame mata jiki a duk sanda ta kalli kanta,taga kuma ubangiji ya saita mata rayuwarta,ta fara maida abubuwan data rasa a baya a rayuwarta masu yawa,tana godewa Allah da miyagun qaddarorinta basuyi nisan zango ba,tana godewa Allah da bai dubi halinta ko kuma abinda ta aikata ba. cikin rahama tausayi da jin qansa ya wadata rayuwarta da abubuwa masu kyau. Cikin kayanta ta laluba mayafin daya dace da shigarta da 'yar jakar hannu da take dura takardunta,ta yafa ta hada da takalmi sannan ta fara takawa zuwa tsakar gidansu,cikin wani taku da ba nata ba,wanda wala'alla sauyin yanayi da kuma rayuwa ya sanya dukkan dabi'unta na ainihi sake fitowa. A hankali ta tako zuwa tsakar gidansu,qamshin turaren wuta na kaya yana surarowa daga jikinta saboda tsabar yadda ya kama jikin nata,ya hade da sassanyan body mist da take amfani dashi Tsakar gidan nasu tabi da kallo,gaba daya ta rasa meke shirin faruwa a gidan da inna ta kasa zaune ta kasa tsaye,kwana kusan uku kenan innnar tana yiwa gidan kwalema. Iya tuquru da iman din ake aikin,kasancewarta wadda dukka ayyukan gidan suna wuyanta dama,ta riga ta saba,saidai sam ta kasa tambayar innar dalilin kwalimar. Ko yanzun ma kallon innar take ita da mufida sunata sauke kayan kitchen din innar ana fitowa dasu,yarinyar cikin dangin inna na nijer take,tazo mata hutu ne,saboda gama zana jarrabawar common entrance da tayi,da iman din aka fara aikin,amma ganin lokacin makaranta yayi yasa ta saki aikin taje fa shirya.
Sannunku da aiki ta fada tana qarasowa inda suke tana rataya jakarta
Yauwa.kin fito Inna tafada tana dan dubanta kafin ta maida kanta taci gaba da aikin da takeyi
Eh inna,harma naso na makara" tayi maganar tana duba agogon fata mai azabar kyau dake daure a tsintsiyar hannunta. Tana daga kai suka hada idanu da mufida,ta saki murmushi yarinyar
Wannan kallon fa? Iman ta tambayeta itama fuskarta a sake
Wallahi kinyi kyau yaa iman,haka nakeso idan na qara girma nima na shiga jami'a,na kuma zama 'yar gayu irinki
Yar gayu,'yar gayu,'yar gayu,bakinki baya gajiya da gayamin wannan sunan?" Dariya mufidan ta saki
Don Allah inna yaa iman ba 'yar gayu bace?,kuma kyakkyawa
Oho muku,wannan zancan naku yafi qarfina.ungo nan inna tayi maganar tana daukar dari biyar daga kudaden dake gefanta ta miqa iman din
Idan kin fito ki biya ta kasuwa ki samomin turaren bakhur
Bakhur kuma inna?"Ta tambayi innar cikin mamaki
Eh shi,laifi nayi kika tsareni haka da kallo?Kai ta kada
A'ah inna,gani nayi kina da turaruka,harda wadanda baki amfani dasu ba,ko wancan satin ma na kawo miki wani turaren wuta Wannan din shi nakeso..ki wuce ki tafi ko kuma ki bani aikena
Sai na dawo" iman din tafada zuciyarta na motsawa,tuna mata da sunan turaren tamkar wani fami ne a rayuwarta,sunan kawai ya tuna mata da wani abu jigo,haka ta ratso ta soron gidan dan fita qogar waje Sauka idanunta yayi kan dakin ya sadiqu,nan ma dai kamar cikin gidan,an fidda komai na cikin dakin,babu komai a cikinsa da alama shima kwalemar ake,tanason ganin ya sadiqun,amma sai taji ba zata iya shiga dakin ba,don haka ta saka kai zuwa waje zuciyarta na mata wasu wasi Kofar gidan dukka babu daliban malam din,da alama kowa yayi jasa waje,don dama sha daya tayi lokacin tashinsu kenan,babu kowa sai malam din dake zaune saman kujerar da yaje karatu,snaye da farin yadi qal da kuma farin rawani na wani lallausan plain yadi Malam din badai tsafta da kuma kwalliya ba,duk qwaqwarka ba zaja taba rasashi cikun tsafta da qamshi ba,duk kuwa da cewa mafi yawan kayan sawarsa harma da rawaninsa yafi tu'ammali da farare,amma ko yaushe qal zaka gansu kuna fes,hakanan malam din baisan saka tsumma ba,tun a lokacin ma da bashi da mataimaka koda yaushe cikin kyakkyawar shiga yake bare yanzu Sai data duqa tama mallam sallama,ya kuma sallameta da kudin mota kamar yadda ya saba,duk da sana'ar da takeyi amma sam shi bai damu da wannan ba,ta raba a hankali taci gaba da takawa zuwa titin unguwarsu,kwanyarta cike fal da tunanin aiken innar har zuwa sanda fa samu abun hawa ta wuce makarantar.
Daga bakin gate ta sauka ya biyashi,itakuma ta soma takawa zuwa cikin makaranta.huguma
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 38
Kamar ko yaushe daga shigarta ta fara fusgar hankalin maza da dama,duk inda ta ratsa binta ake da kallo,tun abun yana damunta harma ya zame mata jiki,ba mazan ba,hatta da wasu matan suma kallon suke binta dashi a yawancin lokuta,saidai babu fuskar da zaka tunkareta da wata magana,saboda sam bata barin fara'a saman fuskarta har dangane da ajinsu,shi yasa mutane ke kiranta da mabambantan sunaye. Wasu na mata kallon miskila,wasu na mata kallon me girman kai,wasu nacewa ta isa tayi,ai tana da kyan da zata nunawa kowa,mata da yawakuma na kishinta ne sabida tana da kyan dake fusgar hankalin samari ko abokan huldarsu. Itakam bata damu ba,saboda abunda ya kawota kawai takeyi,kuma darajar addua da takewa kanta da rayuwarta,Allah ya tsareta daga dukkan sharri na miyagun malamai harma da daliban,so bataga abunda zai dameta ba kuma. Awa uku kawai dama ke gareta cikin makarantar,saidai a tsahon awa ukun aiken inna ya tsaye mata a rai,bata kuma san dalili ba,kawai dai tasan ta tuna mata da ya amin,saboda shi daya ne a gidan ke mayatar son turaren bakhur,don haka ana tashi ta wuce kasuwar ta siyama innar aikenta,sannan ta zarce asibiti,saboda yaune ranar da zataje taga dr,don duk bayan wasu watanni tana zuwa,saboda gudun dawowar matsalarta,shawarace dr din ya bata,kuma taga alfanunta. Mutum biyar ne a gabanta,tana zaune tana ta juya turaren a hannunta har zuwa sanda aka kirata,saita maida jakarta ta ratayata,sannan ta nufi office din. Da sallama abakinta ta tura qofar ta shiga,ya daga kansa yana amsa sallamar tata,sai fuskarsa ta zarce da mayalwaciyar fara'a,ya maida kansa yana qarasa rubutunsa cikin file amma kuma yana cewa
"Hajjaju,yau kece a gari?" Fuskarta da dan nata murmushin ta amsa masa sanda take zama
"Nice dr
"Marhaban dake" saita sake murmushin tana cewa
"Na gode dr" rufe file din yayi,ya tattara dukka hankalinsa akanta,suka gaisa sannan ya fara mata tambayoyi,daga bisani ya gwada komai.komai normal yake,ya ajjiye kayan gwajin da murmushin nan dai na fuskarsa
Alhamdulillah,hajjaju lafiya ta samu,saidai duk da haka mu bamu gaji da ganinki ba,sannan ba zamu bada shawarar ki daina zuwa ba,koda sau daya.ne ko biyu a shekara" ya fada yana rubutu a file dinta
Tunda komai ya zama normal dr inaga.ai no need naci gaba da zuwa din ko?" Kai ya gyada
Idan hakan yayi miki fine godiya tayi masa sosai sannan ta buqaci amsat file din ta maida reception,saidai yace
Noo..barshi a nan hajjaju,kawai abinda nakeso na duba a jiki
Ok dr,na gode" ta sake masa godiyan tana nufar qofa ba tare data kawo komai cikin ranta ba
Ammmm.hajjaju taji ya ambata sanda ta murda hannun qofar zata fice,waiwayowa tayi,suka hada idanu,idonsa fes bisa kanta
Kice hadiza sabi'u ta shigo
Ok dr ta fada a ranta tana mamakin kallon da ya bita dashi a yau,karon farko.
Tana zaune cikin dakin nata daga bakin katifarta,ta ware fanka sosai iska na shigarta tako ina,sanye take da wata buba ta wani yadi mai sulbi,sai dankwalin inna data dauka ta daura shima mai sulbi,hannunta riqe da biro tana bin assignment din data gama da kallo cike da nazari tana dubawa,tare da bin qwaqwafin inda tayi ba dai dai ba.
Motsim shigowar mufida ya sanyata daga kai tana duban yarinyar,tun dazun suketa aikinsu ita da inna,yau din ko nemanta ba'ayi ba,duk kuwa da cewa aikin abinci innar takeyi,abincin ma wanda iman din ta qware sosai akai,wato hadin wainar shinkafa Agogo iman din ta fara kalla tana duban mufida data dauro alwalar sallar magariba tana qoqarin saka hijabinta,kawaicinta a yau ya qare,ta rasa gane abinda ke wakana cikin gidan
"Wai nikam mufida..inna baqi garega gobe cikin gidan nan?"
Au baki sani ba?" Yarinyar ya fada,da alama tana zumudin bada labarinne
Ban sani ba mufeeda" iman din ta fada tanayin wani kalar tausayi
Duk gyaran nan da akeyi har dakin yaya sadiq?,baqone zaizo gobe,inna tacemin d'anta ne zaizo daga qasar waje,kullum sai ta bani labarinsa,tace tunda ya tafi can baizo ba sai yanzu,tace yana da kirki sosai.sunansaaaaa.ummmm,ya aminu" matsananciyar faduwa da gabanta yayi har sai da biron hannunta ya subuce ya fadi,dama ya amin ne zai dawo?,kowa a gidan ya sani amma banda ita?,indai hakane kuwa kenan basu haqura ba,har yanzu akwai haushinta qasan ransu. Kafin ta sake wani tunani kiran sunanta da ya sadiq yake qwallawa daga qofar dakin nasu ya katseta,saita miqe da sauri,saidai kuma yadda dukka wata laka ta jikinta ta mutu ya sanyata cin tuntube,saura kadan ta fadi,ta dai daita kanta tana amsa sannun da mufida take mata,ta qarasa qofar dakin,ta yaye labulen tana cewa
Yaya sadiqu gani"
Ungo don Allah,hadamin shi,yanzu nakeso nasha" ya fada yana miqa mata yar babbar baqar ledar,data buda sai taga jayan fruit ne, fruit salad yakeso ta hada masa kenan Kitchen ta wuce kai tsaye ta fara aikin,tana aikin tana kallon yadda aka gyara kitchen din,ga jerin kayan abinci nan da aka rage ayyukansu,gobe kenan za'a qarasasu. A sanyaye ta gama hadawa,ta miqa inna din ta fara diban nata,sauran ta ajjiyewa ya sadiq din ta komo daki,data shigo dinma litattafan ta tattare waje daya ta haye katifarta,bata da qwarin gwiwar ci gana da duba assignment din gaba daya,ta rasa mene yake mata dadi,wanne yanayi take ciki,ya amin zaizo?,yaya haduwarsu zata kasance?,da wanne ido zata kalleshi? Tanajin mufida na tashinta tasha nata fruit salad din amma tace mata ta qoshi,wani irin fargaba mutuwar jiki gami da kasala ke dibanta,wanda ita kanta batasan dalili ba,saidai jikinta ya gama mutuwa murus,cikin wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita. Can cikin barcinta hancinta ya dinga debo mata kalolin qamshin girki,ta bude idanunta a hankali,ta juyasu cikin dakin nata,wayam yake babu mufida,da alama tuni ta fice,sai ta miqe da hanzari tana duba agogon wayarta. Qarfe tara ne na safe,yau din lecture daya gareta,itama kuma kamar ta jiya ce,sha daya na safe su gama qarfe daya,saita aje wayar,ta zamo daga katifar tata ta isa bakin qofa tana dan dage labulen tana kallon tsakar gidan,tsakar gidan nasu dako yaushe yake a tsaftace yau a kacame yake,ta saki labulen,ta koma da baya ta dauko set na kayan wankanta sannan ta sake fitowa. Sai data gaida inna dake ta faman loda waina a cooler,tadan tsokani mufida dake da son aiki bata gajiya sannan ta karbi ruwan zafi ta wuce wanka,tana shiryawa tana mamakin yadda kowa bai bi ta kanta ba bare ayi maganar zuwan ya lamin a gabanta,banda mufida ta gaya mata,ta tabbatar babu wanda zai gaya matan. Tsaf ta shirya cikin dinkin bubu na atamfa,wadda tayi mata kyau qwarai,jikinta sai fidda wani sihirtaccen qamshi yake kamar kullum,ta hada duk abinda zata buqata tayo tsakar gidan
Ba zaki tsaya ki karya ba." Kai ta gyada
Sai na dawo dai inna
Allah ya kaimu Wucewa dakin malam tayi,yana zaune da qur'ani gabansa da aka rubuta da jar tawada jikin wasu farin papers
Tun kwanaki naso a rubuta miki qur'anin nan ki wanke ki qara ruwa ki dinga sha..amma zan saka ayi miki keda mufida" malam din ya fada bayan sun gama gaisawa yana miqa mata kudin makaranta
"To a bani wannan malam tunda na gani?" Ta fada tana langabe kai,don a yanzu sau tari tafi jin dadin hira da malam din akan inna. Kai ya girgiza
"Wannan?,banda wannan,na muhammadu aminu ce" dif wuta ta dauke mata,sai ta miqe gwiwa a sanyaye tana yiwa malam sallama,idanunta suka sauka kan wata qanqareriyar shadda da hula tangaran,harda takalmi duka sabbi
Kilan duk na zuwanshi ne?" Ta tambayi kanta,sai ta fita tana mamakin yadda suka daukaki zuwan nasa,sunata shirye shirye kamar wadanda zasuyi wani biki. Ta dakinsu dake soro ma koda bata shiga ba tasan lallai dakin yasha gyara sosai,tana jiyo muryar ya sadiqu da alamu waya yake,sai ta saka kai ta fice a hankali Kusan karatun yau din gaba daya bata wanu fahimceshi dari bisa dari ba,tadai tsinta iya abinda zata tsinta,batasan me yaketa raba mata hankali da kuma dauke mata hankali ba,don koda aka tashi sai data jima kafin ta baro makarantar Tana cikin napep amma duk matsawar da zasuyi gaba zuwa gida sai taji wani iri
Don Allah idan ba damuwa juya dani kabuga" ta baiwa mai adaidaitan umarni
Ba matsala,amma zaki biya
Ka fadi nawa ne zan biya in sha Allah" ba musu ya gangara gefe,sannan ya juya kan motar suka koma baya. Haka kawai taji ba zata iya tunkarar gidansu ba,ba zata iya shiga gidan yanxu ba,ta sauke wani numfashi me nauyi tana lumshe idanunta,tana jin yadda iskar hanya ke bugun fuskarta,ta tabbatar a yanzun idan ya ameen din baya gida to ya kusa isa gidan,shi yasa ta yanke tafiya gidan kawu muntari wajen umma hassana. Suna isa ta fito ta miqa masa abunda yace ta bashi,ta saka kai cikin gidan bakinta dauke da sallama. Ta samu yaran gidan sunata shirin tafiya islamiyya,tana taya umma hassana shiryasu suna taba hira,har ta sallamesu,gidan yayi shuru ba kowa,sai yaron da take goyo Bandaki ta shiga ta canza pad din jikinta,sannan tayi alwala,duk da ba sallah zatayi ba,don dai kawai taji dadin jikinta,kafin ta fito umma hassanan ta zuba mata abinci,ta zauna tana ci suna hira. Bata jima sosai da cin abincin ba jikinta dukka ya mutu,taji tana jin bacci,saita kwanta umman ta bata waje ta fita qarasa ayyukanta,bata jima ba kuwa bacci yayi awon gaba da ita. Ba ita ta farka ba saida akayi sallar la'asar,shima qarar shigowar text a wayarta dake saman kanta ya farkar da ita,ta miqe zaune tana salati,ta jawo wayar ta duba,sai taga saqon daya shigo da number dr ahmad ne,gajeran saqo ne kamar haka
Barka da warhaka hajjaju,cewa nayi bari na gaisheki,fatan kin wuni lafiya,bissalam_*
Dr ahmad kuma?" Ta tambayi kanta cikin mamaki tare da maimaita karanta saqon,abunda ta kawo kawai a ranta shine yayi mistake na tura saqonne,saboda haka saita ajjiye wayar kawai,ta gyara daurin dankwalinta daya zame sakamakon santsin gashinta,ta miqe zuwa tsakar gida wajen umma hassana. Ta sameta tanata hada hadar yin dambu,gashi yayi mata yammaci,ta kama mata,nan da nan suka dora,ta tayata suka tsaftace wajen sannan suka koma daki suka dora hirarsu. Sai bayan an dan jima da idar da sallar magriba,harma.taci abinci sannan tayi ma umma hassana sallama,tana ta mamakin zuwan iman din da kuma dadewarta,har tana tsokanarta da cewa
Allah yasa ki dore da wannan zumunci" murmushi kawai iman din tayi,saboda ita kanta tasan ba zuwan Allah da annabi tayi ba. A hankali kamar wata tsohuwar barauniya take takawa sannu sannu,tun daga qofar gidansu zuwa cikin gidan,ta saki ajiyar zuciya sanda ta fuskanci dakin soron a rufe yake,saita qara sauri amma kuma cikin takatsantsan,ta samu ta shige dakinsu tana sauie ajiyar zuciya,duk da cewa bataji motsin wani abu ba. Jakar hannunta ta ajjiye,ta cire kayan jikinta tana canzawa mufida ta shigo
Yaa iman,yaushe kika shigo,yanzun nan inna ke maganar dadewarki
Kaina ne yake ciwo mufida yanzu na shigo..ina innar?"Tana rumfarta a zaune
"Ita kadai ce?"Eh,ai.babu kowa agidan,tun la'asar su ya sadiq da baqon baturen da suka zo dashi suka fita,basu dawo ba kuma bayanin yayi mata dadi,don haka ta fita a gurguje tayi duk wani uzurinta da zai fiddata tsakar gida ta dawo daki abinta,itadai haka nan takeji..batason su hadu da yaa ameen,batasan kuma me yasa ba
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 39
Washegari ma tashin wuri tayi,ta shirya a gurguje,ta cimma inna a dakinta tana zaune tana sauraren labaran siya, volume din can qasa,ta tadda zata iya jin duk wani motsi.
Binta da kallo innar tayi sanda take gaya mata zata wuce makaranta
"Allah ya kiyaye hanya,saikin dawo"
"Ameen" ta amsawa innar tana ficewa sa dan hanzari,cike da fargaba da kuma tsoron kada su hadu din,shima dai a ranar bata dawo ba sai bayan magrib,tana gidansu bushira,amma ta aikowa da innar yara kan tana can din.
Kayan jikinta kawai ta cire ta sauya wasu,ta zauna gefan katifarta jin shigowar saqo bayan ta jawo wayar tana dubawa
_Amincin Allah ya tabbata a gareki yake kyakkyawa,da fatan kin yini cikin koshin lafiya_
"Dr ahmad?" Ta sake tambayar kanta cikin mamaki,anya ko yana sane yake tura mata wadan nan saqonnin?,ko yauma mistake din yayi?. Bata lalubo amsa ba mufida tayi sallama ta shigo,iman ta daga kai tana dubanta,shadda ce a jikinta me kyau qwarai,dinkin doguwar riga,da alama sabuwace,don bata cikin kayanta kwata kwata da tazo dasu
"Yammatan inna,wannan kyau haka?,ina kikaje?" Iman din tadan tsokaneta,dariya tayi itama tana zama a qasa kusa da iman din
"Taro akayi fa yau,wallahi yaaya iman kinyi missing,baqon inna dan balarabe.......au,ashefa tace danta ne,yaya ameen,shine ya hada taro,ya bude wani qaton shago nayin dinki,kinga kyan da wajen yayi yaa iman?,sai naji inama ni tailor ce,kekunan dinki,injin stone,keken waiving komai dai yaya iman,baki gani ba wallahi".
Sallamarsa ce ta gauraye tsakar gidan,cikin muryarsa mai nauyin nan,wadda a yanzu ke bayyana cikar mazantaka nutsuwa da kuma kamala a tattare dashi,lumshe idanu iman din tayi,wani abu mai nauyi yana tsarga mata,kamar yasa zancansa suke,saita dubi mufida
"Dukanku yau kuna can kenan"
"Eh mana,harda inna da malam fa,wai dan balaraben nan ashe ya iya dinki,sai gashi yahau keke shima yaa iman?" Mufida ta fada cikin alamun mamaki,harda kama baki,duk da yanayin da jiki da zuciyarta ya shiga amma sai tadan murmusa kawai
"Tsohon tailor ne" daga haka ta sake bude wayarta ba tare da tana da abunyi ba
"Yaa iman.....na kawo miki abincinki?" Kai ta girgiza mata,bata jin zata iya cin wani abu
"Na qoshi mufida,kedai sannunki,na gode" sai yarinyar ta matsa wajen kayanta ta canza kayan jikinta,sannan ta fice daga dakin.
Iska mai nauyi da zafi iman din ta fitar tare da sauke ajiyar zuciya,tana ci gaba da taba screen din wayarta,zuciyarta na lulawa duniyar tunani,wanda muryar mufida ta katseta
"Yaa iman kizo inji inna" dokawa qirjinta yayi,ta daga kai da sauri,tana son tambayar mufidan waye da waye a falon,amma tuni yarinyar ta shilla abunta da gudu ta koma.
Sunan Allah ta kiraya kafin ta tashi,saita zari dogon hijabinta ta zura,ta ajjiye wayarta ta fito ta doshi falon,zacuyarta na harbawa da sauri.
Tana yaye labulen wani irin kwantaccen qamshi ya cika mata hancinta,ta bude bakinta a hankali tayi sallama,muryar data amsa mata sallamar ta sake sanyata ta daburce,kanta na a qasa ta kasa dagashi,batasan waye da waye a falon ba,batasan kuma inda zata zauna ba,don haka ga zame mata dole ta daga idanunta ta zabi wajen zama.
Karon farko idanunta suka sauka a kanshi,yana zaune saman center carpet saboda aka shimfida falon innar,wanda iman din kanta batasan yaushe aka sakashi ba,sanye yake da shadda ruwan hanta,sai maiqo take da qyalli tare da fidda qamshi,baqar sumar nan tasa ta ainihin bafillace tana nan a kansa,ta qara kyau cika da kuma wani qyalli da sheqin baqi,duk bata iya ganin fuskarsa sosai,amma tana iya hagen wani lafiyayyen gemu daya zagaye ya kuma qawata fuskarsa,ya qarawa fuskar kyau da kuma cikae kamala da kwarjini,da amaa sunansa na cikakken namiji,da hanzari ta dauke kanta daga wajen,duk da har yanzu hankalinsa nakan mufida,da alama akwai wani zance da sukeyi daya dauke masa hankali,kamar ma labarin qasarsu take bashi.
Cikin sauri ta samawa kanta waje,sai a lokacin ta lura da baraka(yayar alameen wadda ta riqeshi) daga gefe tana sallah,da yake falon na inna akwai yalwa,sai kuma ya sadiqu dake gaban kayan kallo da batasan sanda aka kawosu ba shima yanata qoqarin hadasu.
"Ina yini yaaya,an dawo lafiya?" Waiwayowa yayi a hankali ya dubeta sau daya,sai ya kautar da idanunsa,yadan saki gajeran murmushi
"Bazan amsa ba,saida kowa ya gama yimin sannu da zuwa sannan ke?" Sadda kanta tayi qasa,cikin mamakin yadda ya amsa mata a sake,kamar wani abu bai faru ba,kamar babu abinda ya gitta tsakaninsu,kafin ta bada amsa muryar baraka ta ratsa tsakani
"Banda abinka aminu dan makaranta ai bashi da wani sukuni,babu zama ko iman?" Nauyi ya kuma saukar mata,ita kanta yaya barakan kunyarta da nauyinta takeji,saita gyada kanta ta daga kai ta kalleta
"Ina yini yaa baraka,ya hanya?"
"Lafiya lau imani,gamu yau a kano,ya gida ya makaranta?"
"Alhamdulillah" ta amsa mata tana murza yatsun hannunta,tanaji kamar zata nutse,musamaman sa kwanyarta take mata tariyar abinda ya shude shekarun baya,duk da cewa ba wata magana data yana hadata mara dadi da yaa barakan ko a baya,amma ta tabbatar tana da labarin komai.
Hirace qasa qasa mufida da amin sukeyi,sai yaa barakan dake janta da hira,yayin da sadiqu ke nashi aikin,kafin daga bisani ya saki aiki yaja tsaki
"Nafa gaji gaskiya,kaga ka taso muje kawai na rakaka,kaga dare yayi,idan mun dawo ko zuwa gobe a qarasa"
"Alright" ya amsa a taqaice yana miqewa
"Idan na dawo maci gaba ko" yace da mufida,ya tako a hankali ya gifta iman din,idanunta ya sauka saman qafarsa daa sake haske da fresh,zaratan yatsunsa sun cika da gashi
"Yaaya zamuje mu dawo"
"To kwace ina gaisheta" suka saka kai suka fice,yayin da yabar qamshinsa mai yawa a hancin iman din,ya kuma bar zuciyarta da tunani da kuma wasi wasin inda zasu,duk da yadda take jan zuciyartata amma ta nace dason sanin inda suka tafin,har sai da inna ta shigo sannan ta samu sasauci,ta bata abun shara tace ta gyara spare dakin dake kusa da nata,baraka zata kwanta a ciki.
Haka kawai ta dinga kasa kunne taji shigowarsu,bata samu jin shigowar nasu ba kuwa sai wajen sha daya da rabi na dare,ta sake lumshe idanunta tana jin muryarsa daga can nesa yana magana,da alama yana daga soron,bai shigo cikin gida ba,ta sauke numfashi tana gyara kwanciyarta zuwa daga side din.
Basu sake haduwa ba ita dashi tun daga ranar,washegari dama yaya baraka ta koma,ita kam sunyi sallama.
Satinsa biyu taji labarin ya koma daga bakin mufida,abun da ta danji ya mata susa a ranta kenan,lallai tabbas duk wata alaqa dake tsakaninsu da amin din ta lalace kenan,banda haka......inda yadda ya dauketa a baya yanzunma hakanne,ba shakka itace mutum ta farko da zata fara sanin komawarsa.
A bakin mufidan takejin labarin nan da wata shida zai gama karatunsa ya dawo gaba daya,yace ma a nan za'ayi bikin salla qarama dashi,mufidan ta dauko wayar inna da tace shine ya siyawa innar,ta nunnu mata sabon shagon da tace sunje bikin budeshin.
Shagone mai kyau na dinkawa da kuma saida kayan sawa,sutturu kala kala daga na maza har na mata,ba wani qatoto bane,amma kuma yana da yalwa da kuma girma,bugu da qari yadda aka tsara wajen dole ya burge mutum,an tsara komai bisa tsari me qayatarwa,sannan ya sadiqu shine shugaban wajen da zai dinga kula da gurin.
Kanta ta jinjina,har yanzu ya amin bai rabu da dinki ba kenan,yana nan cikin jininsa?,saita miqawa mufida wayar tana murmushi tare da cewa
"Gaskiya yayi kyau wajen"
"Wallahi yaa iman saima kinje,yace ayimin dinkin sallata acan ma,har ya zabarmin atamfofi,wallahi dan gidan innar nan yana da kirki sosai sosai yaa iman" murmushi ya subuce mata,mufidan ta tuna mata da wani abu,ta tuna mata sanda take kamarta a shekaru,sanda ya amin din yake nata take tashi,sanda yakeji da ita,yake kula da komai.nata cike da kulawa da takatsantsan
"Sosai ma kuwa" ta amsa mata tana jijjiga kai,sai mufidan taci gaba da bata labarin ya amin din da kirkinsa,ita kuma ta bata lokaci tana sauraren yarinyar.
Ko a washegari tana ta kasa kunne taji ko inna ko ya sadiqu ko malam wani zaiyi maganar amin da ita,saidai babu wanda yace mata komai,abun sai ya bata mamaki,amma kuma ita a qashin kanta ta gayawa kanta,suyi mata maganarsa suce mata meye?,a sanda ta yankewa kanta hukunci ba wanda tayi shawara dashi,sannan a yanzu duka rayuwar amin da mu'amalarsa bai shafeta ba,indai zata yiwa kanta adalci,ya kamaci ta tsame kanta,da wanna ta sanya abun wani sashe can na cikin ranta,duk da ta sani abune mai yiwuwa ace ta mantar da kanta al'ameen din.
*_BAYAN WATA UKU_*
Tsaye take a parlor din inna tana hada tea,bayan ta gama duk wani shirinta na tafiya makaranta,don hatta da jakarta ma tana falon innar,sai data gama hadawa tsaf sannan tafara kurba tana tsaye kusa da fridge.
Labulen uwar dakan inna aka daga,innar ta fito cikin atamfarta mai kyau England,tayi tsaf da ita,kana ganinta kasan tana cikin jin dadi da samun kulawa sosai,don tsufanta da shekarunta basu wani bayyana ba sosai,musamman da yake ba wani haihuwa tayi me yawa ba,mayafinta a hannu iman ta kalleta
"Au fita kema zakiyi inna?"
"Eh amma yanzu zamu dawo ai,cewa mufida tayi hanzari ta fito" sai ta ajjiye cup din hannunta tana daukan jakarta da mayafinta itama
"Naji ya sadiqu yana magana dame adaidaita,idan hanya daya zamuyi ku saukeni a makaranta mana,na huta fita titi tarar abun hawa"
"Bari sadiqu yazo muji" inna ta amsa mata tana zura hijabinta,dai dai lokacin sadiqun ya shigo,shima a shirye tsaf cikin wani tattausan yadi da al'ameen ya kawo musu iri daya shi dashi
"Inna game adaidaita yana qofar gida yana jira"
"Ya sadiqu idan hanyatace ku saukeni nima"
"Muje,amma sai mun fara biyawa ta inda zamu din kan a qarasa makarantarku"
"Ba matsala idan ba dadewa zakuyi ba,nima akwai sauran lokaci" da haka suka dunguma suka fita gaba daya,bayan ya sadiqun ya kulle gidan,saboda babu kowa,malam ma ya fita.
Sam bata fuskanci inda zasu ba sai da suka dauki hanya taji ya sadiqu yana yiwa inna bayani
"Yayi qoqari gaskiya sosai,shi yasa kudin hannunsa suka kusa yankewa,filin babba ne,ya siya kayan gini da yawa,farawa zasuyi"
"Aminu badai qoqari ba,Allah yaci gaba da dafa masa"
"Ameen inna,gaskiya dai kam,yayi dabara da bai saki sana'arsa ba,kinsan wasu daliban idan suka fita qasar waje,sai suga ai faduwa ce suyi sana'a,zama suke cima zaune sai abinda gwamnati ta aiko musu dashi,sanda ma.basu samu ba haka zasu rungumi hannu" kai inna ta jinjina
"Kaga kuwa wannan aiba dabara bace,ni nasan aminu da zuciyar nema,bazai taba zama haka ba dama" kaman bata a cikin motar haka tayi,saidai kunnuwanta na tare dasu,har zuwa sanda suka qaraso unguwar suka soma shiga cikinta.
Sababbin gidaje ne a unguwar,kana gani kasan mazauna cikinta duka basu jima da fara tarewa ba,saida akwai gidaje ba laifi,unguwace me kyau da tsari,a hankali har suka qaraso bakin wani kango,wanda zagayeshi kawai akayi da doguwar katanga.
Cikin adaidatan tayi zamanta,ganin babu wanda yayi mata tayin ta fito din,bayan wajen minti talatin sai gasu sun sake fitowa sun ci gaba da tattaunawa,bakin inna cike fal da addu'a akan amin din,har sanda suka qaraso bakin motar ya tayar suka tafi.
Bayan watanni biyu shirye shiryen daukar azumi ya kankama,rana daya taga an fara gyaran gidan nasu,an gyara tsakar gidansu an shimfida marbles,parlor din inna an sassaqe an masa tiles,haka rumfar malam ma,bandakin gidan shima ba'a barshi a baya ba,sai dakinsu ta sadiqun shima da aka maida shi tiles da tiles har jikin bango,sannan akabi gidan aka yi masa fenti.
Dama can gidan nasu gini ne tsayayye me qwari da kyau,ga kuma innar gwanar tsafta,sai gashi ya sake dawowa sabo fil,aka shirya komai a muhallinsa,cikin qanqanin lokacin gidan yayi wani haske gwanin sha'awa.
Cikin taimakon Allah da huwacewarsa aka dauki azumin ramadan,sannu a hankali kwanakin suka fara shurawa,har aka shiga goman qarshe,sai gashi ana zancan jibi sallah,a ranar ne iman din suka tafi qunshi da gyaran kai ita da mufida,yanayin cikowar sallah daban wajen masu lallen da gyaran kai,wannan yaja musu basu suka dawo gida ba sai bayan sallar isha'i.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 40............Inna a bani abinci,kamar banci komai ba wallahi" iman ta fada tana tuje dankwalin kanta,sassalkan gashinta da yasha gyara ya bayyana,ta zauna saman kujera tana jawo flask din data gani,ta bude ta tsiyayi kunun ciki Anan parlor din inna taci abincinta ta qoqarta tayi sallar asham,qarfe tara da wani abu saiga ya sadiqu,mufida ta anshi ledar hannunsa bayan tayi masa sannu da zuwa,ya amsa yana zama,iman ma tayi masa,sai mufidan ta matso tana shirin ajiye masa ledar
A'ah dauke,ai ba tawa bace,kayan sallarku ne aciki" murna sosai ta kama mufida,ta miqawa inna ledar,innan ta fara fidda kayan ciki tana dubawa. Atamfofine kala uku a dinke na manya,dinki me kyau da tsari,sai kuma lace guda daya,sai na mufida kala biyar itama,atamfa uku lace biyu,dukkaninsu kana ganinsu zasu burgeka,daga dinkin har kayan kasan wanda yasan kan abunne ya zabesu
Wannan inji al'ameen,saiki zaba kalolin hijaban da kukeso gobe idan na fita sai nasa a dinko muku,da size na takalmin mufida,ke dama 38 ne ko?" Ya fada yana kallon iman,kanta ta gyada gami da amsa masa da
Eh". Godiya inna taci gaba dayi kamar ameen din yana wajen,yayin da sadiqu ya soma bata labarin yadda shagon daya bude keta samun hubbulowar jama'a
Wallahi inna baki gani ba,yadda kikasan an yiwa wajen yayyafin farinjini,sai yanzu nake gasgata dabarar ameen din,daa inata cewa kar ya bude,ashe shi ya dade da sanin albarkar dake cikin dinki"
Banda abunka ai tsohuwar sana'a ce da qasar hausa ta gajeta,mutane ke raina sana'ar,amma duk wata sana'ar hannu ai albarka gareta,har yanzu akwai manyan gidajen da basu bar gadonsu ba,saidai sun zamanantar da ita kamar yadda aminun ya zamanantar da ita shima
Gaskiya dai,ai na gani" ya sadiqun ya fada,yana rufe bakinsa wayarsa ta dauki ringing
Kinga shine ma yake kira" sadiqu ya fada yana duban inna
Dan halak kenan,yaqi ambato" ta fadi tana murmushi,suna gama gaisawa ya miqawa inna,bayan sun gaisa tayi masa godiya sosai,sannan ta hadashi da mufida,a nan ne suka dan jima suna magana,da alama zolayarta yaketa yi tana dariya. Tsam iman ta miqe,ganin yadda koda yaushe suke sake maidata kamar wata bare ko baquwa a cikinsu,saita wuce dakinta ta barsu a parlor din. Kira ne ya shigo tata wayar sanda ta gama wanka ta dawo don sauya kaya,bata samu dagawa ba har sai da aka sake kira,ta qarasa fesa turarenta ta ajjiye ta qaraso ta dauki wayar tana duba me kiran. Dr ahmad ne,ta danji mamaki,don bai taba kianta ba,iyakarta dashi tex,shima iyaka gaisuwa ce,ita kuma ta maida masa masa da thanks,ko tace masa na gode sosai. Tana daga tsaye ta daga kiran,sallama yayi mata daga bangarensa ta amsa masa
Har na fara tunanin ba zaki daga wayata ba
Saboda me?,nasani ko wani maganin ka samomin?" Dan qaramin murmushi ya saki
Wannan karon idan akwai wanda za'a bawa maganin ma nine" bata gama fahimtar maganarsa ba ya sake sako gaisuwa
Ya gida ya ibada"
"Alhmdlh,ya akaji da marasa lafiya?"
Gamu nan,mun godewa Allah" shuru ne yadan ratsa,kafin daga bisani ya sake magana
Inata miqo gaisuwata hajiya amma bana samun wata gamsashshiyar amsa banda ta godiya,ni kuma ba godiyar nan nakeso naji ba"
Toooo..to me kakeson ji dr?" Dan murmushi ya saki
So nake a tambayeni dalilin yin gaisuwar" dan murmushi kawai ta sake,saboda yadda yayi maganar ya bata dariya
Ai nasan akwai kyakkyawar mu'amala tsakanin likita da mara lafiyansa ko?"
Duk da hakanma..amma yanzu wannan likitan yanason sake qarfafa alaqa da dangantakar dake tsakaninsa da patient dinsa,bayan waccar alaqar" ya zuwa yanzu ta sansano wani abu a cikin maganganunsa,amma sai tayi kamar bata fahimta din ba
Idan babu damuwa,inaso ayimin izini nazo yawon salla,koda ba za'a bani barka da sallah ba" Dr ahmad yana da kima da mutunci a idanunta,amma saidai batajin zata bashi wannan damar,ita a yanzun gaba daya ta sare da lamarin maza,tsoro suke bata,to ta bawa dr ahmad din damar zuwa malam ya ganshi tace masa meye?
Kayi haquri dr.ba yanzu abubuwa sunmin yawa
Sai yaushe kenan?" Ya ritsata da tambaya,kasa gano amsar daya dace ta bashi tayi,sai kawai bakinga ya subuce da fadin
Nan gaba kadan zan saka ranar" ajiyar zuciya ya sauke,duk da ba haka yaso ba amma yace
Allah ya nuna mana lokacin" kasancewarsa bame zafi ba,hakanan bashi da tsawwalawa,yana da sauqin kai da kuma saurin fahimta.
A sauqaqe yadan jata da hira,bai kuma matsa da yawa ko ya kaita bango ba yayi mata sallama,suka katse wayar dukansu. Tana ajjiye wayar ta waiwaya wajen mufida wadda ta shigo rungume da kayanta,har yanzu akwai farinciki qarara saman fuskarta
Yaaya iman..wannan sallar xan sha kwalliya wallahi,irin taki da daurin nan da kikeyi xakiyimin" murmusawa tayi
Aikam dai ya kamata" ta amsa mata a taqaice,saboda haka kawai takejin batason magana. Kwanaki biyu a gaba musulmi suka sauke azuminsu,washegari akayi idi,ranar sallar suna gida,saidai sunyi kwalliya gaba dayansu,sunata baqi jifa jifa inna na saukarsu da tuwon sallaj da basa fashin yinsa duk salla,a ranarma taga inna nata shirye shirye,kamar wancan karon na zuwan ameen din,ta tabbatarwa ranta shi dinne zaizo,saiai bata sani ba,gobe ne ko kuma jibi.
Karfe sha daya na safe ta gama shirinta tsaf cikin kwalliya,cikin daya daga cikin sababbin atamfofinta,sam bata da matsala sutura koda shekara nawa zatayi bata siyeta ba,hakan ya sanya zaiyi wuya ka ganta da kaya ka sake ganinta dasu a kurkusa. Tsaf ta gama shirinta,saidai tana dubawa yaga mufida da zasu fitan tare bata shirya ba
Wai meye haka mufida?,tsaiwa zanyi jiranki?"
Nafa fasa zuwa yaa iman,yaya ameen ne zai dawo yau" sai da taji qirjinta ya amsa,amma ta dake ta amsa mata da to ai shikenan,ta yiwa inna sallama ta wuce gidan kawu muntari.
Wuni guda hankalinta a rabe yake gida biyu,idan alameen ya dawo yanzu ya dawo kenan,ta yaya zasu rayu gida daya tare ita dashi?,wannan tambayar itace ya hanta sukuni,harta qaraci wuninta ta dawo gida. Koda takoma gida boyon kanta tayi a daki,ta kuma fake da ciwon kai,ta tilastawa kanta baccin wuri,washegari kuma still ta sake fita,data dawo dinma ta qunshe kanta a daki,a rana da uku ne yunwa ta sanyata tashin wuri,bataso amma dole haka ta fito,tana sanye da doguwar rigar bacci mai kauri da taushi,sai baby hijab data dauran saman kanta,ta tsallake mufida dake bacci ta fito tsakar gidan nasu ta zarce kitchen. Gidan shuru ba motsin kowa,da alama basu tashi ba,don haka take komai cikin takatsantsan karta tashi wani,kitchen din nasu ba kasafai ya fiya dattin dare ba,sabida suna gama girki inna ke sawa a wankeshi kota wanke da kanta saboda gudun zaunuwar qwari,don haka dan sake goggoge shi tayi,ta duba abinda suke dashi,ta dora breakfast din,cikin ranta tana danjin marmarin yin girkin,saboda tadan kwana biyu bata shiga kitchen din ba.
Tana aikin tana lissafin inda zataje yau din,taga miscal na munira,saidai bata bi ta kanta ba har yau,muniran nata nacin ci gaba da qawancensu,da kuma son wanke kanta game da aurenta da bassam,tana gaya mata itama batasan haka bassam yake ba,da bazata bari ya samu iman din ba,ita duka wannan yanzun ba shine a gabanta ba,an riga an wuce wajen,tunda dai qaddararta tazo da sauqi tana godewa Allah,kawai dai sam a yanzun bata sha'awar qawancensu da muniran baki daya,shi yasa taketa ja baya da ita,layinta na yanzun ma sabo ne data canzashi baya ya fara zuwa makaranta,batasan ya akayi muniran ta samu number ba.
Wani mummunar faduwar gaba ce ta ziyarce tana kwashe kaskon qarshe na chips din data soya,daga dan nesa kadan take jiyo muryarsa,da alama yana bakin qofar shigowa tsakar gidanne,a hankali muryar take kusantota,bugun zuciyarta na qara daduwa,duk da haka ta aro jarumta tana ci gaba da kwashe dankalin don kar ya qone,har zuwa sanda taji muryar tasa fa fito sosai,da alama yana baki qofar kitchen din kenan a tsaye,sai a sannan ta fahimci waya yake,waya kuma cikin taushi da Idan ban takuraki ba zan iya samun ruwan dumi?" Ya fada cikin laushin muryar san nan da ya sanya wani abu ya tsarga mata,sa'annan ya kuma tuna mata da wani lokaci acan baya,lokaci me matuqar dadi cikin rayuwarta,lokacin da duk safiya yakanzo ya tsaya kamar haka,yakanzo yana mata hira tana aiki,ko yana tayata..idan kuma da idanun inna yakanyi monitoring dinta.
Ci gaba yayi da wayarsa hankali kwance yana kallon wani wajen,saita juya jikinta na dan rawa kadan,ta debo masa ruwan zafi,tunda ba kamar baya bane da take da yaqinin zaizo,wanda take debo ruwan ya samu ya huce kafin yazo sha.
Gashi" ta fada tana miqa masa,sai a sannan ya waiwayo,itama kuma sai a sananan taga fuskarsa tarwai,ya sake hada wani kyau cikar kwarjini da kamala,gashin da ya barwa fuskarsa ya sake maidashi cikakken matashi mai jini a jika,kyansa kamar ya ninka na baya,saboda ya cakuda da ilimi hutu da jin dadi,ba kamar na baya ba dake hade da fita nema a kullum,cikin zafi rana ko ko kuma ruwa. Batasan yadda akayi ba ta saki kofin ya sube,sai ga cup din shi sa ruwan da yake dauke dadshi sun zama pieces qasan tiles.
Subhanallah" ya fada da hanzari yana cire wayar da yakeyi din daga kunnensa,cikin sauri ya duqa yana cewa
Garin yaya haka?,ai ban karba ba,bakiji ciwo ba dai ko?" Kanta ta girgiza alamun a'a,sai ta juya da sauri zuwa cikin kitchen din nemo tsintsiya a rude
A hankali mana" ya fada da dan sauri,saboda yadda yaga tana tafiya da sauri sauri,har tana shirin taka fasashen tangaran din
Move ya fada yana qarasawa kitchen din,a hankali ya maida wayarsa aljihu,sannan ya matsa inda dust bin da tsintsiyan yake,ya daukosu,ya duqa a hankali ya sharesu ya zuba a dust bin din,sannan ya matsa kusa da flask din,ya bude ya zuba wani ruwan zafin ya fice a kitchen din yana cewa
Ki dinga lura Gaba daya ji tayi jikinta ya sake,ta kasa ci gaba da aiwatar da komai,ta koma jikin cabinet na kitchen din ga jingina tana sauke numfashi,har yanz rawan da jikinta yakeyi bai dai daita ba,ta kusa minti goma sha biyar a haka,sannan ta motsa taci gaba da aikin,wanda ba jimawa mufida ta tashi,ita ta kama mata wasu ayyukan,don gaba daya wani karsashi na jikinta babu shi ya gudu. Har ta kammala aikin bata sake ganin wulgawarsa ba,sai kawai ta zarce da wanka,ta fito ta shiga dakinta ta shirya tsaf,sosai tayi kyau cikin wani lace da aka yiwa dinkin riga da skert, color din lace din ta haskata sosai da sosai,lite makeup tayi kamar yadda ta saba,fatar fuskarta nada kya da sheqi,hakan yasa yawancin lokuta koda lite makeup tayi zakaga tai masifar yin kyau,koda lio gloss kawai ta shafawa lebbunanta,ko abincin bata iya ci ba ta dauki mayafinta da jaka ta nufi dakin inna. Daga bakin qofar falon tadan tsaya,gabanta ya fadi saboda jiyo muryarsa da tayi daga cikin falon,kamar ta koma,saidai kuma babu yadda za'ayi hakan ta kasance,saidai cikin biyu ayi daya,ko tayi shahada ta shiga ta nema izinin fita,ko kuma ta koma fa haqura da fitan,wanda a zahiri tana buqatar ta fita din. Mayafin kayan ta ware ta yafashi saman kafadunta,sannan ta dan runtse idanunta kafin ta sanya hannu ta bude labulen ta shiga da sallamarta. Ameen dinne ya amsa hankalinsa nakan hada tea,yana zaune saman center carpet da kayan breakfast a gabanshi,yayin da inna ke saman kujera can gefanshi suna hirarsu. Bai daga kai ya dubeta ba har tazo ta gotashi zuwa gefan innar,murya a qasa tace "Inna zan fita...yau zanje gidansu
Au,ai na tsammaci aiki kika samu" cira kai tayi ta dubi innar
Aiki kuma inna?"Eh,da naga kina sintirin fita kullum..halayyar da kika tsiro da ita kenan iman?" Ajjiye cup din yayi ya miqe a hankali ya fice daga parlor din,hakan ya sanyainna ta maida hankalinta sosai ga iman,fuskarta a dinke tsaf fiye da daxu.[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 41
*_KU BIBIYENI TA AREWABOOKS DOMIN SAMUN SABBIN PAGES DA DUMINSU_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62beaa7c93b638ade30a0e93
41
"Baqin hali da baqar zuciya kika koyo?,daga ina?,duk fice ficen da kike ina sane fa,nayi shuru ne na zuba miki ido naga gudun ruwanki.....tun zuwan aminu na farko na karanci take takenki,bakyason ganinsa saboda ya miki laifi?,bakyason ku hadu ko?,duk wata sabga data shafeshi ko ta shafi uzurinsa baki saka hannu babu ke a ciki,shine yanzu kika tsiri fita saboda ya dawo gida,to baro kiji,saidai ke kibar gidan,saboda aminu ya dawo gida kenan,idan ma baqinciki kikeyi saidai ki yishi ki gama ke kadai......mara tunani kawai" tunda inna ta fara fadan kuka ya kubce mata,haquri kawai take bata,tama rasa da bakin da zatayi mata bayanin da zata fuskanceta,sam abinda innar ta fahimta ba haka bane......sai ta miqe da sauri sauri ta fice daga parlor din,ganin innar ta kasa fahimtarta.
Dakinta ta isa,ta fada kan katifarta tana sakin wani sabon kukan,ta yaya zata fahimtar da inna kunyar alameen takeji?,yaya zata ganar da ita nauyinsa takeji?,tana nadamar furucinta a kansa ne na baya?,tana nadamar ayyukanta na baya,da kuma jin kunyar lafuzanta,duk sanda ta ganshi saita tunasu,saitaji kamar a yanzune take ce masa bata sonshi,kamar a yanzune take furta me zatayi dashi,kamar a yanzune take fadin Allah ya kiyaye ta aureshi,bata gaba ko fushi dashi......saboda bai cancanci tayi ba.
Haka ta dinga kukanta ita daya,mufida ta jima a kanta cikin rashin jin dadi tana bata haquri,kafin ta wuce ta bar mata dakin.
Ta jima ahakan,kafin daga bisani bacci ya dauketa,baccin da tayi na awa biyu,bata farka ba sai qarfe daya saura,kai tsaye ta daura alwala,ta dawo ta sauya kayan jikinta zuwa masu sauqi wadanda ba zasu dameta ba.
Kitchen ta zarce ta fara musu shirin abincin rana,tayi alqawarin faranta ran innar da dukkan wani abu da tasan tanaso,zai kuma faranta mata,indai kula da amin ne damuwarta zata gyara in sha Allah,saidai tana tunanin yadda hakan zata kasance,tana tunanin yadda shi kansa zai karbeta ta koma kamar da.
Lafiyayyen girki ta tsara,wanda ta jima batayi irinsa ba,sannan ta hada lemo,don a yanzun basu da matsalar wajen sanyi,fridge biyu keda innar,daya a falonta,daya na rumfar malam,ta saka a ciki don yayi sanyi.
Kamar yadda ta saba haka ta hada tray guda na abincinsu takai parlor din inna,sannan ta koma daki ta zuba nata taci,abincin bai shiga da yawa ba,saboda yadda ranta yake babu dadi,haka abincin bai mata taste a baki ba,tadaiyi qoqarin dora walwala akan fuskarta saboda innar,data gama ci ma sai ta dawo parlor din ta zauna suka kunna kallo,saidai gaba daya hankalinta bashi a wajen
"Kinga mufida.....nasan yayunki na hanya sun kusa isowa,dinga daukan abincin nan a hankali kina kaiwa dakinsu,ga muqulli ki bude" inna ta fadi,mufidan ta tashi ta karba muqullin,duk iman din sai taji ba dadi,saboda aikinta ne,amma ta bari,tunda mufidan zata iya,ta dinga diba da kadan da kadan harta gama din,bayan minti wajen goma iman ta tuna da lemon,tasan basu fiya son abu yayi sanyi da yawa ba,gwara a cire musu shi a kai musu,kafin suci din xai huce,don haka ta miqe,ta cire lemon ta nufi dakin bayan mufida ta gaya mata sakaya qofar kawai tayi bata rufe ba.
Hankali kwance ta tura qofar,saboda tasan babu kowa a ciki,wani sanyin dadi ya bugi hancinta,dakin ya sakw wani girma kyau da haske,tunda akayi gyaran bata taba shigowa dakin ba sai yanzu,ko ina tsaf tsaf,tiles din nan yasha guga,mamakin ma wanda ke gyara musu dakin haka ya kamata,ta duqa a hankali tana ajjiye jug din,dai dai lokacin da ameen ya fito daga toilet.
Da sauri ta miqe,har jug din na rawa kamar zai biyota,saida ameen din yace
"Kula fa" batayi zaton yana dakin ba,hannun rigarsa a nade zuwa gwiwa,ya cire links din rigar,fuskarsa zuwa hannun da qafar tasa duk jiqe da lema,da alama alwala yayi,hakan ya bawa kwantaccen gashin dake hannunsa damar sake kwanciya lif,sai taja da baya tana shirin fita,ya sadiqu ya sako kai.
Dubanta yayi sosai
"Yau kuma a gari inji maqi baqo?" Binsa tayi da kallo,yana qarasawa gami da bude kwanukan abincin
"An gama nunqufurcin kuma yau anyi abinci kenan" ameen dake ware hannun rigarsa bayan ya shimfida abun salla ya xuba mishi idanunsa
"Xakazo muyi sallar tukunna ko sai ka gama sharhin?"
"Da alwalata fa,amma dai bari na sake wata.....idan kin shiga ki cewa inna mun dawo" wannan ya bata damar juyawa da hanzari ta fice,tana godewa Allah da bai samu damar sauke mata nashi kason ba.
"Wannan abun sam banajin dadinsa ba sadiqu" amin din ya fada sanda sadiqun ya fito daga alwalar
"Me akayi?" Tsaiwarsa ya gyara
"Ya za'ayi a takura yarinya haka?,dazu dazun inna ta gama yi mata fada,sannan kai kazo da naka zaka dora?,duka takurar ta meye ne?,kowanne bawa da kalar tasa qaddarar,kuma duk yadda ta riskeshi haka zai karbeta,don ban auri iman ba a baya ba wani abu bane,ba hakan na nufin dukka wata kyakkyawar alaqa dake tsakaninmu ba ta yanke,bata sona ne.....kuma ba wanda zai zauna mata dani,ta samu rabonta nima kuma na samu nawa,komai.ya qare a tsakaninmu,ba wata sauran alaqa,amma kuma har yanxu tana nan a matsayin qanwata.....to kuma meye na tsananin?"
"To akaramakallahu......tayar mana da sallah" sadiqu ya fada yana jinjina karamci irin na amin din,yana tuna irin wahalar da yasha a asibiti shekarun baya sanda iman din ta zama ta wani,amma ko a sannan nunawa yake ba silarta bane,muqaddari ne daga Allah.A yanzun kuma yana qoqarin sake share komai tsakaninsu,da kuma yunqurin maida matsayinta irin nada,lallai iman din tayi asara iya asara,asarar da bayajin zata maida kamarsa,tunda kusan zaice mai rabo ta dauka......
Ranar wuni tayi cikin gidan,kuma cikin parlor din innar,babu inda taje,duk don ta faranta ran innar,sai kuma taga ma gaba daya ma baya zama a gidan,daya shigo yake fita,da alama akwai wani abu me muhimmanci da yaketa aiwatarwa,wanda ya hanashi zaman.
Hudu ga sallah ya shirya zuwa jigawa wajen yaya baraka,mota har qofar gida mai kyau ya dauka shata shi kadai,batasan mufida zata bishi ba,sai gani tayi tana shiryawa,tayi shuru tana tuna shekarun baya da suka shude,a irin lokaci irin wannan itace kan gaba wajen tafiya jigawan,idan sukaje a qalla sukanyi kwanaki uku acan,yaaya barakan tana lelenta gami da ina ka aje da ita.
Tana parlor tana yiwa inna moping ya shigo parlor din,sanye yake da wata danyar shadda ruwan sararin samaniya,wadda ta dinku ta kuma zauna a jikinsa.hakanan ta dace da jikinsa,kansa babu hula,hakan ya bayyana kansa daketa qyalli,da alama ta samu gyara ainun,hular tana riqe a hannunsa kawai,da alama baida sha'awar sakata,kallo daya zaka yi masa kasan cikakken dan gayu ne,wanda yasan ma'anarsa,bawai a baki kawai ba,har a aikace,duk indanya gifta kuma sai ya bar tsarabar qamshinsa mai sanyi a wajen.
Kallo daya tayi masa ta sadda kanta qas,wani kwarjini yake mata a yanzun sosai fiye da shekarun da suka shude,bata sani ba ko a yanzun yafi cika idanu ne,shekaru da cikar sametakarsa da suka bayyana muraran oho
"Ina kwana?" Ta fada kanta a qasa,don tasan ba zata iya hada idanu dashi ba,waiwayawa yayi yayi mata kallo daya ya amsa da
"Kin tashi lafiya?" Yasa qarasa takawa zuwa ciki,idanunsa kan agogon bangon parlor din innar
"Alhmdlh" ta amsa masa a gajarce,saboda sam bata saba da irin wannan gaisuwar tasu ba,baquwace a gurinta,kuma sun fara irinta ne tun sanda komai ya lalace a tsakaninsu.
Kamar ko yaushe ya tsugunna a ladabce ya gaida inna,ta amsa tana cewa
"Tashi aminu karka bata jikinka,wajen a danyace yake bai bushe ba" sai ya saki murmushi kawai yana cewa
"Inna zamu wuce"
"To ma sha Allah......sai yaushe kenan?"
"Eh to,ina jin ba zamu wuce gobe ba,saboda cikin satin nan nake saka ran fara shiga office,kuma har yanzu ban gama shirya komai da komai ba"
"To madalla,madalla......bari na baka saqo ka kaiwa barakan" sai inna ta miqe zuwa cikin dakinta,tsalelen agogon hannunsa mai tsada ya kalla,sai ya sauke hannunsa yana sake gyara zamansa,yana dan tsokanar mufida da lallausan muryarsa,akan yadda ta zaqu su tafi,har zuwa sanda inna ta dawo da leda babba ta miqa masa,ya amsa suka sake sallama
"Allah ya kiyaye hanya" kalmar data amsawa mufida da ita kenan sanda take ce mata sun tafi.
A ranar tayi zaton zata sake sosai,saboda dodon nata baya nan,amma sai taji sam ba haka bane,hasalima gaba daya sai takejin wani kewa da rashin dadin zaman gidan,daga bisani ta alaqanta hakan da rashin mufida,tunda zuwa yanzu sun saba sosai,har inna na shawarar daukota gaba daya,tunda tasan da gudu iyayenta zasu bata ita.
**** *WASHEGARI.......* Samun kanta tayi da tsara abinci me kyau,abincin ma kalar wanda tasan ya amin din yanaso,tunda taji sunyi waya da inna,ya tabbatar mata zuwa yamma zasu taho,yasan zasu qaraso kafin magariba,tunda tazarar dake tsakanin jigawar da kano bai wuce awa biyu da rabi ba.
Sosai innar taji dadin abunda tayi,itama hakan sai ya faranta ranta,tunda dama tayine saboda innar,burinta kuma ya cika,innar ta dinga janta da hira,abunda ya jima bai faru a tsakaninsu ba.
Sai hudu na yamma ta gama komai,ta fada wanka sannan ta shiga dakin don ta kintsa jikinta.
Tsaye tayi a bakin madubi tana kallon fuskarta,ita kanta tasan yau fuskar tata ta cika da annuri,hakan kuma yana da alaqa da yadda suka wuni yau da inna cikin dadin rai,sai ta samu kanta da yiwa kanta alqawarin lallai zata ci gaba da yin hakan,kodon ta samu irin wannan kulawar data rasa a baya.
Barin gaban mudubin tayi da sauri ganin lokacin sallar la'asar na nemam qwace mata,ta isa ma'ajiyar kayanta,ta fitar da wata doguwar riga mai budadden hannu,wuyan me kwala ne,haka nan qasar rigar a bude yake sosai,ta saka ta shafa powder da lip gloss,sannan ta saka hijabinta ta tada salla.
Tana idar da sallar ta fara azkar dinta na yammaci,kamar jira wayar tata take ta idar din ta dauki kida,ta miqa hannu ta dauko tana duba me kiran,dr ahmad ne,kuma ko shekaran jiya ya kirata ya gaisheta kamar yadda yace,saita daga wayar ta kara a kunneta hadi da sallama.
Cikin sakewa da sauqinsan nan ya amsa mata,sannan ya fara gaidata,abunda yake dada sakata jin nauyinsa kenan,shi bai wani damuwa da ta gaisheshi,mutum ne mai.matuqar sauqin hali da sauqin kai,saita maida.masa gaisuwar,ya amsa sannan ya fara janta da hira.
Tadan saurareshi,saboda tana kunyar qin tsayawar,don sau biyu yana kira tana taras da miscalled kuma.bata bi kiranka,kuma ko a yanxun bai mata qorafin rashin daga wayar ko kuma qin biyo kiransa ba.
"Har yanzu lokacin baiyi ba da za'a bani dama nazo?" Kanta ta girgiza kamar tana gabansa,amma a furuci sai tace dashi
"Kayi haquri" ajiyar zuciya ya sauke
"Inata haquri hajjaju......amma zan gaya miki gaskiya,kawaici kawai nakeyi,inason nazo mu tattauna seriously,zuciyata kullum qara ragwancewa takeyi,kada naje ina zaune ayin overtaking" duk da ta gama gano manufarsa a kanta,amman yanzun da ya fara bayyanawa sai da abun tajishi wani iri,batasan me ya dauki dr ahmad ya fada sonta haka ba,amma koma meye tanaso su rabu lafiya,saboda mutum ne daya girmamata qwarai da gaske,ya kuma taimaki rayuwarta sa shawarwari da kuma kulawa ta musamman irin ta likita,amma zance na gaskiya ita a yanzu kwata kwata babu wanu tsari ko maganar aure a ranta,batajin akwai wanda zata iya bawa filin zuciyarta ya shiga.
"Akwai lokaci"
"Ya ubangiji,ka nunamin wannan lokacin" taji ya fadi da confidence dinsa,saita sake masa murmushi kawai.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 42
Ana idar da sallar magarib da hijabin jikinta ta shiga falon inna,ta sameta itama ta kammala sallar
"Inna kinga su mufida shuru har yanzu"
"Zancansu nake nima a raina,ke nake jira kizo ki kamo min su a waya"
"To" ta amsa dashi,saita zauna ta fara lalube a wayarta,cak ta tsaya daga bisani,tunawar da tayi alameen inna keso a kira mata ba ya lamin na shekarun baya ba,sai ta sauke wayar tana dan duban inna,saboda bata da number wayarsa a halin yanzu,batason kuma ta fadi inna ta tunzura,saita miqe a fakaice,ta dauko wayar inna ta saka numbers din ta fara kira.
Dab da zata tsinke taji ya daga,muryarza fes,da wannan sautin mai nauyi da kuma taushi yayi sallama,saida gabanta ya fadi sannan ta amsa sallamar a hankali,shuru ya ratsa tsakani na aqalla sakanni goma,daga can bangarensa yayi shuru yana saurare,duk da zuciyarsa ta gama shaida masa wacece,amma ko afuska baiyi alamun da zai nuna ya gane din ba
"Wace?" Ya jefa tambayar kai tsaye,zare wayar tayi daga kunneta a hankali,wani abu yana mata susa a qirji,dama bai kamata ta kira ta kama wayar ta qanqame ba,saita miqawa inna tana cewa
"Gashi"
"Yauwa" inna ta fada tana karba,miqews tayi ta matsa gaban kayan kallo ta maida gaskiya plus wanda suke gabatar da shirin zamantakewa,sai da innar tace
"Gashi" sanna ta juyo ta karba wayar,tana shirin sakata a charge ya sadiqu ya shigo falon
"Inna kinjisu al'ameen shuru ko?"
"Eh yanzu muka gama waya dashi,ashe mota ce ta basu matsala a hanya"
"Haka yace wallahi,ya kirani"
"To Allah yakiyaye,ya kawosu lafiya"
"Ameen ameen.....me kuka dafa ne inna,inaso zan fita" yayi maganar yana kallon iman,kafin ta amsa masa sai kuma yace
"Yi sauri ki zubomin,na makara" miqewa tayi ta zuba ta kawo masa,yana ci suna hira da inna,har ya gama ya miqe zuwa dakinsu da sunan zaiyi wanka,iman din na kallonsa tanason tsokanarsa kan zance ya fara zuwa ne,saidai ganin yana sauri yasa ta barshi har ya fice.
Ba'a rufa awa daya ba sallamar mufida ta fara iskowa cikin gidan,ta shigo dakin innar bakinta a washe,tana janye da wani babban buhu da yafi qarfinta
"Inna mun dawo" ta fada tana sakin buhun gami da zubewa
"Lale maraba da mutanen jigawa tarin Allah" tsokanarta iman ta fara yi,daidai lokacin da muryar amin ta bayyana a tsakar gidan shima yayi sallama,gabanta ya fadi kamar ko yaushe,ta lumshe idanunta tana kiran sunan Allah,sai kuma muryar tasa ta gauraya data ya sadiqu,dukkansu suna yunqurin shigowa parlor din
"Kaima ance ka siya mota kaqi,ka tsaya wani noqe noqe,kullum baka da aiki sai shatar mota,kana zaune zan siya mota,ka zauna kallo,ana gama maganar gidansu yarinyar nan motar zan hara" ya sadiqu ya fada sanda suke shigowa falon,yana kan gaba,sanye da wata dakakkiyar shadda ruwan hanta,ya kafa hula abunsa yayi kyau sosai,shima sadiqun a wadan nan shekarun sai hamdala,saboda tuni ya daina aikin gyaran mota,ya fara sana'ar siyar da sabbin spare parts na motar,kuma samu yake sosai
"Zan siya,komai a hankali ake abinsa mr sadiq" ameen dake shigowa rataye da jaka a bayanshi ya bashi amsa,ya zarce da sauke idanunsa a fuskar iman wadda keta qoqarin gyara zamanta ba tare da dalili ba.
Ita ta fara masa sannu da zuwa sannan ta zame jikinta tabar dakin,duk sanda yake waje batajin sakewa kwata kwata,sai taji kamar ya cika dakin,bata iya wani qwaqwaran motsi.
Takusa minti arba'in a zaune gefan gadonta,suna musayar text da dr ahmad daya matsa mata ta tayashi hira,mufida ta shigo janye da wata leda ta miqa mata
"Gashi inji yaa baraka" ajjiye wayar tayi ta janyo ledar tana cewa
"Toooo,me muka samu?" Cikin ranta tana mamakin yadda yaa barakan ta aiko mata da saqo haka?
Mangoro ne mai kyau da yawa,wanda a wajen fatarsa kore ne,amma ta ciki ya nuna,irin mangwaron da take matuqar so,sai gyada mai bawo dame gishiri mai yawa kowacce a qulle daban,sai dinya da yawa.
"Kai duk wannan nawa ne?" Kai mufida ta gyada
"Tace sanda kuke zuwa da ya amin sune kayan da kika fiso" wani nauyi da kunya suka kamata,tabbas haka ne,a sanda take mutum kafin ta zama BUTULU KUFAN WUTA,ashe yaa barakan bata manta ba?,hakanan abunda tayiwa dan uwanta bai sanya ta gaza aiko mata da tsarabar ba?,wanne irin karamci ne har haka?.
Fita tayi da kayan ta adanasu,ta diba gwargwadon yadda zai isheta ta dawo daki.
*************Daga tsaye take cikin parlor din innar daga wajen bakin qofa, breakfast take hannu baka hannu qwarya saboda gab take data makara,sanye take da wata abaya saqar qasar dubai,wadda ya dace da jikinta,tayi mata kyau matuqa,saika zata daga wanca jinsin ta fito.
Ta jiyo takun takalmin daga tsakar gida,amma bata kawo komai ba saboda hankalinta bai wajen,sai da aka yaye labulen falon,haske ya cika falon tare da sassanyan qamshinsa sannan ta ankara da waye.
Al'ameen ne,cikin wasu irin suit masu matuqar kyau da aji,idanunsu suka sarqe cikin na juna,take bread din da take qoqarin hadiyewa ya tsaya mata a wuya,ta hadiyeshi da qyar,sai kuma qwarewa ta biyo baya.
Dagowa yayi a hankali daga qoqarin cire rufaffun takalmansa daketa qyalli saboda yadda suke fes babu ko digon qura a kai yadan dubeta
"Ki nema ruwa kisha kafin abinda kikaci ya dawo" ya fada a hankali cikin nutsuwar nan tasa,yana qarasa fidda takalman,ya tako zuwa cikin falon bakinsa dauke da sallama,daidai sanda inna ta bude labulen uwar dakanta ta fito tana cewa
"Wannan gaggawar da kike ba dole ki qware ba.....ba'a yiwa abinci haka ai.....aminu......ka fito?" Cikin girmamawa ya gaidata ta amsa masa cikin kulawa
"Ina kwana?" Ta gaidashi tana daukar jakarta,wani irin kunya ce ta kamata,bataso yaga kamar ganinsa yasa ta qware din
"Kin tashi lafiya?" Ya maida mata
"Alhamdlh.....inna na wuce" ta amsa masa hadi da yiwa inna sallama,saboda tana da tabbacin matuqar taci gaba da tsaiwa cikin falon bata isa ta yiwa idanunta shamaki da kallonsa ba.
"Ka zauna kaci wani abun mana" inna tace dashi bayan fitar iman,saiya girgiza kai
"Ana jirana inna,kuma yau zan fara shiga office din,bai kamata naje a makare ba,sannan ma kuma akwai abubuwan daya kamata ace nayi settling a yau din" addu'a sosai innar ta kwarara masa,ya miqe cike da jin dadi da kuma qwarin gwiwa ya fita,yana jin dadi da kuma farinciki mayalwaci cikin qirjinsa,ko babu komai,ya samu wadda ta zame masaadadin mahaifiya,yake kuma samun da ɗaɗan addu'o'in da yake ganin tasirinsu cikin rayuwarsa,lallai babu ko shakka,inna nada wani madaukakin matsayi da kima a idanunsa.
Already akwai mai napep dinsa,yana qofar gida yana jiransa,yana shiga ya gaidashi cikin girmamawa,sannan yaja motar suka fara gangarawa zuwa bakin titi.
Har sun gota yatsaidashi,ya sanyashi ya koma da baya,iman dince a tsaye tana duba agogon hannunta,sam bata kula da tsaiwarsu ba
"Shigo mu saukeki" muryar amin din ta cika kunnenta,ta daga kanta da sauri ta saukesu a kanshi,ba ita yake kalla ba sanda yayi maganar,wayar hannunsa yake latsawa,ta janye idanunta daga kanshi ta fara takowa a hankali ta shiga motar,sanna yaja suka fara tafiya..
Shuru ne ya ratsa motar,ba qarar komai saita iskar dake shiga tana fita,da kuma daddadan turaren jikkunansu daketa gauraya cikin motar,duk juction din da suka tsaya sai idanuwa sunyi musu ca,shi kam idanunsa nakan wayarsa baisan me ake ba,tana tajin qarar tura saqo na watsapp.
A junction din qarshe wata budurwa ta ratso ta tsakiyar motocin ta yiwa mai adaidatan magana tanaso ya sauketa a gaba,ya girgiza kai alamun a'ah,murmushi tayi,idanunta nakansu iman din
"Hala ango da amarya ka dauko ko?,nice couple,wallahi kun dace,tun acan baya na hangoku,kun burgeni sosai" dubanta sosai iman din tayi,yayi da amin ya daga kai yayi mata,sai aka rasa mai bata amsa,harta ratsa ta cikin motocin ta bace musu.
Tsaiwa maganar tayi cikin zuciyar iman din,zuciyarta ta dinga azalzalarta ta kalli yadda suka dace din ita da ya amin ta madubin motar tana qoqarin kaucewa, lastly dai daga qarshe haka zuciyarta ta rinjayi idanuwanta,takai dubanta ga madubin,cikij rashin sa'a ya daga kansa yana duban hanya saboda jin sun koma tafiya slowly......karaf idanuwansu suka hadu,cikinbl wani irin hanzari da waskewa ta kauda idanun nata. Qaramin sauti taji ya fita daga bakinsa,wanda idan har ta canka dai dai murmushi yayi mata,gabanta ya fadi,kada dai ace ya ganta,tun daga lokacin bata sake wani qwaqwaran motsi ba har suka sauketa yaja sukayi gaba.
Wunin ranar a makaranta babu abunda take tunawa illa wannan dan zaman nasu da sukayi a tare,wani lokaci sai taji kamar jikinta yana tashin qamshin irin turarensa ne,ranar gaba daya bata da wani kuzari sam a jikinta har aka tashi.
********Aiki sosai alamin ya kama babu kama hannun yaro,babban kamfani ne da suka bashi babban matsayi,kamfani ne dake kula da gine gine da kuma qawar gidaje,suna da rassa iri iri a fadin qasar nan,babban reshensu yana a china,albashi suka sanya masa mai tsoka,amma duk da albashin da zasuke bashi.....da baiyi niyyar yin aiki dasu ba,hankalinsa yafi karkata ga bunqasa harkar dinke dinkensa,kamar xasuyi fada da sadiq ka hakan,saidai daya zauna sukayi shawara da inna da malam,malam ni ya nusashe dashi alfanun karbar aikin,zaiyi amfani da albashinsa ya bunqasa wajen ba tare da yabar aikin ba,wannan shawarar tayi masa,ya kuma gamsu da ita dari bisa dari,don yasan cewa abinda babba ya hango,yaro ko yahau bushiyar rimi bazai hangoshi ba.
*******A hankali ta gyara yafen mayafin doguwar rigar da take jikinta,sannan cikin sanyi ta dauki tray din dake jere da abincinnasu ta soma takawa zuwa dakin nasu,don dai babu yadda zata yine,amma gaba daya batason wani abu da zai kawo kusanci ko ya sanya su kebe da ya amin din.
Idanunta ta lumshe tana zuqar iska sosai zuwa huhunta sanda ta tsaya qofar dakin,ko ina na jikinta kamar an zare masa laka,ta tabbatar ya sadiqu baya nan,yatabbata zance yake zuwa,don kuwa magana har ta fasu cikin gidan,a yau dinma yana can,saboa haka tana da yaqinin ameen dinne kadai cikin dakin,tunda ya dawo ba zata iya tuna sanda ta shiga kai masa abinci yana shi daya ba,yawanci ma a yanzu a falon inna yakeci,idan kuma a dakin nasu zaici,mufida ke tsayawa daga soro tayi musu knocking su karba ta koma ciki,to yau mufidan tana dan zazzabine,bata jin dadi sosai.
Sallama tayi daga bakin qofar dakin
"Shigo" taji muryarsa tarrr yana bata umarni,wani abune mai qarfi cikin muryar lamin din,wanda duk sanda yayi magana koda bada ita yake ba sai taji ta saukar mata da nauyi saman zuciyarta da wani irin yanayi mai wuyar fassarawa,bataso ta shiga din,bata qaunar hakan,saboda haka tayi kamar bata ji ba ta sake maimaita sallamarta
"Come in" ya sake fada daga cikin dakin,a yanzu kam idan taci gaba da tsaiwa yasan cewa tayi ne tana sane,bata da wani sauran chance illa kutsa kai zuwa cikin dakin,idanunta sauke a qas,saidai tana shiga natural sanyin da dakin yake dashi,da kuma mayen qamshin nan nasa yayi mata sallama.
Yana zaune saman daya daga cikin kujerun dake gefe daya a dakin,wandda tayi kyau sosai a mazauninta,saboda yadda dakin ya qara kyau fili da kuma qayatuwa,sanye yake da wata baqar jallabiyya bai gajeran hannu,wadda tayi masifar haska fatarsa,kamar wani balarabe cikin jinsin wadanda basu cika hasken fata ba,sumarsa na nan a kwance cikin tsafta da burgewa,kai zaka dauka ba shine mutumin da bai jima da dawowa daga office ba,wayace maqale a kunnensa,yayi relax cikin kujerar sosai,babu lallai ka iya jin abinda yake fada.
Bata yarda ta kalli sashen da yake ba,qarasa a hankali wajen da suka ware saboda cim abincin tana dora tray din
"Miss you too.....i will call you" kalmar da taji daga bakinsa kenan,wadda taji kamar zuciyarta zata tsinke ta fado
"Zo nan" taji ya fada cikin wata murya dake nuni da umarni kai tsaye,cak ta tsaya,sannan ta waiwayo a hankali,dai dai sanda yake sauko da qafafunsa qas tare da matsowa zuwa gaba kana ya zauna sosai.
*_Arewabooks link_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62beab3c93b638ade30a1fc7
_please follow me_
@HUGUMA
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 43
*_follow my account @arewabooks as HUGUMA,for latest pages_*
"Dage curtains din" ya sake fadi kafin ta qaraso inda yake,sai ta koma a hankali zuwa bakin qofar ta yaye labulen yadda ya buqata,waje ta bayyana tarwai,ta yadda duk wanda zaya wuce zai hangi cikin dakin,sannan ta tako inda yake,tana jin qafafunta kamar sun lanqwashewa,kamar ba zasu iya daukarta ba.
"Uhmmm,zauna a nan" ya fadi yana pointing mata wajen da yakeso ga zauna din,wajen ta kalla,a qa'ida yayi mata kusanci dashi da yawa,bata da yaqinin idan ta zauna kafin ga tashi zuciyarta ba zata fashe ko ta tarwatse ba,ko kuma wani abun bazai sameta ba,dole taja qafafunta ta zauna a hankali a wajen,saidai a matuqar takure da kuma dar dar
"Iman..." Ya kira sunanta da wani irin heavy sound,wanda banda ta riqe numfashinta da kyau ba shakka zata samun daukewarsa na wucin gadi,duk da haka bata tsira ba,sai daya haifar da wani yanayi na daban cikin zuciyarta
"Me yasa kike qoqarin canzawa?,ko kuma nace kika canza?" Ya dakata a nan,ya zuba mata idanunsa dake da nauyi da kuma dafi a kanta
"Yanzu meye hakan?,kalli yadda kika zauna?,dodo ne ni ko meye?,duk wani abu da yake cikin idanunki ina iya karantarsa cikin lokaci qanqani......,bcoz.....nine mutum na farko da zan gayawa duniya wace ke,idan don abunda ya faru ne ki aje wanna issue din a gefe,ya wuce har gaban abada.....inaso ki saka a ranki da zuciyarki,babu wata kalma data taba shiga tsakaninmu dake makamanciyar wannan,ki sawa ranki har yanzu ya lamin dinki ne,wanda bai gurbata alaqar da take tsakaninku ba......idan hakan shi ya haifar da wannan ciwon,ki manta dashi,ki dawo iman dana sani a baya,na sani......kina takura kanki kan abinda ya shude har abada.....ki canza ki kuma gyara,ran inna yana baci,idan kuma kikaci gaa da wannan silly behavior din......ranki zai baci" yana kaiwa nan hawaye suka sauko mata,hawaye masu dumi,wasu maganganun nasa sun dada maga,wasu kuma sun tashi hankalinta,sun kuma sakamata shakku,tare da wani yanayi na tsaka me wuya.
"Ehnnnnn.....idan kin gama kukan kya iya tafiya" ya fadi yana komawa baya,yayi relaxing jikin kujerar ya janyo wayarsa yana dannawa.
Cikin dauriya da juriya ta goge hawayen fuskar tata,sannan tayi magana cikin harshen dake nuna anyi kuka
"Kayi haquri,zan gyara"
"Da kyau,Allah ya tashemu lafiya" ya amsa mata yana ci gaba da danna wayar still,saita miqe,tana takawa a hankali har tabar dakin.
Ita kadai tasan me takeji a cikin zuciyarta,ita daya tasan yanayin da maganganunsa suka jefata
"Su koma kamar da?,kamar yaya lamin da iman din inna?,kamar wata alaqa bata taba hadasu ba,hakan fa yana nufin yankewar komai da komai a tsakaninsu kenan" wadan nan maganganun ta dinga juyawa cikin ranta,barci kuma ya qauracewa idanunta,tana jin wani suya cikin qirjinta,har sai bayan da dare yayi nisa sannan ta samu baccin yayi gaba da ita.
*******Cikin kwanakin taga abinda ya fada mata din a aikace,da gaske ya maidata iman dinsa tada,ya dawo da caring irin na yaya da qanwa dake tsakaninsu,saidai a wannan karon akwai jan girma a ciki,wani lokaci harda wannan dadadden miskilallen halin nasa,ya koyi yi mata fada idan tayi ba dai dai ba,ba kamar baya ba da kome tayi zai dinga qoqarin bata kariya a idanun mutane,akwai haduwar jini tsakaninsa da mufida,don haka 'yar gidansa ce ita din,yadda zaiwa mufida hakanan yake mata,babu wani banbanci a tsakani,tayi qoqarin ganin ta warware itama,ta ajjiye komai a gefe ta koma yi masa kamar daa,saidai akwai wani strong feeling cikin zuciyarta,mai matuqar qarfin da itakanta take kasa controlling kanta a yawancin lokuta,sau tari sai ta bude WhatsApp dinta ta ganshi a online,kota duba dp dinsa,duk da ba ma'abocin saka hotonsa bane,a dp din,duk wani movement nashi hakanan ta samu kanta da interest akai,saidai babu wani abu data gani na daban tattare da alamin din,face fsohuwar alaqar da take tsakaninsu zalla da ya sabuntata.
Rana daya ta kalli kanta a madubi taga tana ramewa,abunda ya bata mamaki,ta kalli kanta ta sake kalla,tasan akwao stress na karatu,amma koma behind it akwai wani abu da ake kira rashin sukunin zuciya.
Tun da bata da wani aboki ko qawar shawara saishi,a yanzun kuma batajin zata tunkareshi da wannan batun,abu me matuqar saka jin kunya ga duk wanda aka budewa karatun,bushira ce kawai tazo ranta,duk da suna haduwa a chart suyi hira da ita,amma a yanzu ba shakka tana buqatar ganinta,tasan cewa ita kadai ce zata bata gamsashshiyar shawara bisa amana da kuma sirri,wannan yasa ta kirata tun safe ta gaya mata tana zuwa,da yammaci tayi qoqarin gamawa inna komai,ta shirya tsaf cikin atamfarta riga da skert,ta dora babban hijabi me hannu da ya saukar mata har qasa ruwan makuba neat dashi abun burgewa,kalar ta farare ce,hakan ya sanya yayi mugun mata kyau,don ko ita data tsaya gaban mudubi ta gani,tana godewa Allah kan tarin baiwarwakin da yayi mata,babu wanda zai kalleta ko a mafarki yace ta taba aure,duk da auren a suna ne kawai,bai amsa sunansa ba.
Gayu da qamshi sun matuqar zaunar mata,don haka ko zama kayi sosai kusa da ita kana iya diban tsarabar sassanyar qamshinta,wanda sai kana gab da ita ne zaka jishi.
A parlor ta tadda ina ta shaida matan zata fita gidansu bushiran,bata hanata ba,bushira sananniya ce,sannan tana yawaita ziyartar iman din,ta kalli mufida dake bacci a kujerar falon inna
"Ga 'yar rakiyar tawa tayi bacci"
"Eh saidai ki maza kije ki dawo"
"Yanzu kuwa inna in sha Allah" ta amsa mata tana sanya plate shoes dinta daya dave dace da shigarta ta nufo waje.
Kamar ko yaushe cikin nutsuwa tsari da kamun kai take tafiya,duk da yadda idanuwa kan mata caa idan ta fito amma bata daga kai bare ta damu dasu,tasan ita din wace,ta kuma san mutunci da darajar kanta,cikin mintina qalilan ta isa gidansu bushiran.
Ta samu gidan ba kowa sai ita,tana ta wainar fulawa,wadda qaninta ya roqeta tayi musu shida abokansa,kujera taja ta zauna zata tayata
"A'ah,wallahi bakiga yadda kikayi kyau ba,kada ki bata jikinki da manja,rigimar alqasim ce kawai ya tsiri na musu waina,ni da nake karatun exams,kedai bari na saka miki kici kawai" saita zaro plate ta saka matan,tana ci tana bude mata flask din tana zuba wadda ta soyu.
"Naji kince akwai magana,tun dazu nake dakon shigowarki" ta tambayi iman din bayan ta gama ci,yanayin yadda fuskarta ya koma kawai ya gayawa bushira she's serious kan maganar daya kawota.
"Magana xamuyi dake bisa yarda dake da amincin da yake tsakaninmu,duk duniya ba wanda zan iya gayawa wannan maganar saike,na dauki tsahon darare da kwanuka ina qaryata kaina,saidai kuma kan nawa shima qaryatani yake,har kuma ya rinjayeni.....bushira na kamu da son ya alameen" ta qarashe maganar cikin wani rauni,har idanunta suna tara hawaye.
Tsoro mamaki ko razani ta tsammaci gani daga fuskar bushira,amma sai murmushi da nutsuwa akasin wadancan ababen ya bayyana,abunda ya bata mamaki,ta tsaya tana duban bushira.
A kalla minti biyu suna a haka sannan bushira ta magantu
"Na baki mamaki ko?,to ai hajiyata wannan maganar a bude take,ke kika yaudari kanki kika kuma ha'inci kanki,kin dade kinason ya alameen.....rudar kanki kikayi,da kuma salon taki qaddarar data jefo miki da bassam,ya rikita qaramar zuciya da qwaqwalwarki dake ginuwa a lokacin.....kika dauki son da kikewa ya amin kika bawa bassam,a zatonki bassam din kikeso,bayan kuma bashi kikeso ba......bassam ya taka sahun barawo ne kawai a hausance" dif iman din tayi,tana jinjina kaifin basira da hangen nesa irin na bushira,ta karanta tsaf abunda ta jima tana surantawa a ranta da tunanin yadda zata fito dashi.
"Me kike jira da baku koma bigiren da kike akai ba keda ya ameen a yanzu tunda kuna da dama?" Kanta ga girgiza cikin alhinantawa kanta
"Mun koma......amma ba irin bigiren dake kike hasasowa ba......na koma matsayina na qanwarsa ne kawai,yakuma gayan iya hakane buqatarsa"
"To shine me?,zama zakiyi kina kallo ya zama rabon wata?,ko bari zakiyi ya subuce miki,a wannan zamanin da nagarta tayi wahala,samun miji na gari yake neman zamewa diya mace garari?,idan zaki tashiga ki maida kanki zuciyarsa cikin siyasa......bazan boye miki ba,randa na sake ganin ya amin nima ya tafi dani wallahi,kawai don nasan ajiya ce ta amana shi yasa na basar kawai" dole bushiran ta bawa iman dariya
"Da gaske nake miki,ki qoqarin daidaitawa kafin kiji sold out" wannan karon dariyar iman din sai data fito,ta daki cinyar bushiran
"Wai sold out kamar kaya"
"Tabdi,irin ya alameen ai kayanne masu tsada"
Wannan maganganu da kuma tattanawa da sukayi da bushira ta dade tana juyasu cikin ranta,tana aunasu a mizanin dacewa da kuma rashin dacewarta,tabbas soyayyar al'ameen ta yiwa zuciyarta wani wawan kamu da batasan yaushe hakan ta kasance ba?,idan har zata budi idanu taga ya zama rabon wata ta auna ta kuma gwadawa zuciyarta zata iya jurewa?,bataga mafita kota ina ba,to amma kuma ta yaya zata dorashi akan irin mizani da saitin da bushira ke mata nuni?,akwai abubuwa masu tarin yawa dake sanya zuciyarta cikin kunya nauyi da kuma shakku duk sanda zata daga kai su hada ido da ya ameen din,a fuska take qoqarin maida komai ba komai ba.....kamar yadda ta gaya matan shi a nashi sashen haka yake,saidai ta sani abundan ya farun wani abune da zai matuqar wahala ya gogu a zahiri.
Zuwa yanzun zuciyarta na gaya mata kamar ya alameen din yafi qarfinta,tako ina qofofin samu da kuma na arziqi ne suke bude masa,sabon shafin wadata da arziqi wanda suka bayyana hatta da saman fatarsa,zaka dauka cewa ba cikin gidan nasu yake rayuwa ba,duk da cewa gidan nasu a yanzu a layin yana cikin sahun gidaje dake da kyau da kuma tsari,can qasan ranta zuciyarta tana rawa tare da kwana da kuma tashi da fargabar kada ya kamo zuciyar wata ko shi a kamo tashi.
Bai cika shekara da kama aikinsa ba kawai yazo da takardun gida,gidane me kyau da kuma tsari daya siyawa malam din,da sunan su tashi daga nan,a barshi a mazaunin makaranta,su kuma su koma sabon gida,da farko malam ya fara fada
"Yaya zakayi haka aminu?,wanne irin bahagon tunani ne wannan kayi?,kai da kake da fili kake kuma gini?,muke saka ran ku gama kai da sadiqun kuyi aure kwana kusa?" Lafazin auren da malam ya ambata shi ya sanya iman miqewa tsam ta fara takawa tabar wajen,saboda ambaton kalmar dai dai yake da bugun guduma a tsakiyar kanta,batasan ya suka qare ba,daga bisani dai ta tsinci maganar tabbatuwar tashinsu,ta fara hada kayanta kamar yadda taga kowa yanayi,ranar wata alhamis bayan sallar magrib suka bar unguwar,bayan sunyi sallama da kowa.
Ginine me kyau irin na zamani,gidane madaidaici,wanda bai cika girma sosai ba,hakanan ba qarami bane,kamar gidan amarya,an tsara komai bisa tsari da kyau da kuma burgewa,duk wanda yazo sai ya yaba gidan,hakan 'yan rakiya da sauran 'yan uwa suka dinga fatan alkhairi tare da fatan tarewarsu a sa'a.
***********"Wayyo" tadan fada can qasan maqoshinta,tana miqewa daga durquson da tayi,har yau dakunansu basu gama zama ready ba,gyaran gidan suketa yi,wuni na uku kenan,saidai zuwa yau alhmdlh komai ya kusa kammala.
Ja da baya tayi tana kallon kanta a sabon madubinta,ta fito tar,duk da cewa batayi wanka ba amma ba zaka iya gane hakan ba,tana sanye da wata doguwar riga me zubin A shape,ta wani black cotton material ce mai touches na white,kanta kuwa siririn mayafin rigar ne ta daure kanta dashi,amma qanqantarsa ya sanya baifi rabin gashinta ya rufe mata ba.
Kishirwa take ji,don haka ta ajjiye sabbin kwalaben turarukan data siyo bayan ta gwada fesa daya,ta taka a hankali zuwa parlor din gidan don ta dauka ruwa a fridge tasha,kasancewar yau garin akwai hucin rana babu laifi,duk da cewa yamma liqis ne yanzun.
Sai data shaqi qamshin dake parlor din na sabunta da kuma turaren da suka kunna wanda tuni har ya gama cinyewa,saidai qamshinsa yana nan,ta qarasa fridge din ta bude ta dauko pure water guda daya ta bula ta fara sha,sannan ta juyo a hankali da nufin komawa dakinta.
Tsaye yake cikin parlor din,sanye da suit dinsa,hannunsa riqe da brief case,bata tsammaci ganinsa ba ko kadan a irin wannan lokacin,wannan yasa ruwan da take sha ya zarce mata take kuma ta qware,ta hau tari sosai.
https://arewabooks.com/chapter?id=62beaa7c93b638ade30a0e93
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 44
"Ya salam,garin yaya?" Ta furta sanda yake qarasowa inda take tsayen,kasa daga kai tayi bare ta bashi amsa,tana jin haushin kanta na yadda duk sanda zasu hadu sai tayi misbehaving,batason taci gaba da yin abubuwan da zasu janyo ta bada kanta
"Sannu" ya fada yana ja da baya kadan,kafin takai ga amsawa yace
"Ina inna?"
"Tana daki" ta amsa masa ba tare data iya daga kai ta dubeshi ba,qamshin turarensa ke haifar mata da wani abu cikin zuciyarta
"Qyaleta" ya fada yana juyawa zuwa qofar da zata fiddashi daga parlor din,ta kuma sadashi sa sassan su shida sadiqu,a sace tabi bayansa da kallo,kullum sake kyau yake da kuma sake zama wani na daban,cikakken namiji me aji,hutu jin dadi da kwanciyar hankali na sake bayyana muraran,tun daga kan fuskarsa har saman fatarsa.
Kadan ya rage ya kamata sanda take kallonsa,cikin wani irin hanzari ta dauke kai lokacin da ya waiwayo
"Me kuka dafa?" Yayi mata magana kamar yadda ya saba yi mata ayanzu,cikin dakiya shariya wani lokaci tare da burbushin halayyarsan nan miskilanci
"Tuwo ne" sai yadan murza goshinsa da yatsunsa
"Zan iya samun wani abun nadaban,wanda bazai wuce rabin awa ba" kai ta gyada masa,sai ya juya yaci gaba da takawa,maimakon itama ta koma dakin,sai kawai ta zarce kitchen,a yanzu bata da burin daya wuce yace yana buqatar abu kaza,wanda ita kuma a yanzu ba kasafai hakan ke hadasu ba.
Cikin minti talatin din da ya buqata ta gama shirya komai,ta dauki wayarta ta laluba number dinsa,sai datayi kamar zata kira sai kuma ta fasa,kada ta zaqe da yawa,don haka ta dawo parlor tayi zaune kawai bayan ta kunna tv din dake aiki cikin parlor din,hannunta riqe da wayarta tana duba wasu hotuna da sukayi biki a nijer watannin baya da suka wuce.
Tun kafin ya qaraso qamshinsa ya cika wajen,abinda ya qara gudun zuciyarta kenan,tana ga qoqarin hana kanta daga kai ta kalli qofar,wani sashe na zuciyarta kuma na azalzalarta,a haka sallamarsa ta cimma parlor din lallausar muryar nan tasa.
Sanye cikin wani lallausan farin yadi mai shara shara,wanda har kana iya hango singlet dinsa ta ciki,Hannunsa daya saye cikin aljihunsa,daya hannun kuma yana amsa waya dashi.
Fadin yayi kyau ma bata baki ne,wani sassanyan kyau mai tafiya da aji da kuma nutsuw,sumarshi tasha gyara sosai,lallai ta yarda ameen data sani a yanzu ba shine alameen din data sani a baya ba,komai ya saka yi masa kyau yake,ado mai cike da tsari da tafi da hankali.
Karamin dining da aka sawa innar a parlor wanda taketa mita akanshi ya nufa,har yanzu wayar yake amsawa,yayin da iman din ta gaza tashi daga inda take zaunen,saboda ta tabbatar idan taje din sai tayi wani abu da ba dai dai ba kamar yadda ta saba.
Parlor din ya dauki shiru bayan ya gama wayar,sai qarar plate da spoon dinsa daya fara cin abincin bayan yayi serving kanshi,cikin nutsuwa yake kai abincin bakinsa,fitowar inna ta katse shurun da ya wanzu a wajen,ta qarasa inda yake tana tambayar yaushe ya shigo
"Tun dazu inna,har na shirya zan sake fita ma,nasan aiki kike shi yasa nace a barki" tana daga kan kujerar amma kunnenta na wajen,fiye da rabin hankalinta yana kan hirarsu,tunda ya shigo din hankalinta ya gaza kwanciya,shigar da yayi ta tabbatar mata fita zaiyi,abun tambayar shine ina zashi da yammacin nan lis?.
"Don Allah inna idan sadiqu ya shigo kice ya jirani,na kira wayarsa ban sameshi ba"
"To shikenan,a dawo lafiya"
"Ya ameen a dawo lafiya" mufida itama ta fada,dole itama tabi sahu,ya amsa ba tare daya duba sashenta ba ya fita.
Kamar ya fita da dukkan wata walwala tata da kuzari,sai taji duk zaman parlor din bai mata dadi,wayarta na a hannunta tana chart,saidai kuma a hankali ta daina fahimtar abunda take dubawa cikin wayar
"Na zuba mana abinci yaa iman?" Mufida ta tambayeta,sai ta kashe datar tana kallonta
"Banajin yunwa yanzu kam,ci abincinki,sai zuw anjima" tayi maganar tana zamewa saman doguwar kujerar falon,bayan ta saka mufida ta miqo mata remote ta canza tasha.
Duk da kallon da take yadan dauki hankalinta,saidai hakan bai hanata duba agogo ba duk bayan wasu mintuna,suna nan zaune a parlor har sanda malam ya shigo inna tayi wajensa,falo ya zama daga ita sai mufida,da yake yarinyar mayyar kallo ce,takwas tara goma duka tayi a idanunta,babu alamun shigowar ameen din,a hankali ta dinga jin zuciyarta tana takurewa waje guda,wani abu ya tsaya mata a wuya,a hankali zuciyarta ta fara yi mata zafi,saita lumshe idanunta kawai tana sauraren bugun zuciyarta.
Sallamarsa ce ta ratsa tsakar gidan har zuwa parlour din,saita maida idanunta ta lumshe,tana jiyoshi lokacin da yake shaidawa inna ya dawo,sai kuma muryarsa cikin taushi yake kiran mufida wadda ta fara gyangyadi,bata da dogon bacci,hakan ya sanya yana kiranta ta miqe ta fita waje,saita buda idanunta tabi mufida da kallo har zuwa sanda yarinyar ta dawo parlorn.
Dauke take da wata baqar leda mai adon zaiba,bakinta har kunne ta fara magana
"Ya iman,tashi ki gani" qarasowa tayi gaban iman din ta tsugunna ita da ledar tana qoqarin ciro kayan ciki
"Ya ameen ne ya bani,zance yaje yau,yacema tace tana gaisheni" tabbas inda mufida tasan yanayin da zata shiga da ba zata bata wannan labarin ba,gaba daya tun daga cikin kwanyarta zuwa tafin qafarta kamar an xuba mata kiyashi haka ta dinga jin wani abu,kamar ana yamutsa kwanyarta,tana daga kwancen ta kasa amsawa mufida kamar yadda ta kasa tashi,da idanu tabi kayan da yarinyar ke fitowa dasu da idanu,pepper chicken ne sai meat pie da samosa,sam bata fahimtar abunda mufida ke fadi,taga dai tana miqo mata kayan bayan ta kaiwa inna ta dawo,abu daya ta iya shine girgiza mata kai,sannan ta kira sunan Allah can qasa ta yunqura ta sauke qafafuwanta qasa,ta fara takawa a hankali zuwa dakinta,saidai tana jin kamar qafafuwanta ba qasa suke takawa ba,kamar gangar jikinta ba zata iya kaita daki ba.
Tana shiga ta murzawa dakin nata key,ta kuma sulale a qasa a hankali ta saki wani kuka mara sauti,saidai mai cin zuciya da kuma gangar jiki gaba daya,don gaba daya ta cure waje daya,jikinta kuma ya kama rawa,sanyi take ya lullubeta,saita sake qanqame waje daya,ta tura kanta tsakanin cinyoyinta.
Wani irin zafi zuciyarta keyi,wanda ya sanya hatta da hawayen dake fita a fuskarta masu zafi ne,indai har da gaske mufida take,indai har ameen ya fara zuwa zance,hakan na nufin ya fara son wata?,hakan yana nufin zuciyarsa ta fara qaunar wata ba ita ba?.
Ya ilahi zata iya jurewa?,zuciyarta zata iya dauka?,bata da tabbas.....bata da tabbacin hakan,amma ta sani cewa gagarumar matsala da damuwa ke fuskantota,ta yaya zata tunkari ameen da batun soyayyarsa?,ta yaya zata bayyana masa abunda take ji a zuciyarta,ta yaya zata gaya masa tun da can da yanzu shine dai cikin zuciyarta?,shine ya mamaye dukkan wani sashe na zuciyarta da kuma rayuwarta?,saita xame a wajen ta kwanta gaba daya saboda yadda kanta yake sara mata,bata damu da sanyin da yake busowa ta wajen ba.
Sau biyu mufida tana knocking qofar amma saidai tayi mata gyaran murya,daga bisani data gaji bata qara bugawar ba.
Tayi kuka a ranar iya son ranta,kukan da sai daya sanya taji kanta kamar an saqala mata dutse saboda nauyin da yayi mata,batasan yawan lokacin data dauka kwance a wajen ba,illa dai daga bisani taja jikinta zuwa saman gadonta ta kwanta da qyar,jikinta saboda zafi kamar ana hura wuta,a zahiri kuma wani irin sanyi takeji sosai a jikinta.
Tayi sa'a sallar asuba bata kubce mata ba,saidai tana rawar dari tayi alwalar tazo ta tada sallar,bayan ta idar saita bude key din data sakawa dakin,ta dawo ta kwanta tana sake curewa sosai,saboda azabar zazzabi da sanyin dake ratsa mata qasusuwa,ta lumshe idanunta,har yanzu tana jin qunci da zafi da zuciyarta take mata.
K'arfe bakwai mufida ta shigo dakin
"Yaa iman....ya iman" baccin wahalar daya fara daukarta ya katse,sai ta bude idanunta a hankali tana duban yarinyar
"Ki fito,kizo kiga motar da ya lamin ya siyo,haddadiya,yanzu yaje ya daukota,kinga yadda tayi kyau kuwa?" Taci gaba da bata labari,ba tare data lura da yadda idanunta suka sauya ba
"Ki taso ki gani inji inna"
"Bazan iya tashi ba mufida" cak ta tsaya tana kallonta sosai,ta matsa kusa da ita
"Jikinki hucin zazzabi yakeyi yaa iman,dama baki da lafiya?,sannu......bari.naje na gayawa innar" mufidan ta fada fuskarta cike fal da damuwa,sai ta juya da hanzari ta fice daga dakin.
A 'yar qaramar farfajiyar gidan motar ke fake,inna sadiqu da kuma lamin din kansa suna tsaye jikin motar,sadiqu na qoqarin budewa ya shiga ya kunnata,saboda yace yanason yaji ya kafiyar engine dinta yake kamar yadda aka tabbatarwa da lamin din,motace da bata cika girma ba,amma sai azabar kyau da daukar ido,ta tsaru sosai,duk wanda ya kalleta sai ta bashi sha'awa.
"Inna....inna" mufida ta fara kiranta kafin qaraso,dukka sai suka waiwayo
"Inna wallahi bata da lafiya,bakiji zafi a jikinta ba" sake murfin motar lamin yayi ya maida hankalinsa ga mufida dake bayani,sadiqu kuwa tuni ya shige cikin motar yana qoqarin kunnata.
"Dama bata da lafiya amma ta shige daka ta kwanta,a gidan nan dama ita da aminu ke wannan shashancin banzan......,kice mata ta fito taci abinci ta samu magani tasha" amsawa mufida tayi ta koma ciki,babu jimawa ta dawo
"Inna ta kasa tasowa fa" yarinyar ta fada fuskarta cike fal da damuwa
"Ko zaki duba ki gani inna,ciwo baya yiwa iman ta dadi tun ba yau ba" lamin ya fada,fuskarsa na nuna alamun kulawa
"Zan iya dagata ne,idan ka bibiya langwai ne fa kawai irin nata" ya sani sarai kara kawai inna keyi,don haka saiya qwanqwasa baqin glass din motar,sadiqu ya sauke.
Yana qoqarin gaya masa engine me kyaune sosai ya rigashi yana cewa
"Ka shiga ciki ka duba iman mana"
"Me ya sameta kuma?" Ya tambaya yana dan yamutsa fuska
"Kamar zazzabine haka mufida tace"
"Master qyaleta,tasowarma ba zatayi ba sai an dubota?,ita har yanzu kallon yarinya takewa kanta" qas yayi da muryarsa yadda inna baza ji ba
"Ni kakeso naje na fiddota?,me hakane sadiqu?" Fuskarsa ya kalla saiya sheqe da dariya,ya kunce seat belt din daya daura ya fara qoqarin fitowa yana cewa
"Inason wannan mood din naka,idan ka zama serious ko?,u are looking wani boss....banda ni dinma nine tsoro zaka dinga bani kenan ko?" Murmusawa yayi kawai da salon murmushinsa mara zurfi,ya ciro kansa yana amsa mishi
"Kai dinne wani lokaci kamar na makeka,bakasan me ya dace ba kwata kwata?" Shidai ciki yayi yana cewa
"Sai kayita yi kuma,da wasu shanyayyun idanunka a wajen" murmushi ya bishi dashi,hakan daya fada sai ya tuna masa da quruciyarsu,sanda yake tsokanar iman dame idanun mage,idan shi din ya shigar mata kuma,shima ya karbi rabonsa dame shanyayyun idanuwa.
Minti kusan goma ya bayar da rata saboda ya basu daman yin duk abinda zasuyin,sai ya fara takawa zuwa cikin parlour din,jikinsa sanye da baqar jallabiyya me sulbi,ya boye hannayensa cikin aljihunta.
Saman daya daga cikin kujerun parlour din take zaune,ta dafe kanta da tafin hannunta daya,wandata dogare hannun nata da gwiwar hannunta a hannun kujerar da take kai,dan kwalinta me sulbi daya janye baya saboda sulbinsa da santsin gashin kanta ya bayyana gaban gashinta sosai.
Yana shiga inna na fitowa daga kitchen
"Zan kintsa dakin malam,idan ruwan yayi dumi ki gwadawa mufida ta sauke miki,ki samu kisha kiyi wanka ko zakiji qwarin jikinki,amma da wayonki kina zaune da ciwo,ko kamar mufida yanzu ba zata zauna ba" ta juya ta fice tana qananun mita.
Tabbas taji shigowarsa da tsaiwarsa a wajen,koda bataji ba qamshinsa data riga ta haddaceshi ya riga ya gama gaya mata wanzuwarsa a wajen,amma tana sane taqi waiwayowa,bataso ta juyo ta kalli idanun nan masa masu wani irin qarfi da kuma tasiri a tattare da ita,batason ta juya su hada idanu har yaga raunin da ya mamayeta.
Tana jinsa sanda ya tako zuwa side din da take,sai ta zabi sauke qwayoyin idaunta zuwa qasa,har zuwa sanda ya samu mazauni dab da qofarsu ta kitchen,ya zauna hannun kujera
"Ina kwana" ta gaidashi da dasashshiyar muryarta
"Lafiya ya jikin?"
"Da sauqi"
"Ma sha Allah" ya amsa yana janye idanunsa daga kanta bayan ya mata duba guda daya,koda batace komai ba...ko bai kalleta sosai ba ya san jiya zuwa yau din da gaske taji jiki,cikin gidam yafi kowa iya karantar ciwonta.
Waiwayawa yayi inda mufida ke zaune yace ta duba ruwan yayi zafi,ba jimawa ta dawo ta amsa masa,sai ya miqe da kansa ya shiga kitchen din.
Farin ruwa inna ta dora,ya laluba da kansa ya nemo kayan qamshi ya watsa a ciki,ya bari ya tafasa sannan ya hada tea din ya bawa mufida takai mata,shi kuma ya dora wani ruwan ya tafasa farin ruwa yadda ya saba,ya juyeshi a mug,ya fito dashi a hannunsa yana jiran ya huce zuwa matakin dumi yasha yadda ya saba.
Idanunta a lumshe take kurban tea din,zafinsa na ratsawa sassan cikinta,kamar wadda ke shan magani haka take jinsa,batason yiwa inna musu ne kawai,ya qarasa ya rage fankar parlor din,dai dai sanda wayarsa ta fara fitar da wani daddan busar sarewa.
Hannunsa ya sanya a aljihun gaban rigarsa ya zaro wayar
"Morning.....how was your night?" Abunda ya fadi kenan,sai yayi shuru yana saurare. Ci gaba tayi da riqon cup din,ta kasa ci gaba da shan tea din,cikin rashin sa'a ta saci kallonsa,murmushi yake fitarwa saman fuskarsa,koda batasan wanda ya kirashi ba tayi hasashen hakan,saita sauke kanta,ciwon kan nata yana sake qaruwa
"Ba wani labari.....gaskiya zaiyi wuya,autarmu ce babu lafiya" batasan me akace masa ba taji dai yace
"Ok....bye" ya katse wayar ya saka a aljihu,shuru ya kuma ratsa wajen,ya maida hankalinsa ga ruwansa hankali kwance yan auna zafinsa,jin bai huce ba har yanzu,saiya fara yin hanyar barin parlor din
"Kiyi qoqari ki shirya muje kiga likita,ba'a zama da ciwo haka nan,Allah ya sawwaqe" bin bayansa tayi da kallo ba tare data shirya ba,hawaye na tara kansu zasu biyo kuncinta,yaushe ta fara wannan dakon?,yaushe kuma zata saukeshi?,wanne irin qoshin wahala ne ya sameta haka?,sai tayi hanzarin dire cup din,ta kuma miqe da hanzari zuwa dakinta duk da yadda kanta yake sara mata,don batason tun a nan wajen hawayen su fidda kansu.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 45
Duk yadda taso kaucewa tafiya asibin tare dashi bata yiwu ba,saboda bata da wata hujja da zata bayar na aiwatar da hakan,tafuyarsun tare tasan babu abinda zata haifar mata illa fama mata wani tabo da miki dake tsaka da ciwo da kuɗa,yake kuma jan ruwa mai zugi cikin tsokokin zuciyarta,haka nan ta shiga tayi wanka,ta shirya kanta cikin doguwa riga saqar k'asar turkey,wadda take a bude sosai me hannun roba,two colors brown da baqa,tayi mata kyau sosai,duk da yadda fuskarta ke cikin yanayi,a haka idan ka kalla zaka zaci straight skart ce daga qasa sama kuma ta dora baqar half gown,da mayafin rigar ta yane kanta ba tare data tsaya rolling ba,ta saka wani black plate half cover shoe,wayarta kawai ta fito.
A parlor ta yiwa inna sallama ta fice,tun daga qofar falon ta hangi mufida,ta shirya tsaf abunta,anata murna zaa fita da ita.
Ta maida idanunta kansa,duk da bayansa kawai take iya hangowa amma sai daya haifar mata da faduwar gaba,shaddace a jikinsa me tsada ko a idanu,amma an mata dinki yarbawa,iya gwiwa mai gajeran hannu da manyan aljihu hagu da dama,sai dogon wando,shima half cover ya saka irin na maza mai asalin kyau da tsadan,daga nesa kadai kana iya gane tsaftarshi qwarai bare ka matso kusa dashi kayi arangama da sassanyan qamshinsa,ganin yana qoqarin juyowa sai ta dauke kanta zuwa wani sashen daban....kafin ta qaraso har ya bude qofofin motar,da kansa ya budewa mufida front seat yana tsokanarta,tana murna kuwa ta shige,ya maida ya rufe ya zagaya nashi seat din ya shiga,daidai sanda iman din itama ta shiga baya.
Bismillah yayi ya tada motar,yayi reverse sannan ya daidaitata cikin layin suka dauki hanya.
Hirarsu suke shida mufida abinsu,kamar ma babu wani cikin motar sai su,kanta yana jingine da murfin motar,idanuwanta a lumshe,duk wata kalma ko harafi da zai futa daga bakinsa tana saurare,duk wata magana da zaiyi mai ma'ana ce,wadda ke nuna zallar hankali tare da nutsuwar wanda furucin ke fita daga bakinsa,da alama ita kanta yarinyar tana ji dashi sosai,tana kuma jin dadin hirar tasu,cikin excitement take bashi amsa,duk da ba cikin lafiyarta take ba,amma jirar tasu saita dinga burgeta.
"Akwai asibitin da kike zuwa inji inna,meye address din?" Ya fada yana karkata akalar motar tashi zuwa babban titi,ta cira kai a hankali,tana mamakin yadda ya iya tuqi haka cikin nutsuwa da qwarewa,ta dade da saninsa,shi ba mutum bane me karban aron abun hannun abokai,tun a wancan lokacin akwai abokansu da yawa dake da mota,babu yadda basuyi dashi yazo ya koya ba ko ya dinga aran tasu amma yace sam,zaman wajen dinkinsa yafi masa wannan yawace yawacen.
Hakan kawai taji batason kaishi asibitin,amma tunda ya riga da yasan nan din take zuwa ba yadda zatayi,a hankalibta fada masa sunan asibitin,tayi zaton zai tambayi hanya sai taga yaci gaba da hirarshi,tafi tafi sai gasu a asibitin.
Cikin nutsuwa yayi parking,ya kashe motar yana fadin
"Alhamdilillah" ya zare belt dinsa ya fita ya budewa mufida qofa.
Tabbas son yara cikin jininsa yake,had yanzu kuma bai barshi ba,daga yadda yakewa mufidan zaka gane hakan,ta tabbatar matsayinta mufidan ke shirin hawa,gurbinta take nema mayewa,ta kalli yadda yake riqe da hannun yarinyar,sai taji wani abu ya taba ranta,dab da zasu qarasa entrance na asibitin ta danyi kiranta,bai juyo ba amma ya zame hannunsa daga nata,sai yarinyar ta tsaya shi kuma yayi gaba,ta qarasa ta kama hannunta,sannu tayi mata,ta dauka ko tafiyar ce bata yi mata dadi shi yasa ta kirata ta tsayata.
Tafiyar tasu ba daya bace koda lafiya take bare yanzu da bata jin dadi,don haka kafin ta qarasa har an fidda file dinsu yana biyan consultation fee
"Hajiya iman....wani aure kika qara ne?,gaskiya kina da sa'a,duk mazanki babu na yarwa,harma wannan yafi wancan kyau ma sha Allah,duk da kema ba baya bace,shi yasa kike samo irinsu" wata nurse halima ta fada,irin matan nan ne masu barkwanci da kuma shegen surutu,kafin iman din tace wani abu ta sake duban alameen
"Yallabai inafa tayaka murna,ka dace da mace gaskiya" ta gefan ido take satar kallonshi tana son taga ya yanayinsa yake,saidai bata gane komai ba,hasalima sabgarshi yake da wayarsa kamar ma bay wajen
"Wata nawa ne cikin?za'a saka jikin record din kadin nayi miki bp da kuma weight dinta yallabai" sai a sannan ya daga kai ya dubu nurse din,tun asali bayason mace me yawan surutu shi kam,ko don ba kowanne lokaci ba kuma da kowa magana ta cika damunsa ba,ya tabbatar da sadiqu ta samu saidai ya matsa ya basu waje
"Sorry madam,ba matata bace,ba awo tazo ba,just tazo ganin likitanta ne"
"Ayyah sorry,kuyi haquri,dr ahmad ne,yana ciki ma,amma akwai mutum kusan shida a gabanku,idan sun fito sai ku shiga" bai bi ta kanta ba ya fito da kudin ya ajjiye mata a gabanta,ta dauke ta fara rubuta musi receipt ta saka a file din nasu.
Mabanbantan wurare suka zauna suna ci gaba da hirarsu da mufida,har zuwa sanda layin yazo kansu.
Shine a gaba suna bayansa,da sallama ya shiga,dr ahmad na rubuce rubuce kan wani file ya daga kai yana amsawa,har zai maida kansa ya hangi shigowar iman din,hakan yasa ya ajjiye biron da yake rubutu dashi,murmushi kwance saman fuskarsa ya miqe tsaye,hakan ya sanya alameen waiwayawa ya dubi iman din.
"Bismillah,ga wajeku zauna"yayi musu izinin zama bayan sunyi musabaha da ameen,mufida ma ta gaidashi,ya amsa mata cikin sakin fuska.
"Yaya?,jikin ne?" Dr ahmad ya tambayeta cike da kulawa,ya tattara dukka hankalinsa da nutsuwarsa a kanta,kai ta gyada a hankali saboda jin da take kamar zai cire
"Subhanallah" ya fada adan rikice
"Jikina ya bani dama,tunda nayita kira jiya babu amsa,haka tex ma......garin yaya haka ta faru hajiya?" Ya sake tambaya fuskarsa a narke cikin matuqar kulawa,abunda ya sanyata jin wani iri,ta daga idonta a hankali zata saci kallon alameen dake tsaye,hannayensa duka zube cikin aljihun rigarsa,tunda suka shigo dama bai zauna ba,yana jingine da bangon office din,yayi crossing legs dinsa.
Taci sa'a tsimammun idanuwansa suna kanta shima,suka hada idanu,sai ya miqe ya tsaya sosai bisa qafafunsa yana cire hannayensa daga aljihu ya maidasu qirjinsa ya harde,cikin wata qasaita yayi magana
"Eheenn....ki bude baki ki masa bayani,ko kuma na baku space,tunda akwai sirri tsakanin likita sa patient ko?" Ya fada a hankali yana raba bayansa da bangon,sannan ya fara takawa,murmushi dr ahmad ya saki
"Kawai dai naga alama tana tsoron yayan nan namu,but she can explain ai ko a gabanka dinne"
"Kada ka damu abokina.....idan kun gama ina waje" yayi maganar yana sake bashi hannu,sannan ya nufi qofa,mufida ta tashi ta biyo bayansa,sai ya dakata yace da ita
"No,ki xauna ku fito tare"
"To" ta amsa masa tana komawa ta zauna.
Wani abu mai tauri ne ys tsaya mata a wuya,kunnuwanta na jin takun fitarsa daga office din,wato ko oho?,bai damu da ita ba?,baya kishinta kenan,har zai iya fita ya barta da dr ahmad din,bayan ta tabbatar da duk wanda yaga reaction na dr ahmad zai gane cewa akwai wani manufa mai qarfi a zuciyarshi dangane da ita?.da gaske babu komai a zuciyar ameen a kanta ko kuwa me?,yana son tabbatar mata ta fita daga kansa?.
A dabarance ta janye idanunta tare sa sauke ajiyar zuciya,ta maida ga dr ahmad daya taso daga seat dinsa,ya dawo kujerar dake opposite dinta,bayan ya turata baya kadan,cikin sanyin murya yake mata magana
"Meye damuwar?,can you share it with me?" Yayi tambayar yana kallonta,sanya nata idanun tayi itama cikin nasa,tana karantar damuwa da yayi qarara da lamarinta,sabanin alameen din,da bata tsinci kowanne sauyin yanayi dangane dashi ba,illa dai zallar nuna tausayi,wanda dama ko ba'a kanta kadai ba,shi mutum ne mai tausayi,musamman ga na qasa dashi
"Banaso ki koma yanayin da kika baro a baya,ina fargaban komawar taki,saboda babu lallai abun yazo da kyau,kada ki sanyani yin asarar da ban shiryata ba" idanunta ta dauke daga kansa,tana jan numfashi tare da sauke ajiyar zuciya,ta maida bayanta jikin kujera ba tare datace komai ba.
Wayar land line dame office din ya janyo,nurse ya kira kamar yadda ta saba don tayi mata awon BP,ya maida wayar ya ajjiye yana tattara nutsuwarshi a kanta.
Tunda suna doso wajen hankalinta ya dauko ga ameen,hannunsa riqe da wata leda mai dauke fried plaintain,guda daa kuma yana hannun mufida tana ci,zuna zaune daga saman motar tashi,da alama labari take bashi kamar yadda ta saba,fuskarsa na fidda wani qaramin murmushi,yayin da yake dan cilla qafarsa kadan.
Yanayin yadda yayi fresh da kuma yadda motar ta dace dashi dole ya dauki hankalin kowacce mace,komai isa kyau da kuma taqamarta,don babu abinda baya dashi wanda zaija hankalin,kwarji na musamman yake dashi,ita kanta tana mamaki wani lokaci, totally ba lameen din shekarun baya bane wannan,wani rauni taji yana cika zuciyarta,tana ji a jikinta alamun faduwarta kan samun soyayyarsa da rashin nasara dake tunkarota.
A hankali ya sauka daga saman motar,ya ajjiye abunda ke hannunsa,fuskarsa a sake ya miqawa dr ahmad hannu suka sake musabaha
"Kun gama dr"
"Mun gama yayanmu.....Allah yasa na canki dai dai" murmushi kawai yayi masa ba tare daya amsa ba
"Don Allah ayimin alfarma a kulamin da ita,akwai damuwa cikin ranta dakeson tada ciwonta" sauke idanunsa yayi akan iman din dake gefe guda,sai ya ciro key din motar daga aljihunsa yana dauke idanunsa daga kanta,sannan ya dannan ya bude musu motar yana cewa
"Ku shiga ciki ku jirani". Sai daya tabbatar sun shiga sannan ya maida hankalinsa ga dr ahmad
"Thank you Dr,amma kuma...wanne damuwa ne haka?"
"I tried to get the information daga gareta amma bata gayamin komai ba,please....kune kuke da kusanci sosai da ita,kuyi qoqari wajen relieving mata damuwarta"
"Ok" ya amsa masa a taqaice
"Can i say goodbye to her?" Ya tambayi alameen,sai ya daga kafadunshi yana takawa zuwa gaba
"Why not?"
"Na gode" ya fada shima yana biyo bayansa.
Tana jinsa ya buda motar ya shiga,saidai bata dago kanta ba,idanunta naga yatsun hannunta tana murxasu a hankali,sosai qirjinta yake mata zafi,kalmar
"Hajjaju" ta shiga kunnenta saitin window din da take zaune,ta daga kai ta kalli dr ahmad dake mata murmushi,a hankali kuma ta saci duban alameen,sai taga wayarsa ma yake qoqarin sakawa a charge
"Allah ya bada lafiya,an hanani address bare nazo nayi dubiya ko?" Murmushi ta fitar na yaqe,wanda bahaushe yace yafi kuka ciwo
"Shikenan,hope to visit you soon,sai munyi waya.....,yallabai.....godiya nake" ya fadawa alameen
"Don't mention it" ya amsa masa,sai ya kunna motar abunda yasa dr ahmad ja baya kenan yana kallonsu har suka fice a asibitin.
Ajiyar zuciya ya sauke yana komawa ciki,har ga Allah yana bala'in son iman din,tun farkon zuwanta asibitin,a sannan ma bai gane matar aure bace sai daga baya da matsaloli sukayita kunno kai,yasan wala'alla wahalar data sha a aurenta na baya yasa ta kasa sake masa,amma yasan a hankali in sha Allah komai zai kawo qarshe,zai kuma shawo kanta.
Ta tafas batace ba tunda suka shiga motat,hirarsu suke shida mufidan kamar dai dazu,hawayenta taketa riqewa,bataso su zuba ya gani,ita kadai tasan ciwon da qirjinta yake mata,wanne irin cin fuska ne ya lamin din yayi mata haka?,ko yaya?....sam babu wani digo na kishinta ko kuma soyayyarta akan fuska da ayyukansa?.
Sai daya tsaya a hanya a wani guri ya siya fruits masu yawa,bayan ya tambayi mufida dame dame sukafi so sannan suka wuce gida,a 'yar harabar gidan dake dauke motar tasa yayi parking,mufida ta fara ficewa da ledojin,rashin qwarin jikinta yasa take komai slowly,ta buda murfin motar zata fita taji yace
"Wait" saita dakata din kamar yadda yace,hannunsa ya sanya a hankali ya saita mudubin gaban motar zuwa saitin fuskarta,ta daga idanunta a hankali tana kallon wajen,saiga fuskarsa tarwa,tsimammun idanunsa a kanta masu nauyi da kwarjini.
Ita ta fara janye idanun nata kamar kowanne lokaci,kafin daga bisani muryarsa ta ratso kunnenta
"Wacce damuwa ce a ranki haka?" Yayi tambayar a dake,cikin ginshirar nan tasa,koda bata kalleshi ba tasan fuskarsa babu alamar wasa,to amma a nata ganin bai kamata yayi mata wannan tambayar ba,tayi imani cewa yafi kowa sanin amsar tambayarsa,koda bata buda baki tayi masa bayanin komai ba,hakan da yake mata kamae titsiye ne.
Bata amsa ba,kuma bata da niyyar cewa komai,shi kuma bai fasa kallonta ta cikin mudubin ba,hakanan ta dunga jin idanunsa na yawo cikin jikinta kota ina,tsahon wasu mintuna kafin ta sake ji yake
"Alright.....shikenan,abu daya zance miki.....lafiya abace mai daraja,saiki kula,zaki iya tafiya" daga haka ya soma cire belt din dake jikinsa,ta saka hannunta a sanyaye ta bude motar ta fito,tana tafiya kamar iska na yawo da ita haka takejin jikinta,zuciyarta a quntace waje guda,kwanyarta cunkushe,a hankali kamar ba zata qarasa ba ta cusa jikinta zuwa parlor dinsu.
*FOLLOW ME ON AREWABOOKS DOMIN SAMUN CI GABA,SABBBABIN PAGES GALLA GALLA*
*_KUFAN WUTA_*
*SABABBIN PAGES DA DUMINSU SUN SAUKA*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾
https://arewabooks.com/chapter?id=62bc3f8a7660dfc79da17d20
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62bc3f8a7660dfc79da17d20
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_YADDA ZAKA SIYA LITTAFI A AREWABOOKS_*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾
*Recharge* - inda ake shiga domin saka kudi cikin account.
*Balance* - Zai nuna kudin account dinku da zaku iya sayayyan littafai cikin kasuwar ArewaBooks.
*Credit/Debit Card* - Hanyar farko kuma mai dadi wajan Recharge din account dinku.
A inda (Enter your amount) za'a saka kudin da akeson Recharge din sai a taba "Proceed". Zaibude muku inda zaku saka bayanan katin banki, kuna gamawa kudinku zaishiga account dinku kaitsaye (instant).
--------
Akwai wasu hanyoyin saka kudi a ArewaBooks account kamar:
*Bank Transfer*
*Airtime Transfer*
Saidai su ba kaitsaye bane (instantly) sai ArewaBooks ta tabbatar da Transfer din, amman bayakai 1hour za'a gansa a Balance.
*Bank Transfer* - kamar yadda akwai bayani a sama da kuma account number ArewaBooks.
_Account No_ - *1220077999*
_Account Name_ - *Arewa Books Publishers*
_Bank_ - *Zenith Bank*
Bayan anyi Transfer dinne sai a cike wannan Form din:
Amount Paid: - Nawa aka tura?
Name used for transfer: - sunan da aka saka wajan turowa
Transferred time: - lokacin da aka turo
Name of bank: - sunan bankin da aka turo dashi
Deposit date: - ranar da aka turo
Sai ayi SUBMIT.
*Airtime Transfer* - muna bada shawaran ayi amfani da *Debit Card* kokuma *Bank Transfer* akan *Airtime Transfer* , amma idan yakama babu mafita saishi tau muna amsar:
MTN,
9Mobile
Glo
Airtel
Amma kamar yadda akayi rubutu a sama afara tuntubar ArewaBooks a WhatsApp domin akwai percent da ake cirewa na canji(convert) kafin kudinka yashiga Balance.
*WANNAN SHINE BAYANAN*[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 46
Sanarwa da inna kawai tayi ta dawo ta wuce daki,ta zube saman katifa tana maida numfashi,kwanyarta na tariyo mata duk abunda suka faru,tana shakka zuciyarta kuma nason tabbatar mata,ta juya ta gyara kwanciyarta tare da runtse idanunta,tana son ta mance da komai ko zata samu sauqin azabar da takeji tun daga gangar jikinta zuwa zuciyarta,saidai bayan kowacce daqiqa tunanin ameen ne a rai da zuciyarta,azabar da takeji kuma tana sake qaruwa,bata samu sassauci ba.
Fruit da magungunan da mufida ta ajjiye mata tace ya ameen ne yace ta tabbatar tasha ta bisu da kallo,me yasa yake bata fake caring?,me yasa yaketa pretending?,bayan tasan ba haka bane?,a yanzu ba wadan nan abebadan take buqata ba,koda taci ko tasha tasan babu wani magani da zasu iya yi mata,zuciyarta shi takeso,shi take da buqata,shine magani kuma abincinta,amma me yasa yaketa avoiding dinta?,yanata nuna bai gane komai?,yanata nuna a yanzun yaren dake kan fuskarta bashi yake ganewa ba?, pillow ta jawo ta cusa kanta a qasa gami da qanqameshi tana fatan Allah ya kawo mata barci ko zata samu sassauci.
Addu'arta kuwa taci,dogon barcin daya dauketa har gefin magariba sannan ta farka,ta ambaci sunan Allah da sauri ta shiga bandaki,ta daura alwala ta dawo ta fara bada bashin sallolin dake kanta,bata tashi ba sai datayi sallar magariba.
Tadan samu relief kadan,ta jawo ledar magungunanta ta dubasu,saita fara shirin miqewa,dai dai lokacin mufida ta shigo
"Yauwa,ashe kin tashi ma,bari na gayawa innan"
"Tsaya mu fita tare" ta fada tans miqewa tare da tambayarta
"Ba kowane a gidan?" Dan dubanta tayi cikin rashin gane ma'anar tambayar tata,amma duk da haka tayi qoqarin amsa mata
"Yaa sadiqu ya tafi zance..." Gabanta ya doka,tana fargabar jin amsa ta gaba
"Ya alameen kuma tunda suka fita unguwa da malam basu dawo ba" saita jinjina kai,tayi gaba mufida ta biyo bayanta.
A parlor ta cimma inna,tana zaune tana gyara saitin stations na radio dinta,akwai tv,amma sam bata wani damu inna ba,idan sun kunna takan kalla,amma idan basu kunna ba saita wuni a kashe ba tare data kunna ba.
Daga kai tayi tana yiwa iman din sannu,ta amsa tana zama saman kujera
"Kinsha magungunan naki?"
"Yanzu dai zansha" ta amsa mata,sannan tace mufida ta samo mata abincin dan kadan a kitchen.
Tana tsaka daci taji sallamar malam,already mufida ta gaya mata tare suke dashi,hakan na nuna sun dawo kenan,sai ta ajjiye farantin gefe saboda yadda taji abincin ya tsaya mata.
Ballar maganin tayi ta riqe cikin tafin hannunta,ruwan na riqe a cup amma tana wassafa yadda zata tanqwara kanta tasha maganin,saboda tun asali bata qaunar magani,sai an sha fama da ita takesha.
Shigowar malam ta sakata ajjiye cup din,taci gaba da riqon maganin a hannunta tana masa sannu da zuwa,sai idanunta yakai kan wanda yake bayansa,ameen ne tsaye sarqafe da hannayensa a qirji,hada ido sukayi,saiya dauke kansa kanshi tsaye bayan ya kalli hannun ta,koda ba'a gaya masa ba yasan yadda zatasha maganin take taraddadi,ya juya a nutse ya fice daga parlor din,yana amsa wayarsa da aka kirashi sanda ya juya din.
Miqewa tayi itama ta koma daki ta barwa inna da malam parlor din,duk da cewa malam din yana da tashi rumfar,amma qila a nan yayi sha'awar zama.
Ko data koma ciki ta taras da miscal din dr ahmad masu yawa,daga bisani kuma taga tex dinshi,duka yana mata sannu da jiki ne,tare da bata qwarin gwiwar kauda damuwa daga ranta,aje wayar kawai tai bayan ta gama karantawa,indai sai damuwa ta fita daga ranta,to tabbas bata da guarantee din ranar warkewa.
Washegari ma haka nan ta wuni,jikin da sauqi,amma babu wani kuzari sam tattare da ita,a dakinta tayi kwanciyarta,bata yarda ko sau daya ta fito sun hadu dashi ba,saidai duka taji muryarsa sanda zai fita,ta lumshe ido wani abu na tsarga mata sanda taji ya ambaci sunanta yana tambayarta,har zuwa amsar da mufida ta bashi,hakanan sanda ya dawo ma taji shigowarsa,hatta da zaman cin abinci da sukayi a parlor shi da sadiq,da fitarsa daga parlor din sanda wayarsa ta dauki ruri,sai zuciyarta ta cilla ta bishi bayan fitar tasa,tana ji a jikinsa da wata zaiyi waya.
Kasa nutsuwa zuciyarta tayi,daga qarshe ta dauko headphone dinta tayi connecting da wayarta,ta kunna suratul baqra cikin qira'ar sheik khalilul kusari,ta rage volume dai dai yadda bazai dameta ba,wannan ya taimaka matuqa wajen janye hankalinta,har ta samu barci ya fara fusgarta.
*****A kwana na biyu ne taji qwarin jikinta,ranar ta wuni a kwance,ta samu barci kuwa sosai yadda ya kamata,hakan ya sanya koda ta tashi fresh ta jita,ta fito parlor tana laluben inna,sai a sannan mufida ta gaya mata ta tafi karben lefen 'yar gidan kawu muktar,ta jinjina kai tana mamakin baccin da tasha,saita koma daki ta cire kayanta ta fada wanka.
Tsaye tayi gaban mudubi daure da towel tana kallon fuskarta,ta fada tayi fayau da ita,sai haske data qara,blue eyes dinta sunyi tas dasu,manta ta jawo ta fara qoqarin shafawa mufida ta shigo
"Ya iman kinyi baquwa"
"Baquwa kuma?" Ta tambaya cikin mamaki
"Eh" shuru ta danyi sannan tace
"Baki santa ba?" Kai ta girgiza
"Ban santa ba,amma dai 'yar gayu kamarki" murmushi iman din tayi,har fararen haqoranta suna fitowa
"Ke kam akwai ki da son gayu mufida,jeki kice mata ina zuwa" ta amsa da to ta juya ta fita tana dariya.
A nutse ta shirya kanta cikin wani Cotton material,ash colour ne mai zanen manyan flowers,dinkin riga da skert ne me kyau daya zauna a jikinta,comb tasa tana taje kanta mai laushi da tsaho,ta duba ma'ajiyar ribbons dinta ta saka daya ta kame gashin nata dashi,ta kalli gashin nata ta cikin madubin,sai takejin ya mata datti tana buqatar zuwa a wanke mata shi,duk da ba wani datti bane me yawa,jikinta tabi da turarenta mai taushin qamshi ta feshe,saita dauki wayarta da zummar idan ta gama da baquwar ta kunna data ta duba group na ajinsu taga me ake ciki,don kwana biyu bata hau ba,daxun kuma tana tsaka da bacci wata abokiyar karatunta da suke mutunci sosai ta kirata,ta bata haquri kan zata kira idan ta tashi.
Sanda ta qarasa parlor din idanunta na kan wayar,sai data shiga sannan ta cira kanta tana yin sallama.
Sanye cikin wani lace orange da aka yiwa dinki bunu na zamani da aka wadata da stones masu walwali,ta yane kanta da mayafi medium,wanda tadan jashi baya,daurin kanta daya fara daga gaban goshinta ya zauna das,ya kuma sake qawata kwalliyarta,matashiyar budurwa ce wankan tarwada,wadda a qalla shekarunta baxasu haura ashirin da biyu ba,tana da doguwar fuska da siraran labba,sai gashin gira wanda ya zarta gashin idanunta cika,tana da kyau irin wanda ake kira da matsakaicin kyau,a wasu guraren kuma direct za'a kirata da sunan kyakkyawa,shigarta kadai zata gaya maka a waye take,hannunta riqe yake da wayarta tana latse latse,gefanta kuma wata matashiyarce,itama cikin doguwar rigar atamfa,saidai ita din batakai wannan kyau ba,kamar yadda a ido kawai zakasan bata qarasa shekarun wancar din ba.
Idanun iman qur bisa fuskokinsu take takowa,saboda duk cikinsu babu fuskar wadda ta sani
"Sannun ku" ta fada da tattausar muryarta,zuciyarta na raya mata batan kai sukayi,ba gidan suke nema ba
"Yauwa sannu" matashiyar dake sanye da lace ta amsa murya qasa qasa,idanunta fes bisa fuskar iman wadda tuni ta qaraso wajen tana dauke idanunta daga kansu karo na barkatai da batasan adadin ba..
Cikin zuciyarta iman take mamakin kallon da baquwar ke binga dashi,mutum ce ita data tsani kallon qurilla,balle ga baqo....baqonma irin wannan da batasan daga ina take ba,kuma me take kallon oho.
A nutse ta samu one sitter ta zauna ta dauke pillow din dake kai ta maida saman cinyarta
"Sannunku ko?" Iman din ta sake maimaitawa,sai matashiyar dake gefe ta amsa wannan karon
"Ina gajiya ya gida?" Iman ta maida musu gaisuwarsu,sannan ta miqe,har yanzu dai tana mamakin su waye,daga inda kuma suke din.
A nutse ta wuce zuwa kitchen don ta gabatar musu da ruwa,kamar yadda suka saba al'adar gidan,koda basusan baqo ba,kallo suka bita dashi,kafin daga bisani su janye idanunsu kusan a tare
"Wai itace autar?" Matashiyar dake gefe ta tambayeta
"Nima dai ina doubting......banga suna kama ba,amma......bari na kirashi kawai" saita dauki wayarta data ajjiye a gefe,ta fara zuba numbers dinsa cikin wayar,wanda ta jima da haddace digits din.
Tabe baki iman tayi bayan ta gama guntun tunaninta akan su waye cikin kitchen,koma su waye kansu suke batawa lokaci idan suka gane ba gidan da suke nema sukazo ba,ta qarasa ta samu babban tray ta zuba robobin zobo mai sanyi da sukeyi suna zubawa a fridge saboda sha,ta hado musu da pure water shima mai sanyi sosai,ta dora cups ta nufo falon.
Tun kan ta qaraso ta fahimci waya take,saidai ba zaka iya jin me take fada ba,har ta qaraso din kuwa bata iyajin komai ba,saboda yadda take maganar kamar wadda ke rada
"Eh......dama mamaki na shirya baka,idan baka yarda ba ka qaraso muna cikin gidan ai" ta fada da wata iriyar murya can qas.
Qarasa dire musu plate din kawai tayi ta koma seat din data taso ta sake zama,ta fuskanci dai gidan nasu sukazo,to amma wajen wa?,for now dai ai ya kamata su fadi wa suke nema,to amma koda waye taji tana waya yana da alaqa da gidan nasu.
Sosai qirjinta ya harba sanda zuciyarta ta raya mata idan ameen ne fa?,siriryar iska mai zafi ta futar daga hunhunta wai ko zaga samu relief,iya wannan tunanin ya sanyata jade girar sama data qasa,ta tsuke fuskarta tas,tsohon tsimammen miskilancinta ya motsa,ta maida qafarta daya kan daya,sannan taja wayarta ta bude,ta fara bin charts din group din ajinsu,gefe daya zuciyarta na qwarara mata gwiwar bata da alaqa da ameen,ba yadda za'ayi tana surukar gidan ta iya tunkarar gidansu.
Parlor din ya dauki shuru,iman din ta maida hankalinta ga chart dinta,sai qarar tv dake tashi kadan kadan,sam taji baquwar batayi mata ba,ta yaya zakizo gidan mutane ki samu guri ki zauna,ki kasa fadin wacece ke?,jin kai ne ko meye?.
A karo na kusa hudu daya abokiyar tafiyan tata ta dubeta,tadan tabata kadan,kafadunta ta dage kana ta daga gira sama ta sauke,ta aje cup din ruwan data sha
"Sunana samha" a nutse iman ta daga kanta ta kalleta
"Wannan kuma qanwata ce subai'a,muna neman iman ne,qanwar alameen" a nutsen ta amsa mata,ambatar sunan al'ameen din da tayi sai da gaban iman din yayi wata mummunar faduwa.
"Gani" kallonta samhan tayi sosai sannan ta dan saki murmushi
"Ayyah,ban san fuskarki ba,shi yasa ban ganeki ba,ya jikin naki?"
"Alhamdulillah"
"To Allah ya qara sauqi"
"Ameen" ta amsa mata a taqaice ta maida kanfa ga wayarta,har yanzu qirjinta bai daina bugawa ba,wani irin fargaba ce ta dinga saukar mata tana kashe mata gabban jikinta,duk yadda samhan taso ta dinga janta da hira amma hakan ya faskara,banda ma bata da tabbacin wacece ita?,kuma wajen wa tazo.....da babu abinda zata zauna yi a parlor din.
Ganin bata samu sakewa da iman din ba yadda ya kamata saita koma hirarta da mufida,da yake mai hira ce mufidan saita sake mata suka taba hirara.
*_Assalamu alaikum,fatan kowa yana lafiya,don Allah ina neman alfarmarku,wani muhimmin abu ya tasomin cikin satin nan har zuwa satin gaba,zaku dinga ganin 1page,idan kuma na samu sarari zaku dinga ganin guda biyu har zuwa sanda uzurin nawa zai kammala,ina fatan za'ayimin afuwa,na gode_*👏🏾👏🏾👏🏾
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 47
Zaman gaba daya ha gama gundurarta cikin parlor din,sam babu wani armashi ko ma'ana,ta gama yanke iya mintocin da idan suka cika zata tashi daga zaman da sam bashi da wata fa'ida a idanunta.
Sallamarsa ce ta ratsa tsakar gidan,cikin husky voice dinsa,wadda duk sanda zata jita sai ta haifar da wani abu mai nauyi dangane dashi a gangar jiki da zuciyarta,don ko a yanzu ma lumshe idanunta tayi tana jin yadda ko wane sashe na jikinta ke amsawa,bude idanunta kuwa yayi dai dai da zare rufaffun takalmansa da yayi ya sako kai zuwa parlor din.
Tsaye yayi daga bakin qofa,hannyensa boye cikin aljihun wandon suit dinsa,idanunsa saman fuskar samha,yayin da fuskar samhan ta wadata da murmushi tana dan jan mayafinta tana rufe rabin fuskarta
"Suby'a har da ke?" Ya fada yana sakin hannayensa tare da takowa a nutse zuwa cikin parlor din,cikin murmushi suby'a din tace
"Ya zanyi mata yaya,indai batazo dubiyar nan ba babu zaman lafiya,tunda taji auta babu lafiya ta hanani sakat"
"Da kyau" ya amsa yana qoqarin maida idanunshi kan iman,wadda ta miqe zumbur kamar wadda aka tsikara,sannan ta wuce kanta tsaye zuwa kitchen ba tare data waiwayo ko kuma ta saurari kowa ba.
Da idanu ya rakata kafin ya janye dubansa daga kanta cikin mamakin reaction dinta,sauke kallonsa yayi ga samha wadda itama ta bishi da kallo,suka hada idanu
"Are you okay?" Ta tambayeshi yanayin fuskarta yana dan canzawa akan yadda ta kalleshi lokacin da ya shigo parlor din,ta hanyar dage mata girarsa ya amsa mata yana sake qarasowa don samun kujerar da zai zauna akai,mufida tayi masa sannu da zuwa,ya amsa yanabin ruwa da drinks din da aka ajjiye musu da kallo.
Bata tsaya ba sai data dangane da jikin cupboard din kitchen din,ta dafe hannuwanta dasu tana qoqarin saidaita gudun zuciyarta saboda hakin da yakeson sarqafeta,koda baice komai ba ta gama karantar komai din,samha budurwar ameen ce,ta kuma zo dubata saboda taji bata da lafiya,hakan yana nufin batasan tarihin abinda yake tsakaninsu ba,wannan shike tabbatar mata da gaske ya ameen ga wanke dukka wata tsohuwar alaqa da dangantaka data taba hadasu da gasken gaske kamar yadda ya taba furta mata.
Kokari take ta fitar da hawaye daga idanunta ko hakan zaisa ta samu sassaucin wani abu mai tauri daya tsaya mata a wuya,ta sunkuyar da kanta qasa a hankali sanda kukan ke zuwa mata,ta kuma saka hanunta guda daya ta toshe bakinta dashi don kada ta fallasa kanta,wasu hawaye masu dumi suka fada kai kawo saman fuskarta,sai taji tsaiwar na neman gagararta,ta sulale ta tsugunna sosai tana cusa kanta a tsakanin cinyoyinta,tabbas ta rasa ya ameen,ta rasashi rashi na har abada,babu abinda idanunta ke hango mata a yanzun sai fuskarsa tare data samha,daga nan inda take tana iya jin muryan samhan,duk da bata iya fahimtar me suke fada,sai tasa tafin hannuwanta ta danne kunnuwanta dasu tana runtse idanunta.
Kuka take wanda ke tafe da qunci nadama da kuma dana sani,bata taba tunani a rayuwarta zuciyarta na qaunar ya ameen ba har haka,bata taba kawowa akwai lokacin da nadama da tashin hankali kan barin ameen zasu risketa ba har irin haka,dama da gaske ne da ake cewa dama sau daya take zuwarma dan adam a rayuwa,itakam da alama ta rasa tata damar,me yasa ya ameen bazai kalli qwayoyin idanuwanta ya karanci meke cikin zuciya da ruhinta ba kamar yadda ya saba mata?,me yasa zai barta ita daya sonshi yana wajigata ta duk inda yaga dama?,idan ma horo ne ya zuwa yanzu zuciyarta ta gama horuwa,koda yadda zuciyarta ta cika fa tumbatsa da qaunarsa kawai ya barta tabbas ta karbi dukkan sakamakon daya kamata.
Batasan sanda innata shigo gidan ba,saidai kawai ta tsinci muryarta tana doso qofar kitchen din tana kiran sunanta da alama nemanta take.
Da hanzari ta miqe,ta kuma juyawa qofa baya tana fuskantar sink na kitchen din,ta kunna famfo ta tara hannayenta ta fara wanke fuskarta,dai dai sanda innar ta qaraso tana fadin
"Me kike haka a kitchen ne tun kusan rabin awa?" Rasa amsar da zata bawa inna tayi,batason ta buda baki da zummar magana innar ta gano tayi kuka,amma dole ta amsa matan indai baso take ta zagayo taha fuskarta bane
"Kokarin dora abinci nake inna"
"Bansan ma me kuka zauna yi ba har yanzu ace ba'a dora abincin dare ba,ki fara samun wani abun me sauqi ki dorawa baqin nan,nace sai sun dakata mun gaisa sosai tunda yanzun na shigo ni"
"To" din da zatace ta maqale mata,ta kasa kunne taji takun fitar innar amma bataji ba,a maimakon hakan sai taji innar tana takowa zuwa cikin kitchen din,abunda ya kidimata kenan ta fara kame kame,sam bata qaunar wani ya fahimci halin da take ciki akan ameen din,matsala ce da ita ya jawowa kanta da hannunta ita kadai,ita kadai din kuma ya cancanci tayi kuka da ita,a sanda dukka masoyanta suke jiye nata zuwan wannan rana....a sannan din ita kuma nata idanun suka rufe,bata ji bata gani,bata hango aibu dacewa ko kuma rashin dacewa.
A gabanta inna ta tsaya,ta kasa daga idanunta balle ta kalli innar tamkar wata mara gaskiya,taji lokacin da innar ta motsa bakinta da niyyar yin magana,sai kuma taji ta maida ta rufe,ta kuma ja da baya taba cewa
"Karki dauko girki mai wahala don kada su qosa da jira" daga haka ta juya a hankali ta fice daga kitchen din.
Lafiyayyar taliya tayi data wadata da kayan lambu,ta shirya komai a tsare,sannan ta kira mufida daga nan inda take din tazo ta dauka,ba tare data fito parlor din ba ta zarce da dora abincin dare na gidan gaba daya.
"Well-done" ya furta a nutse sanda mufida ta ajjiye tray din abincin a gabansa sanda yake zaune saman carpet din parlor din yana amsa wayar bashari,shugaban babban shagonsa da a yanzu yaketa qoqarin ganin ya maidashi company,parlor din babu kowa yanzun,don inna ta basu waje tunda taji iman ta gama abincin.
Da hannu yayima suby'a alama kan tayi serving nasu,tayi yadda yace din,saidai samha ta maqale kafada alamun ba zata ci ba,miqewa yayi tsaye bayan ya cire wayar daga kunnensa
"Ku kammala kafin na fito,kiyi tasting girkin ki fadamin abinda kika ji" daga haka ya maida wayar kunnensa sannan ya taka a hankali ya fice daga falon.
Sai daya bacewa ganinta ta janye idanunta daga kanshi tana sauke ajiyar zuciya,suby'a ta zungureta
"Wai meye hakan?" Murmushi samha ta saki
"Farkon ganina dashi.....ban taba tunaun wata rana zai soni....ko xan sameshi ba suby'a,matan dake sonshi sunyi yawan da har nake ganin ni bazan samu ba" baki suby'a ta riqe,tana mamakin samhan,miskilace ta haqiqa,wadda ba kasafai namiji ke burgeta ba,tana da kyan da yasa ba kowanne namiji take tsayawa ta kula ba,bare har ta buda baki tace tana sonshi,alameen na cikin namiji na farko data taba furtawa da bakinta tana sonshi,har kuma take gaza boye son,bata wasa da sanya da dukkan wani abu daya shafeshi.
"Amma suby'a,anya ko yarinyar nan jinin man ce?"
"Kamar yaya?" Suby'a ta tambayeta tana kallonta cikin rashin fahimta
"Basa kama kwata kwata,saidai kowanne cikinsu da color din nashi kyan,na biyu kuma jin kanta yayi yawa...... infact ma,sai nakeji a raina bata yimin ba,innarsu ta fita kirki" murmushi suby'a tayi
"Kinga,kice dai kawai bata yi mikin ba,amma idan batun jin kaine ina kika baro man din naki?,ko kin manta saboda yanzun kin sameshi?"
"Manta kawai,bani abincin na dandana naji abunda yakeso naji din" ta fadi tana kallon taliyar yadda ta shiryu a idanuma,tun ba'a kaita baki ba.
Tabbas taji different aroma and taste,tasan kuma duk hannun da yayi abincin yasan abunda ake kira da girki,saidai batasan me yasa zuciyarta taqi gamsuwa da harshenta ya yabi girkin ba,daga qarshe ta ajjiye spoon din,ta koma da baya ta zauna tana turama ameen saqo.
Sai daya gama wayarshi tsaf sannan ya tura qofar parlor din nasu,babban parlor din daya wadatu da kyau da kuma tsafta,ko ina a shirye yake da kayan alatu masu kyau da daukan hankali,kusan komai na cikinsa black and white ne,ya sauke wayar yana fadin
"Alhamdulillah" har sau uku qasa qasa amma a fili,shi kansa yasan nasibi da budi da ubangiji yaketa yi masa abune da ba kowanne bawa bane ya samu hakan,cikin shekaru kadan amma ya fara riqe dukiyar dako a mafarki bai taba kawowa kansa zai mallaketa ba,yaci gaba da takawa a hankali zuwa daya daga cikin qofofin bedrooms guda biyu dake parlor din,har ya qarasa tasa,ya tura ya shiga.
Dakin kwanane wanda zai burge duk wanda ya ganshi,komai dake cikinsa fari ne,da alama wannan shine zabin mamallakin dakin,komai tsaf a kammale kamae parlor din,qamshi ne kawai ke fita daga cikinsa da kalolin qamshin air freshener da kuma turarukan da yake amfani dasu wanda suka fara kama bedroom din nashi.
Saman mirror dinsa dake cike da kayan shafa na maza ya isa ya dora wayarsa akai,ya balle belt din jikinsa ya fidda wandon,sai boxer daya rage,sannan ya fara balle rigar jikinsa ya fiddasu daya bayan daya,take faffadan jikinsa wanda ke murde yake kuma cike da gargasa daga qirjinsa zuwa hannuwansa suka bayyana,matsawa ya sakeyi gaban mudubin ya dauki towel yana nutsa yatsunsa saman sumarsa,gami da furzar da iska mai zafi daga bakinsa,abinda ke nuni da cewa a gajiye yake lallai.
Wata qofar ya buda ya shige,sannan ya maidata ya rufe.
A qalla mintuna ashirin cif yayi cikin toilet din daidai sanda wayarsa ta fara tsuwwa,yana cikin nau'in mutanen dake dadewa a toilet,ya fito sanye da rigar wanka data tsaya masa iya singalalin qafafunsa da suka jiqe da ruwa,gashin dake jikinsu suka kwanta luf,hannunsa dayan riqe da towel yanata goge sumar kansa da kyau,jikinsa ba abinda yake sai fidda qamshin shower gel din da yake amfani da ita.
Yana ci gaba da goge kan ga qarasa ga wayar tasa,ya zuba mata idanu a haka ba tare daya taba ba,yana karanta saqon samhan daya shigo wayarsa ya kuma bayyana saman screen din
"I ate,what next?" Qaramun murmushin gefan baki yayi,sai ya ajjiye towel din daga gefe,ya dauki wayar yana maida mata amsa
"Ina da son abinci.....if i said that......ina nufin different types of food,so get ready....." Yana sending mata ya ajjiye wayar,ya daga idanunshi ya maida kan fuskarsa data bayyana tarwai a fuskar madubi da dan sauran danshi a kanta.
Idonsa ya dan rufe kana ya bude,fuskar iman ta gifta cikin kwanyarsa haka kawai, different reactions nata a mintunan da suka gabata suka fara dawo masa,sai ya dauki tunanin ya cilla gefe,ya dauko body cream dinsa ya fara shafawa bayan ya saita wayarsa yadda zata karanto masa saqonnin da yake dasu ta email dinsa,tunda ya baro system dinsa a office bai taho da ita ba.
Ta fara nisa da aikin abincin,kamar yadda tunaninta yayi nisa da gangar jikinta taji inna na kiran sunanta,ta ajjiye albasar da take qoqarin yankawa ta waiwayo tana amsawa,duk da qwalla ce qasan idanunta,amma kuma a nata ganin zata kaucewa kowacce tuhuma saboda zata kafa hujja da albasar da take yankawa.
Dan zuba mata idanu innar ta sakeyi
"Idan akwai sauran abincin can da kika dafa kibari basai kin dora wani ba,malam yayo waya,bazai samu tahowa yau ba,zai kwana a can"
"To" tace tana tattare kayayyakin
"Lafiyarki kuwa?" Inna dake shirin fita ta dakata ta tambayi iman din,bata da wata amsa da zata bata,don haka ta gaya nata yanayin da takeji kawai
"Kaina ne yake ciwo" jim kadan inna tayi
"To basai ki lalubi maganinnki kisha tun yanzu ba?,Allah ya sawwaqe"
"Ameen" ta amsa mata tana sake danne zuciyarta,ta tattara komai a tsaitsaye saboda yadda ciwon kan keta qara gaba ta wuce daki.
Alwala tayi tayi sallah,saidai ta kasa tashi daga saman abun sallar,tayi imani a yau idan batasha maganinta ba akwai matsala,ta miqe a hankali tana duba ma'ajiyarsu cike da dauriya,saidai ta taras babu komai,ta dafe goshinta tana kiran sunan Allah.
Tasan dole ta nemo maganin indai tanason samun sassaucin radadin da take ji,matsalar su daya,a yanzu basu da dan aike a gidan,duka almajiran malam an barsu a tsohon gida,yanzu acan suke karatunsu,unguwar tasu kuma wata iriyar unguwa ce,wadda idan kana neman abu sai kayi tattaki ka fita daga cikinta,bata da sauran option face ta fita din,don haka da hijabin jikinta ta zura slipper ta dauki wayarta ta fito.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 48
Har yanzu suna parlor din,saidai zuwa yanzu sun miqr tsaye,da alama suna shirin tafiya ne,kanta ta kawar tayi hanyar dakin inna,ta samu innar tana hada wasu kayayyaki a leda,da alama baquwar tasu zata bawa
"Yaya?" Innar ta tambayeta tana dubanta
"Maganin ciwon kan nan zanje dubowa inna"
"To....amma kuma darene ai,ko kuma bari na yiwa aminu magana,idan zasu fita ya fita dake" bataji dadin abunda inna tace ba,batason hada tafiya dasu kwata kwata,inda tasan tafiyar tata ma zatayi dai dai da tasu da bazata fito ba har sai sun wuce,a yanzu kuma tattalin duk abinda zai bata ran innar takeyi,saboda haka babu damar musa mata,sai ta amsa mata da to,tabi bayan innar sanda take fita daga dakin riqe da ledar.
Suna fitowa zuwa parlor din yana daga labule shima yayi sallama,kallo daya iman tayi masa ta janye idanunta zuwa wani sashe na daban,saboda wani kishi da taji yana shirin shaqe mata kafar iska,wani mugun kyau taga yayi mata cikin qananun kayan da ya saka,sun daukeshi fiye da yadda za'a gaya ma mutum,kana masa kallo daya zaka san cewa hutu wayewa da ilimi sun ratsashi qwarai da gaske,idan dai batayi kuskure ba tana iya ganin yadda samha ta kafe ameen din da idanu,fuskarta kuma na aika masa da saqon murmushi,saita janye jikinta a hankali zuwa baya,ta lalubi kujera daya ta zauna akai,tana qoqarin controlling kanta.
Duk sallamar da sukewa inna tana jinsu,da ledar da suka ajjiye da sunan kayan dubiyarta
"Al'aminu.....xaka biya da iman da Allah zata duba maganinta,kanta ke ciwo"
"Ya salam.....sannu,jikinne ya dawo?" Samha ta fada cikin nuna kulawa,fuskarta na bayyana damuwa.
Kanta kawai ta gyada mata ba tare data dubeta ba,tana iya jin idanun lamin din a kanta,har zuwa sanda ya janyesu yana amsawa inna,suka qara sallama dukka sukabi bayansa tana zaune a wajen ko motsawa batayi ba.
"Tashi kije kada su jiraki" inna dake neman wajen zama ta fada,saita gyada kai
"Zan tashi inna,so nake kan yadan dai daita" ta fada tana tallafe kan nata da tafin hannunta
"Sannu....Allah dai ya sawwaqe wannan ciwon ya yayeshi"
"Amin" ta amsa qasa wasa muryarta na dan rawa saboda hawaye da suke qoqarin taruwa cikin idanunta.
Bata motsa ba har sai da mufida data musu rakiya ta dawo tace ya lamin yace ta fito sannan ta miqe tana ficewa,ita kuma yarinyar ta fara tattare wajen.
Shuru cikin motar ya dauka bayan wucewar mufidan takai saqon da alameen din ya aiketa dashi,shi yana qoqarin saka frequency na gidan radion arewa zaiji labaran dare da yake mayen jin news ne.
Ajiyar zuciya samha ta sauke,tana dan kada yatsunta,ta waiwaya a hankali zuwa sashen da lamin ke rage volume tana duban fuskarsa daga side daya,ta lumshe idanunta kanata bude,daga cikin abubuwan dake burgeta tattare da lamin din yanayij nutsuwarsa da kuma komai nashi bisa tsari da aji,lumsassun idanunsa da kuma kwantaccen gashin dake habarsa zuwa gefe da gefan fuskarsa,wanda ko sau daya babu wanda zaice ya taba ganinsa ba'a tsare ba
"Man" ta kirashi kai tsaye da wata kwantacciyar murya,kansa ya daga suka hada idanu,sai ta sakar masa murmushi,sexy eyes dinsa suna sake tsuma soyayyarsa dake zuciyarta
"Dakai da iman,waye ne yafi miskilanci ne?" Karamin Murmushi ya saki,yana relaxing bayansa da kujera da yake kai,sannan ya gane tafukan hannayensa waje guda yana dubanta
"Ni din miskili ne?" Ya tambayeta yana dage dukka girarsa sama,abunda ya qara masa kyau da kwarjini kenan,sai ta lunshe idanunta sannan ta gyada kai
"Kwarai kuwa,don har yanzu ban manta abubuwan da suka faru ba kafin na sameka" murmushin gefen baki ne ya kubce masa,sai ya gyara zamansa sosai ya na fuskantar gaban motar,dai dai sanda iman ta fito daga ciki,tana kuma takowa a hankali,iska na kada hijabinta daga hagu zuwa dama,dama zuwa hagu,jikinta ba kuzari abinda ya qarawa tafiyarta slow kenan,idamunsa fes a kanta,sai ya dora hannunsa daya kan sitiyarin motar daya hannun kuma ya fara qoqarin tayar da motar sannan yace
"Wala'alla kiga dabi'u masu tarin yawa dake kamanceceniya tsakanina da iman....saboda ita din raino ce" da sauri samha ta kalleshi
"Rainonka?,amma kuma man....sai nake ganin kamar ba sister dinka bace ta jini,ina nufin uwa daya uba daya"
Dubanta yayi kafin ya dauke kansa ya mayar gabansa
"Me yasa kikace haka?"
"Kawai zuciyata na rayamin haka,kuma akwai tarin alamomin tambaya akan fuskarka data iman"
"Ba lallai sai kowa ne da kuka fito ciki daya bane take zama 'yar uwarka ai,ko suby'a a yanzu ta zama 'yar uwata,ko ba haka bama,musulunci ya kulla dangantaka ta 'yan uwantaka a tsakanin kowanne musulmi,bare inna da malam,inda akwai wani matsayi daya gota na uwa da uba,tabbas sun cancanceshi.....ko kinsan lamin ba kowa bane face almajiri?"
"Almajiri?" Ta tambaya cikin mamaki tana dubansa da kyau,saiya gyada mata kai ba tare daya waiwayo ba
"Yes,hala kinyi mistake da kika fara soyayya da almajiri ko?" Ya fadi wani ciwo na motsuwa cikin ransa na abunda ya shude shekarun baya can,murmushi ta saka
"Ko kadan,koda akwai matsayin da kake ganin yafi na almajiri muni ni bai dameni ba,kuma baya gabana,saboda muhammad al'ameen din gundarinsa nakeso" lafazinta ya sanyashi waiwaya ba shiri ya kalleta,lokaci daya yaji matsayinta ya qaru a ransa,a da yana wani hasashe da kuma d'ari d'ari a kanta,amma a yanzu ta wanke komai.
Kafin ya amsa mata iman ta qaraso,ta bude gidan baya daya side din ta shiga,suby'a ta amsa sallamar tata tare da yi mata sannu,yayin da samha a wannan karon batace da ita komai ba,lokaci daya wani kishin iman din taji ya kama zuciyarta da mugun qarfi,duk wata soyayya da kulawa da take qoqarin bata babu ita ta zagwanye,kishi ya maye gurbinta,itama iman din bata lura da wani sauyi daga samhan ba,saboda dama ba wai qaunar shishshigin da take mata take ba,ta tattara dukka hankalinta ta mayar ga window,tana kallon gine gine da kuma titunan da suke giftawa.
Kasa kasa take iya jin hirar da samha kewa amin,amma ba zaka iya jin me take gaya masa ba,idanuwanta ta mayar ta lumshe kawai,tana jin sautin bugun zuciyarta da qarfi,addu'a take sukai inda zata sauka ta fita a motar,don ko meye za'a bata ba zata yarda ta dawo a cikinta ba.
Bata tashi bude idanunta ba sai da taji sun sauka daga titi suna gangarawa zuw cikin wani layi,ta bude idanunta a hankali tana kallon unguwar.
Kofar wani gida ya tsaida motar,gidane mai bene hakanan mai girma tun daga yanayin katangarsa ta waje,yana da tsaho a fuskar gidan ma,gininsa a tsaye yake,ko ba'a gaya maka ba kasan masj gidan akwai abun,duk da yanayin ginin na nuna ya dan kwana biyu.
Suby'a ce tayi mata magana tana shirin fita
"Allah ya qara sauqi,sai anjima"
"Ameen,na gode" ta amsa da muryarta data cakuda da sanyi,tana sake maida kanta gefe
"Man....shikenan?,sai yaushe?" Samha ta tambaya a narke tana duban ameen,idanunsa na kallon gaban motar,yayin da ya yiwa sitiyarin motar qawanya da hannuwansa duka biyun
"I will see you soon"
"Ka tabbata?" Saiya jinjina kai wannan karon bayan ya kalleta
"Na tabbata"
"Is okay,byee,qanwarmu,Allah ya bada lafiya" ta fada tana kama murfin motar ta bude sannan ta fice,iman din ba zata iya tantance ta amsa mata ko bata amsa ba,illa dai tasan tayi qoqarin motsa labbanta,amma batasan sautin ya fita ko maqalewa yayi ba,samhan ta zagaya a hankali yana tsaye har zuwa sanda ta bude murfin qofar gida ta shige bayan ta tsaya tayi waving masa hannunta.
Shuru ya ratsa motar na wasu mintuna
"Taso ki dawo gaba" umarni ya fita kai tsaye daga bakinsa,umarnin daya sake tattaro dukka wani kishinta da bacin ranta waje daya,abunda ya matsa mata qwallar da take dannewa ta gangaro mata,sai tasa gefen hijabinta ta tsaneta,sannan ta bashi amsar da ita kanta batayi tsammani zata iya bashi ba
"A'ah,a nan zan zauna" shuru ya sake ratsawa na second biyar kafin taji ya saka hannu ya buda murfin motar,ya fito a nutse yana takawa zuwa side din da take zaune,hannu yasa ya buda murfin motar
"Fito" ya fada da dakakkiyar muryarsan nan wanda duk sanda yayi amfani da ita wajen yi mata magana......maganar ke shiga har cikin qashi da bargonta.
Kamar yadda yace haka taja jikinta a matuqar mace ta fita,ta bude gaban ta shiga,ya maida murfin bayan ya rufe,ya zagayo seat dinsa ya shigo ya maida mufin shima ya rufe.
Takure jikinta tayi gaba daya waje daya,tana jin wani mugun kusanci a tsakaninsu,zuciyarta na sake canza yanayim bugunta,qamshin turarensa ya mamayeta gaba daya,kai kace tayi mayafi ne da suturarsa,kwantar da kanta tayi saman cinyarta bayan ta rungume gwuiwoyinta cikin jikinta,tana fatan hakan xai bata dukka wani qwarin gwiwa da take nema,xai kuma hana hawayen dake idanunta zuba.
Tanajin sanda ya tashi motar,hawaye suka silalo mata masu dumi,wane irin hukunci ya ameen din yake mata haka?,saita kifa fuskarta kawai tana ta gayawa kanta cewa bai kamaci tayi kuka ba a yanzu,a jikinta takeji kowacce rana zuciyarta na sake samun rauni ne,raunin da ta tabbatar indai haka zata ci gaba da kasancewa......watan watarana zata gaza,zata gaza ci gaba da daukar komai.
Basuyi tafiya mai nisa sosai ba taji ya sake tsaida motar,ya fita ya zagaya seat din baya ya dauki kwalin maganin daya sulale a hannunta ya shiga pharmacy din dake gabansu,bai jima ba ya fito,ya sake shiga motar yana dan sauke numfashi sannan ya tada motar,dai dai sanda wayarsa ta dauki ruri,ya daga wayar ya sakata a handsfree yana ci gaba da tuqinsa
"Kana ta inane?" Muryar ya sadiqu ta cika motar
"Na fita maida baby......daga nan kuma zan shiga ayimin aski,bana jin dadin kaina haka" kalmar babyn tayi matuqar yiwa iman din zafi,ta runtse idonta gam tana ambaton sunan Allah
"Oh okay,yanzu zan qaraza gida nima,idan ka dawo ma jone"
"Ba case" ya amsa masa yana kashe wayar,saiya ajjiyeta a tsakaninsu ya maida dukka hankalinsa ka tuqin da yake,saidai lokaci zuwa lokaci wani abu na dan dauke masa hankali.
Ko qwaqwaran motsi taqiyi,har cikin ranta takejin kamar da biyu ameen din yake komai,ta yaya zai dinga pretending ne a kanta,bayan duk duniya shine mutum na farko dayafi kowa karantar zahiri da badinin zuciyarta,shin ina wannan karatun?,ko shina ya zagwanye tare da dukka soyayyar daya gwada mata a baya?,ko shima ya tafi tare da dukka wata qauna tata dake ran ameen din?,baisan wani irin ciwo me zafi yake dasawa ranta da rayuwarta ba,baisan yana kasheta bane deep inside her.
Katafaren gidan aski ne na isassun maza wanda ya amsa sunansa,koda sau daya ka dubi wajen kasan waje ne dake tafe da tsari da kuma ilimi gwanin burgewa,baya ga aski har manicure and pedicure,duk inda kaga yaje aski ko gyaran farce a kano to babu yadda zaiyi ne,yafi ganewa na nan wajen,ya cire belt dinsa ya buda qofa a nutse ya fice.
Tunda ya fita idanunta na alumshe,saidai qarar da wayarsa ta fara yi akai akai ya fara damunta,dole ta juyo da fuskarta a hankali zuwa sashe da wayar take wadda keta haske kiran na sake shigowa.
Sign na heart ne kawai ke blinking akan screen din,ta zubawa screen din wayar idanu,zuciyarta na ci gaba da bugawa a hankali,haka wayar taci gaba da shigowa tana kuma yankewa har kusan sau uku.
Tana shirin dauke idanunta don ragewa kanta bugun zuciyar saqo ya shigo a karo na qarshe maimakon kira
_"Nasan duk yadda akayi driving kake man,duk da na qiyasta for now yaci ace ka isa gida,hala kun tsaya wani guri ne, anyways..... take care of yourself"_
Wani abu me matuqar zafi cakude da bacin rai ne ya tasowa iman,me wannan matar ke nufi?,batasan waye ameen a wajenta ba?,koda babu komai batasan shi din yayanta bane?,batasan sunfi kusa ba?,kalamanta na nuni da tuhuma da kuma shakka a fakaice,saita daga hannunta a zafafe da niyyar kashe hasken wayar don ta daina ganin gilmawar saqon a idanunta,dai dai lokacin da ya bude motar,idanunsa ya sauka a kan wayar,kana ya janyesu ya maidasu kan fuskar iman,qwayar idonta ta shiga cikin tashi,saita janye idanun nata tana kuma qoqarin maida fuskarta daya side din dai dai sanda ya jefa mata tambaya
"An kirani ne?" So take ta cire masa shakkun abinda ya gani din,kada ya dauka damuwa tayi da wayar yasa har haka,saboda zuwa lokacin ya dauki wayar yana buda Tex din
"Kararta ce take damuna,am trying to mute the sound" murmushin gefan baki ya saki mara sauti,wanda ita kanta iman din bata ankara da hakan ba,shuru na wasu sakanni ya sake ratsa wajen da alama saqon yake karantawa,kafin daga bisani yace........
GIRMA DA KIMAR IYAYE TA WUCE WASA,A DUK SANDA KA SABAWA MAGANARSU KODA KA FISU GASIYA,INDAI BA KAUCEWA FADAR ALLAH BANE,KO YAYA...KO YAYA SAI KAGA BA DAI DAI BA,DUK WADDA TA ZABA IRIN ABUNDA IMAN TAYI,ZATA IYA GAMUWA DA SAKAMAKON DA YAFI NA IMAN,wallahi wallahi iman nata da sauqi,da Allah yaga dama sai ta hadu da cutar hiv din daga jikin bassam har qarshen rayuwarta,sabawa umarnin iyaye yana daga cikin gagga gagga laifuffuka da bai kamata ayi sakaci ko sasauci wajen fadakarwa a kansu ba,littafi yanzu ya zama kamar wani madubine da al'umma suke kalla su gyara wani abu da ba dai dai ba,Allah yasa mu dace
*please follow me on arewabooks*
HUGUMA
Add my story to your library for more latest pages
https:/arewabooks.com/chapter?id=62bff720a306c9b48f09f552
Thanks.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 49
"Fito ki duba cikin biyun wanne ne zai miki maganin,an samu different colors" ya fadi mata yana juyawa, trying to call number samha din.
Gaba yayi tana binshi a baya,tana jin sanda yake baiwa samhan excuse,tare da alqawarin kiranta idan ya gama abunda yake,tabi bayansa da kallo ta cikin hasken fitilun dake wajen,wani abu mai nauyi na sake ratsa qirjinta da zuciyarta.
Dab da zasu shiga wajen saiya rage saurinsa,harta cimmasa suka dai daita tazarar dake tsakaninsu sannan suka shige,babban store ne,wanda bayan magunguna suna saida abubuwa iri daban daban na ciye ciye.
Da hannu yayi mata nuni da area din magungunan suke,ta fara takawa a hankali tana shiga wajen,idanunsa na biye da ita,kafin daga bisani ya janyesu yana qoqarin dai daita kansa.
Tana duba magunguna amma kuma hankalinta na wani waje na daban,zuciyarta ta nace maimaita mata duk abubuwan da suka faru tun daga zuwan samha har zuwa tsaiwarsu qofar wajen
"Wow....wacce iriyar sa'a na taka yau din?" Da sauri ta waiwaya jin muryar data sani na magana,kuma daf da ita ake maganar,dr ahmad ne,yana sabe da wata baby girl wadda aka yiwa kwalliya dai dai gwargwado,gashinta yasha adon ribbons masu kyau.
Bakinta ta washe masa kamar yadda hake binta da murmushi,don dai ita din ba zata kira abunda tayi masa da sunan murmushi ba
"Dr,barka da dare"
"A'ah,ki barni na fara gaisheki mana hajjaju,banyi tsammanin ganinki a yanxu ba a wannan wajen,sai gashi Allah ya dubi idanun bawan Allah" murmushi ne yaso qwace mata ganin yadda yayi,ta miqa hannu don ya bata yarinyar tana cewa
"Zo baby....ya sunanki?" Ba qyuya kuwa yarinyar ta taho wajen nata,duk da batasanta ba,sai dr ahmad ya buda baki yana kallonta
"What?,lallai kin ciri tuta wajen milha" ya fada cikin mamaki,saita dauke idaunta daga fuskar yarinyar,wadda ganinta sak fuskar dr ahmad din
"Me kenan?"
"Bata yarda da kowa sai wanda ta saba gani,zaiyi wuya kiga taje wajen baquwar fuska" murmushi tayi kawai maimakon amsa maganarsa,ta rasa abun cewa don haka tace dashi
"Kana tana yawon dare kenan?" Da sauri ya daga hannayensa sama
"Rufamin asiri hajjaju,wallahi ba haka nake ba,kada a kashen kasuwa" murmushi ya kubce nata ganin yadda ya haqiqance har da saurin rantsuwa
"Maganin hajiya ne ya qare shine na fito nemo mata" saita gyada kanta tana ci gaba da yiwa yarinyar wasa,yarinyar taji ta burgeta,ta kuma kwanta mata a rai,duk da dama itadin mayyyar yara ce,saboda yadda ta taso itace qarama a gida,bata da qani ko qamwa,idanun dr ahmad a kansa,yana fargabar ya zamana wani ne ya kawota ba,ya hadiye abunda ke taso masa ya daure ya tambayeta
"Kefa?,Allah yasa ba 'yan overtaking bane sukayi overtaking din dani" qaramin murmushi ta maida masa itama,sannan ta amsa mishi
"Nima maganina na fito nema,ni da ya ameen ne"
"Oh... okay" sai taga kawai ya dauki kwando ya fara zuba daukan kaya yana zubawa,bata kawo komai a ranta ba,tunda tasan cewa yana da iyaye,sannan uwa uba mutum kamar dr ahmad din bazai kasa shigowa guri kamar wannan ba ya fita bai dauki komai ba.
Mintuna kusan takwas ya sake dawowa inda suke,ya cika kwandon da kaya
"Muje na biya kudi,daga nan sai mu gaisa da yayan namu ko?" Kamar tace mishi a'ah,sai kuma wani abu ya darsu a ranta,don haka kai tsaye tace masa
"Ok,ba damuwa" yaso amsar milha amma tace masa a'ah
"Ina ka samo baby ne me kama da kai?"
"Magana ce daya kamata ayita a nutse,bazan gaya miki komai akai ba,har sai randa aka bani dama nazo ni dake muka zauna sosai.....don Allah ki tausayamin ki gajarcemin wannan jiran da bansan lokacin yankewarsa ba" ya fadi yana marairaicewa,yanayin maganar tasa yasa murmushi kubce mata,dai dai sanda ameen dake tsaye yana jiranta ya daga kansa daga wayarsa da yake dannawa,idanunsa kuma basu sauka ako ina ba sai a kansu,kallon second uku yayi musu ya sauke kan nasa again akan wayar tasa,kamar bai sansu ba,ko bai gansu ba,yaci gaba da latsa wayarsa.
Daga can qasan zuciyarta taji wani dadi ya zarta mata kadan kan ganinsu tare da ya amin din yayi,duk da ba haka taso ba ace ya dauje idanun nasa da wurwuri haka,ta tsurawa fuskarsa idanu sanda suke takowa inda yake tsayen,zuciyarta cike da hope din ya sake daga idanu ya gansu taren,saidai kuma addu'arta bata ci ba,don har suka qaraso wajen tamkar baisan Allah yayi ruwan halittarsu ba,har sai da dr ahmad yayi masa sallama sannan ya daga kansa yana amsa masa,suka miqawa juna hannu.
Ci gaba tayi da satar kallon fuskarsa sanda suke gaisawa da dr ahmad,wai ko zata karanci wani abu na sauyawarsa ko kuma wani yanayi na daban,saidai duk qwaqwarta ta kasa gane komai,tilas ta kama kanta daga nacin kallon da take masa,qwaqwalwarta ta shiga searching,daga bisani ya karba milha daga hannunta,ya matsa kadan daga inda suke tsaye yana ta yiwa yarinyar wasa,sai kuma ya fara takawa a hankali yana komawa cikin store din,yana tafe yana daukar mata kayan wasa da sauran kayan ciye ciye na yara.
Bai tashi dawowa ba saida uban siyayyan kayan wasa dana ci kala kala,dai dai sanda aka gama yiwa Dr Ahmad lissafi ya kuma biya da cash,shima ya matsa aka lissafa ya basu atm dinsa suka cira,don bau wadataccen kudi a hannunsa.
Tare suka jero da dr din suna taba hira,saika dauka sunsan juna ne,hirace irin tasu ta maza data shafesu,tana biye dasu a baya,saidai gaba daya ya ameen din ya gama kwance mata duk wani lissafi nata da yayi saura,duk wata hanya da zata saka masa tarko ko kuma ta gane wani abu ya tosheta.
A seat din gaban motar dr ahmad din ya ajjiye yarinyar,ya kuma ajiye mata ledarta a gefanta,sannan ya sha sumarta ya cewa
"Byee baby"
"Byee uncle"ta amsa masa tana dariya tare da kada hannunta,ya maida murfin ya rufe mata,sannan ya nufi motarsa.
"Bamuyi haka dakai ba dr,yanzu nacewa ya ameen me?,kawai daga haduwa saika hau yimin siyayya,shi kansa ya amin din ai bazaiji dadi ba" iman tace da dr ahmad,wanda ya jajirce sai ta karba uban siyayyar da yayi da sunanta
"So nake innar dama ta tambayi waye ni,qilan hakan zaisa a bani damar bayyana kaina,amma maganar ya ameen na tabbatar bashi da matsala,muje kawai" yayi gaba riqe da ledar.
Tsaiwa tayi ta kasa binsa kamar an riqe mata qafafu,inda tasan haka zata faru da bata tsaya ba,tana kallonsa har zuwa sanda ya isa bakin motar amin din,ya zagaya ta window yayi magana,sai taga ya dage booth din motar ya saka ledar ya rufe,sanna ya waiwayo inda take tsaye,ya sakar mata murmushi yana daga hannuwansa biyu,alamun komai yayi dai dai,sai a sannan ta fara takowa a hankali kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki.
"Matsoraciya kawai,kina da yaya mai sauqin hali da kuma fahimta amma bakisan hakan ba" yafada yana dariyar tsokana,itadai bata iya cewa komai ba,sai yayi gaba ya bude mata murfin motar,ta zura jikinta a hankali,tana ji dama baya ya bude mata ba gaba ba,ya maida ya rufe yana cewa
"Na gode hajiya.......yallabai godiya nake" yaja da baya don ya bashi damar tada motar,kafin ya juya zuwa tashi motar.
Shuru shine abinda ya wanzu a motar,daga ita har shi babu wani da yake cewa da dan uwansa komai.
Inda so samu ne kuka takeson tayi ko zata samu relief,kuka irin sosai din nan,duk wannan abun da tayi tayi ne saboda ya ameen din,tayi ne di ta caje zuciyarsa ko zata tsinci wani abu da zai bata qwarin gwiwa,saidai da alama babu komai a ciki da yake da nasaba da ita,hawayen sun taru ta maidasu har batasan adadi ba
Wani tuqi yake ba irin wanda yayi daxu ba,ya qara speed na motar fiye da dazu sosai,hakanan ya tattara hankalinsa da idanunsa kan titi fiye da dazun dai,a haka suka qarasa gida,yayi parking sannan ya kashe motar
"Ki daga booth ki kwashe tarkacen can.....don idan kika barsu zanyi sadakarsu ne" wani kallo ta watsa masa da yafi kama da harara,yau inda akwai wasa tsakaninsu saita yaba masa maganganun da wala'alla zuciyarta zata sassauta,bata taba yardarwa kanta ameen kwata kwata bata gabanshi baya kishinta ba sai yanzu,qafafuwanta suna rawa ta soma takawa cikin gida ba tare data tsaya diban kayan ba,saboda hawayen da taketa riqewa daya balle mata.
A zafafe shima ya fita daga motar yabi bayanta,taku hudu qwarara ya cimmata ya kuma sha gabanta,cikin wani irin zafi yake duban fuskarta
"Abokin wasanki ne ni?.....nace ki kwashe kayanki ki taho kibarsu cikin motata?,inyi me dasu?" Ya fada cikin muryarsa da tayi nauyi,take kuma cike fal da fada.
Gudun hawayen fuskarta suka qaru,sai kuma a sannan ya lura dasu,sassauci ya sauki saman fuskarsa ba kamar dazu ba,yaja numfashi yana qoqarin danne kansa
"Wadan nan hawayen kuma na meye su?,me akayi miki?" Yafadi yana hade girarsa waje guda,qas tayi da kanta ba tare data iya cewa dashi komai ba,tsahon wasu sakanni sannan ta bude baki a hankali
"Ciwon kaina ne ya dawo" idanunsa ya dauke daga kanta,daga can bakin qofa ya hangi sayyadi,yaron da malam ke aikowa gidan wasu lokutan ya kawo sakonni,cikin kaurin murya ya kira yaron,ya qaraso da hanzari a ladabce,saiya nuna masa motar
"Jeka ka bude bayanta zakaga leda ka daukota gaba daya"
"To" ya amsa mishi yana juyawa.
A hankali ya dauke idanunsa daga kan yaron ya maida fuskar iman din,sai ya hade hannayensa a qirjinsa ya zubawa fuskar tata idanu yana iya ganin yadda hawaye yake diga yana faduwa qasa,kallonsa yana da matuqar dafi da kuma tasiri a jikinta da zuciyarta,saiya qara mata wani weakness daya sanya ta kasa dogara da kanta sai data jingina da bangon hanyar da zata sadaka da parlor din,ta kuma boye fuskarta cikin hijabi.
Dawowa sayyadi yayi da ledar a hannunsa,ameen ne ya karba ya ajjiyeta a gefe,taku uku ya qare ya rahe tazarar dake tsakaninsa da iman din,yatsaya gab da ita sosai,cikin wani irin lallausan murya yace
"Yanzun ciwon kan kikewa kuka haka?" Batasan me zatace dashi ba,shima bai jirayi amsarta ba yace
"Ki qoqari ki tsaya haka,don ciki zaki shiga,ni kuma ba zamu shiga tare ba kina wannan kukan inna ta dauka wani abune ya faru" sai ya saka hannunsa a karon farko tsahon rayuwarsu yaja hijabin data duqunqune fuskarta dashi ya fara qoqarin wareshi.
Kam ta riqe hijabij,qaramin murmushin da iyakarsa fatar baki ya saki,ya gwada mata irin nasa qarfin,tashi guda ya cireshi gaba daya,har hakan ya kusa haifar da fadawarta jikinsa,saidai ya tareta da hannunshi kana ya matsa baya.
Hannayensa ya zuba a aljihun wandonsa yana kallonta,ya tsare gida sosai kamar bashi ba
"Zagaya muje ta bayan gida" ya bata umarni kai tsaye,dole kayi shakkansa yadda ya sauya fuska lokaci guda,ta fara takawa kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki shi kuma yana biye da ita suka bi ta hanyar bayan gidan.
Saida yasa ta wanke fuskarta a bakin famfon wajen,ya miqa mata handkerchief dinsa mai cike da sassanyan qamshi ta dauke danshin fuskarta dashi sanna ya mata nuni data wuce,ta taka a hakali zuwa ciki ya rakata da idanunsa.
Babu kowa a parlor din sai tv dake aiki,ta qarasa cikin qarfin hali ta kasheta,sannan ta nufi dakin inna,labulen tadan daga kawai ta gaya mata ta dawo,zata wuce tasha magani ta kwanta,innan tayi mata sannu ta zarce dakinta tana jin sanyi cikin ranta na yadda innar bata ga fuskarta ba,kota kan kayan da suka baro waje bata sake tunawa ba,tabi lafiyar katifarta bayan tasha maganin tana sauke ajiyar zuciya,taji relief a cikin zuciyarta qwarai,hakan kuma bai rasa nasaba da dan caring da ya ameen ya nuna mata,duk da bai taka kara ya karya ba,ta rufe idanunta tana hango yadda lumsassun idanunsa suka bude da kyau sanda ta kusa fadawa jikinsa ya kuma ja baya da sauri,saita sauke ajiyar zuciya tana tura kanta qasan pillow.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 50
Da gaske ta dinga yaqi da zuciyarta cikin kwanakin don ganin ta samarwa da zuciyarta nutsuwa,saboda yadda takejin yanayin jikinta komai zai iya faruwa da ita.
Duk wata hanya da zasu hadu da ita tayi qoqari ta tosheta,saidai duk da hakan bata tsira da jin muryarsa da kuma tunani da zuciyarta ke yawan kawo mata,wanda take yaqi qwarai wajen kawar da wannan,saidai kusan a banza wai man kaza,data kore tunanin batasan lokacin da zai mamayeta ya dawo ba.
A haka ta dinga juriya tana dannewa,tayi qoqari ta maida hankalinta kan karatunta,saboda karatune da ko yaya damuwa ta shiga cikinsa sai kaga ba dai dai ba,hakanan tana shekarar qarshe,kada ya rage mata ta zama cikakkiyar nurse.
*********Safiyar wata lahadi,a ranar bata da wani uzuri da zai fiddata waje,don haka bayan ta gama komai na ayyukan gidan tayi wanka ta sake komawa ta kwanta,babu jimawa barci ya debeta.
Can cikin barci yunwa ta tasheta,ta sauko a hankali daga gadonta,ta miqe ta shige toilet,bakinta ta sake wankewa ta dauraye fuskarta ta tsaneta da towel sannan ta fito,ta jawo hijab dinta iya gwiwa ta zura,saboda yau din weekend,tasan ba za'a rasa mazan gidan a kusa ba.
Parlor babu kowa,saidai tana iya dan jiyo muryoyi daga parlor din malam,sai ta zarce dakin inna taga ko zata sameta?.
Bata ciki,ba kowa ma a ciki,ta dan kalli dakin,sai taji ya kamata ta sake kintsa mata shi,duk da atsaftace yake,amma wasu kayan ba guraren daya kamata a ajjiyesu kenan ba.
Ta rufe dakin tana juyowa sukayi kacibus da inna
"Yanzu na dubaki ban ganki ba"
"Eh ina wajen malam,muje ciki dama inason ganinki" gaban iman din ya fadi,saboda a yanzun babu abinda taqi jini irin ta batawa inna ko malam rai,tun bayan kuskuren data tafka a baya,jikinta babu qwari tabi bayan inna.
Atsaye ta sameta tsakar dakin
"Wannan kayan na waye?,tun rannan sayyadi ya shigo dasu,yanayin jikinki yasa ban miki zancansu ba,na manta dasu ma a dakin sai daxu ina neman wani sabon rawanin malam" idanunta takai ga ledar,gabanta ya sake faduwa,ta tuna da ita,shaf ta manta da ita sai yanzu,ta dubi inna taga yadda ta tsareta da idanu,koda bata yi mata hakan ba babu wani 'yar boye boye tsakaninta da inna,tayi wannan alqawarin daga sanda mai faruwa ta faru,har zuwa randa ita ko innar wani zaibar wani a duniya
"Dr ahmad ne ya bani"
"Wayeshi?" Ta tambayeta yanayin fuskar innar yana sauyawa
"Likitan dake dubani tun ina gidan bassam,ranar dana fita siyo magani muka hadu dashi a store din"
"Kina nufin a gaban aminu?,kuma ya sani?" Kai ta gyadawa innar a sanyaye,shuru ya ratsa dakin na kusan minti guda
"Shikenan,kije,dama malam yace yanason ganinki" gaba daya sai gabbanta suka saki,ta kasa motsawa,ta kuma kasa hadiye tambayarta sai data jefawa inna ita
"Malam kuma inna,wani laifin nayi?" Kallonta tayi,sai taji tausayinta ya tabata,don haka tayi mata murmushi
"Babu wani laifi,shikenan babu ganawa ko tattaunawa tsakanin uba da diyanshi sai ya zamto wani laifi suka aikata masa?" Ajiyar zuciya ta sauke,ta samu relief yanzu,don haka ta juya ta fita a dakin innar,innar ta bita da kallo a sace harta qarasa fitar,saita sauke ajiyar zuciya,ta laluba gefan gadonta ta zauna tana fadin
"Ya Allahu,ya Allah ka shiga wannan lamari,Allah ka kawo mafita ya rahman,Allah kai kasan yadda zakayi da bayin nan naka,ya Allahu" murya qasa qasa,qafafunta gaba daya sunyi sanyi,ta jima a zaune kafin ta miqe ta shiga abunda ga kawota dakin.
Yankewa tayi kawai ta fara shiga kitchen ta samu wani abun ta toshe yunwar dake sakadarta kafin ta wuce wajen malam din,haka kuwa akayi,ta biya ta can ta hada tea tasha,ta samu ragowar soyayyan qwai tana murmushi ta fara gutsira tana ci,da alama na mufida ne,sabida tafi kowa son soyayyen qwai a gidan,tadanji cikinta yayi mata dai dai sannan ta wuce wajen malam din.
Tun kafin ta shiga rumfar malam din ta fara jiyo muryarsa mai cike da nutsuwa da taushi,da alama wani bayani yakewa malam din,ta tsinci kanta cikin faduwar gaba kamar kowanne lokaci,ta zuqi iska sosai sannan ta fesar,ta tabbatar shigarta parlor din sai yabar baya da qura,basu taba hada wajen zama dashi ba bata tsinci zuciyarta cikin wani sabo kuma mahaukacin sonshi ba,abun kamar jarrabi a gareta,haka ta tattaro dukka wata jarumta da juriyarta ta yaye labulen tare da yin sallama.
Idanunsa ya dauke daga kan paper din dake hannunsa ya saukesu a kanta,ya motsa labbansa yana amsa sallamar tata kafin ya janyesu ya sake maidawa kan takardar gami da dakatawa da bayanin da yakeyi.
Tun hada idanun da sukayi dashi karo na farko ta janye daga kallonsa,tun kuma a sannan ya sakar mata wasu dafi masi qarfi xuwa kowanne sashe na jiki da zuciyarta,yayi azabar kyau cikin shadda wadda aka yiwa wani irin dinki,yar ciki me dogon hannu da wata daga sama kamar top,taji aikin hannu da zare mai kauri,dinkin ya zauna masa kamar yadda shaddar tayi bala'in tafiya da qirarsa da kyan surar da Allah yayi masa,sumar kansa a kwance sai qyalli takeyi,kwanakin data dauka bata ganshi ba sai taga kamar an qara masa kyaune,wani abu mai sanyi ya ratsa zuciyarta,idan hancinta ba qarya yayi mata ba qamshinsa ne kawai cike a falon,wani sihirtaccen qamshi da batasan da wanne kalar turare yake amfani ba,tun yana lamin dinsa asal qamshinsa na dabanne,gwani ne wajen iya zabar kalar turare
"Maraba da autar inna,hajaratu ayar Allah" malam ya tsokaneta da suna da kuma salon da a baya yake tsokanarta dashi,murmushi ta saki,saboda abun yayi mata dadi sosai,abune data jima rabon data jishi daga bakin malam din,wannan dalilin ya sanya ta zabi zama kusa da malam din,saita zarce mazauninsa,ta zauna dai dai qafafunsa a qasan carpet ta soma gaidashi.
Cikin kulawa ya amsa mata,ta maida dubanta ga lamin
"Barka da safiya" hankalinsa na kan takardun gabansa ya amsa mata,hakanan ya sadiqu shima takardun dai yaketa dubawa yana shiryasu.
Ita d malam suke dan taba hira,yayin da sadiqu da amin din suka karkata da hada takardun,suna kuma dan musayar maganganu a tsakaninsu,duk da hirar da suke da malam din amma hankalinta na kanshi,a sace take kallonsa ta gefan idonta,glass din da ya sanya a yau din ya qara masa kyau da kwarjini na musamman,ta yarda sanya abu ma ya karbeka baiwa ce,shikam yana daga cikin baiwarsa,tun zamanin da yawancin suturunsa ma ba masu tsada bane,bare yanzu da kudade suka fara zaunar masa.
Ta lura da yadda wayarsa keta haske yana kasheta,da alama kira ne yaketa shigowa,sai taji rata ya raya mata samha ce,take zuciyarta ta jagule,karo na qarshe yadan saki siririn tsaki ya kashe wayar gaba dayanta wanda cikin rashin sa'a ya kamata tana kallon nasa,da wani mugun hanzari ta dauke kanta kamar bashi take kallo ba,tana iya jin siririn murmushi mai qaramin sauti daya fitar,yaci gaba da aikinsa.
Kusan mintuna talatin sannan suka kammala
"Komai yayi dai dai,rana kawai mukeso malam ya sanya mana da za'a bude company din" alamin ya fada a ladabce da nuna tsananin girmamawa,daya daga cikin abubuwan da suka sanya malam din yakejin bala'in so da qaunar alamin din,wani irin yaro ne da Allah ya zuba masa sanin ya kamata,mai matuqar ladabi biyayya tausayi da kuma girmama na gaba,ba shakka duk da iyayensa basu mori komai daga kyakkyawar haihuwar da sukayi ba,amma kuma sun barwa duniya kyakkyawan iri abun misali,mutane da yawansu basusan ba malam bane ya haifi lamin din ba,sai dalili ya kawo,kai malam din ya jinjina
"Ina ganin mu barwa ranar juma'a ko?,bayan saukowa daga sallar juma'a,tunda kace akwai masallaci daura da ma'aikatar"
"To Allah ya kai mana rai da lafiya" ya amsa a ladance
"Ameen ameen" malam da sadiqu suka amsa
"Sanna kuma...." Ya sake magana yana motsawa
"Akwai wani abunda na soma nema yanxu haka,shirye shirye nason bude compy na saida spare parts na motoci da kuma maida tsofaffin motoci zuwa sababbi wanda nake saka ran sadiq zai ja ragamarsu,abun yana da wahala ne malam da kuma buqatar kudade,to amma kuma cikin ikon Allah da muka fara aiki kan abun,sai komai yake zuwa mana da sauqi,mun samu manyan mutane da suke da sha'awa kan abun,kuma zasu zuna share dinsu,yanzu haka muna saka ran nan ba da dadewa ba shima za'a gama komai yafara aiki"
"Allahu akhbar,Alhamdulillah,mun godewa Allah,ubangiji ya qara sanya albarka cikin lamuranka kai da 'yan uwanka,ba shakka wannan babban abun alfahari ne a garemu.....ke hajar,kiramin innarku" ya fadi yana duban iman,tarin walwala da farincikin dake saman fuskarsa ba zasu misaltu ba.
Ko minti daya bata cika ba inna ta shigo,ta ajjiye wasu kwanuka gaban malam din,ta koma gefe daya ta xauna tana sauraren bayanan malam.
Ita kanta kasa boye murnarta tayi,tayi musu addu'a sosai tare da fatam samun nasara kan duk wani abu da suka sanya a gaba.
"To ku bani hankulanku nan,akwai muhimmiyar maganar data sanya na buqaci ganinku,na kuma taraku a nan....." Sanun cewa duk sada malam din yayi haka magana me muhimmanci zaiyi yasa kowa sake shiga nutsuwarsa,suka kuma zubawa malam din idanu suna jiran abunda zai fita daga bakinsa.......
*afwa da qaramin page,nayi busy ne👏🏾👏🏾*[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: "Alhamdulillah.....Alhamdulillah,mungodewa
Allah da yadda rayuwa tayi da kowannenku,kuma
ubangiji gayi muku baiwa da kyauta wadda ba
kowane ya samu kwatankwacinta ba...….ya zuwa
yanzu kowanne ya samu duk wani rufin asiri na
rayuwa,ya kuma samu madogara da madafa
koda babu ranmu,abu guda daya ne ya rage
muku,ku dukka ukun kun isa kun kuma kai
munzalin daya kamata ace kowa nada aure a
cikinku......" Matsananciyar faduwar gaba ta
saukarwa iman,jin malam ya ambaci kalmar
aure,uwa uba kuma cikin jawabin nasa harda
ita, kenan ko meye zai fito daga bakin malam
din.……kowanne irin hukunci ne ya shafeta?,harda
ita a ciki kenan?,take taji gaba daya jikinta ya
saki.tafin hannaventa dana gafafunta sukayi wani Saki,tarn hanhayenta dana q'dravunta sukayiWanl
irin sanyi,saita fara murxasu tana addu'a cikin
ranta, ko meye zai fito daga bakin malam
din,indai maganar aure ce Allah yasa a tsameta a
ciki,ta maida hankalinta tana son jin qarashen
bayaninsa
"Dukkaninku kowa yana da sukunin ajjiye
iyali,gurin zama da sana'ar yi,sannan hankali a
yanzu ya game kowa a cikinku……..kema kuma kin
qara hankali,a yanzuk kinsan dai dai,kinsan ba
dai dai ba, kinsan me ya kamata, kin kuma san
abinda bai kamata ba,saboda haka,inaso kowa a
cikinku ya gabatar min da wanda zuciyarsa ta
kwanta masa dashi,duk da dau na fara samun
labarai daga wajen innarku,amma inason naji ta
bakin kowa"
Shuru ne ya ratsa parlorn,aka rasa wanda zai
fara magana a cikinsu,iman dai kanta na
qasa,yayin da lamin iya nashi idanun ni a
qasa,yana caccaka yatsansa cikin carpet din qasa,yana caccaka yatsansa cikin carpet din
dakin, fuskarsa babu yabo babu fallasa,sadiq
kuwa sai faman shafa sumar kansa yake yana
murmushi
'"Waye babba a cikinku ne?,ya fara magana"
malam ya fada ganin alamun jin nauyinsa sun
bayyana a fuskokinsu
"Nine" sadiqu yayi hanzarin fada,abunda yasa
lamin daga kai,ya jefeshi da harara kai
tsaye,murmushin fuskarsa kuma ya dara na dazu
"Mara kunyar banza, mayen aure kawai"
"Babu komai,ni ai tawa maitar ce ta fito fili,amma
dai na tabbata bankai wanda kusan duk asuba
kafin ya tafi sallah sai yayi wanka ba"harara, auk magandr dd sukdy Can gas sukdyI,la
yadda babu mai iya jinsu,saika dauka wani abun
suke tattaunawa,lamin din baisan duk abinda ke
faruwa dashi sadiq din yana sane ba sai
yanzu,tabbas badon su malam na wajen ba sai
yakai masa mugun naushi
"To malam babba,muna saurarenka" malam ya
fada yana crossing qafafunsa waje guda,qas yayi
dakai yana sake shafa kan nasa
"Eh....ni sunanta fatima,gidansu yana unguwar
dorayi,sunan mahaifinta alhj usman"
"'Ma sha Allah,ka rubutan cikakkem address da
komai,zan sanya ayimun bincike akanta kafin ka
shaida mata ta gayawa iyayenta su saurari
zuwanmu.
"'In sha Allah" sadiq ya furta kansa a "To... kaifa malam aminullahi" malam ya furta
yana murmushi,idanunsa akan lamin
din,hakanan zuciyarsa,wadda ke cike da fata da
buri,duk da jikinsa yana bashi abune mai wuya
gurguwa da auren nesa inji bahaushe,koda
burinsa da fatansa basu samu tabbatuwa ba
bayajin cewa hakan rashin kyautawa ne face
tsantsar adalci da zai gwada masa. Ba malam kawai ba,hatta da inna idanunta
akansa suke,duk da tana kallonsa ne afakaice,ta
yadda babu lallai ka gane kallon nasa take kai
tsaye,haka kawai ta tsinci zuciyarta na bugawa
fiye da yadda ta saba buga matan,itama nata
idanun cike suke da fata da kuma burin,burin da
itama rashin tabbas yafi rinjaye a cikinsa,iman
kuwa......gaba daya rinse idanunta tayi,tanajin
inama ace mallam bai gayyaceta wannan waje
ba,inama ace ita daya ya kebe?,saidai amsar data
fito daga bakinsa zuwa ga malam ta sanya taji
gaba daya jikinta ya dauki rawa, kamar wadda
aka yiwa wanka da ruwan qanqara "Sunanta samha,mahaifinta alhj mutallab
garba,a unguwar court road take,nan wajen
tudun murtala,duk wanda ya nemi gida
mahaifinta zaa kaishi har can" Nannauyar ajiyar zuciya inna ta sauke tana
saukar da idanunta qas, wani abu na son rige
zuciyarta amma tana yaqi dashi,cikin taimakon
Allah ta kawar dashi,saidai zuciyar gaba daya taqi
karbar yanayin da lamin din yazo dashi,saidai a
hakan tana gayawa zuciyar tata,dole ta rusuna,ta
kuma karbi dukkan abinda lamin din yazo dashi a
matsayin zabi hannu bibbiyu.
"Ma sha Allah,alhamdulillah" malam ya fada
wani nauyi yana cika muryarsa,yana kuma rage
armashi da karsashin maganarsa "Kai bani da matsala, unguwar tasu ina da aboki
acan,malam gambo,zan masa magana akai,idan
ya kammala zan shaida maka kaima ta shaidawa
iyayenta"
"Allah ya qara girma da lafiya" lamin din ya amsa
yana russunar da kansa ga malam
'"Amin amin" ya amsa yana waiwaya gefen iman
"To nazo kanki auta" yayi furucin yana
murmushi,saidai kiranta da malam din yayi wani
nauyi taji ya hau kanta,tanajin kamar gaba daya
mutanen duniya aka tara mata suke kallonta
suna kuma sauraren ta basu amsa game da wani
in baracu tanail a
suna kuma sauraren ta basu amsa game da wani
gagarumin al'amari daya tunkarosu,tanaji a
ranata da zuciyarta wanna shine titsiye mafi
wahala da kuma fargaba da zata fuskanta tsahon
rayuwarta
"Waye shi?,a ina kuma yake?" Malam ya jefa mata
tambayar da shi kansa yasan babu lallai a samu
cikakkiyar amsa daga bakinta,tunda dai bai taba
jin anyi zancan wani cikin gidan ba tun bayan
fitowarta daga gidan bassam,kuma shi shaidane
na yadda take barin samarin nata a waje,wani
lokaci sadiq yake sawa ya sallamesu. Yatsanta takeson ta motsa wai don ta tabbatar
qwaqwalwarta na aiki kuwa yadda ya
kamata? idan tana aiki wa zata kira sunanshi ta
gabatarwa da malam shi?,wa take saurare?, waye
ta bawa damar da suka fahimci juna da zai iya
tsayawa a mizani da ma'aunin mijinta?,idan duka
ya cika wadan nan yana da gurbi a
zuciyarta?,gurbin da zai bashi damar zama
mijinta?,ta zauna dashi cikin soyayya qauna da
kulawa?,sam!…...duka biyun babu ko daya da
wani da namiji zai samu daga gareta. Akwai dimbi tulin tarin masoya,saidai babu
wanda ya samu koda taku daya na fili a zuciyarta
da sunan tana so qauna ko jin shaugi a
kansa,mutum daya ne dai tak!,wannan wanda
yafi kowa sanin wacece ita duk duniya.......wanna
wanda yafi kowa sanin ciwonta!..
......wannan
wanda baya ga iyayenta shi daya zai iya tsaiwa ya
gayawa duniya wace ita ya kuma tabbata
hakanne!….
...Wanda koda yayanta da suka kwanta
ciki daya,tanajin bashi da wannan qwarin gwiwar
da kuma cancantar.
„.shine dai kuma mutumin
data butulcewa!…
„..butulci mafi munil,ta karya
zuciyarsa!,ta iya kallon tsabar qwayar idanunsa ta
shaida masa BANA SONKA! ,ALLAH YANKIYAYE NA
AUREKAI,DANA AUREKA GWARA NA KASHE
KAINA!,ta zame masa KUFAN WUTA!,ta tafi ta
barshi da tarin tabo da ciwo!,ta zabi waninsa,waninsa din da baisan ciwonta ba,ta
kasa waiwayarsa,zuciyarta ta dode,ta kasa tuna
komai,ta kasa tuna wayeshi a tare da ita,taji masa
mummunan ciwon da ba kasafai masoya ke
warkewa ko su mata ba.....shin a yanzu,a dalci ne
ta tsammaci samun juyowar soyayyarsa
gareta,ko kadan. Take kwanyarta ta fara mata
hasashe da laluben cikin masoyanya dake
karakaina,wadanda suketa turo da applications
nasu waye ya cancanta?,wa take gani ya kamaci
ta gabatar da sunansa?, waye zai hau mizani ko
nagartarsa zata iya maye mata koda kwatar
kwatar wannan babban gibi?
"Dr Ahmad" ta samu kanta da furtawa ba tare
data gama tantancewa ba,ita kanta sai da sunan
ya fita sannan ta tsaya tuhumar kanta,yaushe ta
bashi damar da yaketa nema akan zuwa ya
sameta su tattauna har suka gama fahimtar juna
Ladaamanchi7tamhavar data dashi?,da har zata bada sunanshi?,tambayar data
sake sauke duk wata gaba ta kuzari datayi saura a
jikinta
"Wayeshi?" Malam din ya tambayeta kanshi tsaye
idanunsa a kanta,zuciyarsa nata fadin inama
inama.…...saidai dole abar komai a yadda yazo,yafi
tunanin haka Allah ya tsara,bayason yiwa kowa
shishshigi cikin al'amarinsa
"Likitan da nake gani ne"
"Kin tabbatar?" Ya jefa nata tambayar dashi
kansa yasan bata gama cika ba,yana fatan ko
yaya ne hankalinta yakai kai
"Eh" ta amsa tana gyada kai,tare da bawa kanta
qwarin gwiwa.
"To ba laifi, ki bawa wani cikin yayunki address
dinsa da komai da komai,ubangiji ya zaba mana
abunda yafi alkhairi,Allah yasa kuma dukkaninku su zamto silar qarin arziqi da shiga aljannarku"
"Amen" muryoyin mutum uku suka amsa,banda
iman da bata gama tantance wanne hukunci ta
yankewa kanta ba,me kyau ne ko mara
kyau,waye dr Ahmad a badininsa,meye
halayyarsa,duka bata sani ba,illa dai tasan kawai
ta bawa malam sunansa. addu'a malam din yasa
alameen ya rufe musu da ita,zuciyarta ta dinga
bugu kamar zata faso qirjinta sanda daddadan
muryarsa mai taushi ke fita cikin sautin addu'ar
da yake karanta ga da harshen larabci, murya ce
mai tarin daraja da muhimmanci a wajenta,iya ita
kadai idan taji yana saukar mata da wata
nutsuwa,saidai a yau jin muryar ya haddasa mata
tara qwalla mai yawa cikin idanunta,tana kuma Tuna mata da cewa tayi bankwana da zama mammallakiyar me murya da dame ita sun kusa zama malamin wata A sanyaye inna ta taso daga inda taje zaune bayan malam ya sallamesu,ta qaraso inda ta
ajjiye kwanukan abincin malam din ta fara
budesu a nutse,ta zuba komai yadda ya
kamata,sai ta koma ta zauna wajen,
Kallonta yayi,kamar zaiyi magana sai kuma ya
fasa,ya dauki kwanon abincin,ya saka hannu
kamar yadda ya saba yayi bismillah ya fara ci.
Kasa hadiye abunda ke ranta inna tayi,gani
take kamar ba yanzu malam din xai gama cin
abincin ba,kamar baya sauri,sannan uwa uba
yanayinsa bai nuna zaice komai ba
"Malam…..….kagayadda abun ya kasance ko?" Kai
ya gyada
"Eh,Allah ya sanya hakane yafi alkhairi" sosai
fuskarta ta nuna damuwa "Amma malam shikenan kuma?,me yasa ba zaka
ankarar dasu ba?,me yasa ba zaka qarasa aikinka
ba?" Tsame hannunsa yayi daga abincin,ya
ajjiyeshi a gabansa, murmushin dake cike da
kamala dattako da dattijankata ya subuce masa
"Ashe duk abubuwan da akewa hajar ana sonta
har yanzu?" Kai ta karkada,tasan malam din yana
sha'awar tsokanarta ne kawai, banda haka har
akwai wanda ya kaishi son iman din,da rashin
son ganin abunda zai zama illa ko aibu ga
rayuwarta,maida dubanta tayi gareshi ba tare
data iya bashi amsa ba,shima a sannan fuskarsa
ta koma serious
'"Duk yadda kikai ga son ganin iman da amin sun
zabi junansu baki kaini ba binta,kullum ko a dare
ko a rana idan na saka goshina a qasa,ad du'ata ko a rana idan na saka goshina a qasa,addu'ata
itace,ya Allah idan da alkhairi a tarayyarsu,idan
har tarayyarsu zata zama wani sabon mataki
kuma tsani na dorewar zumunci da ganin
mutuncin juna muda 'ya uwan aminu Allah ya
qulla,idan kuma har tarayyar tasu zata haifar da
sharri,yankewar zumunci ko tabarbarewar
al'amura,Allah ya hada kowa da rabonsa na
alkhairi.
.…..ta iya yiwuwa ubangiji ya duba cewa
babu alkhairin,shi yasa ya aiko da abun a
haka,…...idan mukace zamu matsa ko mu takura
to tabbas zamu yiwa Allah shishshigi ne,sai ya
qyalemu da iyawarmu muyita shan wahala,kuma
bugu da qari shi kansa yaron bamuyi masa adalci
ba,a baya bamu iya tanqwara diyarmu ta aminta ba,a baya bamu iya tanqwara diyarmu ta aminta
dashi ba....sannan kuma a yanzu shi zamu
dubeshi muce ya auri diyarmu?,bayan ina da
tabbacin ko ruwa mukace ya fada zai fada babu
musu?,ba dai dai bane wanna,saboda haka, mu
tattara muci gaba da gayawa Allah,da kuma
addu'ar zabi mafi alkhairi" .
Kai inna take jinjinawa,ta yarda ta kuma gamsu
da bayanan malam,babu son rai ko son zuciya a
cikinsu ko kadan,hakanan sun sake saukar mata
da nutsuwa,saboda haka ta dai data kanta,tare
da fadin "Ubangiji yayi zabi mafi alkhairi"
"Amen bintu" sunan da ya saka inna sakin
murmushi,shi kuma ya dauki plate dinsa yaci
gaba da cin abincin,yana kuma janta da hira.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 52
Empty take jin qwaqwalwarta sanda take takowa daga parlor din malam zuwa dakinta,fayau take jinta kamar wadda ke tafiya saman iska,kwanyarta kamar an share mata komai,ba zata iya tantance a wanne yanayi take ciki ba.
Tana saka qafa a dakin wayarta dake charge ta dauki ruri,ta ja qafafunta zuwa inda wayar take,don dama tana da buqatarta,ta riga ta sani,malam din baya daukar magana biyu,don haka tunda ta furta dole tasan yadda komai zai tafi.
Dr Ahmad shike kira,tamkar yasan dambarwar dake faruwa a kansa,taja da baya a hankali kamar zata zube a qasa,sai kuma Allah ya taimaka ta samu gefan gadon ta zauna,ta latsa wayar dai dai lokacin da take dab da katsewa.
Ajiyar zuciyarsa ce ta fara sauka a kunnuwanta,kafin daga bisani yace
"Ni kadai nasan damuwa da kuma dimuwar da nake shiga,duk sanda na kwadaitu da son jin muryarki,na taki rashin sa'a baki daga kirana ba"
"Duka wannan ta qare, finally iman na gayyatarka zuwa gidansu a yau" sak yayi a wajen kamar wanda jinin jikinsa ya qare,daga wayar yayi ya kalla,ya kuma tabbatar iman din ya kira,amma duk da haka.....mamakin da ya shiga yasa ya kasa shuru
"Idan wasa kikemin,ki tamakeni ki gayamin,kada sai daga baya,saboda wallahi zuciyata ba zata iya daukan wannan wasan ba"
"Mun taba irin wannan wasan dr?"
"Ko kusa"
"To kana iya daukarsa duk yadda kaso,either ka daukeshi da wasanne ko kuma ka daukeshi a gaske" saita zarta yatsunta ta shafe wayar ta kashe,ta kuma zame a hankali ta kwant a wajen.
Jinjinawa girman katobara da kuma aika aikar da take shirin yiwa rayuwarta tayi,tasan cewa ba komai ta aikawa kanta da kanta ba illa wani dan qaramin ta'addanci da zai iya zama silar wargajewar dukka wani farinciki a rayuwarta na din din din,ko sau daya bata taba jin dr Ahmad a koda gefan zuciyarta ba.....kai bama shiba,tana jin hakanne akan kowanne da namiji illa halitta daya,abu daya ta sani shine,tana matuqar ganin girma da kimarsa,saboda kasancewarsa nagartaccen mutum,hakanan kuma nutsatstse ne,bashi da makusa tako ina,saidai ita zuciyarta ba wannan take hange ko kuma kalla ba,duk wani bugunta da fitar numfashinta qwalli daya tak tana kiran al'ameen ne,saida shi din yayi mata nisan kiwo,nisan dake alamta mata bazaiji kiranta ba.
Idan taqi zaben dr ahmad hakan bazaisa malam ya qyaleta da zancan aure ba,idan bata zabi dr ahamd ba batasan kalar wanne zata zaba ba,qila a sannan babu me quality dinsa ma sam a kusa.
Waiwayawa tayi tana duban tex din daya shigo wayarta dava dr Ahmad
"Godiya tayi kadan wajen bayyana miki farincikina da kuma yabawata da karramawar da kika yimin a yau,ki zuba idanun ganina,ki kuma tanadi wanne kalar tukuici zan baki" rufe wayar tayi haskenta ya bace daha screen din,ta lumshe idanunta kana ta maidashi wani side din cikin rashin sanin madaafa.
Wata iriyar juriya da dakiya ta ara wadda bata taba tunanin samunta anan kusa ba,to juriyarce ma ko kuma zuciyarta ce ta gama qeqashewa?,ta qone babu wani qauri yanzu da yayi saura?,ta fita tayi aikace aikacenta tana qarfafawa kanta gwiwar cewa,babu ita a zuciyar ameen ya kamata itama ta fiddashi daga tata zuciyar,ya kamata ta jingineshi ta fuskanci reality dinta,a haka ta gama girkin rana ta kuma dora dana dare.
Loma daya inna tayi a abincin ta sake kallonsa cikin mamaki,saboda a yau girkin sam baiyi kama dana iman din ba,qwararriya a fannin girki,tarin kura kurai fal cikin abincin,saita qyaleta bata yi mata magana ba,saidai ta leqo sanda take ta hidimar hada sanwar dare ba tare da ita ta sanyawa cikinta koda qwayar shinkafa ba tun tea din safe tace da ita
"Ki tattara hankalinki waje daya iman,yau din akwai yiwuwar malam zaiyi baqi,kiyi abinci me kyau"
"To inna" ta amsa mata da salon son nuna she's okay
"Ko na turo miki mufida?"
"Qyaleta inna,damuna zatayi da surutu" kai ta jinjina kawai,uwa uwa ce,ta karanci zallar damuwa kan fuskarta,duk da qoqarin boyewar da take,saita juya ta fita ranta fal damuwa,cikin zuciyarta tana cewa
"Ya hayyu ya qayyumu,ya rahmar rahimin,bi rahmatika nastagisu ya Allah".
Karfe biyar da ashirin da bakwai ya shigo gidan,ta jiyo muryarsa a parlor amma bata taba kawowa kanta zai qaraso kitchen din ba,wannan amannar data yi ya sakata ta sakankance,taci gaba da yanka albasa saman chopping board,a hankali kamar wadda ke yankae naman jikinta,saboda yadda zuciyarta da gangar jikinta ke neman gazawa da yaqin da take tayi da kanta kan hana kanta tunane tunane.
A hankali yake takowa zuwa kitchen din,hannunsa dauke da cup din daya cika da damammen fresh yoghurt na L&Z da fura,bai samu suger a parlor din ba,shi yasa ya yanke qarasowa kitchen din,mufida yaso bawa ta zuba masa,saboda baison zaqi da yawa yasa ya yanke zuwa da kansa.
Yana saka qafarsa ya hangeta,bai tsammaci tana cikin kitchen din ba,sai ya dakata daga bakin qofar kitchen din saboda babu hijabi ko mayafi a jikinta,yayi matuqar qoqarin ganin ya hana idanunsa qare mata kallo amma hakan yaci tura,kamar wanda ake ingizawa ya bita da kallo,tun daga qafafunta dake sanye da slipper na robber zuwa sama,skart dinta daya zauna sosai a jikinga ya fidda shape na qugunta,hakan rigar jikinta duk da cewa gefenta daya yake iya hangowa,gashinta dake daure cikin dankwali ya fito ta qasa yabi bayanta sosai ya kwanta,saboda gashin buzaye gareta irin na inna.
"A'uzu billahi minash shaidanir rajim" ya furta a hankali cikin zuciyarsa,jin wani abu ya fara yawo cikin jininsa,sai yaja da baya ya koma a hankali,yana fatan kada ta ganshi gudun zubewar mutuncinsa a idanunta.
Mufida dake kallo a parlor ya miqawa
"Jeki ki kai mata ta zubamin,amma kada ya wuce cokali daya,sannan kice mata idan babu mayafi a jikinta ta nema ta saka"
"Tom" yarinyar ta fada tana miqewa da sauri ta karba tayi kitchen din,ya zame a hankali ya zauna saman kujerar yana sauke ajiyar zuciya yana ci gaba da kiran sunan Allah tare da korar shaidan daga zuciyarsa,jiran fitowar mufida ya amsa furar ya wuce ne kawai ya tsaidashi,amma banda haka da tuni ya tsufa a daki,don dama yunwa ta dawo dashi ya shigo ya samu abunda zaici ya koma,to abincin da zaici ya tarar yayi sanyi,shi kuma bai iya cin abincin daya huce har haka ba,inna tace yayi haquri a gama na dare,don dama girkin ba kowa zainiya cinsa ba,wannan ta sanya ya nema furar.
Idanu iman ta zubawa mufidan sanda take gaya mata saqon ameen din
"Na nemi mayafi na saka?,kenan ya shigo?,yaushe?" Duka ta maimaita tambayar wa kanta da kanta,sai data karba cup din xata zuba masa sugern hancinta ya zuqo mata qamshin turarensa wanda ya tabbatar mata da shigowar tasa,to amma batasan yaushe ba,kuma har ya fita bata ganshi ba.
Tana gama afawa ta miqawa mufidan,sannan ta janyo hijab dinta wanda tun dazun dashi ta shigo ta saka taci gaba da yankan albasarta.
Ta sake komawa duniyar data fito wato duniyar tunani,tayi nisa sosai,har bata iyajin motsin abinda ke gefe ko kusa da ita,a hankali hancinta ya fara shaqo mata wannan mayen qamshin,qamshin da aduk sanda ta shaqeshi saiya birkita mata duk wani lissafinta,tadan tsaida yankan albasar,tanajin kamar akwai mutum a cikin kitchen din,kuma a gefanta,kamar duminsa ma take ji,ta waiwaya a hankali take fuskarta ta fada cikin tashi.
Kwayar idanunsa cikin tata yake kallonta,dab da ita yake tsaye,riqe da cup din a hannunsa,take dukkanin jikinta ya amsa,saita dan matsa kadan kamar yadda shima yaja baya,yabi albasar da take yankawa da kallo,koshi da yake namiji amma sam baiga nutsuwa cikin aikinta ba,hasalima wata albasar bata gama baruwa gaba daya ba
"Ya akayi aka zuban gishiri instead of sugar?" Yayi maganar da lallausan muryarsa wadda ta sake kashe mata jiki.
Cikin dakiya ta fiddo idanunta waje
"Gishiri?,sugar dai" ta fada adan daburce,batason yadda yaje kafeta da mayun idanunsa,ita kadai tasan me yake bar mata,wanda a yanzun wannan yanayin da yake barwa jiki da zuciyarta zai iya zama barazana ga dukkan wata jarumta data shirya aiwatarwa.
Cup din ya miqa mata kawai batare da yace komai ba yana ci gaba da kallonta,a hankali ta miqa nata hannun zata amsa,abunda ya kawo haduwar yatsansu waje guda,kowanne kuma ya janye hannunsa, cup din yayi qas zai fadi ya tarwatse,cikin wani zafin nama da kuma mazantaka ya sanya daya hannun nasa ya taroshi,sannan ya dorashi saman drawer din kitchen din,ya taka a hankali ya rabeta,ya dauki wani cup din da kuma sugarn ya fice a kitchen din a hankali,yanajin yanayinsa kamar yana shirin canzawa zuwa wani irin feeling dake kashe gabban jiki,wanda a yanzu baya nemansa ko fatan zuwanshi.
Hannayenta duka biyun ta saka ta kama kanta sosai,tana tambayar kanta da kanta meye yake damunta ne haka?,me yasa ta gaza samun nutsuwa?,saita matsa inda ya ajjiye cup din,ta saka yatsanta ta lakaci furar ta dandana.
Tabbas gishiri ne ta zuba maimakon sugar,ta sauke ajiyar zuciya mai matuqar nauyi,kamar zata hado da zuciyarta,ta tura cup din cikin sink,ta matsa wajen chopping board din ta dauki wuqar tana kiran
"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" taci gaba da yankan.
*_BAYAN WASU AWANNI_*
Sosai ta tsurawa kanta idanu a gaban madubin,cike da wasi wasi da kuma tunanin anya abunda take shirin aikatawa shine dai dai?,to idan ba dai dai bane meye yafi dacewa ta aikata din?,me zatayi?,zata zauna ne har sai ruwa ya qarewa dan kada ko kuwa?.
"Ya iman,baqonki yazo" muryar mufida ta katse mata tunaninta,ta waiwaya a hankali ta dubeta
"Yana ina?"
"Yana qofar gida,amma naga ya ameen ya masa iso,ya bashi kujera ma ya zauna"
"Ya ameen?" Ta fada cikij dimbin mamaki
"Eh,sun gaisa ma sannan ya wuce" baya tayi a hankali ta zube saman gadonta,ya ilahi me ameen yake buqata da ita ne?,ko sai ya manna mata ciwon zuciya zai qyaleta,sai yaga ta haukace sannan zai daina nunawa duniya ya daina yi da ita?,kullum kwanan duniya sai yayi abunda zai tabbatarwa da kowa baya qaunarta baya kuma kishinta,ta gaji da gani hakanan,yana kasheta ne ba tare da kowanne makami ba,ya kamata yabarta hakanan
"Me za'a ce masa?" Mufidan ta katseta
"Kikai masa ruwa da lemo,ina zuwa" ta fada ba tare da tana da tabbacin iya futar tata ba.
Ta jima zaune a wajen tana dai daita kanta sannan ta miqe,ta fesa turare sama sama,ta yafa mayafin daya dace da kayan jikinta sannan ta fito,takunta a kasalance,zuciyarta babu dadi ko kadan,ta gayawa inna ta fita,innar ta bita da kallo
"Saikin dawo" ta amsa mata a sanyaye.
Tunda ta fito idanunsa na akanta,murmushin dake nuna zallan farincikin da yake ciki yaqi gushewa daga kan fuskarsa,miqewa yayi kafin ta iso ya kuma gyara mata kujerarta
"Barka da fitowa sarauniyar mata"tale labbanta kawai tayi ta yadda tsokokin fuskarta suka bada shadow na murmushi,don kwata kwata babu wani digo na farinciki da zai haifar da murmushi na ainihi a saman fuskarta
"Barka kadai likita,ya na ganka kai kadai?,ina babyn?" Ta tambayeshi tana shirin zama
"Milha?,tana wajen mamanta" shima ya amsa mata yana zama
"Halan batasan zaka fito zance ba?" Ta tambayeshi tana qoqarin bude masa robar lemo,duk a qoqarinta na kauda dukka wani alamu da zai alamta samuwar matsala rashin walwala ko takura a tattare da ita.
Dariyarsa taja hankalinta
"Da kin zaci diyata ce kenan?,eh diyata dince,amma bani na haifeta ba,'yar lil sister dina ce......any way na godewa Allah,ko babu komai hakan yana nufin ana kishi na" murmushi ta qirqira kadan tana aje masa cup din.
Baibi takan lemo ba sai gaisuwa da suke sabuwa,ya kuma gabatar mata da kanshi,cikakken suna da tarihinsa,ya kuma sake jaddada mata soyayyarsa sannan ya rufe da cewa
"Ina fatan za'a karbeni a yadda nazo,gani dai qaton tuzuru ne ni,wanda yasha gori har ya godewa Allah" murmushi tadanyi kawai kanta a qasa tana murza yatsunta
"Idan har kin aminta dani,kin kuma amince zaki aureni,toki gabatar dani ga malam,ba dogon lokaci nakeso a dauka ba,so nake ayi komai a gama ki zama mallakina"
"Amma bakajin ka tauyi kanka,kana saurayi zaka fara da bazawara?,ba kuma zaka samu matsala daga gida ba?"
"Wace bazawarar?" Yayi tambaya yana dube dube,kamar me neman wani abu,lamarin da yasa dole murmushi yafita daga fuskarta
"Ki ajjiye wannan batun please,bashi ake yayi yanzu ba,ana yayin samun nagartaccuyar macene,wadda ta fito daga gidan tarbiyya" saita jinjina kawai bata iya cewa komai ba.
Bai jima sosai ba yayi mata sallama,yana jaddada mata ta gabatar dashi,ga komai nashi da ake buqata suna iya yin bincike a kansa,ya tafi ya barta da gift na zobe mai kyau,wanda bai bar wajen ba sai daya tabbatar ta sanyashi a yatsanta,ya zauna kuma yayi matuqar yi ma zara zaran fararen yatsunta kyau.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 53
Kwanakin da suka biyo baya gaba daya gidan cikin hidima da shiri suke na bikin bude katafaren kamfanin ameen din,wanda suke samar da dukka wani nau'i na suttura na qasashe daban daban,kama da dinkakku da wanda ba'a dinka ba,na maza da mata yara da manya,abayas ne yadididdika laces harma da mayafai takalma da jakankuna,ga bangaren qwararrun teloli da yanzu yanzu ka siya kaya za'a canza musu kamanni da dinki na kece raini kowanne kala kakeso,wajene da zai kafa tarihi mai dimbin yawa,kuma guri ne da duk wanda ya kalla sai ya juya ya sake kallonsa,shi kansa ameen din ya qarar da duka abinda ya mallaka a wajen,saidai sam bai damu ba,sabida yana da kyakkyawan zato da kuma fatan zai maida adadin abinda baisan yawansu ba.
********Yammaci ne lis,wanda yayi dai dai da washegari itace ta kasance ranar juma'a,ranar da za'a gudanar da bikin bude companyn IB COUTURE,ya zabi ya sakawa wajen sunan malam ne,saboda girmamawa a gareshi,da kuma nuna jin dadinsa da godiyarsa bisa halaccin da yayi masa a rayuwa.
Zaune suke a 'yar qaramar harabar gidan ita da dr,wanda wannan shine zuwansa na biyu bayan malam ya bata saqon ta shaida masa cewa ya turo da magabatansa,ya gama bincike a kansa ya kuma tabbatar da ingancinsa.
Gaba daya ya sanyata a gaba da kallonshi,ya kasa boye mata abunda ke ransa,farinciki zumudi da kuma fatan zuwan ranar da zaace ta zama tasa
"Allah yasa kada malam ya saka doguwar rana" dan dubansa tayi
"Ka shirya kenan?"
"Na dade ai a shirye Hajiya,ke kadai nake jira dama" murmusawa tayi kadan
"Inda zai tambayi shawarata,zance masa a bari sai na gama dukka sauran watannin da suka ragemin a makaranta,saboda hankalina yafi tattaruwa waje daya"
"Mene?" Yafada da sauri yana fidda idanu,sai kuma ya hade tafukan hannayensa waje daya
"Ki rufamin asiri,kar kimin haka,indai makarantace baki da matsala dani,practical dinma sai kiyi a asibitina,koda bakiyi ba gaki ga likita matsalan me kike dashi?" Dai dai sannan aka tura dan madaidaicin gate din gidan mota ta fara yunqurin shigowa.
Dauke idanunta tayi sanda ta fahimci motar alameen ce ke shigowa ta maida wani sashen daban kamar bata ganshi ba,batason su hada ido ko waga magana ta hadasu bare zuciyarta ta karye,duk wani guntun qwarin gwiwa data tattaro ya zagwanye ya barta da tarin rauni.
,don haka ta waiga da dan sauri.
Yaya baraka ce,miqewa tayi a nutse murmushi na subucewa daga fuskarta,matar nada kima da daraja a idanunta,ko sau daya kuma ko a fuska bata taba nuna mata wani canji ba kan abunda ya faru tsakaninta da alameen ba,yadda ta saba mata har a lokacin da kuma yanzu babu wani abu daya canza
"Yaa baraka....." Ta kirayeta tana qarasawa bakin motar,fuskar iman qunshe da murmushi,sai itana ta juyo tata fuskar kamar gonar auduga
"Hajaru hanjartu" sunan da take kiranta dashi tun zamanin quruciya,tun sanda suke zuwa mata hutu jigawa
"Sannu da zuwa yaya,ashe kina hanya?" Ta fadi tana duban 'yar budurwar diyar yaya barakan,wadda a hakan itace autarta
"Wallahi dai kin gani,sai da aminu yaje ya daukoni,wai lallai sai nazo bikin buda kamfani,ni kuma naga me zanzo nayi ga inna ga malam,sai yace wai malam dinne yace lallai lallai nazo din"
"Gaskiya ne,ai ya kamata" iman din ta fada har yanzu fuskarta da murmushi,tana kuma dauke idanunta daga kewayen da ameen ke tsaye,ta fara qoqarin amsar jakar hannunta,diyarya badi'a tana gaida iman din,ta amsa mata cikin kulawa tana sake cika da mamakin girman badi'a,yarinyar da idan sunje qauyen take goyata a baya,ta taya yaa baraka rainonta.
Ita tayi musu jagora zuwa cikin gidan suna taba hira abunsu da yaa barakan a sake kamar yadda suka saba a baya,kusan daura da dr ahmad xasu wuce,don haka tadan dakata sanda ya miqe tsaye yana gaida yaa baraka
"Bari na rakata ciki"
"A fito lafiya" ya bata amsa cikin nuna kulawa,ya bi iman din da kallo,abinda yasa ya gaza ganin tahowar ameen,har sai daya kusa gotashi.
Cikin girmamawa ya bashi hannu sukayi musabaha,sannan ameen din yayi gaba,saidai kafin yakai ga qarasawa ya dakata,ya bawa sayyadi jakar kayan nasu yace ya qarasa musu da ita ciki,sai kawai ya koma cikin motarsa ya tasheta ya fita daga gidan.
Sosai suka kaure da murnar ganin juna ita da inna,don an dan kwana biyu ya barakan batazo garin ba,an saba da juna an zama tamkar 'yan uwa,har kowacce tsakanin inna da yaa barakan takejin 'yar uwarta cikin jikinta sosai.
Bata baro ciki ba sai data tabbatar inda yaa barakan zata zauna ya saitu,ta samu dr ahmad din ma yanata waya,fitowarta yasa ya sauke wayar,ya tarbeta da murmushi
"Barka da fitowa gimbiya" murmushi ya kubce mata,taja kujera tana shirin zama qofar gidan ta sake budewa,saita maida hankalinta ga can maimakon zaman.
Tun kan ta qaraso fa ganeta,bushira ce,suna hada idanu suka sakarwa juna murmushi,ta miqe tana tunkararta
"Wata sabon gani,yaushe a gari inji maqi baqo?" Iman ta fada tana dariya,harara bushira ta watsa mata
"Au haka ma zakice?"
"Tuba nake" iman ta fada tana fadada murmushinta,saboda tasan ta yiwa bushiran laifi,sai suka gamu a hanya sannan suka sake takowa zuwa ciki
"Dr......ga childhood friend dita,sunanta bushira" iman ta fada sanda suke qarasowa inda dr ahmad ke zaune.
Cikin fara'a suka gaisa da ita,kasnacewarta itama bushiran gwanar kirki ce da fara'a,sai ya miqe
"Hajjaju zan wuce gaskiya hakanan,na fuskanci kina da baqi da yawa yau,bari na basu aronki na yau kawai" murmushi tayi sannan ta taka masa har qofar gida inda motarsa take fake sukayi sallama ya wuce,sannan ta dawo ciki.
A inda dr ya tashi ta samu bushiran zaune tana jiranta,hannunta riqe da wayarta
"Waye wannan kuma?" Bushiran ta fara da tambayar iman sanda iman din ke saka jan kujera daya ta zauna akai
"Ba zamu koma ciki ba kika zauna a nan?" Iman ta maida ma bushira tambayarta da tayi
"Nan dinma ai yayi,mu gama gaisawa dake,saiki rakani ciki na gaida inna" kai iman din ta gyada,shuru na kusan sakan uku ya ratsa sannan tace
"Ya kika ganshi yayi ne?" Tayi tambayar da dan guntun murmushi saman fuskarta,murmushin da ya sanya bushira ta zuba mata idanu kafin ta amsa mata
"Yayi,bashi da wata makusa,yana kuma da kirki a idanu"
"Haka dabi'arsa ma ta badini da malam ya bincika" kai bushira ta jinjina
"Wayeshi din?"
"Dr Ahmad, shine wanda zan aura" tayi maganar babu wani armashi ko confidence a tattare da ita,ido bushira ta zuba mata sosai,ta buda bakinta a hankali
"Ina kuma ya lamin din?" Lumshe idanu iman tayi,ta kuma bude lokaci guda tana girgiza kanta,yanayin fuskarta ya canza a take
"Yafi qarfina zuwa yanzu,don kuwa ya fitar da wata matar,ya lamin ya kasa gane duk wata kulawa da nake bashi soyayya ce,ya kasa gane duk wani motsina a kansa zazzzafar qauna ce,ya kasa fahimtar furucina motsina da aiki na,kamar yadda yake fahimta a baya" sosai bushira ta gyara zama ta kuma ajjiye wayarta,tana iya hangen wani pain mai kaifi daga zuciyar iman din
"Indai har ya lamin ya cancanci a soshi,me yasa zaki jira sai ya gano wani motsi da action naki?, just go straight forward.......ki sameshi ki furta masa kamar yadda ya furta miki,meye a ciki?,dan uwanki ne kuma yayanki ne" kai iman ke kadawa a hankali a hankali
"Bazan iya ba bushira.....bansan ta yaya zan tari namiji nace masa ina sonshi ba,karfa ki manta,har abada ni din diya macace,ya ameen kuma namiji ne"
"Akan hakan kin gwammaci ki rasashi?,kin gwammaci wata ta sameshi?"
"Ina addu'a,kuma Allah yana sane idan har na cancanci na sameshi ta kowacce hanya bazai hanani shi ba,idan kuma ahmad ya zabarmin na gode masa,bazan iya cusa kaina zuwa ga wulaqancin namiji ba bushira,a wannan matsayin da nake kai,addu'a da tattarawa ubangiji lamarina shine kawai abinda yafi dacewa dani"
Kai bushira ke jinjinawa,sosai iman tayi matuqar bata tausayi,maganganunta akan hanya suke,tabbas kowacce mace tana buqatar kare martaba da kuma kimarta wajen namiji kodon gaba,amma ita a nata hasashen,case dinta dana alamin daban yake da sauran cases.
Miqewa iman tayi tana daukar jakar bushiran
"Mu shiga ciki bushira,mintuna kadan suka rage a kirayi magrib" miqewa tayi tabi iman din,tana kallon yadda aketa kokawa tsakanin zuciyarta da kuna qwarin gwiwar da take dashi.
******yadda gurin ya qawatu haka ya cika da jama'a wadanda suka halarci taron bude kamfanin,sosai kamfanin ya qayatar,ya kuma bada mamaki fiye da zato,waje ne mai girma da tsari,kowanne sashe daban.
Floor na farko anan masu dinki suke,dinki kowanne nau'in sutura,second floor wanda xaka hau sama shi kuma anan suke ajjiye kowanne kaya da aka gama hadasu dama wadanda ba'a dinka ba game son siyansu a haka,da sauran tarkacen su takalma da kayan ado,third floor kuwa acan office na mai kamfanin wato lamin da sauran ma'aikata yake.
Bayan bude kamfanin ta hanyar yanke wani dan zare,tarin 'yan press suka cika ma'aikatar,aka kuma gama komai akan idanunsu,sannan akayi qwarya qwaryar walima jama'a suka shiga suka ga yadda waje yake da ayyukan da za'a dinga gudanarwa,daga nan wasu suka fara ma lamin sallama da fatan alkhairi,abunda ya fara rage cinkoson kamfanin.
A hankali take takawa cikin kamfanin,bayan an ajjiyesu waje na musamman ita da inna da mufida an gabatar musu kayan ciye ciye da shaye shaye da kowa yaci a wajen,sosai kamfanin ya burgeta,tana kuma jinjinawa lamin na yadda ya zama tsayayyen namiji,bai bar sana'arsa ta asali ba,hasalima ya qara qaimi ya kafa kanshi ra hanyarta,ya kuma zamanantar ta zama abar sha'awa ga kowa.
Doguwar barandar ta dinga bi tana kallo qasan kamfanin har sai data kai qarshenta,wanda a wannan kwanar office din din CEO yake wato lamin,ganin taka qarshe sai ta fara qoqarin juyowa ta dawo
"Me yasa samha....i told you har yanzu akwai mutane da yawa,da kin zauna abunki iya abunda kika yimin ma i appreciated it" muryar lamin ta ratsa kunnenta,yana rufe baki kuma muryar samhan ta biyo bayanta
"Yanzu my man.....daga abun arziqi,a qa'idama fa dani ya kamata a gabatar da komai ina ta damanka.... but ka bani excuse kuma na karba,na bari sai da aka ragu,don nazo.naga kamfanin mijina laifi nayi?"
A hankali iman ta juya idanunta zuwa sashen da takejin muryoyinsu,lamin na tsaye daga qofar office dinsa,sanye da suit da yayi amfani dasu a wannan rana iri daya da ya sadiqu ash da da ratsin orange dan kadan,suit din da sukayi masifar tafiya da imanin mutane,sai samhan tana tsaye itama tana fuskantarsa,sanye da Dubai abaya zoom material,ta yane kanta da mayafin abayar,an qawata mata fuskarta da makeup,da alama takanas taje akayi mata ita,qafafunta sanye da high shoes masu tsinun dunduniya,qaramar jaka ce a hannunta dakuma wata leda wadda ke dauke da gift data shirya musamman saboda lamin din.
Dauke numfashinta iman tayi,ta sake dage takunta da kyau,qirjinta na bugawa saboda kusancin data gani tsakanin lamin da samhar,taku biyu idan ya qara yana iya hade tazarar dake tsakaninsu,saidai bata kai ga cimma nasarar barin wajen ba kamar ance masa ya juya suka idanunsa ya sauka a kanta,yasan tabbas ta gansu shida samhan
"Zonan" ya fada a dake cikin salon bada umarni,maganar da taja hankalin samha itama,saita iman din ta tsaya cak ba tare data waiwayo ba
"Rakata ta gaida inna" ya fadi yana sanya card dinsa jikin qofar office din zai bude.
Idanun samha qur akan iman sanda take qarasowa inda iman din take,wadda tunda ta tsaya bata juyo ba,daga sama har qasa take qarewa dressing dinta kallo,wani abu taji ya caki zuciyarta me kama da kishi,me yasa tunanin yin irin wannan shigar bai shiga kanta ba?,ta tambayi kanta,dressing me aji wanda kana kalla zai gaya maka mamallakiyar shigar tasan me takeyi.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 54
Tare suka jero,saidai girman kai ya kama kowa,kowacce ta gaza yiwa 'yar uwarta magana,kishi yana cin zuciyar kowaccensu,yayin da samha tata zuciyar ta cika da qyashi irin na kyan da iman din tayi,zuciya nata raya mata yanzun qila tare suka taho da ita a mota guda,wala'alla ma ita ta zauna a gaban motar,wannan kwalliyar qila shi ya fara ganinta kafin kowa ya gani,yanzu da wannan kyan nata suke rayuwa gida daya dashi?,gaskiya batajin zata juri barin iman din ta dinga zuwa mata gida duk sanda sukayi aure da alameen din,duk da itama me kyau ce,amma batasan me yasa kyan iman din ya tsole mata ido har haka ba,tana da azababben kishi,ita kanta tasan da haka,tayi.mamaki ma da yazo mata da sauqi akan iman din,bata iya furtawa,saidai yana cinta cikun zuciya qwarai da gaske,wala'alla ko don ta lura basa wani good time da alameen dinne yasa bakinta ya iya har yayi controlling kansa ba.
Daga qarshe shawarar zuciyarta tabi,wadda ta kwabeta kan ta daure zuciyarta ta tanka mata
"Dake da ameen bansan wanda yafi wani miskilanci ba,duk miskilancin da ake fadin ina dashi sai nazo na tarar da wani kuma daban" ko kadan maganar tata bata burgeta ba,saima haushinta daya ninku cikin zuciyar iman din,wannan wanne irin rashin ajine da xaki biyo mutum cikin taro irin wannan,da familynsa a wajen da komai,bayan gidansu da kika tattaka da qafafunki kikaje,wannan duka bai isheki ba
"Innar tana tacan" ta tsaya daga baya tana yiwa samha nuni da wajen da innar take,saita qarasa jikin glass na ginin saman ta tsaya,tana ci gaba da kallo farfajiyar kamfanin,inda tsirarin mutane da suka rage suke ta kai komo,wasu na fita wasu na shigowa,saidai fiye da rabin hankalinta ba a na wajen yake ba,ya lula duniyar tunani.
Zafi sosa zuciyarta take mata,tanata qoqarin controlling kanta ne,tana ta hadiye abubuwa, bataso su taru suyi mata yawa,tana fata Allah ya cire mata amin daga ranta kwata kwata,kwana take ta kuma wuni tana addu'a,batason ta nacewa kanta da damuwa kan abunda ba zata samu ba,batason zuciyarta ta dinga wahala akan abunda tasan yayi nisa daga gareta,bataso ta dinga damuwa da tarayyar samha da amin,tanaso wadan nan abu uwan su fita daga ranta ko xata huta,saidai babu wani ci gaba da take gani kan abunda take roqo din,ta dai sanyawa ran nata lokaci ne.
Ruri wayarta ta fara yi,a sanyaye ta daga tana kallon screen din wayar,dr ahmad ne,ba zata iya share kiransa ba,saboda yana matuqar damuwa da al'amuranta da kuma bata kulawa ta musamman.
Ita tafara masa sallama,ya amsa mata yana tambayarta yanayin taron,yaso zuwa qwarai amma ranar yana da patient da zaiyiwa theatre har mutum uku,dole ya haqura
"Alhamdulillah,taro ya tashi lafiya" ta bashi amsa a taqaice
"Ma sha Allah,Allah yasa albarka"
"Ameen,thanks" shuru ya ratsa wayan,cikin zuciyarsa yana ji muryarta batayi masa yadda ya saba jinta ba,kamar tasan tunanin da yake kenan tace dashi
"Zamuyi waya anjima please"
"Alright, take your time and be safe"
"Thank you" ta sake amsa masa tana katse wayar,a yanzun bata jin zata iya wata doguwar magana,shi yasa tayi masa sallama.
Numfashi ta fitar daga bakinga hade da iska,tana ci gaba da kallon waje,cikin jikinta takeji kamar ana kallonta,idanun kuma ya wuce na mutum daya,sai ta maida hankalinta ga wajen,tana tsammanin daga canne wasu suke hangota.
"Alameen" muryar yaa baraka ta bayyana daga bayansu,da sauri gaba dayansu suka juya,babu wanda yasan da tsaiwar ya baraka a wajen,iman ta sauke kallonta ga alameen dake tsaye a baya ta wanda a yanzu ya waiwaya ga yaa baraka,saidai akwai tazara sosai a tsakaninsu,batasan tsahon yaushe ya dauka a tsayen ba,kamar yadda gaba dayansu basusan tsayin lokacin da itama ya barakan ta dauka a tsayen ba.
Dukkaninsu suka taka zuwa inda take tsaye
"Me kuke a waje?,innar aka bari ita daya a ciki?" Shafa kwantacciyar sumarsa mai kyau da qayatarwa yayi
"Ba ita kadai bace,tana tare da baquwa"
"Baquwa kuma muka samu?...." Bata tsaya jin amsarsa ba kuma sai ta shigo da wata maganar
"Wannan matattakalar taku badai yawa ba,yanzu kullum haka zaku dinga dawafi daga qasa zuwa sama?" Sai da sukayi murmushi gaba dayansu,dai dai sanda suka fara takawa zuwa ciki,suka sanya yaya barakan a tsakiya
"Akwai na'uran dake ragewa mutum tsahon tafiya,daga sama ta kawoshi qasa,ko kuma daga qasa ta kaishi sama"
"Ayho,koda naji" daga haka kuma sai hirar ta koma tsakaninta da iman din kawai,kusan wasu abubuwane da batasaji game da iman din ba take tambayarta,kamar karatunta da sauransu,a haka suka qarasa inda innar take.
Kanta ta dago daga hirar da sukeyi da samha tana amsa sallamar tasu,shigowar tasu a haka sai wani abu ya mintsini zuciyar inna,ta bisu da kallo a yadda suka shigo din,tana jin inama inama,inama ace.....
Tunaninta ya katse sanda yaa barakan take zama tare da mitar barin innar ita daya,murmushi inna tayi
"Basu barni da kadaici ba ai,ga mufida muna tare,daga baya ma saiga diyata kuma ta shigo" duba sashen da samhan take yaa baraka tayi,kasancewar batasan wacece ba batace komai ba,dakin ya dauki shuru kamar qiftawar tsawa,inna ta san lamin din nada kara,bazaya iya gayawa yaa barakan wace samha ba,amma tayi zaton iman zata gabatar da ita sai taga wayarta ma take dannawa kamar bata cikin dakin,tilas tadanyi gyaran murya
"Baraka,gafa surukar tamu,yarinyar da ameenu zai aura in sha Allahu" da hanzari ta kalli gefanta inda samhan take,a sannan ta sadda kanta qasa tana kuma dan murmushi dake nuna kunya
"Too ikon Allah"abunda ya barakan tace kenan,bayan ta gama amsa gaisuwar samhan dakin shuru ya sake dauka,sai inna dake qoqarin jefowa samhan hira saboda kore zaman shurun nasu,duk wanda ya kalli fuskar ya barakan yasan ta canza,ba haka yanayinta yake a dazu ba,saidai bata ce komai ba,amma tana biye da hirarsu da inna.
Lamin ne ya duba agogonsa bayan ya sauke wayarsa da aka kirashi
"Inna ko zaku wuce kada ku gaji da zaman,an kai malam yaron daya kaishin ya dawo"
"To babu laifi,hakan yayi" daga haka suka miqe suka fara shirin tafiyar.
Yaa barakan tana tason yin magana da lamin,saidai samhan tana maqale dashi sanda suka fito gaba daya,tana masa magana qasa qasa,har suka qaraso bakin mota.
Inna lamin ya budewa gaban motar,sai taqi shiga tace samha ta shiga,tadan doje kadan kan innar ce zata shiga,bata sake jan zancan da tsaho ba ta bude ta shigan,ya baraka ta fara shiga baya,sai iman sannan samhan,yaa baraka ta leqa ta window
"Yau komai dare idan ka dawo ka nemeni,inason yin magana da kai"
"To in sha Allah" ya amsa mata cikin girmamawa yana rufe murfin motar.
Cikin motar ma dif kowa yayi,samha aka fara saukewa sannan su aka qarasa gida dasu.
Kamar jira ya barakan take,suna shiga parlor abinda ta soma shine qorafi,a sannan iman tuni tayi daka,saboda gajiyar da takeji a jikinta.
"Yanzu inna,ta yaya kuna gani kuka bar aminu ya dauko wannan yarinyar?" Dubanta inna tayi tana cire abun hannunta
"A iya abunda ido da kuma bincike ya nuna bata da wani aibu,tuni malam ya gama duk wani bincike a kanta,abunda yasa ma yace kizo din lallai,ina kyautata zaton jibi za'a kai kudaden aurensu shi da sadiqu.....dana 'yaruwarsu ma gaba daya" zama ya baraka tayi,gaba daya wuta ta dauke mata,ashe ita abunda take lissafi tattare dashi da kuma iman din ba haka bane,yaya amin din zai aikata wannan gangancin da kuma katobarar?
"Amma binta,tsakanin da Alla ta yaya gida bata qoshi ba za'a bawa dawa?,har iman din bada ita za'ayi?" Murmushi kadan inna tayi,inda ita ke da ikon sarrafa al'amuran zuciyar kowannensu,da tuni ta gama da tabbatarwa ameen iman
"Dama ce aka bawa kowa ya zabi abokin rayuwar da yake ganin yafi dacewa dashi baraka,baka isa sauya abunda Alla ya rubuta ba" kai ta girgixa,a karon farko da takejin zata ja da wani hukunci akan lamin din tsahon shekaru sama da ashirin da uku
"Zanyi magana da malam,wannan ba abunda zaa zuba idanu bane ace haka Allah ya tsara bane,a fara jarrabawa,idan bai yiwu ba sai ace haka Allah ya tsara din,ni zanga malam din da ameenun ma gaba dayansu"
"To Allah yayi jagora" abunda inna ta iya fada kenan saboda kara,uwa uba can qasan zuciyarta sai ya cika da fata da kuma burin cika da tabbatuwar abinda baraka ke hari.
*IMAN*
Tun bayan shigarta daki Allah ya taimaketa barci me nauyi ya dauketa,baccin daya dauketa lokaci mai tsaho,koda ta farka taga lokacin data share tana baccin bata damu ba,saboda tasan tana fashin sallah,sannan babu wani sauran aiki cikin gidan,tun kafin su fita ta gama komai na gidan,saita dan yaye labulenta tana hangen waje,sararin samaniya har tayi duhu wanda ya gauraya da ragowar hasken magariba da bai gama dusashewa ba,ta saki labulen a hankali ta kuka zarce bandaki.
Ruwa mai dumi sosai ta saka tayi wanka,ta fito tana qamshin shower gel dinta mai taushi,gaban madubi ta tsaya,ta tsane jikinta ta mulkeshi da mayukanta masu kyau da tsada,wanda zuwa yanzu sun zame.mata jiki ta saba amfani dasu,sun karbeta matuqa,qamshinsu kuma ya zauna sosai a fatarta,ta gyara gashinta shima ta feshe shi da hair mist,sannan ta shirya cikin wasu ready made data siya a wani kanti,riga budadden hannu da straight skeet,kayan basu da nauyi sam,shi yasa take sonsu takejin dadin sakasu,cikin kayanta ta duba hijabi qarami da bai wani sauko da yawa ba ta zura,zaman dakin ya isheta,don haka ta qarasa inda wayarta take ta dauko tana dubawa,saqonni da kuma miscal masu yawa,wanda batasan dasu ba,sabida saka wayar da tayi a silent tun sanda zata kwanta,saita zarce da fita waje kawai wayar na riqe a hannunta.
Ba kowa cikin parlor din,amma ta dan jiyo murya daga sashen dakin inna,tunawa da tayi yaa barakan tace tanason ganin ameen komai dare yasa ta yanke fita can bayan gidan ta zauna abinta,don babu mamaki shi dinne suna tare,itako batason duk wata harka da zata hadata dashi,a yanzun lallaba rayuwa da kuma zuciyarta takeyi.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 55
Wani yanayi me haifar da walwala ne ya sauka a zuciyarta sanda ta fita qaramar harabar tasu takuma zuqi fresh air dake kadawa,iska ce mai wani irin taushi a cikinta,kamar ta farkon shigowar damina,idanunta suka sauka a hankali kan motarsa dake fake adan filin gidan nasu,tabbacin ya dawo kenan,dole kam ta kama kanta itama,saita kalli hagunta da damanta,tana shawarar daga wanne side zata zauna,karkata zuciyarta tayi da bangaren hagunta,wanda yake daura da wajen ajiyar motar sannan kuma ventilation ne da suka jere tukunen shuke shuke,ba kasafai aka fiya zuwa wajen ba,saboda daga nan zai sadaka da qofar babban parlor dinsu ameen din dake dauke da dakunan baccinsu,wajen yana da dan tsaho,hakan yasa idan kana daga ciki ciki ko daga baki baki ba zakasan da wani a farko ko qarshe ba.
Tana takawa tana duba saqonnin dake wayarta,kusan fin rabinsu daga Dr Ahmad ne,wanda yaketa mata bangajiya da kuma alhinin rashin samunta a waya,har ta qaraso wajen,ta daga ido taga plastic chair guda daya a wajen,takai hannunta guda daya da bai riqe da wayar ta niyyar jawota.......sai kuma ta tsaya cak,cikin sakanni kuma zuciyarta ta balle da wani irin gudu,qarfin jinta ya qaru,kamar yadda harbawar jinin dake jikinta ya birkice ya sauka daga kan tsari,fitar muryar alameen din na dauke da wani saqo da bata taba ayyana jinsa daga ba daga gareshi
".............duka ba haka bane yaa baraka.....kuma nima nasan da wannan,amincewar kowanne sashe shine jigon zamantakewa,sannan na roqeki kibar wannan maganar, let bygone be bygone,abunda ya wuce ya riga daya wuce,tun a wancan lokacin na shafe babinta daga raina da zuciyata gaba daya,na maidata matsayin wadda muka fito ciki daya,koda bata taba auren wani ba a yanzu bani da sha'awar aurenta kwata kwata bare ta taba auren wani, I can't.....bazan iya ba yaa baraka,infact ma a yanzu dai bana son iman kwata kwata,soyayya dai irin ta aure,kiyi haquri,ki kuma yi qoqari ki fahimceni,bazan iya ba" so take ta zauna din ko zata daina jin abunda takeji amma kuma batason taci gaba da sautaren maganganun dake fita daga bakin ameen din,kalaman da sukayiwa kunnuwa da zuciyarya matuqar munin da ba zata iya fasalta kamarsa ba,cikin juriya da jajircewa ta fusgo numfashinta da yake qoqarin yi mata wahala,ta cira qafafunta ta kuma tunkuda kanta da kanta zuwa gaba da sauri da sauri.
Cikin taimakon Allah ta lalubi hanya tas ta maida kanta zuwa daki,ta wurgar da wayarra ta bude bandakinta,ta kuma saki rufa afamfo ta dinga tara tafukan.hannuwanta tana watsawa a fuskarta,bata damu da yadda jikinta yake jiqewa ba,illa dai hucin da takeji.kamar yana fita daga saman fuskarta duk sanda ta watsa ruwan,a hankali a hankali ta soma jin na'urorin jikinta suna dai daita,saita kashe famfon,ta kuma ja da baya ta sulale a hankali zuwa qasa,a lokacinne kuka ya samu hanyar fita.
Tayi kuka kwatankwacin kukan datayi sanda ta gane waye bassam,waisu dama maza basu da alqibla?,waisu maza dama idan ka kamu da soyayyarsu baka tsintar komai face wahala da tashin hankali?,dama haka soyayya take?,me yasa soyayya bata karbeta ba kwata kwata,me yasa take wajigata?.
Me yasa zaki tsaya fana wahal dake tana wajigaki?,ki karbeta aduk yadda tazo miki kawai,idan ta barki kema ki barta ki huta,ki maida hankali da tunaninki ga barayin da ake da buqatarsu,a yanzu komai yazo qarshe tsakaninki da ya lamin,kin samu cikakkiyar amsar da kika jima kina lalubenta,meye kuma yayi saura?,a nan wajen cikin hali na zafi da quncin zuciya zuciyartata ta yankewa kanta da kanta hukuncin,hukuncin da takejin koda bataso xata tilasta kanta,ta tanqwara kanta ta karbeshi a haka,ta miqe ta zare kayan jikinta da suka jiqe,ta fito ta canza wasu cikin wani irin yanayi na siyawa kai jarumta,da son danne qunci da halin tashin hankali da zuciya ke fuskanta.
Saqon qarshe data fara dubawa taci karo da maganganun ameen ta koma ta sake dubawa
_"Ki shaidawa malam,gobe idan Allah ya kaimu su kawu zasu zo,sai a basu lokacin da yafi dacewa,kiyi mana addu'a,Allah yasa wannan shine matakin ingantacciyar rayuwa a garemu gaba daya"_
Da qwarin gwiwarta ta maida masa amsa,tana jin wani confidence yana shigarta sanda rauni yake qoqarin rinjayarta,ta ajjiye wayar gefanta itama ta zauna cikin matuqar kasala da mutuwar jiki,lokaci yayi da zata ajjiye komai,ta haqura itama,duk da tasha gayawa kanta wannan kalmar,amma tana saka ran wannan snine karo na qarshe da zata gayawa kanta haka.
Turo qofa mufida tayi ta shigi,ta ganta ta mudubin dakin don haka bata juyo ba
"Ya iman.....ya ameen yace akai masa abinci" ta mudubin ta zubawa yarinyar idanu
"Akai masa abinci,wato amfaninta kenan kai abinci?,me zaiyi da abincin da hannuwan wadda baya so suka dafa?,daga yau ta yanke,ta kuma canza,ta tashi daga wannan iman din zuwa wata daban" tayi dukka wannan tunanin da hukuncin cikin zuciyarta
"Kice musu a kwance nake,a kishirya food flask din a nutse kikai musu da daya da daya,zaki iya"
"Tom" yarinyar ta fada tana dan kallonta,sabida yadda taga yanayinta,batace dai komai ba ta juya ta fita sannan taja mata qofar.
Ba zata iya fita tayi magana da kowa ba,don haka taja wayarta ta turawa ya sadiqu text kan saqonnda dr ahmad din ya bayar,bayan ta tabbatar ya tafi saita kashe wayar gaba daya,ta hada da qwan dakin gaba daya ta kashe ta koma ta kwanta lamo,kamar ba daxu dazu ta tashi daga kwanciyar ba,bawai barci takeji ba,a'ah,tanason ta tattara duk wani courage nata da zata fuskanci rayuwarta da mutanen da take rayuwa dasu daga gobe idan Allah ya kaimu.
*********Da sakakkiyar fuskar dake boye da damuwa fal bayanta ta fita ta kama dukka wata sabgar data saba,kamar kunnuwanta basuji komai ba,kamar kuma babu wani ciwo cikin zuciyarta,ta yadda ba shakka duk wani abu daga tilastawa kanka yinsa zaka aikatashi,koda zuciya da gangar jiki bata gamsu da hakan ba.
Qarfe sha daya na rana tana dawowa falon xata ciri charger dinta datayi charge da safe ta tadda yaa baraka na fitowa daga dakin data sauka,'yarta na tsaye saqale da jakar kayansu
"Ke kuwa baraka,aiko azahar kya bari kikai idan su malam sun dawo daga kai kudaden auren nan" baki ta tabe
"A'a...a'ah,ai gwara na tattara komatsaina,tunda na fuskanci gidan yanzu ya zama gidan marasa son gaskiya,zamana kuwa bazai amfana komai ko ya rage komai ba" iman dake takowa parlor tasan komai,saidai babu wanda yasan ga sani din,cikin dauriya ta kalli badi'a
"Ke badi(haka take kiranta wasu lokutan)yanzu ko dan zaman nan ma na sati daya kiyi mana baxaki iya ba,qafarki qafar yaaya?" Murmushi badi'an tayi
"Makaranta wallahi yaa iman,yanzu ma kinga don a weekends muke,amma dai in sha Allah wataran zanzo" kai ta jinjina tana fidda dan murmushi
"Muna zuba ido....ya baraka da sauri haka?" Murmushi tayi
"Kada ki damu diyata kinji,zan dawo ko don saboda ke,bawai na tafi kenan ba" tayi maganar duk da tasan bawai lallai iman da duk wanda ke wajen ya fahimci abinda take nufi ba,hakan kuwa yake,saidai akace babba babbane,inna ta fahimci inda maganarta ta sanya gaba.
Tsaf murmushin fuskarta ya dauke sanda ta hangi shigowarsa,sanye cikin jallabiyya milk color mai gajeran hannu,duba daya zaka yiwa fuskarsa ka gane yana tsaka da barci ya taso,saita janye jikinta daga wajen,ta zagaya wajen chargenta ta cira,ta dawo daga bayan yaa barakan tace
"Yaa baraka zan shiga wanka,ina da makaranta yau,Allah ya tsare hanya,ya huta gajiya,Allah ya qara zumunci"
"Ameen imani" ta amsa mata cikin kulawa da jin dadi,ta yiwa badi:a magana kan ta biyota ta karbi saqo,batako waiwayi inda yake ba tayi gaba,tana jinsa shima yana qorafin ta tsaya su malam su dawo,ya karbi motar daga hannun sadiq,koda bai kaita jigawa ba ko wudil ne ya ajjiyesu,saidai fir taqi tace ko minti guda bata qarawa cikin ikon Allah.
Wani abu yadan tarar mata a wuya,ya sadiq ne kenan ya tafi kaisu,saidai da qarfi tayi qoqarin kawar da abun,ta duba wani seat na turaren jiki sabulu da spray ta bawa badi'a,dadi sosai ya kama badi,tayita maga godiya ta fito da abunta.
Da idanu ya kalla kwalin bayan badi'a ta fito dashi tana nunawa yaa barakan,yasan kudinsa sarai,don ya taba siyawa samha gift dinsa,saidai batayi amfani dashi ba,sabida tace scent din bai mata ba,shi kuma ya siyo ne saboda irin launin qamshin da yakeso kenan,sai yace ta barwa suby'a ya canza mata da choice dinta.
Bata sake fitowa ba har sai data kammala shirinta na fita zuwa makaranta,tayi kyau cikin fararen kayansu data dora baqar after dress akai,komai na iman din mai kyau ne da sanyi kamar dai yadda take ada can,wannan yanayi nata yana ja mata farinjini da masoya masu yawan gaske a cikin makarantar dama wajenta,sauqinta daya,bata bada fuska,miskilancinta idan ya motsa ba zaka taba cewa wannan iman din bace.
Komai take a ranar dauriya ce kawai take yinta,amma bata da wani kuzari ko karsashi,a duk sanda ta tuna a yau za'a bada ita ga wani,a yau kuma za'a bada alameen ga wata sai zuciyarta ta buga,saidai tanata gayawa kanta, she's ready to face any challenge......zata kuma iya jurewa,zata iya dauka.
Daga makaranta bayan ta gama duk abinda takeyi kasa wucewa gida tayi,sai ta wuce gidan kawu muntari wajen matarsa,mutuniyarta ce qwarai,ta tarbeta kamar koda yaushe,suka gaisa ta tambayi kawu muntarin
"Kawunki har yanzu bai dawo ba,tun daxun dai daya shigo bayan sun dawo daga kai kudaden auren yayanki,sai kuma ya sake fita,yace malam yayi masa waya ya dawo,yaron dake nemanki yace wakilansa na hanya.....to tun lokacin dai bai dawo ba".
Idonta kawai ta lumshe,zuciyarta na gaya mata shikenan,ta faru ta qare,alameen ya zama alqawarin wata,kamar yadda itama wala'alla kawo yanzu ta zama alqawarin wani,sai kuka tayi maza ta kauda wannan tunanin da kuma duk wata fargaba data taso mata,sanda zuciyarta ta tuna mata da kalamansa,kamar a sannan yake gayawa yaa baraka su.
Tana idar da magriba tayi haramar tafiya,dai dai sanda kawu muntari yayi sallama ya shigo gidan,saida gabanta ya fadi data tuna daga inda yake,suka gaisa,yayi mata Allah ya sanya alkhairi sannan sukayi sallama ta wuce gida.
Daga baya baya tasa me napep ya ajjiyeta,ta qarasa takowa a qafa,idanunta kan motar dake fake a qofar gidansu,data duba da kyau sai taga motar lamin dince,kuma suna tsaye a jiki shida ya sadiqu suna maganganu,ta wucesu a hankali ba tare data ji ko ta saurari abunda suke tattaunawar ba.
Da idanu yabi bayanta sanda take giftasu ta gefe,cikin takunta a hankali,sai kuma ya lumshe idanunsa yana janyesu,ya sake maida hankalinsa ga sadiq sukaci gaba da maganar da sukeyi yana jin wani baqon abu cikin zuciyarsa,wanda bai iya tantance meye ba.[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 56
Tunda ta shiga cikin gidan taketa tattalin farincikinta,da wankanta da cin abinci duka tanayi ne cikin son share kowanne tunani da dora sabuwar rayuwa bisa tsakiyar zuciyarta.
Tana dakin malam ya aiko kiranta,kamar wancan lokacin batasan ba ita kadai bace sai data shiga rumfar tasa,suna zaune sadiq din da ameen,a wannan karon wayar ameen din tana a tsakaninsu,da alama wani abu suke kalla,shigowarta kuma bai canza komai ba,sai ta rabesu ta isa ga malam ta yiwa kanta mazauni ta fara gaisheshi,ya amsa mata cikin kulawa.
"Alhamdulillah,kowannenku akwai alqawarin aure akansa nan da watanni shida,mun sanya hakane saboda kusan kowanne bangare a shirye yake,iman....kece zakiyi haquri,don ba lallai yayi dai dai da sanda zaki gama jarrabawarki ba,saiki addu'a Allah yasa haka ne yafi zama alkhairi"
"Ameen" ta amsa idanuwanta a qasa,sannan kuma ta miqe tabar dakin ba tare data bari ta kalli koda sashen da yake ba bare yaga idanuwanta.
*********Yanayine mai matuqar wahala wajen jureshi,yana da matuqar daki tsanani da kuma wahala me yawa a cikinsa,ba qaramin abu bane kaso mutum so mai yawa,baya ga yawan kuma yake cike da zallar gaskiya da sahihiyar soyayya,kana sanya ran samun koda kwatankwacin abinda kakeji ne a matsayin tukuici da sakamako......sai kuma ya zamana abunda zai dawo maka shine dauke kai.....rashin nuna halin ko in kula da yanayin da kake ciki.
A duk da hakan ta dinga dorawa hadi da lallaba rayuwarta,ta kuma rungumeta a yadda tazo mata,tayita tasa al'amuranta a gaba tana watsa damuwarta baya,saidai duk da hakan babu wata nasara me yawa data ci,domin kuwa a kwance damuwar take a qasan zuciyarta,duk wata walala da fara'a dake saman mu'amalarta ta yau da gobe fake ce,wato jabu.
A hankali ranakun suka dinga zuwa suna wucewa fewww kamar ana jansu,watannnin da malam ya sanya na aure suka dinga qaratowa,a lokacinne iman din ta dinga wata rama a tsaye tana qarewa,saidai hakan bai hanata duk wasu sabgogi nata ba,musamman makaranta da karatunsu ya sake daukar dumi,dama bahaushe yana cewa idan aski yazo gaban goshi yafi zafi,sau tari inna na binta da kallo fana qiyasta ramar datayi,sau daya ta kwatanta yi mata magana tace mata
"Inna,makarantar nan babu sauqi,don dai kawai burina ce da tuni na barta,bakiga karatun dake gabanmu ba inna da sai kin tausaya min" da wannan amsar ta fuskanci inna,ta qyaleta akan hakanne amma badon ta gamsu ba.
A lokacinne sadiqu yayi mata zancan motarta wadda ta taho da ita daga gida bassam,motar da tun a sannan take ajjiye,cewa tayi a tattara a saida komai daya danganci gidan bassam din,saboda batason koda tuna cewa ta taba rayuwa dashi,aka siyar din kuwa,saiga kudi tarin yawa,ya buqaci jin me take so ayi mata dasu,tace ya tarkata kudin kawai ya bawa inna ta ajjiye mata,saboda a yanzun bata da nutsuwar sanin me za'ayi mata dasu.
A nutse sannan kuma a hankali shirye shirye suka gudana cikin gidan na auren cikin ruwan sanyi,bata data cewa kamar yadda bata da wani feeling akan auren,dukkan wata kulawa da tattali tana samunta dari bisa dari wajen dr ahamd,ta yadda gwanine ta fannin soyayya,ta kuma yadda da cewa likitoci ba baya ba wajen iya soyayyar, they are very romantic,saidai kwata kwata babu wata gamsuwa ko burgewa tattare dashi a ranta.
Hutun da suka samu juma'a asabar da lahadi taji tana sha'awa matsawa daga bigiren da take izuwa wani,tayi gajeran tunani akai,nijer yayi mata nisa,hakama maiduguri,sai ta yanke zuwa jigawa,gurin data jima bata je ba,duk da cewa garin na daya daga cikin garuruwan da take qauna,sai faduwa tazo mata dai dai da zama,dama kuma yaa baraka tana yawan qorafin yadda ta zubar da ita gaba daya.
Ta sanarwa inna batun tafiyar,inna ta gayawa malam,babu wanda ya hanata,saboda gidan yaa barakan kamar gidane a wajensi gaba daya,a ranar tahau shirinta,ta kuma kwana dashi,washegari qarfe goma na safe ta gama komai,ta fidda qaramar jakar hannunta ta matafiya,mayafinta na rataye bisa kafadarta batakai ga yafawa ba ta fita parlor.
Mutum na farko data fara gani alameen dinne,sanye da shadda wadda aka yiwa dinkin zamani,yana zaune saman carpet,ya tanqwashe qafafunsa yana cin funkaso da miyar da tayi da safen,hularsa na aje gefe,wayarsa kuma na saman hular a ajjiye,sai muqullin motarsa daga qasa daban shima.
Kamar ko yaushe gabanta ya doka,wani sassanyan kyau me aji yake fitarwa,sumarsa dako yaushe take qara kyau tayi kwance tana ta qyalli,tadan saci kallon hannunsa,har yau bataga mutum mai tsananin gayu da tsafta dake cin abinci da hannu ba irin ameen ba,yayi masifar iyawa kuma,abun sai ya zama wani ado,kamar irin yana cin abincin ne in a stylish way kuma gangan.
"ina kwana" ta gaidashi ba tare data kalleshi kota tsaya ba tana takawa zuwa gaba,shima hankalinsa na ga tv ya amsa mata yana ci gaba da cin abincinsa a nutse.
Qaramar ajiyar zuciya inna ta sauke a fakaice tana fuskantar iman
"Har kin fito?"
"Eh inna,inaso na isa ne kafin rana tayi zafi,kinga ya baraka da zumudi harta kirani wajen sau biyu fa wai na taho kuwa?" Tafada murmushi na subuce mata,kyawawan farare kuma jerarrun haqoranta suna bayyana.
Sunan ya barakan data kira yadanja hankalinsa,da idanu yadan dubeta sanda blue eyes dinga kega inna,amma yana iya hangen fuskarta tar,fuskar data qara haske amma ta dan sirance kadan,a yadda yake kallon wajen ba zaka taba zaton ita yake kalla ba,saboda tsabar qwarewa wajen iya basarwa,jigawa kenan zata je?,amma ko jiya da daddare sunyi waya mai tsaho da ya barakan amma bata gaya masa ba,hakanan ita dinma jiyan daya dawo ya taddasu parlor amma baiga alamun zata wani waje ba.
Zaren tunaninsa ya katse sanda inna ta miqe tana cewa
"Malam yasan kayarsa,shi yasa kafin yafita yabar miki saqo yace koda zaki tafi kafin ya dawo din"
"Wallahi inna,banaso rana ta take din nan ban isa ba" tayi maganar tana kallon agogonta dake daure a tsintsiyar hannunta,daga bisani kuma ta sauke,ta maida dubanta ga mufida,wadda taqi magana tun daxun,cikin qaramar dariya tace
"Wai har yanxu fushin ake dani saboda nace bani zuwa dake?,yanzu banda abunki mufida.....kwana uku fa kacal zanyi na dawo,ta yaya zamu yoye mubar inna ba mataimaki?,ki bari na miki alqawari kuna hutu zan kaiki,indai ya baraka ce tana maraba da kowa" sai a sannan ta saki ranta.
Inna ta dawo da saqon tana miqa mata ya miqe shima,ya dauki dukka kayansa
"Zan wuce inna,sai na dawo"
"Har ka gama?"
"Eh ya isa haka"
"To Allah ya bada sa'a,a dawo lafiya,Allah ya tsare" ta rakashi da kyawawan addu'o'inta kamar yadda ta saba gami da fatan alkhairi,sannan ta maida hankalinta ga iman tana sake mata bayanin saqon malam da kuma kudin motar daya bayar a bata.
A hankali take takowa zuwa harabar gidan,tana tunanin tashan da zataje ta samu mota mai kyau wadda kuma zata tashi da wuri,ta buda qofar gidan ta fita tare da fatan samun abun hawa da wuri,saboda unguwar tasu wani lokaci wahalar abun hawa akeyi.
Batayi nisa ba taji nishin mota daga bayanta,bata damu ta juya ba don tasan adai dai take ba sama hanya take tafiya ba,motar na gotata kadan tayi parking,sai a sannan ta dubi motar.
Ya ameen ne,kafin ta qaraso taga ya bude front seat,hakan yana nufin kenan ta shiga. Tsaiwa tayi sanda ta qaraso wajen,saboda murfin motar ya rufe hanyar da zata iya wucewar
"Shiga mu tafi" taji ya sake fada,ta kalleshi idanuwansa na kan hanya,fuskarsa kuma sam babu alamun fara'a ko kuma wasa,lallai yau akwai damuwa,idan batayi wasa a yau din ciwonta zaisha sabon fami,ita da ameen din a mota daya?,da kuma kusanci irin wannan?,bata da sauran option face shigar,ta janyo murfin motar ta rufe,ya dage dukka gilasan sama tada motar ya fara gangarawa a hankali,sannan ya saka hannunsa ya kunna ac madaidaiciya yadda ba zaka takura ba.
Shuru ne ya ratsa cikin motar,sai wani slow music dake tashi can qasa cikin qaramin sauti,tafiyarsu ta dauki kusan mintuna goma,sannan lallausar muryarsa mara son hayaniya ta motsa
"Da gida yaa baraka zaki baki gayamin ba?" Yayi maganarne idanunsa nakan kwalta,hannunsa daya kan sitiyarin motar,daya hannun kuma yana zagaya labbansa da 'yan yatsunsa.
Yadda yayi maganar koda bata kalleshi ba tasan 'yan sarautar ne suka motsa masa,tafi kowa sanin halayyarsa ciki dabai,sau da dama tana iya gane mood dinsa daga sound dinsa ba tare data kalleshi ba.
Bataga dalilin da yasa saboda zata wani waje sai ta gaya masa ba,kamar hakan a yanzun bashi da alaqa da rayuwarta.
"Na zaci ka sani" itace amsar data iya bashi kawai,saiya waigo ya dubeta ya kuma maida kansa ga titin duka cikin abunda baifi second uku ba,kafin yace komai wayarsa ta dauki qara,yadan saci kallonta,sai ya sauke hannunsa guda daya ya latsa wayar ya maqalata a kunne
"Wa'alaikumussalam....." Yafada da muryarsa mai nauyi a wasu lokutan,murmushi ya danyi,abunda yasa iman juyar da kanta sosai ga taga tana tabe baki
"Alhamdulillah" ya sake shuru kafin ya kuma cewa
"Zan kiraki,ina tuqi ne..... okay,nima haka,byee" ya zame wayar a hankali ya maidata inda take,bai kuma cewa komai ba,itama bata sake magana ba,don dama bata son magana a tsakaninsu,taci gaba da kallon titi.
Kamar zatayi magana sanda taga yanata wuce tashoshin motar daya dace ace ya sauketa,amma kuma daga bisani itama sai ta shareshi,tunda yafi kowa sanin ya daukota,tun tana saka ran zai sauketa a wata tashar qila a gaba har ta debe tsammani,saboda sun fara barin kano,sun wuce tamburawa ma,don haka saita zaro wayarta kawai ta kunna data ta shiga WhatsApp.
Tayi chart mai yawan gaske da qawaye da kuma dangin da take mu'amala dasu,tanata kasa kunne taji yace sauko amma shuru,sannu a hankali sai gasu a garin wudil,ya gangara gefan titi,ya shiga wani layi,tabi layin da kallo tana mamakin yadda aka samu layi me kyau da girma haka cikin qauye,saika dauka cikin unguwar gadon qaya dake birnin kano kake,baiyi nisa a layin ba taga ya tsaya,ya dauki wayarsa yayi kira
"Gani na qaraso..... okay.... okay" wayar ya ajjiye ya sake taka mota zuwa gaba,sannu a hankali sai gasu a qofar wani babbar katanga,ya sake daukar waya yayi magana,bai sauke wayarba mutum ya fito daga babbar qofar dake maqale da katangar
"Ku qaraso ciki mana" mutumin ya fada da murmushi,yana yiwa wani dake zaune a wajen magana kan ya bude qofar,ya dage musu alameen din ya saka kan motar ciki,sai gasu a wani katafaren waje dake da yalwar shuke shuke iya ganinka.
Baice komai da itaba ya fita,saidai ya zagayo side din da take yabuda murfin motar,take iska me kyau da dadi ya fara shiga tana fita,ya juya cikin takunsan nan mai cike da aji yabi mutumin sukayi ciki,ba jimawa suka bace cikin wajen.
A hankali take nazartar wajen,data lura da kyau ya fahimci gidan gona ne,saidai da alama wajen ya mutu ne,ma'ana ba'a aiwatar da komai a ciki,taci gaba dabin wajen da kallo,saita sauke ajiyar zuciya ta sake jan wayarta tana duba lokaci.
Batasan me yasa. Ya daukota nan yakeson bata mata lokaci ba,duk da cewa ta sani inda motar hayane babu lallai ma ace yanzu sun kawo wudil din.
Tana tsakiyar tunanin taji ana sallama,ta waiwaya a hankali,su biyu ne a tsaye riqe da manyan ledoji guda hudu,da alama mutanen karkara ne
"Hajiya yalallabai ne yace a kawo,a saka a cikin mota"
"To bismillah baba" ta fadi tana bude musu seat din baya,suka saka ledan suka rufe,basukai ga bacewa daga wajen ba taga bullowarsa tare da mutumin,kusan minti goma suka kashe a waje suna sake magana sannan sukayi sallama,ya sake shigowa motar,yayi bismillah ya kunnata suka fice daga wajen.
Tun kafin su shiga wajen ta karanci tasha suka shigo,a nutse ya sanya motarsa a ciki,bau saurari masu tararsa suna tambayarsa inda zashi ba,da alama yasan wajen wanda zashi,baiko tsaya ba har sai daya qaraso.
"Bismillah muje" yafada yana bude motar,yadda yace haka ta biyoshi a baya,tana tsaye sukayi magana da wani,kafin a bude qaramar golf,lamin din yace ta shiga,aka debo wadancan ledojin aka saka a ciki,ya qaraso bakin window din motar
"Ki gaisheta,Allah ya kiyaye" yayi maganar idanunsa tar akanta
"Ameen" ta amsa ba tare data iya dubanshi ba,sabida tasan tayi qarya a yadda suke very close ta iya kallon qwayar idanun nasa,janye dubansa yayi zuwa ga driver din
"Mutumina ayi tuqi a hankali"
"In sha Allahu yallabai,ni daka biyani harda riba,gaggawar me zanyi kuma?"
"To Allah ya tsare"
"Ameen ameen" daga haka yaja da baya,shi kuma ya tashi motar suka fara ficewa daga tashar,zuciyarta natason ta waiwaya saboda ta tabbatar yana tsaye yana kallonsu amma ta hana kanta aiwatar da hakan,ta saki ajiyar zuciya sanda suka hau titi tana duban hanya,duk da ya biya kudin motar wa ita kadai babu takura babu matsi,amma hakanan kawai taji tafiyar ta rage armashi,ba kamar dazun ba.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 57
Ina ka saka ina ka aje yaa baraka ta dinga yi da iman din,farincikinta ya kasa boyuwa,kamar zata goyata,wanda dama ko a baya kusan hakace tsakaninsu da ita.
"Aah,shine ya kawoki?" Ya baraka ta tambayi iman din sanda ta isar mata da saqonshi,farinciki na taso mata
"A'h,yadai ajjiyeni a wudil,yaje wani waje ne" farincikin data soma ji sai ya koma,batajin zata iya qyale wannan abun yatafi a haka,ba zata barsu duka su biyun suyi asarar kyakkyawan yabanya da iri ba,kara da alkunyar malam da inna tayi yawa,ta tabbatar dukkaninsu suna da buqata da kuma interest akan tarayyar iman da ameen,amma dukkaninsu suna duba wani abu daya faru a baya suna dauke kai da bawa ameen din dama,bayan dukkaninsu asara ce ace kowanne bangare sun rasa wani tsakanin iman da ameen din.
Sosai ya baraka ke ririta iman,cikin kwanakin data debo zatayi,sun sake sabo sosai a tsakaninsu,suna zama suyi hira mai yawa,irin wadda a baya basu taba yin irinta ba,a nan ta sake jij tarihin ameen din da kyau,tayi shuru tana tariyo maganganun da yaa barakan ta gaya mata,lallai sun sha gwagwarmayar rayuwa,kuma dama yawancin irinsu ameen din ariqi Allah yake musu na ban mamaki,gashinan kuwa,kome ya saka kansa zaiyi sai Allah ya sanya masa albarka.
Kwanakin da iman din taso yi wajen yaa barakan ta koma gida bai samu ba,saboda zazzabi da ya kama ya barakan,iman dince ta dinga kula da ita,tayi treating nata sosai,cikin kwanaki biyar ta soma murmurewa,ta warware sarai abunta.
********Karfe takwas saura ne na dare,suna zaune a tsakar rumfar ya barakan wadda ke wadace da haske saboda qaramar wutar solar da ameen din ya hada mata,tuwon dare suke ci,iman ya baraka yaranta maza ukusai autarta,kana ganinsu xakasan cikin walwala suke,har iman din.
Wayar yaa baraka ce tahau tsuwwa,iman dake zaune dab da wayar ta dauko tana duba mai kiran,AMINULLAHI ne a jiki kamar yadda ya barakan tayi saving
"Waye?" Ta tambayeta kafin ta miqa mata,batace komai ba sai ta miqawa usama da yafi kusa da ita ya miqa mata,yayin data ja kwanon tuwonta a hankali taci gaba da ci.
Har sukayi wayar suka qare batace komai ba,yaa barakan ta ajjiye wayar tana sake jan kwanon abincinta
"Qarfe nawa zaki tafin gobe?" Ta tambayi iman,ta daga kanta tana dubanta
"Sai wajen yamma inajin,tafiyar ranar nan bata da dadi ga motar haya,duk sai ka jigata kafin ta isa gida,sannan juma'a ce,zuwa yamma an sauko daga masallaci....akwai wani abune?" Kai ta girgiza
"O'o'o'o imani,akwai saqo ne da nakeso na baki ki kaiwa inna"
"Okay" ta fada tana ci gaba da cin abincinta.
Gefanta ta duba itama inda tata wayar ta kada,da alamun kira kenan,dr ahmad ne,dama kuma kusan lokacin kiransa kenan,sai ta tsame hannunta tana daukar wayar ta miqe a hankali,ya baraka ta bita da kallo,itama tasan me kiran,haka kawai take kishi dashi,bata sani ba....ko kishin da ya kamata qaninta yaji ne ita take jiye masa?,tana kallon sanda iman ta wanke hannunta ta kuma shige daki,saita sauke idanunta a hankali tana addu'a qasan ranta,zuciyarta tana motsuwa.
**********Washegari tunda suka tashi suka kammala abincin safe iman taga ya baraka nata hidimar hada dambu
"Shi kike sha'awa kuma yau yaya?" Iman ta tambayeta tana murmushi sanda take tayata tsinke zogale
"Wallahi,kuma baqi zanyi ma yau din" daga haka bata sake tambayarta komai ba,don ba dabi'arta bace bin qwaqwafi ko yawan tambaye tambaye.
Sun dan dauki lokaci kafin su gama hada komai,ta dauraye hannunta ta tashi tana bude tukunyar da badi'a ta saka musu ruwan zafi na wanka,ta diba ta sirka tana cewa
"Naga alama kadan ya rage dambun nan ya gama turara,bari kiga na fara shiri"
"Don Allah ki qara kwana yaa iman" badi'a ta fada tana kwabe fuska,don sosai taji dadin zuwan iman din,taji kuma dadin zama da ita,ta qaru da abubuwa masu yawa sosai,hakanan ta qara mata sha'awa da kuma qaimin zama nurse itama
"Makaranta badi'a" ta fada tana dan fidda blue eyes dinta
"Kai" badi'ar ta fada tana dan kare fuskarta tana dariya
"Me?" Iman ta tambayeta
"Wadan nan idanun naki ya iman.....aisai su tsiratani,kinga sheqin da suke a hasken rana?,na yarda da maganar kawu aminu kam"
"Me yace?" Ta tambayi badi'ar cikin mamaki
"Idanun imani na musamman ne,akwai wasu abubuwa masu yawa a cikinsu,amma ba kowa ne yake ganewa ba,amma ni nafi kowa fahimta da karantar haka' haka yace,amma nima yanzu na gani,idanunki na gayu ne" murmushi kawai iman din tayi,bata iya amsawa badi'a ba,sai kawai ta tsugunna ta dauki botikinta ta shige bandaki tana cewa
"So kike dai ki tsaidani badia,idan na biye miki lokaci zan bata,azahar ta kusa".
Koda ta fito alwala ta daura ta shige dakin d aka sauketa,ta tsane jikinta da kyau ta zube kayan shafarta ta fara gyara jikinta,komai na iman din mai ajine,farawar karatunta yazo mata da sauyawarta zuwa 'yar gayu ta gasken gaske,duk da cewa dama tunda ta taso ita mai son ado ce,Allah kuma ya hadata da lamin dake fiddata cikin tsararrkinta da dinkuna masu ban sha'awa,wanda ko a sannan sai jikin wance da wance,style kuwa duka yaran layinsu a wajenta suke karba.
Cikin wani lallausan lace mai zanen manyan flowers ta shirya,ba makeup tayi ba,amma yadda hodar da ta saka tabi fatar fuskarta man leben ya haska jajayen labbanta....daurin kanta ya zauna da kyau cikin wani style mai ban sha'awa ya sanya zakayi zaton zama tayi tayi kwalliya,iman me kyau ce har yau har kwanan gobe,kyanta yana da wani irin sanyi da kuma fusgar hankali,inda Allah ya rufa mata asiri,ta tashi gidan tarbiyya,batasan shigar banza ko fidda tsiraici ba,da mazan da zasu halaka ta sanadinta suna da yawa.
Tsakar gida ta fito zata shiga rumfar yaa baraka ta dauko jotter dinta da tayi amfani da ita jiya ta barta,zata qarasa rubutawa badi'a sunan wasu litattafai da zata dinga dubawa saboda turancinta ya zauna sosai,ya barakan dake cikin daki tace ta duba mata dambu ya nuna,ta zame murfin tukunyar ta bude buhun ta debo tana tabawa,dai dai lokacin da sallamarsa ta ratsa tsakar gidan,abunda batayi zato ko kuma tsammani ba,don haka ta waiwaya gefanta inda qofar shigowa take.
Aminullahi ne,cikin shigar manyan kaya,komai nashi fari tas,kayan da suka qara masa cika kwarjini da kuma kamala,fuskarsa tayi fes fresh da ita,ba abunda take fitarwa sai annuri,gashin kansa dana fuskarsa yasha gyara,duk da cewa matafiyi ne amma jikinsa bai nuna hakan ba,sassanyan qamshinsa ya busa da iskar dake kadawa cikin tsakar gidan ta kwasoshi da gudu izuwa hancin iman,yanayin da ya haifar mata da faduwar gaba,tsimammun idanunsa masu dauke da wani magnet suka so kashe mata jiki da zuciya,cikin tata jarumtar ta janye idanun nata tana amsa sallamarsa,tare da qoqarin saka dambun data debo da yatsun hannunta a baki ta fara taunawa.
Idanunsa sauka kan labban nata da suke qyallin lip balm,tana motsasu a hankali saboda taunar da takeyi,ya dauke kansa da sauri saboda wani abu daya zuba cikin jikinsa,ya waiwayawa ga usama da musa da suke biye dashi
"Kun dauko komai?"
"Eh kawu" sai yaci gaba da takowa zuwa cikin gidan,wanda kafin ya qaraso iman ta shige rumfar yaa barakan,a saurin da take na dauko jotter din tayi tabar masu falon.
Saidai kuma sanda ta dauka take shirin juyowa tuni ya cire rufaffun takalman qafarsa ya sanyo qafarsa zuwa parlon,dole cikin hikima ta koma da baya ta zaune cikin kujerar da tafi kusa da ita tana buda shafukan jotter,batason a yau ta bashi dama ko qofa ko guda daya da zata bada kanta ko aikata wani abu ba dai dai ba,don haka tabi sahun 'yan sannu da zuwa ta marabceshi kamar kowa,dai dai sanda ya baraka ta iso falon fuskarta cike fal da fara'a
"Wai dama da gaske kake?,kai dake da tarin ayyuka fal a gabansa?,da kayi zamanka ai tunda na warke,itama iman din anjima kadan zata koma"
"Bazan nutsu bane idan banzo na ganki ba" ya qarashe furucin idanunsa na sauka akan iman,tayi masa wani kyau daya jima bai gani ba,shigar ta karbeta abundanita bata sani ba,abunda yadan ja hankalin ya baraka,ta gefan idanu take qoqarin gano me yake kalla?,saita saki boyayyen murmushi kafin ta amsa masa
"To ai gani lafiya qalau alhmdlh,babu abinda ya gutsireni ko?" Maida dubansa yayi gareta,cikin girmamawa ya fara gaisheta
"Barka da yamma,mun sameku lafiya?"
"Alhmadlh,ya inna da malam,ya ka barosu?"
"Lafiya qalau,sunce na gaidaki da kyau"
"Na gode sosai,na warware" waiwayawa tayi inda iman take
"Iman,muna da ruwa kuwa?" Sai a sannan ta daga kanta,cikin wani salo da bilhaqqi batasan tayishi ba tayi maga a yangance
"Ba za'a rasa ba" saita ajjiye jotter din ta fara takawa a hankali zuwa tsakar gidan,inda a rumfar da aka kafawa qofar dakunan yaa barakan dan madaidaicin fridge dinta da lamin din ya siya mata yake,kamar wanda ake jansa haka yaji zuciyarsa na mararin binta da kallo,amma ya nuna matuqar mazantaka ya danne kansa
"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" ya dinga maimaitawa,baisan me ya faru dashi ba,wani tsohon abu......wani tsohon miki keson tasar masa,wani tsohin feelings da kuma wani mataccen yanayi daya jima da zubdashi a wani waje mai nisan gaske.
Da ruwan dama sauran lemon kunun aya datayi musu a jiya ta shigo saman dan faranti,tana shigowa ya baraka ta miqe
"Zuba masa ina zuwa,bari na sauke dambun"
"Ki bari na sauke yaaya" iman ta fada tana sauri saurin dire masa ta fice
"A'ah,wanka zan shiga ai daga can,ni kaina zafi nakeji,wasu zannuwa na nakeso kiyi musu iron inason sakasu anjima zan leqa suna hayi" bata saurareta ba ta nuna mata dutsen gugar ta sanya kai ta fice.
Daga tsakar gida ta yiwa yaran magana kan kada wanda ya shiga parlor din,ta sauke dambun,ta saka badi'a shiryawa ameen nasa a fulasai masu kyau sannan ta wuce wankan.
Daga can parlor kuwa kamar an buge mata gwiwoyinta haka iman taji,bata shirya zama dashi waje daya ba amma yaa baraka ta rushe mata dukan plan din nata,hasalima inda socket din gugar yake yana daura da ameen dinne,saidai duk da haka ba zata bari yaga lagonta ko karayarta ba,don haka ta qarasa gabansa ta tsugunna,ta bude lemon ta fara tsiyaya masa a cup daidai misali,sannan ta dauko zata miqa masa.
Batasan duk abinda take ya kafeta bane da ido sai data miqa masa lemon,maimakon yakarba sai yaci gaba da sauke mata nauyin idanunsa
"Gashi" ta fada cikin jarumta,duk da yadda taji zuciyarta kamar ta fara narkewa
"Mantawa kikayi cikin gidan nan ba mata bane kadai akwaisu usama?" Da mamaki ta dago ta kalleshi,saidai ta kasa jurar kallonshin,saboda idanunsa sun ninka nata a nauyi da dafi mai tarin yawa
"Su usama kuma?"
"Eh,ko su ba aure a tsakaninku?.....duk da ban sani ba ko wancan likitanne ya baki wannan damar......" Daga haka ya miqa hannu zai amshi cup din,ta fada nazari kan ma'anar maganarsa,abunda yasa bataga tahowarsa ba,sai sukar dumin hannunsa saman nata hannun,take ya ratsa dukka wasu sassan jikinta qashi da jini yakai ga qwaqwalwarta cikin sakannin taqaitattu.
Kamar jan wayar wuta hakanan kowannensu yaji,suka janye hannunsu lokaci guda,sanadin barewar lemon kenan saman skeet dinta,ta miqe da sauri sakamakon sanyi daya ratsata,kallon kallon sukayi na second biyu,sai ta juya da hanzari ta fita a parlor din.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 58
Ajiyar zuciya ya saki yana maida jikinsa zuwa bayan kujerar yayi relaxing yana sauke ajiyar zuciya,wani yanayi na bin dukka sassan jikinsa,gajiya na sauka a gabbansa kamar wanda aka yiwa duka,gajiyar da tuqin ma da yayi daga kano zuwa jigawan bai jita ba,a haka yaci gaba da kasancewa,shi baisha ruwan ba bai kuma sha lemon ba,hakanan bai buda idanunsa ba har saida ya baraka tayi sallama cikin parlor din,idanunta kan fuskarsa sanda ya bude idon nasa tana karantar yanayinsa
"Ya bakasha komai ba?"
"Am ok,da ruwana a mota ma.....qarfe nawa masallacinku suke tayar da sallar juma'?" Yayi tambayar yana duba agogon hannunsa don kaucewa tuhumar ya baraka
"Qarfe biyu ne"
"Ok,bari muje can muyi salla mu dawo,naga biyun saura" saiya miqe yana kashe wayarsa ya barta nan saman kujerar,ya zare agogon hannunsa yana kiran usama
"Kuyi alwala mu wuce masallaci,kuna kusa da masallaci amma ku dinga zama a gida?,ba zaku tafi da wuri ba har sai kunji an kira sallah?,kunsan falalar zuwa masallaci da wuri kuwa?" Da wannan fadan suia fita tsakar gida,badi'a ta zuba masa ruwa a buta yayi alwala,ya cire babbar rigarsa ya bata suka wuce masallaci shida 'yan mazan.
Tana daga daki tana jiyo badi'a dake shanshana rigar ameen
"Kai jama'a,kawu wanne irin turare yake sakawa?,waishi wanne irin dam gayune?,komai nasa qanshin yake,yaaya,Allah rannan da yazo ya kwana yace na hada masa kayan datti cewa nayi basuyi datti ba,don ni dai qamshi naji sunayi" bata ji dai amsar da ya baraka ta bata ba,amma taji badi'ar tayi dariya sannan ta wuce zuwa cikin parlorn.
Shuru shuru basu dawo ba,harsai da ya barakan ta fara jajjabi da cigiyarsu sannan taji shigowarsu,muryar usama taji yana lissafa mata gidajen 'yan uwa sa sukaje,yaje gaida tsofaffi cikin danginsu da kuma yi musu alkhairi kamar yadda ya saba,wannan al'adarsa ce kuma dabi'arsa ce duk sanda ya shigo jigawa zaiya zagayawa dattijai da manya na gari dama na cikin familynsa,wannan ya sanya masa farinji da kuma daukaka,sannan ya siya masa soyayya mai tarin yawa daga wajen mabanbantan mutane,iyayensa da suka rasu kuma suka samu addu'o'i masu tarin yawa daga makwancinsu.
Tanaji ya baraka na kirata,sai kawai ta miqe ta tayar da sallah abunta,data idar ma zamanta tayi,sai data ji tana sake kiranta sannan ta tashi,ta sauya kayan jikinta tun dazun zuwa wata bubu ta material ruwan makuba mai dan haske kadan,ta yane kanta da mayafinta ta nufi dakin.
Shi ta fara gani,sabida ya zauna ne yana fuskantar qofar shigowar,cikin babban faranti aka zuba musu dambun shi da usama da musa suke ci tare,yana da wannan sauqin kan qwarai da kuma son mutane,a jininsa yake,ita shaida ce,kanta ta kawar cikin basarwa da nuna halin ko in kula ta qarasa wajen ya baraka
"Ya zaki zauna daki kowa yana zaune yana cin abinci?" Murmushi tayi,murmushi da ya qawata fuskarta qwarai
"Sallah nayi,yana raina,har Alla Allah nake na idar" agogo ya barakan ta kalla
"Ai gwara ki hanzarta,don kamar qarfe biyar naji yace zaku wuce" dan turus tayi,ita sam bata wani kawo tare zasu tafi ba,kuma ko yanzun batajin zata bari su tafi tare,bata marmarin hakan,gwara kowa yayi hanyarsa
"Ko?,tafiyar tamu zatayi dai dai?,ko na biyo shi a motan kasuws gudun bata lokaci?" Tas ya gano inda ta dosa,ya kafeta da idanunsa daga nesa inda yake zaune yana karantar fuskarta
"Aha saboda wahalar dakai?,ki gama a nutse,abunda baki hada bama na taho miki dashi idan zan wuce maiduguri" a hakali ya dauke dubansa daga kan iman ya maida kan ya baraka,me zataje yi a maiduguri kuma?,iyakar saninsa a danginsu basu da kowa a can bare yace zumunci ko kuma wani abun zai kaita,bai tambaya ba,sai ya maida kansa kawai ga abincin da suke ci.
Karo na biyu kenan badi'a ta shigo dakin,ta dubi iman dake xaune sosai abunta,kamar ba ita ya ameen din ke jira ba
"Yaa iman.....yace ki fito,ke kadai suke jira wallahi,har ya kunna motar" a nutse ta dubeta hankali kwance
"Tare mukazo da xaki damu yana jirana?,ba nace miki yayi gaba zan taho a bayanshi ba?" Dan buga qafarta kadan tayi sannan tace
"Wallahi na gaya masa....shine ya sake turoni"
"To kije ki maimaita masa,tunda saqon dai dana baki kenan" daga haka ta jawo wayarta tana duba kiran dake shigowa,ba kowa bane dr ahmad ne,saita daga wayar ta kara a kunnenta.
Kashe motar yayi yabar key din a jiki bayan badi'a ta gama bayaninta,ya zuro qafafunsa a hankali ya taka zuwa cikin gidan,ransa yadan baci amma kuma ya danne,zuciyarsa nata lissafa masa abubuwa iri iri kan ma'anar qin tafiyarta dashi.
Kai tsaye dakin da take ciki ya nufa,yasa hannu a nutse ya yaye kabulen dakin,hasken da ya bayyana shi ya ankarar da ita wanzuwarsa a wajen.
Wayar dake kunnenta fa sauke,yabi wayar da kallo kafin ya maida dubansa kan fuskarta
"Tashi ki wuce muje" ya bata umarni kai tsaye cikin dakakkiyar muryarsa yana kallonta tsakiyar idanunta kanshi tsaye,irin kallon da a baya yake mata can shekarun baya duk sanda tayi wani laifi yakeson kuma nuna mata tayi laifin ba tare da ya magantu ba.
Bata da zabi illa miqewa da tayi,saidai fuskarta ba annuri,ta qarasa inda ta ajjiye akwatinta ta kuma dora mayafinta akai sanda tayi shirin tafiyarta tun na dazu,ta yafa mayafin ta fidda takalmanta ta sanya duka yana tsaye,saita tako a hankali zuwa bakin qofar fita,sai kuma taja ta tsaya,saboda babu wani sauran space daya rage mata da zata iya fita,idan kuma tace zata saka kai a hakan ta fita to ba shakka saita fara mannuwa da jikinsa.
Kamar xata saki kuka yadda ya tsaya ya zuba mata idanunsa yana kuma hukuntata dasu ba tare da ya dauke kallonsa ba,ya kuma sani cewa lallai saiya matsa din xata samu hanya,duk da yadda ta dauke masa kai amma jikinta yana karbar horo yadda ya kamata,idanun ameen din nada wani irin tasiri tattare da ita,don ko sanda tasha giyar maqaryaciyar soyayyar bassam tayi tatil bata iya kallon qwayar idanunsa ta gaya masa magana kanta tsaye
"Zan wuce" ta fada ganin bai da niyyar matsawa
"Wuce" yace da ita,ta daga kai tana duban hanyar daya bata,tazarar bata da wani yawa,idan ba mugun kulawa tayi ba saita shafeshi,wannan wanne irin sabon abune kuma ya amin din yazo dashi?.
A hankali kuma cikin takatsantsan ta soma ratsawa ta gabansa,sai dataje tsakiya ya rufe hanyar,numfashinta gaba daya ya tsaya a maqogoronta,da tabbas ko yaya ta motsa cikin faffadan qirjinsa zatayi masauki
"Duk randa na sake cewa ayi abu kika musamin zakiga yadda zanyi dake,idan kin manta na tuna miki....lameen ne.....yayanki daya raineki da hannunsa tun kina majina a hanci,wannan girman da kuma auren da kika tabayi bazai sauya komai ba" ya qarashe maganar yana duqawa har tana jiyo saukar numfashinsa saman fuskarta,ya sabule jakarta data ruqo
"Wuce ki jirani" ya fada tana dai daita tsaiwarsa,wuf tayi ta samu ya fice,qafafunta na sarqewa saboda tsaratan da tayi,saboda ta tsammaci lamin din rungumeta kawai zaiyi saboda tsabar kusancin da yayi yawa a tsakaninsu.
Luf tayi a gidan gaba,tana jin yadda kowanne sashe na jikinta yake amsawa,ajiyar zuciya take saukewa a jejjere,idanuwanta a rufe har zuwa sanda badi'a ta kawo mata jakarta ta sanya cikin motar,tazarar kusan minti biyar taji muryarshi,ta karkata kanta zuwa gefe a hankali,ta hangeshi yana rabon kudi wa su usama da abokanshi,fuskar nan a tsume,batasan me yasa idan ya hade rai irin haka yake qara masa kyau ba,sai ta maida idanunta ta lumshe,don bata fatan ya juyo yaga tana kallonshi ta kunyata,ko kuma ajinta ya zuba.
"Subhanallazi sakkara lana haza wama kunna lahu muqrinun,wa inna ila rabbina la munqalibun" ya furta addu'ar da lallausar muryarsa bayan ya kunna motar,har zuwa sannan bata yarda ta bude idanunta ba,a hankali ya fara motsata suka fara barin layin.
Wata tafiya sukayi ba um ba um um,sai daga bisani ya dannan wani karatu wanda ke magana kan bin iyaye da kuma haqoqinsu akan dansu,a hankali karatun ya dinga shigarta,ya kuma kashe mata dukkan wata laka ta jikinta,sosai karatun malamin ke shiga duk wani bargo na jikinta ya kuma bi ta magudanar jini,lallai da gaske a baya ta tafka kuskure mai girma a rayuwarta,Allah ne yaji qanta ya kuma tsamota,da kuma addu:ar da ta tabbatar su innan sunci gaba da yi mata ita,koda a zahiri sun nuna basa tare da ita.
Ko wayar da dr ahmad keta faman yi mata kasa dagawa tayi,tayita rejecting tana maida idanunta ta kulle,sunyi nisa sosai ya sake kira
"Koki kashe ko ki sata a silent,ko kuma ki daga,qararta yana damuna,idan kuma na karba ta tafi kenan,ta window zan cillata" sosai kalamansa suka bata mamaki,wai yaushe ya lamin din ya koyi zafi haka?,tadan saci kallonsa da hanzari ta kuma dauke kanta,har yanzu fuskarshin a cakude take,sai kawai ta tura masa gajeran saqo tans hanya,idan ta isa gida zata sanar masa,ta kashe wayar gaba dayanta ta jefata a jakar hannunta,ta gyara zamanta da kyau ta lafe cikin kujerar motar.
Sun baro jigawa da wuri,to amma wajen shigowa kano anan matsalar bata lokacin take,sun tadda tarin traffic a hanya daya dinga bata musu lokaci,wannan yasa basu isa gida ba sai ana sallar isha'i,don suna shiga ma a toilet din farfajiyar gidan ta daura alwalarta tayi ciki,Allah yasa ma ya tsaya a wani masallacin hanya na matafiya sunyi magarib,ya kuma siya musu takeaway.
Da idanu inna ta bisu sanda suka shigo mata,wani abu na taba zuciyarta,tana kuma rayawa cewa inama a matsayin miji da mata suka shigo mata?,sunyi bala'in dacewa,irin dacewar data amsa sunanta,sannan fili da badini kuma babu ta inda basuyi marching ba.
Mufida kam dadi ya isheta yaa iman ta dawo,sadiqu ya kalleta
"Idan tayi aure naga ya zakiyi,ba zaki iya zama gidan nan ba kenan" sadiq na gama fadawa miqewa ameen yayi,hannayensa cikin aljihunsa yace
"Zan shiga na watsa ruwa,a gajiye nake,idan ka shigo xakaji yadda ake ciki da mutanen nan,dazun inakan hanya sun kirani"
"Okay,karka damu,ka huta sosai,ko zuwa gobe ma tattauna"
*********** Da sauri da sauri kwanakin bikin da aka sanya suke qara rage kansu,lokaci yaci gaba da wullawa yana kuma matsantowa,ya zuwa lokacin iman din sam ko a jikinta bata wani jin cewa aure zatayi,kawai kallon kowa da komai takeyi,a yanzun hankalinta gaba daya yafi tattara ga karatunta,saboda batason ta samu wani kuskure ko tasgaro,tanason koda bata tsira da komai ba ta tsira dai da karatun nata.
*********Ranar wata laraba da yammaci ta dawo daga makaranta sukaci kacibus da yaa baraka a qofar gida,tana rataye da jakarta,sadiqu na biye da ita da wata babbar leda a hannunsa
"Ashe da rabon dai zamu hadu,shi yasa ya gana ta zaunar dani" ta fada fuskarta fal murmushi tana duban iman,murmushi itama iman din ta maida mata,a wannan karon ta cika da mamakin yawan ganin ya baraka da take a gidansu,wanda a baya sam ba al'adarta bace,takan jima bata shigo kano ba saida wani dalili,amma kuma data tuna bikin dake cikin gidan nasu harda na dan uwanta qwaya daya tilo sai mamakinta ya ragu,saidai kuma taji ta ambaci yaagana,badai bikin da ya rage sati kusan hudu ta tahowa tun yanzu ba?.
"Don Allah ya baraka ki bari sai gobe,kinga fa yamma tayi sosai,kafin kije dare yayi,kuma naga ya lamin din baya kusa bare ya kaiki koda tasha ne" ima din ta fada cikin kulawa
"Ahaf.....rabu da dan nema,dama banaso yasan nazo din ai,saidai yaji labarin zuwan nawa....kedai ki kwantar da hankalinki,tun ana saura sati tahowa kano ya sameni,sai an gama komai 'yan jigawa zasu kuma ganina" murmushi kawai iman tayi wanda ya tsaya mata iya wuya,ita kanta kenan tana farinciki da auren samha da dan uwanta,saidai sam bataga laifinta ba,babu wanda bazaiso ace nashi yaci gaba ba,dole a nan sukayi sallama ta bata sallahun gaida mata da badi'a ta sanya kai zuwa cikin gidan.
A hankali tayi sallama cikin parlor dinsu,saidai a maimakon ya gana dake zaune a parlor din ita da inna ta amsa,saita rafka mata guda,gudar data sanyata karaya,wasu tarin tawagar hawaye suka danno kai,saidai tayi qoqarin tsaidasu,sannan uwa uba salatin da taji yaagana ta rabza wanda ya sanyata tsaiwa cak cikin tsoro tana dubanta...
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 59
"Yau me zan gani ni aishatu?" Ta fada tana kame baki tare da qarewa iman kallo,kallon da ya sanyata ta tsargu,ta kuma soma bin jikinta da kallo,mufida ce da itama ta tsorata tayi qarfin halin tambaya
"Mene yaa gana"
"Amarya nake gani gayanta,babu wani canji,babu kuma wani abu da zai nuna maka cewa amarya ce,wannan abun kunya har ina?,ke binta kina me?" Cikin kara da kuma alkunya irin ta innar ta miqe tana murmushi,ba zata iya cewa yaagana komai ba a matsayinta na yayar mijinta,sai kawai ta fada kitchen tabar su mufida da dramer.
Cikin sanyin jiki dana gwiwa iman ta fara takowa,a qalla tadan samu wani qwarin gwiwar,tsoron da ya ganar tasa taji ya ragu
"Wallahi yaagana kin masifar ban tsoro,na dauka wani abun kika gani a jikina"
"Wani abunne mana,wannan abun kunya har ina?,kina can zaki qare a yawon boko,auranki saura 'yan satittika amma baki canza daga yadda na sanki ba?,to Allah ba za'ayi wannan abun kunyar damu ba,wannan auren dole ayi masa shiri na musamman ehe...saboda wancan babu rawar da muka taka,so nake ki canza gaba daya,idan ba kyakkyawan sani akayi miki ba banason a ganeki" baki kawai iman din ta saka tana kallon yadda yagana ta haqiqance,wai ko don basusan yadda takeji bane a zuciyarta?,jinta take kamar mutum mutumi,basusan ta fidda miji bane saboda ba zata iya cewa malam bata da kowa ba?,ta fidda mijine saboda ta fuskanci sun shirya aurad da ita?,batason tace bata da tsayayye kada hakan ga sake bata musu rai.
Duk lissafe lissafen da yaagana ta shiga yi kallonta taci gaba dayi,so take ta sarara mata ta barta ta shiga dakinta ma ta raba kanta da kayan jikinta.
Kamar bushira tasan me akeyi saiga sallamarta,ajiyar zuciya iman ta saki
"Yauwa,don Allah bushira qaraso"
"Eh qaraso ciki,dama ke nake nema" yaagana ta fada,akwai kyakkyawan sani da kuma alaqa mai kyau tsakaninta da bushira,tun zamanin rikicin aurenta da bassam
"To gani yaagana,Allah yasa ba laifi mukayi ba?" Ta fada tana dariya hadi da neman wajen zama
"Qatoton laifi ma kuwa,zaman me kuke naga amarya gaya babu kayan hadi?" Kallon iman bushira tayi,ta danne dariyarta sanda iman din ta rausayar dakai,duk ta zama kalar tausayi,da alama kwata kwata lissafin yaagana baizo dai dai da kwanyarta ba a wannan lokacin,babu abunda maganar ke qara mata sai sake jefata a rudu da takeyi
"Kiyi haquri ya gana,daga gobe in sha Allah xaki fada ganin canji"
"Yauwa,so nake kowa yatabbatar yanzu zatayi aure,kuma ita din jinin kanuri ce,nan da kwanaki biyar ma idan zan tafi tasata zanyi a gaba mu wuce borno,idan hidimar ta matso ma dawo tare,saina tsumata na jiqata da kyau" miqewa kawai iman din tayi,ta kuma ja hannun bushira,saboda duk wata dauriya tata ta qare,kuka ke shirin kubce mata.
Suna shiga dakin kuwa ta saki kuka sosai,bushira ta fidda idanu tana jawota zuwa kafadarta,babu musu kuwa ta dora kanta akai
"Meye haka iman?,so kike ki tadawa mutane hankali?" Da qyar ta samu tayi controlling kanta,cikin sautin dake dauke da kuka kanta ta fara magana
"Wai me yasa bani da sa'a kwata kwata bushira?,me yasa soyayyaa take zuwa a hagunce?,cikin mummunar rashin sa'a" da sauri bushira ta dakatar da ita
"Ki gyara kalamanki iman,yanzu kuma me kikaga anyi?" Wani dunqulallen abu mai ciwo ta hadiye kafin ta iya bata amsa
"Kinga fa,wannan auren nawa sukewa murna haka?,wannan auren nawa kowa yake ciwa alwashi?,auren da har yanzu bani da tabbacin na shirya ko ban shirya ba?" Hannu bushira tasa tana goge mata hawayen,ta kuma ja tsaki
"Wannan shine tashin hankalinki?,indai shine ki kwantar da hankalinki,indai har kina yin addu'a kici gaba dayi,na tabbatar da cewa ubangiji yana tare dake,kuma yana sauraronki,hakanan bazai kunyataki ba" cikin hikima da tatausan harshe da qawar da tasan ciwon qawarta bushiran ta saukar da ita qwarai,har iman din ta shiga wanka bayan ta sanya mufida ta kawo musu abinci.
"Na jiki kina gayawa yaagana wai daga gobe zan fara gyaran jiki,toni bazan iya wannan aikin ba,hasalima bansan wajen wani gyaran jiki ba yanzu,iya mayukan da nake amfani dasu sun isheni,idan baya sona a haka har sai an masa gyaran jiki ya haqura" iman ta fada suna tsaka da cin abincin ita da bushira.
Murmushi ya kubcema bushiran
"Shikenan,saiki shirya bin yagana maiduguri ta kaiki ta killaceki" wani kallo tabi bushira dashi
"Babu inda zani,don a satin nan din ma da take zance,muna da abu mai muhimmanci cikin makaranta"
"Kinga to muyi magana,Alla yagana da gaske take,kuma matuqar taga bamu fara anan ba,babu wanda ya isa ya hanata tafiya dake,idan kinason ta barki ki yarda kawai a fara goben ta gani,idan ta tashi tafiya saiki bata uzuri,wala'alla ta yarda,idan don wajen gyaran jikine,ga AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISES" ambatar sunan ya tuna mata da wajen,ba shakka matar duniya ce wajen iya gyaran jiki,ita ganauce ba jiyau ba,hakanan ya tuna mata da lokaci irin wannan,lokacin da batajin bari,lokacin da suke kan digimi da rawar qafar aurenta da bassam,ya Allah!....kada ka kawo abunda bazai wuce ba, tafada tana lumshe idanunta,har kwanan gobe tana jin haushi da kuma zafin aurenta da bassam,inda ace tana da iko da zata dawo da rayuwarta ta baya ta shafe bassam a ciki,tunda suka rabu basu hadu ba,batasan ma wacce rayuwa yake ciki ba,bata kuma fatan haduwarsu ko jin labarin nasa,don hakan kamar famin ciwone zaiyi mata.
"Bani number dinta nayi loosing tawa tunda na canza layi,don a karan kaina ina buqatar zuwa wajen matar dama,har kema,bawai sai amare ko matan aure kawai ba,ko babu komai zaka kwaso sirrin qamshi da sirrikan gyaran jiki"
"Ni kuwa nasan da haka,ga number don bana rabo da ita,kona rasata ma ina da ita a rubuce saboda bacin rana irin haka" wayarta ta buda ta fara karanta mata number kamar haka 08067558902.
Iman din tayi serving ne kawai ba tare da tana da tabbacin cewa zata je wajen ba,duk da yadda tayi amanna da yaqinin iya gyara da kuma sirrikan qamshi masu gigita hankalin abokan zama dama oga mai gida gaba daya,amma da yaagana ta tashi tafiya ta tabbatar zata tafi da itanne kamar yadda tace,babu shiri ranar daga makaranta ta wuce wajen,sukayi total ta biyata kudaden gyaran jikin na tsahon satittikan da suka rage,tayi mata transfer take ta tura mata,rai da zuciyarta fal haushi,don tana ganin kamar asarar kudinta tayi.
Kwata kwata ko a mafarki bata kawo zancan fidda anko ba a ranta,amma saiga bushira da atamfa
"Bushira......wai meye hakan?,ko aurena na fari banyi anko ba sai yanzu?,wai da wanne irin farinjini dr ahmad yaxo muku ne?"
"Aurenki na fari daban da wannan ai,shi kuma dr ahmad ai kowa da irin nasibinsa" kai iman din ta kada ta jawo wayarta tana latsawa
"Banga amfanin yin anko ba,saboda ba taro zanyi ba ni"
"Eh ai dama iya na ran yini ne malamarsu sai walima kuma"
"Itama walimar bance ma dr zanyi ba"
"Ni na gaya masa da kaina" bushira ta bata amsa tana miqewa
"Already ma yaagana ta bada kudin an sarota,duk meso ki hadani dashi,karki damu kanki sai kin shiga harkar bikin nan" daga haka bushiran tayi gaba abunta,sai iman din ta bita da kallo,tana mamakin yadda suka daukaki lamarin gaba dayansu.
Dauke kanta tayi bayan fitar bushiran ta mayar kan wayarta tana neman number dr ahmad din,karon farko da zatayi kiranshi tsahon tarayyarsu,tana son suyi magana dashi,batason wani bidi'a ko wani abu daya danganci shagalin biki,saboda a yanzun gaba daya ba wannan bane a gabanta.
Sau wajen uku tana kira amma number taqi shiga,sai ta ajjiye wayar tabar kiran,ta miqe ta ta dauko wata qaramar hula mai santsi ta sanya a kanta,gashinta dake fake cikin ribbon ya fito ta qasan hular,baqi sidik dashi mai santsi da daukan idanu,saboda ita din ba baya bace wajen kula da gyaran kanta da jikinta gaba daya,wata irin 'yar gayu ce iman wadda bata wasa da duk wani abu daya shafi gyaran mace,kama daga turaruka mayukan da sabulai na wanka masu kyau da qamshi,don ko lalle da wuya ka dubi yatsunta ka ganshi fari babu jan lalle,dama ba kasafai ta fiya yin baqin lalle ba.
Bata tsammaci samun kowa a parlor din innar ba,saidai tana sanya qafarta dashi idanuwanta suka fara cin karo,yana zaune qasan tiles saman dardumar daya shimfida,sanye yake cikin wani lallausa yadi ruwan sararin samaniya wanda aka yiwa dinki me kyau da aji irin na matasan zamani,hannunsa dake sanye da lafiyayyen agogo na fata me tsada na kamfanin Prado yana riqe da paper da kuma biro yana ta rubutu yana kansile wani,kaya ne masu yawan gaske a tsube a tsakiyar parlor din,kama daga atamfofo laces mayafai da jakankuna.
A hankali ta janye idanunta daga kansa,ta rasa yadda zata hana kanta jin faduwar gaba duk sanda haduwar waje daya ta gamasu,dai dai lokacin da ya sanya yatsansa guda daya ya sake gyara zaman glass din fuskarsa,ya daga kansa a hankali xaiwa anty hassana matar ya muntari magana,idanunsa suka sauka a kanta sanda take takowa fuskarta na fidda murmushi,idanunta akan fuskar anty hassana
"Kai....anty yaushe kika shigo?" Iman ta fada da muryarta data zama mai wani irin sanyi
"Shigowata kenan inna tace na zauna na duba kayan nan ko akwai abunda babu a ciki,to bamu gama ba kuma sai gaki kin fito" qarasowa tayi ya zauna a hannun kujerar dake dab da anty hassana ta fara gaidata sannan ta duqa tana daukar yaronta dake saman cinyarta Tana dan masa wasa,kana cikin basarwa ta gaida ameen din ba tare data dubi sashen da yake ba.
"Lallai amarcin nan da Alama zai karbeki da kyau,irin wannan kyau haka?,amma ko wace tayi miki wannan gyaran jikin ta iya...." Kamar wanda aka fusga hankalinsa ya daga idanunsa a hankali ya sauke a fuskar iman din sanda take duban jikin nata gami da tabe baki
"Wallahi yaagana ce,haka kawai ina zaman zamana ta tattago min aiki,ko naje ayimin ko ta wuce dani maiduguri,haka ta sakani ba shiri na fidda kudina naje na biya" sauke idanunsa yayi daga kanta yana fidda wata ajiyar zuciya,ilahirin gangar jikinsa tana amsawa,sai ya ajjiye abun rubutun ya miqe yana xuba hannayensa a aljihun rigarsa
"Idan kun gama dubawa mom(haka yake kiran anty hassanan)kuyimin magana,sai aga abunda ya kamata a qara din"
"To to shikenan,ba damuwa" ta amsa masa,saiya juya a hankali yana takawa har ya fita a parlor din,abunda ya bawa iman damar sakewa ta zauna sosai sukaci gaba da hirarsu da anty hassana,harma ta manta cin abinci ne ya fiddota,bata bar wajen ba sai da antyn tayi maganar kayan lefen ameen dinnne ake hadawa,ta duba taga sunyi?.
Maida dubanta tayi ga agogo tana son hadiye da kuma basar da abinda ke taso mata,sai ta miqe tsaye
"Ba lokaci anty hassana,kema ai kinsan kan kaya sosai,munyi da me gyaran jikin nan kada nayi yamma sosai"
"To shikenan" daga haka ta samu ta wuce kitchen,ta zuba abincin ta tsaya a nan ta cusa shi,don dama ba wani abincin kirki take iya ci ba,a haka take tilasta kanta saboda gudun ulcer,don a jikinta ta fara ji kamar tana son kamata ne.
Ba lokacin tayi niyyar fita a gidan ba amma dole ta fidda kayanta don yin wanka,sai ta tuna sunyi da bushira zata zo da yammar,don haka ta qarasa wajen wayarta da niyyar kiranta kada tazo bata cimmata ba.
Envelope guda biyu dake nuna shigowar saqonni daga mabanbantan gurare cikij wayarta ne suka nuna,ta zuba musu idanu kafin ta shafa fuskar wayar ta bude ta nufi ma'adanar saqonnin nata.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 60
Daya saqon daga banking da take amfani dashi ne,suka turo mata alert na shigowar kudi a wayarta naira dubu dari hudu da hamsin,mamaki sosai ya kamata,ta duba sunan wanda ya turo babu suna,pos agent ne,da alama daga wani shagon pos din kudin suka shigo,to waye zai turo mata wadan nan kudaden?,fita tayi ta buda daya saqon
*_Assalamu alaikum warahmatullah,ga saqo nan na gyaran jikine,here is my new number_*
Dr ahmad ne yazo kanta,layi ya sauya kenan,shi yasa koda ta kira kiran bai shiga,ta sanshi da busy,wala'alla wata sabgar ce ta riqeshi,saita sauka gaba daya,tayi copyiny number ta fara trying layin daya turo saqon,saidai kuma abun mamaki a kashe ta sameta,gajeran saqo kamar haka ta tura masa
*_thanks_* ta sauka ta sake kiran bushira
"Ai saidai kiyimin haquri yau amarya,wallahi umma ta aikeni gidan basira,amma zamu hadu gobe in sha Allah"
"Ba matsala,ki gaisheta" ta sauke wayar tana shiga bandakin.
Tsaf ta shirya cikin atamfa riga da skart,jikinta ba abinda yake fiddawa sai qamshin hadaddiyar humrar da turarukan jiki dana kaya da aka samar a amaryar kb global enterprises,ita kanta a karan kanta jin dadin qamshin turaruka take,abinda ya sanyata ta fara amfani da abinta kenan,ta dauko hijabinta da yasha karin guga kala da kayan jikinta ta sanya,sai tayi wani irin kyau me sanyi,kyakkyawar fuskarta ta fita ta tsakanin colour din hijabin da yayi masifar fidda kyau da haskenta wanda ya cakuda da lafiyayyen gyaran jikin da take samu daga amaryar kb global enterprises.
Tayi sallama da inna da anty hassana ta wuce zuwa farfajiyar gidan,daga can sashe daya na 'yar farfajiyar gidan nasu ta hangi malam da amin,malam din na daga tsaye,amin din ya russuna kadan da alama magana sukeyi.
Cikin girmamawa ta yiwa mallam din barka da warhaka
"Ina zuwa da yammacin nan" dan murmushi ta saka tayi qas da kanta,tanajin nauyin yi masa bayani,a jikinta takejin idanunsa na kanta
"Zanje waje me saida turare ne"
"To yayi kyau,kada kiyi dare"
"In sha Allah" ta fada tana takawa zuwa gaba a hankali ta tura qofar ta fice a gidan.
Layin nasu babu mutane sai jefi jefi,hakan baya rasa nasaba da kasancewar yammaci ce,duk da dama dai unguwar bata fiya cunkoson jama'a ba.
A hankali iska ke kada hijabin jikinta daga hagu zuwa dama,lokaci lokaci tana saka hannu tana riqeshi saboda yadda yake damunta,kwanyarta na mata tariya na da lissafin kwanakin da suka rage mata na zamantowa matar wani,sam bataji tahowar motar ba,sai uban horn da ya kusa gigitata,saitinta ya tsaya,ya sauke glass na motar,idanunsu suka hadu waje daya,ita ta fara janye idanunta kamar ko yaushe
"Tunanin me kike haka har kin fara hawa hanya baki sani ba" ya fada da muryarsa mai nauyi da kwarjini,har yanzu idanunsa na bisa kanta,amsar da zata bashi ta laluba ta rasa,ita sam banda ya fadi bata wani lura ta hau kan hanya ba,kafin ta gama qulla amsar da zata bashi,har ya bude murfin motar dake daura da ita
"Shigo muje" seat din ta kalla sannan ta kalleshi,kamar zata musa masa,amma bataga alamar wargi ko wasa saman fuskars ba,a dinke take tsaf,sai tayi taku uku ta qarasa jikin motarta saka jikinta a hankali sannan ta janye qafafunta ta maida murfin ta rufe,a hankali ya danna ya dage dukka gilasan sama,a boye ya sauke wata boyayyar ajiyar zuciya tare da qoqarin danne kanshi da zuciyarsa,wani irin qamshi jikinta ke fiddawa wanda bai taba jin qamshi me taushi irinsa ba,ya kunna ac motar ya daidaita sanyinta,sannan ya tashi motar cikin wani kasalallen tuqi suka fara tafiya.
Kamar wadda aka hana ta gaza ce masa komai,tana so ta gani ne yasan wajen da zata ko kuwa?.
Zaman kurame kawai sukeyi,zaman duka ya gundureta,gaba daya ya cikata da kwarjininsa ya cika motar gaba daya,baya ga qamshinsa da ya cika mata hanci ya haifar mata da wata irin kasala da kuma wani irin yanayi mai nauyi a zuciya.
Sannu a hankali sai gasu a amaryar kb global enterprises,mamaki ya kamata,ta dan juya kanta kadan da nufin duban sashen da yake zaune,saidai yayi mata kwarjini da yawa,ta gefan idanu dai tana iya ganin yadda ya maida hankalinsa ga gabansa,baiko juyo sashen da take ba,abinda yasa itama ta dake kenan,ta sanya hannu ta buda murfin motar ta kuma fice a hankali.
Ta mudubin gaban motar yake hangenta,tana takawa a hankali,wani irin cat walking take,wanda idan ka nutsu tsaf zaka fahimta,haka yanayin tafiyarta yake,sai ya janye idanunsa daga kanta yana gargadar kansa.
Taci sa'a ita daya take jira,don haka suna zuwa basu bata lokaci ba aka fara yi mata,tasan makamar aikinta,ba bata lokaci suka kammala,ima din tayi tsaye a gaban babban mudubin dake wajen tana kallon fuskar tata,yadda kullum take sake kyau da sheqi kamae ta jariri,ita kanta tasan gyaran yana karbarta yadda ya kamata,saidai gaba ta laluba zuciyarta kaf babu wani abu me suna farinciki ko qanqani a cikinta.
Waiwaya tayi ta miqa hannunta sanda take miqa mata wani turare da kullum take mulke jikinta dashi baya gama gyaran,ita kanta tana son turaren qwarai saboda yadda yake da wani irin sassanyan qamshi,ta karba ta zuba ta shafe jikin nata,ta maida zaman hijabinta a jikinta sukayi sallama ta fito.
Turus ta tsaya cikin madaukakin mamaki,alameen ne a booth din motar,ya harde qafafunsa waje daya,wayarsa a hannunsa,sai earpiece da ya sanya kunne daya,da alama waya yakeyi,kallo daya zaka masa ka karanci zaman bai wani dameshi ba,take zuciyarta ta shiga taraddadin ba ita ya zauna jira ba,qila wajen wani yazo.
Ta fara takawa da zummar ta wuce sai suka hada ido dashi,ya katse wayar a nutse ya zare earphones din dake kunnen nasa,sannan ya sauka daga saman motar a hankali,ya taka yana bude murafun motar,dole ta dawo ta bude ta shiga itama ta rufe murfin ya tada motar,saidai a wannan karon sauke gilasan motar yayi duka iska ta dinga shiga tana fita ba kamar wancan karon ba,a hankali yaje furzar da iska daga bakinsa,saiya qara gudun motar ba kamar daxu da suka tafi akan low speed ba.
Titi suka hau sosai,yayin da ta kama gefan mayafinta tana wasa dashi,tunani iri daban daban fal zuciyarta,ta rasa da wanne zata fara,abu daya yafi damunta zamansun tare waje daya,babu abinda ke haifar mata sai matsala daga zuciyarta zuwa gangar jikinta
"Dame dame kuka tsara zakuyi na biki?" Tambayar tazo mata a bazata,har sai data waiwaya ya dubeshi sanda yake kallon titi,ta dauke kanta tana son yiwa maganar tasa muhalli,tanajin kamar ba ita ya kamata ya yiwa wannan tambayar ba,me ya kawo tambayar gareta
"Babu abinda aka tsara" ta amsa masa kai tsaye,saboda tana ganin babu amsar data wuce haka,baice komai da ita ba yaci gaba da tuqinsa har zuwa sanda suka tsaya a qofar katafaren wani shago na saida furnitures.
Har ya gyara parking ya fito ya zagayo inda take zaune ya bude mata murfin motar tana zaune
"Bismillah" yace da ita idanunsa nakan shagon,sai kuma ya fara takawa zuwa gaba a hankali,bata da wani zabi illa fitowar,duk da batasan me ya kawosu wajen ba.
Bata fuskanta ba kuwa saida suka shiga cikin babban store din,ya sadiqu ta samu a tsaye a ciki shida anty hassana
"Wayarki saura kadan ta zama mara amfani,ayita kira bakya dagawa" ya sadiqu ya fada cikin mita,dai dai sanda alameen yayi zaune kan wata kujera dake wajen,ya kuma ci gaba da amsa wayarsa,wayar data dinga ji cikin jikinta kamar da samha yake.
"Banji ba wallahi yaya" ta fada tana kiciniyar ciro wayar daga jaka
"Kinga yanzu ba wannan ba,ki zagaya ki zabi kalar furniture din da kikeso,dare yana qara yi,anty na sauri zata koma gida"
Kamar wadda aka bugewa qafafu sai ta koma ta zauna kan daya daga cikin kujerun dake wajen
"Ya ana magana kika koma kika zauna?" Kai ta girgiza,bata jin zata iya aiwatar da komai a yadda takejin jikinta,ta lura ba iya bushira da yaagana suka daukaki abun ba,kusan kowa ma hakane,kamar dama sun gaji da zamanta,har yanxu bata rufa shekaru biyar a gabansu ba,hakanan duka duka har yanzu shekarun haihuwarta basu wuce ashirin da uku cikin da hudu ba
"Ya sadiqu,ga anty sannan kuma ace da kaina zan zaba kaya?,don Allah kayi haquri bazan iya ba wallahi" ta qarashe maganar tana jin wani weakness yana ratsata
"Kaga sadiqu muje,mu zaki tsaya yiwa fulako" cewar anty hassana tana jifanta da harara wasa,qas tayi da kanta itadai,batasan yadda al'amarin ya kaya ba,illa dai tasan bayan tsahon wasu mintuna anty ta qaraso wajen tana ta sumbatun kayan,da kuma kudin daka kashe wajen siyansu,suna daga motar taga fitowar ameen daga shagon hannunsa dauke da receipt,bata iya qara cewa komai ba har suka sauke anty hassana su kuma suka dunguma gida.[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: "




Menu
Dashboard
My Library
Create Story
Home
About us
FAQ's
Privacy Policy
Terms of service
Logout

KUFAN WUTA
Free page 01
*TAFIYA DA GWANI ME DADI*
*ZAFAFANKU BIYAR sune suka sake dawo muku da wasu sababbin tsararru kuma zafafan labaransu guda biyar kamar yadda aka saba*
RAYUWAR MACE
rano
NOOR ALB
Mamuhghee
MASARAUTA
miss xoxo
BAK'AR INUWA
Billyn Abdul
KUFAN WUTA
Huguma
Zaku samu gaba daya labaran akan naira
1k kacal
2_400
3_500
4_700
*Zaku saka kudin ta wannan account din*
1487616276
BILKISU IBRAHIM MUSA
ACCESS BANK
*SAI KU TURAWA WANNAN NUMBER SHAIDAR BIYANKU*
09032345899
*KATIN MTN KUMA*
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
_MUJE ZUWA_🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️🏃🏾♀️
Dogon layi ne sosai kamar irin na kowacce unguwa ta masu matsakaicin qarfi,hagu da dama na layin gida jene a jere na masu matsakaiciyar rayuwa,wadanda basu cika mugun kyau ba,kamar yadda kuma basuyi lalacewa da rashin kyan gani ba,duk da cewa wani gidan yafi wani kyau,kamar yadda kowa da irin yadda ubangiji S W T ya tsara masa matakin rayuwar da zai wanzu a kai.
Yawancin gidajen plate ne masu soraye,masu ginin benen daga cikinsu 'yan qalilan ne,haka nan gaban gidajen akwai kwata wadda tabi ta kowanne qofar gida,saidai kuma a rufe take da slap,duk da cewa zakaga daya biyu na wani gurbi da babu slap din,gurbin dake nuni da cewa cirewa yayi ko karyewa,ko kuma an tsigeshi ne bisa qarfi da da yaji,da kuma qiriniya irin ta yara,wanda bisa dukkan alamu ma slap din an hada taro da sisi ne daga mazauna layin an ginashi.
Daga can tsakiyar qarshen layin,wanda zaka iya karya kwana ta shiga dakai wani layin daban,dandazon yarane a tsaye carko carko sunata hargowa,idan daga nesa ka taho,zaka iya hangen yadda qura take tashi a wajen,alamu dake nuna cewa fada ake sosai a wajen.
Idan ka duba tsakiyar wajen sosai,yara ne guda biyu,wadanda gaba dayansu ba zasu zarta shekara goma ba gaba dayansu,'yar baqar dirarriyar yarinyar nata qoqarin kada abokiyar fadan nata,wadda idan kayi mata kallon farko ba zaka zaci zata iya dambe haka da abokiyar fadan nata ba,kasancewar bata kai wancar garin jiki ba,fara ce ba sol ba,kana iya hangen doguwar sumar kanta me santsi yadda ta debi qasa da yashi na wajen,sakamakon cirewar danwakalin kanta,baya ga hijabinta data ci damar dashi tun daga sanda za'a fara fadan.
"Iman.....iman.....ga malam nan" wata yarinya ta qaraso wajen bayan taja birki tana haki,da alama daga wani sashen ta kwaso gudunta ta kuma tuqe a nan.
Sarai iman din ta jita,saita qara himma da hanzarin ganin ta yar da rahama kafin malam din ya qaraso,ta tabbatar matuqar bata gama ba ya qaraso fadan yazo qarshe,hakanan kuma babu makawa itace me laifi a wajen malam din,koda kuwa ta fisu gaskiya.
Saidai bata kai ga cimma burin nata ba taji tsawar malam din a kanta
Dattijon mutum,wanda a qalla shekarunsa sun tasamma hamsin,sanye da fararen kaya qal,riga 'yar ciki da wando,sai babbar riga malum malum,kansa sanye da farin rawani,hannunsa dauke da buzu daya nade wani abu a ciki,daya hannun nasa kuma yana riqene da baqar leda
"Ke hajaru,kinci gidanku!,saketa nace" Ya fada cikin kaushin murya idanunsa duka bisa yarinyar.
Tunkude rahama hajar iman tayi,ta duqa tana kwasar takalmanta da dankwalinta da suka turbude cikin qasa,ranta a bace na rashin samun damar tumurmusa rahama da batayi ba,dai dai lokacin malam ya waiwaya ga yaran yana musu fada,tare da kora kowa zuwa gida,bayan ya bude ledar hannunsa ya fidda alewa ya rarraba musu.
"Muje gida ke kuma,'yar qaniya" ya fada yana tasa qeyar iman zuwa gida,suna tafe yana mata sababi har suka isa qofar daya daga cikin gidajen dake jere a layin.
Tun daga qofar gidan zaka karanci cewa gida ne na makaranta,ma'ana gidan da ake karantar da almajirai,saboda babbar rumfar kwanon da tabarmi dake malale saman simintin dake qasan rumfar kwanon,tun daga malalen simintin,tabarmin dake shimfide din zuwa qasar dake gaban gidan a share wajen yake fesss,kai kace lomar tuwo zata fadi ka duqa ka dauka abarka kaci saboda tsabar tsabta.
Da hanzari almajiran dake zaune a wajen,wadanda basufi biyar ba suka miqe
"Sannu da zuwa malam" duka suka furta,daya daga cikinsu ya matso yana niyyar karbar ledar hannun malam din,sai ya dakatar dashi
"Yi zamanka habu....inasu haladu?" Ya jefa tambayar ga daya daga cikin mazauna wajen,wanda ya fisu girma da wayo
"Basu dawo ba tukunna,amma nasan suna hanya" kai malam din ya jinjina
"Shikenan,ku fara shirin sallar magariba,duk wanda ya dawo kada ya fita,inason ganinku gaba dayanku"
"To malam" suka amsa masa cikin girmamawa,saiya juya ya saka kai zuwa soron gidan.
Faffadan tsakar gida ne mayalwaci sosai,wanda ke dauke da bishiyar mangwaro da babu kamarta a unguwar,wata iriyar bishiya da Allah ya sanyawa albarka,me yawan fidda 'ya'ya masu dadin gaske da kusan kowa yake amfana da ita.
Dakuna biyu ne daga hannun damanka wanda suke falle daya da kuma rumfa da uwar daki,sai wasu da suke kalloka kana shigowa gidan,suma rumfa da uwar daka ne gaba dayansu,baya ga wani babban dakin falle daya dake a soron gidan.
Gab da soron gidan anan rijiyar gidan take,ma'abociyar ruwa me kyau da sanyi,wanda koda da rani ne nata qafewa,anan kusan duka 'yan unguwar ke diban ruwa idan aka shiga yanayi na rani wanda ake yawan samun qafewar rijiyoyi da kuma janyewar ruwan famfo,bandakinsu na daga can wani dan sakaye sai kitchen dake taqi kadan daga dakunansu.
Yadda qofar gidan da sorayenshi suke qal haka cikin gidan yake,komai a killace cikin tsafta a kuma muhallinsa.
Daga qofar kitchen din wata farar macace zaune saman kujera 'yar tsugono,sanye da wata jar atamfa data qara ma haskenta kyau,duka duka matar shekarunta na haihuwa zasuyi arba'in,saidai da alama ita din ma'abociyar tsafta ce da ado.
Kwando ne a gabanta wanda ke cike da alayyahu tana tsinkewa,baya ga albasa data gama yankanta tuntuni,cikin sauri sauri take aikin,da alama bata saba kaiwa dare kamar haka bata gama abincin dare ba.
Sau daya tak ta daga kai ta kalli iman wadda fa shigo tana gursheqen kuka,tabi takalmanta da ta riqo a hannu saboda tsinkewar da yayi,saita maida kanta taci gaba da aikinta,kamar ma batasan da wanzuwarta ba,abinda ya sake tunzura iman din,tayi zaman 'yan bori a waje tana aje takalman nata a gefe,tare da sake bude muryarta tana sakin kukanta.
Ko dagawa ta sake kallon iman batayi ba,saboda irin wannan koke koken da rigimar ta banza da wofi ba yau ne farau ba a wajenta,kusan kowa na gidan yasan da zaman wannan,har zuwa sanda malam yayi sallama ya shigo,sai tayi qoqarin rage sautin kukan nata,ta hau zazzare idanu.
Da malam din ya kalleta dariya ta bashi,amma saiya danne,ya maida kansa ga matarsa safiya da ake kira da inna,wanna tuni ta miqe tana masa sannu da zuwa,bayan ta ajjiye aikin da takeyi ta qaraso ta rusuna ta karbi ledar hannunsa.
"Yanzu ke hajaru.....bakya jin fada kenan ko?" Malam din ya fada yana kama kunnensa da hannu daya
"Sau nawa zan hanaki fada da yara?,.....ina cewa ko sati ba'ayi ba kukayi fada da asama'u....naja miki kunne,shine har kin manta?" Tsuru tsuru tayi tana raba idanu,tsoron yadda malam keta fiddo mata manyan idanunsa irin nata ya shigeta,takan jima har ma ta manta kafin malam yasa hannunsa ya daketa,duk ranar da ya daketa din kuwa lallai ba shakka ta qureshi ne.....kuma fa zata ji a jikinta
"Daga yau bazan sake miki magana ba,amma zan saki a mari idan baki wasa ba" ya qarashe maganar yana sakin kunnen nasa.
Inna da tuni ta koma bisa aikinta tana saurarensu,haushi sosai yake cikata kan yadda malam din bai iya zagewa ya daki iman sosai kamar yadda takeso,saida yakan gaya mata cewa,duka baya tarbiyya,kuma bashi ke gyara yaro ba,saidai ya batashi,nasiha da kuma nusarwa sune suka kamata.
Sannu da gida yayi mata kamar yadda ya saba,yana tambayarta kowa lafiya,ta amsa masa da lpy qalau,wannan kusan dabi'arsa ce,mutum ne shi managarci,wanda yake matuqar kula da iyalinsa dama buqatunsu,bakin gwagwadon ikonsa,abinci abinsha da suttura duka bai yarda sunfi qarfin iyalinsa ba,komai qanqantar abu ya daukewa gidansa,saidai duk da haka bai hana inna sana'a ba,saboda sanin muhimmancinta ga diya mace.
Gangarawa malam yayi ya daura alwala,ya maida rawaninsa yana shaidawa innar zai sake fita,bazai shigo ba sai an idar da sallar isha'i
"A dawo lafiya,Allah ya tsare" tasan ya fadi hakanne don kada ta damu da rashin gamaabincinta akan kari,shi yasa ya fita ya bata sarari don ta samu ta kammala a nutse.
Fitar malam din kamar dama jira hajar take ta sake bude baki da sabon babin kuka,abunda ya qule inna sosai,tayita qoqarin danne zuciyarta don kada ta kaiwa hajar din hannu,amma ko alamun sassauta kukan hajar batayi ba,abinda ya dinga tunzura inna kenan,taji babu makawa saita jibgi hajar din sannan zataji sassauci,don haka ta saki dambun data gama hadawa tana maidashi madambaci hawa na biyu,ta miqe a fusace.
Malam na gyara hannunsa daga qofar fita daga gidan,yana magana da wani babban dalibinsa sahabi,ya daga kansa a hankali sanda ya fara jiyo muryoyinsu,duk kuwa da cewa basu kai ga qarasowa inda yake ba,amma kuma har zuciyarsa ta tafi inda suke.
Su dinne kuwa,matasan yara su biyu ne tafe,suna jere da juna,dukkaninsu shekarunsu basu wuce sha bakwai ba,yanayin fuska da kuma yadda suke tafe cikin raha zai iya sawa mutum yace 'yan biyu ne,saidai kuma kamanni da sukayi matuqar shan bambam a tsakaninsu zaisa ka gane ba twins din bane.
Matashin farko ya dara dan uwansa fari da haske da kuma tsaho kadan,wanda idan baka da lura ma babu lallai ka gane hakan,yana da zagayayyar fuska da madaidaicin hanci mai tudu,siraran labba masu kyau da kwantaccen gashin gira,duk da cewa akwai sauran shekaru masu tarin yawa a gabansa.....amma kuma sai gashi saje ya fara fito masa sosai,alamun dake nuni da cewa mutum ne me yawan gargasa,don sumar kansa ma kawai ta nuna alamun hakan.
Wani irin idanu gareshi kamar na mai jin bacci,saidai idan kuma ya budesu sosai xaka fahimci manya ne suna da girmansu,duk da bai gama girmansa ba,amma kuma zaka fahimci shi din dogo ne,ya fito daga jinsin yaren da sukafi alaqa da fulani,yana sanye da riga t,shirt me kwala mai gajeran hannu,sai wani wandon jeans wanda ya danyi fari kadan,qila saboda yawan morarsa da yakeyi ne,saidai kana kallon jikinsa kasan gwani ne wajen tsafta,domin kuwa.....duk da wuni da yayi wajen aikinsa,hakan baisa koda karin gugarsa ya bace ba bare akai ga yin dauda,muhammad al'ameen kenan.
Saurayi na biyu shima farine,don har yafi dan uwansa fari,hakanan shima ba baya bane wajen kyau duk da cewa shima shekarun nasa basu gama bayyana komai ba,abu gudan da ya sake bambanta su....yafi dan uwan nasa garin jiki,shi kuma shadda ce a jikinsa,duk da cewa ba wata ta azo a gani bace ba,amma shima fes yake,saidai hannunsa da yayi baqi,sabida aikin gyaran mota da yake koya a wani garage,umarul farouq kenan wanda ake kira da faruku.
A ladabce dukkaninsu suka qarasa daura da malam,suna masa barka da yamma,fuskarsa fadade da fara'a,zuciyarsa kuma cike da alfahari dasu yake amsa musu da
"Yawwa.....ya wajen aikin?"
"Alhmdlh" suka amsa masa a kusan tare
"To ma sha Allah" sai suka miqe suka nufi cikin gidan,wanda al'adarsu ce kowacce rana,idan suka dawo gida lokaci irin wannan,basa shiga dakinsu dake soron,wanda shi suke fara tararwa,har sai sun shiga sun yiwa innar sannu da gida sun shaida mata dawowarsu.
A fusace inna ta ciri wayar radio dinta dake a gefanta,wadda ko awa biyu ba'ayi da kawota daga gyara ba,aikin da ya kacame mata yasa bata samu tashi ba bare ta miqa ta daki,sai tayi kan iman cikin fushi tana fadin
"Bari na dakeki da kyau.....sai kiyi kukan me dalili"
"don Allah innarmu" kalmar data ratsa kunnensa kenan,abinda ya sanyata tsaiwa cak daka dukan iman da tayi niyyar yi,ko da bata juya ba tasan waye,ba yau ta fara jin hakan daga bakinsa ba,matuqar yana gidan,matuqar kuma yana kusa baya yarda da adaketan,ya gwammace ya horata ta sassauqar hanya,amma baya qaunar a daga hannu a daketa.
Kafin innar ta gama miqewa tsaye daga durquson dukan da tayi shirin mata....tuni har ita iman din ta miqe da hanzari,ta kuma falla da gudu tayi inda alameen din yake tsaye.
Kafin ta iso ya duqa,ya kuma yiwa jikinsa garkuwa da hannyensa,saboda yasan tana zuwa din jikinsa zafa fada da shagwabar nan tata,abinda ya jima da yi mata shamaki da aikatashi,saboda yadda a kullum take qara girma,shekarunta suna daduwa.
Ilai kuwa tana zuwa abinda ta shirya yi kenan,saidai ya sanya hannayensa ya riqe nata hannuwan,ta sakar masa kuka,cikin sigar lallashi ya fara magana
"Ya isa haka.....ya isa,karki bari aga hawayenki mana" yana maganar ne tare da sanya gefan dankwalinta yana goge mata fuskarta,sannan ya miqe daha durquson da yayi ya kama hannunta suna takawa zuwa tsakar gidan.
Tsaki yaji daga bayansa,ya kuma san ba kowa bane illa sadiqu,wanda ya tabbatar da cewa zuciyarsa yayi matuqar kaiwa nesa,da kuma kara da yayi masa yau,banda haka tabbas ya sani....da tuni ya jima da kai hannu jikin iman din,kamar yadda ya saba duk sanda wani abu irin haka ta faru.
Yana riqe da hannunta har suka qarasa inda inna ke tsaye daura da qofar kitchen,ya russuna yana fadin
"Barka da gida inna" yana kuma ajjiye mata daya daga cikin baqaqen ledoji guda biyun da ya shigo dasu
"Barka kadai aminu,ya wajen aikin?"
"Alhmdlh inna"
"Ma sha Allah,Allah ya qara albarka" ta fada tana ajjiye kallonta kan Ledar da ya ajjiye ya tura gaban innar
"Alhamdulillah inna" ya amsa mata,saidai hankalinsa yana kan iman,wadda har yanzu take kumburi
"Me iman tayi inna?" Lamin ya maida dubansa ga innar bayan ya dauke idanunsa daga kan iman
Sai da innan ta tabe bakinta sannan ta ja ledar ta fara budawa kafin ta bashi amsa,amsar da tasan koda ta bashin babu abinda zai sauya zani
"Fada dai fada dai ita da yara,fadan da kuma kai da kanka sai da ka rabashi amma malam ya ganta da yaran bata haqura ba,ita ba za'a gaya mata ba taji kenan?".
Kansa ya juyar ga iman,wadda ta sake tale baki tana shirin fara wani sabon kukan
"Me yasa iman?,ina cewa ni da malam duka mun raba wannan fadan ko?" Cikin muryar dake nuni da cewa tana gab da sake sakin wani sabon kukan tace
"To ba sune ba.....da na fito sai su fara tsokanata....bayan kuma ni ban kula su ba.....wai idona irin na mage" qaramin murmushin da ya sake qawata fuskarshi ya sake,yana kuma duban qwayar idanun da take magana a kai,tabbas qwayar idanun nata dama eye lashes dinta ba irin na kowa bane,wannan yasa yara da yawa suke tsokanarta,abinda ita kuma ta tsana kenan,yake kuma yawan hadata fada da yaran,tasha sanya kuka kan a cire mata idanun a sauya mata wasu,duk saboda yadda yaran suke tsokanarta,ko kallonta inna batayi,alameen dinne yake tsayawa ya lalace bata haquri da lallaminta,tare da qoqarin yi mata bayanin cewa ba ciwo bane.
Cikin nutsuwa ya tattara hankalinsa a kanta
"Sau nawa zaance ki daina damuwa uhmm?,dukanmu muna son ganinki haka,kuma ke me kyau ce,bakiga duka kin fisu kyau bane?ke ta dabance kinji?,ki daina damuwa da abinda zasu fada" murmushi ta saka kamar kowanne lokaci idan ya yarrasheta irin haka,sai ta gyada kai tana murmushi,abinda ya sanya dimple dinta na hagu da dama lobawa,sai shima ya biye mata wajen sakin murmushin
"aminu.....an kira salla,ka tashi kayi buda baki ka rabu da wanann sakaryar" cewar inna,tana turo jug na ruwan sanyi data jefawa qanqara gabansa,waiwayowa yayi ya dauki ruwan kana ya miqe yana duban iman
"Zanje sallah na dawo...."
"Ina tsarabata?" Ta fada a shagwabe tana langwabe wuya tun kafin ya qarasa maganar da yakeyi,murmushi ya sakamar mata,shi kansa yana yaba rigima irin na iman,shi yasa babu wanda suke shiri dashi kaf gidan saishi kadai,sai kuma malam wani zubin
"Zan taho miki da ita" ya amsa mata yana shirin daga qafarsa
"Qaniyarki....ke me yasa kullum bakya hankali?"
"Idan na iso wajen saina balla mata dan yatsa,laifinsa da yake biye mata" saddiqu daya gama daura alwalarsa a bakin famfo ya fada bayan ya zubda ruwan kuskure bakin da ya guntsa,yana warware dogon hannun rigarsa tare da jefawa iman din harara kamar idanunsa zasu zazzago qasa
"Amma dai ina cewa ba da kai take ba ko?,to ba ruwanka" alamin ya fada yana watsawa saddiqun nashi idanuwan,sanda yazo gab da shi zai fice daga gidan,xuwa qofar gidan don miqawa malam kofin ruwan sanyi suyi buda bakin tare,kamar yadda suka saba,kusan dukansu suna azumin litinin da alhamis,hatta da iman qaramarsu ta fara,yau dinne kawai ya zamana shi da malam ne kawai suka samu damar yi,saddiqu yayi zazzabi na kwana biyu,bai jima da warwarewa ba,abinda ya hanashi yi kenan,ita kuma inna uzuri irin namu na mata,sai kuma iman wadda tun safe al'amin ya daure mata qarqashi kan cewa yau akwai rana,tasha ruwa abinta,ta bari sai ranar alhamis tayi,inna tayita mita har ta haqura ta sanya musu idanu,idan da sabo ta saba da wannan dabi'ar ta al'amin da iman,bama ita ba,duk wanda ya rayu dasu koda na 'yan kwanaki ne sai ya fuskanci haka.
_ina matan dake fama da qaranci ko daukewar sha'awa saboda gajiya qarancin sinadarai ko kuma gajiya a jikinsu?,kina fama da maigida wajen rashin samun gamsuwa fannin auratayya?,dukka matsalarku ta yanke da HILTI UNISEX CHOCOLATE,maza garza kizo ki nema taki_
_CHOCOLATE CE da zaki shata kamar sauran chocolate,saidai kuma aiki a jiki,ba ruwanki da neman tarkacen magunguna mata marasa inganci,AKWAI TA UWAR GIDA AKWAI TA MAIGIDA_
_GAME BUQATA KO KUMA SON QARIN BAYANI,SAIYA TUNTUBI WANNAN NUMBER_
+234 818 401 7452
*Tasted and trusted*👍🏽👍🏽
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: https://arewabooks.com/book?id=628235bbb77ff582983d6c6b
*FREE PAGE 02*
_ina matan dake fama da qaranci ko daukewar sha'awa saboda gajiya qarancin sinadarai ko kuma gajiya a jikinsu?,kina fama da maigida wajen rashin samun gamsuwa fannin auratayya?,dukka matsalarku ta yanke da HILTI UNISEX CHOCOLATE,maza garza kizo ki nema taki_
_CHOCOLATE CE da zaki shata kamar sauran chocolate,saidai kuma aiki a jiki,ba ruwanki da neman tarkacen magunguna mata marasa inganci,AKWAI TA UWAR GIDA AKWAI TA MAIGIDA_
_GAME BUQATA KO KUMA SON QARIN BAYANI,SAIYA TUNTUBI WANNAN NUMBER_
+234 818 401 7452
*Tasted and trusted*👍🏽👍🏽
_____________________________
Basu shigo gidan ba su duka sai bayan sallar isha'i,saboda suna tsayawa daukan karatu wajen malam cikin almajiransa,hannunsa riqe da baqar leda wadda taketa maiqo dauke da awara me zafi da tasha cabbage da yaji mai uban yawa.
Dai dai lokacin da iman din ke zaune gefan tabarma tare da innarmu wadda ke lazumi bayan ta gama tata sallar,abincinta na gefe bata tabashi ba,innar tana ankare da ita amma bata kulata ba,iman din irin yaran nan ne da ko kadan basa qaunar abinci,wani lokaci har sai innar ta ajjiye madoki kusa da ita sannan zata ci abincin,wannan dalilin yasa bata da kumari ko kadan,kusan duka sa'anninta sun fita girman jiki.
Tana jin sallamar alamin ta miqe daga shirin kwanciyar da takeyi,ya qaraso gefanta ya zauna yana ajjiye mata ledar awarar,fuskarta a wadace da murmushi ta janyo ledar ta fara budawa tana cewa
"Na gode yaya alamin" shima murmushi kawai yayi ba tare daya amsa ba,suka bita da kallo sanda ta miqe zuwa kitchen,da alama plate din da zata juye awarar take nema.
Kusan lokaci daya suka dauke idanunsu shi da inna,sai innar ta ajjiyr carbin hannunta gefan daddumarta tana cewa
"Zauna aminu" sabule slippers din qafarsa yayi,ya zauna daga gefa,cikin yanayi na nutsuwa
"Me yasà koda yaushe saidai ka yita biyewa shirmenta?,ta yaya ku da kuke nema ya kasance koda yaushe baka da aiki sai batar mata daa kudi?,yanzu meye laaifin daambu da bazata ci ba,saidai awara?" Murmushi ya saki kawai,sannan a nutse yace
"Inna mu din mune dolen imaan,mu ya kamata ace munyi mata daman,idan bamuyi mata ba waye zaiyi mata,kuma bata roqan kowa a waje saimu da muke yayyenta,kuma ma amfanin neman kenan inna,iman ba wani abu take tambaya ba da ya wuce dan abun marmari" kai kawai innar ta raausayar,dama tasan zaa rina indai lamin ne,wannaan ba shine karo na farko da magana irin wannan ta ratsa tsakaninsu ba,ta rasa wacce irin qauna da kulawa ce wannan da yakewa imaan din,duk da cewa sun kyautata masa matuqa da gaske,kyautatawar da duniya ma ta shaida da hakan,amma kulawar da iman ke samu daga gareshi ta musamman ce.
Koda ta matsa wajen ganin cewa ta hanashi,ko kuma ya rage tasan bata bakinta ne kawai,lamin din bazai sauya ba,a nata hasashen da ganin kamar ya kamata ya rage din,tunda ko babu komai akwai yayarsa dake aure a qauyensu,wadda wasu nauye nauye nata dana yaranta duka ya daukesu bisa wuyansa,kasancewarsa yaro jan gwarxo,mai himma qoqari da kuma neman na kansa,komai dadi komai wuya,kuma komai rintsi,kwata kwata baisan wata kalma ta lalaci,son jiki ko kuma qyuya da ganda ba,dukkan wani aiki da zai samar masa da kudi na halak yana tallafarsa,ya kuma karbeshi hannu bibbiyu yayi,babu girman kai babu ha'inci ko son jiki.
"Shikenan,Allah yayi muku jagora,yasa albarka a nemanku"
"Ameen inna...ameen" ya fada yana jin dadin addu'arta,uwa ce me yawan addu'a ga 'ya'yanta,kome qanqatar alkhairi idan sukayi,bakinta baya gajiyawa da yi musu addu'a dare da rana.
Duk sanda tayi masa addu'ar sai yaji dadi qwarai da gaske qasan ransa,ya rasa mahaifiyarsa tun hankali bai fara riskarsa ba,sai gashi Allah ya musanya masa da wata makwafinta a sanda baiyi zato ko tsammani ba,a lokacin da ya dauke haso ya kuma debe tsammani daga samun dukkan wani tattali kulawa ko kuma jin dadi,cikin tausayi da kuma jin qai na ubangiji ya hadashi da wasu kwafin na iyayensa.
Daga inda take zaune take binsu da kallo,sanda ya karbi awarar da kansa ya juye cikin farantin robar da iman din ta dauko,sannan ya zauna yana gutsutsura mata da daya da daya yana miqa mata tana ci suna hira,kallo daya xakayi musu ka tabbatar da cewa lallai akwai shaquwa me girma a tsakaninsu.
Lumshe idanunta inna tayi,bahaushe yayi gaskiya da yake cewa
"Da da da dukiya babu wanda yasan me morarsu sai Allah" ta Sauke idanunta tana tuna ranar farko da suka fara sanin lamin,ya kuma shigo rayuwarsu ya zama daya daga cikin iyalan gidan.
Malam ibrahim khalili shine cikakken sunansa,haifaffen garin maiduguri,cikakken babarbare wanda ya fito daga gida na ilimi da karatu,asalin gidansu malam khalili gida ne na malamai,da suka gaji karatu tun daga kakanninsu,malam khalili yana daya daga cikin yara uku da suka gaji mahaifinsu,duk kuwa da cewa su biyu rak mahaifiyarsu ta haifa Allah yayi mata rasuwa.
Khalili ya tashi da son karatu da kuma nema tuquru,wannan yana daya daga cikin dalilan da suka sanya yabar maiduguri,ya shiga duniya neman karatun qur'ani dama na addini haiqan,daga gari zuwa gari,har ma wasu qasashen da muke maqwabtaka dasu.
Sosai karatu ya daukewa khalili hankali,bai samu yin aure da wuri ba,har zuwa sanda ubangiji ya nufeshi da zuwa qasar niger.
A canne ya hadu da fatima buzuwa,tana zuwa daukan karatu makarantar wani abokinsa,yarinya ce a sannan me qwazo da kuma hazaqa,don lokacin ma ta kusa kammala haddar qur'ani,tana izifi na hamsin da biyar,tun daga baqara take rubutawa a allo ta haddace sannan ta wanke a sake yi mata qari,ta samu tarbiyya me kyau da kuma kulawa,duk da cewa mahaifinta ya rasu,amma mahaifiyarta batayi sakaci da tarbiyyarta ba,saboda ita daya Allah ya basu.
Lokaci daya soyayya da shaquwa ta shiga tsakaninsu,suka fahimci juna da kyau,manya suka shiga maganar aka tsaida maganar aure,ba dadewa suka angwance,ya kuma daukota ya taho da ita garin kano,inda anan ya bude tsangayarsa shima,yana karbar almajirai daga kowanne gari ko qasa.
Almajirancin makarantar malam khalili ba kamar sauran almjirci bane da muke gani ayanzu,wada aka watsar da duk wani mutunci da kuma kimarta a yanzu,yara suke wahala da sunan neman ilimin alqur'ani me girma,wanda sam hakan bashi da tushe bare asali sam cikin addininmu.
Dukka yaron da zai karba sai ya kasance makusancinsa ne ya kawoshi,zaa rubuta adreshinka da lambar wayar wanda ya kawoka,sunan gari dana qauyenka da kuma inda za'a iya samunka,sanna bai yarda a kawo masa yaro babu haka ziqau ba babu abinda zaici,abun kwanciya da kuma kayan baqatun yau da kullum,saboda shi din bai yarda da fita bara a makarantarsa ba,karatu aka kawo yaran shi sukeyi,yakan baka zabi idan ka soma hankali,kana da sha'awar karatun boko?,idan kana dashi zai shaidawa iyayenka ya sanyaka a makaranta,idan baka buqata kuma zaka kama sana'a ne,don bai yarda da zama babu sana'ar yi ba,saidai kowacce sana'a kake kana yinta ne bisa sanya idanunsa da kulawarsa,da kuma tabbatar da cewa sana'ar da kakeyi din bata sabawa addini da kuma al'ada ba.
Wannan dalilin ya sanya makarantarsa ta kasance mai tsari,mutane da dama sukeso kawo yaransu karatu nan wajensa,saidai duk shekara akwai adadin da yake dauka,idan suka cika kuma baya sake dauka sai wata shekarar.
Zamansa da fatima wani irin zama ne me matuqar dadi da kuma ban sha'awa,khalili wani irin mutum ne managarci,mai halaye da kuma dabi'u masu kyau,tsayyen akan harkar gidansa da kuma sauke nauyin iyalinsa,idan kaga fatima zakayi tsammanin tana auren wani me halin ne,saidai ko daya,tsabar kula da take samu ne da kuma tsaiwar mijinta wajen sauke nauyinta,babu abinda ta nema ta rasa,tana matuqar jin dadin xama dashi,kamar yadda shima yake yaba mata,yake kuma matuqar jin dadin xama daa ita,saaboda ita din macace ta gari,mai tarin biyayyawa mijinta,wadda tasan dai dai ta kuma san akasin hakan,bai taba cewa tayi ta musa ba,kamar yadda bai taba cewa ta bari taqi ji ba,Shi yasa shima yake qaunarta,da kuma qoqarin ganin ya hidimta mata iyakar iyawarsa,bata nema komai ta rasa ba cikin gidanta,cikin wannan yanayin,shekara biyu da aurensa Allah ya albarkaceta da samun haihuwar santalelen da namiji,aka sanya masa abubakar saddiq.
Daga kan saddiq tayita haife haife suna mutuwa wato WABI,makusanta da wasu cikin dangi sukayita so malam khalili ya qara aure,amma yace sam baiga dalili ba,yanajin dadin zama da matarsa,bai nema komai ya rasa ba,idanma ta hahuwa ce,kana iya haifar yaro guda daya amma ya zame maka me albarka fiye da masu tarin yaran,indai yana da rabo a haihuwa zata qara,ita kanta a sannan ta bashi dama amma yace bazaiyi ba,Cikin ikon Allah kuma sai Allah ya basu haihuwar hajar iman,haihuwar da duka fidda rai da ita,zuwan iman a daidai wannan lokacin ya janyo mata soyayya mai tarin yawa,saboda tazo a sanda basu zata ba,ta kuma zo a dai dai lokacin da suke marmari da buqatar qaramin yaron cikin gidan.
Shekarar iman daya a duniya da watanni biyar lamin ya shigo rayuwar cikin gidan a lokacin.
Yadda jama'a keta yabawa malam khalili kan yadda makaranta da kuma dalibansa suke a tsare ya sanya malaman wasu tsangayun dake unguwarsu da kuma wasu unguwannin suka shiga adawa da kuma takun saqa dashi,suke kuma matuqar jin haushinsa,ganin cewa ya fita daban da sauran malaman tsangayu,babu bautarwa ko azabatarwa ga dalibansa,kamar yadda bai yadda ya zama cima zaune me matacciyar zuciya ba,sai abinda iyayen yara suka dauko suka bashi,aah,shima kamar kowa,duk sanda ya tashi dalibansa shima yana tafiya neman kudinsa,ya dawo kuma lokacin da aka kusa sake zama ci gaba da karatu,komai nasu na tafiya a tsare ne,kana ganin dalibansa da yadda yake tafi da komai dole ya baka sha'awa.
Daren wata jumma'a ne,tana zaune tsakar gidanta daya kasance sai ita daya,sai hajar dake kwance a gefe saman wani abun shinfidarta me hade da katifa maras tudu,duk kuwa da cewa akwai motsin almajirai da hayaniyarsu daga qofar gida amma cikin gidan ba kowa,saboda babu wanda ke shigarwa malam gidansa gaba gadi don suna almajiransa,idan kaga yaro cikin gidan,to qaramine wanda shekarunsa basu wuce wanda shari'a ta wanzar da hani na shigarsa gidajen matan aure ba,tana da mai mata aike da maiyi mata wanki ana biyansa duk a cikinsu,bai yarda suyi mata aiki ba tare daya biyasu ba,saboda yace su din mutane ne suma kamar kowa.
A hankali hayaniyar tasu ta fara raguwa,da alama an gama rabon abincin dare ne,wanda ake auna cikin abincin kowa a hada,manya a cikinsu su dafa a rabawa kowa,a wani gida da suke zaune wanda yake daura da gidan malam din,gida ne da wani bawan Allah ya bayar kyauta su dinga kwana,hankalinta bai wajen sosai,yana can ga tunanin abinda ya tsaida malam da din bai dawo yadda ya saba ba,shi da saddiqu da yayi masa rakiya.
"Taho a hankali....riqeshi sadiqu" ta jiyo maganar malam din tun daga soro,abinda yasa ta ajjiye allon da take rubuta fasayakfika humullah ta maida hankalinta ga qofar shigowa gidan.
Malam dinne da sadiqu da wani dan farin yaro da bata sanshi ba,ta miqe tana masa sannu da xuwa,ya amsa hankalinsa yana kan yaron
"Maza dora ruwan zafi innar saddiqu" malam din ya fada yana tsugunnawa a gaban yaron,yana yage ragowar rigar jikinsa,da hanzarinta ta koma madafa,ta hada ragowar itacen data gama girki ta kunna ta dora masa ruwan,sannan ta dawo tsakar gidan,inda malam ke tsugunne gaban yaron yana masa sannu,sadiq na tsaye a saman kanshi yana kallonsu.
Kujera 'yar tsuguno ta jawo ta zauna,idanunta akan yaron da yake cikin hali na galabaita ta yiwa malam sannu da zuwa
"Yauwa binta" ya amsa da alamun rashi na a bace ne
"Ki duba maganin zafi don Allah idan akwai,idan ruwan yayi zafi ki juye sadiqu ya tayashi gasa jikinsa,bari naje na dawo" daga haka malam din ya miqe ya fita.
Duk yadda malam din yace tayi haka tayin,ya gasa jikinsa da kyau,sauran ta sakashi ya shiga bayi yayi wanka dashi,cikin kayan sadiqun ta zabo wasu ta bashi ya sanya,don xasuyi kai daya dashi,yana gamawa ta zuba masa abinci,ta koma ta dauki iman data tashi ta fara rigima ta fara bata nono,daga inda take din tana kallon yadda sadiqu ya sanyashi a gaba yana kallo,tun dazun shima zuciyarsa a karye take fuskarshi ta nuna hakan.
Malam ne yayi sallama,ya qarasa gaban yaron yana duban yaron daya ambata da lamin,ya bashi paracetamol din daya shigo dashi da kuma ruwan tea me zafi a leda,yace idan ya gama yasha yasha maganin,sai saddiqu ya kaishi daki ya kwanta.
https://arewabooks.com/book?id=628235bbb77ff582983d6c6b
Da ɗumi-ɗuminsa💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
Please
*_Follow me_*
*_Share_*
*_Comments_* akan abinda ya shige maka duhu.
*_ZAFAFA BIYAR (5) ZAZZAFAR TAFIYA🔥🔥👇👇👇_*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR🔥🔥🔥🔥_*
_____________________
*KUFAN WUTA*🔥🔥🔥🔥🔥🔥
_AREWABOOKS, dan zaku dinga samun sabbin pages galla-galla akan lokaci insha ALLAH. Maza garzaya ka karanta naka hankali kwance. Ka kuma yi following ɗina ko dan kar ayi babu kai, da a baka labari gwara ka bayar🥰🥰🤝🏻👇🏻_
*YADDA AKE BUDE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form din kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/book?id=620032232dff83519bbad5a3
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 03
https://arewabooks.com/book?id=628235bbb77ff582983d6c6b
🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥
*ZAFAFA BIYARRRRR*
*_INGANCIN LABARAI_*
*_FASAHA NUTSUWA DA IYA SARRAFA ALQALAMI_*
*_TSARI DA TSANTSAGWARON HIKIMA_*
*_SOYAYYA MAI RATSA ZUKATA DA NARKAR DA ZUCIYA_*
*_JIGON LABARAI DA YASHA BAMBAM DA NA SAURA MAI SANYA ZUCIYA MAMAKI DA TUNANI_*
*_YIN LINQAYA CIKIN DUNIYAR LABARI KAJI KAMAR DAKAI AKEYI DA GASKE NE_*
*DUKA SAI CIKIN GAMAYYAR LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*
*_ADADE ANAYI SAI GASKIYA_*
*_HIKIMA KASHIN KWANCE_*
*ABOKAN HIRA NE GA WANDA KE CIKIN KADAICI!*
*ABOKAN TAFIYA GA WANDA KE CIKIN NISHADI*
*WARWARAR MATSALA GAME NEMAN MAFITA*
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
______________________________
Ajjiye iman inna tayi sannan ta nufi daki,ta dauko babbar tabarmar malam din da yakan zauna a kai ta shimfida masa,sannan ta gabatar masa da abinci da ruwan wanke hannu,ta zauna nesa kadan dashi tana ci gaba da shayar da iman wadda ke rigima saboda bata qoshi ba,ta sakeyi masa sannu da xuwa
"Yauwa sannu binta,ya hidima ya gida"
"Alhmdlhi" ta fada tana dan murmushi,duk data saba da irin wannan kulawar tashi,amma duk sanda ya tambaya din hakan yana mata dadi,saboda tasan cewa mata da yawa ne suke neman hakan basu samu ba
"Wannan yaron da kike gani sunansa lamin,na tsinceshi ne a can unguwar da naje nida saddiqu dubiyar abokina,abinda ya bani mamaki yaro qarami yashe gaban famfon tuqa tuqa,jikinsa duka tabo na duka,yasha ruwa yanata amansa,wadda ina tsammanin babu komai ne a cikinsa,yayimin kama da almajiri don haka na matsa kusa dashi,sai daya dan rage aman na tambayeshi sunansa da kuma inda yake,yamin bayani,ashe almajirin makarantar malam dan lami ne,sai na tuna kwanaki uku da suka wuce tabbas naji ana neman wasu cikin daliban,na tambayeshi me yakeyi to a nan,kansa tsaye ya shaida min guduwa yayi,na masa fada na kuma nemi dalilin da yasa yabar makarantarsu,shi baya jin tsoron wani abun kada ya sameshi,a yadda na fahimta tsoron malamin da makarantar yafi tsoro akan duk abinda zai sameshi,abun takaicin kudi malamin yake sanya musu duk ran laraba,kowa sai ya kawo wadan nan kudaden,idan kuma ba haka ba,zai ma yaro duka mai tsananin da zai gwammace koma ta yayane ya samo ya kawo masa,to shi kusan duk sati sai an dakeshi,saboda baya iya kawo komai,don yace bazai iya yadda sauran sukeyi ba,don cikinsu harda masu sata don kawai su kawo,lamarin ya dagamin hankali,na daukeshi na maidashi gaban malamin,duk da inajin tausayinsa,amma babu gatan da xanyi masa da ya wuce hakan,saidai abun mamaki abun takaici kuma abun haushi,sanda naje ga malamin,tunda ya tambayi waye ni ya fara yimin wani kallo,nasa ma'anar kallon,tunda sarai nasan waye malam dan lami,yana daga cikin masu adawa da tsarina,amma ni hakan bai dameni ba,burina da fatana shine kowa ya gyara,tun kafin nakai ga cewa komai ya soma dakawa lamin tsawa,tare da jifansa da miyagun sunaye da kuma kalamai,ya kuma fara hanqoran neman manya cikin dalibansa su dauke lamin su saka masa shi a mari,abinda bai jima da fita daga ciki ba,a nan na nuna masa nima ainihin xafina,na hana kowa yaxo wajen ya taba yaron,a nan malam dan lami ya tada husumar cewa dalibinsa ne,kuma babu wanda ya isa ya hanashi yi masa duk hukuncin da yaga dama,tunda a hannunsa aka danqashi,indai kuwa bazai hukunta laminu ba,saidai yabar masa makarantarsa,ya koreshi,ya kori yaron ba tare daya tsaya yaji meye zance ba,bai tsaya yaji me yaron shima zaice ba,bai kuma sanar da magabatansa ba bare susan ina yaronsu ya koma"
"Na fuskanci tijara yake ji,don haka bance komai ba na tattaro al'aminu,na wuce dashi chemist saboda yanayin ciwuka da raunin dake jikinsa na tabon bulalai da duka da kuma mari daya dade a qafarsa ya zame masa ciwo. A hanya nake tambayarsa wayeshi da kuma qauyensu,ya shaidamin shi din dan birnin kudu ne,mahaifiyarsa ta jima da rasuwa tun yana qarami,yayarsa da ita ta riqeshi har zuwa sanda ya tasa,mijin yayar yace bazai iya daukar nauyinsa ba saboda shima bashi da komai,yayarsa bata da yadda zata riqeshi saboda shi da itan duka marayu ne,hakan ya sanya mijin yayar ya kawoshi bara,ya damqa shi a hannun malam dan lami,tunda kuma ya tafi bai waiwayoshi ba,duk da cewa bai wani jima a makarantar ba,azaba ba wacce bai gani a waie malamin ba,don kusan karatun ma dana tuntuba ba wani mai yawa bane,azabar da suke sha tafi karatun yawa,wanna dalilin ya sanya na yanke shawarar kawoshi makarantata yayi karatu,zuwa sanda zai warware kuma mu nemi ita 'yar uwar tasa ko mijinta mu gaya masa inda yake a yanzu".
Kai inna ta gyada idanunta na kan lamin,zuciyarta cike da tausayinsa,tunda malam yake kawo almajirai bata taba ganin yaron da taji ya kwanta mata ba kamar lamin din,a dan awannin da yayi dasu wanda bai wuce awa daya da rabi ba,ta fuskanci nutsuwar dake tattare da yaron,komai nashi a hankali yakeyi cikin nutsuwa
"Allah ya rufa asiri,ya gyara mana xukatanmu" shine abinda inna ta fada,suka kuma fara rayuwa da lamin din,wanda cikin kwanaki biyu ya sake da sadiqu,wani irin sabo sukayi sosai dashi,saika zaci sun dade tare.
Tun farko dama aminu din bai soma kwana cikin almajirai ba,cikin dakin saddiqu suke kwana,hakanan hatta da suttura ta saddiqun yake sanyawa,kafin daga bisani malam ya bayar da kudi inna ta samo musu gwanjo masu kyau shida saddiq din,sosai sadiq ke murnar samun dan uwa,lokaci kadan lamin ya shiga jiki da zukatan su inna,saboda yarone haziqi,duk wani aiki da saddiq keyiwa inna da malam alamin din ya daukeshi,sai malam da inna na hanashi suna raba musu kowa ya dauki nasa.
Kusan tare sukayi rainon iman da inna,idan inna tana aiki tofa iman tana hannunsa,yayita tiri tiri da ita kenan,tun tana masa qyuya har ya zamana duk cikin gidan babu wanda take yarda dashi Kamar yadda take yarda da alamin,wani lokaci idan aiki ya kacamema innan idan ya dauki iman sai tayi da gaske ta korashi makaranta sannan zai tafi,sannu a hankali sai sabo da shaquwa suka shiga tsakaninsu,baya son kukanta,baya son abinda zai taba iman din,da a daki iman din gwara a dakeshi,koda malam ya sanyasu makaranta sai ya zamana sai ya fara kai iman sannan shi zai wuce,koda kuwa shi xaya makara,kudin break dinsa kuwa badai yaci a cikinsa ba,komai ya gani shi zai kwasowa iman din ya kawo mata,idan kaga yadda yake matan sai ka rantse da Allah ciki daya suka fito.
Kamanni ne kawai zasu tona asiri,saboda kowa a cikinsu kamanninsa daban,hasken fata ne kawai ya hadasu,tun iman na qarama ta fita daban,tana da kyan fuska qwarai da kuma yalwar suma,wadda ta gajeta daga wajen inna.
'yar lele iman take a wajen alamin tun tana da qananun shekaru,zai iya hana cikinsa ya bata,duk abinda tace tana so to matuqar yana dashi sai ya bata,idan babu kuwa zai nema mata,abinda yasa ya tashi kenan da zuciyar nema,zama da madaukin kanwa inji hausawa sukace shike kawo farin kai,tun saddiqu bashi da ra'ayi har zama da lamin ya sanya ya zama mai neman na kanshi kamar alamin din.
Kusan duk kudin daya samu wajen nemansa fiye da rabinsa siyawa iman wannan ne siya mata wancan,tun bata isa ado ba yake mata siyayyar kayan kwalliya da qyale qyale,tun malam da inna na fada,har suka fahimci a jininsa yake kulawa da iman,bazai iya dainawa ba,dole suka haqura suka sanya masa idanu,saidai innan tayi masa fada da kuma dabarar ya dinga aje wani abu saboda yayarsa,wadda a yanzu shekaru ke sake jaa nauyi na dada hawa kanta,tana kuma da buqatar taimako ko yaya ne.
Alamin shine kewa iman komai,itama duk abinda take da buqata alamin din take durafafa kanta tsaye,bata ko kallon sadiqu dan uwanta,saboda yana da zafi shi din,hakanan yanzu yanzu ba wani abu bane yakai mata bugu idan tayi ba dai dai ba,sabanin alamin.....wanda bashi da daukan zafi a kanta,hasalima yana tare duk wani abu da yasan xai bata ranta ko ya cutar da ita,idan tayi ba dai dai ba cikin ruwan sanyi zai nusasheta ya kuma gyara mata,tana kuma daukan maganarsa fiye data kowa cikin gidan.
Dinki dashi lamin yafi qwarewa,ya iya dinkin mata kamar masifa,har zuwa yanzu da yake kan shekara ta kusan goma sha shida,wannan yasa iman dake da shekaru goma sha daya cikin rayuwarta tun a sannan ta zama abun kallo,indai tayi kwalliya kowa sai ya yaba,tana da kyau sannan kuma alamin din yana fitar da ita da dinkuna sai kace wata qatuwar budurwa,don idan kaga dinkunan da take sanyawa saika tambaya waye yayi mata,sau tari idan yayi dinkuna ya samu kudi sosai,yakan je kasuwa ba tare daya gayawa kowa ba,ya samo mata atamfa falle bibbiyu masu sauqin kudi ya mata skert da riguna tsala tsala,saboda bata iya daura zani ba har yanzu,abinda yake hadata da inna kenan,kullum fama take amma har yanzu iman din bata iya ba,koda yaushe saidai ayi mata riga da skert ko kuma doguwar riga.
Idan kaga iman din saika dauka diyar wani ce,saboda bata rasa komai ba,kullum tsaf zaka ganta cikin suturu masu kyau.
Amin Abubakar haifaffen garin birnin kudu ne dake jahar jigawa,bafulatani ne uwa da uba,abinda yasa ya gaji kyau kenan shima tun quruciyarsa,tun shekarunsa basu fara nuna ba,yaro ne da tun a halittarsa Alla ya masa baiwa masu tarin yawa,yana da nutsuwa qwarai da gaske wadda ta hade masa da miskilanci,miskilancin da tun zamanin quruciya ya sanya ba kasafai zaka ganshi cikin wasanni irin na yara ba,yafi ganewa yana zaune daga gefe yana kallonsu,idan abu ya burgeshi ya saki murmushi kawai.
Kafin rasuwar mahaifiyarsa ya samu tarbiyya qwarai daga wajenta,wannan tasa ya zama wani na daban,idan yana wasu abubuwan saika dauka wani babba ne me shekaru.
Yadda malam da kuma inna suka riqeshi abune da bazai manta dashi kafatanin rayuwarsa ba,sun masa wani gini sun kuma zame masa garkuwa kuma ginshiqi cikin rayuwarsu,ya fahimci daga inna sadiq da kuma malam dukkaninsu suna qaunar iman,suna dannewa ne saboda yanayi irin na tarbiyya,shi kuma baiga abinda zaiyi ya faranta musu ba fiye da kula da abinda sukeso,hakan yasa ya sanyawa kansa bawa iman din dukkan kulawa,sannu sannu kuma sabo da shaquwa suka shiga tsakaninsu.
Wani lokaci har mantawa yakeyi,yakan kallo iman din a matsayin 'yar uwarsa ta jini,har sai idan wani abun ya gitta da zai sanya ya tuna cewa ba jininsa bace.
_shimfida kenan......muje zuwa_
_ina matan dake fama da qaranci ko daukewar sha'awa saboda gajiya qarancin sinadarai ko kuma gajiya a jikinsu?,kina fama da maigida wajen rashin samun gamsuwa fannin auratayya?,dukka matsalarku ta yanke da HILTI UNISEX CHOCOLATE,maza garza kizo ki nema taki_
_CHOCOLATE CE da zaki shata kamar sauran chocolate,saidai kuma aiki a jiki,ba ruwanki da neman tarkacen magunguna mata marasa inganci,AKWAI TA UWAR GIDA AKWAI TA MAIGIDA_
_GAME BUQATA KO KUMA SON QARIN BAYANI,SAIYA TUNTUBI WANNAN NUMBER_
+234 818 401 7452
*Tasted and trusted*👍🏽👍🏽
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 🔥🔥 *KUFAN WUTA*🔥🔥
NA
*HUGUMA*
Free page 04
*_MASOYA 'YAN QASAR NIJER,ZAKU TURA KATIN WAYA(AIRTEL/MOOV) TA WANNAN NUMBER_*
+22795166177
Zaune take saman kujera 'yar tsugunno,sanye da uniform na makarantar primary din da take zuwa,tana ta qoqarin daura takalmin sandal a qafarta,komai nata tsaf kuma fes,karin guga ya kama uniform din jikinta sosai,shaidar cewa suna samun kulawa yadda ya kamata,hatta da takalmin sandal din qafarta qyalli yake,kamar yadda farar safarta take qal kamar baa sakata.
Wannan kusan duka aiki da horon lamin ne,idan baiyi mata da kansa ba,to ya riga ya koyar da ita,iman din akwai tsafta kamar yadda lamin din yake,bare ma kafin ta yiwa kanta wani abu sau daya yayi sau goma,wankinta da nashi duka suna wuyansa,kama daga uniform dinsu zuwa kayansu na zaman gida.
Lamin din na tsugunne gefan kitchen yana shirya mata abinci a wani dan qaramin kwando me kyau,wanda shi da ita sukaje ta zaba ya siya mata,tana ta masa surutu yana biye mata,wanda duka akan jarrabawar common interence da zata zana ne a yau,inna na daga cikin kitchen din tana zubawa shi yana shiryawa har ya gama,dai dai sanda ta gama sanya safa da kuma warin takalmi daya,dayanne ya gagara,don haka lamin din ya qarasa wajen ya tsugunna ya kama takalmin yana daura mata,sannan ta miqe tana diban takardunta sabon pencil biro har ma da cleaner dasu sharpener da lamin din ya siya mata.
Suka miqe suna yiwa inna sallama,saboda lamin din ne zai kanta har can inda zasu zana jarabawar da kansa,daidai lokacin malam ya shigo
"A'ah,har kin gama shiryawa kenan,to ai Allah yasa motar bata tashi ta barki ba" malam ya fada yana danna wayarsa Tecno keypad dake hannunsa saboda yaga lokaci
"Dama ba tare zamu tafi ba,ya lamin ne zai kaini" iman ta fada tana duban malam
"A'ah,wanne irin sakarci ne wannan,ya ga motar makaranta zaki ce saidai laminu ya kaiki?,ki wuce ki shiga cikin 'yan uwanki dalibai ku tafi"
"Ai malam kada ma ka bata bakinka,babu yadda bayi dasu ba,tun jiya nake sababi,amma dole ne naja bakina na tsuke,saboda shine yake goya mata baya,wai kada ta shiga cikinsu uniform dinta ya cukurkude......sai kace tafi kowa" jin inna ta sako baki ya sanya iman ta fara narai narai da ido kamar me shirin sanya kuka tana duban lamin din,so take ya sanya baki,kada su malam su hanashi ya rakata.
Zahiri ita tsoro takeji,saboda yadda taji wadanda suka gama primary wancan shekarar suke fadan wahalar jarabawar,duk da yadda lamin din ke qarfafa mata gwiwa tare da nuna mata cewa ba wani abu,suma sunyi fa,iya karatu tasan ta yishi,don a rana suna kwashe awanni masu yawa lamin din yana mata lesson,tana da matuqar qoqari da fahimta,saboda haka duk karatun da yake mata tana daukeshi,wannan dalilin ne yasa lamin din yaci burin tayi karatu mai zurfi,duk sa'ilin da suka zauna suna hira kuwa rabin maganarsa kenan,wannan abu yayi tasiri itama cikin ranta,bata da burin daya wuce ta ganta ta gama qaramar makaranta ta shiga jami'a,ta zama likita lawyer ko 'yar jarida,cikin ukun nan takeso ta zama daya.
"Malam kasan wannan shine karonta na farko da zata fita wani waje tayi jarrabawa irin wannan,rakatan kuma zai qara mata qwarin gwiwa,tunda makarantar basu hana ba malam ka bari na kaita" da qyar lamin yasha kansa ya barsu suka fice.
A soron gidan ya dakata yana cewa
"Bari na tada sadiq ya rakani,tafiya bibbiyu tafi dadi"
"Yaaya,Allah bazaije ba koka tasheshi" iman ta fada tana jan tunga,sai ya waiwayo ya kalleta,taso bashi dariya yadda ta tsuke dan qaramin bakinta ta marairaice,ya fuskanci so ne batayi yaje din,don tabbas idan suka tafin tare bazai barta ta sake ba,duk kuskuren da tayi saiya taso mata da fada hantara ko kyara.
"Ina zuwa dai" ya fada yana saka kansa cikin dakinsu.
Saidai duk yadda yaso tada sadiq din ya rakashi ya qiya,sai ya cusa kansa ma qasan filo yana cewa a dawo lafiya,Allah ya bada sa'a,dole ya fito daga dakin ya barshi.
Dadi iman din taji,ta dinga boye dariyarta har sai data fito ta dara,harara lamin din ya watsa mata da lumsassun idanunsa
"Ni kikewa dariya saboda ya yarfani ko?" Sake qyalqyale masa tayi da dariyan
"To ai yaa lamin kai kam baka iya harara ba,hararaka irin ta masu jin bacci ce" fara'ar fuskarta kadan ta ragu
"Ya lamin,ni dakai me yasa dukanmu bamu da lafiyar ido?" Ta tambayeshi sanda suka kusa ficewa daga layin nasu tana dubansa,da alamun damuwa cikin muryarta.
Murmushi ya sake wansa iyakarsa saman lebansa,duk da qarancin shekarunsa amma yanayinsa kamar wani babban matashi,akwai wani iri kwarjini na daban dake fita saman fuskarsa.
Duk da cewa a shekara ta sha bakwai yake amma hankalinsa tabbas yafi na iman din nesa ba kusa ba,kasantuwarsa namiji ita kuma diya mace
Cikin harshen da yake ganin zata iya fahimta ya fara mata magana
"Lafiya lau idanunmu suke ni dake,ba kina gani sosai ba?,ko akwai wani abu da bakya iya gani" saifa girgixa kai alamun a'ah
"To kin gani ba.....nima ina gani sosai,har daga nan ina iya ganin wanda ke tsaye gaban rumfar malam dalha" ya fada yana nuna wajen da yatsa,abinda ya sanyata tada kai ta kalli wajen,kawai tazarar nisa a tsakaninsu,don haka abun ya bata mamaki,har ta fidda idanu,sannan ta waigo gareshi
"Yaaya" kai ya jinjina mata,bata sake kokwanto ko tantama ba,saboda tasan halin lamin din tunda ta fara wayo,qarya itace abu na qarshe da baya kusantarta a rayuwarsa kaf,koda ya gaya mata waye a tsayen,da suka isko wajen saita ga shi dinne kuwa,abinda ya sanyata sakin dariya
"Na yarda Allah yaya,lafiyarmu qalau" murmushi ya kuma saki a maimakon dariya
"Na gaya miki dama,yanayin halitta ce,kowa da yadda Allah ya halicceshi,kamar yadda yayi wani dogo,wani gajere,wani fari wani baqi,wani me kyau wani akasin haka"
"Wani me suma me kyau irin taka,wani kuma tashi irin ta yaya sadiqu ko?" Wannan karon dariya ta bashi,har haqoransa suka bayyana
"Zaki bayani duk randa kika fada a gabansa,shima sumarsa me kyau ce sosai iman....,amma taki tafi tasa kyau sosai" murna ta cikata,tadanyi tsalle kadan
"Don Allah yaya ba na fishi kyau ba?"
"Neeeesa ba kusa ba" ya fada yana duban fuskar dake cike da quruciya,murmushi na fita daga kan tata fuskar
"To amma me yasa yake cemin me idon mage,mummuna?" Ta tambayeshi tana tura baki,saiya sake sakin murmushi,indai yana tare da iman din bata bari fuskarsa da bakinsa su huta
"Ki rabu dashi,kishi yake dake" ta saki qaramar dariya cikin nishadi,tana jin dadin zama da ya lamin fiye da kowa cikin gidansu,duk sanda zai bata amsa,yana bata amsa ne ta yadda zata dace da ra'ayinta da kuma abinda takeson ji,indai yana nan baya bari bacin rai ya zauna saman fuskarta,da irin wadan nan hirarrakin sannu a sannu har suka samu abun hawa,ya kaisu inda daliban shekarar daga makarantun wannan qaramar hukumar zasu zana jarrabawar.
Sai daya tabbatar da shigewarta exam hall din sannan ya juyo zuwa gida,a qafa ya zabi ya tako zuwa gidan,saboda kudin dake gareshi su isa kawosu gida shi da iman din zuwa la'asar idan an gama jarrabawar.
Yana gab da isowa qofar gidan nasu ya hangi yarinyar na tahowa,ubaida 'yar layinsu ce,ya fuskanci duk sanda xasu hadu da yarinyar saita dinga wani sinqe sinqe,idan sukayi clashing kuwa haka zata gaidashi cikin girmamawa,duk da cewa kwata kwata shekarun da ya bata basu wuce biyu ko daya ba,saidai yanayin garin jiki da kuma kwarjinin da yake dashi,zaka zaci cewa wani babban yayanta ne.
Yanzun ma yana kallonta tayi wuf ta shige soron wani gida ta buya,saidai taci gaba da leqensa har ya wuce ta sannan ta fito.
Yana da yawan gumi,don haka sanda ya isa dakinsu ya jiqe da zufa,ya samu sadiqu ya fito a wanka daga bandakin da ba'a dade da yi musu ba cikin dakin nasu,wanda suka hada kudi abinsu shi da saddiqun aka musu,saboda girma da sukaga sun fara,lamin ne ya kawo wannan shawarar,kuma ta kwantawa saddiq din,da yake dakin ma sha Allah yana da girma,don ya dauki katifunsu guda biyu bayan leda me kyau dake malale a dakin,da yake ba wanda yake shigar musu kuma wuni suke wajen sana'a ledar lafiya lau take,sai kujera guda daya doguwa da kuma kwabet ta katako mara tsaho amma kuma tana da fadi,anyi mata bangare biyu kowa da sashen kayansa,kusa da kujerar akwai wani dam teburin na katako da talabijin ta zaune,da receiver a kanta,wadda suka jona daga maqota,dama ba wani kallon arziqi suke ba,sunfi kallo sanda ake ball da wani waje,shima kusan sadiq ne me wannan nacin,lamin din yafi ga sauraren news a redio.
Suna hada ido ya harari sadiq din wanda yake daura tazugen gajeran wandonsa
"Baka kyauta ba wallahi,abinda kake sam bai kamata ba"
"Allah ya sani bazan iya irin rayuwarka ba,yarinya sai shegen fi'ili da shagwabar banza da wofi,kamar wata yayayya,ayita riritata,yarinyar da an kusa bude mata littafin ayyukanta nan da wasu shekaru kadan" sadiq din ya amsa masa yana zura riga a jikinsa,harararsa lamin ya sakeyi
"Idan bamu kula da ita ba da waye ne zamu kula?,ita kadai ce fa a gabanmu?,kuma ma ina wani shagwaban yake?,kaidai matsala ce dakai kawai,kuma idan baka canza ba bazamu taba dai daitawa ba" daga haka yaja towel dinsa dake hannun kujerar ya shige bandaki,yana jiyo sadiq yanata qananun maganganun indai iman bata canza ba shima bazai canza ba.
Kansa kawai ya kada cikin takaici,dukkaninsu har yau sun kasa karantar iman,kamar shi daya shi da.malam ne suka fuskanceta,ba shakka tana da sakalci da shagwaba wani lokacin da gabunta irin na yaran da ake haifa daga qarshe,to amma fa tana da hankali da wata irin nutsuwa,haka kuma tana da fikira da saurin fahimtar abu,ko yaya ka zauna da ita zaka san cewa uwa ta gari ta taka muhimmiyar rawa wajen nutsuwarta da dabi'unta,yarinta kuwa har yanzu bata wuce lokacin ba,so dole sai an dinga mata uzuri ana nusasheta harta wuce lokacin.
Sanda ya fito lallausar sumarsa mai santsi da zaka zaci relaxer yake sanya mata tanata digar ruwa,zuwa sannan har sadiqu ya shiga cikin gida ya karbo musu abun karyawa,kunu ne me zafi sai qamshin lemon tsami yake,sai kuma fanke da qosai wanda ya tabbatar qosan nashi ne,saboda shi fanken bai dameshi ba,qosai ne koda ya huce zai cishi a haka yana jin dadinsa,koshi ko alala,sau tari sadiq na tsokanarsa da cewa
"Wai lallai saika nuna kai cikakken bafullaci ne,qauna ce shadidiya tsakaninku dama da qosai" wani lokaci yayi dariya ya barshi,wani lokaci kuma ya rama.
"Yauwa,daga kan plocker dinka akwai saqo gashinan an bani,ka duba" sadiq ya fada yana qoqarin kai cup din kunun bakinsa,ajjiye towel din da yake goge kansa dashi yayi ya qarasa gaban locker din,wadda take dauke da tarkacen kayan shafa na maza,kai kace wani zabgegen saurayi ne,tarin turaruka ne kala daban daban,kama daga roll-on, sure,body spray,body mist masu sanyi,da turaruka na kaya shaving cream,da body cream masu sauqin kudi,man wanki baki da mayukan gashi na maza,sai kuma man saka takalmi yin qyalli.
Hannu yakai ya dauki farar takardar da aka nannadeta four corners,ya ware a hankali,sannan ya zuba mata sleepy eyes dinsa da suke a lumshe,yana bin yadda aka zane takardar da zanen furanni da kuma tsuntsaye,sannan ya sauka ga saqonnin soyayyar dake rubuce a tsakiyar wani lafcecen heart (zaku iya tunawa da wasiqar soyayya da ake rubutawa zamanin quruciya?,ya kai zunzurutun zinaren mazirarin zuciyata?😂).
Maida wasiqar yayi sama a qasa yana lalubo sunan marubuciyar,sunan ubaida ya bayyana,saiya linke takardar,sannan ya waiwaya ya dubi sadiqu
"Yaushe ka mayar dani dan iska ka fara karbo wadan nan abubuwa kana kawomin?,bari to na ajjiye na kaiwa malam,kada wataran ya kamaka ya zaci bakinmu daya,ko kuma ni nake aikenka" da hanzari sadiq ya tashi yana danne dariyarsa yasha gaban lamin dake zura jallabiyarsa ta barci
"Kaga.....ni kada ka yimin sharri,ni ina ruwana?,ina zaune ta aiko qanwarta ta kawomin,kaga kenan bani na janyota ba ko bare kace" tsayawa yayi yana duban sadiq din,ya sanshi qwarai da rawar kai,saboda yawancin lokuta idan yaga ana tashi daga aiki lamin din ya biyo masa ya sakashi a gaba sunyo gida,suna isowa anyi magariba sunyi masallaci,saga can sun zauna karatu da malam,ana tashi hira cikin abokansu lamin din baya bari su zarce awa daya zai takura sadiq din kan su shiga gida,ko su zauna a dakinsu suyi wata hirar,ko suyi karatu,ko su kalli ball idan nepa sun agajesu da wuta,ko kuma su zauna tare da inna kafin malam ya shigo,yakan yi qorafin
"Waikai.....sai kace wasu mata da Allah,kai ko dan 'yammatan nan da akeyi na layi bamu da,kana gani su buhari fa,yarinyar nan ta bayan layinmu har dan wasiqa suke aikawa junansu" kallonsa kawai lamin yakanyi
"Shekararmu nawa ne?"
"Sha bakwai mana,ni harda watanni ma"
"Tabdijan,a shekara sha bakwan har mukai wannan matakin?,meka ajjiye?,me kake dashi?,wanne mataki ka taka a karatu?"
"Mtseeww,ka gane mana,bafa wai aure zamuyi bafa,kawai irin dai soyayyar nan da kowa ke tabawa ce,ai abun kunya ne a yadda mukafi dukka samarin unguwar nan kyau amma ace mune bamu da budurwa"
"Nidai a wajena ba abun kunya bane,amma tunda kai a wajenka haka yake,kaje Allah ya bada sa'a" daga haka ya maida hankalinsa ga qaramar tvn dake gabansa,wanda suke hasko wasan da ake bugawa ta gasar nahiyar turai,tsakanin Manchester da Barcelona.
Yana jin sadiqun yana mitar yanzu kallon qwallon ma sudanje gidan kallo suyi cikin mutane amma abu ya gagara,kowa yana can ma su suna cikin gida kamar mayu.
Shi sam irin wadan na shirmen na tashen girma Allah ya tsameshi,baya bashi sha'awa ko kadan,yadda yake gudanar da rayuwarsa yafi masa dadi,shi mamaki ma yake idan yaga sa'anninsu suna soyayya,tome zasuce a wadannan shekarun nasu?,dariya suke masa idan ya fadi hakan,sau tari sukance
"Dama mune muke da kyau irin naka?,kai don bakasan yadda 'yar mata matan nan ke sonka ba,miskilancinka kawai yasa suke shakkar yi maka magana".
Hannu lamin ya sanya kan locker din tasa bayan ya gama wannan tunanin,ya ciro wani man fito da saje da qasumba da sadiq din ya siyo tun rannan,wurgi lamin yayi dashi saman kujera
"Shi yasa dama ka siyo wannan saboda kayi sauri ka hada gemu kai dole gaka babba ko?" Yadda lamin yayi maganar cikin jin haushi ya sanya sadiq qyalqyalewa da dariya dole
"To wai kai din da kaketa haka waliyyi ne kai?,girman nan fa yana tahowa na gaya maka gaskiya,don ko a yanzu haka habarka ta fara gemu,toni kuma saina zauna a haka a rainani?,ko kai rannan ina ganinka kanata matse matse?,waye yayi wankan asuba shekaran jiya?" Ya qarasa fada qasa qasa saboda kar a jiyosu.
Kafin sadiq ya ankara lamin ya kwada masa wani comb da yake taje sumarshi,a baki yaso ya sameshi Allah ya taqaita masa ya goce ya samu kafadarsa,sai yayi qofa yana sheqa dariya
"Kaga kenan gwara ni,kiran girman kawai nake,kai kuwa ya fara samunka,idan ka gama shiryawa ina jiranka a wajen inna" saboda wajen sana'arsu zasu wuce,don suna hutu ne saboda sun kammala rubuta jarabawar qualifying,suna jiran wucewarsu S S3,bugu da qari ma kuma weekend ne.
Yana shiryawa maganar sadiq na dawo masa,a ranar ya faki idanun sadiq yayi wankansa ne baisan yana ganinsa ba,bayason sadiq din ya sani,saboda yana kunyar abinda zaice masa,duk da cewa daga shi har sadiq din ba jahilai bane,tun kafin zuwan wannan lokacin malam ya musu bayanin xuwan nasa,saidai shi abun naso yazo masa da wani yanayi na daban,yana jin cewa halittarsa ta dabance,don kusan bai taba ganin ko ji daga sadiq din ya shiga yanayi irin nasa ba.
A nutse ya shirya,kamar ko yaushe tsaf dashi,cikin wani yadi mai sanda sanda me sauqin kudi,yayi kyau,dai dai da matashi mai qananun shekaru.
A tsakar gida ya samu inna da sadiq din,ya miqe suna yiwa inna sallama,ta rakasu da kyakkyawar addu'a da kuma fatan alkhairi,ta bisu da kallo tana jin alfahari da 'ya'yan nata,wanda tsakanin sadiq din da lamin bata banbace wanda tafiso a cikinsu,tun bayan shigowar lamin din rayuwar gidan.
Tun qarfe uku ya katse dukkan ayyukansa bayan ya dauki uzuri waje ogansu ya koma daukar iman din.
Baifi jiran minti talatin yayi ba daliban daga makarantu daban daban suka fara fitowa,yana tsaye harde da hannayensa ya hangota,ya zuba mata idanu yana murmushi ganin yadda take waige waige,ya tabbatar da cewa shi take nema,yadan sake sakayewa kadan don ya gani ko zata iya ganoshi,saidai batayi wani nisan zango ba golden eyes dinta ya hango mata shi,saita taho da dan gudunta ma gauraye da quruciya tana dariya,tana zuwa ta daneshi.
A hankali yasa hannunsa yana zareta daga jikinsa,ita kuma tana sake maqaleshi tare da fadin
"Ya lamin mun gama...."
"Imaannn" ya ambaci sunanta yana dan dagewa kadan
"Sakeni mana" turus tayi bayan ta sakeshi tana kallonsa,baki a tabe alamun shagwaba
"Yaya me nayi maka?"ganin yadda fuskarta ta nuna rashin jin dadinta saiya duqa a gabanta yana duban golden eyes dinta
"Iman.....daga yau kin girma fa,kin zama babba,ko baki gani bane?,kin zana jarabawar fita daga primary,zaki tafi secondary,duk wanda yaje secondry kuwa ya girma.....wadda ta girma kuma ba'ason tana taba maza kinji?" Saita tura baki gaba
"Ni bana kula kowa Allah ya lamin,ko mazan ajimu ma Allah,kaine kawai,kuma kai ba yaya na bane?" Kansa ya gyada yana sake fidda murmushi
"Yayanki ne,amma ko nidinma daga yau na hana kinji?saboda kin zama big girl" Kanta ta gyada,saidai da alama har cikin ranta bata gamsu ba,yana ankare da ita yadda tayi kicin kicin da rai,duk yadda yake janta da hira kan yadda taji jarabawar taqi sake masa ta bashi labari,bai gaji ba yaci gaba da janta da hirar har suka iso bakin titi don su tari abun hawa.
Dalibai ne birjik da masu daukarsu,daga gefansa wata 'yar matashiya ce riqe da hannun wata daliba,da alama qanwarta ce,tunda ya shiga wajen dauko iman ya lura da yadda taketa satar kalloshi,dauke kai yayi yanzun ma kamar dazu,ya sanya hannunsa cikin aljihunsa ya fito da baqin glass dinsa da yakan sanya lokaci lokaci.
Sanyawar da yayi saita sake haska kyanshi cikin farar fatarsa,ya miqa hannu yana tsayar musu da adaidaita sahu,gaba kadan dasu ta tsaya,ya taka ya tsaya yana masa bayani inda zai kaisu.
Yana shirin shiga yarinyar ta qaraso tana fadin inda zata itama
"Shiga muje" mai adaidaitan ya fada mata jin hanya daya ce,abinda yasa fasa sanya qafafunsa,ya kuma dauke kwandon iman da ya zura a motar yaja baya yana cewa
"Kuje kawai" binsa ta danyi da kallo
"Dukkanmu qannenmu muka dauko,kowa gida kuma yakeson zuwa,kuma tunda yace muje ai hanya dayace ko?" Ta fada tana dan fara'a,kai ya gyada
"Ga wasu 'yan uwanki can daga gaba,idan hanya daya zaku shikena sai ya cike dasu" yanayin fuskarta ya nuna bataso ba,amma haka ta saka qanwartata itama ta shiga.
"Yaya sun tafi fa,dama shiga kawai mukayi" sosai ya kalleta sannan ya amsa mata
"Babu kyau hada maza da mata guri daya,nima bazanji dadi ba idan kika shiga keda wani" tadai jishi ne,amma bata fahimta abinda yake nufi ba.
Basu dade ba suka sake samun wani abun hawan,a hanya ya siya mata tarkacen alawoyi,abinda ya sanyata sakewa kenan,ta dinga bashi labarin jarrabawar,da kuma yadda ta amsa kowacce tambaya,don kusan duk abinda ya karanta mata shi taga ya fito.
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 🔥🔥 *KUFAN WUTA*🔥🔥🔥
NA
*HUGUMA*
*ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥
*LAST FREE PAGE*
*_GA WADDA KE BUQATAN BIYAN KUDINTA,ZATA IYA TUNTUBARMU TA WANNAN NUMBERS DIN_*
09032345899
KO
09166221261
Tun bayan zana jarabawarta ya soma mata tanadin tafiya zuwa makarantar gaba ba tare da kowa ya sani ba,ya siya duk abubuwan da yasan zata iya buqata da kadan da kadan,zuwa lokacin ya fara canza yanayin kusancinsu,sabida girma daya fara zuwan mata,a sannan ta shiga shekara ta goma sha uku,duk wasu abubuwa daya kamata ace ta sani yana koyar da ita cikin dabara da kuma hirarsu,abubuwan da ya kamata diya ta sani a shekarun fara girmanta,bugu da qari innarta itama ba baya bace,sau da dama idan ya gaya mata wani abun takan ce inna ta gaya mata,saidai bata fiya daukarsa serious ba kamar idan shine ya gaya matan,tafi maida hankali idan shine ya fada mata da kansa.
Cikin sa'a jarabawarsun ta fito,taci wata government school da basu da nisa da ita,ba bata lokaci malam ya fara mata shiryen shiryen komai,saidai ya tadda amin yaci rabin aikin,shuru malam yayi cikin mamaki tare da qara qaunar amin din har cikin jininsa,irin kulawa da iman ke samu a wajensa ko dan uwanta da suke ciki daya sadiq bata sameta ba.
Bashi da abinda zaice masa banda godiya,godiyar da take saka amin din jin nauyi da kunya,saboda shikam har yanzu a nasa ganin bai sakawa su malam din da komai ba,don har kwanan gobe arziqinsu yakeci,sun sanyashi cikin iyalinsu,yana kwana ya tashi muhalli daya dasu,kuma har kwanan gobe malam din bai daina ciyar dashi da dauke masa wasu buqatu irin na uba da dansa ba.
Duk da haka malam din ya kwakkwafeshi kan ya dinga adani da tanadi,ya daina qarar da duka nemansa akan iman din kadai,ya shaida masa yana taru,bai nutsu ba sai daya samu tabbacin hakan daga bakin sadiqu.
Bangaren inna ma saidai addu'a da fatan Allah ya jiqan mahaifansa,amin din hannun kyauta gareshi,abun duniya bai rufe masa idanu ba sam,kulli yaumin baya taba shigowa hannunsa rabbana cikin gidan,wannan dabi'a tasa har sadiqu ya koyeta,hakan kuma bai sanya ya manta da yayarsa dake garinsu ba wadda tasha dawainiya dashi ba,duk sanda zaije ganinta yakan riqe wani abu me kauri yakai mata.
Cikin nasara iman ta fara zuwa makarantar,yarinya ce mai hazaqa da kaifin basira,gefe daya kuma ga alamin,ya soke hirar dare saidai karatu,idan sun gama karatun ayi hirar kafin inna ta korata ta kwanta,cikin qanqanin lokaci tayi suna cikin makarantar.
Sannu a hankali rayuwa keci gaba da tafiya musu cikin nasara,iman ta gama js 1 ta tafi js 2,har ta tafi zuwa js 3,a sannan tuni yammatanci ya fara zuwar mata,duk wani baiwa da surar kyau na 'ya mace ya fara bayyana a jikinta,wani irin sassanyan kyau wanda hatta da inna ya sanya take sake saka hankalinta da kulawarta akan diyartata,don ko ita duk da tashen kyau da tayi zamanin quruciya bata kai iman din ba,inda Allah ya taimaketa iman din nada wani irin nutsuwa da kuma kamun kai,bata da hargagi ko hayaniya,ko rawar kan yaran da suke tashen girma.
Ta bangaren alamin ma ya sanya kulawarsa sosai akan iman din,bama shi ba harda sadiqun da suke ganin kamar bai damu da al'amuranta a baya ba,saboda lokacine na sabbabin qawaye,kuma lokacine da qananun samari da suma suke tashen girma suke iya shiga rayuwar yarinya,su sauya ta tare da koya mata dabi'u kala daban daban.
A sannan Allah ya fara sanyawa nemansa albarka,don cikin shagon nasu da suke dinki a yanzu haka shima ya mallaki keke nasa ma qashin kansa,idan bashi da makaranta zama yake ya wuni yana dinkinsa,idan kuma yana da lectures sai ya bada haya wani ya hau,da kudin dinkinsa yake sponsoring karatunsa da komai na rayuwarsa,ya taimaki yayarsa da a yanxu babu abinda zatace dashi sai hamdala,hakanan daga inna har malam gajiyar alamin din sukeci sai godiya.
Yana da tsari da kuma bin komai a sannu,bai dauki rayuwarsa da zafi ba,bai kuma dauki kansa a wani ba,komai nashi moderate yake yinsa tsaka tsaki,babu qarya a ciki,baya kallon wai collage yake,dole sai yayi abinda wane da wane sukeyi,idan ka ganshi baka isa ka aibatashi ba ko kai waye,yana da tsafta da sutura ta zamani bakin gwargwado,saidai duk abinda yasan zai zame masa wahala baya kawoshi cikin rayuwarsa,hatta da wayar hannunsa mai matsakaicin kudi ce,bai damu da sai ya riqe babba ba,tunda wannan din zatayi masa komai da babbar zatayi masa,yakanyi tunanin gwara ya sanya kudin cikin sana'ar dinkinsa,don a yanzu wani keken yakeso ya sake siya banda wanda yake dashi.
Dukkan wani rufin asiri da kuma kyautatuwar rayuwa ya sameshi,iya shi da sadiqu a qananun shekarunsu sun tsayawa gidan,sun saukewa malam abubuwa da yawa su sukeyi,don hatta da harkar karatunsu,kama daga kudin registration da sauransu su sukewa kansu da kansu.
**********Kamar yadda al'adar gidan ranar kowacce juma'a tuwon shinkafa akeyi miyar taushe,wannan juma'ar ma hakan take,gefin magariba IMAN ta gama komai,ta kuma killace gidan kamar yadda ta koya daga mahaifiyarta,saboda a yanzun da shekarunta suke goma sha biyar,dukkan wani aiki da ada yake wuyan innar yanzu ya dawo wuyanta,ta horu da wannan tun tana da shekara goma a duniya,don haka sam komai baya bata wuya a yanzu.
Tsaye take gaban dogon madubin dake jingine,wanda ya kusa rabin qofar dakinta,gefe da gefansa sama da kuma qasansa an zagayeshi da katako mai kauri saboda ya bashi kariya,tare da samun damar tsaiwa sosai a muhallin da aka ajjiyeshi.
Daure take da zanin data fito daga wanka dashi,sai tasa hannu ta zare dan qaramin hijabin da take xurawa duk sanda zata shiga wankan,take jiqaqqe gashinta daya kwanta har gadon bayanta ya bayyana,yasha ruwa sosai,saboda wankan tsarki da tayi na al'ada data gama.
Sai data sanya qaramin towel ta sake goge gashin nata sarai,tadan fifitashi kadan yasha iska,sannan ta shafeshi da mai,ta kuma sanya cumb ta tajeshi,take ya dauki sheqi,cikarsa kuma ta bayyana,taja kujera ya qarama da takan zauna akai idan zatayi kwalliya,ta fara mulke jikinta da mayukanta da take amfani dasu.
A nutse ta gama shafa manta,ta shafe fuskarta da powder,tana yi tana duba dan qaramin agogon dake manne a saman mudubin nata,wanda lamin ya siya mata,saboda tashi tafiya makaranta.
Gaban akwatinta dake shaqe da kaya ta zauna tana duba kayan da zata sanya din,batason ta saka wadanda zasu dameta,saboda zafi da akeyi,uwa uba ma kuma ba jimawa zasuyi a jikinta ba zata cire ta saka na kwanciya barci.
Garin daga kayan idanunta suka sauka kan wasu kaya baqaqe masu adon farin zare,da sauri ta sanya hannu ta daukosu tana waresu,sai yanzu ta tuna dasu,kayan da inna rabi ta bata(yar uwar innarta),kaya ne na buzaye masu kama da saqin fulani,saidai shi plain zani ne da kuma riga mai kama da buba,wadda iyakarta cinya,kala biyu ne kayan,akwai jajayensa,dukansu ta ajjiyesu da zummar zata saka kuma bata saka din ba,sai yanzu data binkito wajen ta gansu.
Miqewa tayi ta fara gwada rigar,ta isa gaban madubi,tar kamanninta suka fito,baqaqe kayan sun kwanta saman farar fatarta sun qara mata wani irin kyau,sun kuma tafi da qirar jikinta,duk kuwa da cewa a sake suke,sai ta dan soma jujjuyawa kadan tana sin ta sake ganin yadda suka amsheta,tana qiyasta ranar da zata sakasu.
Qwalla mata kiran da inna tayi ya dakatar da ita daga abinda takeyin,tana daga dakin ta amsa tana duba agogi,tasan ba shakka ta gota lokacin da take kaiwa su ya saddiqu abinci,don haka ta rarumi zanin kawai ta daura,ta yafa dankwalin kayan saman kanta.
Innar bata tsakar gidan,tabbacin cewa daga rumfarta take mata wannan kiran,bata kai ga shiga rumfar innar ba ta jiyo muryarta tana fadin
"Ki dauki abincinsu aminu ki miqa dakinsu,ashe tun yammaci ya dawo bashi da lafiya,bai qaraso ciki ba ya shige dakinsu ya kwanta abinsa,sai yanzu da abubakar ya shigo yake gayamin" har cikin ranta taji wani rashin dadi jin cewa baijin dadi,bai kuma gayawa kowa ba,bayan ita idan bata da lafiya bai barinta tayi jinya ita kadai,tun daga zamanin quruciya har yanzu data fara sanin ciwon kanta,sai ta amsawa innar da to,ta juya da sauri zuwa kitchen,ya debi kayan abincin data riga ta shirya musu,wanda dama ba kasafai take kai musu ba,sunfi shigowa su dauka da kansu,ta nufi soron tana takawa a hankali,cikin ranta tana fatan samun jikin nasa da sauqi.
Tana dab da bakin qofar dakin nasu sadiq ya daga labulen ya fito
"Ki zubamin a plate ya dan sha iska,yanzu zan dawo" ya fada yana sanya takalminsa,ta amsa da to kana tayi sallama ta saka kanta zuwa cikin dakin.
Babu kowa a dakin,sai motsin ruwa daga toilet din nasu,ko ina fes yake,sai qamshin tsintsiyar turare da kuma turarukan da suke amfani dasu daya gauraye dakin,tanason dakin tun ainihi,saboda yafi kowanne daki dake gidan sanyi da kuma dadin zama,a zamanin quruciya,tasha shiga dakin ayita nemanta,har bacci yayi awon gaba da ita.
Table din da tasan suna ajjiye karikicen kayan abincinsu ta qarasa kai ta dora a nutse,sannan ta bude fa fara zuba lafiyayyen tuwon farar shinkada,da miyar taushe wadda aka sakawa tantaqwashi,cikin mintuna qalilan qamshi ya bade dakin.
Plate biyu ta zuba harda lamin din,saita koma saman doguwar kujerar dake dakin ta zauna,tana dakon ya fito tayi masa sannu,duk ranta babu dadi sosai,dama kusan sati guda suna sabani dashi,basa haduwa sam,inna ta gaya masa yana wasu dinkunan biki ne,shi yasa yake fita da wuri ya kuma dade bai dawo ba,ga kuma makaranta.
Tana tausayin yadda yake nema tuquru,ya dauki sana'arsa da muhimmanci,fiye da yayanta sadiq,don shi wasu lokutan yakan zauna a gida yace bazai fita ba,musamman idan lectures suka hade masa ranar yasha wuya,amma bata taba ganin lamin din yana hutu ba,idan tayi magana sai ya saki murmushin dake qarawa idanunsa lumshewa yace
"Babu wani hutu a nan duniya,namiji kuma da struggling aka sanshi".
Yana da dabi'ar jimawa yana wanka,don haka sai ta tura hannunta cikin gashin kanta tana dan warashi saboda ya sake samun iska,a hankali har dankwalinta ya zame daga kanta,saita kamo gashin ta rabashi biyu ta fara kitsa kalba wai ko zaifi saurin shan iskan.
Sai da ya sanya hannu ya sake sharce gashinsa da kyau,sannan ya kama murfin qofar bandakin ya murdata ya bude a hankali cikin rashin qwarin jiki.
A hankali idanunsa suka fara sauka a kanta,tayi nisa da kitsa jelar kalbar,kayan jikinta sun haskata ainun,har suna canza mata yanayi zuwa ainihin bafulatanar niger kuma shuwa zam.
Bin jelar da take kitsawar yayi da kallo,zuciyarsa ta wani buga,sai ya lumshe idanunsa kana ya budesu duka lokaci daya,maimakon dauke idanunsa da yayi niyyar yi daga kanta,haka sai ya gagara,ya maida idanun nasa yana ci gaba da kallonta
"Anya ko zaka iya ci gaba?,zaka iya daurewa?,zaka iya cika alqawarin daka daukarwa kanka?" Jerin gwanon tambayoyin da ya jefawa kansa kenan,sai ya sake lumshe lumsassun idanuwansa da zazzabi ya sake sanyawa suka rusuna suka kuma janye,ya budesu lokaci guda yana qoqarin hadiye wani abu,kana yayi qoqarin jan qofar bandakin ya rufe,lokaci guda kuma yana takowa zuwa cikin dakin,yana qoqarin daure fuskarsa.
Motsin nasa yaja hankalin iman,bata damu da rashin walwalar dake fuskarsa ba,saboda tasan cewa bashi da lafiya,qila shine abinda ya kawo qarancin walwalar.
"Sannu ya amin" ta fada cikin nuna tsantsar kulawa
"Yauwa" ya amsa mata a dan dake,saita sake zubawa fuskarsa idanu,yau kadai sai take ga ya canza mata,wani girma da kwarjini da tsahon rayuwarsu tare bata taba gani saman fuskarsa ba a yau take gani,kodon yaune ta fara yi masa kallon qurilla?,ko don yaune kadai ranar da zata iya tunawa ya hade mata rai haka?
"Ina dankwalinki?,me yasa zaki bude kanki gaban abincinmu?,ko so kike ki haramta mana ci?" Yayi maganar still a dake,hannunta ta sanya ta baya ta janyo dankwalinta ta lulluba saman kanta,tun daga sanda ya horar da ita zama da dankwali,mawuyacine ka sameta babu shi,maimakon ya zauna sai ya nufi inda kayan shafarsa suke,ya janyo turaren da yake mulke singalalin hannayensa dasu ya fara shafawar,wannan dalilin yasa komai nashi qamshi yake,komai nasa kana iya ganeshi saboda qamshinsa na daban da yake yawan amfani dashi,abu guda daya cikin rayuwarsa da bai daukeshi da sauqi ba,yana kuma iya sanya ko nawa ne ya siyeshi wato TURARE.
Bayan ya gama ya dauki na jikin ya fara fesawa,cikin lokaci qanqani sassanyan qamshinsa ya budade dakin,iman dake zaune ta lumshe idanunta tana zuqar qamshin har cikin zuciyarta,tana mutuwa da mayatar son wannan qamshin tun ba yau ba,tayi tayi ya siya mata ko ya san mata nashi amma ya gaya mata turaren maza ne,mata kuma basa sanya turare maza,dole ta haqura,take amfani da wanda ya zaba mata,har kawo yau.
Bata ankara ba taga ya iso gaban flask din,ya bude flask din data zuba dan farfesun busashen kifi datayi musu da sauran kifin da malam ya siyo musu tun shekaran jiya waccar,basu iya cinyeshi ba saboda basu da yawa a gidan
"Ka kawo na zuba maka ya amin" ta fada tana kai hannunta da sauri kan kwanukan,saidai cikin rashin sa'a sai hannayensu suka hadu waje guda,saboda ya kawo nasa hannun ne shima don ya zuba,itama takai nata.
Da sauri ya janye nashi hannun,zuciyarsa na wani irin lugude cikin qirjinsa,karon farko itama a rayuwarta data ji wani shock har cikin jijiyoyinta,shuru ya ratsa na second guda,kafin ta rigashi sake maida hannunta tana yunqurin zuba masa,tare dayi masa sannu da jiki,ranta da zuciyarta yana bata cewa yau miskilanci ne ya hadu da ciwo hala,abinda ta jima bata gani ba tattare dashi.
Idanunya ya sauka kan jelar kalbar datayi guda daya,wadda keya reto gefan kunnenta saboda tsahonta
"Da sauqi alhmdlh" ya amsa yana janye idanunsa,tare da lalubar kansa,wai yau din me yake damunsa ne?,kamar yau ne ya fara ganin iman din.
Sosai yayi qoqarin hana idanunsa sake maida idanunsa kanta,saboda ya tabbatar a yau din akwai wani sabon al'amari dake shigarsa wanda baisan dashi ba
"Shikenan yaya?" Ta fada tana sake nannade jelar kalbar cikin yatsanta guda daya tana kuma kallonshi
"Eh" ya amsa mata a taqaice
"Allah ya qara lpy" ta fada tana juyawa zuwa hanyar fita,don ta karanci da gaske yau 'yan miskilancin ne a kusa,ta kuma fi kowa sanin halinsa idan suka motsa masa,idan ya sauko da kansa zai nemi inda take,ita kuma tayita qorafi kenan a sannan,saidai yayi murmushi kawai yace baisan sanda shi hakan ta faru ba.
Baisan ita yabi da kallo ba sai da ta fita a dakin,idanunsa suka sauka kan labulen dake lilawa,saiya dauke idanunsa da sauri,ya zamo daga gefan katifarsu ya sauka qasa sosai yaja abincin gabansa,yanata qoqarin ganin yaci,saidai duk da hakan tunani ne fal ransa.
Yana tuna maganar da sukayi da malam tun yana ajin farko a collage,malam din ya masa kyautar da har duniya ta nade bazai taba mantawa dashi ba,ya shaida masa ya bashi iman din halak malak,ya bashi ita a matsayin matar aure.
Sosai alamin yaji girma da nauyin kyautar malam din,bazaice baya son iman ba,kamar yadda bazaice yanajin soyayyarta a ransa ba,soyayya irin ta aure ba,yana mata soyayya irin ta 'yan uwantaka,saidai shi kansa yasan cewa matsayi ya bata a zuciyarsa bana wasa ba,matsayin da take dashi a wajensa ba na nan kusa bane,saidai koma mene a sannan yana ganin tayi matuqar qanqanta ya tunkareta da maganar soyayya,tunda yaci mata buri da kuma tanadi nayin zuzzurfan karatu,ya karba hannu bibbiyu kuma ya samu zuciyarsa tayi na'am da hakan,saidai ya barma ransa akwai ajiyayyen lokaci da zai fara tunkarar iman din da dasa mata soyayyarsa ta hanyar data dace,ta hanyar da bata kaucewa shari'a tsari da kuma al'ada ba,saboda haka ya nemi alfarmar malam din bayan ya gabatar masa da qudurinsa,ya shaida masa babu komai,shidai fatansa Allah ya sake hada kansu,sai gashi a yau rana tsaka ya soma jin wani baqon lamari game da iman din,tun lokaci bai kai masa Target din da yayi ba.
*1*~ *_KUFAN WUTA_*🔥
_Safiyya Huguma_
*1*~ *_BAQAR INUWA_*💥
_Billyn Abdul_
*1*~ *_RAYUWAR MACE_*💅
_Hafsat Rano_
*1*~ *_MASARAUTA_*💪
_Miss Xoxo_
*1*~ *_NOOR ALBI_*❤🔥
_Mamuhgee_
Guda 1👉300
Guda 2👉400
Guda 3👉500
Guda 4👉700
Guda 5👉1k
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM_*
*_DUK WADDA TASA HANNUNTA TAYI MAN SHARING LITTAFI NA ZUWA WANI WAJE ALLAH YA BIMIN HAKKINA DON ISARSA DA BUWAYARSA_*🤲🏽🤲🏽🤲🏽🤲🏽
*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,ZAKI IYA TUNTUBARMU TA WANNAN NUMBERS DIN*
09032345899
Ko kuma
09166221261
06
Daki ta wuce kai tsaye don cire kayan,tana tafe tana hangen fuskarsa cikin idanuwanta,bata taba ganin wanda miskilanci yakewa kyau ba irinsa ba,ba tun yau ba,tun shekarunta basu kai haka ba tasan da wannan.
Sake shanshana hannunta tayi karo na barkatai tana sheqar qamshinsa data dauko wajen saurin bude masa Flask din abincin,saita saki ajiyar zuciya,haka kawai yau din take jin zuwan nata dakinsu wani iri,cikin kasala ta qarasa cire kayan,sai ta zumbula doguwar rigarta kawai,ta dauki littafanta ta tafi dakin inna,saboda yau ta tabbatar babu zancan karatu,tunda amin din baya jin dadi.
Sanda ta shiga dakin innar ta fita dubo amin din nata,babu jimawa ta dawo,tana ta mitar yadda ya dawo ya shiga daki ya kwanta da ciwo a jikinsa bai gayawa kowa ba,motsi kadan sai tambayo sadiqu jikin nasa,bata samu sukuni ba sai data tabbatar da sauqin.
Wani abu daya tsayawa iman din a rai,yadda ta dinga juyi wajen bacci tana hango fuskar ya amin din,sai zuciyarta ta dinga raya mata kodai laifi tayi masa,qamshinsa daya nacewa hannunta ya dinga shiga hancinta,a ranar ta jima tana juyi kafin ta samu bacci yayi awon gaba da ita.
Washegari abokansu na unguwa da wajen aiki daidaiku suka dinga zuwa dubashi,abinda zai baka tabbacin yana da kyakkyawar mu'amala da jama'a,dole inna tasa bayan ya dawo daga makaranta,da zata dora sanwar dare ta qara mudu,ta kammale komai kafin magariba kamar yadda ta saba,ta shiga bandaki tayi wanka saboda zafin da ake dan tabawa,sannan ta shirya ta dawo falo wajen inna sukayi sallar magariba.
Tana saman abun salla tana dakon baqin da suka shiga dakinsu ya sadiq din su fita ta shiga ta dubashi,don da safe da zata wuce makaranta ta samu yana barci,data dawo tanata aiki ga kuma 'yan dubiya,abinda yasa wunin yau gaba daya bata ganshi ba kenan,duk sai takejin babu dadi,take kuma ji wani iri,kamar akwai nisa distance dake shirin shiga tsakaninsu kenan,ta lura tun daga sanda ta shiga js2 yayi bala'in sauyawa,ko wasa da dariya da zaman hira da suke ada yanzu babu kaso casa'in cikin dari,saidai kulawar da yake bata babu abinda ya sauya
"Naji hayaniyar ta ragu,ki leqa kikai musu abincin,nasan halin amin,indai yana ciwo bason abinci yake ba" tsam ta miqe tana gyara yafen mayafinta data yi sallah dashi,sannan ta nufi kitchen ta debi abincin tayi soro.
Da sallama ta cusa kai soron,wata baqauwar murya ce ta amsa mata,matasa ne guda biyu da zasuyi shekaru kusan daya dasu sadiq,daya na zaune saman daddumar da aka shimfida masa saman ledar dakin,dayan kuma na zaune gefan katifar sadiq.
Dan daburcewa tayi kadan saboda yadda taga sun zuba mata ido,sam bata saba cudanya da maza ba,uwa uba kuma ta zaci lamin da sadiq ne kawai a cikin dakin,saita taras da akasin haka
"Yana bandaki,yanzu zai fito" daya daga cikin samarin ya fada ganin yadda tayi turus,saita duqa a hankali ta ajjiye kwanukan,tana samun waje gefe daya ta tsugunna don jiranshi ya fito bayan ta gaidasu.
Shuru yadan ratsa a tsakani,daya daga cikin samarin da tun dazu yake satar kallonta ya fara janta da hira,da qyar take amsa masa tambayoyin da yake mata,qasan ranta haushinsa na kamata,don me zai dameta da wata hira,bayan ita ba itace ta kawota ba?.
Minti kusan takwas sannan ya bude toilet din ya fito,jikinsa da lema sosai,har jallabiyar daya sanya tana mannewa a jikinsa.
Da ita ya fara hada idanu,kowannensu ya janye idanunsa daga na dan uwansa,wani nauyi yau daya taji idanun nasa sunyi mata,rashin fara'arsa ta kwanakin nan gaba ta sauyashi,ta sanya tana jinsa kamar wani baqo a wajenta.
"Ya amin....barka da dare,ya jikin naka?" Sai daya gyada kai yana hadiye wani abu daya tsaya masa na haushi da takaicin junaid,saboda ya lura da irin kallon da yake binta dashi
"Da sauqi alhmdlh..... I hope kinje makaranta?" Yayi mata tambayar dai dai sanda sadiqu ke shigowa da lemukan fanta masu sanyi a hannunsa,sai maltina ta gwangwani guda biyu,dama abinda yaje siyo musu kenan,da zummar idan ya dawo yaje ya dauko musu abincin
"Naje yaya"
"Ma sha Allahu,qanwar saddiq ce da alama?" Junaid ya tambaya idanunsa a kanta yana washe baki,bata amsa ba saiya gyada kai,ta maida idanunta tana kallon yadin mayafin dake jikinta kamar ba bata ba
"Tubarakallah......kina aji nawa yanzu?"
"Js 3"
"Kune 'yan placement na bana ko?" Sai ta sake gyada masa kai kawai,don ta ankara da yadda ya lamin din yayi dif kamar baya dakin,hasalima man shafawarshi yake budewa zai shafa,saidai fuskarshi a dinke take tsaf
"Muje ki lalubi cokula ki bani" sadiq yayi saurin fada sanda junaid ke qoqarin jefa mata tambayar,abinda ya sanyata miqewa sadiq yabi bayanta,duk da hakan sai da junaid din yace
"Kaje ka dawo muyi magan.....ko mu fara da amin kafin ka iso" ya fada yana dariya dariya,daya dan saurayin yana tayashi,suna dan duban amin da suke zaton zai tanka,saidai baice dasu komai ba,hakanan yanayin fuskarsa na nan a dinke,abinda yasa ya musu kwarjini ya kasa maganar dashi,don dama tuni sun dade da sanin halinsu,tun suna 'yan qasa da shekara sha takwas,lamin din ba kowanne yayin magana da shirmen magana yake tankawa ba.
Har sadiq ya dawo da spoon din ya zuba abincin suka fara ci yanayinsa bai koma dai dai ba,yanajin sanda junaid din ke neman izini daga wajenshi ko sadiq din ya gana da iman,domin yace shikam ta gama yi masa,yadda yaketa kodata da yabata yasa wani abu yayi masa tsaiwar mashi a wuya,ya dinga jin kamar ya kai masa naushi a fuska,abinda ya sanyashi miqewa ya fice zuwa qofar gidansu ya zauna saman dakali.
Fayau yau qofar gidan yake,saboda kusan dukkan almajiran malam sun tafi ganin gida,sau biyu dama yake barinsu suje duk shekara ganin gida,su kuma dawo lokaci daya sanda ya sanya musu.
Iskar zafi na kadawa sosai ta wajen,sai ya jingina bayansa da ginin qofar gidan,ya lumshe idanunsa yana sakin ajiyar zuciya,saman harshensa yana jin wani daci daya tabbatar bayan na rashin lafiyar da yayi,harda mugun kishin iman din daya tsinci kansa a ciki.
Baisan ya akayi haka ba,daga jiya zuwa yau gaba daya iman din ta birkita zuciyarsa,sonta ya taso masa da wani irin qarfi da a baya bai taba jin makamancinsa ba,daga jiya zuwa yau kuma da abokansu wajen mutum hudu ke taya iman din sai yaji ya kasa sukuni,shigowarta na qarshe da daddare kawo musu abinci ya sanya yayi mata kallon qurillar daya tabbatar da cewa eh tabbas ta girma ta kuma fara zama budurwa.
Bai dauka cewa girma zai zowa iman din haka gadan gadan ba,duba da yanayin jikin fulani da take dashi,to ashe duk ganinta da yake cikim hijabi yasa yake wannan hasashen,girma da murjewa take ta ciki ba tare da an ankara ba,har ga Allah bazai iya fadan yadda ya dauki bashi itan da malam yayi da matuqar qima da daraja ba,saboda kima da mutuncinsu da yake gani,to amma ya sakawa ransa cewa bazai tunkari iman din da wata magana ta soyayya ba a yanzu,zaici gaba da bata kulawa ne kamar yadda suka saba a baya,har sai ta shiga ajin qarshe ko na kusa da qarshe na kammala secondary dinta.
Tun ba'ayi nisa ba ya gane akwai gyaran daya kamata yayiwa tarayyarsu,kamar yadda suke kusa da juna koda yaushe din nan ya kamata ya janye,ta dinga kallonsa a matsayin yaya da gaske,don tun farkon girmansa ya fuskanci cewa yana da wata dabi'a a halittarsa a matsayinsa na da namiji na yawan sha'awa,inda Allah ya taimakeshi me yawan kamewa ne shi,banda hakan......yadda 'yammata ke mutuwar sonsa.....iya cikin matan dake kawo musu dinki kawai,banda na 'yan ajinsu a makaranta,gefe guda kuma ga 'yan unguwa da sauransu,wannan ya sanya ya sake janyewa iman din,abinda yaketa bata mamaki kenan da taraddadin shin me tayi masa ne?,duk da cewa qasan ransa shima baijin dadin hakan,saidai hakan shine dai dai,kuma zai sanya nutsuwa a zukatan malam da inna,koda basu nuna masa hakan saman fuskarsa ba.
Tsakiyar tunaninsa yaji hayaniyarsu junaid suna fitowa,suka masa sallama ya amsa musu sama sama,ya bisu da kallo sanda sadiq ke taka musu zuwa bakin titi sunata hayaniyarsu irin ta samari,sai ya bisu da kallo har suka dan kaucewa ganinsa.
Ba jimawa yaga dawowar sadiq din,ya qaraso inda yake zaune ya dafa kafadarsa
"Tashi mu koma ciki,wajen na akwai sauro,ko gama warkewa bakayi ba kazo ka zauna ka baza masa jikinka yanata gutsira a banza" yunqurawa yayi ya miqe cikin qarfin hali yabi bayan sadiq din zuwa cikin dakin nasu.
Sunwa wajen kaca kaca kamar yadda akasan yanayin cin abincin maza samari yake,yana jin sadiq din ya buda murya ya fara kwadawa iman din kira,yasan kuma cewa zaiyi tazo ta gyara wajen ta kwashe kwanukan,sai lamin din ya dakatar dashi
"Dakata malam,kuturu ne kai da bazaka iya kai kwanuka ba?,ni idan na gama zan gyara wajen,daga yau ma banason ta sake kawo abinci indai akwai baqi a ciki,saidai idan kaine a ciki" waiwayowa yayi ya zubawa lamin din ido,ya karanci tsabar gaskiyarsa yake fada saman fuskarsa,sai ya saki murmushi ya dawo ya zauna gefan lamin din
"Duk da cewa bani na kar zomon ba....amma zan baka shawara,kada ka tsaya kallon ruwa kwado yayi maka qafa,diya mace duk yadda kake raina girmanta tasha kan tunaninka,kana mata kallon kamar tayi qanqanta da soyayya,ka gwada mata bayani kaga idan bata dauke karatun ba gaba daya,ni na rasa abinda ma kake jira,an maka kyauta an kuma baka dama amma ka tsaya wani tsari naka?,ka saka kai kawai,Allah ya bada sa'a" sadiq ya qarashe yana dukan kafadar lamin.
Yana cin abincin yana tattauna zancan shi da zuciyarsa,akwai kunya soyayya da yarinya tsakanin mahaifinta da mahaifiyarta,mutanen da yake musu kallon mahaifansa,abu daya ya yankewa ransa,zai fara bata kulawar data banbanta da irin wadda yake bata a baya,zai fara dafa zuciyarta da soyayya ba tare da ya furtata gareta ba,ta yadda da kanta zatayi dako ta kuma zaqu da ranar da zaya furta mata din,saiya saki wani murmushi wanda ya qawata fuskarsa data dan qara haske kadan sabida zazzabin da yasha.
*********Kamar kowacce rana da bata da makaranta asabar ko lahadi,yauma haka ta tashi tayi dukkan wasu aiki na gidan,kama daga shara wanke wanke da kuma dora karin safe.
Ta gama komai tas inna na daga rumfarta tana sallar walha,ta debo kayan data bata din zuwa bakin famfo nan tsakar gida,sannan ta koma kitchen tana goge duk inda ta bata din.
A nutse yake takowa zuwa cikin gidan,sanye da jallabiyyarsa da yake amfani da ita yawancin lokuta idan ba fita zaiyi ba,hannunsa riqe da ledar da mlam ya bashi ya kawo cikin gidan bayan sun gama karatun da sukeyi duk safiya da wurwuri bayan an tashi almajirai.
Kai tsaye ya isa rumfar inna da sallama,ya cire slipper dake qafarsa ya shiga.
Tana zaune saman abun sallah tana jan carbi,fuskarta ta wadata da murmushi sanda ya tsuguna a gabanta yana gaisheta,cike da kulawa ta amsa masa tana sake tambayarsa qwarin jikinsa,duk da cewa ya warware
"Alhamdulillah na warware ai inna,yau ma zan fita aiki in sha Allah"
"Ma sha Allahu,Allah ya qara lafiya"
"Ameen inna...ga wannan ledar,malam ne yace na kawo a dafa masa"
"Tana kitchen ai,saika miqa mata,kace kada ta cika masa yaji da yawa" innar ta fada bayan ta bude taga meye a ciki,ya amsa da to ya miqe tsam da ledar ya nufi kitchen din.
Ta bada hankalinta ga aikin da take sosai taga kamar inuwar mutum cikin kitchen din,abinda ya sanyata zabura kenan,ta waiwayo da sauri,har tsummar hannunta tana faduwa a qasa.
Idanu suka hada dashi,yana tsaye jingine da jikin qofar,ya zuba mata idanu yana binta da kallo,gabanta yayi wani mugun faduwa,kamar karo na farko kenan data taba ganinsa,cikin sanyin jiki ta duqa don ta dauke tsummanta tare da cewa
"Ya lamin.....ka bani tsoro" kusan a tare suka duqa din,shine ya samu nasarar dauke mata tsumman,suka dago a tare,idanunsu ya fada cikin na juna,yadan ja baya kadan saboda sunyi kusanci da yawa,ya miqa mata yana ci gaba da kallonta tare da cewa
"Dama can matsoraciyar ce" idanunta ta janye daga nasa,saboda nauyin da taji zuciyarta nayi,qamshin turaren jikinsa yana busowa zuwa cikin kitchen din,kai bakace baiyi wanka ba,tsabar abotarsa da turare ne kawai,yayi wani fresh 'yar cutar da yayi kwana biyu,sai sumar kansa dake adan hautsine saboda bai gyara ta ba,daga sallah makaranta suka zauna kawai,hakan kuma sai ya qara masa kyau.
"Yaaa banfa zata ba" ta fada da salon shagwabar data saba masa magana a baya,sautin muryarta yaji ya tabashi,ya kuma saukar masa da kasala,ya sauke boyayyar ajiyar zuciya,tare da dora ledar hannun nasa kan kantar da take gogewar
"Barka da safiya yaya,ya jikin naka?" Ta furta tana kaucewa kallonsa,saboda wani yanayi da takeji duk sa'ar data kalleshin
"Alhamdulillah,na warware.....gashi nan,malam yace adafa masa,inna tace karki cika yaji da yawa" a marairaice ta waiwayo
"Yaaya,na gama komi fa,Allah saura wanke wanke,kwanciya nakeso nayi" yadda tayi masa maganar ya sake tafiya dashi,sai ya harde hannayensa a qirji ya zuba mata idanu harta gama,duk da bashi take kallo ba,amma tanajin idanunsa a kanta
"Yanzu idan mijinki yace yanason ki dafa masa abu kamar haka hakan zaki ce?" Banbarakwai taji maganar tasa,fa waiwayo da sauri sai taga ita yake kallo,fuskarsa ta wadata da murmshi
"Inna na miki haka ne saboda tanason ki gina gidanki da kulawa,ki shagwaba mijinki da soyayyar da zatasa ki tsaya masa a zuciya" wata irin kunya ce ta rarrafo ta rufeta,saboda yanayin yadda yake mata maganar kawai ta sanya taji kamar qasa ta tsage ta shige,wannan kuwa ya lamin dinta ne?,magana yake mata da wani irin sound da bata sanshi dashi b,wani irin kallo na daban da sexy eyes dinsa,gaba daya taji kaman ya zare mata laka,sai ta juya tana ci gaba da aikin a hankali,kunya na nuqurqusarta.
Bata ankara ba har ya dauki kwanon dake kusa a ita ya juye kifin a ciki yana cewa
"Tunda raguwa ce ke bari na tayaki" tare suka dawo tsakar gidan,tana wanke wanke,shi kuma yana gyara mata kifin,gaba daya sai ta jita cikin wata takura da bata taba jin irinta ba tsakaninta da lamin din,saboda duk wani motsi ko daga kai da zatayi saita samu tagomashin wani kallo da ta kasa farrasa na meye?,saidai yana sanya zuciyarta karyewa da kuma yin laushi.
Ya sakankance sosai abinsa,yanata aikata mata da kallon da yake da tabbacin zai wuce kai tsaye zuwa cikin zuciyarta ne yayi masauki me kyau,koda bai furta komai a gareta ba,baya da fargaba saboda inna tace zata shiga tadan kwanta,malam kuwa yayi baqi a waje,wanda yasan yawanci idan sukazo sukan dauki awa biyu tare kafin su tafi,sadiq kuwa baida matsala dashi,shi ba baqonsa bane bare yaji kunyarsa.
Kusan tare suka gama komai da ita,sannan ya wuce dakinsu bayan ya sanyata ta saka masa ruwan wanka.
*HILTI UNISEX CHOCOLATE*
*_chocolate ce ta musamman daga qasar TURKEY_*
*_Maganin matsalarki hajiya keda mai gida cikin tsari babu yane yamen magunguna_*
*Ki tuntubi wannan number don k'arin bayani*
08184017452[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 07
*_ZAFAFA 5 NA MIKA GAISUWAR TA'AZIYYA ZUWA GA MARUBUCIYA UMMY AISHA, TA KUNGIYAR HASKE WRITERS ASSOCIATION, BISA GA RASHI NA MAHAIFIYAR TA DA TAYI. MUNA FATAN ALLAH YA JIKANTA DA RAHAMA, YA GAFARTA MATA, YA KUMA BASU HAKURIN WANNAN BABBAN RASHI AMIN._*
__________________________________
_SAKINA VENDIBLES_
_SAKINA VENDIBLES_
_SAKINA VENDIBLES_
_(INDE HARKAR TURARUKA NE MASU KAMA JIKI DA GIDAH KAI HARDA TSUGUNNO. SAKINA VENDIBLES ITACE KAN GABA)_
_SUNA DA KAYA INGANTATTU MASU MATUKAR KYAU AKAN FARASHI MAI RAHUSA.)_
_KINASON ASAN KIN ISA MACE? WADDA ZAKUYI GOGAYYA DA MASU SAKA DESIGNER TURARE AMMA KI FUSU KAMSHI? DUK INDA KIKA GIFTA ASAN EH. KEDIN TABANCE , KIN ZARCE SAURAN MATA)_
_AKWAI KHUMRAH WHITE AND BLACK_
_KULACCAM BLACK (FOR HAIR( AND WHITE FOR BODY_
_WASU DAGA CIKIN KAYAYYAKIN MU SUN KUNSHI👇_
Turaren wuta list*
Queens special
Kajiji mix
Kajiji whole
Gabgab
Brown Hawiii
Special Halut
Sandal balls
Sandal strips
Sandal flakes
Dubai oud
White Hawii
Classy Dufr
Black bange
Black bange
Musky Dorrot(Na tsuguno)
Cous cous
*_DA SAURAN SU DA YAWA_*
*_Handles_*
*Instagram* @sakina_vendibles *Facebook*
@Sakina vendible *Tiktok*
@Sakina vendibles_
Tsaye take gaban mudubin nata tana karanto addu'o'i,bayan ta gama shirinta tsaf na tafiya makaranta don zana jarabawar placement,kamar kullum,tayi kyau cikin uniform din da a kullum idan ta saka zaka dauka ta sanyashi ne da nufin gayu ko ado,saidai sam ba haka bane,qirarta ce,haka Allah ya yita,fatarta na daukar kowanne irin nau'in dressing.
Lokaci daya gabanta ya dan fadi,ta kuma lumshe idanunta sanda ta jiyo muryar ya al'amin yana tambayar inna bata fito ba,wannan wani baqon yanayine da bata jima da tsintar kanta a ciki ba,a duk sanda zataji murya ko motsin ya al'amin din.
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana wara idanunta da suka dauki mintuna a kulle sanda ta tsinci muryar inna tana kiranta,cikin yanayi na me kama da me alhini ko tsoron haduwa da ya al'amin din ta zura takalmanta half cover masu kyau,wanda al'ameen dinne ya siya mata,kamar yadda fiye da rabin komai nata da take amfani dashi na rayuwarta.
Dashi suka fara hada idanu sanda ta fito tsakar gidan,saita sauke idanunta daga kanshi da hanzari saboda yanayin kallon da ya jefeta dashi,wanda shi kansa baisan yayi ba,tayi masa kyau sosai yau din,duk da ya saba ganinta amma yau din kamar an qara mata girma da shekaru,itama cikin ranta take tadinshi,yayi wani kyau cikin shadda light blue daketa qyalli,bisa alamu sabuwa ce kar,yau ya fara sanyata,hakan kuma baya rasa nasaba da daurin auren dan abokin malam din da zashi,wanda malam dinne ya wakiltashi yaje,saboda a jiya shi ya wuce Niger,can dangin inna da akayi mata rasuwa zai musu gaisuwa.
Ko kadan bata zargi kanta kan yadda takejin sauyi da baqunta tattare da ya al'amin din ba,saboda ita kanta tana ganin kamar shima ya sauya,kallo da yanayin firarsu gaba daya ya canzata,bata saba jin nauyinsa ba idan suna hira a baya,tana hira dashi kamar yadda takeyi da ya sadiq,amma a yanzu tanajin akwai wani banbamci a tsakaninsa da ya sadiq din.
Tana qoqarin gaidashi inna ta fara mata fada
"Kinsan yana jiranki zaki shiga ki zauna....."
"Innaaa.....bansan lokaci yayi bafa....girkin nan shi ya cinyemin lokaci" ta fada a shagwabe kamar yadda ta saba,boyayyen murmushi ya kubce masa,abun ya zame mata cikin jininta,ta saba maganarta a haka,abinda ke sake daukan hankalinsa dangane da ita kenan,duk da yana qoqarin boyewa da kuma dannewa
"kaima duk da kai aminu,da tafiyarka,tasan hanya ai,ta tafi da kanta"
Baice komai ba,yadan saki sassanyan murmushin nan nasa,sannan ya matsa inda ta hada komai nata ya sanya hannu ya dauka yana fadin
"Mun wuce inna,daga wajen daurin auren shago zan wuce"
"Ba zaka dawo ka karba abin karin naka ba" sumarsa irinta buzaye daketa qyalli ya shafa da hannunsa
"Ina da ayyuka da yawa ne inna.....akwai dinkin wata amarya da nake,nace mata tazo jibi ta karba,banaso tazo ban gama ba" kai inna ta gyada,ta sanshi da matuqar qoqari wajen cika alqawari,mutum ne shi kaifi daya,mai matuqar qoqarin ganin ya cika alqawari,sam bashi daga cikin jerin layin teloli
"Haka ne,to Alla ya dafa ya tsare mana ku,sai kun dawo"
"Ameen inna" suka amsa gaba dayansu,sannan ya sanya iman a gaba suka fice.
Cikin jikinta take jin kunya nauyi da kuma wani irin yanayi,yayin da shi kuma tunaninsa yayi nisa game da yadda zai tafiyar da koma a tsakaninsu bisa tsari da tsafta,tafiyar sai tazo da sabon salo,saboda ba haka ya saba rakata zana jarrabawa ba,sau biyu tana satar kallonsa,ya ganta sarai,amma sai yayi kamar bai ganta din ba,har zuwa sanda sukayi tsaye a bakin titi suna jiran abun hawa,daga layin cikin layin da yake facing dinsu,wata mata dake sanye da uniform fari da ash,wanda hakan ke alamta ma'akaciyar jinya ce wato (nurse) take tunkaro bakin titin,dukkaninsu sun ganta,har zuwa sanda ta iso titin daga daya tsallaken ta tsaya
"Kamar haka nakeson ganinki.....ina miki sha'awar karatun jinya,ina miki sha'awar ilimi me zurfi"muryar al'ameen wadda ta fara cika da amo na mazantaka a 'yan watannin nan ta ratsa kunnen iman din.
A hankali ta daga kanta ta sanya dubanta ga matar,tun ba yau ba dama ta sani wannan shine burin al'amin din a kanta,ta dade da haddace hakan,kusan kowa a gidan ya sani,don haka sau tari idan suna irin wannan hirar ma babu me ce musu uffan,tsakaninsu ne
"Kiyimin alqawarin zaki cikan wannan burin" cikin mamamki kalamansa ta daga idanu kamar zata klalleshi amma kuma ta kasa,saboda tuna yadda take ji,da kuma yadda idanuwansa ke mata nauyi yanzun a jiki da zuciya
"Bake da kula kowanne irin saurayi,bake ba soyayya" lafazin nasa ya ratsa ta tsakiyar tunaninta ya katse mata shi shi wani sauti mai taushi kuma qasa qasa.
Wata irin kunya ce ta dirarta mata,ire iren maganganunsa kenan da suke caza mata kai,da kuma sake sanyata jin kunya da nauyinsa,maganganun da a baya baya mata su,tadan sadda kanta qasa,qaramin murmushi yana qwace mata
"Eh,wannan ce hanya daya da zaki taimaki cikar wannan buri nawa,ki bari,idan lokaci yayi,ni zan zaba miki ɗanɗasheshen miji da zai dace dake" qarasa rufeta kunyar tayi,sai ta kare fuskarta da hannunta tana cewa
"Ni ban kula kowa ya al'ameen,kuma ma waye zai kulani nima?,dubeni fa?" Murmushi ne ya qwace masa sanda ya saka hannu yana tsayar musu da wata adaidaita sahu sannan ya bata amsa
"Kina da kyau imani....ke kyakkyawa cw ta ajin qarshe ko farko zance,irin kyan dake jan hankalin kowannw namiji....wanda ke ba zaki gane hakan ba,amma a taqaice,ke sarauniya ce" wanda tun daga ranar ta samu sunan queen daga wajen al'amin,sunan da ya koma kirata dashi lokaci lokaci,musamman idan ya zamana babu malam ko inna a wajen,don ta sadiq dama ya maidashi kamar wani kakansa,ba wai kunya ko nauyinsa yakeji ba,yayin da sunan ya tsayewa iman,yake kuma matuqar yi mata dadi,zuciyarta nata mata saqe saqe akan al'amin din,me yasa ya canza?,me yasa yanzu yake tsaye mata a rai?.
Cikin guntar karatun litattafan hausa data fara a boye ya samu amsoshi da dama,saidai kuma har yau bai furta mata ina sonki iman ba,to hakan meyake nufi?.
*******. ******. ********
Tun dazun data zauna a wajen hankalinta yake rabi da rabi,daya a wajen,daya kuma ya karkata kan jinkirin shigowar al'amin gidan yau,sau biyu tana tura almajiran gidansu suna gano mata rumfar karatu ko yana wajen malam sai ace mata baya nan,tunda ta gama ayyukanta tayi alwalar magariba ta shimfida musu tabarma ita da inna a nan wajen sukayi sallah take saka ran shigowarsa,amma shuru kakeji,gashi har qarfe tara na dare na haramar yi,har sadiq ya shigo yaci abincinsa ya sake fita.
Ta gwada kiransa ta wayar inna kuma sau uku ana ce mata a kashe wayar take,har inna dake jin radio ta rage sautinta tana jajjabin rashin shigowar tasa,wanda bata sauke ba sai ga sallamarsa.
Wani boyayyar ajiyar zuciya da batasan daga inda ta taho ba iman din ta sauke,shi dinma koda ya shigo idanuwansa suna kanta,ta miqe a kunyace a kuma nutse tana gyara daurin dankwalinta tare da qoqarin yi masa sannu da zuwa tana yunqurin karbar ledojin hannunsa
"Yauwa Queen" ya furta qasa qasa yadda innar ba zata jiyo ba,saita saki murmushi tana dora kayan saman daddumar data tashi a kai,inda shi kuma ya qarasa yana zama a kai tare da yiwa inna barka da gida,ta miqe daga kwanciyar da take tana amsa masa tare da tambayarsa dadewar da yau yayi,har tana shirin tura sadiq ya dubosa.
Murmushi yayi yana jin dadin yadda har kullum inna ke nuna masa qauna da soyayya irinbya da da uwa
"Aiki ne yau ya riqeni inna,ban gama musu ba,kuma gobe zasu shigo da safe su karba,na katse ne na shiga kasuwa,shi yasa dinkin ya kaini har dare" jinjina kai inna tayi,tana sake jin qaunar al'ameen din cikin rai da zuciyarta,har kullum shi mutum ne dake sanya cika alqawari gaba da komai a rayuwarsa,ya tsani saba alqawari
"Sannu da qoqari,Allah yayi jagora"
"Ameen inna" .
Iman na daga kitchen tana qoqarin hado masa abincinsa tare da dora masa ruwan wanka take jiyo hirar tasu,ta hada komai a nutse a kuma tsaftace kamar yadda inna ta horar da ita ta fito dashi zuwa inda yake zaunen.
"Sannu da aiki autar inna" ya furta cikin kulawa,ta saki murmushi bayan ta duqa ta aje a gabansa
"Kinga bar abincin nan,zo kiga.....siyayyarki ta tafiya nasreen memorial academy" sosai maganar tayi mata ba zata,makarantar da inna ta kusa dukanta a kanta,saboda yadda ta nace ta kafe tanason makarantar,ita kuma inna ta haneta da zancanta,saboda private school ce da duk term ake biyan kusan dubu goma sha biyar,innan kuma tasan matsawar alamin din yaji tofa sai ya kaita,shi yasa ta sanyata a daki ta ja mata kunne,koda ta sanarwa malam murmushi yayi
"Bansan ko tabarar auta ke damu hajar ba,banda haka.....yaci ace wasu abubuwan zuwa yanzu tafara ragewa,yaron nan hidima da kuma bautar da yake mata ko ciki daya suka fito iyaka kenan,kinyi dai dai,taci gaba da zuwa ta gwamnatinta yadda ta saba,tunda ita takeyi tun tasowarta,kuma tana da basirar gane abubuwa,gashi lafiya lau komai ke tafiya"
Laqwas jikinta yayi sanyi sanda yake fiddo siyayyar da yayi mata yake kuma shaida mata sati me zuwa zata fara zuwa,an gama koma,idanunta suka ciko rau rau da qwalla tana satar kallon inna,tana tsoron kada tace itace ta tusashi gaba ka dole sai ya kaita,ko kuma ita ta gaya masa zabinta.
Ta bangaren innar ma jikinta sanyin yayi,wane irin yaro ne al'ameen din?,ta tabbatar yinin da yayi har dare a shago kudin wannan siyayyar ya hada ya kashewa iman din gaba daya,tabi kayan da ya zazzage din da kallo,litattafai ne tari guda, school bag,takalmi me kyau da 'yan makaranta,biruka da pencils,hatta da uniform din makarantar gashinan a dinke a goge sai sanyawa kawai.
Fada sosai inna ta rufe iman dashi,wannan karon harda al'amin din,kan me yasa zai dinga biyewa iman din da duk abinda tace tana so,ita din 'yar wace da bazata ci gaba da zuwa makarantar gwamnati ba,kamar yadda saura suke zuwa?.
Sosai yaji babu dadi saboda kukan da yaga iman din tanayi,saida inna ta soma sassauta fadan sannan ya mata magana cikin kwantar da kai,yana mata bayani zafa fahimta banbamcin karatun makarantun gwamnati da kuma da na kudi,tare da nuna mata shima yana sha'awar ya canza mata makaranta dama,bawai ita ta sakashi ba,ya dade yana wannan tanadin.
Saida inna ta tabbatar ba iman ce ta tursasashi ba sannan ta fara saukowa,saidai duk da haka bata bar mita ba
"Yanzu kai da kake da nauyin 'yar uwarka a ka,ga naka karatun,sanna kuma ka dauka duk wata lalurar iman ka rungume?" Murmushi kawai ya sake
"Ba komai inna,Allah zaiyi,mudai aci gaba da yi mana addu'a.....sannan don Allah inna karki sake cewa komai sadiq yaji" ya fada da sauri,saboda jin muryar sadiq din dake shigowa da sukayi,kuma yaga reaction na fuskar iman,yasan sadiq din dan hada waje ne,maimakon ya gyara saidai ma ya bata,saidai duk da hakan daya shigo shima sai daya tofa albarkacin bakinsa,magana dai bata mutu har shigowar malam,shine ya yayyafawa abun ruwa,ya sanya albarka a ciki,ya kuma ja kunnen iman,sannan ya kebe da al'amin din bayan kowa ya tashi ya basu waje.
"Yanzu kai malam al'ameen haka za'ayi dakai?" Cikin fargabar ko wani laifi ya yiwa malam ya daga kai ya dubeshi,malam din ya fahimci abinda ke yawo saman fuskarsa,sai ya saki murmushi
"Kai da zaka zama magidanci nan gaba,haka zaka zauna sai abinda takeso zakayi mata?,shifa namiji kullum so ake ya zama tsayayye,yana da kyau a dinga bawa mata dama kan raayi da zabinsu,amma kuma bafa akan komai ba,qarqashinka zata zauna nan gaba kadan,to dole tun yanzu ka dinga azata akan tsari da tafarkin da kakeso ta kasance akai" cikin hikima malam din ya dinga nusasheshi,daga bisani kuma suka fada hira,wanda wannan ba sabon abu bane dama tsakaninsa da malam din ba,sunawa juna kallo da da mahaifi ne.
Ya jima yana nazari kan maganganun malam,su suke ganin kamar yana biyar son ran iman dinne,wanda sam shi ba haka bane,duk abinda yakewa iman....tun kafin ya soma jinta da wani matsayi daban a cikin zuciyarsa kawo yau,yana mata ne saboda ta cancanta ta kuma dace yayi mata hakan,sau tari kuma zabu da ra'ayinsu ana samun arashi yana zuwa daya,iman din ta dabance cikin rai da rayuwarsa,duk da yana ganin abubuwa sosai tattare da ita,ita dinma kamar ta canza,amma nan gaba kadan zai qarasa bude mata komai,yana son yabi komai ne bisa tsari na hankali da dacewa,da wannan ya kwanta a ransa.
*ZAFAFA BIYAR 2022*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKANFARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA_
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 08
*_LITTAFIN KUDINE,ZAKI IYA TUNTUBAR WADAN NAN NUMBERS DIN DON SIYAN NAKI_*
09032345899
Ko kuma
09166221261
_______________________________
Misalin takwas da rabi na safiyar ranar litinin din,zaune take saman doguwae kujerar dake falon principal din nasreen memorial academy,tayi neat cikin shigar uniform din makarantar da shima ya karbeta fiye da makarantar data baro,idanunta sunyi narai narai tana kallon al'amin daya miqe yana sallama da principal din,bayan sun gama komai shi da sadiq sun damqata ga hannun hukumar makarantar,baqunta take ji sosai cikin wannan makarantar,tamkar yau ne rana ta farko data fara zuwa makaranta,al'ameen ya waiwayo a nutse ya sanya hannunsa a aljihun wandon lallausan yadin jikinsa da iya tsahon rigar ya tsaya a gwiwarsa,ya ciro 200 ya miqa mata
"Idan ba zaki iya komawa gida ba ki jirani na dawo,sai na maidake" hannu tasa tana amsa
"Zan iya yaaya" ta amsa mishi a tausashe,principal din yayi murmushi
"Wannan qanwar taka da alama kana ji da ita" ua fada cikin salon barkwanci,sai al'amin ya waiwaya ya dubeshi sannan ya saki murmushi
"Auta ce"
"Oh....i see" ya sake sakin murmushi ya musu sallama yabu bayan sadiq suka fice.
Tana zaune nan tana rarraba idanu,har principal din ya kira daya daga cikin masu goge goge dake aiki a makarantar,tayi masa kiran Assistant monitor din ss 1,ba jimawa ya dawo yace tana zuwa.
Ba'a rufa minti biyar ba tayi sallama,cikin nutsatsiyar muryarta,tana sanye da uniform irin na iman din,iman din ta bita da kallo,tana da haske saidai baikai nata ba,tana da madaidaicin kyau,a qiyasce shekarunsu zasuyi daya da ita
"Ga new student nan,ayi mata seat,sannan a shigar da sunanta cikin register"
"Okay sir" ta amsa a ladabce,sannan ta waiwaya zuwa sashenbda iman ke zaune.
Suna hada idanu ta sake mata murmushi,saita soma takawa zuwa inda take din tana dubanta,har yanzu kuma murmushin bai bar kan fuskarta ba,ta duqa ta dauki hand bag din iman din tana cewa
"Taso muje" saita miqe tana dan jan rigarta tabi bayan yarinyar.
Tare suka jera cikin yanayin baqunta,saita waiwayo ta sake sakar mata murmushi
"Sunana munira hasan......nice assistant monitor na ss 1,monitor dinmu namiji ne.....kefa,meye sunanki?"
"Hajar ibrahim khalil"
"Yadda kike da kyau haka sunanki yake da dadi" munira ta fada tana sakin murmushi gami da kallon iman.
Martanin murmushin iman din ta maida mata tana cewa
"Na gode" sukaci gaba da takawa,maganar muniran na maimituwa a ranta,sai ta sanya hannu ta shafi fuskarta a fakaice,an jima ana fadin ita me kyau ce,saidai ita bata taba ganin kyan ba a karan kanta,hakanan bata taba baiwa maganar wani muhimmanci ba.
Kai tsaye munira ta kutsa kai cikin ajin,wanda ya dauki shuru,kowa ya bada hankalinsa ga allon da malamin dake tsaye yaketa cikashi da rubutu daliban suna kwafa suna mayarwa zuwa ga litattafansu. Sallamarsu sai taja hankalin kowanne dalibi dama matashin malamin dake tsaye gaban allo,ta qarasa daura da malami tana cewa
"Sir,sabuwar daliba ce inji principal,yace a saka sunanta cikin register" kai ya gyada gami da cewa
"Okay"idanuwansa nakan fuskar iman,wadda ta fara jin wani iri,saboda yadda idanuwa sukayi mata caa na dalibai maza da mata,musamman ita da banda primary data yi da maza lokacin bata da wayo, junior dinta ajinau mata ne zalla,kasancewarta government school
"What is your name?" Malamin ya jefa mata tambayar da harshen nasara,cikin sassanyar muryarta data sake janyo mata idanuwa ta amsa masa,sai ya jawo register din kusa dashi ya rubuta sunan,sannan ya bawa munira umarnin tayi mata wajen zama.
Kai tsaye seat dinta ta matsa mata,saboda tsarin zaman duk seat daya mutum biyu yake dauka,da su biyu ne akai ita da qawarta,to bayan an shiga sabon term sai aka canzawa qawartata makaranta,hakan ya sanya take zaune ita daya,saboda ba da kowa ita din take jurar zaman ba.
Ranar farko a makaranta ga duk sabon dalibi rana ce dake cike da baqunta da rashin sabo,kusan hakan taso faruwa ga iman,saidai kuma kirkin munira ya hana hakan faruwa,saboda janta data dinga yi da hira,koda aka fita break tare sukayi break din,aka dawo suka zauna a seat dinsu,tana ta bata labaruka da suka danganci makarantar da yadda take,har zuwa lokacin da aka kada bell an tashi kenan,iman din ta saba jakarta tana nufi qofa bayan ta yiwa munira sallama.
A qafa ta fara takawa sabida tadan qara gaba inda babu cunkoson dalibai sosai,tana tsaka da tafiya taji muryar munira na kiranta,saita dakata ta kuma waiwayo suka hada ido,kowa ya sakarwa dan uwansa murmushi,ta dakaci muniran har ta qaraso inda take,suka jera sukaci gaba da tafiya tare,kafin daga bisani muniran tace
"Ya na ganki kina takawa a qafa?" Waiwayawa iman tayi tadan dubeta cike da mamakin tambayar tata,to ame takeson ganinta?,kamar taji tambayar da ta yiwa kanta sai ta dora
"Ko mai daukarki ne bazai samu zuwa ba?,ranar farko a makaranta kuwa ai bai kamata ya barki kiyi tracking ba". Sai yanzu ta fahimci zancanta,saita murmusa
"Dama can motar haya nake hawa,saidai wataran idan hanya ta biyo da yaa al'ameen ta qofar makarantarmu ya jirayeni mu koma gida tare" kai munira tadan jinjina,tana cike da mamaki,saboda kallon farko data yiwa iman,ta mata duba ne na yaran da suka fito gidan hutu,sam kyan qira da dirin da Allah ya bata tayi zubin gidan yaku bayi ba,ta tsammaci zata ga wata shimfidediyar mota tazo daukarta ne,saita aje tunanin nata tana tambayar iman din unguwar da take.
Sanda ta gaya mata idanu ta fiddo
"Ai bamu da nisa da juna,abun hawa daya zamu hau,tunda nima yau shuru ba'azo daukata ba" ta fada tana saka hannu tana tsayar musu da adaidaita sahu,suka masa bayani suka shige,iman din na qoqarin neman ragi kan kudin da ya gaya musun,amma sai taga muniran bata damu da price din da ya fada ba,don haka itama sai tayi shuru kawai.
Suna tafe muniran na jan iman da hira,a dan zamansu na awanni iman din ta fuskanci muniran kamar daga gidan masu dashi ta fito,koma ba haka ba to tabbas gidan data fito sunfi nasu wadata,tadan saki jiki kadan da ita tana biyewa hirar tata,har aka kawo inda muniran zata sauka,wanda daga nan zuwa gidansu iman baifi naira 20 ba kudin mota.
Kudin da ya buqata munira ta ciro ta biya musu,iman zata doje tayi gaba abinta bata tsaya ma sauraren qorafinta ba,mai adaidaita yaja sukayi gaba,cikin ranta kafin su qarasa gida tana ta yaba kirkin muniran da karamcinta,azamansu na wasu taqaitattun awanni.
A dan gajiye ta shiga gida,saboda akwai qaerin lokacin tashi kadan a wannan makarantar kan makarantar data baro.
Da sallama ta kutsa tsakar gidan nasu qarfe biyu da rabi da minti biyar,inna dake duqe tana baza masarar data wanke don ta samu tasha iska akai niqa ta dago tana amsa sallamartata,idanunta akanta,ta sabule jakar bayanta ta zauna saman kujera 'yar tsuguno tana dan goge zufar goshinta tare da yiwa inna sannu da gida
"Yauwa,an taso kenan?" Ta fada tana juyawa zuwa ga aikinta
"Wlh inna,duk na gaji,makarantar tafi waccan nisa"
"Ah to,aishi sa kai yafi bauta ciwo" tasan mita sarai inna zata dorar,don haka ta saki dariya kawai ta miqe tana daga jakarta
"Amma inna karatun da ake mana a waccar makarantar baiko kama qafar rabin na wannan makarantar ba"
"To Alla ya taimaka" ta amsa mata.
Kamar zatayi gaba sai kuma ta dakata
"Inna ya al'ameen bai dawo ba?"
"Tunda ya fita dai bai shigo ba" saita daga hannunta duban fuskar siririn agogon silver dake hannunta tana duba lokaci,wanda yau ta fara sakashi,kuma al'ameen dinne ya siya mata saboda makarantar
"Amma dai inna ba tuwo zakiyi ba"
"Zanyi ko zakiyi?" Kai ta gyada cikin salo na zaquwa da son jin amsar innar
"To zanyi inna"
"Bashi bane maqiyar tuwo.....dambu nakeso wai nayi" sai fuskar iman din ta dan saki,don ita gaba ce tsakaninta da tuwo,tunda taji batun dambu kuwa,tasan saboda malam da al'ameen za'ayishi,don haka tayi damarar zagewa tayishi yayi kyau yayi dadi ko don al'ameen din,tana matuqar jin dadin yadda yake yaba mata idan tayi girki,da yadda yake nuna jin dadinsa,koma bayan sadiq dake kusheta,wani lokaci har sai malam ya shiga sannan zai qyaleta,duk da shima yana yine kawai saboda tsokana,bawai don bata iya din ba,don ta fannin girki inna ta yarda da ita dari.bisa dari,tun tana da shekara takwas innar ta fara shiga madafa da ita,tana da shekara sha biyu kuwa ta sakar mata girkin,saidai ta dinga tayata ko duba mata,zuwa yanzu kuwa da ake magana fa gama zama cikakkiyar qwararriya.
Ruwa kawai ta watsa tadan tsakuri abincinta kamar yadda ta saba ta fito ta kama aikin,yau dama babu islamiyya,anyi bikin yaye wasu dalibai da suka sauke alqur'ani,don haka aka basu hutu,wanda ida an koma su iman dinne 'yan babban aji,duk da ita dama already tana biyo bayan duk inda aka biya matan da hadda wajen malam,wani lokaci kuma idan abubuwa sunwa malam din yawa al'ameen ya karba mata.
Cikin karsashi da kuzari take aikinta,tana yi tana yiwa inna surutun makarantar,wanda ada al'ameen din ta tarawa labaran,saidai tasan ba lallai ta sake ta bashi labarin sosai ba,sabida kaifi da nauyi da idanuwansa a yanzu suke mata,ta rasa dawa kuma zata tattauna wannan,qawarta daya a unguwarsu,to itama takan jima basu hadu ba saboda yanayi na karatu da kuma tsarin tsaron fita a gidan kowannensu,saidai tanata timing da sanya lokacin da zata fita taje susha hira da ita.
Ganin ta kammala hada komai,dambun ya hau wuta,kuma tsakar gidansu babu kowa,saita debo 'yan qananun brassier dinta da ta fara amfani dasu a boye ta zuba a botiki ta zauna daga bakin famfo,wanda yake daura da qofar shigowa ta fara wankesu.
Ta jima tana ajiyarsu,tun wani lokaci da sukaje nijer,anty raheena 'yar uwar inna ta bata tace ta ajjiye zasuyi mata amfani,bata aminta da hakan ba sai sanda amfaninsu ya taso mata,ta rasa wanda zata gayawa tana buqatarsu.
Babu irin wannan hirar tsakaninta da innarta tun farko,ya alameen din nata kuma koda wasa ba zata iya tunkararsa ta gaya masa tana so ba,sai ta tuna da ajiyarta, doon haka ta debo abunta ta fara amfani dasu hankalinta kwance,amma tanata boye boye,don sai irin haka gidan babu kowa take wankesu ta shanyasu a bayan qofar dakinta,ko idan ta shiga wanka.
Tana wankesu tana dan rera karatun qur'ani da tausashiyar muryarta mai cike da sanyi nutsuwa da kuma tashen 'yammatantaka.
Daidai lokacin da al'ameen wanda kansa ke ciwo ya shigo cikin gidan,tun daga soro yayi sallama kamar yadda ya saba,saidai muryarsa bata da wani qarfi me yawa saboda gajiya da kuma ciwon kai,wanda ya tabbatar stress ne na dinki.
Sam bataji shigowarsa ba,kamar yadda shima ya ganta bagatatan a farkon qofa,don sam bai kawo samuwar wani mutum zaune a wajen ba.
Saman fuskarta ya fara sauke ganinsa,ta langabe kanta gefe guda,qaramin bakinta me dauke sa jajayen labba yana motsawa a hankali,sautin karatunta yana fita da kadan da kadan,gefan da kanta ya karkatan jelar manyan kitso guda hudu dake kanta sun kwanto ta nan har saman qirjinta.
Tayi masa kyau ainun,fuskarta da maqerin budurci ke aikinsa a kanta tayi wani fresh tare da annuri na daban,saiya lumshe idanunsa qirjinsa yana bugawa,wani abu mai sanyi da qarfi da girma ya tsaga qirjinsa ya sauka saman zuciyarsa,ya tabbatar wani feeling ne me cike da soyayya da kuma qauna ya saukar masa,sai ya bude idanun nasa yana saukesu zuwa ga abinda take wankewar.
Idanu ya qurawa brasssier din nata yana mamakin yaushe ta fara amfani dasu,qaramin murmushi ya qwacewa fuskarsa,ya sani tunda can tana da yawan zama da hijabi cikin gidan,to amma kwanaki yaji yadda inna ke qorafin bata cirewa ko cikin daki tasha iska,wala'alla yana da nasaba da hakan?.
A firgice ta dago sanda taji sallamar mutum saman kanta,a zabure ta miqe saboda ba zatan ganinsa,har tana fatali da ruwan wankin da abebaden dake ciki tayi dakinta da gudu,sai ya bita da kallo,dariya ta qwace masa,ya duqa a hankali ya kwashe mata abubuwanta da hannu daya ya maida ga botikin,sannan ya tako zuwa cikin gidan yana aake jaddada sallamarsa,inna dake can uwar daki ya fito zuwa rumfarta tana amsa sallamar,saiya taka a hankali zuwa rumfar innar yana cire takalman qafarsa,rabin hankalinsa na ga dakin iman din data turo qofar ya murmusa ya shiga rumfar innar.
*_HILTI UNISEX CHOCOLATE STILL AVAILABLE, GRAB YOURS NOW,DAB TAKE DA QAREWA_*👌🏽👌🏽👌🏽👌🏽
08184017452
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 09
*Game buqatar biyan kudin zafafa biyar,zai iya tuntubarmu ta wannan number*
09032345899
Ko kuma
09166221261
__________________________________
"Tunda ta shigo ta fara tambaya da cigiyarka,nasan kuma labarine kawai cike taf da bakinta zata baka na makaranta" inna ta fada mishi bayan sun gaisa,tana ninke abun sallar data bari a wajen ta gashi ta shiga ciki,murmushi ya sake yana dan shafo kansa,yana funa dramer dinsu ta yanzu yanzu
"Aiki take tayi ai inna,na dauka yau zata huta sabida gajiyar sabuwar makaranta" dan satar dubansa kadan inna tayu,duk sanda ya nuna wata kulawa kan iman din hakan namata dadi qwarai,kuma dama shi ba baqon abu bane a wajensa,tana da tabbaci da yaqinun diyarta qwaya daya tilo ta dace da mijin aure,namijin da yasan abinda yake,mai yawan tausaya mata da qaunar farincikinta
"Diya macace al'aminu,gwara taci gaba da sabawa akan hakan,na gana nauyun iyalinta ne zai hau kanta,mace bata da wani hutu da ya wuce tayi abinda ya dace a matsayinta na mace,to daga baya saita huta din" dan nauyin innar yaji ya kamashi,saiya gyada kai sannan ya miqe yana yiwa inna sallama.
Koda ya fito tsakar gidan babu ita har yanzu,hakanan babu motsinta,ya gifta inda ta tashin idanunsa nakan botikin wankinta,ya sake sakin murmushi ya wuce soro,ya saka key ya bude dakinsu ya shiga.
Saman kujera ya zube yana furzar da iskar daya zuqota tun daga hunhunsa,hannunsa yana saman kansa yana shafa sumarsa daga gaba zuwa baya a hankali,yanajin yadda kansa ke sarawa,gefe guda kuma yana qarewa dakin nasu kallo,yasan hargitse kadan yana buqatar gyara,kwana biyu bashi da isashen lokaci da zai zauna ya gyara din,dinki yake na jama'a tuquru saboda gabatowar azumi,yanason ya samu isashen kudi a hannunsa da zai yiwa gidan siyayyar kayan azumi,ya yiwa iman kayan sallah sannan yaje ya gano yayarsa itama da nata kayan azumin dana sallah,inna tasha hanashi saboda sadiqu da malam duka suna tasu siyayyar,amma sam yaqi yarda,inda daga qarshe yace baya jin dadin hakan a ransa,sai yaga kamar innar ta warshi ne shi,wannan furucin yasa ta qyaleshi,bata sake magana ba.
Ruwa ya fara diba ya shiga wanka ko zaiji dadin jikinsa,bayan ya fito ya murzawa qofar dakin nasu key,duk da yasan babu me shigo musu kai tsaye,ya sanya boxer da singlet ya koma ya kwanta saman doguwar kujerarsu yayi rub da ciki.
Idanunsa ya runtse gam,tunanin iman na dawo masa,surorinta na bayyana cikin idanunsa,wani yanayi na mamayar ilahirin jikinsa,tsigar jikinsa na tashi,sai ya sake gyara kwanciyar tasa yayi rub da cikin da gaske,ya sake rufe idanunsa a hankali yana ci gaba da dulmiya cikin tunaninta,murmushi na qwace masa saman fuskarsa lokaci bayan lokaci,sai daga bisani yaso dakatar da kansa saboda ganin yadda tunanin ke neman qara ta'azzara ciwon kan nasa,don haka ya haqura da kwanciyar,ya miqe ya balli paracetamol biyu cikin magungunansa yasha,ya sanya jallabiya ya jawo qofar dakin nasu ya fito zuwa qofar gida.
Yaci sa'a malam yana nan,an gama karatun yamma yana shirin sallamar yara,ya cire takalmansa yayi tattaki cikin girmamawa zuwa gaban malam din,yayin da shima malam ya bishi da kallo wanda ke nuna tsantsar kulawa.
Gefansa ya zauna,bai kuma yi magana ba har ya gama sallamarsu
"Al'ameenu.....lafiya kake kuwa?" Malam ya jefa masa tambaya,sai ya daga kansa cikin murmushi ya dubi malam,yana yabawa da jinjina qoqarin bayin Allahn,yadda suke iya hakaito damuwar daje tattare dashi,ta ciwo ce ko akasin hakan
"Kaina ne yake dan min ciwo"
"Subhanallahi.....matso nan" malam din ya fada,saiya matsa gabansa kadan,ya sanya hannu saman kansa ya kama masa shi da addu'o'i,ya matsa bayan ya gama yana masa godiya,wanda babu jimawa yaji ya fara sauka,daga bisani ma suka shiga tattaunawa,har zuwa sansa sadiqu ya dawo dava wajen aikinsa shima ya zauna nan wajensu yana cewa
"Na biya ta wajen aikinku mu taho tare,saina taras waika taho"
"Kaina ne ya fara ciwo,saina yanke na dawo gida na huta" cikin yanayin nuna alhini da damuwa yace
"Subhanallah,sannu"
"Yauwa,da sauqi ai,malam ya kamamin ya sauka" ya fada ganin yadda fuskarsa ta nuna damuwa
"Kaine ma man,ka dinga kwanciya wasu kwanaki kana hutawa,kana stressing kanka da yawa wallahi" murmushi kawai ya sakar masa ba tare da yace komai ba,shi a karan kansa a jikinsa yakejin akan struggling bai fara komai ba,namijin duniya dan gwagwarmaya ne,abinda ya saba gayawa sadiqu kenan.
Basu shiga gida ba anan suka yada jam'in sallar magariba su da sauran jama'ar dake salla a wajen duk sanda malam ke kusa,aka idar suka sake zama hira,irin zaman da ba kasafai lokaci ke basu damar yinta ba,saboda baqi da kuma yanayin aikinsu,daga bisani malam din yayi baqo,suka shiga tattaunawa,hirar sauta koma ysaka insa da sadiqu,sunaga qus qus dinsu saboda kada malam yaji,saboda hirar irin tasu ce,yana bashi labarin yarinyar datace tana sonshi,al'ameen din nata sukar abun,saboda shi sam yana qalubalantar mace tace tanason da namiji a irin wannan zamanin,daga qarshe malam ya tura daya daga cikin almajiransa su sanya a fito da abinci,wanda dama da wuya kaga anyi girki a gidan dai dai cikin masu gidan,saboda baqin da malam din kanyi lokaci zuwa lokaci,sadiqu yacewa yaron ya gayawa iman ta hado da nasu.
Cikin gidan babu kowa sai ita,don haka inna ta tsaida yaron malam din,ta taya iman shirya abincin,yaron ha daukar mata wani ita kuma ya dauki wani suka fito dashi.
Tunda ta doso wajen idanuwansa na kanta,cikin lullubin hijab har qasa,duba daya zaka yiwa hijabin kasan tsafta ta wadaceshi,don harda karin guga,idan kuma ta kusanto inda kake zaka iya jin qamshin body mist din da take amfani dasu,'yan 300 ne,saidai suna da sanyin qamshi,tana da maitar son qamshi da turare,don haka tun kafin ma takai haka ta iya zaben turare, training din al'ameen dince,tun daga tsafta zuwa son qamshi,girki ne kawai aikin inna.
Har zuwa sanda ta fara isa gaban malam ta ajjiye musu nasu abincin bayan ta duqa ta gaidashi shi da baqonsa idanunsa na a kanta,girma da 'yammatancinta yana sake cika sosai,ta zama budurwan gaske,saita qaraso gabansu a hankali,daidai sanda baqon malam ya furta wata magana data dauke hankalin al'ameen daga wajen kwata kwata ta maidashi kan hirar su malam din.
"kada dai ace hajarunka ce ta girma haka?" Murmushi malam din yayi
"Itace mana" kai ya gyada
"Ikon Allah,girman dan mutum babu wuya"
"Ka kwana biyu baka ziyarcemu bane shi yasa" malam ya amsa masa gana wanke hannunsa cikin kwanan wanke hannu dake gabansa wanda inna ta hado dashi
"Lallaifa an kwana biyu" sai yadanyi shuru kadan sannan yace da malam
"Ni kuwa malam khalilu,da zaka amince ai da mun qulla wani alkhairi" daga kai malam yayi ya dubeshi sanda yake qoqarin bude kwanonin abincin
"Ina saurarenka malam basiru"
"Me zai hana yaron wajena ilyasu yazo yaga hajaru,bamusan me Allah zaiyi ba,kaga idan Allah ya daidaita tsakaninsu ai mu shikenan,kakarmu ta yanke saqa,tuwona mai na"
Saura kadan maganar tayi tafiyar yaji da numfashin al'ameen,idanunsa suka fara laluben iman dake duqe a gabansu tana ajiye musu nasu abincin sabida bacewa ganinsa da take neman yi,zuciyarsa tayi wani bugawa tare da qara adadin gudunta.
Ajjiye murfin hannunsa malam yayi yana duban baqon nasa
"Zanfi kowa jin dadi matuqar hakan zata kasance,inama ina da wata diyar bayan hajaru da na baku,kuyimin aikin gafara,tuntuni na bayar da hajar,lokaci kawai muke jira a zartar da komai nan kusa in sha Allahu".
Nannauyar ajiyar zuciya alameen din ya saki,yana share gumin dake goshinsa tare da duban tsakiyar blue din qwayar idanun iman din dake haske cikin dan hasken dake kewaye da wajen,kamar tasan ita yake kallo saita daga kai suka hada idanu,ta sakar masa da murmushi tana sadda kanta qasa cike da jin nauyi da kunyar abinda ya faru dazun,abinda ke alamta masa cewa bataji maganar dasu malam ke tattaunawa ba,nauyin numfashin ajiyar zuciyar da ya saukar ne ya sanyata daga kai suka hada ido da ita.
Kusan baici wani abincin kirki ba ya tattara ya koma cikin gidan,dakinsu ya fara shiga saidai ya kasa zama,yanason yin magana da iman din,ba kasafai ya fiya son kebewa da ita ba saboda kare haqqin sharia sa kuma gujewa shaidan,amma dole ya zaqulo dalilin da zai sanya su zauna suyi magana da ita,don haka ya dauki sabuwar wayarsa daya siyo a dazun ya juya da niyyar fitowa,dai dai sanda sadiq ya shigo ya wuce cikin gidan ya barshi a dakin yana amsa waya.
Dakin malam da ya gani a bude ya tabbata malam din ya shigo cikin gida,kuma idan ya shigo din inna na tare dashi,hakan ya sake bashi qwarin gwiwar isa ga rumfar inna.
Cikin saa ya sameta zaune tsakiyar litattafanta,ta bajesu tanata qoqarin gwada assignment din da aka basu a yau din,wanda zasuyi zanen zuciya ne tare da fitar da kowanne chamber na cikinta.
A hankali ta daga kanta tana amsa sallamar tashi,sai kuma ta maida kan nata ta duqar tsakanin qafafunta tana juya abun zanen dake hannunta,ya sake sakin murmushi,ya qarasa a hankali kan kujerar dake daura da ita ya zauna saman hannun kujerar,cikin lallausar muryarsa daya ragewa kaifin sauti yace
"Hajar 'yammata" ji tayi tamkar zata lume a wajen,sautin muryarsa a yau din ya zama na da an cikin kunnuwanta,uwa nauyinsa da takeji ya ninku cikin ranta daga sanda yaga abinda taje wankewa dazun
"Ina fatan kin kwashe wankinki,saboda banason kowa yazo ya gani" saita saki abun rubutun ta juyar da kanta ta sanyashi saman kujerar tana boye dariyarta cikin jin nauyi,ta tabbata zaiyita tsokanarta ne idan batace wani abu ba,don haka cikin siririyar muryarta tace
"Don Allah ya alameen....don Allah" yasan me takeson fada,saiya saki qaramin murmushi me dan sauti kadan,ya zamo ya zauna sosai saman kujerar yana cewa
"To shikenan....duk da dai an boyen.....shikenan dai,ungo wannan,sakamin a charge" a hankali ta juyo tana avoiding hada idanu dashi,tasa hannu biyu ta karba wayar da yake miqo matan
"Laaaa yaya,taka ce?" Kai ya gyada mata tana juya wayar a hannunta
"Tawa ce" saita narke kadan,duk da bata bari sun hada ido ba
"Don Allah yaya yaushe zaka siyamin nima,kaga fa na shiga senior" ya santa qwarai da son waya,saidai a yanzu bashi a ra'ayin ta riqe qaya torching kwata kwata saboda wasu dalilai
"Wannan bata ishemu ba?,abuna ai naki ne"
"Yaaya,idan ka fita fa da abarka zaka dinga fita"
"Zan dinga bar miki ita duk weekend kina danawa,shikenan?" Cikin murna tace
"Yauwa yaya,na gode"
"And....idan naga yanayin performance naki a wannan term din,zan siya miki qaramar keypad indai inna da malam sun bari" sosai ta nuna murnarta,ta tashi ta fara qoqarin saka masa a chargyn
"Idan kin gama kizo zamuyi wata magana" ya fada yana saukowa tare da buda takaddan data fara zanen yana kallon zanen nata.
Tana gama sanya chargyn waigowar da zatayi taga ita yake kallo bayan hannunsa na riqe da zanenta,wani weakness ya saukar mata,duk kuzarinta na daxu ya gudu,batasan wane irin power da magnet ne a idanun yayan nata ba,wanda a baya da babu su sai a yanzu
"Zauna a nan" ya mata nuni da wajen da yake buqatar ta zauna din,inda zai zamana suna fuskantar juna ne,ta zauna ta lanqwashe qafafunta
"Wa kikeso a zuciyarki?" Ya jefa mata tambayar kai tsaye,abinda ya sanyata daga kai ba tare da tako shirya ba ta dubeshi saboda jin saukar ba zata da tambayar tashi tayi mata,idanunsa cikin nata ya jinjina kai
"Yes.....zuwa yanzu kin girma queen,ke din ba yarinya qarama bace kamar yadda kike kallon kanki,zuciyarki zata iya fadawa soyayya at any time.......wa kikejin kina so" sosai ya jefata cikin nazari,kafatanin rayuwarta batasan kowa ba bata saba da kowa ba sama dashi,bata taba kallon kowa ba taji wani abu na daban a kanshi ba sai shi,inda tasan soyayya ko alamominta,ba shakka zata iya cewa wala'alla shi takeso,amma yanzun batasan shaquwa ko ganin girma bane,duk bata sani ba.
Maganarsa me nauyi ce,don haka ta girgiza masa kai kawai
"Uhunnn..... talk to me mana,ki gaya min" sake girgiza kai tayi da qarfi,murmushi me qarfi na son qwace mata,wanda ya cakuda da kunya
"Don Allah yaya,babu kowa fa" kamar yace
"Harda ni?" Sai kuma ya danne wannan a ransa,ya saki nannauyar ajiyar zuciya,ya sake cooling muryarsa sosai
"Bani aron hankalinki iman" sau daya ta daga kai ta kalleshi ta mayar qasa tana sake gada nutsuwarta kamar yadda ya buqata
"Inaso ki bani dama guda daya tak a rayuwarki iman,ina da wani tanadi na musamman cikin rayuwarki"
"To yaya" ta fada a sanyaye.
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 10
*_Wannan littafin na kudi ne,game buqata zaki iya tuntubar wadan nan numbers din_*
09032345899
Ko kuma
09166221261
"Imannnn" ya danja sunan nata,ta amsa da na'am,har yanzu idanunta suna qasa
"Bana so ki kula kowa,banason kiyi soyayya da kowa..... infact ma,na miki zabin mijin aure wanda zai dace dake in sha Allah.....kin yarda?" Kai fa gyada tana sake saukar da kan nata qasa
"Kinyimin alqawari?" Saita sake jinjina masa kan,ya sauke numfashi mai nauyi daga qirjinsa yana furta
"Alhamdulillah".
Shuru yadan ratsa dakin,yana ci gaba da kallon zanen nata,saidai zuciyarsa ta rarrabu kashi kashi wajen tunani iri daban daban
"Zanen nan yayi kyau,ina tunanin yadda kika iya zanen zuciya har haka.....soyayyarki zata kasance me kyau haka" da sauri ta daga kanta suka hada idanu,wadanne irin manya manya kalmomi ya al'ameen ke mata amfani dasu ne haka,gashi ya ritsata da idanu yana kallonta,sai ita ta janye nata idanun tana sake qunshe fuskarta waje daya,ya saki murmushin nasarar da yake hangowa,yana iya hasashen yadda yake samun ci gaba da kuma galabar narkar mata da zuciya kowacce rana idan ta bullo kafin ta fadi.
Shi ya zauna ya tayata aikin gaba daya kasancewar science yayi shima,banda rashin zamowarsa dan wani shi din mutum ne me matuqar qwaqwalwa daya kamata ace ma zuwa yanzu yayi nisa a karatun likita da yake jarabar so,suna aikin yana dan janta da hira don ta saki jikinta,tadan sake amma ba kamar yadda suka saba ba,bai bar cikin gida ba saida inna ta fito daga wajen malam,sannan ya wuce dakinsu ya barta da tarin tunani cikin kwanyarta.
********WASHEGARI******
Bayan tasowarta daga makaranta wanda shima tare da munira suka taho,ta kuma sake biya mata kudin mota,bayan tayi wanka ta sauya kaya taci abincinta inna ta bata dakan garin kunu wanda akewa malam,tace takai bayan layinsu ta tsaya a daka ta taho dashi
"Don Allah inna zan leqa gidansu bushira" bushiran ba boyayya bace a wajensu,nutsatsuyar yarinyace da suke taba qawance da iman,wanda tun quruciya itace kadai ta dauke halayyar iman din,duka sauran irinsu rahama abokan fadanta ne,banda yanzu da girma da hankali yazo ake gaisuwar mutunci a wuce wajen.
Tana kaiwa mai dakan kudin ta zarce gidansu bushira,wanda gidajen dake tsakaninsu da gidan dakan bai wuce gida shida ba,tayi sa'a fa sameta a gida,dama kuma ba inda take zuwan,islamiyya ce,kuma makarantarsu daya,anyi musu hutun sauka sai wani satin xasu koma
"Wata sabon gani" bushira dake cire lallen data yiwa yatsu hannunta ta fada tana tabe baki bayan sun shiga dakinta da suke kwana da qannenta,murmushi ima tayi suka shiga tsokanar juna da hirar duniya,kafin daga bisani iman din fa budewa bushira abinda ke tafe da ita.
Shuru iman din tayi na kusan minti goma tana juya bayanan da bushira tayi mata,baya ta gama bata labarin komai,ta dauke hannunta daga kumatunta
"Amma bushira,ta yaya yaya al'ameen zai soni,bayan yayana ne?"
"Yayanki,ciki daya kuka fito?,ko yaya sadiqu ne?" Kai ta girgiza alamun a'ah
"To kuwa kinga ya halatta kuso juna ku kuna qaunaci juna,dama kuma abinda yafi dacewa kenan,don kusan dama ke din rainonsa ce......kuma ko ke qarya kike kice baki sonshi munafuka" bushira ta qarashe maganar tana ɗakawa iman duka a cinya gami da sakin dariya wadda ta sanya uman din dole ta tayata
"Ya al'ameen ya gama haduwa iman,idan ma bakiso wata ce zata daukeshi,yana cin list na sahun farko na kyawawan unguwan nan wanda babu na biyunsu,duk yadda zan gaya miki yadda 'yammatan unguwar nan ke sonshi da fatan ya sosu ba zaki gane ba,abu daya ya rage miki....ki jira sanda zaice kawai yana sonki ki karbi tayinsa hannu bibbiyu.....idan ma yayi nauyin baki ke ki furta kawai a wuce wajen" duka iman ta kaiwa bushira a gadon bayanta
"An gaya miki bani da ajine,duk yadda muka taso tare dashi bazan bari ajina ya zuba ba"
"Gaskiya ne tawan,kema a unguwar yayinki ake,kawai shakkar malam dasu ya al'ameen din ya hana a fara tareki ko sallama dake,amma ni kaina masu kamun qafa dani a kanki suna da yawa,harda masu motoci wallahi" miqewa iman tayi tana daure gashinta mai santsi da ya ware wanda dama babu wuya ya warware din,ta maida hijabinta saman kanta tana fadin
"Su riqe motocinsu.....kinga na manta shaf da aiken daya fito dani ma"
"Muje na taka miki" bushira ta fada itama tana janyo hijabinta suka yiwa ummansu sallama suka fito tare.
*******SANNU SANNU******
Kwanaki ke shudewa sa iman cikin makarantar nasreen,zuwa sannan bata da wata qawa ko aminiya data wuce munira,shaquwa me qarfi ta fara shiga tsakaninsu,duk da banbancin halaye da kuma dabi'u dake a tsakaninsu,gami da sukunin rayuwa.
Cikin sati uku ta fahimci wace munira,'ya mace guda daya tilo da mamanta ta haifa bayan yara maza qannenta guda hudu,tana ji da ita ainun,tana bata kulawa da gata,kusan mafi yawa daga cikin familyn su munira masu arziqi ne masu sukuni,saidai shi mahaifin muniran rufin asirin Allah gareshi,mamarsu muniran ta fishi kudi,hakan ya sanya komai na gidan take tafi dashi yadda takeso idan ma maigidan yayi wanda baiyi mata ba,tana ji da munira sosai,hakan yasa ta daukaki rayuwarta,tanason rayuwa me tsada sosai,hakanan takan kutsa kanta inda Allah bai kaita ba,gidajen 'yan uwan mamanta masu dashi ainun babu inda bata sani ba,wani lokaci idan ta shilla ta debi kayanta ta tafi daya daga cikin gidajen nasu,takan jima bata dawo nasu gidan ba,har ma sai kayi zaton 'yar gidan ce.
Da yake fara ce hakan sai ya sake qawata fuskarta,ya kuma ja hankalin samari a kanta,tana da samari sosai,kuma dukkaninsu 'ya'yan manya ne,wayar hannunta kuwa a lokacin babbar iPhone ce,dukkan abinda take ta'ammali dashi,tun daga sutura zuwa cima masu tsada ne,komai zatayi saita siya me tsada,saboda mamanta ta tsaya mata,batason sam taga muniran tata ta shiga cikin danginta an raina ta,hakan ya sanya take kashe mata kudi tuquru.
Saidai kuma muniran nada kirki daidai gwargwado,hakan shi yake taimakawa wajen boye da yawa daga halayyarta da basu dace ko kamata ba.
Ba komai na halayenta iman ta sani ba,tunda iyakarsu makaranta,da an rabu shikenan,sai kuma washegari,iya abunda ta sani muniran tana da kirki da kuma yawan kyauta,duk da tana zillewa duk wani abu da zaisa muniran ta kashe mata kudinta,kamar tafiyarsu tare,da yawan lokuta zillewa take tayi tafiyarta saboda kada muniran tace zata biya mata kudin motar.
*MONDAY MORNING*
Cikin clean uniform dinta da suka dauki karin guga kyakkyawar matashiyar hajar Ibrahim Khalil ke takowa tana nufar ajinsu,kafadarta daya saqale da jakarta,daya hannun kuma dan madaidaicin flask din abinci ne a ciki.
Kana duban fuskarta zaka karanci ranta a bace yake,saidai hakan wani kyau ya qara mata na musamman,sandin bacin ran nata makara datayi,aka kuma shanyasu a bakin gate har na wajen awa daya cikin rana,wanda wannan shine irin punishment din makarantar tasu.
Kamar ance ta daga kanta saman varander dinsu,ta daga kyawawan blue eyes dinta,idanunta sauka ga malamin,sir arabi,malamin daya takurata tun zuwanta makarantar,da shegen kallo naci da kuma shishshigin shiga harkarta,shike daukarsu darasin turanci wato English,yammatan makarantar da yawa suna yinsa,saboda motar da yake hawa,kana kallonsa kasan ba talauci ko babu suka sanyashi koyarwar ba,saidai ita sam imani hakan bai dameta ko ya dadata da qasa ba,don sam jininsu ita bai hadu dashi ba,ya fiya jin kansa saboda yaga yana tashen samartaka,yana sanya shaddodi da hawa mota,ita sam a rayuwarta batason mutum me jin kansa ma,izza da fadin rai,shi yasa tako ina ya al'ameen yake burgeta.
Yana da wani irin kwarjini gami da aji,uwa uba miskiline naqin qarawa idan baiso ba,hakan yasa baya daukar raini ko izgili,amma sam baida girman kai ko dagawa.
Ta sauke nata idanun tana jan tsaki qasa qasa,gami da qare hade ranta gab da zata shiga cikin ajin nasu,sabida yadda yawanci lokaci irin wannan sanda tazo a makare mazan ajin ke binta da kallo,abinda ta tsana ita kuma kenan,don haka a dake ta shiga ajin.
"keda mutumin naki ne?,na hangeshi tsaye upstair" munira ta fada tana danne dariyarta sanda iman ke zama kusa da ita,tana duba littafin subject din da akeyi
"Shine mana,me shegen kallon tsiya,banason mutum me kallo"
"Tsaurin idanu dai,kwata kwata baki dace irinsa bama,shi bai gani ba kedin kalar matar manya ce" waiwayowa iman tayi sanda take dora littafin saman table dinta
"Kamar yaya?" Murmushi munira tayi tana ci gaba da copying note dinta
"Kamar har yanzu bakisan baiwar kyan da Allah yayi miki ba,ai kyan kyau irin naki ki morewa babban gida,inda zaa jiqaki da kudi da mota,fita qasashen waje babu kama hannun yaro,shine kika mori kyanki,amma ba kowanne irin kalar namijine zaizo ya tsaya gabanki da sunan yana sonki ba" tsaki iman taja,saboda ta dauki maganar munira a matsayin shirme,ta bude littafinta ta fara kwafar note din da sauri da sauri don ta fuskanci ya kusa dawowa ya goge wanda ya fara.
"Am telling you fa,kina ganin kamar wasa ce maganata?,to Allah koni da ban kama rabin qafarki a kyau ba,zakiga kalar mijin da zan zaba"
"Don Allah ki shiru ki barni da bacin ran da yake damuna" dariya muniran ta saki tana ci gaba da rubutun,har zuwa sanda malamin ya kammala yayi musu explanation ya sallamesu.
"Me ya hanaki zuwa makaranta Friday ne?" Iman ta tambayi munira tana maida littafinta jaka,sai data juya manya idanunta,da alama amsar da zata bayar amsa ce da take mata dadi cikin ranta sosai sannan tace
"Kinsan biki muke na wata cousin dita,so ran Friday muka tafi garinmu acan zaa daura aure,kuma ina cikin wanda aka siyawa ticket zasubi flight,kinga ko bazan bari nayi missing ko damata ta wuceni ba,nayita neman number dinki na gaya maka,sai dana fara checking wayana naga ashe bamu taba exchanging numbers ba......ki bani number dinki saboda irin hakan,kinga nama canza sabuwar waya,ranar aka bani gift dinta" munira ta fada tana saka hannunta a aljuhun rigarta.
Kallo daya zaka yiwa wayar kasan cewa bata qananun kudade bace,hakanan sabuwa ce fil sai sheqin sabunta take,munira tabi wayar da kallo sannan ta amsa mata
"Nikam ai bani da waya,ta ya al'ameen nake ara duk weekends nayi game ko browsing" kallon mamaki qarara munira ta jefi iman dashi,harda dan ja baya
"Kina ss 01 amma ace baki da phone iman, jokes apart please,wasa kikemin ko number dince ba zaki bani ba?"
"Tunda baki yarda ba ai babu amfani na dage saina gamsar dake,duk yadda kika dauka hakane"
"Am sorry my friend,Allah na dauka wasa kikemin....amma kuma,ba sani ba wallahi,da dana canza na baki dayar,sai qanina na bawa wanda yake bin me bina" idanu iman ta fidda
"Ni shegiya kaza,ya al'ameen bazai bari ba,amma ina saka ran muna gama wannan term din zai siya min keypad sabuwa in sha Allah,yayi alqawarin idan nayi abun kai zai siyamin" dariya sosai munira ta saki tana kallon iman
"See you don Allah,wani irin keypad?,to ko 'yan aikin gidanmu banjin akwai me keypad,don Allah karma ki fada wani yaji,sai ajinki ya zuba,mazancan da kike jawa aji saisu rainaki,su dauka qaramar yarinya ce ke".
Rai sosai iman ta bata tana dubanta
"To sai me?,ni ina farinciki da duk abinda nake dashi,kuma iya abinda yake ganin ya dace dani kenan,kuma ina farinciki da hakan"
"Wait mana iman" munira tayi saurin dakatar da ita ganin kamar taji haushi
"Nifa ba abinda nake nufi kenan ba,ki fahimceni.....ina nufin yanzu budurwa kamarki,ai ya kamata a sakar miki mara a siya miki waya me kyau saboda gudun raini daga wajen tsararrakinki.....na tabbatar yana da kudin da zai iya siya miki babbar waya,ko yaya ne kaima kayi dan abun xamanin nan da kowa yakeyi" duban munira kawai take,tabbas ya al'ameen idan tace tana so zai siya matan,amma a hakan ma babu lallai su malam su yarda ba,sai tayi shuru bata sake cewa komai ba,saboda isowar wata 'yar ajinsu da tata wayar,tazo munira ta tuttura mata pics da wasu videos,da kadan kadan sai ga masu wayar suna zuwa,sunata sending ma junansu abunda kowa keson sawa a wayarsa.
Tana daga gefe tana kallonsu,kowacce wayar hannunta babbace,wata daga gidansu wata kuma saurayine ya siya mata,ba shakka tana bala'in son waya da maitarta,amma ba zata takura ya al'ameen din ya siya mata sama da wadda yace zai siya matan ba.
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 11________________
*_Huuuuuum! Idan kaji hanci a sama yayin gittawar mata ƴan ƙwalisa ko shiga gidajensu kasan maganar ta ƙamshi ce_*
*_Ina magana ne aka kayan ƙamshi ƴan gaske ba saka iska ta hure maka ba_*
*_Ina mata ƴan ƙwalisa ma'abota so da ƙaunar ingantattun haɗin turaruka ƴan gaske? To kuzo maza ga dama a tafin hanunku cikin sauƙi da sauƙaƙawa._*
*_Ana siyarda Turarukan Wuta na yan Maiduguri Set na amare. Ana bada sari kuma._*
*_Sannan akwai kayan gyaran jiki. Akwai zumar qiba result cikin 1 week. Turaren daki, jiki, kaya, tsuguno, humra, colacca, turaren wanka, mopping scents, air freshener._*
_Address Kano, Mariri Maiduguri Road. WhatsApp number 07068145252_.
*Sai kunzo🤳🏻*
___________________________________
Tare suka jero da muniran bayan an tashi kamar yadda suka saba,suna tafe suna dan hira munira na tsokanarta
"Nikam kullum aka tashi daga makaranta dalibai basa gajiya da kallonki iman?" Tsaki taja,itama abun yana damunta,don har ta yanke shawarar fara sanya niqabi
"Sai suyita ai,kamar kai dayane mutum,su ba bil'adama bane 'yan uwanka"
"Kin fita daban seriously,shi yasa kike shan kallo" munira ta fadi sanda take nufan wata mota ash jaye da hannun iman,dakatawa iman din tayi tana qoqarin kuma zame hanunta daga na munira
"Ina kuma zaki kaini ga hanyar titi?" Waiwayowa tayi tana dubanta,fuskarta dauke da murnushin nan
"Oops,sorry,na manta in gaya miki,me daukana ya dawo da daukata,dama shike maidani gida indai naje gidan uncle jibril,yawanci ina bin motar haya ne idan ina gidanmu" kai iman ta jinjina tana saita hanyarta zuwa titi
"To sai gobe,Allah yabamu alkhairi" da sauri tasha gabanta
"Ban gane ba,bayan ta hanyar unguwarku xamu wuce,ki shigo don Allah,yana da kirki,zai ajjiyeki unguwarku,cousin dina ne sadam,lokacin tashinmu lokacin ne shi kuma yake komawa gida cin abinci,shi yasa yaje biyowa ta nan ya daukeni mu wuce tare" kai iman ta jinjina
"A'ah fa,zanbi adaidaita kamar yadda na saba" dambu taliya ta kada iman amma taqi,har sau da na cikin motar ya fara mata horn,dole ta haqura tace da ita
"Shikenan,bani number wayar to"
"Idan kin kira amma kice ni kike nema,don ya al'amin ko inna cikinsu wani zai daga,saboda numbers dinsu ne" dariya munira ta saki
"Allah ya sawwaqe,yanzu inda saurayi kikayi haka zaki gaya masa kenan?"
"Ke kika sani,ni bani da wani saurayi ma" da wani mamakin take duban iman din,saidai ta share ta soma karanto mata digit's din tana lodawa a wayar tare sa serving,sukayi sallama tana jajata mata Allah yasa ta samu mota da wuri,saboda sadam ya gaya mata ana wuyar abun hawa yau din,sakamakon taadar da man fetur yayi,da yawa wasu masu ababen hawan sun haqura sun ajjiye abun hawan nasu a gida.
Ta samu tulin dalibai kuwa masu jiran abun hawa,haka nan tabi sahunsu itama,tana fatan su samu da wuri kodon ranar da ake dasawa.
Kusan duk motar da zatazo ta wuce a cike take,wata kuma kafin ta qarasa inda ta tsaya wasu sun shige sun cikata,tana nan a tsaye tsayin wasu mintuna ta hangi kamar gilmawar motarsu munira,sai kuma taga ta tsaya taja da baya ta dawo dab da ita
"Why not ki qyaleta....ba'a dole wajen taimako fa" sadam daya dan hada rai ya fadawa munira
"Qawatace,banason ganinta tana sha ranar nan,kayi haquri minti daya"
"Ok" ya amsa qasa qasa yana jona wayarsa a chargy,munira ta bude murfin motar ta fito ta nufi inda iman take.
Da farko musu taso ta sake mata,sai da taga muniran taji haushi,sannan kuma me motar ya fara buga musu horn sannan ta bita,sanyin ac ya ratsata sanda jikinta ya shige motar,ta maida murfin ta rufe sanda munira ke mita
"Haka kawai ki tsayar da kanki a wannan ranar babu gaira babu dalili,bayan ga abun hawa,ai tsaiwa a ranar nan sai dole"
"Ina yini" tayi qoqarin gaida matuqin motar ba tare data amsa mitar da munira ke mata ba
"Laf....lafiya qalau.... 'yammata" harshensa yadan sarqe,bayan idanunsa sun sauka a fuskar iman dake ciro jakar bayanta zuwa saman cinyarta ta glass din gaban motar,gabansa yadan fadi,ya zuba mata idanu na wasu sakanni ba tare daya iya dauke idonsa daga kanta ba,tunda yake bai taba ganin halittar mace da komai yaji.....ta kuma tafi da imaninsa irin wannan ba,wani irin kyau mai cika idanun me kallo,abinda yasa yadan daburce har ya qara mata da kalmar 'yammata kenan ba tare da ya sani ba,kalmar kuma data dan ja hankalin munira tabi sadam din da kallo,don tasan ba dabi'arsa bace hakan.
Haka kawai ya samu kansa cikin rashin nutsuwar da yake da tabbacin ya fada kogin soyayyar iman ne farat daya,ya dinga satar kallonta lokaci bayan lokaci,har sai da iman din ta ankara,ta kuma tsargu,tare da tuhumar kanta na meye xata shiga motar wasu,koda rana zata kasheta?,sai ya basar,ya fara soko musu hira,yana kuma jan iman din din
"Wanne layi zamu shiga?" Ya tambayi iman din kai tsaye,idanunsa na kanta ta cikin mirror
"Ya isa,anan ma zan sauka" ta fada tana sake gyara jakarta
"A'ah,ai da kin barmu mun cikasa ladanmu ko?" Ya fadi yana dan saki murmushi,munira ma ta saki nata tana gyada kai
"Aikuwa dai"
"A'ah na gode,babu nisa,zan qarasa da qafata" bai sake cewa komai ba ya fara qoqarin faka motar,sannan ya saka hannunsa a aljihun gaban motar ya budeshi,ya ciro wrapper din 'yan dari dari sababbi ya miqa munira
"Bata,tasa kati a waya"
"Ina taga waya,saidai tasha chocolate" munira ta fada cikin sigar zolayar iman tana miqa mata kudin.
Kememe iman taqi amsar kudin,saima ta soma takawa tayi gaba abinta tana cewa sai gobe
"Ni nasan ba zata karba ba,amma ka barni da ita,zan kai mata gobe" tace da sadam,saiya sauke ajiyar zuciya,cikin kasala ya tada motar
"Ban taba ganin yarinyar data yimun ba irin qawarkin nan ba,ki shigemin gaba don Allah na mallaketa" dariya munira ta saki
"Karka damu,indai zaka saki kudi duk ba zaya gagara ba"
"Mayyar kudi,bansan ina zakikai son kudi ba muni" dariya ta sake
"A'ah ya sadam,kudi fa abun sone,babu meson wahala ko talauci,ko aikin nan da kake yanzu ba kudin kake nema ba?". Murmushi yayi kawai,don yasan wajen magana badai a kada muniran ba,gaba daya shi yanzu hankalinsa ya tafi ga iman.
Koda washegari taje mata da kudin makaranta cewa tayi ba zata karba ba wallahi,harda qarin handset daya siya ya dora mata akai,kusan fada sukayi da iman din akan hakan,ita ta dage saita karba,dan uwanta ne,kuma babu dadi maida hannun kyauta baya,yayin da iman din tace sam batasan wannan zance ba,kawai daga haduwa da mutum sai ta karbi abun hannunsa?,tace waye ya bata ma a gida?. Wani kallo muniran tayi mata
"Au daman duk yammatan da samari ke musu kyauta nunawa suke a gida suce wanene ya basu?,kowacce boyewa take tayi amfani dasu abunta,ki karba kawai,don gaskiya bazan iya maida masa ba,don bansan bayanin da zanyi masa ba"
"Ki riqe na baki kyauta tunda ba zaki iya mayarwa ba"
"Bani ya bawa ba,amma zan ajjiyesu har zuwa randa zaki amsa" ta fada cikin bacin rai tana zuge handbag dinta ta jefasu ciki,zancan bikin qawayensu guda biyu dake matsowa da aka zauna yi shi ya raba gardamar,duk da haka muniran bata sauko ba.
Koda aka tashi tun daga bakin gate ta lura da motar jiya ce tazo daukan muniran saita zame ta gudu,ta canza hanya ta shiga motar haya tayi gida,washegari ta dinga mita da qorafi iman din tace da ita
"Kada ma ki soma batawa kanki rai,don Allah bazan sake shiga motar wani a gida baa sani ba" tasan da gaske take idan tayi magana,don haka bata sake cewa da ita komai ba,sai kumbure kumbure da take mata alamun tashi fushi,dariya ta saki
"Kyayi ma ki sauko" amsar da iman din ta bata kenan.
********. ******. ********
A nutse ya ajjiye almakashinsa saman keken da yake kai,sannan ya miqe ya nufo inda iman ke zaune saman wani stool tana fuskantarsa.
Ganin ya dosota saita dauke idanunta a hankali,ya saki qaramin murmushi da ya sake qawata fuskarsa,ya zauna saman wani keken dake daura da ita,ya dora qafarsa daya saman wata kujerar roba da babu kowa akai.
Shagon nasu yanzu babu kowa sai wani dan matashi guda daya daketa faman dinki,da alama masu kayan suna hanya ne,koma bayan sanda ta shigo din da yake cike da matasan,sunata shirin fita wata ball ta abokinsu,shi dinne yace ba zashi ba,don ba wani abokinsa bane na kusa,saboda dama ba mutum ne shi me tara abokai da yawa ba.
"Banfiyason zuwanki shagon nan ba,kina ganin dai yadda kullum yake cike da mutane" dan turo baki gaba tayi
"To ya alameen,idan ka dawo gida inna ba zata bari muyi magana bafa.......kuma lokaci yana qurewa,bikin gaba daya saura uku" idanu ya zubawa lips din da take turowar,kamar ya kama ya tsotse haka yakeji,saiya dauke idanun nasa yana tattara kansa waje guda
"Me yasa baki kirani a waya ba?" Saita fidda idanunta duka a kanshi
"Ka manta ne,inna ta hanani taba wayarta,tace ina qarar mata da kati"
"Haba da Allah haba,ya zaayi ace budurwa kamanki aron wayar inna kike?,ai kinfi qarfin haka,wani idan ya ganki zai zaci babbar iPhone ki manya manyan Huawei kike riqewa" ya fada da salon tsokana.
Kallon da al'ameen ya jefeshi dashi yasanya shi jan bakinsa yayi shuru,kafataninsu sunsan halinsa baya daukar wargi,hatta da ogansu me shagon wani lokaci kamar shakkar al'ameen din yake saboda kwarjinin da Allah ya zuba masa,uwa uba kuma mutum ne shi mai tsaiwa akan gaskiya,idan kaga ya dage kan abu,to idan akayi zuzzurfan bincike shine me gaskiya
"Bani mu gani" ya fada yana miqa mata hannu,sai tabi hannun nasa da kallo daya nannade hannun rigarsa zuwa gwiwar hannu saboda yaji dadin kallo,cike yake da gargasa da jijiyoyin da zasu shaidamaka cikin jikinsa a murde yake,kuma qaqqarfan namijin duniya ne.
Kunya ta kamata sanda ta miqa masa yankin atamfofin guda biyu taga ya janye hannunsa yana jan hannun rigarsa yana rufe hannayen nasa,idanunsa kuma na bisa fuskarta,da alama yaga kallon data bishi dashi kenan.
Murmushi ya saki sanda taja hijabinta ta kare fukarta,yana qoqari yaga ya gujewa duk wani abu da zai sanya taji wani abu tattare da ita,bayason ya raba mata hankali tun yanzu ko yayi cikakken wasa da hankalinta,saidai lokaci yana nan zuwa da zai mantar da ita kowa cikin duniya saishi kadai.
Tana miqa masa ta sauka daga kan kujerar don ba zata iya ci gaba da zama ba
"Qawata zata kawo dinki yaaya don Allah,kada kace aiki ya maka yawa"
"Karta damu,indai ta wajenki ta biyo"
"Saika dawo" ta fada tana masa sallama,bai amsa ba illa binta da yayi da kallo,kominta a nutse kuma a tsare Allah yayi mata shi,yana jin sara qiris ya fara tilastata sanya niqab,yana jin ciwo cikin qirjinsa da zuciyarsa duk sansa ta fita koda makaranta ne,yafi jin dadi da samun nutsuwa udan ya dawo gida ya sameta cikin gidan.
Wani irin shauqinta yakeji yana fusgarsa har ta bacewa idanunsa,ya sauke ajiyar zuciya yana sauka dubansa ga qyallen atamfofin data bashi,ya daga kai a hankali ya dubi matashin daketa aikinsa
"Yahaya......ka dubamin atamfar nan don Allah ka gaya min kudinsu gobe ko jibi"
"An gama" ya fada yana miqewa tare da miqa hannu ya karbesu.
*********. *******. ******
K'arfe hudu da minti ashirin da hudu wayar inna ta kada,iman data kai jug din data hadawa munira lemo kitchen ta dire da sauri ta dawo ta daga tana amsa kiran,munira ta tsammata,kuma ita dince,saita aje wayar tana jan babban hijabinta ta dora saman atamfar dake jikinta,wadda al'ameen ya zauna ya bata lokaci sosai ya tsara mata dinki na gani na fada
"Inna zan leqa waje na shigo da ita"
"Saikin dawo" inna dake zaune tana qoqarin gyara saitin radio dinta ta fada,tana son ta kamo freedom radio don jin shirin mu qyaqyata kafin biyar na yamma tayi. Slippers dinta ta zura ta tako zuwa soron gidansu.
Gab da zata fita shi kuma yana qoqarin shigowa,saura kadan suyi gware,taja da baya tana yarfe hannu tare da yamutsa fuska,abinda ya taimaka qwarai wajen fitowar dimple dinta duk sanda ta motsa fuskarta,yayin da shi kuma yaja da baya yana qare mata kallo.
Yana iya hangen yadda tayi wani kyau duk da cikin hijabi take,yana jin shi daya ne a duniya yake iya ganin kyanta koda cikin lullubi take,kuma a kanta kadai yake da wannan baiwar
"Ina zakije?"
"Qawata din nan da zata kawo maka dinki zan shigo da ita"
"Koma ciki" saiya koma da baya ya qwalawa daya daga cikin almajiran gidan kira,yace ya duba layin,idan yaga wata baquwa tana neman gidan nan ya shigo da ita,ya dawo ya zarce dakinsu sannan tuni iman ta kona ciki,duk da taso ya barta taje da kanta ta shigo da ita,saidai ba zata iya yi masa musu ba.
Ba jimawa saiga sallamar munira,iman ta fito da sauri,suka rungume juna cikin murna,kamar wadanda suka jima basuga junansu ba,kai tsaye suka fada dakin inna.
Cikin girmamawa ta gaida inna,innan ta amsa mata,sannan ta miqe ta fice zuwa dakin malam da tun daxu dama takeson shiga ta gyara masa kayan sawarsa ta barsu su biyu cikin rumfarta.
"Hajar ibrahim khalil" munira ta fadawa iman wadda keta qoqarin zuba mata lemo da abinci bayan ta qarewa falon nasu kallo
"Munira sulaiman"
"Yaudai gani a gidanku,naga randa zakizo nima namu gidan" hararta tayi cikin wasa
"Aiba zuwana kikayi ba,kawo dinki ne ya kawoki ko?"
"Eh duk da haka,inda hakanne ma ai da shagon zan tambaya nakai musu direct,da qyar mafa yaron da kika aika ya ganoni" ta fada tana daukan lemon takai bakinta
"Nazo fita mukaci karo da ya al'ameen,shi yace na koma ya tura sa'idu" ajjiye lemon tayi
"Yaudai zanga ya alameen da zancansa ya cika mana kunnuwa aka hanamu sakat,ya al'ameen din nan me shegen tsauri da takura,hala ku biyu inna ta haifa kawai" kai ta girgiza mata tana murmushi
"Mu uku ne,kawai yaya sadiq"
"Amma ban taba ji daga bakinki ba" zamanta fa gyara saman kujera
"Barshi wannan,bamu cika shiri dashi ba" dan dariya muniran tayi suka ci gaba da casa hirarsu,har ta soma bata labarin bikin wata cousin dinta da zasu fara,wanda tsiran kwana ukune dana qawarsu amina,wadda ta kawo dinkin ankonta yanzun.
Yadda taketa bawa iman labarin bikin da yadda aka tsara komai ya tabbatar mata tana matuqar ji da bikin,har ta zolayeta da haka
"Keee,ba dole ba,kinsan manyan mutanen da zasu halacci bikin?,inda naji dadi ana ya gobe dinner din amina zaayi kamu,ran dinner din amina ranar event din gidansu ango za'ayi ba namu bane,so babu lallai naje,washegari ne zaa tashi bikin gadan gadan"
"Wai ita aminan dinner zatayi?"
"Eh mana,wannan atamfar ai ita zaa saka ranar" tabe baki iman tayi,saboda ita duk wata harkar dinner ba zuwa take ba,bata damu da ita ba,koda ta damu dinma tasan ba dabi'ar gidan bace,babu me barinta
"To inajin babu ni a zuwan"
"Saboda me?,ya al'ameen zai hanaki ko?" Dariya ta kubcewa iman
"Au,sharri zaki masa?har kinyi tafsiri ma?" Itama tana dariyar ta amsa mata
"Eh to ai nasan qarshen zancan kenan,nidai badon yayanki bane Allah cewa zanyi da wata a qasa,wannan tsanani da boyo haka?,barima dai ya shigo inga ya yake ya alamin din" maganarta saita dan shigi iman,duk da haka tana dariya ta miqe
"Yama fa shigo gidan amma kin jishi shuru,bari na duba koya gama na masa magana" ta fada tana ficewa,ta manta bata dauki hijab din nata ba.
*LITTAFIN NAN NA KUDI NE,KI TUNTUBI WADAN NAN NUMBERS DIN DON BIYAN KUDIN NAKI*
09032345899
KO KUMA
09166221261
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 12
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
____________________________________
Tun daga bakin qofar dakin nasu qamshin turarensa ke karakaina,ya cika soron gaba daya,taja numfashi sosai ta sheqi qamshin,tana matuqar son qamshin turarensa,har yau kuma bata taba jin kowa da irinsa ba,babu abinda yake kashewa kudi sosai wajen siyansa irin turare.
Knocking tayi yace a shigo,ta tura qofar a hankali,idanunta suka sauka a kanshi,yana tsaye gaban mudubi yana ajjiye kwalbar turaren da ya gama fesawar yana qoqarin dora hula saman kanshi,yayi kyau cikin shadda ruwan makuba,dinkin zamani daya fidda samartaka sa zallar kyan da Allah ya bashi.
Ta cikin madubin ya kafeta da idanu,abunda bataso,sai ta kauda da kanta tana cewa
"Yaaya,ta iso tun dazu tana jiranka"
"Ganinan fitowa,wani waje zani na tsaya ne na shirya gaba daya kar na saba alqawari" ya fada yana daura agogon hannunsa,saita gaza tafiya yaci gaba da satar kallonsa har ya fuskanci haka,ta basar da sauri,sabida wani iri takeji da ganin kwalliyar da yayi din
"Yaa ina zaka da yammar nan" sai daya gama daura agogonsa tsaf sannan ya amsa
"Akwai wani da muka hadu da yace nakai takarduna,wala'alla idan da rabo zan samu scholarship,tunda suna da hanya"
"Allah yasa a dace" tayi masa addu'ar da har cikin ranta haka yake
"Ameen qanwata,na gode" tadanyi murmushi sannan ta miqe ta nufi hanyar waje.
Cikin tattausar muryarsa yayi sallama cikin falon,munira ta daga kanta daga danna wayarta da takeyi tana amsa sallamar
"Wow"bakinta ya motsa ta furta kalmar qasan zuciyarta,ta gyara zamanta sanda suke magana da iman
"Karbomin fura wajen inna" ta amsa da to sannan ta miqe ta fita zuwa wajen innar,dakin ya danyo shuru,saiya qarasa kujerar dake daga bakin qofa ya zauna a hannun kujerar.
Cikin fara'a gami da mutuntawa munira ta gaidashi,ya amsa kadaran kadaham,sanda iman din ta dawo da furar a cup ta miqa masa itama ta koma ta zauna.
Sai daya fara kurbar furar a hankali cike da nutsuwa sannan yace
"Muga kayan" saita dauka ledar ta aje masa a gabansa ta fidda kayan tana masa bayani,baice komai ba harta gama yana shan furarshi,sai data kammala dai dai sanda ya gama sha ya miqe da cup din a hannunsa
"Imani....ki dauka ki aje wajenki,idan zan fita jibi ki tunamin"
"To yaya" ta amsa masa sanda yake fita.
"Wow....wow,wannan shine ya al'ameen?,badan wani abu ba da na saka kai wallahi" harara iman ta balla mata
"Ba zaki yaudararmin yayana ba,saboda nasan baida kudin da zaki tsaidashi takara" dariya ta saki,tabbas abinda ke cikin zuciyarta kenan,saidai ba zata iya fitowa kai tsaye ta gayawa iman din ba,tako ina al'ameen yakai namiji,abu daya ya rageshi rashin 'ya'yan banki masu yawan gaske da zasu maisheshi wani,amma banda haka tabbas gawurtacce kuma isashen namiji ne.
"Yanzu haka maganar ci gaba da karatunsa ce ta futar dashi" iman tadan bata labari
"Allah sarki yayanmu,Allah ya bada sa'a"
"Ameen" iman ta amsa mata,daga haka suka fada wata hirar.
********. *******Tana daga zaune gefan katifar dake shimfide dakin iman,bayan ta karbi dinkunanta da sukayi kyau sosai wanda al'ameen din yayi mata,wayarta na hannunta tana ta danne danne,da yake gwana ce qwarai ita din wajen danna waya,shi yasa babu inda ke mata wahalar shiga loko da saqo na kowacce irin waya
"Kiyi sauri don Allah muje kada mu samu layi" munira tace da iman wadda ke shiryawa zasu wuce gidan qunshi,saboda gobe zaa fara bikin qawartasu
"Na gama ai,hijabi kawai xan saka" ta fada tana ware gogaggen hijabinta me kyau
"Kiwa Allah ki aje hijabin nan,wallahi wajen 'yan gayu ne sai kisa a dinga mana kallon tara saura kwata,ko kamar nawa mayafinne ki saka,tunda kinga dai babba ne,kuma bashi da shara shara" inan din ta buda baki zatayi magana munira ta dakatar da ita
"Nasan yanzu zaki kawo karatun ya Alameen,goben ma kenan haka zakiyi?" Murmushi kawai iman tayi,don kamar ta shiga zuciyartata,maganar al'ameen din ya hanata saka mayafai zatayi mata,saita aje hijabin,ta bude ma'ajiyar kayanta,ta ciro daga cikin sabbin lafayar da yagana ta bata,wata 'yar uwar mahaifinta har guda biyar masu azabar kyau da tsada.
"Kai kai kai,ke kinga kyan datayi miki kuwa,ma sha Alla,da ana musayar kyau Allah da tuni na karba naki na hadaki da nawa" munira ta fada cikin nuna santi da yabawa da kyan iman din tayi,wanda zahirin gaskiya gaskiya ta fada,wani kyau lafayan tayi mata,idan ka kalleta kamar ba zaka dauke ido ba,ita kanta dai data juya ta sake kallon kanta a madubi ta gasgata hakan.
Tana tsaka da sanya halfshoe dinta da ya alameen ya siya mata 6k wanda ya dace da lafayar jikinta wayarta da ya alameen din ya bata tecno ta dauki tsuwwa,munira ta kalli sashen da wayar take,ta tuntsire da dariya tana cewa
"Ana kiranki a rakani kashinki?' sai data manna mata harara sannan ta isa inda wayar take
"A haka nakeson kayata"
"Amma dai wallahi ba girmanki bane,dressing dinki sam bai kamaci wannan wayar ba" ta saba da jin wannan lafuzzan daga bakin muniran,don haka tayi banza da ita ta isa inda wayar take ta daga abunta.
Sai data gama wayar ta dubi muniran
"Su hamra ne,already wai suna wajen,har an fara yiwa wasu,mu kadane bama nan"
"Nasan zaa rina dama,munyi delay da yawa" munira ta fada tana daukar ledar kayanta.
Saida suka biya wajen inna,munira ta yiwa innan sallama da kuma godiya,ita kuma iman ta karbi kudin qunshin sannan suka fito suka wuce.
AMARYAR KB BEAUTY PARLOR,katafaren wajen gyaran amare da uwayen gidaje,yammata harma da zawara,waje ne na alfarma wanda ya kasance iya kudinka iya shagalinka,wajene daya amsa sunansa,duk sanda kaje haka zakaga manyan hajiyoyi suna karakaina,suna dukkan wani nau'in gyaran jiki da kuma kayan magunguna na gyaran jiki da aka warewa waje na musamman a ciki.
Amarya sakina itama iyayenta da danshinsu,hakanan wanda zata aura din shima ba baya bane,tun asali gidansu basu damu da karatun boko ba,kasuwanci sukafi bawa qarfi,don haka sanda miji ya fito mata ya kuma tabbatar musu zai siya mata dukkan wani certificate,basu wani jinkirta ba aka cireta daga karatun aka fara shirin auren nata.
Tun daga shigarsu wajen iman tasan waje ne na matan da suka isa,dukkaninsu qawaye ne,saidai bata wani saba can dasu kamar yadda suka shaqu da munira ba,don haka bayan 'yan caftarsu ta qawaye da murnar shigowarsu,sai ta samu waje saman kujerun da aka tanada a wajen tayi zamanta,tana sauraren hirarrakin dake tashi a wajen,da kuma shige da ficen 'yan gayu mazansu da matansu.
Hira suke irin ta matasan yammatan dakeji da tashen quruciya,dukkansu babu wadda ba daga babban gida ta fito ba,kusan ita daya ce ma kawai zaa ce iyayenta ba wasu masu kudi bane,saidai ita din ma shigarta fes take,kai bakace hakan ba.
Abu daya ne idan ka lura dashi zaka gane banbamcinsu,manya manyan wayoyin dake hannun kowaccensu,da kuma irin kudaden dake jakarsu,kowacce ta fito da tata tana harkar gabanta.
Mutum uku cikinsu saida samarinsu sukazo har qofar wajen suka basu kudin lallaen da gyaran gashi,kowanne cikin babbar mota,hakan kudin da suka basu sababbin ne a rafarsu.
Kafin zuwan nasu suka saka gasa,duk wadda kudin da aka bata yafi na sauran yawa ita zaa fara yiwa,daga qarshe fahima ita ta cinye,dole ita aka saka za'a bari a fara yiwa.
Ita dai nata idanu,sai wata matashiya dake kusa da ita wadda batafi sa'arsu ba da aka sawa lalle,tun dazu ake kiranta babu me daga mata,don haka iman din ta matsa kusa da ita
"Bari na daga miki"
"Yauwa na gode" ta fada a yagance tana murmushin jin dadin hakan da iman din tayi mata,ta riqe wayar da kafadarta ta fara amsa kiran,murya can qasa,wanda da alamu saurayinta ne ya kira,don sunyi doguwar waya sosai,har aka gama yiwa amarya sakina qunshinta da qawarta da sukazo tare,ango yazo daukarta,dukka suka tashi mata takiya,munira na cewa sai sunje sun gaisa.
Ko alamar motsawa iman batayi ba,amma munira ta finciki hannunta,dole ta bisu.
Yana jingine jikin fara qal din motarsu,wadda da alama sabuwa ce,su biyune shida wani matashin saurayin kamarsa,cikin fara'a da barkwanci irin na angwaye da qawayen amarya,tana tsaye daga gefe tana kallonsu,don ita komai ma sabo ne a wajenta,saboda wannan shine karonta na farko na bikin qawa a waje,ko cikin dangi ma ba kasafai take zuwa ba saboda nisa da suka dan mata,daga na uwa har na uban,sai dai daiku dake nan garin da suke.
Kowa cikinsu ta fara gabatar masa da kanta da kuma sunanta,har aka gama,munira ta waiwayo
"Matso mana iman" abinda yaja hankalin angon da abokin nasa kenan"
Idanu abokin ya zuba mata sosai,ya furta
"Subhanallah" har zuwa sanda ta iso idanunsa yana kanta
"Itama cikin qawayenku take?" Saurayin me suna hashim ya tambaya bayan ta gama gaidasu
"Eh....iman,ba kasafai ta fiya son shiga jama'a ba ai"
"That's good" ya fada yana gyada kai,still ita yake kallo,abinda yasa ta takura kenan,taja da baya tana fadin
"Bari naje kafin ku gama,kada azo kanmu babu kowa"
"Wait iman....ki tsaya ki karba kudin liqi mana" kafada ta daga
"A'ah,na gode sosai wallahi" daga hakata qara sauri tayi ciki tana mita cikin ranta,gaba daya batasan me yasa mazan yanzu suke da shegen kallo ba.
Basu jima sosai ba suka dawo,sauran su uku kenan da suka rage ba'a yiwa ba
"Haba iman.....haba da Allah,me yasa kike abu kamar baki waye bane,ke dan samarin nan ma na yayi da akeyi ki kasa yi,guy iya haduwa amma ki yarfashi ki taho,ke kinga yadda ya rude da zancanki bayan kin taho,Allah annabi a hadaki dashi?,at last dai dole muka bashi number dinki" idanunta ta zaro
"Me yasa zaku bashi don Allah,me yasa zakuyimin haka?" Ta fada adan rude,dukkaninsu suka sanya dariya
"Seriously da gaske nake,yanzu me zance da ya al'ameen idan yaga wani ya kirani?"
"Waima.....wai.ya al'ameen,to meye a ciki?,shi kansa yasan kin isa a kirakin,waima idan bai bari an kirakin ba,jiqaki zaiyi yasha?,a yadda Allah ya halicceki iman saidai idan ba zaki dinga fita ba a gida zaki boye kanki" munira ta qarashe bayanan suka kuma goyi bayanta
"Gaskiya kam,koni da za'a bani dama yaya na zan yiwa kamu" budurwar da ta taimaka mata dazu ta sanya baki a hirarsu,kowa ya sanya dariya.
Ko a jikin munira ta qara gaba ta cire dan kwalinta don a fara yi mata gyaran gashi,yayin da iman ta dinga binta da harara tana gasa mata ita.
Daidai sanda aka gama musu wayar muniran ta dauki tsuwwa,ta daga da hanzari
"Ina zuwa.....Allah bazanyi missing ba,gani nan zuwa" shine abinda muniran ta fada tana maida wayarta jaka
"Don Allah don annabi qawalli ki rakani kamun nan,ban zaci abun haka aka shiryashi ba sai yanzu da batula ta kirani,ba zamu jima ba in sha Allah zamu taho,kinga hanya daya zamuyi,gida zan koma zan debo kayana,sai gobe zan wuce gaba daya" da farko uzuri ta bata kan yamma tayi sosai,kafin suje ma magariba tayi,kuma malam yana fada idan tayi dare a waje,haka ya al'ameen,da qyar munira tasha kanta,tace zata rakata har gida ta yiwa inna bayani,zannan ta aminta,nan cikin kayan data amso dinki ta zabi daya daga ciki ta sauya,ta kuma biya aka mata lite makeup,tayi tayi iman ta dauki wani a ciki itama ta sauya tace aa,kayan jikinta sun isheta.
Tun daga shigansu wajen iman ta tabbatar lallai bikine na manya,wadanda sukaci suka tada kai,wani mahaukacin gida ne mai dauki da tafkekiyar haraba,wanda ama qawata ta da decorations irin na biki,duk yawan jama'ar dake wajen ta daukesu tsaf,harda ragowar sararin da motocin gidan ke fake abinsu basusan anayi bama.
Tunda suka shiga din iman ta samu seat ta zauna,daga inda take din tana iya hango yadda komai ke wakana,amarya tayi kyau iya kyau tare da angonta,sai gudanar da komai ake cikin fariya boko da kuma nuna wadata.
A hankali ta daga kanta ta kalli yadda sama ta fara duhu,alamu suna nuna anyi kira sallar magariba zuwa yanzu,duk da bata iya jiyo kiran ba saboda tashin kidan daya karade wajen. Kome take kuma ko a ina take bata wasa da salla,haka aka tarbiyyantar da ita,don haka ta laluba wayarta ta fara kiran munira babu qaqqautawa,wanda sai a kira na biyar ta samu ta daga,tace mata gatanan zuwa,ba jimawa kuwa sai gata,da alamu biki yayi biki
"Nifa zan wucw gida gaskiya,gashi har anyi sallah mu bamuyi ba"
"Don Allah ki bani minti goma kacal,ummi ce zata bani saqo na tafi dashi" mahafiyace,ba zata iyace mata karsu jira ba,saita rausaya kai
"Idan na koma gida malam ya koroni kyasan inda zakiyi dani,kaini wani wajen nayi sallah" dariya ta saki
"Ba korokin da zaiyi,ya kori auta ai babu wannan maganar,muje na rakaki" tare suka jera da ita,saidai duk inda suka gifta sai an kalli iman din,yawanci kallo ne na baqunta da kuma tsarin surar da Allah yayi mata,wadda ta fita daban data sauran mata.
Ganin yadda hanyar shiga gidan ke cike da mutane sai iman din ta dakata da bin munira
"Gaskiya ki samarmin wani gurin inda zan kebe ni kadai nayi sallata,cikin gidan nan da alama a cike yake,kuma ni babu wanda na sani" tayi qoqarin nuna mata babu komai ta shiga amma tace a'ah,don haka ta jata can bayan gidan,inda garden din gidan yake,wanda ke wadace da grass carpet,da kuma famfunan da ake bawa lambun ruwa
"Yauwa,yanzu naji daidai" iman din ta fada tana ware idanunta cikin wajen saboa yadda ya birgeta,wata iska ta daban wajen yake fitarwa,bugu da qari shuru yake kamar ba cikin gidan dake cike da hayaniyar biki yake ba
"Ki kirani idan kin gama saimi wuce,ni hutun sallah nake"
"Baki da matsala,amma dana gama zazu zamuyi gida"
"In sha Allahu" ta fada tana juyawa da sauri zuwa ciki,iman ta bita da kallo,cikin ranta tana mamakin yadda muniran ke bala'in son alaqa da masu kudi,take kuma qaunar bikinsu,saita dage kafada,qila don ta taso taga haka danginsu yake.
A hankali take takawa zuwa wajen wani famfo daketa zuba shi kadai yana aika ruwa zuwa sasannin shuke shuken dake fadin lambun,ta tsaya a gabansa cikin nutsuwa,ta waiga ta tabbatar babu kowa,sai ta fara ware lafayar dake jikinta don kada ta jiqe,ta ajjiyeta gefe,ta daura alwalar,sannan ta dauketa ta yafata a matsayin mayafi kawai ta tada sallarta,sai data idar sannan ta miqe,ta zameta daga kanta ta fara daura abarta a jikinta.
Sau uku tana nadata tana jin batayi mata dai dai a jikinta ba,karo na hudu taja tsaki ta fara warewa da xummar sake daurawa
"Kawo na tayaki tunda kin kasa" sautin muryar daya daki dodon kunnenta kenan wanda ya razanata,ta kuma rude gaba daya,ta damqe lafayar tata da hannayenta gaba daya,a kuma matuqar tsorace sannan a razane ta waiwaya don ganin waye?,daga ina kuma ya shigo ko ya fito?.
*ZAFAFA BIYAR*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*13
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
____________________________________
Matashin saurayi ne tsaye a bayanta,fari qal,wanda har wani yellow yake saboda haske,ma'abocin kyau na gaske,wanda fuskarsa ta cika da baqin gemu da kuma sumar kai,ba siriri bane kamar yadda yake ba mai qiba ba,jajayen lips dinsa dauke suke da murmushin da ya bayyana fararen haqoransa,yana sanye da wata muguwar shadda daketa faman zuba qyalli da maiqo,ruwan hanta wanda ta dace da fatarsa da kuma fitar da kyansa muraran,hannayensa na goye qirjinsa,wanda hakan ya bayyana muqullin motar dake soke cikin daya daga cikin 'yan yatsunsa.
Tsoro ya sanya ta sake ja da baya ganin yadda yake ci gaba da kallonta,murmushi shimfide saman fuskarsa,cikin wata murya mai zaqi ya sake cewa
"Gashi nadin yayi miki kyau sosai da sosai,saidai kuma kuma baki iya daurawa ba,halan mama ce ta daura miki kafin ki fito?" Rasa amsar bashi tayi sai idanu da take rarrabawa
"Wannan auta ce da alama" ya sake fada yana komawa da baya a hankali ya zauna saman kujerar concrete dake wajen,har yanzu bai janye idanuwansa daga kanta ba,hakanan murmushin da yakeyi baibar kan fuskarsa ba
"Iman.....iman" sautin muryar munira ya fara shigowa wajen,da alama ita take nema
"Uhunnn.....da alama ke suke nema,abokan tafiyarki ne ko?" Ba tare daya jira amsarta ba ya dora
"ki daura abarki,lemme close my eyes" ya fada yana lumshe qananun kyawawan idanunsa.
Ta tabbatarwa kanta ba zata iya fita a haka ba,saboda al'ummar dake harabar wajen sun ninka shi a yawa,saita leqa a hankali,ta tabbatar da gaske idanunta a rufen suke,don haka cikin sauri ta fara daurawa.
"Are you finished......an min izini na bude idanuna?" Ya fada a tausashe
"Eh" ta amsa cikin sanyi,ya bude idanun nasa tarwai saman fuskarta
"Wow.....wow I didn't realize yadda ta miki kyau kamar yanzu da nake kusa dake, please ke wanne yare ce?......i think kanuri ne suke amfani da ita ko?" Yadda yayi maganar har saman fuskarsa ya nuna da gaske so yake ya sani,don haka ta gyada kai
"Eh sune"
"It means ke din kanuri ne?" Kafin tace komai munira ta iskota
"Canza waje kikayi kenan inata bul......" Maganarta fa maqale a maqoshi sanda idanunta suka sauka a kansa,saita rusuna da sauri cikin girmamawa
"Yallabai barka da yamma" cikin wata dakiya wadda bada ita yanzu yanzu suke magana da iman ba yace
"Barka" kafin wani a cikinsu ya sake magana wata muryar ta sake cika wajen da kiran sunan
"Bassam.......bassam"
"Hey guys.....wannan kiran fa?" Ya fada yana daga sautun muryarsa dake da zaqi,wanda har sai da iman tadan sake kallonshi.
Mutum biyune suka qaraso wajen,dukkansu samari ne da kana musu kallo daya zakasan sunaji da jini da ajiki da kuma tashen samartaka,kowannensu kalar shigar dake jikinsa zata fallasa maka wadatar da yake ciki
"Shege....baka da mutunci wallahi,na dauka da gasken kayi tafiyarka" daya daga cikinsu ya fada yana cika yana batsewa,tare da jifansa da harara,baki ya tabe kamar yadda mata kanyi
"Gab nake da tafiyan ai,rabo yasa na ratso ta nan" yayi maganar kansa tsaye yana nuna iman da yatsan hannunsa,dukka suka waiwaya suna kallonta,abinda ya sanyata gaba daya taji ta tsargu ta kuma takura,
"Rabon samun matar aure" kamar saukar tsawa iman taji maganar,wanne irin magana ce wannan yakeyi,bayan har yanzu basu zarce mintuna ashirin da fara ganin juna cikin rayuwarsu ba,batasanshi ba bai santa ba,har yanzu ko kalma daya tak bata furta gareshi ba,saita rutsashi da kallon mamaki,ganin haka shima ya tsareta da nasa kallon tare da murmushi mai qawatarwa
"Yes,da gaske nake" ya tabbatar mata yana lumshe idanunsa tare da budesu a lokaci guda
"Muni......qawarki ce?" Daya daga cikin wandanda suka shigo wajen ya tambaya,cikin murmushi tare da madaukakin farincikin da muniran keta qoqarin dannewa tace
"Eh yaya ahlan,aminiyata ce......"
"Zaku iya bamu waje mu tattauna?" Matashin da aka kira da bassam ya fada still bai iya dauke dubansa daga kan iman ba,sai ahalan din yaja da baya
"Baka da matsala,but kada ka dade da yawa"
"Alright" ya amsa a taqaice,dukkaninsu sai suka juya suka fara barin wajen,yayin da iman ta bisu da kallo cikin taraddadi,tamkar ta bisu amma ta gaza daga qafarta daga wajen.
"Have a seat please" ta tsinci muryarsa yana tsaye daga bayanta kamar wani bodyguard da uban gidansa,ya tashi daga mazauninsa ya bata daman zama,bata da abun cewa illa qarasawa da tayi,a hankali ta zauna kamar yadda ya buqata,saidai bata wani saki jikinta ba kamar wadda ke dosane saman garwashin wuta.
Qarasowa yayi a hankali,ya shimfida handkerchief a gabanta qasa saman grass carpet din yayi xaman dirshan,tazarar dake tsakaninsu ba me nisa bace,saidai bai kusantota da yawa ba,ya aza mata dukka idanunsa sannan ya fara magana da ita.
"sunana bassam balarabe madaki....." Kai tadan daga kadan ta kalleshi,kamar tasan sunan,kamar tana dan jinsa cikin kafafen yada labarai
"Nine da na uku a wajen mahaifina,da na farko a wajen mummy na,shekarata ashirin da da takwas,'yan kasuwane mu duk da muna karatun boko me zurfi,hasalima nine jagoran dukka kamfanonin madaki general enterprises,ban taba aure ba,saidai for now zan sanya damba,domin kuwa naga matar aure,sai kuma inda qarfina ya qare,ki daga kanki ki kalleni da kyau kiga nayi miki ko banyi miki ba,saboda ni din mutum ne kaifi daya,banason boye boye kuma ban iyasa ba....."shuru ne ya ratsa tsakani,bata ko motsa ba bare ta daga kai ta kalleshi,sai wani bugu da zuciyarta keta famanyi,saboda tsayin rayuwarta bata taba tsaiwa da wani da sunan saurayi ko soyayya ba saishi.
Duk yadda yayi kan ta dubeshi ko tace wani abu taqi,har wayarta ta dauki tsuwwa,sunan inna ya bayyana,abinda ya sanyata miqewa zumbur kenan
"Innata ke kira,tun daxu muka fito,kuma tacemin kada nakai dare a waje" tayi masa bayanin tana qoqarin bin bayan kiran inna daya katse.
Wayar ya zubawa idanu har zuwa sanda kiran ya shiga,a dan rude takewa innar bayanin gata nan a hanya,bata saurareta ba sai fada da taketa tsula mata kamar xata rufeta da duka ta cikin wayar,dai dai sannan munira ta sake shigowa.
"Kije xan rakota zamu fito" amsar daya hawa munira kenan,saidai kafin ya miqe iman har tabi bayan munira,cikin azama ya cimmata suka jero.
Sai gaba daya ta duburce saboda yadda idanuwa suka dinga yawo a kansu,suka dinga jan hankalin mutane,ta lura sam ko a jikin bassam,sai hira da yake janta dashi cikin lanqwashashiyar murya,idanuwansa a kanta duk bayan sakan uku zuwa biyar,har suka qaraso parking lot na gidan.
Milk color din wata jibgegiyar mota ya bude mata yana fadin
"Bismillah" baya taja,idanunta na nuna alamu na tsoro
"Xan qarasa titi nahau napep" waiwayawa yayi ya kallo munira
"Ke baki gaya mata anguwarnan ba'a samun abun hawa na haya ba?"
"Bata sani ba" munira ta amsa masa cikin wani salo na yauqi irin na 'yammatan da suke ji da kansu
"Ok,muje na fitar dake titi a motar,amma bisa sharadi daya......idan ba'a samu abun hawa ba,zan kaiki unguwarku" a jikinta takeji zaa samu,don haka tace masa ta yarda,saiya gyada kai yana murmushi
"Allah kasa nayi winning", ya fadi harda daga hannayensa sama,tadan dauke kai kadan yana son bata dariya ganin yadda ya haqiqance bilhaqqi.
Wani sassanyan qamshi ke tashi cikin motar,ko ba'a gaya maka ba kasan turaren da yake amfani dashine ya hadu da qamshin freshener na mota da kuma sanyin ac ya bada wani yanayi me mugun dadi,tun daga waje dama zakasan motar sabuwa ce,cikin motar kuma shi xai qara tabbatar maka da hakan.
Addu'ar bassam itace taci kuwa,don sun jima suna tsumayin samun abun hawa saidai babu shi,dole hakanan tana ji tana gani suka dauki hanya zuwa unguwarsu,zuciyarta ta dinga bugun uku uku,ranta cike fal da tsoro da kuma fargabar kada ta hadu da wani dan gida.
Tunda suka soma tafiya yake janta da hira,cike da nuna tsantsar kulawa da wani salo dake nuna zallar shauqi,baiji kunya ko nauyin ganin idanuwan munira ba ya dinga fayyace mata zuciyarsa,kalamansa suka dinga yi mata nauyi aka,har kunya tasa ko cikakken motsi ta kasa,karo na farko da wani ya zauna yana shirya wasu manyan kalamai wai duk don saboda ita,ta yadda lallai kamar yadda ya gaya maya ne,shi din bashi da boye boye ko kuma rufa rufa,a haka har suka iso dab da layinsu,tasa ya ajjiyeta daga baya baya.
Har tasa hannu zata buda murfin motar da hanzarinta,ya danna mata Lock
"Ya zaki tafi ki barni haka?,babu gamsashshiyar amsa,sannan kuma babu madafa,so koke gobe ayi jana'izata?"
"Me kake buqata?"
"Phone number dinki" ya amsa mata kai tsaye,so take ya barta ta wuce don haka ta fara karanta masa yana serving,duk da haka bai barta ba har sai daya kira yaji ta shiga sannan yace
"Thank God" ya furta yana fitowa shima da sauri dava motar,ya zagayo inda take ya bude mata cikin girmamawa.
Waiwayowa tayi ganin ya fara take mata baya yana biye da ita kamar wani bodyguard,ta buda baki zatayi magana,ya ritsata da kallon nan nasa
"Tattaki zan miki angel...."ya amsa mata tambayarta tun batakai ga yinta ba
"A'ah,don Allah ka bari,wallahi na gode,zan qarasa,munira zata rakani" hannayensa ya sanya ya rufe fuskarsa kadan yana furzar da iska
"Banso kika dakatar dani ba....but,ba yadda zanyi,abinda zuciyarki keso ya zama kamar umarni ne a gareni.....munira" ya kira sunan muniran da tayi mutuwar tsaye a gefe
"Ki kulamin da ita,har ku isa gida banaso ku quda ya tabata.....deal" tunda ya fadi hakan tasan me yake nufi,ko banza yau za'ayi mata yayyafin kudi,tasan a zaune take wannan,haka suka jera da iman din zuwa cikin layinsu,bassam ya bita da idanu,yana jin kamar ya hadiyeta,wani wawan kamu soyayyarta tayi ma zuciyarsa,irin kamun da ba'a taba yi mata irinsa ba,bayajin zai iya haqura da yarinyar ba tare da ya mallaketa ba.
*ZAFAFA BIYAR*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 14
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
_____________________________________
Cikin wani irin zumudi da zakwadi munira tayi hanzarin kamo iman suka jera
"La'ilaha illallahu,wallahi kin cika 'yar baiwa iman.....dama ni jikina yana bani ke matar manya ce,da alama ke zaki zama tararuwar gidanku.....iman,kinsan kuwa waye bassam a karan kanshi kafin akai ga mahaifinsa?,kinsan yammatan dake layi da kai kawon kama qafa dashi?,bakya amfani da social medias ne,amma da basai na gaya miki waye bassam ba" hankalinta duka yayi gida,saidai tana saurara gami da fahimtar kowacce magana ta muniran ke magana akai
"To sai akayi yaya?"
"Don girman Allah kada kiyi mana baqulu da baqinciki,don wallahi bake kadai ba,hatta ni na warke,na kuma sake zama babbar yarinya,don Allah kada ki qauron baki,kada kice baki sonshi,saboda bassam irin mazan da kowacce mace ke buri da qauna ce" munira ta fada tana marairaicewa
"Nifa tsaya kiji,na yiwa ya al'ameen alqawarin bazanyi soyayya da kowa ba" idanu munira ta fitar kafin ta maidasu
"Kamar yaya?"
"Eh,yace idan lokaci yayi zai fitarmin da miji" dariya ta saki sosai cikin nishadi
"Dalla can,ashe ke baki da wayo,ya fadi hakane fa a sannan saboda qananun shekarunki,kada farinjinin da kike dashi maza suyi amfani da kya da kike dashi su yaudareki,amm kawo yanzu ai kinkai munxalin fara zance ma,tunda dukkanmu zance muke,ga wasu ma an fara aurarwa,koshi yaga bassam zai miki sha'awarsa,zai kuma so ya zama surukin gidanku" kai iman ta kada
"Duk abinda ya al'ameen ya fada yana nufin abinda ya fada din"
"Ikon Allah,nifa ban ganewa wannan dagiyar ta ya al'ameen ba,banda yayanki ne ai da sai nace ko kansa yakewa tanadi ne?" Waiwayawa kawai tayi ta kalli muniran,saita dauke taci gaba da tafiya batace komai ba,kunnuwanta na sauraren magiyar muniran kan kada ta tankwabar da soyayyar bassam kamar yadda ta yiwa dan uwata sadam
"Ke kamar bakisan rayuwa ba iman,wasu har rubutu da maganin farinjinin samun mai kudi ake musu,ke kuma kin samu daga Allah amma zaki wofantar da damarki,ki godewa Allah wallahi,koda bakison sadam ko qawance kukayi wallahi saikin tserewa sa'a a cikin dangi da qawayenki,saikin wuce kallon raini,ke ba zakisan haka ba,amma ni naga abubuwa da dama kuma ina kan gani cikin dangin umma na,saboda mahaifina ba kowa bane,mahaifiyata tana auren mutumin da ba wani ba" wannan hirar ita ta kaisu ga qofar gidansu iman,wanda babu mutane sosai,sai dai daikun daliban malam da suka dawo daga gurare daban daban akayo gida kuma,wasu na cin abincinsu na dare wasu na hira,saboda yau din ba ranar karatu bace,uwa ba kuma alamu na nuna malam din baya kusa ma.
Kallon da inna ta watsa mata sanda ta shiga shi ya sanyata ta shiga taitayinta,munira ta qaraso ta rusuna gaban inna
"Don Allah inna kiyi haquri,wallahi gidan qanwar umma ta rakani,ummance kuma ta tsaidani zamu amshi saqo mu taho mata dashi,don Allah inna kiyi haquri,laifina ne"
"Allah ya tsare gaba,amma ku kiyaye,kada ku bari ku dinga yin dare a waje,'ya'ya mata ne ku"
"In sha Allahu inna,ayi haquri,na gode" munira ta fada tana miqewa,suka qarasa dakin iman din
"Don Allah qawa na roqeki,nasan zai kiraki,koda baki sonshi ki tsaya ki saureshi a rabu lafiya" munira tace da iman cikin lallabawa sannan ya fito bayan sunyi sallama.
Kayan jikinta ta fara cirewa ta sanya na zaman gida,sannan ta daura alwalar sallar isha'i,ta dawo dakinta ta tayar,data idar tayi zaune saman abun sallar,tana jin gajiya na nuqurqusarta,ta daga kai ta dubi agogo,bataji duriyar alameen ba,da alama bai dawo bane,da tuni ya nemeta.
Idanunta suka sauka kan ledar da munira ta ajjiye mata me kayan takeaway na bikin data hadota dasu,ta janyo ta bude ta gani,su souvenir's ne kala kala harda na banza da rashin sanin ciwon kudi,sai kuma kayan ciye ciye.
Jakarta ta zaro cikin kayan ta bude don ciro wayarta,hannunta ya sauka kan wasu abubuwa,ta zazzagesu da hanzarinta. Sabbin kudade ne fil a miqe,yan 200 bandir guda,idanu ta fiddo waje cikin tsoro da mamakin yadda akai kudin suka samu,sai kuma tayi tunanin na munira ne,tunda jakar na hannunta,don haka ta dauki wayarta ta cire lock din ta fara qaqarin nemanta,saita ga alamun tex,ta buda don duba daga ina yake.
Ta zaci daga kamfanin mtn ne,don su kadai ke tura mata saqo,saidai a yau din akasin hakanne,don kuwa wata tsararriyar number ce dauke da wani zazzafan saqo,wanda ke cike da wasu shiryayyu kuma tsararrun kalamai dake nuna zallar shauqin soyayya da ma'abocin saqon ya tsinci kansa a ciki.
Sau uku tana karanta saqon tana komawa farko,sai daga qarshe idanunta suka kai kan sunan bassam,ta maimaita sunan sannan ta goge saqon da sauri,zuciyarta na bugawa,ta fita ta kira munira
"Kinyi mantuwar kudinki cikin jakata fa"
"Ba nawa bane,naki ne,bassam yace a baki" kicin kicin tayi da ranta
"Amma me yasa zayimin haka?,kinsan dai bana karbar kudin kowa ko?ko sadam da yake dan uwanki ban karbi kudinsa ba kin sani,bare wannan da bansan kowa nasa ba"
"iman.....wai me yasa kike haka ne?,kinsan dai babu kyau maida hannun kyauta baya ko?,ya zaa dinga miki alkhairi kina qin karba?"
"Na karba idan an gani a gida nace me?"
"Dama ni bance ki nuna ba,idan kinsan za'ayimiki fada ki ajjiye abinki ki dinga zara kina amfani dashi"
"Banaso munira,kizo kawai ki karba abinda ki maida masa" dariya taji ta qyalqyale dashi
"Toni ina zan ganshi yanzu?,bayan kin fita daga motar naji yana waya,a taqaice dai a abuja zai kwana ba'a kano ba,sannan na riga da nayi masa alqawarin zame masa jagora wajen samunki,kinga idan kina tsoro ma kina iya bashi dama yazo gida yaga malam......hakan zaisa kuyi tarayyarku babu tsoro ko shakku,kiyi amfani da kudinki kawai malama,sai da safe" munira ta katse wayarta abunta ta barta da waya a hannu.
Karar shigowar kira ya sanyata zabura,saura kadan wayar ta subuce a hannunta,tayi qoqarin saka wayar a silent sannan ta nutsu ta duba me kiran,idan har idanunta dai dai suke nuna mata number dazu ce data tura mata saqo,saita samu kanta da latsa ok,ta kara wayar a kunneta.
Zazzaqar muryarsa ce ta fara dukan kunnenta,a hankali ta amsa masa sallamarsa
"Kin tafi kin barni da kewarki,inajin kamar ba awannin da suka shude bane muka rabu,kamar wasu shekaru ne suka raba tsakaninmu....." Yayi maganar cikin salon iya jan hankalin diya mace,da kuma zallar qwarewa wajen sace zuciyar diya mace
"Don Alla kice wani abu kafin zuciyata ta fashe imani......zuciyata ta kamu da mahaukacin sonki,wanda har ta fara hasashen yadda rayuwa zata kasance mata babu ke". Wata ajiyar zuciya cw ta subuce mata saboda nauyi da kalamansa suka fara yiwa zuciyarta
"Me zance maka to?" Ta samu kanta da furtawa
"Koda bakice komai ba ki saki jiki ki bani dama,don koda baki fada ba na samu labarin nine mutum na farko da zan fara bude zuciyarki,so inason ayimin alfarma a kuma bani dama,nayi dashe me kyau,wanda zai bada kyakkyawar yabanya......don Allah beauty" ya qarashe maganar cikin marairaicewa.
Murmushi mara sauti ya subucewa fuskarta,ashe itama watace,ashe takai a gaya mata kalamai har haka anema soyayyarta,itama ashe takai,kalaman baqine ga kunnenta,saboda haka nan da nan ta sake ta bashi kunnuwanta,yayi amfani da wannan damar ya dinga mata hira me matuqar dadi,yana kodata gami da yabata takowanne fanni,tare da kuranta matsayin data samu cikin 'yan daqiqu,da kuma yadda zuciyarsa ta mato mata.
Kiran sunanta da taji inna nayi daga tsakar gida ya dawo da ita daga nisan kiwon da tayi,cikin hanzari ta katse wayar,ta kuma kasheta gaba daya ta tura qasan filo,cikin yanayi rashin gaskiya ta kwasa ta yiwo waje da sauri ta tsaya kan inna
"Gani inna" kallo ta bita dashi a nutse kafin daga bisani tace
"Me kika shiga daki tun dazu kika zauna kinayi ko abincinki baki dauka ba?"
"Sallah nake inna?"
"Qara'insu kikeyi?" Da sauri ta girgiza kai
"A'ah inna,isha'i ce kawai,gajiya tasa dana gama nadan kwanta,kinsan munsha zaman lalle"
"Yayanki ya shigo,bakiji shigowarsa ba?" Tayi mamaki,don har ga Allah bataji shigowar tasa ba da gaske,karo na farko da irin hakan ta faru,don babu wani abu dake shagaltar da ita ta kasa jin shigowar al'ameen din
"Banji ba inna,gyangyadi ya saceni" ta fada tana istigfarin qaryar data sharara
"Dauki abincinsu kikai musu,daga nan ki cewa sadiqu yazo ina kiransa"
"To inna" ta fada tana daukar babban farantin kayan abincinsu tayi dakin.
Kamar ko yaushe sai data tsaya tayi sallama aka bata izini sannan ta cusa kai,dashi idanunta suka fara karo,hannunsa riqe da wayarsa yana kallon wasu styles na dogayen riguna daya dora a account dinsa na Instagram,wanda bai jima da budeshi ba bisa shawarar sadiqu.
Sexy eyes dinsa da suka sake lumshewa saboda gajiya da yunwa ya buda a hankali ya sauke a kanta,ta qaraso a nutse ta ajjiye farantin
"Sannu da zuwa yaya"
"Yauwa queen.....ya gida?"
"Lafiya lau yaya,ya aiki"
"Alhmdlh,zubamin abincin" ya fada yana zamowa daga saman kujerar zuwa qasa,hankalinsa akan lallenta baqi da ja wanda yayi masifar zanuwa saman farar fatarta me haske sosai
"qunshin yayi kyau sosai queen" ya samu kansa da fadi sanda take qoqarin zuba masa abincin,saita daga kai suka hada idanu,cikin jin nauyinsa tace
"Na gode yaya"
"Amma garin yaya kikayi dare haka?" Dan raurau tayi da fuskarta
"Allah yaya munira na raka wajen event din cousin dinta,kuma ta yiwa inna bayani"
"Ki kiyaye please,kinga ke Queen ce,bai kamata sarauniya guda a dinga ganinta a araha a waje ba har dare" murmushi ya sake subuce mata,ta gyada kai tana murza yatsun hannunta,daidai sannan sadiqu ya fito daga bandaki
"Zubamin nima ina zuwa,abu me sanyi yau nake sha'awar sha" ya fadi yana nufar qofa
"Inna tana kiranka ma"
"Tom" ya qarashe amsa matan yana ficewa.
Yana cin abincin yana satar kallonta,sake kyau da zama cikakkiyar budurwa take,hatta da fuskarta ta nuna hakan balle gangar jikinta,kamar ma so take ta haura shekarunta,tana dagowa suka hada ido,sa ya mata nuni da wata leda
"Ga mayafinki can" cikin murna ta tashi ta dauko tana dubawa
"An gode yaya,Allah ya qada budi,amma yaya kala biyu ne fa"
"Wannan zai hau kowanne kaya cikin ankon,kiyi amfani dashi,daga baya saina sama miki dayan" kai ta gyada kawai,amma bataso hakan ba,saboda anyi duka qawayensu kala daya zasu saka.
Tana maidashi cikin ledar sadiqu ya shigo da lemukan a hannunsa,ya miqa mata wasu
"Ki dauki daya ki kaiwa inna sauran" ta karba tayi godiya sannan ta fice.
A wajen inna abincinta ta karba tace zataci a daki,hankalinta da tunaninta duka ya koma kan wayarta,koda ta shiga dakin,kunna wayar shine abu na farko data fara yi,tana gama kunnuwa saqonni suka fara rigen rigen shigowa a jere kusan guda biyar,saita koma ta zauna,murmushi na subuce mata tana qoqarin budawa ta karanta.
[7/19, 10:01 PM] Mummyn Yara: 15
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
_________________________________
Dukkan saqonnin nasa suna tafe da kalaman dake nuna rudun da ya shiga kan katsewar wayar da kuma jinta a kashe da yayi bayan ya sake kira,magiya yake mata kan ta taimakeshi ta buda wayar tata,ta daure tayi kiransa,murmushi ta kuma saki,yanzu kashe wayarta kawai ya sanyashi a damuwa?,wanne irin so ne wannan?,har ta dannan kiransa ta fasa ta katse,ta ajjiye wayar ta jawo abincinta tahau ci,saidai tana ci gefe guda kuma zuciya da qwaqwalwarta suna dawo mata da abubuwan da suka faru wunin yau,tun daga haduwarsu kawo yanzu,duk kyanta da yake fadi gani take ya fita,saita miqe ta isa gaban mudubi tana qarewa fuskarta kallo,kalamansa a kanta na dawowa kanta turyan turya,sai ta kuma sakin murmushi,ta juya ta dauki kwanon abincinta da kayan ciye ciyen bikin da muniran ta hadota dashi don ta kaiwa inna ko zata iya cin wani abun a ciki.
***********Washegari*******. Da saqonsa tayi karin kumallo,wasu irin shiryayyun kalamai dake dauke da dandasa dandasan kalaman zallar soyayya,dolenta murmushi ya subuce mata bayan ta kammala karantawa,yakansa ta shiga mamakin wai ita din me muhimmanci ce har haka?,itama ashe watace data cancanci samun qauna maqura?,tana wannan tunanin saiga kiransa,ta sake yin sauri wajen saka wayar a silent.
Sai data katse ya qara kira sannan ta daga
"Beauty.....girmanki ne,amma kuma so kike na haukace na kasa aiwatar da abinda ya kaini abuja?kinsan kuwa samun hadin kanki shine kawai abinda zai bani nutsuwar aiwatar da abinda naje yi din?" Murmushi ta saki a boye
"Ni wacece da hakan zata faru da kai?"
"Kina mamakine ko kina tantama?,lallai da alama har yanzu bakisan irin matsayin da kike dashi a wajena bane,kinsan tunanin kina da wani masoyin da ranki keso kadai daga jiya zuwa yau ya sanyani nayi zuru zuru,zakiyi mamakin yadda na koma,please beauty......kicemin ni kadai ne wanda ya fara yaqin neman soyayyarki,duk nasan mafarkine kawai nakeyi,amma mace kamarki lodi lodin maza nasan ke gware a kanta" yadda yake maganar cikin laushi da sanyi ya bata dariya,har batasan tace dashi
"Kai kadai ne" ba,wani qaramin ihu ya saki,wanda yake nuna zallar farincikin da zuciyarsa ke ciki
"Yes.....kice na sanar da mommy a daidai" idanu ta zaro
"Me?" Ta tambayeshi cikin mamaki da fargaba
"Eh, already labarinki yaje wajen mommy,tun a jiyan ban iya barci ba sai dana gaya mata komai dana sani game da ke,infact ma ita harta matsu taga beautyna,na gaya mata,ta qara haquri har na shawo kanki tukunna"
"Bassam" ta kira sunanshi a karon farko
"Nifa na yiwa yayana alqawarin bazanyi soyayya da kowa ba, already ma yace shine zai zabarmin miji" wani mummunan faduwa gabansa yayi,take ya rikice mata,har abun yayi matuqar bata mamaki,da gaske yake kan duk abinda ya fada,da gaske ne yadda yake kururuwar sonta
"Please give me a chance beauty,ki bani dama....na miki alqawari indai na kasa sace zuciyarki da samun soyayyarki zan amshi sunan looser,zan kuma rabu daki,amma na tabbata yayanki baya nufin abinda ya fada" sai data ce ta bashi damar sannan taji salama da sukuni cikin muryarsa.
Da hanzari tayi masa sallama tana katse wayar,ganin ya kusa cinye mata lokacin aikinta,ta cusa wayar qasan pillow,sannan ta janyo dankwalinta ta daure sassalkan gashinta ta futo tsakar gida,qirjinta cike fal da bitar kalamai da al'amuran da suke gudana tsakaninta da bassam,tun daga haduwarsu kawo yau.
Tana tsaye a kitchen tana dama kunu,tayi nisa cikin tunaninta,a hankali ya qaraso bakin qofar kitchen din,idanunsa suka sauka a kanta
"Assalamu alaikum" yayi sallama cikin tattausar muryarsa dake cike da wata irin nutsuwa ta halitta,ta waiwayo a hankali suka hada ido,sai ta saki murmushi tana dan motsawa kadan
"Wa'alaikumussalam,ina kwana ya amin"
"Lafiya qalau queen,ki tashi lpy?"
"Lpy qalau....."
"Ma sha Allah,na godewa Allah da queen ta tashi lpy" murmushi ta sake,sai taji kalamansa na mata kama dana bassam
"Zan samu ruwan dumi?" Tunda taji haka tasan daga motsa jiki ya dawo,shi yasa suk safiya bata rabo da ruwan dumin saboda shi,matuqar tana kitchen din,tasan yana shigowa zai nema
"Eh yaya" ta fada da sauri,tana juyawa zuwa inda ta ajjiye flask din ruwan zafi,ta fara zuba masa,idanunsa na biye da ita.
Daidai yadda tasan zai iya sha ta zuba ta miqa masa,hannu biyu yasa ya karba
"Na gode" murmushin da ya sake fidda dimple dinta tayi,tana jin kunya ta masa abu ya gode mata.
Ta zaci fita zaiyi a kitchen din,amma sai taga yaci gaba jingina da qofar,yana kurban ruwan yana binta da kallo,yana monitoring duk wani motsinta,wutar qaunarta tana sake ruruwa cikin ransa,yana jin cewa lokaci kadan ya rage komai yazo qarshe,banda ma delay da ya samu naci gaban karatunsa yadda yaso,da tuni zuwa yanzu komai yayi nisa,saboda ya riga ya tsara ci gaba da karatun iman din a gidansa,hankalinsa sai yafi nutsuwa da hakan
"Akwai wani abune yaya?" Ta tambayeshi cikin jin kunya da kuma nauyinsa,miskilin murmushinsan nan mai cike da nutsuwa da wata izza izza ya sake,ya tashi daga jinginar da yayi ya tako zuwa kitchen din,ya dora mata cup din kusa da ita
"Babu komai.....kawai ina kallom queen dita yadda take qara girma kullum tana zama 'yar budurwa"
"Kai yaaya" ta fada da sauri tana sunne fuska,shi kuma ya saki 'yar qaramar dariya mai sauti kadan,ya taka ya fita a kitchen din.
Wunin ranar gaba daya bassam bai barta ta huta ba,kowanne motsi nashi sai ya gaya mata ga abinda yakeyi,duk wani schedules nasa daga safiya zuwa dare tsaf sai data sani,tamkar tare suke aiwatar da komai.
Ko wajen kamun surayya haka tayita fama da saqonninsa,yayin da munira ta hanata sakat da zancansa,batasan ya akayi ba sai ji tayi qawayenta sun fara tsokanarta da MRS BASSAM,kowacce a cikinsu cewa take
"Gaskiya ba qaramar sa'a kika taka ba,yaro ne matashin saurayi da jini ke zagayawa a jikinsa,yaro ne da kudi amma hausawa sukance abokin tafiyar manya, friend dina ne a insta,kije kiga yadda 'yammata ke rushing a kansa,daya daga cikin qawayensu ta fiddo wayarta,ta shiga account dinsa na Instagram ta buda mata hotunansa ta miqa mata.
Ta jima riqe da wayar a hannunta tana bin duk wani abu nashi daya dora a can,ta yadda da duk abinda suka fada din,daga kan hotunansa dake kan shafin nasa zakasan ba qananun kudi yake riqewa ba,kowannw hoto sutturu na alfarma ne a jikinsa,rabu da matan social media da kyakkyawan namiji,tarin followers ne dashi jingim maza da mata,abun ba'a cewa komai,kowanne hoto nasa ko wata magana da zaiyi,zaka tadda tarin comments da likes rututu a qasanta,ta sake gyara zama tana bin wallafar tasa.
Ba qarya bane,komai yaji tattare da bassam din,ta sauke ajiyar zuciya tana sakin murmushi sanda wata 'yar ajinsu da ba wani magana suke da ita can can ba ta shigo tana tsokanarta itama da mrs bassam
"Ya hadu guy din,bazan boye miki ba,nayi iya qoqarin na sameshi,to amma nasan ni ba type dinsa bace,shi din sai kyawawa dama irinku,ina tayaki murna gaskiya iman" murmushi kawai iman din ta bita dashi tana sake maida idanunta kan fuskar bassam.
Kwana biyu sukayi suna casar biki,tana zaune qawayenta nata liqi wa amarya,saboda tasan ita din bata da kudin da zatayi liqin,sai daga bisani ta bude jakarta dauko wayarta don duba lokaci,batason ta sake dare kamar na rannan idanunta suka sauka kan kudin da bassam din ya bata,bata taba komai ba a ciki banda kudin transport datayi musu ita da qawayenta,saita zari masu yawa a ciki,itama ta isa saman stage t fara liqawa ango da amarya,take taji kanta daidai da sauran qawayenta dake wajen,suka dauki ihun sai mrs bassam,abinka da zuciya da kuma aikin dan adamtaka,sai taji kata yana fasuwa a hankali,sannu sannu sai datayi liqi me yawa da ya sanya mc kama sunanta sannan ta sauka ta kona gurin zamanta,cin maganinta ya sanya samari da yawa dakeson kawo mata caffa suka kasa qarasowa inda take.
********Washegari**********
Wunin sakina,ranar ne kuma za'a kaita,saidai dukkaninsu basuje ba sai yammaci,dukka qawayen suka hadu,cikin daya daga cikin lafayoyinta da bata taba sanyawa ba ta shirya kanta,duk tafisu tsada shi yasa ta zabi ta sanyata,milk color ce me haske,sai adon gold a jiki,takalmin qafarta me tsini ne kuma mai tsinin dunduniya,ta ciki wani lace ta sanya mara nauyi,wanda ya amin yayi mata dinkin straight skeet da riga me dogon hanu,ta tara gashinta tayi masa nadin alkaki ta qasan daurinta samfurin ture kaga tsiya.
Fadin kyan da tayi a lokacin bata bakine,saika rantse da Allah daga gidan wasu hamshaqan ta fito,saboda kulawa da take samu gami da sutura me kyau,kowa kaffa kaffa da dama dama da ita yake cikin qawayenta,abinda ta lura dashi ya fara faruwa tun sanda munira ta shaida musu bassam shine masoyinta
"Komai yaji,wanka iya wanka,amma wallahi kika fito da wayar hannunki sai naji kamar zan nutse" munira ta fada dai dai yadda iman dince kadai zata iya ji.
Sauke wayar tayi tana duban munira,wanda dama ta dauko wayarne saboda jin qarar shigowar saqo,wanda kuma take da yaqinin ba daga kowa yake ba illa bassam
_"Kinyi kyau iya kyau baby.......,yanzu na shigo gida daga tafiya,amman bazan iya daurewa ba.....sai nazo naga wannan kwalliyar beautyna"_ wannan shine saqon da taci karo dashi,wanda mamaki ya kamata kan ta ina ya hangi adonta.
Maimakon ta bawa munira amsar maganarta saita buge da tambayarta
"Ya akayi bassam yaga kwalliyata?" Idanu munira ta wara
"Wallahi ban sani ba,shida baya nan yana abuja?"
"Ya dawo gida yanzu,kuma yana zancan zuwa ya ganni ba tare daya nemi address ba,bari naga gudun ruwansa,ta ina zai lalubo ni?" Ta fada tana gyara zamanta gami da gyara rufin lafayarta.
Murmushi munira ta saki
"Har yanzu bakisan waye bassam ba,mai kudin da idan yaso zai iya sanin duk wani motsi naki,amma bari mu gani,da rabon muje gidan amarya a lafiyayyar mota" munira ta fada cikin murna,batabi ta murnar munira ba,don tasan babu lallai yazo din,tunda baisan ina suke ba,saita dan goce kadan ta jingina da kujerar dake daura da ita.
A hankali zuciyarta da qwaqwalwarta suka shiga tunani,suka shiga hasko mata fuskokinsa data gani cikin hotunansa na ista cikin mabanbantan yanayi da shiga kala daban daban,tarin tulin 'yammata daketa commenting akai,da kuma qoqarin jan hankalinsa zuwa private chat,a hankali taji shauqin son ganin fuskar tasa na saukar mata,saita lumshe idanunta tana bitar lausasan kalamansa da suka zame mata abokai cikin kwanakin nan,dasu take kwana dasu take tashi,ta kuma hadasu da fuskarsa iya shiga da tsari na jikinsa,take taji komai yayi mata dari bisa dari,sai ta lumshe idanu tana sauraren hirarrakinsu,tare da kasa kunne taji xai kirata ko zai turo saqo ya nema address?.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: *_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM_*
16
Taji mamaki sosai sanda yake shaida mata yana qofar gidan,ta dubi munira duban tuhuma,ta daga hannayenta sama alamun ba ruwana.
A matuqar darare fa shiga motar sanda ya bude mata da kansa ya mata izinin shigar,shima saboda idanuwan yammata dake qofar gidan ana shirye shiryen daukar amarya da sukayi musu caa kamar zasu cinyesu.
Nannauyar ajiyar zuciya ya saki yana shafar qirjinsa
"Thank God,sai yau dana ganki sannan naji kamar an ciremin qaya, beauty,i really missed you" kunya ce tadan saukar mata,taja lafayanta ta sake boye fuskarta ta murmushi
"I liked it baby,inason kunyar nan taki,amma dai ya kamata adan fara rageta,a nunamin soyayya ko?".
Hira yake janta da ita sosai cikin wani salo da yasan yana tafi da zukatan 'yammata,ya hada mata abubuwan sha da ci duka cikin motar saman dan wani abu da ake janyowa me kama a table,saidai taqi taba komai saboda bata saba ba,ba zata iya cin komai a gabansa ba,uwa uba kuma a takure take jinta,ga kalamansa daya cikata dasu wadanda suka yiwa kanta nauyi,taketa jin kunyar yadda yake marairaice mata kamar zai kwanta aka ta soshi don Allah,yayi alqawarin zai mallaka mata komai.
Abinda bai sani ba tuni ya fara barin burbushin wani abu a cikin zuciyarta,ya sanya zuciyarta ta fara narkewa da kadan da kadan,hakanan tanajin wani abu na tabata duk sanda ta kalleshi,ta kuma tabbata kowacce mace ma dole taji irin wannan,saboda dan gayu ne iya gayu,wanda gayun ga hade da kyau da kuma ilimi quruciya da kuma wadatar arziqi.
Kafewa yayi kan shi zai kaita gidan amarya,bazai barta tahau motar kowa ba,nan kuwa ta samu qawayenta 'yan tayi,kowacce tace a motar itama zata,a haka suka dibi mutum hudu daga cikinsu suka wuce.
Ko a hanya ma bai barta ba,hira yake mata qasa qasa cikin kalaman da zasu iya wafce ko sace zuciyar kwacce irin mace,idam yaji tayi shuru cikin murya me kama da rada zaice
"Uhmmm baby......baby kice wani abu mana,don Allah karki haukatani" wani abun ko bataso saita amsa masa.
Da suka isa ma hanata fita yayi yaci gaba da dasa mata dashe me wuyar cirewa,su sauran suka shige ciki,sai da yaga an ragu sannan ya mata tattaki har qofar gidan ta shiga,sannan ya daw jikin motarsa ya jingina yana jiranta.
Tana shiga kamar dama jiranta sukeyi kowacce ta shiga ihu da kuma zolayarta
"Ku keshan soyayyarku,amma nice nake sumewa" inji zee qawarsu
"Gaskiya gaskiya kika bar wannan guy din kin tafka asara,keee.....me tsada be wallahi wannan,samun namijin da komai yaji a tare dashi kamarsa ai abune me wahalar gaske,tabdi,gaskiya kin shiga sahun mata masu sa'a a duniya" daga daga cikinsu ta sake fada
"Banda zaman amana ake ai ni zanyi wufff dashi" batasan ta jefa mata harara ba sai da suka kwashe mata da dariya
"Almura,ashe ya fara sace zuciyar da akaqi bawa kowa dama". Haka suka hadu sukayita yi mata cari.
Duk yadda taso ya barta ta samu abun hawa na haya ta koma gida yaqi ji bare gani,duk ta gama tsurewa,yayi parking qofar wani babban store ya fita bayan yace tazo su shiga tare amma taqiya.
A qalla kusa minti talatin ya barsu cikin motar ita da qawayen nata kafin ya dawo,siyayya yayi mata mai ubansun yawa data sanya iman din tsurewa,ya dubi su munira yace su shiga ciki su karbo sauran kayan duka nasu ne.
Sai da suka fita ya fidda wasu qananun leda guda biyu,daya daya bude wani dan qaramin akwati ne me azabae kyau,zobe ne a ciki me bala'in kyau da daukar idanu ya miqa mata
"Saka,so nake naga yadda zaiwa kyawawan hannuwanki kyau" ya fada yana murmshi,yadda ya tsareta da kallo ya sanya dole ta saka zoben,ko don ta tsira daga kallon da yake jifanta dashi
"Ma sha Allah,da dama da nayi kissing wannan kyawawan yatsu,Allah ya mallakamin su" tsananin kunya ya hanata magana,sai kawai ta janye hannun nata ta boye cikin mayafi.
Leda ta biyu still shima wani kwalin ne,wanda ke dauke da wata santaleliyar wayar hannu,wanda ko ba'a gaya maka ba kasan cewa ba qaramar wayar bace,bawai a girma na jiki ba,a'ah,kudaden da aka zuba kafin a mallaketa.
Miqa mata wayar yayi,ta janye hannunta taqi karba tana dubansa
"Na siyeta ne saboda ke,an saita komai da komai nata,akwai layi a ciki,na siyeshi ne saboda ni kadai,nafison duk sanda na kiraki na sameki available" babu jan dogon bayani tace mishi ba zata karba ba,yaji babu dadi har saman fuskarsa,saidai a nata ganin haka shine daidai,don batasan inda zata sanya wayar ba.
Wannan dalili yasa ta kasa musanta masa sanda ya bata gift na ledar daya loda mata siyayya,suna tafe munira na mata rakiya kamar kowanne lokaci,saidai jikinta asabule yake
"Munira,nufar gidanmu fa kike da wadan nan kayan"
"Na sani,ki tsaya ki gani mana" ta bata amsa babu alamun damuwa a tattare da ita.
A bakin famfo suka samu inna tana tarar ruwa a buta,da alama bandaki zata zagaya,ta daga kai tana amsa sallamarsu,cike da ladabi kamar kullum munira ta gaida innar,ta amsa mata tana tambayarta mutanen gidan,ta soma gajiya da ganin yarinyar tare da iman,bata fiyason mu'amalar iman din da baqin fuskar qawaye ba,duk da dama silar bikin sakina ne ya kawota gidan.
"Inna wai kaya ne da sakina ta bayar a rabawa tsakaninmu qawayenta da muka yi mata hidiman biki,shine nace ta ajjiye mana a wajenta,idan yaso in an tashi sai a raba,sai iman din ke tsoron kada ki fada,shine nace bari na roqeki don Allah"
Idanu innar ta sauke kan ledar da muniran ke nuna mata,kowaccensu tayi shuru tana jiran jin amsar da innan zata bayar,kamar ba zatae komai ba sannan ta amsa
"Ba damuwa,amma karsu jima,banason ajiyar abinda ba naka ba"
"In sha Allahu inna" daga haka ta miqawa iman ledar,sukayi sallama ita ta juya ta fice.
Cikin kwanakin gaba daya bassam ya sanya wuta wajen nema soyayyar iman din,ya kuma ci galaba da gagarumar nasarar da bai taba kawowa kansa zai samu ba,ita kanta iman din ta fada wani muguwar soyayya da bata taba tunanin zata fada ta ba,sannu a hankali ta dinga ganin kyan da bassam da kuma sauran jama'a ke kururutawa tata,ta kuma hango dacewar da sukayi da bassam din. Da kuma dacewarsa da zamantowarsa miji a gareta.
Ta samu sakewa da dukka kaya da siyayyar bassam sanda taje maiduguri ta dawo,saita sanya dukka kayan cikin tsarabar da yagana tayi mata,a zuwan ita ta bata su,ta fidda fella fellan laces din ciki ta bawa al'ameen ya dinka mata.
Haka kawai yaji jikinsa yayi sanyi sanda ya bude laces din xai dinka,tailor ne shi da yasan aikinsa,ya kuma san kudin kaya masu tarin yawa,a idanu kawai akace ka yiwa lace din kudi kasan ba qarami bane bare aje ga ainihin kudinsa,kusan guda uku ne kuma dukka haka suke.
Yagana 'yar kasuwa ce,tana kuma samu sosai da kasuwancinta,to amma kuma laces din sunyi tsada da yawa,saidai daga bisani ya gargadi kansa,yakuma share maganar cikin ransa,tunda ya riga ya aminta da wace iman din,rainonsa ce,ta kuma tsotsi tarbiyya daga inda suka tsotsa,wato wajen inna da malam,ya budesu yayi mata dinkuna masu kyau,da suka sanya ta dinga murna sanda ya kawo mata su,ta kuma ajjiyesu,batayi amfani dasu ba sai da bikin murjana,daya 'yar ajintasu.
Ta fita sosai cikin qawayen nata,ta kuma fita daban,ta haska yadda ya kamata,ta dinga jin kanta yana fasuwa cikin qawayenta,saidai tayi qoqari matuqa wajen hana kanta jin izza ko girman kai.
Kasancewar bassam ma'abocin tafiye tafiye ne,baya nan akayo bikin murjana,yaji babu dadi sosai,saboda yaso su kasance tare a lokacin,don har yanzu abu na gaba da yake buri da buqata shine ta gabatar dashi a gidansu,ya samu 'yancin zuwa ganinta kai tsaye a duk sanda yaso.
Saidai ita a nata bangaren cike take da tsoro da kuma fargaba,tsoron yadda zatayi bayani wa malam inda ta sanshi,a inda suka hadu,da kuma yadda akai har suka saba babu wanda ya sani,ina zatace ta samu lasisi ko kuma umarnin sauraronsa,uwa uba kuma ta sani,burin ya ami tayi karatu,basuyi cewa zata gabatar da mijin aure a dai dai wannan gabar da take aji biyar a makarantar secondary ba.
Duk da baizo ba amma tuni wayarsa ta samu baquncin hotunanta tsala tsala ta hannun jakadiyarsa munira,wanda suka sake haukatashi tare da susutashi,suka kuma sanyashi qara daura damara da cin burin kasancewa da iman din,da kuma maidata ta zama matarsa kuma mallakinsa,ko me zaya kashe kuwa.
Tafiyar al'ameen zuwa jigawa garinsu ya sake qulla wani sabon kusanci da kuma shafin soyayya tsakanin iman da bassam,saboda wayarsa daya bar mata aro kafin ya dawo,ita kuma tayi amfani da wannan damar,ta bude account na Instagram WhatsApp da Twitter,yadda zata samu damar ganin bassam din yadda ranta yakeso.
Ta kuwa kalleshin,babu wani hoto nasa data tsallake ba tare data masa kyakkyawan kallo uku ko sama da haka ba,gayu iya gayu,kudi iya kudi ta gansu,gefe guda kuma ga ilimi kamar yadda take da sha'awa,daya qyalla idanu ya sameta ta WhatsApp kuwa kamar zaiyi me saboda murna,hakan ya sanya ta sake zama mayyar waya,kullum tana manne da ita a daka,Allah Allah take ta gama abinda take ta dauki wayarta su kasance tare.
Tuni inna ta fara lura da canje canjen dabi'u da kuma halaye tattare da iman din,abinda yasa ranar da amin ya dawo daga qauye,suna tsakar gida,inna na saman babbar tabarma,shi kuma yana kan kujera 'yar tsuguno yana bawa inna labarin ci gaban da qauyensu keta samu,iman din na saman tabarma daban,ta tattara hankalinta gaba daya saman wayar,abinda yaso jan hankalinsa kenan,duk da suna hira da inna,amma kusan bayan kowanne minti sai ya daga kai ya kalleta,yasan cewa ba haka suka saba da ita ba a lokaci irin wannan daya dawo daga tafiya,tana nuna kewarta sosai a kanshi,abinci na musamman take masa,ta hada da ruwan zafi na wanka takai masa,yana cin abincin tana damunsa da hirar abubuwan da suka faru bayan baya nan,shima kuma tana tambayarsa abubuwan daya gani da sauye sauye da aka samu.
Miqewar da tayi yasa inna tace
"Ina zuwa?" Fuska tadan ya mutsa kadan
"Kwanciya zanyi inna,na gaji" idanu ta kafeta dashi
"Me yake damunki ne kwana biyu da kika koyi kwanciyar wuri?"
"Kawai inna,saboda makaranta ma,da shirye shiryen qualifying da mukeso mu fara" sam maganar bata shigeta ba bare al'amin,wanda ya maida kansa ga qaramar keypad din daya tafi da ita,yana serving station din da yake yawan sauraran labarai a cikinsu
"Wannan wayar ke daukan hankalinki iman......" Maganar da taso tadan tsoratata,amma saita dake,saboda tasan halin innar da matuqar bin qwaqwaqwafi
"Games ne da yawa na dauko inna,kuma inajin dadin yi"
"Dole ki maida masa wayarsa,tunda tana neman canzaki" saita marairaice cikin tsoro da faduwar gaban kada a yanzu yanzu innar tace ta miqa masa abarsa tunda ya dawo,kafin kuwa ta gama tunanin nata abinda ta zata din ya afku,innar tace da ita
"Bashi wayarsa maza,tunda Allah ya dawo dashi lpy alhmdlh,aikin mori abinda kika mora,dama kullum malam cikin fadan me yasa ya barta a hannunki yake"
"Don Allah inna........"
"Karki min magiya"
"Zan karba gobe inna,ki qyaleta" al'ameen ya shiga maganar,saboda ko waye mutum komai qanqantarsa bazaiso irin wannan titsiyen ba,zuciyarsa kuma fes take kan iman din,baya shakka ko zargin zata aikata wani abu ba dai dai ba,ko kuma ya saba da tarbiyyan gidan,yadai bata uzuri kan cewa rashin sabo ne,da kuma daukin wayar tunda ta jima tana sonta.
_________________________________
*mg's skincare*
Shin Ina matan suke🗣️🗣️🗣️maza kuhanzarta kumatso kusa kuma kubani aran kunnuwanku domin sanin albishir dawannan shahararran company yazo muku dashi😃🤩
Hakika tabbas duk macen data amsa sunanta bazataso afita b Koda da kwayar zarra domin hakane wannan shahararren company yazomuku da ingantattun hadaddun kayan gyaran jiki masu matukar gyara fata cikin kankanin lokaci batare da sunyima fata lahani ba domin kayan mg's organic products ne bawai na bleaching ba zasu gyara ma mutum fatane yafiddomashi da ainihin natural beauty din mutum👌hakika duk wacce batayi anfani da kayan mg's b anbarta acan karshen bayama kuwa domin Koda sabulunsu kadai kuka dana fatanku seya fita dasauran mata ballentana Kuma kuyi anfani da gbdy beauty kit dinsu wohoho wani abun baa mgn sewanda yajaraba shine zai tabbatar❣️
Shin kinafama da
Pimples, black spot,sunburn, stretch mark,acne,black head, wrinkles,knuckles dama duk wani matsalan fata?
Shin fatanki tana tattarewane ko kinshafa cream yabatamiki jiki😫
Shin inamasu cewa sunjaraba Basu dace b bi'iznillah sister's duk Wanda yayi using mg's sai godiya domin Koda iya herbal whitening black soap din kikayi anfani dashi zakiga ynd fatanki zaiyi clear Yana walwali jikinki zeyi fresh kina glowing my dear bare Kuma ace set dinne gbdy 🤗ga amare uk wnd yy using bridal set dinnan baya bukatar kowani gyaranjiki domin yadda jikinki zekoma yazarce misali DNT be left behind
Bridal kit:18k
Beauty kit:11k
Student package:7k
Herbal whitening soap:3k
Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Facebook: mg's skincare
Instagram:glow_with_mgs
Take note pls iya wadannan numbers dinne kawai zakusamu kyn mg's babushi akasuwa🤝
Do you guys wanna achieve that milky skin that turns head wherever you go🤩
Then @mgs skincare gat you covered 💯
Now is time to glow😍
Pamper ur skin🦵
Shine like bride👰🏻♀
Glow🧖♀️
💯 tested nd trusted🤝
Guarantee
Sannan muna da hadaddun frames masu kyau gamai bukata yayi mgn 07046881166
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 17
_YERWA INCENSE AND MORE: MASARAUTAR KAMSHI:_
_THE SCENTS WITH DIFFERENT ESSENCE FOR YOU AND YOUR HOME_
_DO YOU WANT THAT MAIDUGURI AND SUDANIAN SCENTS THAT LASTS LONGER AND LINGERS? YERWA INCENSE AND MORE GOT YOU AND YOUR BELOVED ONES COVERED WITH LUXURIOUS SCENTS. KAMSHIN YAN YERWA DA SUDAN💘🙏 20% OFF ORDERS. MUN CIRE KASO 20 NA KUDIN KAYAYYAKIN MU_
_KHUMRAHS_
_KULACCAMS_
_TURARUKAN WUTA_
_NA TSUGUNNO_
_NA KAYA_
_NA GIDAH_
_NA GASHI_
_NA WANKA_
_NA WANKI_
_NA MOPPING_
_AIR FRESHENER_
_CURTAIN AND CHAIRS SPRAY_
_WARDROBE BALLS_
_SCENTED PEBBLES_
_ARABIAN OIL PERFUMES_
_HAIR SPRAY AND CREAM_
_DILKE AND HALWA SET_
_KABBASA_
_BURNERS_
_KASKO_
_TONGS_
_COAL IGNITERS_
_SKIN CARE PRODUCTs_
_OUR TURARE SAMPLE SETS_
_BRIDAL SET (SAITIN AMARE)_
_KUJERAR TSUGUNNO_
_SABULAI NA GYARAN JIKI DA SAURAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAMSHI . KOMAI DA KOMAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA_
_MUNA TURA KAYAYYAKIN MU A KO’iINA A FADIN NIJERIYA DA KETARE_
_SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH, 100% TESTED AND TRUSTED_
_instagram:yerwaincense_and_more_*
_WhatsApp: 08095215215_
__________________________________
Washegari bai karba wayar ba kamar yadda yace din,saboda sabgoginsa na dinki da kuma neman samun damar ci gaba da karatunsa da yaketa fafutuka,saidai a ranar yanajin yadda inna ke mitar yadda iman din fa tashi a makare ta fara ayyukan gida,wanda saboda quracewar lokaci bata samu gama aikin ba,inda daga qarshe ta shirya ta wuce makarantar a makare,innan kuma ita ta qarasa sauran aikin da ya rage din.
Washegari qarfe takwas saura minti biyar na safe ya fito a shirye zashi su hadu da mutumin daketa masa fafutukar ganin ya samu tallafin karatu,ya gaida inna dake dauraye flask din malam na kunu sannan ya tambayeta malam,tace yana qofar gida,ganin takalman iman na makaranta yasa ya tambayi inna iman dun bata wuce makarantar ba?
"Ina zata wuce,ta zama abunda ta zama,babu abinda ta iya sai kasala da sakalcin banza" sai yaji a ransa indai waya ce take sanyata hakan bai kamata ya barta da ita ba,don ko a jiya da daddare yana jin bambamin sadiqu kamar zai bugeta kan yace fa.kiqo masa abinci ta shantake,dama kuma can sadiqun zafi gareshi,bai cika haquri ba,don haka sai ya qarasa rumfar inna da kansa.
Sallamarsa da shigowarsa gaba daya yayita,tana zaune a qas tana saka farar safarta,ta daga kai tana murmushi gami da amsa sallamar tasa,gabanta yadan fadi da fari,saboda ganin da tayi ya danyi mata zubi da bassam saboda adon da yayi
"Ina kwana yaya?" Maimakon ya amsa mata sai ya maida mata da tambaya yana dan tsuke fuska
"Me kike har yanzu baki tafi makaranta ba?"
"Yaya makara nayi wajwn tashi"
"Kin fara wasa da karatunki ko?" Saita girgiza kai
"Aah yaya,bacci ne......"
"Is ok,idan na dawo zan karbi wayata,ki sakamin a charge idan sun kawo wuta tayi full" a sanyaye ta gyada kanta,sam batason ya karba wayar,saidai......wayarce ta shiga ranta ko kuma alaqarta da bassam ce bataso ta yanke?.
Tare suka fita shi da ita,sai daya sanyata a abun hawa ta tafi sannan ya tari nasa yahau,kasancewar ba hanya daya zasuyi ba.
Tun a makaranta ta turawa bassam saqon maida wayar,ta kuma goge duk wani account da wani abu daya shafeshi,kama daga hotunansa daga tuttura mata,da kuma saqonnin sms,sai data tabbatar bata bar komai akai ba sannan ta maida wayar tata jaka,saidai rabi da rabi na karatun ranar ba shigarta yake ba,tana can ga tunanin yadda zasuyi kewar juna ita da bassam din,ta saba chart dashi,kuma yafi.mata dadi akan kiran ways,a chart dinne take sakewa sosai ta gaya masa sirrikan zuciyarta.
*********Goma da rabi na daren ranar,wanda tayi dai dai da kwanaki biyu da amsar wayar daga hannun iman din,har ya gama shirin kwanciya saboda sammakon da yakeson yi gobe zuwa shagon dinki don kammala dikunan wasu amare,sai kuma ya miqe ya jawo locker dinsa sake jikin katifarsa,ya dauko wayar ya sanyata a charge,saboda tunaqa da yayi zai turawa wani mutum photon wasu takardu nasa.
Gefan katifar ya koma ya zauna yana jiran charge din yadan hau,saboda bashi da tabbacin akwai charge akai,ya bata mintina goma sannan ya koma gaban socket din ya zauna yakunna wayar,bayan ta daidaita ya shiga gallery dinsa ya fada laluben hotunan takardun,tunda already yana dasu,saidai sama ko qasa ya rasasu,ya dinga kaikawo bai gansu ba,har zai haqura ya sake sabbin dauka,duk da yasan ba zasuyi kyan wadancan ba,saboda wadancan din anyi scanning dinsu a computer,sai kuma ya tuna,ya wuce zuwa recycle bin na wayar.
Tun daga farko ya fara cin karo da hotunan da baisansu ba,bai kuma waye mai su ba,sa'an nan baisan mutumin dake jikin hoton ba rututu masu yawan gaske.
Sosai kansa ya daure,ya dinga bin hotunan da kallo daya bayan daya,mamaki na sake cikashi ta yadda hotunan suka shiga cikun wayarsa.
Sannu a hankali ya gangaro kan hotunan iman,iman dinsu dai,cikin salo na gaye da kwalliya,hotunan da sukayi masifar kyau suka kuma fidda duk wani kyau da Allah ya bata,duk da cewa shigarta bata bayyanar da tsiraicinta ba,amma kyan da tayi cikun hoton,kyau ne da bai taba ganin tayi irinsa ba a zahiri.
Gaba daya qwaqwalwarsa so tayi ta tsaya da aikin yin kowanne tunani bare ta bashi hint na abinda ke faruwa,saboda yadda ta dode gaba daya kamar bata taba wani tunani ba,sai ya koma ya zauna dirshan sanda kwanyarsa ta taimakeshi ta tuna masa cewa iman itace mutum ta qarshe da wayarsa ta jima a hannunta.
Wani mummunan faduwa gaban al'ameen yayi,har yaji kamar an samu wani abu an buga masa akai,gudun zuciyarsa ya dadu sosai,sai ya sauka da sauri,ya koma binciken wayar,bakinsa cike da addu'o'i cikin rudewa.
Duk inda ya shiga babu komai an share,manhajar WhatsApp itace abu na qarshe daya duba,ba tare da yana da wani yaqini na samun wani abu ko hujja ba.
Ga mamakinsa yana shiga WhatsApp din ya bude sarai,da alamun account din da akayi amfani dashi shine har yanzu kan wayar ba'a shareshi ba.
Suna da hoton dake kan number farko kuma qwaya daya dake kan account din gaba daya ya sanyashu furta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" dukkan wata dakiya da jarumta tasa ta fara zagwanyewa lokacin da ya fara bin chart history din,yana karanta hirarrakin da akayi cikin inbox din,wani irin gudu zuciyarsa taci gaba dayi kamar zata faso qirjinsa ta fado waje,kunnuwansa sukayi dummm wanda ya dauka har tsakiyar kansa,a hankali cikin wani salon sanda feeling na daina gane abinda ke kewaye dashi ya fara kutsawa cikin jikinsa,yana aikawa kowanne sashe na jikinsa,a hankali ya daina gane komai da kowa sai zallar tashin hankalin daya tsinci kansa a ciki,tashin hankalin da yayi masa ba zata,tamkar zuwan ajali ga dan adam.
A hankali sai wayar ta gagara riquwa a hannunsa,ya zameta a hankali ya saketa gefansa,ya koma ya zauna sosai yana son fahimtar da kansa abinda ke faruwa,kamar bashi da idanunsa ya gani ba,saidai kuma wani sashe na kwanyarsa na gaya masa,ba iman dinsa ba,ba iman dinsa bace,hala ta bada aron wayar itama ga wani,idan ma ita dince ko dai wasa take?.
A sannan ji yayi babu abinda yake da buqata banda yaga iman a gabansa ya tambayeta abinda ke faruwa,yana da burin idan ta tashi amsa masa ta amsa da cewa wasa take,ba da gaske take ba. Ba tare da la'akari ko kuma duba da cewa dare ya fara yi ba ya miqe da hanzar ya nufi qofar fita,yana so ya sadu da ainihin cikin gidan.
Garam sukayi karo da sadiq dake shirin shigowa da ledar balangun da ya tafi siyo musu,saboda dukkanins mutane ne masu son cin dadi a bakunansu,hakan bai basu matsala ba,saboda kowannensu neman kudi yake tuquru
"Haba mana master......saurin me kake?,gani na dawo,wajen ne akwai layi,kasan ya iya gashi" ja baya yayi yana duban sadiqun da yake mulmula goshinsa,wanda shi sam bai ma damu da nasa goshin da ya buge ba,saboda rudanin da yake ciki,gaba daya ma ya manta wai sadiq din ya tafi siyo musu nama.
Idanu sosai sadiqu ya zuba masa yana masa wani baqon kallo
"Amin.....lafiya kuwa?,wani abu ya faru ne bayan na fita?" Qafafunsa dake a mace kamar lawashin da yasha rana ya fara janyewa da baya da baya,bayan hankalinsa a sannan yakai kan agogo,ya kuma tabbatar bazai iya shiga cikin gidan a yanzu ba,sabosa bai taba shiga din ba idan ba wani abu bane ya taso
"Babu komai" ya amsa ma sadiqu yana zubewa gefan katifarsa,tare da yin hobbasa na ganin ya saisaita mood na fuskarshi
"Koda naji" sadiqun ya fada yana cire takalmansa ya dorasu saman abinda suke dora takalma dake bakin qofar dakin sannan ya shigo,ya bude musu naman yana bawa amin din labarai kamar yadda suka saba duk dare kafin su kwanta.
Idan yace yana gane abu daya da sadiqun ke fada to tabbas ya zabga qarya
"Ya baka cine?,wai anya lafiya kake kuwa?" Kalmar da sadiqun yace dashi kenan yana rutsashi da ido,abinda yayi silar daya ringa miqa hannu ya a zaqular naman yana hadiyewa ba tare da ya tsaya cikakkiyar taunawa ba bare ya gane wanne irin taste gareshi,haka ya dinga tsaya masa a maqoshi kamar wanda ke cusa dan wake,abinda yayi sanadiyyar qwarewarsa kenan yahau tari,wanda ya sarqafeshi sosai,sai da yasha ruwan sanyin da sadiqu ya bashi sannan ya lafa,da wannan ya fake yaje ya kwanta,saboda qirjinsa da ya dauki zafi,sadiq yace may be ko ulcer dinsa ce ta motsa kuma.
Tunda ya kwanta idanuwansa a rufe suke gam,ko qwaqwaran motsi baya qaunar yaji a kusa dashi bare magana ko surutu,lokaci bayan lokaci yana bude idanunsa ya sauke ga agogo,yana qididdigar mintunan da suke gabansu kafin wayewar gari.
Zuciya da tunaninsa sunkai sun komo,ya kuma rasa a wanne bigire zai ajjiye tunani da zuciyarsa,karafkiya qaryata juna da sa'insa babu kalar wadda ba'a samu ba tsakanin sashe biyu na zuciyar dake qirjinsa,wata zuciyar na rinjayar da qaryar cewa ba iman bace,haka ba zata faru ba,yayin da wara zuciyar ke tabbatar masa da iman dince,saidai ta aikata komai ne bisa rashin sani,koma meye ya riga ya yankewa kansa hukunci kawo qarshen komai,koma meye zai faru ya faru,qirjinsa bashi da qarfin daukar zuciyar da zata rasa iman haka cikin sauqi,saima ya korewa kansa wannan tunanin da yake kallonsa a baqi kuma mummunar fata cikin rayuwarsa.
Dai dai lokacin da iman din take can kwance saman tata katifar a zahiri,a badini kuma tayi matuqar yin nutso kuma me zurfi cikin kogin qaunar bassam,wanda ta ara masa daqiqa masu dama yana sake karanta mata yadda qaunarta ta tashi zuciyarsa a aiki,irin girma da kuma matsayin da take dashi,abinda ya sake sawa taji kanta ya fasu,alfahari da samun bassam da kuma soyayyarsa ta shigeta,ta bude masa tata soyayar sosai wadda ta narkar da ilahirin zuciyar bassam,ya kuma dauka mata alqawura masu matuqar nauyi a mizani,girma kima da kuma martaba cikin duniyar soyayya,wanda daga qarshe sukayi tarayya kan alqawari guda,duk rintsi.....duk wuya.....suna tare,babu gudu kuma babu ja da baya,dukkan wanda ya sauka daga kai ko kuma ya sauya,la'ana da kuma hukuncin cin amana yahau kansa.
Wannan kusan itace hira mafi dadi da sukayi da bassam a wajenta tsahon tarayyarsu,domin kuwa ko bayan ya sauke wayar sun rabu kasa runtsawa tayi,murmushin dake kan fuskarta cikun duhun dakin yaqi barin fuskarta,hirarraki muryarsa da gwala gwalan kalamansa sukaqi barin qirji da zuciyarta,ta dinga tariyarsu tana jin wani dadi qauna da shauqi yana sake kamata,zuciyarta jaririyar zuciya ce,wadda ta fara soyayya ta zahiri a karon farko,don haka komai baqo ya kasance mata,sai daga bisani fa samu baccin yayi awon gaba da ita,cike da mafarkan bassam,wanda a ciki har ya zama miji a gareta.
Kwata kwata baccin da yayi tsahon daren dukansa bai wuce na awanni uku ba,suma din a tsitstsinke,a kunnuwansa akayi kiran asubahi,yayi alwala suka fice masallaci tare da sadiqu,wanda hakan al'adarsu ce,kuma acan suke tadda malam.
Miqewa sadiqu yayi ya dubeshi bayan an idar da sallar,wasuma har syn fara watsewa
"Nikam yauma idan zaman azkar dinkan nan zakayi saidai mu hadu a gida,don wallahi jiya kwata kwata bacci bai isheni ba" ya fada yana miqa
"Shikenan,saina taho" ya amsa masa yana sake maida kansa qasa,don bayason sadiq din ya fahimci bai samu bacci ba.
Yana kallon sadiq ta qasan idanunsa har ya fice,hakanan yaji bazai iya komawa cikin gidan ba,ya kintata wani lokaci ne da zai cimma iman,duk da cewa yau tana da makaranta alhamis ce.
Cikin wani nishadi da walwala take zuba kunu da awarar data soya cikin cup da plate don taci ya wuce makaranta,ta gama shirinta tsaf,kana duban fuakarta zakasan wani nishadi takeji,bassam ya raya darenta ya kuma qawata mata safiyarta da kyakkyawan saqon barka da safiya.
Ta juyo zata fito kenan yayi sallama bakin qofar kitchen din,idanunsu suka shiga cikin na juna,sai ta hangi baqon yanayi tattare dashi,saidai bata kawo komai ba cikin ranta ta zarce da gaisheshi,ya amsa mata yana nazarinta
"Akwai ruwan dumi?" Ya tambayeta yana jingina da qofar kitchen kamar yadda ya saba,tsaiwarsa kwnan duk sanda zai karba ruwan,duk da yawanci a gajiye yake shigowa dama saboda exercise da yakeyi,sabanin yau,da babu execise din da ya iya fita,saidai zuciyarsa a jigace take qwarai,wanda hakan yayi tasiri har zuwa gangar jikinsa,ya matsu ya kuma damu ya fidda abinda yake zuciyarsa da ransa komai da komai ma ya huta
"Yaaya...gashi" ya tsinci muryarta tana masa magana,da alama tun daxu ta zuba ta miqa masa,sai ya karba ya fara kurba a hankali,bayan ya matsa mata hanya
"Idan kin gama ki dauko litattafanki ina jiranki" har tadan dakata sai kuma ta amsa da to tayi gaba,kasancewar ta saba lokaci lokaci yakan rakata,koda ba har makaranta ba to xai kaita bakin titi,saidai a kwanakin nan abun yaja baya.
*_LITATTAFAN ZAFAFA BIYAR_*
_BIYAR : DUBU DAYA (1k)_
_HUDU: 700_
_UKU: 500_
_BIYU: 400_
_DAYA: 300_
_AKWAI TSARIN VVIP SUITES GA MASU SON HAKAN. FARASHIN SU DABAN, DOMIN KARIN BAYANI SE A TUNTUBE MU TA: _
*_ZAKU BIYA KUDINKU ANAN👇👇_*
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya👇🏼
*_09032345899_*
*KATIN MTN*👇👇
09166221261
YAN NIJAR 👇
+227 95 16 61 77
Ga 'yan nijer zasu tura katin moov ko Airtel zuwa wannan number
______________________
ZAFAFA BIYAR
VVIP SUITES : 3500 (PC/TA PRIVATE KAI DAYA)
VIP SUITES : 3K (VIA GROUP) A VIP GROUP ZAA DINGA TURAWA.
TWO PAGES DAILY
INSHA ALLAH!! MORNING/NIGHT. SAFE DA DARE.
*_TEAM ZAFAFABIYAR_*
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 18
Jerawa yayi da ita kafada da kafada sanda suke takawa a hankali,idanunsa qur saman hanya,zuciyarsa na taraddadi da fargabar abubuwan da zayaji.
Satar kallonsa ta sakeyi a karo na barkatai,ganin sun nufi hanyar makarantar tasu kai tsaye ba tare da ya tsaidan mata da abun hawa ba
"Yaya,a qafa zumuje?,ka manta?,kawai dan nisa fa?,naga munbi ta layin nan" lokaci ya kalla a hankali kafin ya sauke hannunsa ya kuma sake rage speed na tafiyar,ya zaro wayar dake aljihun hagunsa ya miqawa iman idanunsa cikin nata
"Karbi ki dubamin" cikin rashin fahimta ta miqa hannu ta karba wayar,ta kuma bude kamar yadda ya umarceta.
Abinda ta gani din shi ya birkita kwanyarta cikin sakanni,duk da tasan da wanzuwarsa,amma bata tsammaci yaci gaba da wanzuwa cikin wayar ba,take rudewa suka bayyanar mata,saidai tayi qoqarin bawa kanta dakiya da qwarin gwiwa,tunda babu wani na sabo ko rashin tarbiyya kaf cikin charts dinsu,bugu da qari ma tana jin lokaci yayi da zata bayyanawa duniya bassam dinta
"Waye wannan?" Amin ya fada yana kallon wayar kafin ya maida dubansa ga fuskar iman. Har cikin ranta taji tambayar kamar tazo mata a dai dai,don saboda dama ya amin dinne kawai take tunanin zatayi maganar dashi,ya kuma fuskanceta har ya kai zancan gaban malam,to saidai shima duk sanda ta yunqura zata yi masa maganar sai taji ya mata wani mugun kwarjini,amma yanzun komai zaizo da sauqi.
Sunne kai tayi irin na alamun jin kunya
"Saurayina ne ya amin"ta fada tana rufe fuskarta da tafin hannu.
Hasbunallahu wa ni'imal wakil,ita yayi qoqarin zuqowa saga mafitar maganarsa zuwa saman harshensa,sannan yayi azamar dafe wata bishiya da tafiyarsu ta ratso dasu ta gefanta don neman agajin tsaiwa sa qafafunsa.
Kasancewar sautin addu'ar tashi bai samu fitowa ba illa maqalewa da yayi saman harshensa.......wannan ya sanya sam batasan me yake faruwa ba,cikin wani irin tashin hankali yaci gaba da kallon iman duk da fuskarta a rufe take da hannunta
"Iman......ina alqawarin da kika yimin ba zakiyi soyayya da kowa ba?,ina alqawarin da kika yimin na bani damar zabar miki miji na gari?" Yanayinta ya sauya kadan cikin boyayyar fuskarts,duk da bata kalli tasa fuskar ba amma ta fuskanci sauyun sauti sosai fiye dana dazu
"Yaaya.....kayi haquri,na saba maka wannan alqawarin,amma shima ina da tabbacin irin mijin da kakeson zabarmin dinne,kuma zaka yaba da zabina yaya,ya shiga rayuwarta ne katsam" qara dafe bishiyar yayi da kyau saboda jin jiri na dibansa da yayi,babu sauran kwana kwana ko boye boye
"Iman......nine mijin da na yi miki tanadi,ni ya amin dinki nine mijin dana zaba na kuma killace kaina saboda ke,iman.....ni amin nike sonki iman,zuciyata ta girma da sonki ta kuma rayu da sonki tsahon shekaru masu yawa". Kamar wadda aka jibgawa wani abu a saman kanta haka taji,ta yaye fuskarta da sauri da kuma hanzari don tana da buqatar tabbatarwa kanta ba shirin film akeyi a wajen ba,tana son ta gani da gaske ya amin ne?,kuma ba wasa yake mata ba?.
Saidai kuma.....kallon farko ta karanci zallar gaskiyar dake fitowa tun daga zuciyarsas shimfide saman fuskarsa muraran,abinda ya sake firgitata,ta danyi baya kadan tana jin tashin hankali yana rufto mata,ta yaya haka zata faru?,ta yaya zaice wai da sonta ya rayu?,me yasa bai gaya mata tun da can ba sai a yanzu data riga tayi alqawari da wani,data riga tayi nisan kiwo cikin duniyar soyayyar wani?,ta yaya zata gane yaren da yakeson koya mata bayan bashi ta iya ba?,meye yake shirin faruwa?.
"Ya ameen,da gaske kake?,nice fa iman dinka?"kai ya gyada mata yana kallon tsakiyar idanunta kai tsaye
"Na sani,iman dita ce,shi yasa nake gaya mata halin da zuciyata take ciki,ina sonki iman......burina kuma na aureki,in fact,malam ya jima da bani ke!" Maganarsa ta qarshe saura kadannta wargaza kwanyarta
"Me?!" Ta furta da wani sauti me kauri da amo
"Eh,malam ya bani ke tuntuni" ya fada yana gyada mata kai tare da tabbatar mata.
Kanta ta soma girgizawa,sam sam kwanyarta ba zata dauki wannan batun ba,wacce iriyar magana ce haka mara dadin saurare?,ta yaya zaizo mata da wannan maganar?,tsahon zamansu da rayuwar da sukayi a muhalli guda bai taba tunkararta da maganar ba sai yanzu?sai daidai wannan lokacin?.
Ci gaba tayi da gigixa kanta tana koma da baya,kafin ta juya cikin wani irin hanzari ta nufi hanyar gida,ya miqe da sauri yabi bayanta yana qwala mata kira,saidai ko waiwayawa batayi ba bare ta saurareshi,har ya fara rufa mata baya,sai kuma ya tsaya cak bayan ya yiwa kansa birki ya kuma gayawa kansa gaskiya kan bai kamata ya bita ba din,jama'a suna kallonsu,sannan kuma gida zata shiga a hakan,shigarsu tare cikin wannan yanayin su duka biyun bai kamata ba,kuma yana biye da ita,sai ya dawo a hankali cikin wata kasala da mutuwar jiki ta gaske,ya duqa ya dauki jakarta data sulale a wajen ya soma takawa a hankali shima zuwa hanyar gidan,kwanyarsa na juyawa,tunaninsa yana hautsinewa,yaya iman ta dauki maganar?,me ya sanyata firgicewa haka?,wadan nan sune tambayoyin da ya dinga maimaitawa kansa su wanda bashi da amsoshinsu.
A hanya komai kama kamar iman bai gani ba,hakan ya alamta masa ta jima da isa gida kenan?,wannan yasa daya dawo shima bai shiga gidan ba,dakinsu ya wuce kai tsaye,ya zame saman katifa yayi rub a ciki,bayajin akwai wani abu da zai iya tabukawa,saboa ya jin kamar qafafunsa ba zasu iya daukar gangar jikinsa ba.
Yadda batasan a gida ya wuni ba itama shima baisan tana kwance cikin dakinsu ba,dukkaninsu wani irin yini sukayi mai wahala qunci da kuma takura,tunanin dake qirjin kowannensu ya nauyayar masa,wani irin yanayi mara dadi na zulumi da kuma fargaba,fargabar data kasance mai tarin banbamci a tsakanin iman da ameen.
Sai magariba da ya shiga cikin gidan inna keta mamakin dama yana ciki?,saboda sadiqu nada aiki da yawa a ranar a garejinsu,abinda ya sanyashi fitar wuri sannan kuma har zuwa lokacin bai shigo ba
"Banajin dadi ne inna,kuma banaso na gaya miki nasan zakiyita damuwa ne" amsar daya bata kenan
"Ikon Allah,don iman bata jin dadine itama,nasan da dole zata bincikoka,nayi mamaki nima da banji motsinka ba ashe jikinne.....don Allah aminu ka daina zama da ciwo baka fada,babu kyau,a qalla ya kamata ko leqaka a dinga yi ko ana ganin yanayin jikin naka,baka zauna a daki kai kadai ba kamar babu kowa cikin gidan uhmmm"
"In sha Allah inna,kiyi haquri" ta amsa masa sa babu komai,yanayin sanyi da yanayinsa ya koma saita azashi da cewa don bayajin dadin jikinsa ne,daga bakin qofar dakin iman din ya tsaya yayi mata sannu saboda wanzuwar inna a wajen kada taga ya wuce,ya jiyota can qasa sosai ta amsa masa,sai ya sake wucewa zuwa dakinsu.
********. ****. ********
Munira ce rike gam da hannun iman din sanda suke zagayawa zuwa bayan ajujuwansu,bata sakar mata hannu ba sai da suka dangana saman wani dan tudu wanda asalinsa tarin qasa ne saboda jimawa a wajen ya koma kamar dutse.
"Tunda kika shigo na tabbatar ba lafiya ba,gashi jiya na dinga zura idanu an bani saqo na baki amma baki shigo ba" munira ta fada tana duban iman dake zaune ta rungume qafafuwanta a qirjinta.
Ajiyar zuciya me nauyi ta sauke,a.hankali ta fara magana cikin sautin da sai ka dauka wani babban ciwo tayi
"Rayuwata na neman fadawa garari munira......na shiga rudani me zurfi daga jiya zuwa yau,irin wanda ban taba hasasowa ba" matse fuska munira tayi tare da sake tattara hankalinta waje daya
"Rudanin me?,me ya faru?rabuwa kukayi da bassam?" Kai ta girgiza
"Muna gab da rabuwarne wala'alla"
"Karki gayamin wannan mummunar kalmar mana iman,kina haukane?,bassam din zaki bari ya subuce miki?"
"Munira.....ya ameen ke sona" saita firfitar da idanu waje
"Yayannaki da kuke ciki daya?,wanne irin hauka ne wannan?"
"Ba ciki daya muke ba,riqonshi inna tayi,kuma almajirin malam ne,dalibinsa ne" sak munira ta tsaya tana kallon iman,tarin mamaki ne fal saman fuskarta,sai iman ta gyara zama ta gaya mata duk yadda akayi.
Fuska munira ta yatsina
"To don yana sonki shine me?,kawai saiki zauna a rabaki da wanda zuciyarki takeso?,wanda zai zama hutun rayuwa a gareki matuqar kika aureshi,karki manta,'yammatan wannan zamanin SHI SUKE BURI" Kai iman ta girgiza tana jin tashin hankali na sake ninkuwa cikin ranta
"Munira.....bakisan halin malam ba,na tabbatar baya magana ta tashi,kuma wallahi wallahi indai ya ameen ya tabbata yana sona malam ya sake fahimtar hakan babu wanda ya isa ya hanashi bashi ni duk duniya" murmushi munira ta saki,sai ta matso kusa da iman din sosai
"Kinga,ayi me baro baro kawai a wuce wajen......ki bude bakinki malama,karki cuci kanki,ki gayawa kowa kina son bassam,kuma shi kike da burin aura,ki gayawa ameen bassam kikeso kanki tsaye,idan kikace zaki tsaya kunya ko kara,to wallahi kina ji kina gani za'ayi babu ke,ni dama na dade ina zargin sonki yake,shi yasa ya tajura rahuwarki ya hanaki sakewa kamar kowacce diya,abu daya ne ya ciremin zargina da kika gayamin cewa yayanki ne.....amma Allah na tuba,me na sama yaci ballantana ya baiwa na qasa,ki duba surarki da kyau....banda ma yiwa kai kasada me zaisa yace yana sonki a irin wannan lokacin da arziqi ya qwala muku kira?,me yake dashi da zai riqeki iman?,ina cewa makarantar da zaici gaba ma kokawa suke shi da ita da fafutukar ganin ya sameta,idan kika auri bassam.....bashi kansa ba,hatta da abokansa dana kusa dashi.....danginsa na qauye rankatakaf sun huta,amma shikenan saboda ya dankwafe rayuwarki sai yace wai yana sonki saboda cuta da mugunta,yana da kyau yana da kwarjini na daukar hankali,amma magana ta domin Allah bashi da sinadarin riqe mace kamarki.......da dinki zaici da ke?,koda karatun da bashi da tabbacin samunsa?ke rabu da gaibu fa ki kama dahir,kuma shima matuqar yana sonki ai zaiso ci gabanki ne,bawai ya aureki ku dankwafe waje daya babu ci gaba ba" ire iren maganganun munira kenan data ci gaba dayi,kamar zata ari baki.
Iman tana saurarenta tsaf,ita ba wannan bace damuwarta,babbar damuwarta soyayyar bassam da zuciyarta ta saba da ita,kuma batajin zata iya jurewa rasashi.
"Gashi inji bassam......,jiya ya aiko yaranshi ya kawo min da daddare saboda ya kikkiraki jiyan bai jiki ba,ya damu sosai,shi kansa yaron nasa idan kinga motar da yake hawa ko......hmmmm" tayi zancan sanda take fidda waya sabuwa dal tana miqa mata.
Wannan karon batayi musun karba ba,jiki a sanyaye ta amsa,saboda tana jin wannab shine lokaci mafi dacewa da su kasance tare da juna da bassam din.
Nan da nan labari wayar ya karade cikin qawaye da classmates dinta,tanajin mazan ajin suna fadan kudin wayar,mamaki ya kamata,ta jujjuya wayar a hannunta tana mamaki yadda mutum zai iya narka kudi kamar haka ya siya waya qwaya daya jal.[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 19
Cikin jiki zuciya ruhi da kuma idanu ya tabbatar akwai matsala,irin matsalar da duk sanda zuciyarsa ta gaya masa akwaita yana qoqarin qaryata kansa da tunaninsa,komai da komai din na iman ya canza kuma ace ya janye daga muhalli da bigiren da ya santa ada,duk dacewa ba mazaunin gida bane shi.....amma kuma gaba daya iman din ta yiwa idaniyarsa qaura,ya daina ganinta,walau da safe koda dare,tamkar wasan buya ta tsiro dashi a tsakaninsu a tsanake,yasha ganin wucewarta wuf a duk sanda ta karanci motsinsa a waje ki tahowarsa izuwa wajen.
Iman din dake tiri tiri da dukkan wani abu da ya shafeshi a yanxu ba ita bace,iman din dako yaushe take shiga kokwanto da wasi wasi duk sanda wasu awanni suka shude bataji motsinsa ko gilmawarsa ba,dukka a yanzu sun kau,kwanaki biyar din da suka biyo bayan maganarsu bai sake sanyata a idanunsa ba,koda muryarta zai iya cewa baifi sau uku ya jiyota ba tsayin kwanakin.
Wata iriyar rayuwa yake a kwanakin wadda shi kansa baxaice ga inda ta dosa ba,saboda rashin gane ainihin abinda iman ke nufi,ina tasa gaba?,meye alqiblarta?, Duka bai sani ba,tarin damuwar dake danqare cikin zuciyarsa ta bayyana cikin ayyukansa na yau da kullum,ada idan gana dinka riga goma a wuni daya,a yanzu biyu yake iyayi,sauran duka tunani ya cinyeshi.
_wannan kenan_
K'arfe takwas na dare bayan kammala sallar isha'i ya shigo gidan,wanda direct daga masallaci gidan ya nufo,tunda dama can shi ba ma'abocin zaman majalissa bane,koda ya zauna din baya wuce minti goma zuwa ashirin zai sallama dasu ya wuto gida yaci gaba da sabgoginsa.
Sanda yake sanyo kai cikin gidan tare da sallama a bakisa yaga kamar wani abu ya gifta wuf zuwa daki,inna ta daga idanunta tabi iman da kallo wadda ita dince tayi hakan,cikin mamaki tana amsa sallamar amin din,ta fuskanci wasu sauye sauye sosai game da alaqar ameen din da iman,yau dinne kuma idanunta suka ganeta real,zuciyarta tadan tsinke kadan,tana fatan kada ubangiji ya sanya wata matsala ce ta afku tsakaninsu komai qanqantarta,don basa fatan hakan,saboda ko a jiya sun jima ita da malam suna tattauna batu akan aminu da iman din
"Barka da dare inna" amin ya fada cikin murmushin sannan me sanyi da akullum yake fuskantar innar dashi,fuskantar da da zai yiwa mahaifiyarsa cikin girmama a tarin ladabi.
Cikin nata salon kulawar da kuma nuna qauna ta sakar masa fara'a
"Yauwa aminullahi,sannu da qoqari,an samu shigowa?" Ta qarashe maganar tana tura masa kujerar tsuguno,sai ya zame ya zauna kan shimfidar abun sallar da iman ta tashi yanzu akai,ya zauna sosai akai ya tanqwashe qafafunsa yana gaidata kamar wanda ba tare suke gida daya ba.
Cikin kulawa ta amsa masa,sai 'yar hira ta shigo kan wajen aikin nasu,aduk sanda wata matsala ko ci gaba suka sameshi kam aikinsa,da ita yake shawara,da ita yake tattaunawa,su kashe su binne,inna takanji matsalarsa dari yayarsa dake jigawa bataji guda daya ba.
Duk wannan hirar fiye da rabin hankalin inna yana kan dakin iman,tana zuba idanu tare sa saka ran ganin fitowar iman,tana fara'a gamida nuna kulawa dayi masa sannu da zuwa,ta kuma debo abincinsa ta gabatar masa kamar yadda suka saba,sabanin haka shuru kakeji.
Hankalin inna ya dan daga kan,ranta kuma sosu,ta kasa jurewa sai data daga murya cikin sauti mai qarfi ta qwalawa iman din kira.
Kai tsaye kuwa kiran ya isa kunnuwan iman,wadda ke kwance rub da ciki kan katifarta,ta nutsa cikin duniyar chart da bassam,wanda har bata iya jin hirar dake gudana tsakanin inna da bassam dake zaune daga qofar dakinta.
Da hanzari ta danna wayar qasan pillow,tunda dama babu wanda yasan da zaman wayar,koda yaushe kuma a silent take,ta tashi da wani irin reaction na rashin gaskiya ta fito waje tana gyara daurin dankwalinta.
Tamkar batasan ya shigo gidan ba,tamkar ba dalilin shigowarsa yasa tabar tsakar gidan ba ta gaidashi,duba daya yayi mata yasan lallai mawuyacine abinda zuciyarsa keta gujewa ba shine ya afku ba,iman din dake marmarinsa a yau ita ke gaidashi babu wani doki babu komai,fara'a da ya santa da ita babu kaso casa'in cikin dari.
Da wani mugun bin qwaqwafi inna ke karantarsu gaba dayansu,saita danne tace da iman
"Wanne irin sakarcine wannan,ki wuce ki dauko masa abincinsa,kin kama kin wani qule daki?,haka kawai kin koyi nunqufurcin banza da wofi na zaman daka?,inacewa baki jima da fitowa ba?,me kika koma yi a ciki ko wutar nepa babu?" Gabanta ya fadi saboda tasan halin inna sarai,tana matuqar qoqari wajen kiyayewa duk wani abu da zaisa inna ta zargi akwai wata a qasa amma a banza,mutum ce ita me mugun kula da kuma tsantseni
"Inna kayana na fito dasu na manta zan gyara na barsu a waje" ta fada cikin marairaicewa
"Saiki wuce ki debo masa abincin" ta sake maimaitawa tana miqe qafafunta da sukeso su fara mata ciwo,dama kwana biyun daurewa kawai takeyi
"Zan fara watsa ruwa,kamar nan da minti ashirin sai a kawomin"
"To shikenan....,idan zaki hada masa ga kwadon xogale can ragowar na malam da yayi buda baki dashi saiki hada masa dashi" da to ta amsa tana nufar kitchen,saidai ranta a bace yake sosai,kawai saboda amin din innan ta sakata a gaba take mata fada,yadda innar ke nuna masa kula da tattalinsa koda yaushe ko ya sadiqu bata yi masa haka,abincinma sai an wani hada masa kulli yaumin kamar wani magidanci,rana dai daine zai shiga kitchen ya dauko da kansa yaci.
Tunda take dashi bata taba ganin aibun hakan ba sai yau,sai yau da zuciyarta ta karkata zuwa wani hanya daban ba wadda a baya take kai ba.
Kwata kwata bata qaunar su kebe da amin din baki daya,wannan shine babban dalilin da haduwarsu cikin gidan ma ta haramatata,saboda batason ya sake dauko.mata magana makamanciyar wadda yayi mata a rannan,shurunsa da rashin nemanta da baiyi ba shima a kwanakin ya sauqaqa mata dukkan wani tsoro da kuma zulumi nata,koda bata buda baki tayi magana ba tana kyautata zaton ya zuwa yanzu ya gane inda ta dosa.
Tana hada abincin tana mita qasan ranta,fuskarta a hade,hakanan bakinta yana ta motsawa,tasan yayi hakkanne kawai don ya samu damar magana da ita,kuma batajin zata sake bashi wannan damar.
Data gama hadawar saita koma daki dauko hijabinta,hasken wayarta dake alamta shigowat saqinnin bassam ya zaunar da ita,ta saki murmushi sanda ta fara bin saqonnin nasa,saita manta da aikin da zatayi ta shiga maida masa amsa.
Ya jima tsaye gaban mudubi gana sharce kansa yana kuma duban fuskarsa,kwanyarsa na masa bitar tarin maganganun dake cunkushe daga zuciyarsa zuwa bakinsa,mamakin yadda komai yake qoqarin sauyawa cikin qanqanin lokaci yakeyi.
Cikin jallabiyya ya shirya bayan ya feshe jikinsa da turarensa kamar yadda ya saba,hatta da boxer na ciki bai tsira ba,sai ya koma saman kujerar dakin ya zauna yana duba lokaci,tayi delay sosai,amma sai ya bata uzuri,kamar hadda hali da dabi'ansa yake,mutum ne shi mai yawan bada uzuri,zaiyi wuya karon farko ya kamaka da laifi,sai ya dora hannunsa saman sumarsa da har yanzu danshin ruwan dake jikinta bai bushe ba,yana shafata a hankali daga gaba zuwa baya,yana jin yadda damuwa ke sandar jiki da zuciyarsa.
Wayarsa ya maida gefe ya ajjiye yana furzar sa zazzafar iska daga bakinsa sanda yayi kiran layinta yaji busy,wani abu ya tsaya masa a maqoshi ya kuma tokare masa maqogaro,a hankali yaci gaba da shafar sumarsa yana lallashin kansa da kansa,sai ya lumshe idanunsa yana sake fitar da iska mai tsaho wai ko zata rage masa nauyin da yakeji cikin qirjinsa.
Kiran wayarsa da akayi shi ya dauke masa hankali,ya kuma zuqe yawan mintunan data dauka bata kawo masa abincin ba.
"To ba damuwa,bari zan kira idan na duba" amsar da ya bayar kenan sanda yaji motsinta,da kuma sallamarta a bakin qofa cikin zazzaqar muryarta,ya bata izinin shigowa yana qoqarin sanya wayarsa a silent,wanda kafin ya gama ya daga kansa harta ajjiye abincin ta juya
"Iman" ya qwala mata kira,ta waiwayo tana jin ba dadi a zuciyarta kan tsaidatan da yayi
"Zo ki zauna......magana zamuyi"
"Yanzu zan dawo" ta amsa masa a taqaice,saiya gyada kai lumsassun idanunsa suna zube saman fuskarta,yana ganin sauyi muraran daga iman dinsa zuwa wata iman din ta daban,ta juya da hanzarinta ta fice,cikin ranta tana jin saidai suyi maganar da wata amma ba ita iman din ba.
Amma kuma tana saka qafarta a tsakar gida inna dake fitowa daga daki ambaci sunanta
"Wai wanne irin baqin hali kika koyo imani?,wannan zobon da kika ajjiye ya gama hada sanyinsa babu mesha ba zaki kai masa ba,bawan Allah azumi yakai fa?" Kamar zata dora hannu aka ta zunduma ihu haka ta dauki jug din zobon ta nufi soron dashi,bata taba jin inama tana da qanne ba irin yau,da babu shakka saidai fa ta tura daya daga cikinsu ta samu ta dawo,domin har a jikinta tana jin bassam nacan yana jiranta,haka fa tura qofar dakin ranta a bace sallamarta a ciki,daidai sannan nepa suka kawo wuta,hasken farin qwan lantarkin dake dakin ya mamaye ko ina,ya kuma taimakawa ameen qwarai wajen ganin yanayin fuskar iman din.
Can nesa ta samu ta zauna bayan ta dire masa jug din,kanta a qasa kamar wata surukarta tace gani.
Baiko motsa ba sabda tayi maganar,sai kafeta da yayi da lumsassun idanunsa na wasu daqiqu,sannan ya miqe cikin nutsuwar nan tasa,ya taka a hankali ya rage tazarar dake tsakaninsu,a hankali ya zame saman carfet ya zauna saitinta,ta yadda zasu iya ganin juna yadda ya dace.
Dakakkiyar muryarsan nan me cike da amo na mazantaka ta fara fita,yau din cikin wani irin yanayi na sany da laushi,duk da cewa dama can ita iman din wannan amon ta saba ji daga gareshi,bai fiya kausasa mata a magana ba
"Iman.....a duniya idan akwai wanda zai fadi halayyata bayan inna da yayata to kece ta ukunsu,banajin ko sadiqu ya sanni yadda kika sanni" sai ya sanyi shuru yana sauke numfashi gami daci gaba da kallonta sannan ya dora
"Kwanaki biyar da suka shude,munyi magana dake.....na bayyana miki komai,saidai kuma har yau na kasa karantar me wannan iman din take nufi?,ina ta fuskanta?,ina ta sa gaba?iman baki sona ne?,ko ya amin din naki bai miki ba?,idan banyi miki ba iman ki fito ki gaya min,saboda ni ba baqonki bane......"ga fada maganar cike da qwarim gwiwar samun akasin abinda zuciyarsa ke raya masa,saida amsar da iman din ta bashi tayi matuqa girgizashi,ta motsa masa zuciyarsa fiye da yadda ya zata ko kuma ya tsammata......amsar da bai taba kawowa koda cikin mafarkansa zai jita daga bakin iman din ba,bai taba zaton zata iya furtata ba
"kayi haquri ya amin........bassam nakeso" ta amsa masa,tamkar dama jira take a bata wannan damar.
Dukkan wata jijiya dake kai saqo jini da kuma iska a jikinsa zuwa muhallansu sai da ta tafi hutu na sakanni,kafin ya samu nasarar zuqo numfashinsa,bayan ya tabbatar numfashin ya koma saman qirjinsa yadda ya dace,sai ya fara kokwanton duniyar zahiri ce ko ta mafarki,saboda haka yayi qarfin halin motsawa kadan
"Iman.....sake maimatawa naji". Yayi maganar sautin muryarsa na fidda wani amo wanda zai alamtawa mai sauraron da kunnensa da kuma qirjinsa ya cika da hikima cewa lallai akwai wani abu mai tsananin nauyi da yake shirin danne zuciyar da wannan sautin ya fito daga gangar jikinta......
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: .20
"Kayi haquri ya amin......basai na maimaita maka ba,abinda na fada din,hakan nake nufi har tsakiyar zuciyata" wannan karon shigar da maganar tayi masa tafi wadda tayi masa dazu,domin kuwa a take launin fari dake qwayar idaniyarsa ya juye zuwa ja,saukar wasu abubuwa masu kama da mãsu yakeji tako ina a jikinsa.
Bai taba hasashen rashin samun nasafa kamar wannan a rayuwarsa ba,bai taba tunani ko hangen failure irin haka ba kafa rayuwarsa,sai gashi kalar tashi faduwar tana son ga riskeshi kan yanayi mafi muni,kan iman.....iman din da duk duniya babu wani abu da yakejin yana da lasisi qwarin gwiwa da tabbaci a kansa kamarta,saboda rainonsa ce,halittar da yaso yake kuma qimantata cikin kafatanin rayuwarsa.
"Zuciyata da gangar jikina ta rayu dake a matsayin wata makusanciya,kuma halitta mafi da kima a idanuna,sannan daga bisani dukka wadan nan suka narke suka koma soyayya me nauyi da kuma qarfi,irin qarfin da zai iya fasa zuciyar duk wanda ya kama......ima,daga ranar da malam ya bani ke daga ranar na laluba zuciyata,sai na tarar ashe yarin sonki ne zallah shimfide a cikinta,dashi ta rayu tsahon zamanta cikin gidan nan,ban fahimci haka ba saboda kallon qanwa ta jini da nake miki kuma muharramata,sai ranar da malam ya tunsar da ruhina halaccin abun sannan na tabbatar da haka.......iman" ya kira sunanta da wani irin taushi da ya sanya gangar jikinta zubawa
"Ki yarda ki soni,ki karbi soyayyata iman,ina miki albishir din cewa,zaki sameni a matsayin cikakken miji GARKUWA INUWA KUMA MAJINGINA ga matarsa,zan maidake abar kwatance cikin mata,zan gatantaki da dukkan wani nau'i na gata da alqaluma suka rubuta aka kuma adanashi da sunan GATA".
Tabbas jikinta yayi sanyi da jin fitar wandan nan kalaman daga bakin ya amin din,tunda bata tana jinsu daga bakinta ba,saidai kuma idan fa waiga ta waigo....zuciyarta ta maimaita mata kabar amin dai dai yake da rasa bassam muddin ranta,sai wani rauni na musamman ya lullubeta,taji ba zata iya ba,ba zata iya barinsa ba,ba zata iya rayuwa babu shi ba,jaririyar zuciyarta ta saba da soyayyarsa,kunnuwanta na iya sake tariyo mata kalaman da ya gama gaya mata yanzun nan,tamkar yasan abinda ke shirin faruwa kenan,cikin karyayyar murya dake nuna karyewar zuciyarsa,baya ya gama roqonta ta barshi yazo gidansu haka nan,ta barshi yazo ya gabatar da kansa wajensu malam,amma tsoro ya sanyata tace aa
"Karki yaudareni iman don Allah,ki soni yadda nake sonki koma fiye da haka,duk randa kika kwatanta rabuwa dani,ba shakka sunana gawa" yayi maganar kamar zai fashe mata da kuka.
Kai take girgizawa a hankali tana dubansa
"Kayi haquri ya amin,bazan iya ba,inason bassam,ina son bassam,zuciyata tana sonshi ya ameen,ka taimaka ka mara min baya mu samu cikar burinmu" sosai yaji hankalinsa ya sake tashi,ya sake kawo kusanci tsakaninsu yana dubanta sosai
"Look iman.......kinsan me kike fada?,ya ameen dinki kike cewa ya barwa wani ke?,bazan iya ba iman.....ki bani dama na wanke wancan daga ranki nayi miki sabon dashe me kyau da ma'ana" ji tayi kamar ya kwara mata ruwan zafi,saita miqe da sauri,wani abu me kama da tsoro da kuma fusata suna cudanya cikin ranta
"Bazanyi maka qarya ba,bazan iya ba......inason bassam.....ina sonshi" wannan kalaman data furta su suka sanyashi runtse idanunsa katamau ya gaza budesu har tabar dakin,fitarsu daga bakinta zuwa kunnuwansa sun aikawa sa zuciyarsa wata irin guba me tasiri da saurin illata dan adam
"Iman....iman" ya dinga maimaita sunan cikin kwanyarsa,kamar sunan baqo ne a wajensa,mamakin yadda iman din ke magana dashi haka kai tsaye,babu haufi......babu kara ko alkunya,iman dinsu ce wannan?,idan itace me ya canza ta?,meye ya sauyata haka?,tabbas akwai abinda ke faruwa ko kuma ace ya riga ya faru,waye wannan bassam din?,yaya akayi yayi nasarar canza iman din gaba daya?.
Wadannan sune abubuwan da suka taru sukayi masa rubdugu,suka saukar masa da wani matsanancin ciwon kai cikin mintuna qalilan,wanda hakan ya tilasta masa kwanciya,yana sauke numfashi a hankali,tafin hannunsa daya dafe da goshinsa.
Abu kamar wasa ciwon kan ya zaunar masa sosai ya kuma sanya masa jinya,kusan kowa na gidan ya damu da yadda alamin din ya kwanta ciwo haka lokaci guda,babu ma kamar inna data tabbatar ranae lafiya lau ya shigo,abunda ya tsaya mata a rai,haka kawai taji bata yarda da iman din ba,musamman da taga qarancin damuwa kan ciwon alamin tattare da ita,abinda bau taba faruwa ba tsahon rayuwarsu tare,ita tafi kowa shiga damuwa da dimuwa duk sanda bashi da lafiya,tafi kowa zamantowa kusa dashi,ta kumafi kowa sake maida hankali da kula da al'amuransa,amma dukka yanzu babu wannan.
Kasa daurewa inna tayi,saboda lokacine da suke gab da cika burinsu ita da malam,lokacine da suke son fahimtar juna da shaquwar dake tsakaninsu tafi tada,amma sai ga wani baqon lamari na kuma shirin bullowa a sanda bai kamata ba,bai kuma dace ya bullo din ba.
Kiran iman tayi ta rufeta da fada kan halin ko in kula data lura yana faruwa,duk da cewa sai mai tsananin kula da sanya idanu zai karanci hakan
"Inna,shirin zana jarabawar qualifying muke fa,kuma ina da buqatar nayi karatu sosai,shi kansa da kansa yake korata yace na dinga zama waje daya ina karatu" salon qaryar data shararawa innar kenan,haka kawai taji bata gamsu ba,kuma hujjar bata ratsata ba,don haka batace mata komai ba ballantana ta amsata.
Misalin qarfe takwas na dare ne,yana zaune qasan ledar din,ha jingina bayansa da doguwa kujera guda daya dake dakin,qafafunsa na miqe sambal,wanda hakan ya sake bayyana baiwar tsayi da Allah ya bashi,sambala sambalan qafafunsan yayi crossing nasu waje guda,yadan daga kansa sama kadan,saidai idanunsa a runtse suke.
Idan ka sanshi kallo daya zakayi masa kaga yadan fada,ba kamar yadda yake ada ba,dakin babu kowa saishi kadai,sai tv daketa faman yi,albarkacin wutar NEPA da ake da ita.
A mintunan da suka shude dazu shida sadiqu ne,wanda ya zauna ya sanyashi a gaba cike da damuwa kan sai yaji mene ne damuwarsa?,amsa daya yake bashi
"Bani da wata damuwa sadiqu,na gaya maka,ciwo ne kawai daga Allah" kansa ya girgiza masa gana dubansa alamun bai yarda ba
"Haka dai ka fada,amma kuma ban yarda,saboda bani kadai ba,duk wanda ya sanka idan ya kalli fuskarka yasan akwai damuwa qasan ranka" murmushin qarfin hali ya sakar masa
"Mutumin da bashi da lafiya har a tambayeshi batun damuwa dama?,ina damuwa ne kada na mutu na barka kai kadai" dariya ya sanya ta qwacewa sadiq din,duk sanda yayi masa irin wannan zolayar a sanda bashi da lafiya dariya yake bashi
"Kaga.....ka samomin abun sha me sanyi mana please kaji?" Yace da sadiqun,saboda yadda zuciyarsa ke masa zafi,wala'alla idan wani abun me sanyi yabi ta maqogaronsa ya ratsa qirjinsa ya samu sassauci,dalilin fitar sadiqun kenan,shi kuma ya lula duniyar tunani,dason warware tarin tunane tunanen da suke cunkushe a kansa.
Sallamarta ta sanyashi bude idanunsa da sauri cike da mamaki,yau kwanaki biyu kenan rabonta da dakin,saidai ya jiho muryarta daga tsakar gida,ko kuma idan zata fice.
Daga sallamae bata sake cewa komai ba,ta wuce tana ajjiye abincin,shima sai ya maida idanunsa ya rufe,amma yana iya gani da kuma bibiyar motsinta ta qasan idanunsa,yadda idan ka shigo ma zaka tsammaci idanunsa a rufen suke,koma bacci yake.
Sosai ya lura da yadda taketa tsutsuke fuska da kuma bata rai,dukkan alamu suka nuna dole akayi mata ta kawo abincin,sai data gama shirya komai ta juya da zummar ficewa,cikin zafin nama ba tare da duba yanayin jikinsa ba ya miqe da hanzari ya tareta.
Kallon kallo suka yiwa junansu,kowa yana duban dan uwansa cikin mabanbancin emotion,ita ta fara kauda idanunta daga kansa,ta kuma ja da baya sannan a hankali tace
"Fita zanyi,inna tana jirana" ba
"Iman,idan har da wasa kikemin......kiyi haquri ki janye maganarki,idan har gwadani kike iman,ki sani wallahi bazanci wannan jarabawar ba" kan nata yana can daya bangaren ta amsa masa,batason ta dubeshi don kada taji nauyi ko rashin kamata
"Wasa kuma?,ka taba yimin wasan furtamin kana sona?" Kansa ya girgiza
"Yadda baka taba min ba.....haka nima da gaske nake bassam nakeso,kayi haquri shi nakeso,shi nakeso,na riga na kamu da sonsa" ta qarashe maganar tana zuba masa qwayar idanun nan nata da a shekarun baya zamanin quruciya yara ke tsokanarta dame idanun mage.
Cikin jikinsa yaji ya kamata ya kauce ya bata hanya,hakan kuwa yayi,yaja jikinsa gefe a hankali,hakan ya bata dama ta daga labulen,ta kuma tura qofar ta fice,zuciyarta na ganin baiken ya amin da yake sake tararta da wannan maganar,maganar da take ga ya isa ya barta hakanan,tunda dama tun asali babu irinta a tsakaninsu.
Yadda ta wuce fuuu zuwa dakinta ya sanya inna dake daura alwala bakin famfo ta saki abunda take ta miqe ta bita da kallo,lallai ya kamata ta tambaya,ta kuma sanya tuhuma tsakanin bassam da iman din.
******Yana zaune daga gefan malam din,saman babbar dardumar dake malale a babban falon malam din,wanda babu komai sai dardumar da labulaye,da filalluka sample din tuntum.
Karin safe malam din yakeyi suna dan taba hira da sadiqu da amin din,yayi matuqar qoqari wajen ganin ya sake jikinsa ta yadda ba zasu fahimci komai ba,amma shi kadai yasan me yakeji a zuciyarsa.
Tashin muryar inna suka fara ji daga tsakar gida cikin tsawa,abinda ya sanyasu su dukka yin sak suna sauraro izuwa tsakar gidan,saboda gaba dayansu baqon abune a wajensu tattare da innar,basu taba jin wani abu makamancin haka daga gareta ba
"Me yake faruwa ne?" Malam yayi tambaya a fili,kamar yana buqatar ansa daga wajensu sadiqu
"Leqa sadiqu,me ya samu binta haka" malam din ya sake fada cikin jimami da mamaki,sai ya miqe yabi bayan sadiqu saboa kasa zama da yayi.
Duk muryarta da suke jiyowa tana daga cikin dakin iman ne,malam ya qarasa a hankali ya sanya kansa cikin dakin,abinda ya manta rabonsa da yayishi,sai ya samesu cirko ciro a tsaye,hannun sadiq riqe da waya yana juyata
"Lafiya binta?" Malam ya sake tambayar inna,wadda ke tsaye a kan iman,ranta a mugun bace,bata amsa masa ba,sai wayar hannun sadiqu data karba ta miqa masa,yasa hannu yakarba shima ya shiga juyata
"Ta waye wannan?" Malam din ya tambaya
"Ta iman ce" sadiq ya amsa masa
"Iman kuma?" Malam ya maimaita cike da dimbin mamaki
"Ita" inna ta amsa with confidence wanda ke cakude da wani irin zallar bacin rai,maida dubansa ya sakeyi ga iman da kanta ke qasa
"Ya akayi kika samu wannan wayar?" Tambayar data fadarwa da iman din gaba,saboda bata shirya amsata ba kwata kwata
"Tambayarki nakeyi" malam ya sake fada
"Malam,tun kafin ka shigo na tambayeta bata cemin komai ba,kamata......" Hannu malam ya daga mata,sai tayi shuru tana saukar dakai,abinda bata taba yi ba iman din ta sanyata yinsa yau
"Iman,karo na qarshe....ina kika samu wannan?"
"Wanine ya bani" dukkansu sai da maganar ta daki kowa a cikinsu,ta kuma sanyasu a cikin rudani
"Wani fa kika ce iman?,wayeshi?"
"Saurayina ne" ta fada da low tune cike da fargaba,saidai zuciyarta na gaya mata wanna shine last option da take dashi.
Shuru dakin ya dauka,kowa yayi dif a cikinsu,malam yana ci gaba da juya wayar,yayin da kansa ha daure,mamaki kuma yake sake nuqurqusarsa
"Muje rumfata" ya basu umarni yana yin gaba da wayar a hannunsa,suka mara masa baya,sadiqu na satar kallon iman din,yana jin kamar a bashi dama ya zabga mata mari ko sau daya ne,saurayinta?,a gidansu kuma wai?,iman din?.
Sallamar malam tasa amin dake zaune a waje bai motsa ba bai kuma tashi ba tunda suka fita,ya daga kansa yana amsawa,tunda suka fitan jikinsa ya bashi akwai wani abu dake shirin faruwa,duk da bayajin abunda suke fada daga can din.
Shiru ne ya ratsa falon na wasu sakanni,har zuwa sanda malam ya jefawa iman tambayar
"Waye saurayin nata?,a ina suka hadu" tambayar data qular da inna da kuma sadiqu,ta kuma sanya amin ya sake saukar da kansa,abubuwa da yaketa qoqarin boyewa da kuma dannewa zasu fasu kenan.
Sosai ta bawa kanta qwarin gwiwa,da kuma jin yaqinin cewa ba zasu tilastata kan abinda bata ra'ayi ko kuma bata so ba,tiryan tiryan ta fayyace musu waye bassam din,da kuma lokacin da suka dauka a tare
Wani abu ya yiwa sadiqu tsaye a wuya tunda ta fara amsawa malam tambayoyinsa,huci yake fitarwa yana jin kamar ya tashi ya rufe iman din da duka,idanunta har sunyi soyewar da zata yi wannan bayanin a tsakankaninsu su hudu?,ameen kam ko motsawa bai yi ba,saboda wani nauyi da yaji qirjinsa yayi.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" malam ya fada qasa qasa,saiya miqawa iman wayar
"Ki kirashi kice inason ganinsa,yazo yau yau din nan,daga yanzu zuwa magariba,idan kin gaya masa ki dawomin da wayar" dukkansu sai sukai saroro da jin maganar da malam din yayi,banda amin da babu wani abu da yaji,saboda yasan waye malam,duk wani hukunci da zai yanke tafe yake da hikima a cikinsa,kuma yana da manufa,sadiqu da inna duka suke zaton zaya rufeta dashi,amma sukaga akasin hakan....saidai koma meye zasu zuba ido suga meye matakin da malam din zai dauka.
Wayarta ta karba ta miqe ta fice tana qoqarin aiwatar da abinda malam din umarceta,tana ji cikin ranta akwai nasara tattare dasu.
K'arfe takwas saura na dare bassam ya iso qofar gidansu iman,bayan ya samu cikakken kwatance daga iman,cikin shiga yake ta alfarma da nuna irin dukiyar da Allah ya bashi,hakanan motar da yazo cikinta,tafi kowacce mota da yake hawa tsada.
Yana tsaye daga jikin motar bayan ya bude Boot na motar,ya kira wasu daga cikin daliban malam dake rumfar gidan suna daura alwalar sallar isha'i dake gabatowa ya sanyasu suka fara kwashe kayan ciki suna shiga cikin gida dasu.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: ''21
Saidai kuma ko sakanni goma ba'ayi ba,sahun farko na yaran da suka fara shiga gidan da kayan suka sake fitowa dauke dasu a kawunansu,kai tsaye suka nufoshi,ya tsaya cak yana dubansu
"Inna tace malam din baya nan,a ajjiye kayan a a waje har sai ya dawo" yasan sunan inna a bakin iman,ya tabbatar ummanta ce,sai ya ciro wayarsa don kiran iman din yayi mata bayanin cewa shine ya aiko,saidai kuma koda ya kira wayar a kashe take,don haka dole ya maida wayar aljihun nasa,ya kuma sa aka lode kayan cikin rumfar.
Ya bude motar yana shirin shiga ya zauna ya jirayi malam din saiga bullowar malam din,ya fahimci hakane saboda yadda daliban nasa keta masa sannu da zuwa,dawowarsa kenan daga wajen saukar qur'ani da akayi na daliban wata makaranta.
Kallon farko yaji malam yayi masa wani mugun kwarjini,dama kwarjinin malam din ba sabon abu bane ga duk wanda ya sanshi,saboda yadda qur'ani da tsoron Allah ya ratsashi,saiya qarasa ya russuna yana gida malam din,ya amsa gana binsa da kallo saboda baisan waye shi ba
"Dan samari daga ina?"
"Bassam ne" ya amsa yana shafa qeyarsa
"Ma sha Allah,to yayi kyau,ka qarasa masallaci muyi sallah,idan an idar sai ka sameni a qofar gida" kira malam din yayi yasa aka kawo masa ruwan alwala.
Sam sadiqu da suke shigowa layin a lokacin shi da amin bai lura da canzawar salon tafiyar al'amin din ba,tunda suka shigo layin yake hangen baquwar motar,zuciyarsa na gaya masa bassam ne,ilai kuwa ya hangi fuskarsa sanda yake alwala daga tsaye,duk ya rikice ruwan nata dawo masa yana bata shaddar jikinsa
"Ina zuqa sadiqu,nayi mantuwa" amin ya fada yana juya ya koma da baya,sam bazai iya hada numfashi da bassam din ba,bazai iya kallon fuskarsa ba,yana jin wani kishi na sukar zuciyarsa,hakan yasa ya yanke shawarar ya kauce daga wajen.
"Ina aminu ne?" Tambayar da malam ya yiwa sadiqu kenan sansa sadiq din ke zama gefan malam,wani side din ba wanda bassam yake zaune ba
"Tare muka shigo dashi,amma yayi mantuwa a shago ya kuma tun dazun" sai kawai malam ya gyada kai,ya gabatarwa da bassam ruwan randa me sanyi da aka kawo masa a kwanon sha,saidai bassam din yace ya qoshi,ba kuma komai ya kawo hakan ba,saboda sam bazai iya shan ruwan daba na roba ba.
"Malam bassam.....naji dadi da amsa kirana da kayi,ni din nan nine mahaifin iman,kuma a yadda al'ada ta tanadar.....da kuma addininmu,a duk sanda saurayi yaga yarinya yana so,zai fara turo magabatansa ne,saboda kiyayewar mutunci kima da kuma daraja ta kowanne gida,idan an bawa magabatansa dama.....zasu sanar masa yazo yaga yarinya,to a taka tarayyar da hajar duka babu wannan,banga laifinka ba,saboda bansan waye kai ba,ban kuma san daga inda kake ba,na tattara laifin na dorashi ga hajar,saboda ita tafi kowa sanin irin gidan data fito da kuma waye mahaifinta,kayi kusakurai da yawa,ka yita hidimawa diyata ba tare da sanina ba,wanda hakan kansa ya sabawa qa'ida da tsari,saidai nata laifin a idanuna yafi naka ...to duka ba wannan ba,abinda yasa nace maka kazo shine,inason shaida maka na dakatar dakai daga mu'amala da hajar,saboda nayi mata miji tuntuntuni,ko ita kanta bana jin ta sani,da haka ba zata faru ba,don haka nake baka haquri....wadan nan" ya janyo ledar gefansa da sadiqu ya shigo da ita
"Duka abubuwan daka taba bata ne,ciki harda wayar hannu,ka duba idan akwai abinda ka taba bata da babu shi a nan wajen kayi magana".
Wani gumi ne yake yankowa bassam,saboda bai taba tsammani ko kawo cew maganar da ta sanya malam ya kirashi kenan ba,wato rabasu zaiyi?,cikin tashin hankali ya motsa baki ya fara roqar malam din kan kada ya aikata haka,ya bashi daman gyara kuskuransa ya kuma bashi iman din ya aura
Murmushi irin na cikakkun dattijai malam ya sake,koda babu al'ameen bayajin zai iya baiwa iman bassam din,aure yakeso yayi mata na mutunci da siyawa kai daraja,auren qwarya tabi qwarya,kini sai kininsa
"Kayi haquri samari,na riga na bada hajar kamar yadda na gaya maka,kuma bama magana mu tadata,saboda shi alqawari abun tambaya ne ranar gobe......idan ka tashi tafiya ga kayanka nan,bama buqatar komai cikin abinda ka kawo din,ka sauka lafiya" daga haka malam ya miqe yayi cikin gida,sadiqu ya mara masa baya ransa fari qal,wannan abinda malam din ya aikata shine dai dai.
Sai da malam din ya gama duk abinda ya saba yi bayan shigarsa gida sannan yasa innar ta turo masa masa iman,wadda ta kasa ta tsare dama tana ta jiran jin abinda ga faru bayan xuwan bassam gidan,tunda a yanxun duka wayoyinta suna hannun malam,ana kiran nata kuwa kamar na tsikarinta ta miqe ta fito.
Cikin kwantaccen harshe malam yayi mata bayanin komai,ya kuma gaya mata cewa ita din an bayar da ita ga aminu tuntuni,shi ya nemi abar abun a hannunsa shi yasa suka qyale
"Nasan lamarin xai iya zamar miki mai wahala,to amma matuqar kika maida komai ba komai ba,zakiga komai din yazo miki da sauqi,tunda dai aminu ba baqonki bane,shaquwa sãbo da kuma fahimtar junan dake tsakaninku yasa mukayi sha'awar hakan ma,saboda haka ki tattara hankalinki waje daya,ku sake fahimtar juna,aminu kamar dan uwanki na jini yake,hakazalika bana jin zaki samu mijin aure tamkarsa,munsan halinsa ciki da bai,hasalima kusan fiye da rabi na halayyarsa rainonmu ne" kai inna ke kadawa cike da gamsuwa,itama sai yanzu hankalinta ya kwanta da hukuncin da malam din ya zartas
"Banason na sake ganin wani shirme ko kuskure makamancin wanda kikayi a yanzu ya sake maimaituwa,tunda na gama magana da yaron,na kuma fahimtar dashi,Allah ya sake hada kanku,ya tabbatar mana da alkhairi,tashi kije,ki kuma yita addu'a".
Da qyar iman ta iya riqe kanta sai data shiga dakinta,wani irin kuka ta saki mai sauti da amo,wanda saura kadan su malam din su jiyota,ta yaya zata iya fara rayuwa da bassam?,ta yaya zata iya rabuwa dashi?,yaya akayi bassam ya amincewa rabuwa da ita?,ina dukka tarin alqawuran da sukayiwa junansu shi da ita, just recently,me yasa malam zai mata haka?,me yasa ya amin za'a hada baki dashi a rusa farincikinta?,me yasa ya dage sai ya aureta?,wadan nan up ta kwana tana yiwa kanta,gefe daya sai ta samu kanta dajin matsanancin haushin amin,shine ya jawo komai,banda ya nuna yana sonta....banda ga karba kyautarta da malam yayi masa da za'a barta ta zabi wanda takeso,ta tabbatar da hakan.
Ta gefan al'ameen kuwa shima daban malam yayi kiransa
"Kayi saken da wani ya shiga gurbinka ya fara yiwa kansa aiki,yanzun dole sai kayi aikin gogeshi,duk da inaji a jikina cewa akasi ne aka samu,saboda haka aikin bazaiyi maka wani wahala ba......,ka sake kula da kyau,banda ka roqi alfarmar abarta ta qarashe makarantarta saboda watanni ne suka rage,da bana jin zaa rufa watan nan ban daura aurenku ba,ko a yanzu babu tabbacin hakan ba zata faru ba,Allah ya sake kiyayewa,ya hada kanku". Da wadan nan maganganun malam yayi tunanin cewa ya gyara komai,kuma komai zai hau kan hanya da kuma tsari,saidai ina.......akwai guguwa a gaba mai tarin qura,guguwar data jirkita gidan da duk wani tsari nasa gaba daya.
WASHEGARI.....kamar ba zataje makaranta ba don har qarfe shida da rabi tana kwance tana share hawayen da tun daren jiya ya gaza tsaiwa,daga bisani taji damuwa kamar zata fasa mata zuciya,ko banza idan taje din zata samu koda aron wayar da zasuyi magana da bassam din,taji ya akayi aka haihu a ragaya,sannan kuma tana da tabbacin samun shawarar wari daga munira,don haka ta sauko daga kan gadonta,ta fita zuwa tsakar gida,taja ruwa a rijiya,ta cika botiki takai bandaki,bata ko damu da tsaiwa ta kashe sanyinsa ba.
Sanda ta cewa inna ta wuce makaranta ba tare da tayi dukka ayyukan data saba ba ba kuma taci komai ba inna batace da ita komai ba,saboda tasan dole damuwa zata biyo baya,amma suna hange da hasashen tarin alkhairin da zai dorarma rayuwarta,damuwar tadan lokaci ce qanqani.
Cikin sa'a suka hade a bakin gate na makarantar kowa na shirin shiga,suna hada idanu kawai kuka ya qwacewa iman din,abinda ya tashi hankalin munira kenan,ta kama hannunta da sauri ta jata bayan ajujuwansu.
Kuka sosai take mata muniran tana kallonta bata ce mata komai ba,kamar yadda bata tsaidata ba,har sai data yi me isarta ta fara tsagaitawa sannan muniran ta magantu
"Ya kamata koma meye ki daure zuciyarki ki gayamin,saboda bazan taba sanin yadda zan kamo bakin zaren ba idan baki gayamin matsalar ba"
Handkerchief din data fito dashi daga aljihunta ta sanya ta share fuskarta,wadda ta hada ja sosai saboda kukan data kwana tanayi,kaf ta kwashe duk abinda ya faru ta shaida mata.
Tsaki munira taja,ranta yana suya da sake baci,haushin ameen ya kamata matuqa
"Babu wanda ke miki maqarqashiya da son ganin koma bayanki face amin,shine kanwa uwar gami,haka kawai mutum ya shigo gidanku ya muku kane kane ya rabaki da iyayenki,duk soyayyar da suke miki,ni ban yarda zasu iya tirsasaki ki auri wani haka kawai bisa radin kansu ba,sai don su faranta masa,idan zaki zage ki karta masa rashin mutuncin da zai cire duk wata soyayya taki dake zuciyarsa ki zage" kai iman ta girgiza
"Ni duka ba wanna ba,mafita kawai nake nema,banason na rasa bassam"
Gyara zama munira tayi cikin seriousness tace
"Akwai plan guda uku....,zamu bi kowanne a ciki,idan na farko baiyi aiki ba zami tsallaka na biyu har zuwa na uku.....na farko,zaki sanya bassam ya turawa malam iyayensa kai tsaye,su roqarma bassam ke,wala'alla girma da kimarsu yasa su cika mishi idanu ya kasa musa musu......idan wannan biyi aiki ba.......zaki je ki roqi ameen ya shaidawa malam ya janye,ki kwantar dakai sosai,ki masa dukkan wata kala ko kama ta ban tausayi......idan wannan baiyi ba,babu wani sauran option sai guda daya" ta furta tana daga yatsarta,idanunta akan iman
"Wanne ne?" Iman din ta tambayeta tanason jin qarashen bayanin muniran
"Maganata da na fara yinta a farko,ki rufe idanunki ki karta masa rashin mutuncin da zai tsigeki daga zuciyarsa,yaji bayason koda hada inuwa dake bare har igiyar auratayya ta hadaki dashi" kai iman din ke girgizawa
"Ba za'a kai nan ba in sha Allahu,kiramin bassam" ta fada tana tattara hankalinta kan jakar munira da take kyautata zaton wayar tana ciki.
Wayar ta miqa mata bayan ta cirota ta cire mata password din,da sauri da sauri ta zuba numbers din bassam din ta danna masa kira.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 22
Fitar sautin muryarsa cikin sallama kadai ya tabbatar mata ya kwana cikin damuwa ne,saboda yadda muryarsa tayi can qasa sosai,amsa masa tayi cikin nata laushin,ya kira sunanta da dan qarfi,abinda ya sanya zuciyarta ta qara karyewa,sai ta miqe ta matsa kadan daga inda munira take,hawaye na qoqarin silmiyo mata.
******BAYAN KWANA HUDU*********
Lokaci mai tsaho take batawa suna hira da bassam a wayar munira duk sanda taje makaranta,hakan ya rage mata damuwa sosai,a nan suka gama shirya ranar da zai turo mutanensa wajen malam,ta saka masa lokacin data tabbatar idan sunzo din zasu malam.
Ranar tun yammaci ta kasa sukuni,tana tsakar gida tana yankan alayyahun miyar taushen data dora,mahadin alkubus da sukayi a daren amma hankalinta gaba daya baya jikinta,inna da suke aikin tare tana lure da ita,tana mamakin yadda gaba daya iman din ta sauya kamar wadda aka yiwa juyen qwaqwalwa,har yanzu ta fuskanci babu alamun gyaruwar mu'amala tsakanin iman din da lamin,abun yana damunta sosai,saiai ta duqufa da addu'a,tana ta gayawa Allah,koma meye Allah ya kawo qarshensa,ya warware cikin sauqi.
Zuwa sanda ta kammala sallar magariba kuwa kamar sabuwar sojar dake koyon parade a karon farko,taji shigowar malam,ta kuma ji fitarsa,amma daga nan bata sakejin kowanne motsi ko kuma tashin wata maganar ba har zuwa wayewar gari.
A washegari a gurguje ta dinga komai,so take ta isa makaranta ta kira bassam din a wayar munira taji me ya faru?,ko baqin basu zo ba?,saidai sanda ta jefa masa tambayar ya tabbatar mata sunje,amma babu wata nasara,domin kuwa,kalar bayanin da yayi masa shi dashi irinsa ya maimaita musu.
Hankalinta ya tashi qwarai,amma ta danne ta dinga kwantarwa da bassam din hankali,inda daga qarshe yace sunyi shawara da abokinsa ya sake turawa dai kamar bayan kwana bakwai.
Hakan kuwa akayi a karo na biyu,abinda ya faru wancan lokacin yanzun ma shi ya sake faruwa,still dai malam ko kiranta baiyi ba bare yayi mata wata magana,daga bakin bassam din taji sunzo,a ranar kusan qaramin hauka sukayi ita da bassam din,daga qarshe suka sake yankewa cewa zai sake dai turawa a karo na uku.
A ranar ne tun bata tambayi bassam ba tasan lallai sunzo,wani qaton kuskure suka tafka a wannan karon,siyayya suka shirgowa malam.din ta fitar hankali kamar za'a bude shago,abinda yayi matuqar bata ran malam din,bashi kadai ba.....harda sadiqu,yayi musu fata fata 'yan aiken,sannan ya dawo ciki ya sanya aka kira mishi iman din,jikinta a sabule ta shiga rumfar malam din,saita taras da al'amin a zaune a gefansa,kanshi a qasa.
Dauke kanta tayi daga inda yake,tana jin wani abu me kama da haushinsa yana kamata,shine sila,shine ya jawo komai,yanzun kuma me yakeyi a wajen malam din?,saita samu waje ta zauna a hankali itama kanta a qasa.
"Tsahon zamanku dashi baki shaida masa waye ibrahim khalilu ba?,to idan bai sani ba ina fatan saqon dana aike masa dashi ya riskeshi,hajar.....idanma abun duniyarsa yake rudarki gwara ki fiddashi daga zuciyarki,ni khalilu ba makwadaici bane,kima da darajata itace gaba da komai,daga yau........indai nine mahaifinki na soke makarantarki.......sannan kuma na sanya ranar aureku keda aminu wata biyu masu zuwa,sati takwas kenan,sadaki kawai nakeso kaje ka hada,daga dubu ashirin zuwa abinda Allah ya hore maka".
Malam din yana kaiwa nan ya miqe cikim bacin rai yana gyara malum malum dinsa,taju daya yayi baiyi na biyu ba iman ta miqe hadi da sakin qaqqarfan kuka,sannan ta sulale a wajen,ko waiwayota malam din baiyi ba yaci gaba da takawa ya fice a rumfar,hakan ya baiwa inna damar yunqurowa,hannunta dauke da murfin samira data sakawa malam abinci,wanda ko kusa iman din bata ankara da tahowarta ba bare abinda ke hannunta ba sai qarar saukar murfin a hannun amin da yayi hanzarin tare bugun da hannunsa bayan ya ankara da tahowar innar,daidai qashin tsintsiyar hannunsa,ya hadu ya bada wani sauti qwalll!.
Idanunsa ya runtse saboda yadda zafin bugun ya ratsashi,sai a sannan iman ta ankarata,cikin azama tayi bayansa saboda samun mafaka ta tsaya tana rarraba idanu tare daci gaba da kukanta,wanda ya hasala inna,ta sake yunqura ta wurgawa iman din murfin,ya kuwa daki kanta
"Gafara aminu ka bani waje.....banason abinda bai shafeka ba na hada dakai,matsa ka bani waje,imani......ashe ke BUTULU CE KUFAN WUTA?,sakayyar da zakiwa aminu kenan?,kukan auren aminu kike saboda tsantsar butulci?" Inna ta fada cikin tsananin bacin rai,hankalinta a tashe kan hannun amin data buga
"Don girman Allah kiyi haquri inna,bada zafi za'a fahimtar da ita ba" da qyar ya lallaba inna ta fita daga rumfar malam din,saidai fada take sosai kamar zata ari baki,abunda basu saba gani daga gareta ba.
Shuru dakin ya dauka bayan ficewarta,babu komai sai sautin kukan iman din,a hankali ya matsa gaba ya bada space a tsakaninsu sannan ya waiwayo insa take tsayen,kuka take sosai kamar zata hadiye da zuciyarta,suna hada idanu ta sulale ta durqusa gabansa,cikin madaukakin kuka harshensa yana hadewa tace
"Don girman Allah ka janye ya amin,don Allah ka gayawa malam ka fasa,ka barmu mu auri juna nida bassam" suka sosai kalamanta sukayi masa qasan zuciyarsa,ya lumshe lumsassun idanunsa sannan ya budesu,bayajin zai iya zuwa ya tunkari malam yace masa ya fasa aurenta,bazai iya wannan aikin ba,amma kuma a yanzun baisan ta yadda zai lallabata ta daina wannan kukan dake ci masa zuciya ba
"Ya isa iman,ki daina kukan haka,kije zamuyi magana" wani abu ta hadiye tana dan jin relief yana saukar mata,sai ta tashi a hankali kamar yadda ya buqaceta ta fice daga dakin,yayin da shi kuma ya bita da kallo.
Idonsa ya runtse gam tare da kama gashin kansa ya riqe da qarfi,wani radadi ciwo da zafi yakeji tsakiyar qirjinsa,bai taba yarda da cewa son maso wani azaba gareshi ba sai yanzu,bai taba yarda da wannan maganar ba sai a yanzun,inama zai iya,inama zai yiwu,da tabbas ya cire wannan bassam din daga zuciyar iman din ya dasa kansa,bai taba kawowa ko a mafarki iman din zata gujeshi ba.
Cikin kwanakin gaba daya gidan ya zama wani iri,da sadiqu da inna gaba daya fushi suke da iman din,yayin da malam keta qoqarin ganin abubuwa sun daidaita ta hanyar nusashshe da ita da kuma janta a jiki,ta bangare daya kuwa ita gaba daya bata wannan take ba,tanata qoqarin komawa ne kamar da tsakaninta da amin din saboda ta samu yayi mata abinda takeso,ya tausaya mata ya janye ya barta da bassam,tana da tabbacin furtawa janyewarsa ce kadai abinda zai samu dama da kuma lasisin kasancewa tare da bassam a matsayin miji da mata.
Koda yaushe idan ta tada maganar yana cewa ta bari zasu tattauna,dawo da kusancinsu da take ta qoqarin yi ya masa dadi,saboda ya sanya a ransa ta wannan hanyar zai sanya kansa cikin zuciyarsa a sannu a sannu,sannan idan tafiya ta fara nisa zata haqura haka yake fata,don haka ta bangare daya ma tuni ya sake dawowa da aikinsa haiqan na dinki,duk da malam yace sadaki kawai yake buqata,amma bazai qyale iman dinsa babu sabbin sutura kamar kowacce amarya ba,uwa uba yana son ya samar musu gidan da zasu zauna da kanshi bawai malam din ya basu ko ya samar musu ba,don haka ya fidda ajiyarsa da yaketa yi,wadda yake saka ran amfani da ita idan ya samu gurbin karatun da yaketa fafutuka,daya duba kuwa kudade ne masu yawa sa zasu isheshi yayi abubuwa masu yawa dasu.
Sam iman bata gane wasa kawai yake mata da hankali ba sai da ya shigo da wasu atamfofi ya kirata yace ta zaba guda biyar a ciki.
Atamfofin ta kalla sannan ta sake dubansa gabanta yana faduwa
"Na menene kuma had biyar?" Murmushi ya saki yana dubanta
"Ta ya zaayi ina tailor guda nabar amaryata babu sabon kaya?" Zumbur ta miqe hawaye na cika idanunta,hankali take take dubansa
"Ashe dama yaudarata kakeyi?,ashe ba zaka iya yimin abinda nakeso ba?" Zaiyi.magana cikin daga murya tace
"Kada ka sake kacemin komai kaji malam" daga haka ta juya da gudu zata fice,sukaci karo sa sadiqu,saita gewayeshi ta fice,ya qaraso dakin a fusace
"Me yarinyar nan take gaya maka?".
Ganin a zabure sadiqun yake,sanna ransa a bace yake,zai iyayi mata komai sai yace
"Ina ruwanka?,zancan miji da matarsa?" Kai ya girgiza ba alamun wasa a fuskarsa
"Tsawa fa naji tayi maka daga shigowata tun dahga farkon soro"
"Koma meye babu naka a ciki" amin din na kaiwa nan sadiqu bai saurareshi ba yayi cikin gidan,amin ya miqe yabi bayansa,saboda ya tabbatar yadda ran abubakar ke a bace kwanakin akan iman din,dama kawai dama yake buqatar samu a kanta lallai akwai abinda zai faru.
Dai dai sanda ya isa kuwa tuni ta samu marin farko daga wajen sadiqu,yana shirin qara mata na biyu amin din ya riqe masa hannu,yana zuwa dakin dama ya saka kanshi da sauri,abinda ya mata rabonsa da aikatawa,saboda sam babu wanda ke shiga dakinta sai inna.
Qarar data qwalla ita ta fito da inna dake uwar dakanta,dafe da kuncinta amin ya sameta hawaye wani nabin wani,zai sake kai mata mari na biyu amin ya riqe hannunsa cikin bacin rai,sadiq din na qoqarin qwacewa yana sababi,tsaiwar inna kadai a wajen ta fahimci abinda yake faruwa
"Ka barshi aminu yayi mata dukan tsiya,shashasha BUTULU,koda baikai ga dukanta ba ni gab nake da na saka ua daketan dama ai,duk irin takunki ina sane dashi,idanuwa kawai na zuba miki" inna itama ta dora da nata sababin,da qyar ya fiddasu daga dakin kowa ya koma nashi ranshi a bace,sannan ya tsaya bata baki,amma ko kallonsa batayi ba har ya gama ya fita,yana fitan ta sakawa qofarta sakata ta koma ta kwanta,tana kin haushi da tsanar amin na shigarta,ko babu komai shine yayi silar dukanta da ya sadiqu yayi,sabida ta manta rabon da ya sanya hannu a jikinta ya daketa.
A daki ya cimma sadiqu yanata huci
"Baka kyautamin ba sam sadiq"
"Nikai baka kyautamin ba,dama irin abinda take maka kenan baka taba gayamin ba?" Kai ya girgiza
"Bata taba yimin ba,kuma kota taba din ma meye naka a ciki?,ina ruwanka,tun asali dama baa shiga tsakaninmu ai kafi kowa sani" kansa ya kada
"Wannan abun ba irin tarayyarku ta baya bace amin,ka daina maida wannan abun ba komai ba"
"Wannan ai ba dabara kayi ba,duka babu abinda zai gyara saidai ma ya lalata,zaka sake dasa mata qin abunne a zuciyarta maimakon ta sassauto"
"Tayita qin mana,ina ruwan wani,aure ne dai sai anyishi,ko tanaso ko bataso,ko gawarta ce sai an kai"
"Subhanallah" amin ya fada yana jin babu dadi har cikin ransa
"Kada ka sake fadin haka,ita zata zauna zaman auren ba wani ba,dole idan taci gaba da qi a haqura a qyaleta,ko cikin addini babu auren dole"
"Eh,amma akwai auren cancanta ko?,kai kana tunanin malam zai janye maganarsa ne?,daga gurinka take samun fuskar yin dukka wadan nan iskace iskancen wallahi" daga haka sadiq din ya miqe abunsa ya tura toilet dinsu ya shige.
Zazzafar iska ya fitar daga bakinsa,gaba daya kansa ya daure,zuciyarsa babu dadi,komai ya daure masa waje daya,iman din tayi sauyawar dako a mafarki yaga hakan za qaryata,wai dukka soyayyar waninsa ce data danne tasa a zuciyarta ko kuwa akwai wani abu na daban da baisan dashi ba?.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 23
MATAKI na sauyawarta ta dauka, option na qarshe da take ganin tana dashi,tun daga lokacin ta soke gaisuwa tsakaninta da ameen,ko magana bata bari ta hadasu saidai idan a gaban malam inna ko sadiq ne,bai taba gayawa kowa ba,sai yama tsiri fitar wuri wajen dinkinsa,ya wuni har dare a can yanayi sannan ya dawo gidan,hakan ya aake qaranta haduwarsu,ya kuma zame masa alkhairi,saboda nan da nan yayi dinkuna masu tarin yawan gaske,kudi kuma suka dinga shigo masa.
Duk wata hidima da take masa a yanzu ta sabule hannunta,babu abinda yake hadata dashi,hatta da abinci ta daina kai masa,babu irin abunda inna batayi mata ba kan batun kai abinci amma ta qeqashe,ita kanta innar kallon iman din take kamar an canza mata ita,saidai bakinta bai fasa addu'a akan iman din ba.
********Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana ajjiye kwalbar turaren da ya gama fesawa a jikinsa,sai yanzu yaji dadin jikin nasa bayan yayi wankan,saboda gajiyar da ya hadawa kansa yau din tana da yawa.
Da baya ya koma yana shirin zama yaga an dage labulen,iman ce dauke da kwanukan abincinsu guda biyu,bazai iya tuna ranar yaushe bane rana ta qarshe da ta shigo dakin har ya ganta kamar haka,amma ko a yanzun idan ka dubi fuskarta da kyau zakasan cewa tilas akayi mata.
Tana ajjiye kwanukan ta juya abinta zata fice ba tare data ce masa kanzil ba,kusan ha saba da wannan sabuwar dabi'artata,gaaba take dashi sosai,don ko kallon inda yake batayi,to amma ayau din yanason suyi magana ta qarshe kuma ta fahimta dashi,don gaba daya salon rayuwar da takeso su shimfida batayi masa ba,don haka cikin zafin nama irin ta zaratan maza yayi wuf ya isa gabanta,ya kuma sanya qafarsa ya tura qofar dakin,ta kuwa rufe ruf,jamlock ya shige
"Meye haka?" Ta fada cikin wata iriyar tsiwa tana dubansa kai tsaye
"Ta yaya zaki tafi kibar angonki?,bayan kwana da kwanaki bai samu kun kebe ba,kuma koda kun hadu a tsakar gida ba'a kallonsa ko a gaisheshi?"
"Wai gaisuwata dama kake zaman jira?,aiko wallahi zaka bushe baka sameta ba,ka matsamin na wuce" wadan nan ba baqin kalamai bane a wajensa,saboda tuni ya saba jinsu,amma a yanzun shi ba wannan bace a gabansa
"Ni ban taba ganin inda ake soyayya dole ba,duk inda aka ce ba'a sonka ya kamata kayi aiki da hankalinka ka gusa daga wajen tun lokaci bai qure maka ba,naci babu abinda zai haifar maka,wanda bai sonka kawai bai sonka,saika qara gaba ka lalubi wata ai ko,ka matsan na wuce ina da abunyi". Sosai yagi qoqarin hadiye maganganunta,tare da danne duk wani reaction da zasu bada saman fuskarsa
"Babu inda zaki,amaryata nakeso gani da gaske" wata irin harara ta watsa masa kamar idanunta zai fado
"Wace amaryar taka?" Saita zubda yawu gefe
"Allah ya kiyaye ya tsareni,ni in aureka?,na aureja nace na auri meye?,wallahi da na aureka gwara na mutu,kai koda an daura an kaini saina caka mana wuqa dani dakai din duka mu mutu" dummn kansa yaji yayi da kalamanta ba qarshe,ya lumshe idanunsa ya furta
"Ya salam,Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla" a fili,saidai muryarsa can qasa,wai dama haka mata suke?,haka suke canza alqibla lokaci guda?,iman ce fa wannan,iman din da ya gama sanin quruciyarta,ya koya mata ababe masu yawa cikin rayuwarta,yau ita take iya tsaiwa a gabansa ta gaya masa wadan nan maganganun.
Wani irin matsawa yayi da baya cikin fushi da hanzari,ya sanya hannunsa ya dauko kakkaifar wuqar da yasha lemon fata da ita tunda safe,ya dawo gabanta ya lalubi hannunta ya sanya mata wuqar a zafafe
"Bismillah,ki fara aiwatarwa tun yanzu,ga wuqar nace,ki nunawa duniya ke cikakkiyar mara hankali ce mara qwaqwalwa ta gaske" ya fada cikin wata irin tsawa data kada hanjin iman din,ya ritsata da idanuwansa da suka sauya launi saboda bacin ran maganarta da yadda zuciyarsa ke tafasa,jikinta ya dauki kyarma,sai ya sanya hannu ya fisge wuqar ya kuma yi jifa da ita,taku uku ya qara zuwa gabanta,tazarar dake tsakaninsu tayi qaranci qwarai,har suna iya shaqar numfashin juna
"Ko a yau aka daura mana aure dake zan iya datse igiyar aurena dukka ukun dake kanki.......tunda har zaki iya daukan rai lallai ba shakka na tabbatar wancan mutumin ya cire dukka imanin dake zuciyarki tausayi da kuma jin qai.....ba abun mamaki bane tunda tuntuni ya cire miki ganin girman maganar iyaye. Tun farko bani da sha'awar auren macen da bata sona koda kuwa wanne irin so nake mata,rashin zarrar da zan bijirewa maganarsu malam saboda su din iyayena ne ya sanya na haqura da tsarina na dauki nasu......badai saboda ina sonki ne ya sanya kike dukkan wasu abubuwa da kike ba?,ki bude kunnenki.....daga yau,ni muhammad amin,na rabu dake har abada,idan kinso kije ki auri billgate" daga haka ha kewayeta cikin wani irin zafi da har tan jin wani irin huci sanda ya giftatan.
Cikin daren juyi ta dinga yi tana hango abinda ya faru tsakaninta dashi,wani irin fushi da bacin rai data hanga daga gareshi
Washegari da safe saiga kiran malam,a lokacin ta samu bacci ya dan dauketa bayan ta shaidawa bassam duk abinda ya faru,ya bata qwarin gwiwa tare da kwantar mata da hankalin lallai nasara tana zuwa.
Tun kafin takai ga zama da dogon hijabinta malam din ya fara sauke mata ruwan bala'in fada,fadan daya rudasu gaba dayansu ita da amin dake zaune a wajen
"Idan ma ita ta tursasaka ko ta sakaka kazo ka fadi cewa ka janye a bata wanda takeso.....to inamai shaida maka daga kai har ita baku isa ba,bazan kuma fasa abinda nayi niyya ba,dakai da ita din gaba daya mu zuba nida ku,tunda haka kuka zaba,ku tashi ku bani waje shashan banza" wannan itace magana ta qarshe da malam din yayi dasu.
Sati guda a tsakani suka wayi gari da baquncin yaa gana,yayar malam kenan,dukka gidan babu wanda baiyi mamaki ba,banda al'ameen da yasan da zuwan nata,hasalima yasan maqasudin zuwan nata,tunda shine sila,rabonta da garin kano an jima,a qalla ba'a qasara an kusa shekara biyar ko shida.
Daga inna har iman data rame ta fada saboda damuwar da take ciki suka tashi haiqan wajen tarbarta da abinci da sauran abubuwa,hira sosai suka sha da inna harma da iman din mutuniyarta,saida la'asar bayan iman din ta zuba mata ruwa a buta tazo ta sanar mata sai ta dubeta
"Wai duk meye silar wannan ramar ta hajar?" Ta jefawa inna tambayar,tabe baki innar tayi
"Gatanan,ki tambayeta" maida dubanta tayi ga iman,saita sunkui da kai hawaye suka fara tsatstsafo mata,tana jin ranta yana suya
"Ke na tambaya ai ba hajar ba"
"Dan uwanta za'a bata,aminu,wanda suka taso gida daya,cikin mutunci da girmama juna,wanda yasan darajarta,tayi tsallen albarka ta dauko wani bare,wanda dukiyar da yake da ita ko ubanta baida rabin rabin rabinta tace shi takeso,ban sani ba ko abun hannunsa ke rudarta" inna na kaiwa nan iman din ta juya da hanzari ta fice a dakin,hawayen da take riqewa suna sauko mata,wato kallon da suke mata kenan?,babu wanda ya kalli cewa soyayya ce sila a cikinsu?.
Batasan yadda suka qare da inna ba,don bata fito daga dakin ba kwata kwata sai da zata daura alwalar magariba,shima tanayi ta koma dakin,sai wajen qarfe goma na dare har tana shirin kwanciya taji anyi knocking qofarta daga tsakar gida
"Ki fito inji malam ki sameshi a rumfarsa" muryar ya sadiqu ta ratsa kunnenta,take ciwon da kanta yake ya sake hauhawa,haka ta miqe a daddafe ta zura hijabinta ta fito zuwa rumfar malam din,gabanta na wani irin faduwa.
Daga gefe guda ta rakube jikin yagana,kamar wadda zata shige cikinta,dukka al'ummar gidan ce cikin fakon,kallo daya malam din yayi mata ya dauke kansa,sannan ya fara magana
"Allah ya sani nayi dukkan iya bakin qoqarina don ganin na baki ingantacciyar rayuwa,na kyautata gobanki amma ban samu hadin kai ba kwata kwata daga gareki ba,kin sanya kwalli kin murje idanunki,kin kuma gaza gane ko fahimtar abunda mu muke hangar miki........shikenan,zan miki yadda kike so din saboda darajar yagana dashi kansa aminun da yakai qarata wajenta yakuma jajibota ta taso ta taho,zan baki yaron da kikeso,amma ba bisa zabi ko son raina ba......zan bashi aurenki amma bisa sharadai kamar haka,sharadi na farko,aurenki dashi babu yaji,babu saki,sharadi na biyu,idan kika saka qafa kika bar gidan nan banason ganin wulqawarki a gidan nan bare naga kina zirga zirga da sunan ziyara,mun yafe masa ke,na uku babu ruwanmu da duk wata matsala da zata taso miki ko ta tunkareki,idan ma hakan ya faru to ki nemi wani gidan amma dai ba nan ba......."
"Amma malam....." Amin yayi qoqarin datsar malam din,saboda jin girman sharadin da yaketa yankowa iman din,da sauri malam ya dakatar dashi
"Idan kace wani abu sau ranka ya baci,tunda kun gama naku kun tursasani saiku barni nima nayi nawa" maganar ta sanya alameen komawa yayi laqwas,saboda bai taba jin malam din ya gaya masa hakan ba sai yau,karo na farko kaf tsahon rayuwarsu tare,yagana.batace komai ba,duk da.sharuddan sunyi tsauri da yawa,tana fatan iman din taji girma da.nauyin sharuddan tace ta janye,wannan dalili yasa batace komai din ba.
"kin yarda kin amince?" Malam ya tambayeta da kakkausar murya,dukka sai idanu ya koma kanta,kowa fatansa a wajen tace a'ah,kowa addu'ar da yakeyi cikin zuciyarsa kenan.
A hankali zuciyarta ke wassafa mata tare da tariyo mata kalaman bassam,irin soyayya da Zai nuna mata,kulawa da kuma qauna tare da daukaka darajarta a cikin mata,ta tuna yadda suke begen juna ita dashi,saita daga kanta a hankali zuwa sama alamun
"Eh" wani irin runtse idanu amin yayi wanda ta saukar masa da ciwon kai lokaci guda,saboda yadda jijiyoyin kansa suka harba sanda ya tsinkayi amsar da iman ta bayar,yana iyajin wani zazzafan huci da sadiqu dake kusa dashi ya fitar,alamun zuciyarsa zafi kawai takeyi,kamar anyi ruwa an dauke haka wuta ta daukewa kowa dake dakin,kalaman malam suka sake ratsa shirun
"Ki kirashi ki shaida.masa cewa......rana ita yau yazo da sadaki a daura muku aure,yazo da shaidunsa biyu sun isa,daga nan ya daukeki ku wuce" ba iman ba,hatta da ya gana saida maganar malam din ta girgizashi,wanne irin hukunci ne haka tsattsaura bayan wanda ya furta kuma dazu,a rude iman take bin malam din da kallo,tana jin maganar tasa kamar a mafarki,a sadaka malam zai bada ita kenan?
"A'ah malam,ba za'ayi haka ba,don bakason mijin data zaba hakan ba shine zai sa ka bada diyarka baka binciki waye shi ba,sannan ka dauketa haka ziqau ka bada ita babu komai kamar sadaka,ba lefe babu dukka wasu kayyayaki da al:ada ta tanada" duban ya gana yayi
"Me zan aikata kuma bayan wannan?,kina tunanin a yanzu akwai wanda zaka tunkara kan neman sanin sahihiyar halayyar me kudi ya gaya maka gaskiyarsa tsakaninsa da Allah?,abune mai wahalar gaske,kaya kuma ya gana da kike magana a kansu,keda kanki kikace al'ada,al'ada kuma ba addini bace,dama a addinance shine zai bata wajen zama,wajen zama kuwa ya hada harda kayan daki"
"To amma ita binta ai zata sanarwa danginta zata aurar da diyarta ko?"
"Babu wanda zan gayawa,yadda ta zabarwa kanta kenan,don haka bazan dagawa kowa hankali ba,tunda shi ta zaba kuma an bata me yayi saura?,wanne muhimmanci muke dashi?,me zamu tsinana mata" inna ta fada tana miqewa tsaye,ta fara takawa tana barin falon,batason taci gaba da zama bare hawayen da takejin suna tsatstsafo mata su samu zubowa,tun dazu take dannesu,batason su zubo bare su zamewa iman din bala'i cikin rayuwarta,tausayin iman din takeji na yadda soyayya ta rufe mata idanu,tun bata gama sanin duniya ba,na yadda tabar lu'u'lu'u ta dauki jan qarfe,bata jin a duniya iman din zata samu mijin da yakai amin nagarta da komai da komai,tabbas diyartata ta tafka babbar asara,a yau kuma a karon farko cikin zuciyarta taji ta buraci inama ace tana da wata diyar bayan iman,da babu ko shakka koda batakai munzalin aure ba ta wanketa ta bawa amin ita,kallon fuskarsa da tayi sau daya bata qara marmarin kalla ba,tabbas dukkan abinda yayi yayi shine saboda tsabar juriya da qarfin hali irin nasa,amma idan kayi nazarinsa da kyau zaka karanci zallar tashin hankali da gigita da ya tsinci kansa a ciki.
Inna na fita sadiqu ya miqe ya mara mata baya,al'ameen ya miqe a daddafe shima yana lalubar hanya malam ya zaunar dashi
"Duk da irin qiyayyar da hajar ta nuna maka.....amma ko sau daya baka taba nuna bakason auren nan ba,baka taba musu damu ba,hakanan baka taba bijirewa umarninmu ba,kai da kake bata tsatsonmu ka fito ba,babu abinda zance dakai saidai nace Allah yayi maka albarka,ya baka mace ta gari wadda zakayi alfahari da samunta" kansa a qasa ya amsawa malam din,sannan ya miqe a hankali yana ficewa,ya gana tana binsa itama da addu'a,ranta duk babu dadi,saboda duk wanda yasan iman a dangi yasan al'ameen,yasan kuma nagarta irin tashi da halin dattakonsa.[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 24
Ba qaramin kai ruwa rana akayi da malam ba kafin ya amince ya saurari ya gana,ya qara bikin zuwa sati uku masu zuwa,don ya rantse ya maya cewar ba zata qara masa wata guda a gida ba,saboda shi kam bazaici gaba da zama da yarinyar da tafi qarfin umarninsa ba,wannan furuci shike daga hankalin iman,bataso ko sau daya taji malam ya fadi hakan.
Munira da tasan yadda komai ya wakana da sauran qawaye da basu sani ba duniya sabuwa,duniya ta samu,nan take aka soma shirin biki gadan gadan,bassam ya sakar musu komai,yace su tsara komai,su fadi dukkan abinda suke buqata kada suji shayi ko wani abu,ya sakar musu bakin aljihu iyaka, events events sai da suka tsara na kwanaki bakwai curr,kuma kowanne kudi za'a kashe ba qarami ba,saidai duk wannan abun malam yace ba cikin gidansa ba,hakanan ya gana ta dauki ragamar komai ta maida gidan wani dan uwansu dake daura da unguwarsu,ya bawa iman din daki guda,sai data koma gidanne ma taji tadan ware,saboda ta daina ganin mugun kallo daga inna,wanda take aika mata dashi duk safiyar duniya har zuwa faduwar rana,suka kuma zame hannunsu daga duk wani abu daya danganci bikin,don malam ma yace bashi da kudin da zai siya mata kayan daki a lokacin bare kayan kitchen,yadai siya katifa botiki buta tsintsiya da labule,ya kuma siya mata fulasai da tukwane.
Munira ce ta tseguntawa bassam abinda ake ciki,ranar saiga kira daga bassam din cikin sabuwar dalleliyar iPhone 13 pro max
"iya abinda suka siyamin din ya isheni,dashi kuma zan tafi" amsar data bashi kenan ta katse wayarta abunta,ranta ya baci sosai kan me yasa muniran zatayi mata haka?,koda tazo take mata maganar cikin bacin rai sai tayi dariya
"Wallahi wallahi ya zuba miki komai a gidanki,kuma ina da yaqinin babu wanda yasan shine yayi miki,to meye a ciki wai?,ai shima yasan basuson auren ne shi yasa akayi miki haka,amma ki kwantar da hankalinki,komai zai wuce" kai iman din ta gyada,duk da cewa wani lokaci idan shna hidimarsu takan manta ta yadda za'ayi auren nata,amma duk sanda ta tuna sai taji jikinta yayi sanyi
"Inajin kamar na fasa auren nan munira,gaba daya daga inna har malam sun jingine ni,kamar ma basa sona" idanu munira ta fitar
"Ashe baki da hankali?,don fa zaki aura,to idan baki sani ba bari na gaya miki,kudi sune qare magana,idan kana da kudi zaka iya siyan komai,zaka iya mallakar komai,ciki harda soyayyar mutane da farinjini,ke har mutunci a yanzu a wannan zamanin kudi suna saiwa mutum shi,bari ki gani,wuyarta ki shiga gidan,sukaga kuna zaune lafiya qalau,kuma abubuwa na shiga da fita daga hannunki komai zai canza,zai zama tarihi kamar ba'ayi ba"
"Na yadda lallai bakisa waye malam ba......babu abinda ke iya canzashi a duniya idan ba gaskiya bace" ta maidawa munira amsa tana kallonta
"Kinga,kada fa ki damu,yau da gobe bata bar komai ba,matso kiga kayan da bassam ya zabar muku,tunda ke kinqi sakin jiki aje a zabi komai dake" ta bude wayarta tana nuna mata kayan masu azabar tsada daya tilar mata da sunan lefe,gefe guda kuma ga kayan dukka events din guda bakwai din,kowanne anko sukayi ita da bassam din,kuma a dinke suke,kana gani kasan anci mutuncin naira a wajen.
Kudi sosai ya ajjiyewa iman din na gyaran jiki da sauransu ta hannun muneera,da kudaden tazo a hannunta tana nunawa iman din
"Yanzu ina zamu ayi miki gyaran jiki sharp sharp na kwanakin nan da suka rage,yadda zaki sake fita"
"Amaryar kb global enterprises"
"Inane haka?" Muneera ta tambayi daya daga cikin qawayensun da tayi magana
"Ai babu inda zamu samu fiye da yadda mukeso irin kamfanin AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISES"
"Babu wasa fa,kinsan mrs bassam ce,duniya zata daukaki bikin nan,dole ne mukaita inda zaa fita kunya,wadanda suka san abinda sukeyi"
"Haba malama,kinfa sanni,ita ta yiwa sakina gyaran jiki?"
"Yes.....nafa tuna,sakina tasha kyau gaskiya......anyita maganar yadda jikinya yayi kyau wallahi cikin qawaye,ga yadda jikinta ya dinga ya dinga fidda wani irin qamshi,ni kaina sai da na tambayeta wanne turare ne,amma kamar tana saida kayan amarya set na kayan qamshi ko?"
"Abubuwan da suke samarwa fa suna da yawa,kinga suna da
Turaren wuta from chad
Sandal flakes
Kajiji
Yellow sandal
Mufaddal.
Senegalese Kajiji
Couscous.
Green sandal.
Sudanese mix.
Shek Bakhur.
Sandal coconut.
Dorot
Hadut.
Gabgab.
Sandal rose.
Green fruity.
Sandal bange.
Kajiji balls.
Sandal balls.
Aroosa.
Khumra
VIP Khumra
Royal princess oil perfume ne
Hair kulacca
Sudanese kulacca na jiki
Sudanese scrub and dilka
Bath fragrance (turaren wankan)
Carpet and curtains perfume
Wardrobe balls
Sai kuma kayan gyaran mata kamar
Maganin infection
Maganin mata 👇🏽
Tsimi
Tula syrup
Tabaje
Kurman namiji
Pussy dessert
Silky syrup
Bata gaban kishiya
Hatsabibin gari
Zumar Chad
Tsimin tula
Tula juice sweetener
Ciccibi
Kaza
Zumar bita zaizai
"Kai,amma matar ta hadu,duk ina kikasan wadan nan kayan nata?"
"Kai kayanta ai dar ne,auty na duk wani qamshi ko gyara da zakiga tayi a maryar kb takeyi,duk sanda mijinta zai dawo daga spain acan ake mata gyaran jiki,karkiso kiga gift din da mijn ke bata idan ya dawo" shewa suka sanya,muneera tace
"Bani number dinta,can zamu kai tamu amaryar a hada mana ita"
"Ok,08067558902". Nan take muneera tayi serving.
Sanda yagana ta tashi komawa maiduguri taje ta dawo kafin satittikan bikin su cika,da kanta ta kira iman din ta sakeyi mata jirwaye da kamar wanka,don sanyi jikinta yayi sanyi,amma kuma babu alamun zata janye daga auren bassam
"Karki dauka kamar na daure miki gindi ne kije ki auri wanda kikaga dama,a'ah....nayi hakane saboda yadda na tsani auren dole,saboda shi yagi sanadiyyar rasuwar jikata balaraba,babu abinda yafi bin umarnin iyaye dadinkoda kuwa ka fisu gaskiya" da wanna kalaman ta tafi tabar iman.
**********Katafaren falone wanda idan ka kirashi da aljannar duniya bakayi kuskure ba,saboda yadda ya wadata yaji dukkan wani kayan alatu na rayuwa,wani abunma idan ka kalla kasan harda nuna fariya a cikinsa,duk kuwa da cewa arziqinsu yakai suyi koma meye,amma falon sak samfurin irin falukan da masu kudin qasashen larabawa ke ginawa kansu.
Babbar macace mai tsaho da kuma kauri,sanye da wani dandatsetsen lace da yasha ruwan stone tun daga sama har qasa,qafafuwanta sunsha jan lalle har zuwa yatsun hannunta,tana zaune saman kujerun alfarma dake falon ta dora qafa daya kan daya,'yan aikine keta hidima da ita,saidai babu wadda ta daga idanu ta kalla,ta bada himma kan canza channel tv daga wada take kai zuwa wata,fuskarta kwata kwata babu annuri ko kadan.
Kyawawan labulayen parlor din aka daga gami da sallama cikin muryarsa me zaqin nan,zaqin da har yaso yayi yawa ta fita daga ta maza zuwa sigar muryar mata irin masu dan babbar muryar nan.
Bassam ne sanye da qananun kaya,idanunsa sanye da qwabjejen baqin glass daya haska farar fatarsa,ya doso inda matar take zaune yana sallama.
Ciki ciki ta amsa masa,yana zama dukka masu aikin suka watse,suka barsu su kadai cikin falon
"Barka da hutawa" ya fada cikin sigar dake nuna boko tayi matuqar ratsashi,sai data ajjiye remote control din a gefanta,sannan ta tattara dubanta a kanshi,cikin wata murya dake nuna a ciki take dashi tace
"Ashe abinda kaje ka jajibo mana kenan?" Ta jefa masa tambayar tana qanqance idanu
"Kamar yaya mom?"
"Yanzu bassam ka rasa yarinyar da zaka auro sai 'yar gidan almajirai?,'yar matsiyata,masu ci da allo da tawada?,wadda iyayenta basu ajjiye komai ba?,duk tulin 'yammatan da kake dasu,babu irin jinsin yaren da qabila da kuma 'yan qasar da babu?babu kalar matsayin da iyayensu basu dashi?, recently 'yar gidan commissioner of finance tazo gidan nan takanas saboda kai,ringidi ringidi ina murna kamar gaske,ashe kai idanunka wata suka hango maka?" Kansa ya shafa yana bata fuska
"Munafukan nan su fahima da sukaje kai lefe ne suka gaya miki,wallahi dama nasan za'a rina" tsawa ta daka masa
"Kai dalla banza shashasha,wanda baisan ciwon kansa ba,su kishin dan uwansu suke idan kai baka kishin kanka,wannan 'yar gidan matsiyatan dama tuntuni kaketa yiwa ruwan kudi,kake rawar jiki kana barnatar musu da kudi,kudin da basusan darajarsa ba,kudin daka zubar musu inda da tabbacin har ubanta ya mutu bazai hada jarin da yakai yawansu ba,wallahi wallahi banda magana tayi nisa ko zaka mutu ba zaka aureta ba,so kake kawai ka tozartani cikin qawaye da abokan gaba 'yan baqinciki da mahassada?" Ciki ciki yace
"Am sorry mom,amma yarinyar ai tayi,nasan zata fiddaki kunya shi yasa na zabeta,don kaf cikin wadanda kike lissafawan babu wadda ta kama qafarta a kyau,kawai talakawa ne dai,amma shi kansa babanta da qyar ya bada ita"
"Kai dalla can matsa,au da qyar ya bayar?,to ai daya riqe abarsa,kada Allah yasa ya bayar din,saboda Allah ya taimakeshi ma zai hada jini damu?" Sake hasala hajiya hafsatu tayi wadda suke kira da mom,da qyar bassam yasha kanta kafin ta sauko
"Wannan gidan naka ka bata ta zauna ba?" Kai ya jinjina mata
"To ban lamunta ba.....me zasu iya zubawa a wannan gidan har ya cika?,matuqar kanason aurenta duk uban abinda suka jera din,a kawoshi nan part din hajj a shareshi a jera" idanu ya fitar
"Haba mom,why?,nifa gaskiya inason sakewa da matata" haiqan ta sake taso masa,saboda tasan halin bassam din,zuma ne saida wuta
"Gidan ubanta yakai parlour daya dake part dinka kima ne?,idan kanasonta ta dawo ta zauna damu,idan kuma ba haka ba,to saidai ka fasa auren nata,wannan gidan sai ka tashi sake auren abokin burmin qwaryarmu sannan za'a shigeshi,amma ba zaka saka min diyar almajirai a ciki ba" daga wannan ta miqe abunta ta nufi stairs ta haye abunta.
Abunda ya sanya inna ta kasa riqe hawayen da taketa qoqarin tsaidashi,ranar da al'ameen ya sauke motoci guda biyu shaqe da kayan gado da kuma kayan kitchen na ban mamaki,dukka wani tanadi nasa da yayi don kansa ya qarar dashi akan iman din kamar yadda ya saba,babu yadda baiyi da sadiqu ya siya mata freezer,home theater da sauran kayan wuta ba amma fafur yaqi,yace sisinsa bazai kashe mata ba,tunda mai kudin duniya zata aura,shima da yasan haka zai qarar da komai nashi lallai da bazai bari ya siya mata komai ba,shikam.kamar bashi da zuciya,ya manta abinda iman din tayi masa ne ko kuwa?.
Murmushi kawai yayi ya kada kai,cikin nutsuwarsa da muryarsan nan mai dauke da wani irin sound yace
"Ko a lahira wani yana cin albarkacin wani bare gidan duniya,diyar data fito daga tsatson inna da malam tafi qarfin na rama mata sharri da sharri,koda abunda tayimin yafi haka girma da muni,aurenta ne bataso nayi.....kuma na yiwa kaina wannan alqawarin yadda bataso har abada aure tsakanina da ita,Allah ya tabbatar da ita gidan mijinta,ya basu zaman lafiya me dorewa" binsa kawai da kallo sadiqu yayi,yanajin kimar amin din tana daduwa cikin ransa da idanunsa.
Daga ita har malam din rasa bakin magana sukayi,saboda ko su ba zasu iya yi mata kayan da suka kama qafar haka kyau da tsada ba,kunya duk ta cikasu,imanndin ta qishi,shi kuma ga abinda ya saka mata dashi nan,daga qarshe yaa gana ce tasa aka yiwa bassam magana kan za'a zo ayi jere,yace ya gama komai,sam ya gana tace sai an jera mata,ya debe wasu daga cikin nashin,hakanan aka kai kayan gidansu bassam,inda mom tace anan zata zauna.
Duk da cewa kayan sunyi iya qurewar gatan yarinyar da iyayenta ke da matsayi irin nasu malam,amma su fahima da suke qanne ga bassam da kuma yayunsa tabe baki sukayi sanda sukaga zatin kayan,saidai kuma sauran da bassam din yayi wanda basusan shine yayi ba shi ya hanasu tankawa.
Biki aka shiga gudanarwa gadan gadan,irin bikin da yake burin 'yammatan yanzu,bikin da ya dauki hankula,yaja magana a social media qwarai da gaske,hotunansu suka dinga shiga wayoyin jama'a,loko da saqo,biki bassam din yayi na kece raini,yayi barnar kudi kamar baisan ciwonsu ba,abinda ya bata ran momy qwarai,tsana da kuma haushin iman ya cikata tun bata kai ga shigowa gidan ba,ta yaya yarinyar da bata isa ba,bata kai komai ba bassam din zai xauna ya dinga kashe mata kudi haka?.
K'arfe tara na dare ya samu ya kutso zuwa dakinsu dake soro,hannunsa riqe da baqar leda,wadda ke dauke da dinkin riga da wando da 'yar ciki na dakakkiyar shaddar da ya zuba kudade masu nauyi ya siyeta,ya kuma kashe kudade masu yawan gaske akayi mata aikin hannu gabanta da bayanta.
Duk yadda inna taqi taro amma hakan bai hana gida samun baqi ba,saboda wasu da yawa sun rugi sun taho bikin ne saboda labarin irin mijin da zata aura da ya kai musu
#zafafabiyar
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: *25 A*
_AM SORRY,ASHE AN SAMU TSALLAKE,GA MISSING PAGE DIN NAN,AMMA NA YAU DANA GOBE NA BAKU KENAN,ASHA KARATU LAFIYA_
25
Cikin matuqar dauriya da juriya yaketa attending baqin da sukazo domin malam,da yawa mutane sunata yi masa Allah ya sanya alkhairi,ga zatonsu shine angon,ya buga kyau babu qarya,don dole idan kazo wajen ka zaci shine angon da gaske din.
Kusan a idanunsa tawagar bassam suka iso,cikin tawagar motoci na kece raini,hadi da tarin dubban al'umma,wanda hakan zai tabbatar maka ba qaramin gangami angon yayi ba,ya dauke idanunsa daga sashen da suke,zuciyarsa na qara yawan adadin bugawarta.
Shuru yayi yana jin tamkar ana dura masa hayaniyar jama'ar dake wajen cikin kansa sanda lasifiqar dake wajen ta yada muryar mutumin dake sanarwar cewa an biya sadakin hajar ibrahim khalil wato iman din naira dubu dari da hamsin da kuma galleliyar sabuwar mota,daga nan liman ya zarcw da sigar daurin aure.
Kamar wasa yaji qafafunsa sun gaza daukarsa,a hankali yaji kamar yana sulalewa,duhu ya soma sauka a idanunsa,abu na qarshe da ya iya gani fuskar sadiqu daya taroshi yana qwala masa kira,daga haka komai ya tsaya masa cak......
********Tunda suka fito daga gidansu take wani irin kuka,bayan ta gama kukan da saika tsammaci wa'adin rayuwarta ne ya qare,har zuwa sanda ta zame tana roqon inna ta gayawa malam ta fasa auren,don sam bata samu ganin malam din bama,saboda yana can asibiti wajen al'ameen,ita kanta innar
"Allah ya bada sa'a" kalmar data gaya mata kenan,tana qoqarin yafa mayafinta don wucewa asibiti wajen al'ameen da aka kwantar tunda safen.
Ko a cikin motar kukan take kamar babu gobe,gaba daya komai yafita a ranta,hakanan hankalinta a tashe yake,saidai dukkan wanda zasu bata baki sunyi iya abunda zasu iya,basusan dawar garin ba,saima suka hau mata shaqiyanci kan gobe iwar haka inda zakaje gidan ragal da ita,su bazasu iya ba,angon ya qarasa rarrashinta.
Babu wanda bai gigita da irin kyau girma da tsaruwar gidansu bassam ba,don duk yadda suke hasashe ya wuce nan,kai tsaye suka nufi part din mom da ita,kamar yadda yake a al'ada,kaiwa uwar miji matar danta,matuqar basu da nisa da juna ko kuma cikin gida daya kamar haka.
Saidai kuma dab da zasu qarasa qofar sashen aka taresu kan su wuce da ita sashenta,basai an kawo mata ita ba.
Kallon kallo aka hauyi,kowa da abunda ya fahimta,hakanan kowa da abinda yake saqawa cikin ransa ko kuma shifa abokin tafiyarsa,haka suka juya da iman din zuwa sashenta kamar yadda mom ta buqata.
*_BAYAN AWANNI UKU_*
A hankali hawaye keci gaba da sauka daga idanunta,wani irin mutuwar jiki da bacin rai dukka sun mamayeta,musamman idan ta tuna irin sallamar da sukayi da inna,malam kuwa dama bataga idanunsa ba bare ya sadiqu,uwa uba kuma lamin dake asibiti batasan a wanne hali yake ciki ba,saidai kuma ta wani sashen ranta yakanyi mata sanyi,musamman idan ta tuna da irin alqawuran da bassam yayi.mata da tanadin kulawa a irin wannan daren.
zuwa lokacin sashen nata yayi tsit,saboda kowa ya watse ya kama gabansa,babu qarar komai saita babban engine da ake zubawa disel wanda shike bawa dukkan gidan wuta,tana
Tun tana sharar hawayen tana kuma dakon shigowarsa,har hawayen suka kafe,tsoro kuma ya mamayi shurun,saita sake curewa waje guda tana sake sakin wasu sabbin qwallar.
Tun tana daga idanu tana duba lokaci har idanun nata suka fara nauyi,sabida gajiyan data tara a jikinta na kwanaki bakwai,a hankali baccu ya rinjayu juriyarta yayi galaba a kanta,ta sulale nan gefan lallausan gadonta ta fara bacci ba tare data sani ba.
Can cikin barcinta taji kamar ana taba qafafunta,abunda ya zaburar da ita kenan ta farka a firgice,suna hada idanu da bassam dake kanta saita sunkui da kai qasa,yana tsaye riqe da babbar rigarsa ya zuba mata idanu,saidai akwai yanayi a launin idanunsa,kamar wanda yayi barci ya farka
"Bacci zakiyi baki sauya kaya ba,hala kin gaji da jirana ko?,abokaina ne suka hada wani dinner iya mu imu,ga wannan,nidai bacci nakeji,saida safe" yayu maganar yana ajjiye mata ledar daya shigo da ita ya nufi saman gadon ya fada akai.
Waiwayawa tayi da kanta gefan da ya kwanta din,yayi dai dai saman gadon,da alama da gaske yake bacci zaiyi,don har ya cusa kansa qasan pillow abinsa ya fara sauke numfashi d'ai d'ai.
Mamakine ya cikata sosai,wanne irin ango ne haka?,ko 'yar sallar nan ta daren farko ma bai damu yayita ba?,ta maida dubanta ga ledar da ya shigo da ita din,sai ta matsar da ita kawai gefe,ta miqe ta lalubi toilytayi fitsari sannan ta daura alwala,ta dawo saman gadon tankwanta daga ca daya gefan.
Ta jima zuciyarta tana mata saqe saqe kafin bacci yayi awon gaba da ita.
Koda ta farka da asuba saita taras har yanzu baccinsa yake,tayita qoqarin tashinsa yana sake juyi yana kwanciya,daga qarshe fincikota yayi cikin jikinsa ya matseta,tayita kiciniyar qwace kanta amma ta kasa,haka ta haqura,tana ji tana gani daga shi har ita sallar asuban ta wucesu.
11:02 AM
Ko ina na gidan tabi tadan kakkabe inda yayi qura ta kuma badeshi da turaran wuta bayan tayi wanka ta kuma sabunta kwalliyarta cikin atamfa,ganin har sanda ta gama din babu wani abu da zasu karya dashi saita shiga kitchen,ta soya qwai ta dafa ruwan tea,tana jerewa saman dining ne bassam.ya fito yana amsa waya,daga shi sai singlet da gajeran wando,tadan waiwaya ta kalleshi,sai ta dauke idanu taci gaba da abinda take,da alama bai jima da farkawa ba sannan yayi salla.
Inda take ya qaraso,ya jata jikinsa ya rungume yana ci gaba da amsa wayar,wannan ya bata damar jin muryar wanda suke wayar dashi,muryar macace,saidai bata iya jin me take gaya masa,suna a haka har ya vama wayar,ya ajjiye nan saman table din da suke tsaye daura dashi
"Amarya bakya laifi"
"Ina kwana" ta gaidashi cikin girmamawa
"Lafiya lau,me aka dafa mana" yayi maganar yana miqa hannu ya bude kwanukan
"A'ah,ba'a kawo abinci daga cikin gida ba?"
"Eh gsky,ban sani ba ko ina ciki an buga anji shuru" daukar wayar tasa ya kira mom.
Ciki ciki ta amsa gaisuwar tasa,ba tare data bari ya dora da maganarsa ba tace
"Ku ba'a isa ku shigo ku gaida mutane ba kenan"
"Yanzu muka tashine mom,na tambayeta ma an kawo abinci tace a'ah"
"Waye bawanta?,idan zata tashi ta girka ta tashi ta girka da kanta" saita datse wayarta abunta
"Oh shit" ya fada yana cije baki,ya sake aje wayar sannan ya saketa ya zagaya ya zauna yana cewa ta hada mishi tea din.
Kadan kadan take kurba cike da baqunta,shi kuma wanda zai sanyata ta saki jikin tunda suka zauna yake amsa waya kala daban daban,har sai daya kusa gamaw sannan ya sauke wayar,ya dubeta yana murmushi
"Saifa kinyi haquri,nidin mutum ne mai jama'a,mai kuma busy sosai,mutane na ne na Media suke congratulating dina" dan qaramin murmushi kawai ta saki tana gyada kai.
To a yanayin gidan amarya da yake da farinjini banda gidan iman din,don kuwa babu kowa a sashen nata,koda kuwa 'yan cikin gidansu bassam din,shi kansa daga bisani kiransa akayi daya daga cikin abokansa,ya shirya cikin dakakkiyar shaddarsa,yayi kyau sosai kamar kowanne lokaci,tana dubansa bayan ta gama tayashi ya shirya tana fesa masa turare
"Ya kamata mu shiga ciki kafin ka fita mu gaida mom ko?"
"Sai na dawo tukunna"
"Zaka biya ya wajensu inna ne?" Ta tambayeshi,don tana zaton zasu gaisuwar surukai ne kamar yadda al'ada ta tanada
"Kai,bana jin haka gaskiya" da wannan amsar yayi gaba bayan ya danyi kissing bayan hannunta,tayi masa a dawo lafiya,saidai tana mamakin me yasa bazai qarasa gidan nasu ba.
Shuru ita daya a sashen,sai tv dake aikinta,duk da cewa gidan sabone a wajenta,amma ko sau daya batayi sha'awar bari ta tashi ta zagaya taga ya gidan yake ba,haka kawai takejin jikinta a mace,sam babu wani karsashi ko walwala tattare da ita,ta dauki waya ta kira inna ya kusa sau biyar amma bata daga ba,so take taji dama yaya jikin lamin,ganin bata dauka ba saita maida akalar kiran wayar sadiqu,shi wayar tasa ma a kashe take,malam shine na qarshe data kira,cikin sa'a kuwa ya daga,saidai daga gaisuwa bai sake barin wani abun ya hadasu ba ya kashe wayarsa.
Tana cikin wannan yanayin su munira ita da qawayenta suka iso,abunda yadan motsata kenan,har ya rage mata damuwar da take ciki,cikin lokaci kadan suka cika gidan da hira,sunata tsokanarta gami da zolayarta kamar dai yadda akasan qawayen amarya kanyi idan sunzo gidan qawarsu sabon aure.
Su munira ne kan gaba,aka shiga kitchen aka shiga dafe dafe,lafiyayyen abinci sukayi,aka fidda kula aka zubawa bassam nashi,daya daga cikin qawayen nasu ce tace
"Amma dai ki dinga saka sanwa da mamansa,duk da suna da wadata da dadi ki dafa ki aika mata" harara munira ta jefa mata
"Kinjiki da wani abu,su masu kudi ina sukasan wannan,babu ruwansu,dadin auren gidan wadata kenan,nasuma basi gama cinyewa ba bare su saurari na suruka".
Ta sake sosai taci abincin a cikinsu muniran,ta sake wanka tayi kwalliyarta dakyau,wanda hakan yayi masifar fidda kyanta,kamar ka saceta ka gudu,ga kyan quruciya da halitta ga na amarci.
"Kannensa sun shigo kuwa?,suna da kirki ko?"munira ta tambayi iman sanda suka kebe,abinda yaketa bawa iman din mamaki kenan tun dazu,babu wanda ta gani daga cikin gidan,ko don itadin bata shiga bane
"Ko fuskan mamansa ban sani ba har yanzu"
"Karki damu tunda zaku shiga anjima,kinsan su masu kudi basu danu da rayuwar kowa ba,surukutar ma ba kasafai ake yinta ba,musamman aka hadu da 'yan boko,su kuma duk sun hada" amsar muniran tadan kwantar mata da hankali.
Suna tsakiyar hirar bassam ya shigo,ya zuba mata idanu saboda yadda tayi masifar yi masa kyau,ya bude mata hannayens babu ko kunyarsu munira,hakanan itama ta isa gareshi saboda kada ta kunyatashi,ya rungumeta tsam a jikinsa yana fadin
"Kinyi kyau beauty,kina da kyau baby" ba shiri su munira suka fara lalubar jaka zasu tafi,kudi masu tsoka ya basu wanda ya sake gigitasu,ya kuma sanya driver ya maida kowaccensu gida.
Ita taimaka masa yayi wanka kamar dazu ya kuma shirya yaci abinci,a lokacin ta sake matsa masa su shiga ciki su gaida mom,yace ta dauko mayafi suje.
Tun daga shigarta ta tadda qannensa kafin fitowar uwar gayyar wato mom tasan cewa bata karbu ba,ba'a kuma maraba da ita,'yammata hudu ta samu a parlor din suna kallo,saidai kaf dinsu babu wadda tayi mata duba biyu bare ta saka ran zasu gaidata,hakan baisa ta kasa gaidasu ba,saboda ta lura biyu daga cikinsu zasu girme mata,biyun ne zasuyi sa'anni.
Sama sama suka amsa kamar wadanda aka yiwa dole,bassam din ya jefesu da harara
"Wanne irin iskancin banza ne wannan,kunaji ana gaidaku" daya daga cikinsu ce wadda ke riqe da tab tana ta faman danne danne ta waiwaya ta masa wani irin kallo
"Tunda mun amsa ai fine"
"Shut off......" Yadan fada mata a tsawace,sai kawai ta miqe ta sauko daga saman kujeran da take kai tana quna quni tayi ciki abinta,sauran ma sai suka fara binta daya bayan daya,kafin daga qarshe mom ta fito.
Kallo daya zakayi mata kasan cewa hamshaqiyar macace da taci ta tada kai,takeji da izzar kudi da kuma isa
"Sai yanzu kuka ga damar zuwa gaisheni?" Mom ta fada tana zama cikin luntsuma luntsuman kujerun da ta kusa nutsewa a ciki
"Tunda na fita ban dawo bane sai yanzu" ya amsa mata hankalinsa nakan wayarsa
"Ita 'yar mulkin ba zata iya zuwa da kanta ba saika sanyota a gaba kamar 'yar gidan sarakai?" Tayi furucin bata ko dubi sashen da iman din ke zaune na,mummunar faduwa gaban iman yayi,fargaba ta saukar mata,jin bassam baice komai ba saita motsa,cikin girmamawa ta qarasa gabanta ta duqa tana gaidata cike da surukuta da girmamawa,wani kallo ta debo tayi mata shi sama da qasa,duk da cewa a zaune take,kana ta amsa mata da amsawa guda daya tak,sannan ta dauke kanta ta tattara hankalinta kan danta suka shiga hirarsu abinsu,kamar ma sun manta da ita,kamar ma Allah baiyi wanzuwarta a wajen ba,sai data gaji don kanta qafafuwanta suka fara tsami sannan ta nemawa kanta wajen zama.
Awa daya babu wani abu a ciki sannan mom ta waiwayo inda take
"Da Allah dan kauce daga nan,muna magana" jikinta a mugun sanyaye ta dan dubi bassam,sai taga hankalinsa yana kan wayarsa,ta miqe a hankali cikin girmamawa tace
"Sai anjima mom" ci kanki batace mata ba,saima dogon tsakin data bita dashi sanda take fita daga falon,don kyau yarinyar tana da kyau,saidai kuma ta samu tawaya ta fuskoki biyu,na farko gidan data fito din bai cancanci ace kamar bassam ya auri diyar gidan ba,na biyu kasancewar mahaifinta malami,batason ya zamana bassam din ya auri matar da zata mallake mata d'a,wanan dalilan yasa gaba daya taji iman din batayi mata ba.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 26
Kwanciyarta tayi daga gefe guda na dakin bayan ta gama addu'o'inta,tana jinsa yanata motsi har zuwa sansa ya jawota jikinsa
"Wai fushi ma kikeyi?"kanta ta girgiza
"Idanma nayi fushi nima ban kyauta ba dana daga maka waya,kayi haquri,amma maganar hijabi,bazan iya daina sakashi ba,dashi aka tarbiyyanceni" tsaki taji yaja
"Su tarbiyya manya,nidai indai kinason farantamin ga abinda nace dake nan" abinda ya fada kenan,daga haka dukansu kowa yaja bakinsa yayi shiru. Daren ranar jagwalgwalan da ake matan ma ba'a yishi ba,itama hakan sai yafi mata dadi,saboda ko babu komai ta kwana cikin salama.
To tun daga waccar ranar ya koyi yawon dare,idan ya dawo daga aikinsa,yaci abinci wanka kawai zai sakeyi ya fice,bashi zai shigo gidan ba sai qarfe daya na dare wani lokacin har biyu yakan iya kaiwa,wani lokaci ko sallar isha'i sai ya dawo zaiyi.
Abun ya shiga cikin jerin abubuwan dake dagula mata lissafi a rayuwar gidan,ta kuma rasa inda yake zuwa,tayi masa duk abinda ya dace don tasan inda yake zuwa amma amsa daya ce,aikine yake riqeshi,daga baya ma data dameshi sai ya daka mata tsawa,ya kuma ce mata shi ba danta bane,kada ta sake gigin masa wannan banzar tambayar,sanda yake gaban mom ba ba'ayi masa wannan sanya idanun ba bare yanzu da yake da 'yanci
"Ni banason takura da sanya idanu,wannan ne yasa na auroki tun kina sha takwas bakikai ashirin ba" wannan maganar tasa ta tsaya mata a wuya,me yake nufi?,me maganarsa take nufi?,bata da wani abokin shawara duk duniya sai munira,amma a wannan karon sai ta gaza furtawa muniran abinda yake damunta cikin gidan nata,koda yaushe idan suna chart gaya mata take komai lafiya
"Shegiya iman,an samu duniya,muma Allah ya sanyamu a danshinku,Allah yasa kada ki canza qawaye nan gaba matan manya a manta damu,inason zuwa amma jarabawa ta hanani,umma ta dage sai na fidda result masu kyau idan inason aure bayan candy" sai a lokacin taji wata kewa ta makaranta ta kamata,ya akayi tayi sakacin da maganar karatunta tasha ruwa?,ta tuna irin yadda ya al'ameen yasha gwagwarmaya akan karatunta,gwagwarmayar da ko nashi karatun bai maida hankalin ya yiwa ba,ta sauka daga chart din,ta lalubo number wayar inna a karo na barkatai ta kirata.
Daf da zata tsinke aka daga,don har ta fitar da rai da za'a daga din,satinta biyar da xuwa gidan,amma sau daya tak ta taba kiranta ta amsa sai wannan karon.
Tanajin sallamar innar hawaye suka sauko mata,cikin rawar murya ta fara gaidata,innar ta amsa a dake kamar anyi mata dole,daga haka shuru ya biyo baya
"Sai anjima" inna ta fada tana datse wayar,saidai can wani saqo na zuciyarta taji yana matsewa,muryar iman dinta ba haka take ba,tabbas ta canza.
A lokacin suna tare da al'ameen wanda ya ajjiye takardun daya shigo dasu gaban innar
"Amintacce......da alama bakinka akwai labari" inna ta fada cikin fara'a sosai,saboda ta hangi wata walwala mai yawa a fuskar al'amin din,abubuwan da suka farun sai suka sake zama kamar wani mabudi na qarin kusanci da fahimtar juna tsakanin alameen din da inna
"Allah yayi inna....na samu tallafin karatu zuwa qasar dubai" idanu inna ta fitar sosai,gaba daya bakinta yaqi rufuwa
"Kaiii....Alhamdulillahi,Allah mun mun gode maka,Allah kaine Allah,Allah ka qarawa annabi muhammad daraja,aminu?,abun ya tabbata?" Kai ya gyada murmushi cike fal fuskarsa
"Wallahi inna,don har na haqura na fitar da rai"
"Rabon kwado ai baya taba hawa sama aminu,kuma ita addu'a babu abinda ta bari" sai taja takardun ta dudduba iya abinda zata iya ganewa a ciki,tayi masa addu'a sosai.
Sun dan jima suna tattaunawa shida inna kafin ya dauki takardun ya wuce daki,saboda yace tun yanzu zai fara shiri,don tafiyar tasu ba zata wuce sati hudu masu zuwa ba in sha Allah.
Iman ce mutum ta farko data fara fado masa a rai sanda scholarship din ya samu,amma yayi gaggawar tsigeta daga ransa ya ajjiyeta a gefe,saboda ya riga da ya yiwa kansa alqawarin sake sabuwar rayuwa da zai shafe babin iman kwata kwata daga cikinta,tun sanda aka sallamoshi daga asibiti bayan baqar wahalar da yasha ta sati daya,ya kuma dawo gida yayi jinyar sai biyu.
*******jaye take da trolley dinsa tana biye dashi a baya,yayin da shi din kuma yake sanye da wasu rantstsun suits masu bala'in kyau da daukar idanu.
Tana biye dashi tana mamakin yadda sam hankalinsa bai kanta,a matsayinsa na magidanci kuma sabon aure wanda bai dorar da komai cikin rayuwar auren ba,zaiyi tafiya ta wata guda cur,amma babu ko alamun damuwa tattali ko nuna kulawa saboda zai tafi yabar amaryarsa agida,sai faman amsa waya ma da yakeyi,har suka isa inda motar da zata kaishi airport ke jiransa.
Sai daya shiga motar kafin ya rufe sannan yadan dage wayar daga kunnensa
"Allah ya kiyaye,ya bada sa'a,Allah ya kaika lafiya"
"Ameen.....ba wata matsala ko?"
"Eh to,waye zai tayani kwana,shine maganar da tun jiya nakeyi maka ita baka amsamin ba"
"Ki shiga cikin gida ki roqi fahima ko fairuza wata tazo ta dinga tayaki......idan akwai wata damuwan kada ki damu,ki bude locker din cikin dakina ta gefan gado,key din na jiki,ki dauki adadin abunda yayi miki,saina dawo" daga haka yaja murfin motar ya rufe.
Kasa daga qafafunta tayi daga wajen,sai hannyenta data goya tana bin motar da kallo kawai,inama yadda yake sakar mata kudi farinciki yake bata haka?,inama ace nutsuwar zuciya da ruhi take samu har haka gurinsa,sam kwata kwata batajin wannan ruhin na matan aure cikin jikinta,tana jinta wani salaf tamkar tana gida,kai......akwai tarin bambance bambance ma a yanzun kan zamanta a gidansu da kuma wannan gidan,saidai kuma.....ta yaya zata daidaita wadan nan al'amuran?,ta yaya zata koma tana jin kanta da ruhinta kwatankwacin yadda kowacce mace takeji cikin gidanta,kamar yadda takejin matan aure na hira cikin group nasu na WhatsApp?.
Sai data shiga sashen nata sannan ta tabbatarwa kanta mawuyacine ta iya kwana ita daya kamar yadda ta kwatantawa ranta,saidai kuma.....ta yaya zata tunkari wadancan mutanen,wadanda suka kaita gefe daya suka ajjiye,sam basa tuna ma akwai wata halitta me rai ta dan adam a wajen?.
Tana tsaka da wannan tunanin sallamar munira ta katseta,taji matuqat mamakin ganinta,suka saki juna bayan sun gama murnar ganin juna,muniran na qare mata kallo
"Me zan gani haka?,ke ko 'yar qibar nan ta amare da akeyi ke babu ke?,sai kyau kawai da fatarki ta qara" baki kawai iman din ta tabe tana miqewa
"Me zan kawo miki?"
"A'ah muje,yau saina zaba na darje,sai nayi qara'in abinda na dade banci ba" tayi maganar tana miqewa,dariya dukka sukayi suka rankaya kitchen.
Tsaye tayi kawai daga gefe tana kallon yadda muniran ta rude,taketa santin babu ce kawai babu cikin kitchen din,ita batasan ko sau daya daga alatu har cimar dake cikin kitchen din ba dai dai da rana daya bata taba ci ko amfani dashi ba taji ya tsarga mata ba ko yayi mata dai dai
"HANGEN DALA FA BA SHIGA BIRNI BACE(huguma) munira" cikin rashin fahimta ta waiwayi ta dubeta"
"Kamar yaya?" A wannan gabar taji ta kawo maqura kuma iyakar da dole kwanyarta ita kadai ba zaya iya wannan ayyukan ba,don haka ta fayyace mata komai,illa ta suturta maganar rashin iya yin komai a gado da bassam din bayayi.
"Mtseww,ni wallahi idan nice ke wannan ba matsala bace a wajena,indai zanci nasha na qoshi,nayi wadaqa da kudina duk su suka jiyo,ke kuwa cikin wadan nan abubuwan dana lissafa babu wanda kike da matsalarsa,yawon daren bassam,yawan mu'amala da waya fiye dake,rashin baki isashen lokacinsa,wannan duka damuwoyin kansa ne ba naki ba,wasu danginsa sa sauransu ba case dinki bane kowa yayi ta kansa,tunda babu abinda kika waiwaya kika rasa" girgiza kai iman dake goye da hannuwanta tayi
"Ba zaki gane bane munira,zaman ya wuce ya baki abinci sutura da kudi,wannan duka wani tunaninmu ne ashe na rashin sanin ciwon kai da kuma quruciya,kinsan da miji ya baki naira dubu gwara ya baki minti dayansa?,ya kalleki duba na so qauna da soyayya?,ya saurareki saurare na girmamawa da jin qai.....amma fa,duka wannan ga macen datasan ciwon kanta ne,wai kuwa kinsan har yanzu bazan iya banbance miki mene bassam yakeso ba da kuma abinda bayaso?,saboda har yanzu ban samu wani isashen zama dashi da zai kaini ga fahimtar hakan ba?,ya tara kudin amma har yau nema yake,ya kasa zama ya huta ko qaqa"
"Gwara yayita nema muku ai keda yaran da zaki zazzago masa" munira ta amsa mata tana tura qatuwar lomar shinkafa wadda fiye da rabinta naman kaza ne data masa gutsi gutsi.
Amsar da muniran ta bata yasa ta qare mata kallo a fakaice,saita gane cewa muniran ba fahimtarta take ba,ba kuma zata gane ba,saboda ba'a cikin system din take ba,don haka ta sakin zancen kawai,ta qyale muniran.
Sanda zata tafi ta bata kyautar dubu biyar,sosai muniran taji dadi
"Kai.....dadin auren me kudi kenan,yanzu irin wadan nan kina dasu nasan bila'adadin,kiyita tara abinki kina aikawa dasu gida a sarrafa miki,kiyi kiyi kema nan da nan ki kama qasa" munira ta fadi tana danna kudinta a jaka,murmushi kawai iman din tayi,suka fito tana taka mata.
Da zasu wucw tayi tayi muniran ta rakata su shiga wajen mom fa tambayo fahima ko fairuza tayin kwana munira tace bata shiga,saboda idan ta shiga suka mata kallon banza ba zata bari ba,haka ta barta ta wuce,data dawo daga rakiyar saita wuce sashen mom din ita daya.
Tana kutsa kai cikin falon gabanta na tsananta faduwa,saboda yau kuma batasan da wacce fuskar zasu tarbeta ba,wacce magana zasu yayyaba mata,a haka dai ta daure tayi sallama cikin lallausar muryarta tana saka kai cikin falon.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 27
Taci sa'a za'ace ko rashin sa'a,ta samesu su dukka hudun suna nan,uku fahima,fairuza da nasma suna can saman dining suna cin abinci,ikram na zaune qasan carpet cikin falon tana aiki cikin system,da yake ita din ta fara aiki a babban kamfanin gidansu,momi ma na daga gafe tana fama da kallon news,idanunta saye da glass din da iman din tafi kyatata zaton medical ne.
Kamar ko yaushe d qyar ta amsa sallamarta ta dauke kanta,ikram ma dake aiki kallo daya ta mata taci gaba da aikinta bayan ta amsa sallamar,a haka duk cikinsu ta fisu sauqi,kuma itace babba cikin matan,su kuwa sauran dake saman dining suna kaiwa ciki suna hirarsu kamarma basusan ta shigo ba.
Ikram din ta fara gaidawa,ta amsa babu yabo babu fallasa idanunta akan aikinta,saita qarasa ta gaida mom,ta amsa tana kallon tv abinta.
Shuru ya biyo baya kamar babu wata baquwar halitta a wajen,tamkar kaya suka aje ko kuma kashi,bakajin komai sai sautin tashin hirar su fahima.
Sai data gaji da zaman kuramen sannan cikin yanayin dari dari da kuma tsoro tace
"Amm....mom dama zuwa nayi na roqi alfarmar fahima ta dinga zuwa tana tayani kwana kafin ya bassam ya dawo"
"Wait!....wait.....me nake jiyowa?" Muryar fahiman ta ratso tun daga inda take zaune,sai iman din ta dubi sashen cikin mamaki,saboda ta zaci tun shigowarta basusan ta shigo ba,ashe sunajinta.
Da wani irin taku fahiman ta sauko daga wajen,ta qaraso gaban iman ta tsaya tsam a kanta,ta jefeta da wani irin kallo na raini da qasqanci sannan ta fara magana cikin fada
"Lallai na yarda ni kadai kika raina cikin gidan nan,yanzu don Allah ki dubeni daga sama har qasa......" Tayi maganar tana nuna kanta
"Kamar ni.....in tafi gidanki tayaki kwana?,ko don kina ganin kanmu daya?,to ai hausawa sunce abanza wai talaka ya girmi sarki,ni ba tsararki bace,sunanki ya fita daga bakina" hannu mom ta dagawa fahima
"Yafi da Allah" sai data ja mata dogon tsaki sannan tayi gaba taba gunagunan maganganu
"Ke kalleni nan" mom ta fada tana duban iman din sosai
"Ina cewa a gidanku ke kadai kike kwana a dakinki,dakin da babu cikakkiyar qofa ma,kinga nan gidan" ta fada taba nuna falon da yatsanta
"Kaf katangunsa dogaye ne masu qwari,babu inda ya zaizaye ko ya cinye,baya ga haka akwai guards a gidan nan,sabida haka idan zaki wuce ki bawa mutane wake kije ki koyi kwana ke kadai ki koya,don bassam ma bai fara tafiye tafiye ba idan shine,banason wani iyayin banza da kwainane" jikinta babu laka ko kadan ta miqe,tana takawa a hankali ranta a bace jikinta a matuqar sanyaye,tana iya jiyo dogon tsakin mom din,sannan tace
"Gayyar tsiya arna a idi" kalmar data sanya hawaye suka silalo mata masu zafin gaske.
Hakanan kuwa ta kwana ita daya a sashen kamar mayyar,fargaba tsoro da kuma baqinciki sukayi mata qawanya,wani abu me kama da nadama ya fara sauko mata,har yanzu har kuma kawo yau ba zata iya dorar da wani abu guda daya da zata ce ta samu naci gaba ba a gidan farinciki ko walwala,banda tarin kudi da yake ajjiye mata wanda batajin dadinsu ko kadan,sannan bata da abunyi dasu.
A haka a haka bassam ya kwashe sati biyu da yin tafiyar tasa,wanda tsahon sati biyun nan idan tace sunyi cikakkiyar waya sau uku to qarya takeyi,kwata kwata kiran da yayi matan ma sau ukunne,idan kuma ita ta kirashi sai yace mata yana wani aikin,ko kuma yana kan hanya ko kuma zai kirata,kiran da bazaiyi mata shi kenan ba,idan ta gashi ta online kuwa,ta tura saqo,sai iya kaiwa kwanaki biyu bai buda ba,hakanan zai gama zamansa online baisan ko sallama ya turo mata ba,amma haka ta dinga danne ranta tana gayawa kanta da gasken ne aikinne yayi masa yawa.
Ashe motsin mutum ma awaje koda ba zakuyi magana ba rahama ne,batasan da wannan ba sai a yanzu da bassam din baya nan,su mom ta fuskanci ba kallon cikakkiyar 'yar adam sukeyi mata ba,don har tafiya sukayi ta kwanaki hudu bata sani ba,randa zasu dawo ta fita tadan tattaka cikin gidan saboda gajiya da tayi da zaman waje gudan taga shigowar motarsu ana mata sannu da zuwa,batayi qasa a gwiwa ba ta qarasa itama ta siga cikin 'yan sannu da zuwan,saidai ko kallon tsiya bata samu ba bare tasaka ran samun na arziqi,haka ta juya ta koma sashenta gwiwa a sanyaye.
Sati na hudu da tafiyarsa gaba daya ta sake zabgewa,ta kuma rame,sai fari data qara da kuma kyau da sheqi da fatarta keyi,a sannan ya turo wani mutum da zai dinga zuwa yana koya mata mota duk yammaci cikin gidan,haka kuwa akayi,sati biyu kacal iman din ta qware sosai,hannunta yafada,har ta fara hawa saman titi tana shawagi titunan gefannin unguwarsu ta dawo,hakan shi ya fara rage mata kadaici da kuma dauke mata hankali,saidai kuma tana shan kallo,abinda yasa tasa aka maida mata gilasanta tint.
Ranar ta gwada kiran bassam tace masa zataje gida,domin zuwa lokacin haqurinta ya qare ya gaza,innarta kawai takeson gani,tana shiryawa amma kuma fargaba ce fal ranta,saboda batasan irin tarbar da innar xatayi mata ba,hakanan fa shirya tsaf cikin wani lafiyayyen lace na alfarma,ta debi kudi masu dama ta zuba ajakarta.
Tana tafe tana duba hanya,harta riski wannan babban store,anan ta tsaya ya loda siyayya me yawa ta kayan abinci me yawa,da kayan maqulashe,irin abubuwan da tasan malam da inna naso sannan tayi hanyar gida.
Tun daga nesa ta fahimci yau ba'a zauna karatu ba,saidai kuma akwai dalibai dai daiku cikin rumfar gidan nasu suna harkar gabansu,a hankali ta sako motarta cikin layin nasu,ta daidaita motar daidai qofar gidan,sannan ta bude ta fito.
Da murna daliban malam din sukayo wajenta,musamman wandanda suke dan dasawa dasu suke mata wanki da sauransu,ta fidda jakarta tayi musu rabon 'yan 200 sababbi fil,sannan tabar musu booth din motar a bude,tace su debo duka kayan ciki su shigo mata dashi ciki.
A hankali idanunta suka sauka a qofar dakin dake garqame da muqulli,ta tsurawa qofar dakin idanu har zuwa sanda tazo zata gifta qofar dakin,ta lumshe idanu gabanta ya fadi saboda wani qamshi data shaqa,qamshin turaren ameen ne da ya kama dakin fiye dana ya sadiqu yake ratsowa ta labulen window din dakin dake bude,taci gaba da saka kai zuwa cikin gidan gabanta naci gaba da faduwa har ta bayyana a tsakar gidan.
Fes tsakar gidan yake kamar kowanne lokaci,tsahon watannin yana nan yadda yake,babu wani abu daya canza,don ko lokacin bikinta ko fenti ba'a yiwa gidan ba bare wani abu makamancin wannan.
Sallama biyu tayi,ana ukun ta jiyo inna daga rumfarta tana amsawa,taci gaba da tafiya har zuwa bakin rumfar,ta sabule takalmanta,ta saka kanta ciki bakinta dauke da sallama.
Sak inna dake saka ruwan pure water a sabuwar qaramin fridge dake kusa da qofa ta tsaya tana duban iman din,da alama tayi mamakin ganinta,sai kuma ta share,ta hade fuskarta waje guda taci gaba da abinda takeyi,kamar bata ganta ba,babu wani reaction najin dadi akan fuskar innar.
Har ta qaraso ta zame tana gaida innar bata bar abinda take ba,ta amsa mata dai taci gaba da saka ruwan,dakin ya dauki shuru,sai motsin yara dake shigo da kaya a tsakar gidan,wanda inna batace komai ba tunda tasan muryoyinsu,ta dauka wani abun suka shigo yi.
Tana gamawa fa rufe fridge din,ta dawo saman daya daga cikin kujerun ta dauki carbinta,sai tayi hanyar fita abinta ta fita daga dakin zuwa kitchen ta kama ayyukanta.
Wasu zafafan hawaye ne suka tsattsafowa iman tana daga zaunen,yanzu innarta ce tayi mata wannan shakulaton bangaron?,innarta da suke zama suyi hira da ita?,innarta dake bata kulawa?,innarta dake gaya mata yadda zatayi kewarta?.....kece sila.....ke kika ja. Wannan itace amsar da zuciyarta ta bata,saita miqe cak tabi baya innar.
"Kawo inna na wanke miki" ta fadi tana qoqarin amsar kwanukan dake hannun inna
"Ni shegiya.....rufamin asiri,barni da kayana,ina ni ina saki aiki hajar?" Kalaman sai suka yiwa iman din girma a kanta,gaba daya saita kasa ci gaba da riqon kwanukan,ta samu gefe ta sulale ta zauna.
Sam inna bata lura da kayan ba sai data gama zata koma kitchen
"Ke meye haka?waye ya kawo wadan nan kayan?"
"Nice inna" ta fada bakinta nadan rawa,tana addu'ar Allah yasa kada innar ta wofantar dasu taqi karba
"Maza maza kafin ma malam ya shigo ya sabar miki kisa a fita dasu daga gidan nan,don bamu da gurbin ajjiyesu,jiya jiya aminu kafij ya tafi yabar mana abincin rabin shekara,babu abinda muke buqata,shida sadiqu sun ishemu rayuwa"
"Ina ya ameen din ya tafi?" Tambayar data fara zuwa mata ka kenan,bata ta sababin da innar keyi,sai daga bisani da fadan innar ya tsananta hankalinta ya dawo kai
"Don Allah inna kuyi haquri,don girman Allah" wani kallo ta watsa mata
"Haqurin me?,me kikayi mana?" Kasa bata amsa tayi,sai qas datayi da kanta hawaye na sauka,lokaci daya gaba daya duniya ta daina mata dadi,ta daina jin wani dandano ko dadi nata.
Duk sababin da inna keyi hakan bai sanya ta tashi tasa an kwashe kayan ba,har zuwa sanda ta jiyo muryar malam yana sako kanshi cikin gidan,mummunar faduwa gabanta yayi,ta ambaci sunan Allah tana daga kanta a gigice sanda taji ya ambaci sunanta,kafin ya iso ta miqe tsaye tana dakon isowarsa.
"Zoki wuce ki koma gidanki,can ne wajen zamanki,mu basai kinzo kin gaishemu ba,wadan nan kayan da kika zo dasu kuma bamu da wajen ajjiyesu,abunka da gidan talaka me nema,uwa uba kuma ya hadu da yaro me hazaqa daya cika masa dan rumbunsa da abincin watanni shida,don kada ya tafi ya barshi da yunwa.....ungo wannan" ya fadi yana miqa mata 'yan 200 din tari,wanda tana ganinsu ta gane wadanda ta rabawa almajiran ne,kenan karbosu yayi
°°"200 ce babu a ciki,wadda kika bawa habu,ya fita aiki,amma ga wata madadinta,saidai ita din tsohuwa ce,idan kuma bakison tsaffin kudi kiyi haquri,idan ya dawo zan karba na ajjiye miki sabuwarki,duk randa Allah ya hadamu saiki karba" sulalewa tayi a wajen tana sakin kuka tare da roqon malam ya barta ko azahar ne ta qarasa kaiwa,amma baibi ta kanta ba,hasalima yaran ya kira,yasa suka dinga jidar abincin suna maida mata boot din nata,inna na kitchen,yadda batace tak ba,hakanan bata waiwayosu ba,har ta gama roqarsa,ta sanya mayafinta da takalminta ta fita.
Tana tuqin tana sharar hawaye,har taso ta tafka shirme,sai da tayi parking gefan titi tadan daidaita kanta sannan taci gaba da tafiya.
Koda taje gida kwance kawai tayi taci gaba da kukanta,ba wanda ya damu da ita bare ta saka ran zaiyi cigiyarta,hasalima sanda tacewa mom din zataje gidan cewa tayi me zatayi mata,kudine?....idan shi take buqata ta tabbatar danta ya ajjiye mata su,tunda tasan dama nan sukafi kauri,maganar data sanyata cikin alwashin ba zata qara gayawa mom din ba din zata fita zuwa gida.
hatta da kayan cikin motar ta barsu batabi ga kansu baba ita ta tashi ba sai gab da magarib,tunda dama tana fashin sallah ne.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 29
Lokacin da bassam din ya shaida mata dawowarsa tayi dukkan wani shiri na tarbarsa,kama daga gyaran jiki qunshi da kuma gyaran gashi,hakanan ranar daya shaida mata cewa jirgin qarfe hudu xasu sauka ta shirya lafiyayyen abinci kala kala duk na taryarss,saidai tun sanda ya shigo din,banda qarar shigowar motocinsa babu abinda ta sake ji,tun tana duban hanya har ta sare,don da alama sashen mom ya wuce direct.
A hankali abincin data jera zafinsa ya zagwanye,kwalliyarta ta fara sulalewa tana yin nata guri,har bayan sallar isha'i,tayi kwance lamo saman doguwar kujera ita daya tana hadiyar zuciya.
Sha daya saura na dare taji ya turo qofar ya falon,tana daga kwance ta daga kai kawai ta dubeshi,bacin rai ya hanata mata motsawa bare ta tarbeshi,sai taci gaba da kwanciyarta kawai,har zuwa sanda ya qaraso kanta ya tsaya
"Ke!" Ya kirayi sunanta da kakkausar murya,a mamakance ta daga kanta ta dubeshi
"Kina jin mutane,su dawo daga doguwar tafiya irin wannan amma ki kasa zuwa ko sannu ki musu,me kike nufi?" Gani tayi ya gama raina mata hankali ma,daya shigo baiko kula da yanayin daya sameta a ciki ba zai dirar mata da fada,saita miqe ta zauna sosai saman kujeran
"A ina na gankan banda yanzu?"
"Ok....amma kinsan ina sashen mom ko?,ba zaki iya shiga can ba ki sameni,da gaske mom take kenan da tace baki qaunar rabarsu,don baqin halima tsahon watannin da nayi amma ace ke daya kike kwan?" Kanta ne ya daure sosai,maganar ta bata mamaki,wanne sabon salo ne haka kuma aka fito dashi cikin gidan,me dame mom ta shirya masa na maganganu,sai zuciyarta ta bata shawarar ta sauko ita,saboda batasan me dame ta gaya masa ba wanda zai iya tunzarasu shi da ita
"Ba haka bane,tunda naga kayi can nasan kana da buqatar ku kebe,ban kuma dauka zaka dauki tsahon wannan lokacin baka shigo ba,duba can abincinka ne har ya huce" dubansa yakai ga dining din,ya hangi kwanukan a jere,tabbas yana da buqatar girkinta,don tunda ya tafi yayi missing taste din abincinta,ko daya dawo ma da zumudin yazo yaci girkinta ya dawo,saidai kuma ya samu tarba daga mom,da kuma nau'ikan abinciccika kala kala,ta kangeshi kuma da nau'in hirarrakin da suka jima basuyi ba.
Saukowa yayi ya sassauta fusatar da yayi,ya miqa mata hannu
"Is okay.....muje ki bani abincin naci,ince dai shikenan ko?" Itama qoqari tayi ta sake danne nata fushin,ta bashi hannun ya dagata,suia qarasa dining din,tayi serving nasa,ta zauna opposite dinsa,yana ci yana bata labarin tafiyar da yayi,mutum ce ita mai zurfi da kaifin gabe abu,ta fuskanci akwai wani abu guda daya behind tafiyar tasa da yaketa ciccirewa yana sauya masa lamiri.
Ruwa ta hada masa me dumi yayi wanka,sai daya shirya ya kwanta sannan ta dawo gyara wajen,zuciyarta na raya mata wala'alla yau wani abu ya wakana a tsakaninsu,ta gama gyara wajen ta shirya itama.
Saidai ko data je bedroom din already ma bacci yayi awon gaba dashi,saita zauna daure da bedside drawer tana addu'o'inta,dai dai nan wayarsa ta kada alamun kira.
Idanunta taka kan screen din wayar,sunan linda ya bayyana,sai hotonta dake blinking,ko bakaga sunan ba hoton kawai ya isa ya gaya maka qabila ce kuma ahlil kitabi wato kafura,kiran yadan dauki hankalinta,saidai kafin takai ga yin komai taji ya motsa,ya kuma kai hannunsa ya dauki wayar da sauri ya kara a kunnensa
"Goodnight,am tired" abinda taji ya fada kenan ya kashe wayar gaba daya ya jefata qasan pillow dinsa,ya koma kwanciyar rub da ciki yaci gaba da barcinsa.
Sosai kiran ya tsaye mata a rai,ta lura ko sati daya ba'a rufa ba da aurensu ta gane yadda 'yammata ke yawan kiransa a waya,iya abinda idanunta suka gane mata kenan,don bata taba daukar masa waya ba bare tayi bincike,tun ranar da abokansa sukazo tsautsayi yasa ta dauka,hakan kuma ya haifar musu da sabani.
To ashe wasa farin girki,tunda ya dawo sai abubuwan suka sake rikicewa,daga bangarensa har zuwa bangaren mom,ita mom tunda ya bata kyautar danqareriyar mota wadda kudinta ya tasamma miliyan goma shikenan suka sanyata gaba ita dasu fahima,ada basa shigowa bangarenta,amma a yanzu sai suka tsiri shigo mata,kai tsaye zasu fada mata bedroom dressing room ko kuma kitchen dinta,duk abinda sukaga dama zasu dauka,su tafi dana tafiya,su barnatar dana barnatarwa,duk da cewa Allah ya wadatasu da komai,babu abinda suka nema suka rasa,bata taba daga idanu ta kallesu ba,amma duk da haka bata tsira da baqar magana da kuma habaici ba,abinda ta lura dashi shine. sun dauki aqidar qwarya tabi qwarya,gaskiya ne da ake cewa idan kaga diyan talaka na aure gidan masu arqizi to ba shakka rabone ya rantse,ko kuma su din irin mutanen nan da ake cewa daya cikin million ne,don zaiyi wahalar gaske kaga hakan,kowa irinsa yake aure,sun maida abun jari hujja.
Bata sake gasgata hakan ba saida matan yayun bassam din sukazo gidan su biyu,dukkansu gudajen iyayensu masu maiq ne kamar gidansu bassam din,haba haba mom take dasu,babu raini tsangwama ko wulaqanci irin wanda suke mata ita,tsakaninta da faccalolin nata dai baina baina,babu yabo hakanan babu fallasa.
Ta bangaren bassan kuwa,tun tana kawaici da yadda mata ke yawan kiransa harta qosa ta fara qorafi akai,abinda ya sanya kenan yake yawaita saka wayansa a silent.
Abun sai ya zame mata biyu,ga lalurarsa da bai taba tsayawa yayi mata wani gamsashen bayani akai ba,ga kuma wannan dabi'a tasa,hasalima kamar ma damuwar da yakeyi a baya akan al'amarin yanzu taja baya sosai,kawai da ya kasa yake tashi yayi wanka yaci gaba da sabgarsa.
K'arfe sha daya saura na dare take takowa zuwa parlor dinsa na musamman dauke da butar shayi mai hade da tray da qananun kofunansu,sanye take da kayan bacci masu kauri riga da wando da suka saukar mata ash color marasa turuwa,sai gashin kanta mai santsi data matse waje daya yanata sheqi a hasken qwan lantarki,duk inda ta gifta sai tabar sauran qamshinta a wajen.
Da sallama ta shiga,yana saman kujera a zaune yana ta aiki da system,kansa ya daga ya kalleta,ya zuba mata idanu,tayi masa kyau sosai a idonsa,iman din badai kyau ba,wani irin kyau ne da ita da baya dusashewa,ko don yanzunne take kan tashen shekarun quruciya da kyan nata?,komai nata daban yake,komai nata na musamman ne.
Sake maimaita sallamar tata tayi sanda ta iso gabanshi,duk da cewa ba wannan ne karon farko,ta saba da halinsa na rashin damuwa da amsa sallama,idanunsa ya lumshe yana amsa mata,yana da feelings sosai akanta wanda har yanzu bai kasheshi ba,saidai kuma ya rasa abinda yasa duk sanda yazo gareta haka tae faruwa dashi,ita kadai.....baisan daga ina matsalar take ba,tun yana damuwa har takai ma ya rage damuwa akai.
"Wannan kwalliyar tayimin,ya kamata na biya farashinta" murmushi ta sake,tana jimawa bataji kalami mai dadi daga bakinsa ba,har takan manta da cewa akwai wasu kalmomi masu dadi da sukayi saura a tsakaninta dashi da zasu iya furtawa juna
"Na gode" ta ambata tana ajjiye masa shayin.
System din taga ya ajjiye ya laluba wasu takardu ya ciro cheque,rubutu yayi akai sannan ya miqa mata
"Na biya kudinta" ya fada yana miqa mata cheque din.
"Na gode" ta ambata tana karba,ta juya tana duba abinda ya rubuta ajiki,naira dubu dari ce.
Gefanta ta ajjiyeta tana tatara hankalinta akansa,don ba wannan ne a gabanta ba,sam yanzu ire iren wadan nan kyaututtukan nashi basa damunta balle ma su burgeta,saboda ta rasa dukkan wani abu daya kamata ace ta samu daga gareshi,kulawarsa da kuma lokacinsa dukka samunsu sun zame mata wani kayan gabas,tana yunqurin bude baki ta fara magana kira ya shigo wayarsa,kamar kowanne lokaci tabi wayar da kallo,bacin rai da baqinciki suna cikata,bata da wani sakewa dashi matuqar wayarsa zata kasance a bude.
Shima kamar wasu lokuta da dama haka ya daga wayarsa abunsa a gabanta,briefly yace zai kira idan ya gama abinda yakeyi,ta bishi da kallo ranta yana quna,bayajin kunyar daukar wayar duk wadda ta kirashi a gabanta,yau din dai ta kasa cinyewa
"A gabana bassam.....a gabana kake daga wayar wasu?" Fuskarsa yada tsuke,saboda ya tsani tayi masa qorafi akan hakan Ai bai kamata ace kina damuwa ba,tunda dai kinsan mutum kamata bazai rasa masu tayawa ba,suna nan jingim da yawa,a cikinsu kuma na zaboki" ranta je taji ya sosu da abinda ya fada,sai kawai ta miqe,yana yawan fadin magangun da bai kamata ace ya gaya mata su ba
"Na godewa Allah da bani na taya ba,nice wadda aka taya" daga haka tayi gaba abinta,tana jiyosa yana faffadar maganganu amma tayi banza dashi,daga baya bayan wasu mintuna data koma dauko wayarta,saita sameshi ya bararraje abinsa yanata hirarsa,kana masa duba daya zakasan da mace yake waya,wani abu ya tokare mata wuya,tana komawa sashensa ta shige toilet tasha kukanta sannan ta wanke fuskarta ta fito.
Tana da tarin matsalolin da batasan dawa zata tattauna ba,waye zai bata shawara,a yanzun bata buqatar shawarar munira,saboda abinda ta fuskanci madubin hangen nesarsu a yanzu ya bambanta dana juna,kowanne a cikinsu da irin abinda yake hangowa daya saba dana danuwansa,a yanzun munira na cikin rudu da gushewar gano abinda gobe zata iya haifarwa kamar yadda itama ta tsinci kanta a ciki watannin baya,wanda sai a yanzunne hijabin daya rufe kwanya da idanunta yake yayewa sannu a hankali,wani baqin gani mara kyau da kuma dimuwa yake bayyana a gareta.
Al'ameen shine sunan daya fado mata a rai,saita lumshe idanunta hawaye suna saukar mata,tana da yaqinin idan da ace aurenta kamar kowanne irin aure ne.....shine mutumin da zaiyi ruwa yayi tsaki wajen shiga matsalolinta da damuwarta,ta tabbatar da babu yadda za'ayi ya tsinci kanta a kadaici irin haka,ba zata rasa mafita ba,ba zata rasa abokin shawara ba,tun ranar daurin aurenta bata sake ganinsa ba,bata sake sanin a wanne hali da yanayi yake ciki ba,hasalima bata san ina hake ba,don kusan zuwanta gidan uku bayan aure da daddare,duk da ba jimawa take ba amma bataga koda gilmawarsa ba,taga sadiqu kuma yaci ace shima ta ganshi,zuwanta na farko taji anyi xancen ya tafi wani waje to ina yaje?,bata sani ba,bata kuma dame amsa mata.
Bai shigo dakin ba sai wajen qarfe daya saura na dare,har a sannan tana kwance kanta na mata wanu matsanancin ciwo saboda tunane tunane da suka cika mata kwanya,a hakan zaka tsammaci bacci take,saidai idanuwanta biyu,har ya gama abinda zaiyi ya haye gadon yaja bargonsa abinsa,ba jimawa taji tashin munsharinsa.
Idanunta ta runtse,wasu hawaye masu dumi suka gangaro mata,a haka munira take cewa ta share tayi sabgar gabanta?,ta dauka cewa samun kudi da sutura da cima kadai sune dadin aure kamar yadda a baya dukkaninsu qwaqwalensu suka basu?,ba shakka tana kan kuskure,wanda bata fata yayi mata jagoranci zuwa rayuwar data tsinci kanta yanzu ita a ciki.
Watansa guda da dawowa ya sake shirya wata tafiyar,wadda zai dauki a qalla wata biyu acan kafin ya dawo,tafiyar data zama mabudin budewar komai,da kuma wani irin rikici daya sake sanyo rayuwar aurenta a gaba.Ya tafi ya barta kamar kowanne lokaci,babu kulawa daga kowanne sashe,sai azabar kadaici da zaman shuru,wata daya da sati biyu da tafiyarsa safiyar wata lahadi30 safiyar lahadi
Tunda gari ya waye tana kwance bata tashi ba,tunda ta idar da sallar asuba,saboda tasan cewa babu wani abu da zatayi koda ta tashin.
Ciwon ka take fama dashi matsananci sosai,wanda ta kusa a qalla wata daya tana fama dashi,tun bayan tafiyar bassam din,koda ba'a gaya kata ba tasan yana da qaqqarfar alaqa da yawan tunani da kuma damuwa da take kwana ta wuni a cikinta.Babbar damuwarta yanzu a rayuwa yadda zata dai daita da inna da kuma malam,ta sani cewa mutum daya ne a rayuwa a yanzu zai iya daidaita tsakaninsu AMEEN,wanda shi kuma a yanzun batasan a wacce duniyar yake ba,ko giyar wake tasha tasan bata isa ta fuskanci ya sadiqu ba,tana da yaqin ranta sai yayi matuqar baci fiye da abinda inna da malam zasuyi mata,dukka danginta ba'a kusa suke ba bare taga wasu,wadanda ke a kusan basu wuce su biyar ba,su dimma babu sa'anninta ko masu qananun yara yammata da zasu kawo mata ziyara bare su rage mata kewa.
Da qyar ta sauka daga saman gadonta,kanta kamar xai fado,ta shiga kitchen ta hada ruwan tea ta riqo a mug ta dawo dakin,gefan gado ta zauna,ta jawo wayarta ta fara laluben number munira,saboda shekaran jiya tace mata zata zo,tanaso ta tabbatar zata zo din.
A kashe wayar tata take,sai ta bude data taba fatan samunta online,tunda wani lokaci akan sameta ta WhatsApp,koda layinta bai shiga ba.
Ta sama take kallon notification na wayarta,saqonni keta shigowa,idanunta suka fada kan wata baquwar number,wadda ta turo jerin hotuna har guda shida,batasan number din ba,hakan ya sanyata ta fara bude saqonta.
Rubutune kamar haka daga farko
hi me gadin gida,ina fatan wadan nan hotunan zasu debe miki kewar wuninki na yau,asha kallo lafiya_
Mamaki ya cikata,ta dannan hotunan cikin sakanni suka bude mata,tarwai kamar gilashin madubi.
Mummunan faduwa gabanta yayi,Har mug din hannunta yana subucewa daga hannun nata,ya fadi a qasa ya tarwatse shida ragowar tea din dake ciki,innalillahi wa inna ilaihi raji'un ta shiga furtawa hannayenta na rawa,zuciyarta na bugawa da gudu kamar zatayi tsalle ta faso qirjinta ta fito waje,tuni ta dade a tsaye tana bin hotunan da kallo daya bayan daya,duk da yadda hannunta ke rawa amma bata fasa binsu daya bayan daya ba,saboda tana jinta ne kamar a duniyar mafarki ba a gaske ba.
Wasu irin qazaman hotunane na bassam shi da wata qedara wadda babu alamun digon musulunci tattare da ita,hotuna ne da babu abinda suka boye na tsiraicin dake jikin dan adam,wasu hotunan suna kwance saman katafaren gadon da dakin yafi kama da hotel,wasu a bakin beach harda wadanda akayi a toilet cikin bathtub,abun babu ko kyan gani.
Jiri ne ya debeta yana shirin kayar da ita,tayi hanzarin komawa ta zauna,wayar ta sulake gefe,sai ta saka duka tafukan hannunta saman fuskarta,ta lullube fuskar,sannan ta fashe da wani matsanancin kuka,nadama da dana sani tana cin zuciyarta.Kuka take haiqan cikin tashin hankali,babu me rarrashinta ko bata baki,tunda take a duniyarta bata taba ganin abinda ya daga mata hankali irin wannan ba,ashe dama haka bassam din yake?,neman mata yakeyi?,kenan lafiyarsa qalau?,ita yake rainanawa hankali ko kuma me?.
Cikin matsanancin hali ta wuni ranar,zuwa dare saiga wani saqon da yafi wancan muni,gajeran video da yasanya numfashinta wucewa,bai dawo ba sai bayan wasu sakkanni,ta dauki wayar tayi wurgi da ita tana gunjin kuka mai sauti,kamar ta tsaga qirjinta ta fidda zuciyarta haka ta dinga ji.Kwananta uku cikin wannan halin ita daya,ta fede ta rame ta lalace ta kuma zabge,depression ya fara kamata,kamar wata mai matsala a qwaqwalwa wani lokaci,ita kadai zata tsaya gaban madubi tana zantuka da kanta tana kuka.
A kwana na hudu munira tazo,ba zata iya gaya mata komai da komai ba,tsairaicin mijinta ne,kai batajin ma muniran zata iya bata shawarar da ta dace,don daga isowarta gidan ta fara surutu kan motar da aka yiwa iman din kyautarta,motar da tunda ta hauta sau daya bata qara hawanta ba,hasalima bata ita take ba,ta kanta takeyi a yanzun,bata buqatar dukkan wani abu daya fito daga hannun bassam din,komai nashi a qazanta take kallonsa,tadai gayawa muniran abunda ke faruwa sama sama,sai ya dan tabe baki
"Shine kika zauna kika fige haka?,to don Allah ta yaya zaki raba mutum irin bassam da yammata da matan waje?,kina ganin yadda Allah yayishi,bai rasa komai ba,su sauran matan dake gidan wadata an gaya miki haka suke zaune basu da matsala,tunda dai.baki rasa komai ba ki barshi yayi sabgarsa kema kiyi naki sha'anin,tunda ya sakar miki mara,bai takuraki ba,wadda take miki ture turen aurenki takeson kashewa kawai" shuru tayi tana mamakin munira,lallai wanda Allah ya ganar dashi ya huta,saita rabu da ita ita da banzan tunaninta.Cikin rahama da jin qan ubangiji,da wani yammaci tana kwance a bushe kamar wadda ta shekara jinya,ubangiji ya aiko mata da bushira,qawarta tun zamanin yarinta.A gigice ta miqe ta nufi bushira,suka rungume juna
"Bushira,ya akayi kikasan gida na?,yaushe kika dawo?" Tambayar data fara jefa mata kenan tun kafin ta zauna,murmushi tayi tabi iman da kallo
"Amarya hala laulayi kika fara,irin wannan dashewa haka?" Maganar sai ta taba zuciyar iman din sosai,har rauninta ya bayyana saman fuskarta,duk.yadda takai ga dannewa saiga hawaye suna ambaliya kan fuskarta,rudewa bushira tayi sosai
"Subhnallah,meye haka iman?,daga magana?,ko na miki ba dai dai bane?" Kai ta girgixa ta qanqame bushira tana fashewa da kuka
"Ina cikin tashin hankali bushira,tunda nayi auren nan ban taba jin dadinsa na kwana uku ba,Allah ya mallakamin abinda na nace akansa,amma kuma sai ya barni da iyawata"
"Zauna muyi magana a nutse" bushira ta fadi tana zaunar da ita saman kujera hankalinta a tashe,babu haufin komai ta shaidawa bushira duk yanayin da take ciki,saboda a duniya a yanzu cikin ranta tana jin babu qawar data kai qawar quruciya,qawar islamiyya,qawar da aka tashi a unguwa tare,qawar kusa da gida wadda ta fito daga gidan tarbiyya,ki qaraci tara sabbin qawayenki,daga makarantu ko ma'aikatu,qasashe da garuruwa,mawuyacine ki samu irinsu,sun saki kin sansu ciki da bai.Bushira ta jina jinjina tarin matsalolin da suka dabaibaye iman din watanni kadan da aurensu,ba shakka akwai wata a qasa,saita daga kai ya dubeta
"Me ya kawo rashin aurenki da ya amin,don na tabbatar nayi imanin yana sonki,sonki yakeyi kamar yadda nayi miki hasashe" kai tsaye ta amsa mata da furucun dake fita daga bakinta cike da tarin nadama qarara
"Ya ajjiye duk wani abu a gefe ya kalleni ya gayamin yana sona,amma nasa qafa na shure,na shaida masa bana sonshi bassam nakeso,saboda a lokacin soyayya ta rufemin idanu,ina ganin bassam ya fishi cancanta Duk abinda ya biyo baya ta gaya mata tsaf
"Subhanallah" bushira ta maimaita sau uku sannan ta dora
"Dukkan wata matsala da kika ci karo da ita,kece kika kirawa kanki ita,tun inaca na fara jin wai wai 'yan gidanku basuson aurenki,na tabbatarwa kaina akwai abinda yake faruwa iman,bakisan ba'a musu da iyaye ba?,bakisan bayan bautar Allah kada ka hadashi da abokin tarayya babin iyaye shine abu na biyu da Alla yake fadi ba?,saboda girmansu ya hada haqqinsu da bautarsa?,bakisan koda kin fisu gaskiya da hujja qarara mabayyaniya mawuyacine Allah bai jarrabeki ba?,abar ta batun ya alameen tunda yanzu wani kike aure amma inason na gaya miki,kin tafka babbar hasarar da bazaki maida gurbinta har abada ya alameen?,kusan shi ya raineki,baya ga inna da malam yafi kowa sanin ciwonki,yafi kowa sanin me kikeso da kuma abinda bakiso?,yafi kowa tattalinki?,shine karatunki suturarki da duk wata walwalarki,koda qiyayya kike masa azuciyarki haiqan....iyaka wadan nan abubuwan basu isa su tsaidashi a mizanin wanda ya cancanci aurenki ba?.iman.....ina tunaninki ya tafi da har kika zaci samun wani makwafin ya alameen a duniyarki?" Fuskarta ta kifa gaba daya saman pillow,tana jin tsakiyar kanta kamar ana yamutsa mata kwanya ko ana mata hajijiya a tsakiyar kanta.
Yanayin yadda ta shiga rudu da yawa ya sanya bushira sassautawa,ta fara kwantar mata da hankali da kalamai masu taushi,bayan ta sanyata ta sauke dukka wani social network dake wayarta,ta kuma shaida mata ta jirayi dawowar mijinta,ta bibiyi maganar a nutse,kada tayi hanzarin yanke hukunci gudun nadama ko dana sani,saboda zai iya yiwuwa sharrin mace ne da kaidinta,muhimmin abu kuma na qarshe da taja hankalinta shine,ta nace ta kuma dage ta dai daita tsakaninta dasu malam
"A yanzu babu abinda nake da buri sama da na ganni a tsakiyar mala da inna,saidai abunda nake fuskanta a duk sanda naje ganinsu da sunan ziyara ya tursasa min zama gefe guda,abunda ke cikin idanuwansu da irin kallon da sukeyimin,sun gaza fahimtar ba dukiyar bassam bace ta jani ga aurensa,koda akwai tasirin dukiyarsa wallahi bushira bame yawa bace,amma rannan inna cemin tayi,wai na matsa da zuwarmusu gida,ta zaci zan canza wasu iyayen ne ai masu wadata,tunda sudin basu da komai,basu kuma ajiye komai ba Kai bushira ta jinjina
"A irin wannan situation din ba kowa ne zaki gaya masa haka ya yarda ba,amma hakanan zaki ci gaba da zuwa kina fuska tarsu da dukka maganganun da xasu gaya miki,yawan maganganun da zasu gaya miki yawan dafi da tsatsar dake wankewa daga zukatansu a kanki kenan,a haka a hankali a hankali komai zai dinga wankewa daga zuciyarsu" kai ta gyada,qwarai taga hikimar hakan,hasashen bushira yayi dai dai
"Amm sannan kuma" bushira ta fadi baya tayi gyaran murya,da alama maganar da zatayi tadanyi mata nauyi
"Maganar matsalar mijinki,ya kamata ki tuntubeshi ku tattana,zama haka bazai yiwu ba,duba da cewa haqqinki ne a kanshi" ta qarashe maganar tadan murmusawa kadan. Dan qaramin tsaki iman taja
"Manta da wannan bushira,ana ta kai wa yake ta kaya?,a wannan yanayin da nake ciki?, infact ma gaba daya Allah ya zaremin abun daga zuciyata,sau tari ka nakan tambayi kaina ko bani da cikakkiyar lafiya ne?,ko romance din da muke na gaza jin wani cikakken wani abu akansa......ni bushira ban ma yarda baida lpy ba zuwa yanzu,idan har hakane,me yakewa ita wannan karuwar data turomin hotunansu cikin qazamin yanayi?,jagwalgwalon da yakemin itama yake mata?" Tayi maganar wani abu me daci da tauri yana tsaya mata a maqoshi.
Girgiza kai bushira tayi
"Kada ki zargi haka,karuwa ce,indai yana da kudi koda bashi da mazantaka zata iya zama dashi,matuqar zai kashe mata abinda yake dashi,dama ba abunda sukeyiwa kenan ba?" Kai iman ta gyada mata,tana dan samun relief cikin zuciyarta,ita kanta bushiran tasan ta gaya mata hakanne kawai saboda ta kwantar mata da hankali.
Cikin yanayin quncin da take ciki kaso dari kaso hamsin ya zagwanye,bushiran ce ta tada girki da kanta ta shiga kitchen,ta shirya lafiyayyar jalop rice,ta zuba musu tare,ta hilaci iman din sai data ci mai dan dama,saidai har zuwa sannan kanta na mata ciwo,tana daurewa ne,sannan ta danji qwarin jikinta abincin da taci.
Ya kamata shima kije kiga likita,bai kamata kita zama da ciwo me naci irin haka baki nema magani ba" bushira ta bata shawara sanda ta shirya zata tafi,kamar ta hana bushiran tafiya haka taji,zuciyarta ta dinga yi mata rashin dadi,batasan tayi missing childhood friend dinta ba sai a yanzu. Haka ta rakata har qofar gate,bayan ta saka mata kudi masu yawa a jakarta,wanda sai da tasha qwarbai da bushiran sannan ta karba,a take ta hangi bambamci qarara mai kuma tarin yawa tsakaninta da muneera.
"Anya da bushira ce muneera zata barni na auri bassam na qyale ya ameen?" Tambayar data dinga yiwa kanta kenan sanda take dawowa zuwa sashents
"Muneera qaunata take ko kuma qina?" Tambaya ta biyu da tazo kanta kenan,wadda ta kasa tantance ta.
Tana sanya kai a parlor din nata taga shigar fahima dressing room dinta,cikin mamaki tabi bayanta,duk da tuni zuciyarta ta gama gaya mata abunda ya shigo da fahiman,tunda ba yaune karonsu na farko da suke mata irin hakan ba.
Dai dai sanda ta shiga fahiman tayi nisa a dudduba laces dinta dake rataye jikin hanger,sau daya ta juyo ta dubi iman din taci gaba da abinda takeyi,kai bakace gidanta kuma dakinta ta shigo mata kanta tsaye ba tare da saninta ba.
Daya daga cikinsu ta ciro daga hanger din,ta kalli jikinsa sosai sai ta ninkeshi,ta matsa sashen takalma ta fara dubawa suma.
A yau din ranta a matuqar bace yake da rainin hankali da kuma iskancin da suke mata,abun ya fara wuce makadi da rawa,sun kuma fara wuce iyaka,don haka ta bude bakinta da dan qarfi tace
"Wai lafiya kiketa yimin dauki dai dai cikin kayana?" Juyowa tayi ta watsa mata wani kallon banza
"Kayanki ko kayan yayana?,ins kukaga arziqin da zakizo da wadan nan kayan daga gidanku" maganar ta sake tunzura iman,a fusace ta qarasa cikin dakin,bata tsaya wata wata ba ta fusge lace din dake hannun fahiman
"Duk da yayan naki ne ya siya na hana bazan bayar ba,matuqar da sunana yayan naki ya siya to babu wanda ya isa ya dauka ko ya tabamin kaya babu izinina,ki fita ki bani waje tun zuciya bata debeni na miki matsiyacin dukan da za'a sake ganeki" tabbas a yadda taga idanun iman din sun sauya kala tana kuma bubbudesu da kyau,furucinta ke nuna tsantsar tunzurarta,tunzarar da bata taba ganin tayi makamanciyarta ba tabbas zata iya aikata abinda take fadi,don haka ta saici hanya tana dubanta Zakisan dani kike,sai kinyi nadama
"Na jima banyi nadamar ba,wacce nadamar ce ta ragemin banda wadda nake ciki,yi waje!" Sai fahiman ta juya tana ficewa daga dakin,iman din kuma ta zube a wajen dafe da kanta da takeji kamar zai tarwatse[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 31
Da qyar ta kawo lanta parlor dafe da kan nata da yake sara mata kamar xai fado,tana zaune anan taji anata fama knockin
"Madam ki bude.....hajiya ce take kiranki" abinda 'yan aikin da mom din keta aikowa taxo suke fada kenan ta window dun parlor,saidai babu wanda ta saurara a cikinsu bare ta bude musu qorar.Muryar mom dince daga qarshe ta bayyana da kanta a qofar falon,saidai a sannan sama sama ma take iya jin abinda take fada,saboda yadda kunnuwanta sukayi dimm gaba daya,ta daina gane komai kamar wadda ta suma,irin suman nan na ido biyu,kamar kuma wadda ta tafi duniyar mafarki Sanda ta koma normal data duba agogo awanni ta diba a hakan,ta miqe da qyar ta koma bedroom tana kiran sunan Allah.
Wannan ya sanya a washegari dole ta miqa kanta asibiti,dr ahmad Abdullahi shine likitan da take gani,yayi mata gwaje gwaje sosai,bayan ya kammala dubata,sakamakon da ya bayyana shine ta kamu da hawan jini,don jininta yakai 190,mamaki sosai ya kama dr ahmad,ya sake daga kansa ya kalleta,sannan ya duba shekarunta dake rubuce jikin file dinta na asibitin.hajiya aqananun shekarunkin nan bai kamata ace jininki ya hau har haka ba,ya kamata ki sakawa ranki nutsuwa da salama.....ko meye yayi zafi maganinsa Allah,kiyi qoqarin kwantar da hankalinki ko domin lafiyarki,hawan jini mummunan ciwo ne dake da hatsari da kuma barazana ga dukka sassan jikin dan adam" wani abu me nauyi taji ya sake saukowa saman qirjinta,ta kwantar da fuskarta saman hand bag dinta,tana jin kamar ta gayawa dr Ahmad matsalolinta,mutum ne mai bala'in nutsuwa haiba da kamala,wanda tun farkon zuwanta asibitin ta zabi ta dinga ganinsa,saboda alamomi na riqo da addini dake damfare dashi
"Kiyi haquri hajiya,at younger age naki irin wannan. ko 20yrs baki kai ba bai kamaci kibar wani abu ya gadar miki da ciwon da zai tarwatsa lafiyarki ba" bai nemi sanin halin da take ciki ba,amma yayi aikinsa na likita ya kwantar mata da hankali da kalaman da suka dace.Sosai tayi masa godiya,ta kuma sawa ranta zatayi qoqarin bin komai a sannu kamar yadda bushira da dr ahmad suka bata shawara.Daga asibitin gidansu ta wuce,ta dauki aniyar yau koda zasu koreta kamar yadda suka saba ba zata ko ina ba,yadda innar ta saba tarbarta haka yau dinma tayi mata,saidai yau din da sassauci bata nemi ta koma gida ba,qarin wani ci gaban yau din bata raba wajen zama da ita ba,saidai babu ruwanta da ita,kamar ma babu wata halitta a dakin sai ita daya.Ko iya hakan ma ya yiwa iman din dadi,tayi kwanciyarta kan doguwar kujerar dake falon tana bin innar tata da kallo,abinda yadan sake mata dadi,yadda kusan sau uku suna hada ido da innar sanda innar take satar kallonta,addu'a take cikin ranta,ubangiji ya sassauta mata,ya sauko mata da zukatan iyayenta ko zata samu salama ta wani bangaren.Shima malam din daya dawo yau data je ta gaidashi babu abinda yace da ita,sai da yana alwalar sallar magariba sannan yace idan ta idar da salla ta wuce gidanta,kamar ba zata tafi ba,kamar tayita zamanta da iyayenta,kamar ta dawo da rayuwarta ta baya haka taji,saidai bata da wani zabi,bata kuma da yadda zatayi,tunda ita ta siyawa kanta ta kuma biya,tafiya ta kamata dole.Daga ranar ta samu.nayi,duk sanda taje asibiti checkup saita zarce gida,ba zata koma gidansu ba sai magariba,wannan ya sassauta mata damuwarta qwarai da gaske,sai taji duka sauran matsalolin dake tsakaninta da bassam minus ne,duk da suna qasan ranta suna cin zuciyarta,bacin rai yakan dawo mata a duk anda ta tuna da munanan hotuna da videos din da aka tura mata.
A wannan karon batasan bassam din zai dawo ba saboda ta ajiye wayarta gaba daya,a yanz ta sake tsanar wayar kwata kwata,ta fita daga kanta Ranar bayan ta idar da sallar azahar,ta dama yoghurt na L&Z da lallausar furar data debo daga wajen inna da ko ci kanki batace da ita ba sanda tasa hannu ta diba furar,ta damata da yoghurt din tasha,bata fiya girki ba,saboda a yanzun sam bata da appetite,kome zata dafa ba dadinsa zataji ba,ta fidda hijabin kanta ta koma saman doguwar kujerar falonta ta kwanta rigingine,hannunta daya saman kanta,idanunta a lumshe,qira'ar shaik shary al_afasy data kunna jikin tv na ratsa falon a hankali,tana bin qira'ar da boyayyen sauti,saidai kuma kana iya ganin yadda qaramin bakinta yake motsawa.
Alamun bude qofar falon bai sanyata ta bude idanunta ba,don bata raba dayan biyu su fahima ne,duk da cewa tun ranar da abun ya faru babu wadda ta sake shigo masa sashe,saidai yadda taji alamun ana tahowa inda take ya sanyata ta bude idanun nata,ta zubesu saman guskar bassam dake sanye da suit ash colour,blue din qwayar idanunta suke fitowar ta saboda rashin kwalli da kuma kodewa da idanun nata sukayi.
Fuskarsa a matuqar murtuke,ta danne zuciyarta ta miqe daga kwanciyar datayi sanda taga ya iso kanta ya tsaya,ta dauki remote ta rage sautin karatun ca qasa sannan ga furta masa sannu da zuwa.
Ciki ciki ya amsa mata yana ajjiye trolley dinsa idanunsa nabin parlor din da kallo.yana sassauta tie dinsa,kamar me neman wani abu
"Me ya samu wayarki?,inatason in sanar miki dawowata amma ba'a samunki"
"Matsala ta samu" ta amsa masa a taqaice tana kaucew kallon qwayar idanunsa,saboda wani tsanarsa data ji ta saukar mata lokaci guda sanda yayi mata zancan waya,wani baqi take gani yayi mata a idanunta,dukk wani kwarjini kyau da qaunarsa da takeji ta laluba taji.babu ko guda daya
"Meye amfanin kudin dana bar miki da bazaki iya dauka ki sayi wata ba" haushi tambayar tabata qwarai,idan kuma tace zata bude baki ta bashi amsa maganar ba zata fita da dadi ba,don haka sai ta miqe kawai a maimakon ta amsa masa,tasa hannu taja trolly din nasa zuwa dakinsa,dakin da tunda yasa qafa ya tafi bata sake shigarsa ba,dakinta da aka zuba mata kayan ameen tafi jin dadin xama cikinsa sau dub
Dukka motsinsa tana ankare dashi,sai wani ciccin magani yake da bata fuska kamar wadda tayi masa wani abu,abunda ya sake bata mata rai da dugunxumata yadda wayarsa ta fara harbawa da kira don masifa,ko awa guda biyu da shigowa cikin gidansa ba,kiran yana shigowa yana katsewa.
Banason hauka..just two hours?,ba haka mukayi dake ba,karki sake kirana,ki barni na huta" sune kalmomi na qarshe da taji daga bakinsa sanda take fitowa daga bandaki bayan ta gama hada masa ruwan wankan da ya buqata.Maganganun da suka tsaye mata a rai kenan,suka kuma sake fama mata mikin dake ranta,ta dinga hadiyar yawu da qyar,ko baya data gama hada masa abincin gaggawan data shirya masa takai masa daki parlor ta dawo tayi zamanta,bata tashi daga wajen ba saida lokacin sallar la'asar ya gabato,sannan ta koma dakin.
Bacci ta sameshi yana yi haiqan kamar wanda yayi tafiyar qasa,kamar ya shareshi ta wuce sai kuma taga bai kamata ba,a qalla akwai hakkin salla a wuyansa,don haka ta qarasa ta fara qoqarin tadashi,saidai juyin duniya yaqi tashin yace ta rabu dashi,ba tun yau ba,bai cika damuwa ba da lokacin sallah saboda ya kubce masa.
Kwarai taso dauke kanta daga wayarsa daketa blinking,da alama a silent ya sakata,saita dawo da baya,zuciyarta na rinjayarta kan ta duba wayar ko zata samu haske kan abinda yaqi gushewa daga zuciyarta,yake kuma kai komo.
Sofa din dake dakin can wata corner ta koma ta zauna akai,hannunta na rawa zuciyarta tana bugawa ta bude wayar,babu nambobin sirri,hakan ya bata damar wucewa kai tsaye zuwa WhatsApp dinsa.Charts ne burjik da 'yammata iri iri,wasu hausawa wasu yare,harda 'yan wasu qasashen,dukka hirace dake nuna qauna da soyayya tsakaninsu,sai kuma receipt na kudaden da yake turawa wasu daga ciki.Harta gota sunan ta dawo da baya,tabbas yayi kama da sunan wadda ta tura.mata saqo wancan watan,ba tare da bata lokaci ba ta danna ta shiga.bata tsaya duba saqon qarshe ba tayi scrolling zuwa sama,saboda tana son sanin meye tsakaninta dashi tun daga farko zuwa yanzu,sai data je qarshe sannan ta fara bin saqonnin,wanda suka fara ne ran uku ga wata,data duba date yayi dai dai da kwananta guda a gidan bassam din,saqon farko shine ya fara tura mata shi kamar haka
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 32
_Baki da hankali ashe jessica?, Da gaske kike dama sai da kika aikata din?,ta yaya zaki haramtamin matata ta sunna?_
Emoji na dariya ta fara aiko masa sannan tace
_mahaukatan ai biyu ne,wato ni da kaii,ta yaya kake da tabbacin bazan aikata abinda na niyyata din ba?,ta yaya kake tunanin zan sake barwa wata diya mace kai?,shekara biyar?,cikakkun shekaru biyar kana yaudarata kan zaka aureni,to na gaji da alqawarin banza,daga yau din kai nawa ne ni kadai,naga macen da zata sake morarka bayan ni_
Bayan wasu sakanni da basu da yawa ya maida mata amsa
_karkiyimin haka?,ki fadi ko nawa ne zan biyaki_
_banason komai daga gareka,aurena nakeso kawai kayi_
_kinsan me kike cewa?,addininmu ba daya bafa?_
_eh,kowa sai yayi addininsa ai ko_
Sauran maganganun da suka biyo baya gaba daya ciki bacin rai yake mata su,da kuma barazana,daga qarshe saqonnin suka yanke,suka shiga wani kwanan watan na daban.
Hoton passport dinta ne da aka bugawa visa ta qasar daya ce mata zaiyi tafiya a sannan,idanu iman ta fitar tana jin wani tashin hankali,dukka saqonnin sun bayyana mata cewa dukka tafiye tafiyen da zaiyi da Jessica yake tafiya,ita ta zame masa madadinta.
Tashin hankalin da ba'a saka masa rana,wato daman watace tayi masa sihirin da bai iya aikata komai idan bada ita ba garin biye biye da neme nemen matansa?,wannan wacce irin masifa ce,dama tafiyar da yakeyi tare suke tafiya,ashe shi yaba samun abunda yakeso shi yasa ya jingineta,ya daina damuwa da situation dinsa,ashe ba lalura gareshi ba?.
Kamar yasan meke faruwa yayi juyi cikun barcinsa da zummar gyara kwancinyarsa,idanu suka hada tana riqe da wayarsa hawaye sun mata face face saman fuska,sai yadan miqe da hanzari ya zauna saman gadon
"Me kikemin da waya?,miqo min wayata" yayi maganar yana hade rai,cikin sautin kukan data kasa controlling dinsa ta fara magana
"Ashe dama haka kake bassam?,ashe kai din baqin kumurcin maciji ne?,ashe dafin da yake tattare dakai kenan?,manemin mata ne kai wata kake dauka kuyi tafiya nisan duniya wata da watanni kabar matarka ta sunna a gida?baya ga tulin yammatan da kakewa hidima bassam,har wata ka ajiye?,dadironka......." Tsawa ya daka mata
"Dalla malama dakatamin mana,ni zaki saka a gaba kamar dan cikinki kinamin wanna titsiyen?,ko uwata bata isa ta bimin qwaqwaqwafi haka ba bare ke,abinda yasa tun farko banson aure saboda banason bin diddigi da takura,kema da nake ganinki me mitsi mitsin shekaru har kinsan bin diddigin spouse dinki?,yaushe kikayi wannan wayon?" Cikin bacin rai ta fara maida masa amsa
"Ko yau nafado duniya matarka ce ni,kuma ka dade kana wasu abubuwan a gabana ka manta?"
"And so what?,eh matatace ke......me kika rasa?,ci sha suttura ko kudi?"
"Basu nake buqata ba,don ba don saboda su na aureka ba" wata dariya ya saki yana zuro qafafunsa qasa idanunsa cikin nata
"Zuqi ta malle inji bahaushe,shi yasa naga kinqi dan uwanki ko.....ke,bari na gaya miki,tarrr idanuna suke kallo kowacce mace,a zamanin nan dama mace tana maka soyayyar gaskiya ne?,duk wadda tace tana sonka saboda Allah qarya take maka,shi yasa nake amfani da damata,in kashe miki kudi nima na amfana dake,na sakar miki komai......saboda haka banason takura ko kuma sanya idanu,ki barni nayi rayuwata yadda na saba,banason takura" cikin xafi da tsananin fushi ta miqe
"Amma ka shayar dani ruwan mamaki bassam...."
"Bakiga komai ba,abinda kika gani kika maqalen shi sauran suka gani suke tare dani,kalleni sama da qasa......wanda bai kaini komai da komai ba ya tara yammata bareni da babu abinda Allah ya rageni dashi, relax 'yammata,kici arziqi kibar arziqi a inda yake,idan kina tunanin zan zauna nayita lallabaki yanzun kina batawa kanki lokacine kawai,i already won the election.......so no need naci gaba da campaign,kin gane?"
"Amma ka zalunceni,ka cutar dani,kakuma cutar da zuciyata......".
Dif wuta ta dauke mata saboda saukar wani zazzafan mari saman kuncinta,wanda ta manta a duniyarta rabonta da irinsa saboda gata da kulawa da take samu
"Stupid kawai........don kinga na qyaleki bayan iskanci da wulaqancin da kikayiwa mahaifiyata?,ina da labari fa amma na dage miki qafa,ko kin dauka nima bansan kima da darajarta ba kamar yadda bakisan kimar naki ba?to ki kiyayeni wallahi, you worth nothing to me,ni mace ba kayan gabas bace a wajena,yanzu yanzu ina iya wullar da ita na canzata da wata" Kalamansa sun matuqar girgizata tare da taba mata tunani,ta kasa koda qwaqwaran motsi bare ta aiwatar da komai,hannayenta saman kuncinta har ya zura slippers dinsa yana jan tsaki bayan ya dauki wayarsa ya fice daga dakin.
Komai tsaya mata yayi cak,ta daina gane komai ta kuma daina fahimtar komai,batasan me zatayi ba,kamar yadda batasan meye abu na gaba da zai sameta ba,saida jikinta ya bata amsa ta hanyar daukar rawa,wanda a take zazzabi yayi mata kirif,jikinta gaba daya ya fra shaking,qafafuwanta suka gaza daukarta,ta sulale a wajen ta cure waje daya.
Wani mugun zazzabi mai uban huci ne ya rufeta,ta jima zaune a wajen kafin taja jikinta zuwa nata dakin,tayi curewar alkaki tsakiyar gadon.
Maganarma ta hana kanta kuka bata taso ba,duk da yadda takejin kanta yana barazanar rabewa gida biyu,ji take kamar duniyarta zata tashi,nadama iya nadama,dana sani mara iyaka wadda ta ninka wadda takeyi a baya tun 'yan kwanaki da aurenta da bassam,ashe ita din banza ce?,ashe ita din wawuya ce?,ashe itadin bata da hankali?,dukka a ture abubuwan da suka faru gefe,a dauko maganar sanin ya kamata dangane da iyaye,tabbas ta tozarta su malam da inna,ta kuma ci amanar ya alameen,ta tabbata BUTULU KUFAN WUTA kamar yadda inna ta kirata dashi,kallonta kawai bassam yakeyi?,amma yayi mata shuru tun a sannan bai gaya mata gaskiya ba saboda burinsa na aurenta?.
Ya tabbata bassam fasiqi ne........haka dabi'arsa take ko daga baya ya sauya,sam sam wannan ba bassam din data sani bane,ba shine bassam din da tayi soyayya dashi a waje bane,shi kadaine hakan?,ko dukka maza haka suke?.
Kafin wani lokaci yanayin da take ciki ya ta'azzara,taji kamar ranta na shirin fita ta numfashinta ne,ta tabbatar taci gaba da zama a haka komai zai iya faruwa da ita,asibiti yafi kamata taje,to amma waye zai kaita?,waye xai tallafeta,bushira da munira sukazo kanta,bushira bata iya tuqi ba,munira ta fita wayewa ta wannan fannin,duk da a yanzun bataso ko qaunar alaqarta da munira taci gaba,amma dole ita din xata kira.
Tana tsaka da yi.mata bayani numfashinta ya fara seizing,wayar ta sulale mata,ta runtse idanunta tana ambaton sunan Allah.
Sanda munira ga qaraso tuni ta fara ficewa daga hayyacinta,haki take sosai,muniran ta kamata bayan ta duba key din motarta,suka fito ta sanyata a motar suka fice ba tare da kowa ya sani ba.
Cikin sa'a suka taras dr ahmad ne on duty,cikin gaggawa ya karbeta ya shiga bata taimakon gaggawa,hankalinsa yayi matuqar dugunzuma da ganin yanayin da take ciki,at her age bai kamata ace tana shiga mummunan yanayi haka ba,shekarunta sunyi qanqanta da yawa,don haka bayan ya daidaita komai ya shaidawa munira yana buqatar ganin iyayenta ko mijinta.
Washegari ta tashi jikinta da dan dama dama,saidai kuma babu qarfi sam,
"Tun jiyan na gayawa bassam kinga har sha biyu na rana na shirin yi bai shigo ba" inji munera dake danne dannen waya,kai ta kada,sam batayi mamaki ba,saboda gaba daya tasan cewa bassam ya sauya,ba shine bassam data sani ba,abun tambayar ina tulin soyayyar da yake mata?,ina tulin soyayyar daya dinga nuna mata?,ina tayi
"Bani waya na kira inna" shine abinda tace da ita maimakon tsayawa su tattauna batun bassam din,ta miqa mata,ta saka numbers din inna data dade da haddacesu ta soma kira.
Bugu biyu ta daga,cikin raunanniyar muryarta ta fara gaidata,innar ta amsa
"Inna bani da lafiya,ina asibiti"
"Allah ya sawwaqe,ya baki lafiya" ta amsa mata kai tsaye,sai shuru yadan biyo baya,iman din tayi ta maza tace
"Inna,ba zakizo ki ganni ba?" Maganar tadan taba innan,amma sai tayi kamar bata jita ba,qarshe ma dif ta yanke kiran.
Hawaye ne ya biyo kuncin iman din,ta tabbatar lallai tana neman taimako,tana neman sanya hannun wani babba cikin al'amarinta,idan ba haka ba za'a wayi gari a samu baqinciki ya kasheta.
Ba bassam ne yazo ba sai dare,koda yazo dinma fada ya fara yi mata wai kan me zata saka qafarta ta fice daga gidan bata shaida masa ba?,ai ba zaman kanta take ba,abun ya daure mata kai,don haka ta bawa banza ajiyarsa,ana tsaka da haka dr ahmad daya dawo zaiyi night round ya taras dashi
"Banda abinka,ai kone patient irin wannan yayi ba'a masa fada a yanayin da take ciki,gaskiya ku kula da.lafiyarta,saboda matuqar za'a bar irin wannan abun na yawaita faruwa da ita zai iya tana zuciyarta,ko ya sanyata ta shiga mummunan yanayi" sake duddubata yayi ya rubuta mata sallama da magunguna,tare da yi mata jan kunne kan ta kula da lafiyarta.
Ko a cikin mota babu wanda ya kula dan uwansa,tuqinsa yake ita kuma ta maida kanta saitin window,hadiyar zuciya kawai take tana qoqarin hana kanta shiga bacin rai saboda warning din da dr ahmad yayi mata.
Suna isa gida ta bude motar ta fice abinta,dakinta ta shiga,ta cire kayanta ta fara shiga ta watsa ruwa,ta hado da alwala tayi sallar magrib data kubce mata ta hada da isha'i,sai taji nutsuwa 'yar kadan ta saukar mata,sannan ta miqe ta fara laluben wayarta.
Batayi duba me yawa ba ta ganta,ta koma gefan gadonta ta zauna tana lalubar number wayar ya gana,ta tattara dukka nutsuwarta. Wayar na ringing zuciyarta na dade karyewa,rauni yana cikata,tana sake qwararawa kanta gwiwa,cike da fatan ya gana zata shiga lamarin nata,ta kuma samar mata da mafita.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 33
Ba jimawa muryar yagana ta bayyana da sautin sallama,muryarta na rawa ta amsa mata sallamar tata,da fari ya gana bata fahimta komai ba cikin muryar iman din ba,saima fara tsokanarta da tayi da cewa
"Ja'ira,tunda na miki haji da ummara kika manta dani sai yau da kika gama sheqe amarcin watannu shida?"
"Uhmmm" kawai iman tace,don idan tace zata bude baki ta bada qwaqwarar amsa kuka ne zai kece mata
"To ya gidan,ya angon naki?,ina fata anata biyayya ko?" Tamkar wannan tambayar kukan yake jira sai kuwa ta fashe dashi,a rude ya gana ke tambayarta lafiya,saidai ta kasa cewa da ya gana komai,sai sautin kukan dake fita daga bakinta,wanda ya faro ne tun daga qasan zuciya,yana bayyana tsantsar quncin da zuciyarki ke ciki.
Bata hanata kukanta ba,sai da tayi mai isarta sannan ta fara labartawa yagana komai,babu abinda ta boye mata a ciki.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" wannan kalmar yagana ta dinga maimaitawa cikin rudewa,hankalinta yayi matuqar tashi
"Kiyi shuru hajar,ya isa" ya gana keta fada
"Wannan shine abinda su malam ke guje miki, shine abinda muke guje miki gaba dayanmu" ta fada feeling her guiltiness,tana ganin kamar itama me laifi ce, da nata kason da ta sanya baki malam ya sauka daga qudirinsa,duk da cewa haka yaran sukaso,duk da cewa babu wanda yasan gaibu,ba wanda yasan hakan zata kasace sai Allah jalla wa 'ala.
Kwantar mata da hankali ta dunga yi da kalamai masu taushi,tare da nuna mata illar saka damuwa a ranta a situation din da dr yace tana ciki a yanzu,daga bisani ta bata shawarwari da kuma jan hankali
"Kowanne gidan auren akwai nashi qalubalen hajar,ki zama jajirtatta ki aiki tuquru ki gyara gidanki,zanzo kanon zan zauna da malam da binta din,suma dole zuwa yanzu su sauki ai su tayaki da addu'a,idanma sunqi na tabbatar cikin zukatansu babu wanda zai kaisu dakuwa da halin da kika shiga" ba maganar data sake sa mata nutsuwa irin wadda yagana din ta gaya mata na zata sasanta tsakaninsu dasu malam din.
Sun jima kan waya tana bata addu'o'i da shawarwari,har sai data tabbatar da ta samu nutsuwa.
Ta sake kiran bushira ta shaida mata,itama ta shiga damuwar,saidai shawarwarin data batan sunyi kusan kamanceceniya dana yagana,duk abinda suka fada ya dace kuma dai dai ne,saidai abu daya da takeji cikin ranta,bassam da aurensa gaba daya sun fice mata fit a rai,kamar fitar kibiya daga cikin baka,wannan ya bata salama,ta tattara hankalinta wajen shan maganinta,tsakaninta da bassam saidai kallo,sai kuma idan sun hadu a parlor,wannan yasa ya dauka fushi take dashi shi yaaa ta watsar dashi,shi kuma sai ya dauki aniyar quntata mata,hakan yasa ya sake fidda ainihin halayyarsa,yake baje kolinsa na hira da 'yammata barkatai,da kuma fiya joint joint dasu yana musu barin kudi,bata duk wani chart bare ta gani ranta ya baci,whatsApp kawai takeyi,shima kuma already tayi mute na status din nasa.
A yanzu kallon kanta take a matsayin me gadin da gaske cikin gidan bassam din,komai nashi ya daina damunta,hakanan ta tattara rayuwarta waje daya,kama daga suttura da dakin kwana ta koma amfani da wanda tazo dashi daga gidansu,sai abunda ya kama dole zatayi amfani da nashi.
A hankali ta fara samun sauqi da nutsuwar rai da ruhi,musamman data maida alqur'ani abokin hirarta,gaba daya ta zama wata iri,wani irin sukuku,ba hirar nan ba kuzari me yawa,babu kuma wani ado na azo a gani,saidai bata yada tsafta da kuma qamshi ba,saboda dashi aka raineta.
Bata damu ba sam,tunda yanzu ta samu matsayin kiran malam da inna su daga,ta kuma gaishesu,hakanan idan taje sun daina korota gida,iya wannan ya isheta.
Bushira na dan zuwa mata,itama idan taje unguwar takan qarasa gidansu susha hira sosai,ta janye jikinta sosai da munira,idan tazo kadaram kadaham,ta daina gaya mata kowanne yanayi da take ciki,hakanan ta daina shawara gaba daya da ita.
*_WATA SABUWA......inji 'yan ca ca_*
Da yammacin ranar litinin,bayan ta idar da sallar la'asar ta fito parlor zuwa kitchen don samarwa kanta abinda zata sanya a cikinta,don rabonta da abinci tun breakfast da tayi da tea da two slices na bread.
Rasa me zata dafa tayi,saboda cikinta ne ita daya,tuntuni ta sauke dafa abinci da bassam,don baya shigowa gidan sai dare ya tsala,sha biyu da rabi daya har biyuma wani lokaci.
Busashen kifi ta gyara hade d wake,ta tsaida sanwar jalop din taliya da wake da busashen kifi,saita koms parlor sanye da hijabin sallarta,hannunta maqale da carbun nan counter wanda a yanzu bata rabo dashi.
Ta gama lazuminta zaman shurun ya mata yawa,saita kunna tv,abinda yakan jima batayi ba kenan,ta fara kallon wani film na tarihin sahabbai daga wata tashar da pure larabci,saidai kuma akwai subtitle na turanci.
Film din ya dan dauki hankalinta,saboda ta kwana biyu bata saka tv a idanunta ba,har sai da sanwar ta jima tana tafasa sannan ta farga,ta miqe da hanzari ta koma kitchen din,ta hada komai sannan tayo hanyar parlor din.
Cak ta tsaya ganin baqin da bata barsu a parlor din ba amma ta dawo ta taras dasu,wasu a tsaye wasu a zaune,wasu kuma daga bakin qofa.
Mom ce ita da fahima fairuza da nasma,sai kuma anty billy wadda take qanwa ce ga mom,shahararriyar mara mutunci ce,wadda bata dauki talaka a bakin komai ba,tunda suka taba haduwa da iman sau biyu iman din bata sake bari sun gamu da ita ba,saboda zallar kallin qasqanci da take jifarta dashi,ta lura ma kusan anty billyn tafi mom zaqewa akan auren iman din da bassam.
Cikin dakiya da sanyawa ranta nutsuwa ta qaraso falon
"Sannunku da zuwa" ta fada a nutse,babu wansa ya kalleta ko ya tanka mata a cikinsu,saima tsaki da Anty billy taja,tana mata wani irin kallo kamar zata sheqa mata mari.
Batabi ta kanta ba tunda ita din ba dolenta bace,saita dubi mom
"Mom ku zauna,ga guri"
"Rasa wajen zama nayi tun daga cikin gida na da zanzo nan na zauna?......kai.....David" ta qwala kira,saiga wasu daga cikin qattan ma'aikata maza na gidan su hudu sun shigo
"Ku shiga store din gidan nan,ku fiddomin dukka wani kayan abinci da abinsha dake ciki ku kawo min shi nan" tak iman din bata ce ba,sai ta koma gefe ta basu hanya kawai tana kallon ikon Allah,gami da tambayar kanta abinda yake faruwa.
Kusan mintuna goma suka kwashe suna fidda kayan,hadda buhun shinkafar da aka bude aka fara amfani dashi,matsowa tayi gaban kayan,ta nuna shinkafar da aka fara amfani da ita tace a maida store din,amma dukkan wasu sauran abubuwan amfani da kayan alatu,kama daga waken gwangwani,kifin gwangwani,indomie,madara lemuka ruwan roba kai hatta da kifi da nama dake cikin fridge tasa an fiddasu,duka aka tattare mata su tace akai sashenta.
Dubanta tayi sosai bayan sun fice
"Nasan zaki ta yiwa kanki tambayar dalilin da yasa na aikata haka ko?,to ba komai bane illa gajiya da nayi da ganin ana ciyar da banza wofi,wata shida da aure amma banga alamun samun qaruwa ba,dan tofe tofen yawu da amai da zazzabin dare duka babu,to meye amfanin ci dake?,dadin ai yayi miki yawa,ki kwana a ac,kici me kyau kisha mekyau,ku saka suttura me tsada amma baby wanu alfanu da kike kawo mana........"
"Wallahi ya hafsa sakar mata maqoshin da kukayi ne ma yasa kwanaki can ta fara yunqurin soma rashin mutuncin nan" kai mom ta girgiza tana kallon billy
"Ai ni ba'a haifi matar da dana zai auro ta rainani ba,kosu mimi da ake gani muna zaune lafiya bina suke su da iyayensu suke wasu,wanda idan ama fadi sunansu ansan da zamansu,idan ita ban isa da ita ba ai na isa da dana ko?......saboda haka" ta fada tana maida dubanta ga iman
"Ki kwana da sanin bassam aure xaya qara,yarinyar da zai aura din tana nan zuwa cikin gidan nan don su fahimci juna,wannan satin ko kuma sati na sama" daga haka suka juya suka fice daga sashen nata.
Shuruuuuu tayi bata iya tanka musu da komai ba,bakinta ya riga da yayi nauyi,idan ma tace zata tanka din me zatace musu?,kowa ya siya rariya yasan zata zubda ruwa,kome ya faru da ita ta jawa kanta,idanunta keta radadin yajin tara hawaye amma ta daure ta hana kanta,bata dawo saiti ba saida hancinta ya fara jiyo mata qaurin girkin data dora,kamar wadda babu laka a jikinta ra nufi kitchen din,ta kashe gas din gaba daya ba tare data damu ta duba ya dahu ko bai dahu ba,illa dai ta bude tukunyar,tabi abincin da kallo kamar wata shashasha,so take taga meye abinda bata ci a gidansu?,meye malam bai ciyar da ita ba?,meye yayyenta basa siya mata idan tace tana da buqata?,wacce cima ce sabuwa a wajenta cikin abinciccikan dake cikin gidan?malam da 'yan uwanta ba ragwage bane,basu yarda taga wani kalar abincin a wani gida tayi sha'awarsa ba'a girka shi a gidansu ba,saita saki murfin tukunyar,ta sulale a wajen,ta kuma saki kukan da taketa faman hana kanta yi,abincin da bata ci ba kenan.
A kwanakin ta fahimci abinda mom din ta aikata da sanin bassam,tunda gaba daya duk wani abu na buqata idan yanaso sassan mom din yake tafiya abinsa ya dauka yayi sha'anin gabansa dashi,idan kuma na amfanin koda yaushe ne,sai yake zubawa cikin freezer na falonshi yake amfanin da abunsa.
Koda wasa bata taba daga kai kota nuha ta damu ba ko ta gane abinda yake aikatawan,a yanzun saukowar iyayenta yafi komai dadada mata rai,hakanan ta fannin abinci dama a yanzun ba wani shiga cikinta yake sosai,so duk abinda ta samu ci take ta kwanta,idan bai mata ba kuma tana fiddawa cikin kudinta tayi magana da masu gadi su siyo mata,ko kuma ita din idan ta fita,musamman ranakun ganin likitanta,ganin likitan da babu abinda ya shalli bassam dashi,komai ita ke kashewa kanta cikin abinda yake ajjiye mata ada,don a yanzun ya daina ajjiye mata komai,tasan kuma duka daga umarnin mom ne,da kuma shima halinsa da ya bayyanar mata qarara a yanzu.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 34
Tun tana bedroom dinta take jiyo motsi da kai kawo cikin falonta,da fari tayi tunanin bassam ne,to amma jin motsin na sake matsowa dakunan kusa da ita ya sanyata ta zura gyara zaman hijabinta,ta ajjiye alqur'anin data qulla qawance dashi ta leeqo don ganin abinda ke faruwa.
Mamakine sosai ya cikata ganinsu fahima na wucewa da kayayyaki dakin dake bashi da tazara da nata,sai ta jinjina kai,batace musu komai ba ta juya zuwa ciki,don dama basu ganta ba,saidai kuma har yanzu tana tunanin abinda zasuyi cikin dakin,dawowa sukayi part dinta ko kuwa?,saita aje tunanin a gefe guda,ganin cewa bazai amfaneta da komai ba,ita dake lallaba lafiyarta a yanzun.
Ta jima tana jin motsi da buruntunsu amma duk da haka bata tashi ba,taci gaba da zarafin gabanta,har zuwa sanda ta gama abunda takeyi din,ta fita zuwa kitchen don ta laluba ko zata samu abinda zata iya ci.
Ta qofar dakin tabi,an jashi an kulleshi,saidai kana iya jiyo qamshin freshner dake tasowa daga cikin dakin,saita kauda kai ta qarasa kitchen din.
Dube dube ta tsaya yi,sai a sannan ta tabbatar lallai bata da wani sauran abinda zata iya ci cikin gidan,shinkafar data rage itama a yanzun babu ita,duk kyau girma da qayatuwar kitchen din dama gidan gaba daya amma babu abincin da dan adam zaici?,wani abu ya tsaya mata a wuya,tsahon rayuwarta a gidansu,bata taba bude ido a ma'ajiyar abincinsu taga babu shinkafa sama da kwano biyar ba,sai gashi yau a gidan aurenta,gidan da kowa yakema kallon ta samu aljannar duniya,gidan da ake ganin koda da dawisu da talo talo taso zata ciyar da kanta,a yau shinkafa gwangwani daya ta gagareta,ruwan famfo shine ruwan shanta musamman idan tayi saken da pure water dinta ya qare,ita kanta batasan suna ko ma'anar auren nan nata ba,saidai kawai tana so tayi biyayya ga abinda yagana tace,ko Allah zaisa ta zame mafa hujja kuma shaida a nan gaba.
Ruwan Lipton ta hada da kuma bread ta dawo dakinta,tana lissafa kwanakin da suka rage da zata koma ganin likita,daga can zata siyo abubuwan da suka samu kafin ta samu ganin bassam ta shaida masa,sabida a yanzu bata da guarantee na lokacin ganinsa.
Abunda yake bata mamaki yadda sam mom bata damu da irin daren da yake kaiwa ba kafin ya kawo cikin gidan,abinda ta fuskanta shine,hakan yana yiwa mom dadi saboda kawai a cusgunawa iman,bata damu da illar da hakan take dashi ba,bata damu da me sakamakon hakan zai haifar ba.
********. *******. *******
K'arfe biyu na rana tana zaune a falon tana yankan farcenta,sanye take d wasu blue black material wanda aka yiwa dinkin doguwar riga bubu,saiya yane kanta da babban dankwalin rigar,ta zauna anan dinne saboda tadanyi kallo fa ragewa kanta kewa da zaman kadaici,wanda dr ahmad ya gargadeta da hakan,baisan cewa zaman kadaici ya zama wani bangare na rayuwarta ba.
Kamshin turarensa daya fara busowa sosai cikin falon ya sanyata dago da kanta,bassam dinne yayi kwalliya sosai cikin qananun kaya,yayi kyau babu qarya,kasancewar yana da wannan baiwae ga daukar ido duk sanda yayi ado,rabonta da ganinsa idan bata manta ba zata iya cewa yau kwanaki bakwai ko takwas kenan,saita dauka kanta taci gaba da abinda takeyi,yayin da shi kuma ha qaraso inda take zaunen,idanunsa a kanta.
Sosai tayi masa kyau,duk biye biyensa har yau bai taba haduwa da mace me sassanyan kyau haka me tafiya da hankali ba irin iman din,duk da cewa ba wata zuzzurfar mu'amala bace take shiga tsakaninsu amma yayi missing skin nata mai taushi da wani irin qamshi,yasha kwatanta yadda zai tsinci kansa idan ya shiga duniyarta ta zahiri.....yanaji a ransa lokaci ya kusa da zai sanya jessica koda bata qaunar Allah ta kawo qarshen abindata aikata masa.
Wannan sharetan da yayi yanaji a ransa shine hanyar da zaibi kawai ya hukuntata,ya kuma nade tabarmar kunyarsa tsaf da hauka,sannan ta yaya kamar shi,shi din da mata ke Rububi mace kamar iman 'yar tsakuwa a cikin 'yammatansa,sabida tayi fushi ya zubda ajinsa ya lallasheta ko ya bata haquri?,yayin imanin dole tata zata kawota,a nan zai jata a qasa ya kuma nuna mata iyakarta,ta yadda nan gaba ko kara ya sanya ba zatayi sha'awar tsallakewa ba,shi yasa yaji dadin kwashe kayan abincin da mom tayi,ko iya su zasu ta kawo kanta gareshi.
Ya zaci zata furta wani abu,amma sai yaga ko sashen da yake ma bata kalla ba,har ya qaraci tsaiwarsa da gyara tie da kuma hannun rigarsa ya soma ganganrawa zai fice,mamaki fal ranshi,wanne irin miskilanci gareta,ya zaci kawo yanzu zatayi laushi tazo ta nema sulhu kamar yadda abokansa ke bashi labarin yadda sukeyi da matansu idan suka kamasu da laifi makamancin haka,sai gashi ita sake dauke masa wuta ma tayi gaba daya.
Karamin tsaki taja sanda ya fita,tana jin yana sake sire mata a rai,ji take kamar ta tattara kayanta tabar gidan,saidai kuma bataso tayi kunnen uwar shegu da maganar yagana,abinda ke sake taka mata burki kenan.
Tana nan zaune a wajen tana ta so ta tashi,amma wani film da ake haskawa ya tsaidata,ta dauke idanunta daga kan tv zuwa bakin qofar falota sanda taji hayaniya,ana kuma qoqarin shigowa falon.
Fahima ce kan gaba dauke da trolley,tanata faman zuba hira da mutanen dake bayanta,don har waiwayawa take,sai fairuza daga bayan nata,da kuma wata baquwar fuska na wata fara qal din matashiya.
Dukkansu sun hada ido da ita,amma sai kowa yayi kamar bai ganta ba,suna takowa zuwa cikin falon tare da ci gaba da hirarsu,wanda rabinta cikin harshen turanci sukeyinta.
Dab da zasu giftata matashiyar cikinsu wadda itace baquwar fuska a cikinsu a wajen iman ta sake kallon iman din sosai,sannan suka wuce,qofar dakin dataji motsinsu a jiya taga fahima tasa key ta bude sun shiga gaba dayansu.
Ko zama basu gama yi ba ta sake jin motsi,saiga bassam ya shigo,tabi hannuwansa da kallo,yana riqe da wata qaramar jaka mahadin trolley din dasu fairuza suka riqo,daya hannun nashi kuma babbar leda ce,wadda duk da baka iya ganin abinda yake ciki xaka fahimci takeaway ne,walau na abinci ko na kayan maqulashe.
Duk da dakewar da yayi amma yanayinsa yadan sauya,kamar bai danji dadin ganinta a wajen a zaune ba,kafin ya qaraso ma saita miqe abinta tana daukar hijabinta dake aje gefe ta wuce dakinta tabar musu falon.
Aqalla awa wajen uku tana ci gaba da jin hirarrakinsu da darunsu daga can dakin,tun tana jurewa har suka fara cikata,saita qarasa bakin qofarta ta rufeta ta murza key,abinda yasa gaba daya ta daina jiyo motsinsu.
Duk yadda taso kauda tunani da mamakin abinda ke faruwa cikin gidan amma hakan yaqi yiwuwa,ta gaza fahimtar komai,idan banda jahilci ta yaya za'a sauki baqo cikin gidanta amma a gaza gaya mata?,wanne irin tsarine wannan.
Ranar gaba daya a dakinta ta qarar da wuninta,har zuwa dare,ta gama karatunta da sallolinta ta kashe fitila ta kwanta,bayan ta saita alarm saboda tanaso gobe ta tashi da dan wuri zata asibiti ganin dr ahmad.
********Karfe goma na safiya ta gama shirinta tsaf cikin abaya,wanda mafi yawa tafi sanyata idan zata fita,duk da yada ta sauya,duk kuma da yanayi na rashin kwanciyar hankalin da take ciki amma hakan bai hanata yin kyau ba,kamar wata balariya haka ta fito,ta murza key din da tun yammacin jiya ta sanyashi bata bude ba sai yanzu.
Tana isowa falon qamshi ya daki hancinta,koda ba'a gaya mata ba tasan cewa daga cikin kitchen dinta qamshin yake fitowa,idanunta suka sauka a qofar dakin,qofar a bude take,saidai ba gaba daya ba,an dan sayata ne,labule kuma ya qara rufe sauran gurbin da qofar bata rufe ba.
Tana iya jiyo sound na murya na tashi daga cikin dakin,sai ta dinga jiyo kamar muryar bassam,amma zuciyarta taqi aminta da hakan,saboa bataga abinda zai kaishi dakin ba ida ana magana na abinda ya kamata,tayi qoqarin dannen zuciyarta,ta qara takawa zuwa gaba tana duba gurbin data ajjiye milkshake dinta jiya tana fatan Allah yasa bai lalace ba,sabida shi kadai ya rage mata a gidan.
Balle murfin tayi takai bakinta,dai dai lakacin da qofar dakin ra motsa,labulen ya daga,tana shirin dauke idanunta bassam na fitowa daga dakin,bai kuma lura da ita ba yayi gaba zuwa kitchen,saiga yarinyar jiya na biye dashi,sanye da kayan bacci masu sulbi,wadanda suka bi jikinta suka kwanta,sumar kanta kuma a bayyane saboda rashin saka dankwali.
Saura kadan ta qware Allah ya taimaketa ta dawo dashi zuwa bakinta,sai ta dire kwalin kanta yana sarawa,ta daure a hankali ta juya tana laluben hanya ta fita daga parlor din.
Sai data kusa minti talatin zaune cikin motarta tana qoqarin daidaita kanta,kuka take sonyi amma kuma ya kasa zuwa,sai zafi da zuciyarta keyi,cikin zafin nama ta kunna motar ta kuma tasheta ta figeta da gudu.
A minti talatin take zuwa asibitin dr ahmad,amma a yay minti ashirin ne ya kaita,tana zuwa mutum biyune a gabanta,saita zauna kawai tana bin kowa da idanu har zuwa sanda akayi kiran sunanta.
Kallo daya dr ahmad din yayi mata ya tabbatar bata rabu da matsala ba
"Lafiya kike kuwa hajjaju?" Kamar jira take dama ya tambayeta,sai kawai ta fashe masa da kuka,ta gaza riqe wajjaj damuwar,abun yana neman fin kwanyarta.
"Subhanallah......subhanallah" ya dinga maimaitawa cikin nutsuwarsa,idanunsa na kan yatsun hannayensa yana dubansu,saboda babu tayadda zai kalli fuskar matar wani,duk da taja mayafin abayarta ta lullube fiye da rabin fuskarta.
Sai daya tabbatar ta rage dafin dake cikin zuciyarta,sai ya miqe ya qaro gudun acn dake office din,sannan ya isa bakin fridge dinsa,ya debo ruwa da lemo da cups,ya dawo bakin table din,ya zuba kowanne a cup ya ajjiye mata a gabanta,sannan ya koma kujerarsa ya zauna yana cewa
"Bismillah,dauki kisha" tabbas tana da buqatar ruwa saboda yadda maqogoronta ya bushe tas,duk da cewa bataci komai ba,amma sai ta dauki ruwan ta kurba,har sai data ji bushewar maqogaron nata ya ragu sannan ta ajjiye.
"Nasha gaya miki,indai kinason lafiyar zuciyarki ki guji abinda zai bata miki rai"
"Bani nake batawa kaina rai ba dr" a wannan karon kasa boye masa komai tayi,ta bashi labarinta gaba daya,tana ji a ranta kamar ya al'ameen dinta ne a gabanta take gaya masa matsalolinta.
Da farko fada ya sakeyi mata akan kuskuren data tafka tun farko kamar yadda duk wanda yaji yake mata
"Iyaye ba wasa bane,saba musu da bujire musu shine kuskure mafi muni da dan adam zaiyi a rayuwarsa,kome zaki gani yanzu cikin rayuwarki sakamakin bata musu ran da kikayi ne,amm alhmdlh,tunda sun fara saukowa ki sanya ran samun raguwar jarrabobinki.......inda ace ni isasheshene da zai iya yanke hukunci kan al'amuranki,da na haramta aurenki da mijinki saboda bayyanar fasiqancinsa,amma bani da wannan hurumin,shawara daya ce zan baki,ki tsananta addu'a babu ji babu gani akan ubangiji yayi miki mafita mafi alkhairi,amma damuwa bata warware damuwa saidai ta qara maka damuwa,ta kuma gadar maka da cututtukan da zasu iya naqasa rayuwarki" kalamai masu kyau da ma'ana ta samu daga bakin dr ahmad,wanda hakan ya sanya ta qara ganin kima da mutuncinsa a idanunta,yayi checking nata sosai,ya sake dorata akan magunguna sa shawarwari,kafin tabaro asibitin ta samu relief sosai,sai kawai ta wuce gidansu,ko banza idan taga inna zata sake samun wani sassaucin.
Bata koma gidan ba sai dab da isha'i,tana shiga suna cin karo dasu,suna zaune dashe dashe a parlor dinta,yarinyar da har yau batasan sunanta ba,cikin dressing din da bai kamata wani wanda yake ba muharraminta ba ya ganta da irin wannan shigar ba,babu kowa a sahen daga shi sai ita suna kallo.
Sam ba tabarmar kunyar da bassam din ke nadewa ne ke damunta ba,ko kuma yadda tazo ta samesun ba,don a yanzun ta sanya bassam din a ajin BABU,dashi da babu duka daya haka ta saka a ranta,ita din kamar mai zaman jiran wa'adinta ne........yadda mom ta bada dama aka kebance da danta na cikinta,aka basu dama suka kadaice,bata ko kishin tarbiyyarsa,ama ture ta tata da suka raina,suke ganin bata kai komai ba......wanda tana da yaqini da kuma tabbacin babu matar auren da zata lamunci ayi mata haka,saidai ita din bassam ba shin a gabanta ba,shi da babu duk daya take kallonsu,don haka ko kallon tsiya basu samu ba bare na arziqi,ta sanya kai tayi ciki abunta,yayin da bassam.ya dage yana aika mata da miyagun maganganu cike da fada da rashin daraja.
"Calm down baby..,..karka bari ta bata mana jin dadinmu mana" yarinyar wadda ake kira da seema ta fada,saidai zuciya nata tunzurashi akan kada ya qyale iman din,sai ya miqe
"Ina zuwa baby" yabi bayan iman din cikin fushi da jin cewa iman din ta wulaqantashi.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 35
Towel ta daura ta kuma zura hijab,tana shirin shiga wanka bassam din ya shigo,saidai kuma suna hada idanu kaifin abinda ya shigo dashi din ya ragu
"Ke.......kina jina ina miki magana saboda kin rainani kika shigo kika barni?wato ga banza shasha mahaukaci ko?" Maimakon ta tanka masan kamar yadda yakeso dinndai ,sai ta sake bawa banza ajiyarsa,ta qarasa ta dauki man wanke gashi ta sakeyin gaba.
Sake fusata yayi sosai,ya daka mata tsawa yana cewa
"Na yarda da gaske kin rainani kamar yadda mom tace,saboda kinga kin dan fara riqe kudade,kina cin mai kyau kisha me.kyau ki kwana a ac"
"Kul!" Ta fada itama cikin daga murya,abun sai ya bashi mamaki,ya buda idanunsa yana kallonta,itama sosai ta bude nata idanun cikin nashi
"Karka kuskura ku zarme cikin maganganunka,shurun da nakeyi bawai yana gwada bansan ciwon kaina ko bani da wayo ba,ina sane da komai,hakanan a shirye nake da faruwar kowanne abu,ina cin me kyau?,ina abun yake?,ina qudan yake ballantana romonsa?,na tabbatar sanda ka daukoni daga gidanmu ba haka nake ba,hakanan ba dusa muke ci ba,maganar kwana a ac kuma kai kanka kasan ka fada ne don kaji dadin bakinka,ac ba shine arziqi ko kuma kyau ba,inda shine......ni hajar bazanyi kyan da ka gani a tattare dani ka nace sai da ka auroni ba......ka rabani da kowa nawa,kazo kana gasani kuna nunamin baqin halayen da babu arziqi ko dattako ko kadan a cikinsa,na rantse da Allah daga yau duk wanda ya sake takani saina takashi ko wayeshi,ka gayawa sauran" tasowa yayi kamar xai daketa,wani jarumta tazo mata,ta dauki fitilar gefa gado ta daga sama
"Duk randa ka sake ka kwatanta dukana,koda da wasa ne,wallahi wannan abar bata da muhallin da zata fashe ta kuma tarwatse illa kanka" sake birkicewa yayi da maganganun tabarmar kunya,ta bawa banza ajiyarsa ta shige bandaki ta murza key.
Famfo ta kunna saboda batason yaji sautin kukanta,ta dinga kuka sosai tana kiran sunan Allah,daga nan tana jiyo yadda yake bin duka lockers dinta yana kwashe kudaden da suke ciki yana fadin
"Zanyi maganinki,zakisan cewa bani da kyau,saboda kinga na sangartaki shi yasa kike dukka iskancin da kikaga dama".
Cikin ikon Allah kafin ta baro bandakin zuciyarta tayi sanyi,data fito din saita kulle dakinta,ta shirya ta jawo takeaway din data shigo dashi ta fara ciba wani da yawa taci ba ta ture saboda yaddaa taste din bakinta ya dauke gaba daya,ta ballo maganinta tasha ta kashe fitila ta haura gado ta kwanta,don ta hana kanta tunani saita janyo wayarta,cikin karatuttukan malamai da take download ta ajjiye ta buda daya ta fara sauraro,a hankali ta sake samun nutsuwa,ta tattara dukka hankalinta akan karatun tana fahimtar kowanne lafazi dake fita daga bakin malamin.
Wata irin rayuwa ake gudanarwa cikin gidan musamman sassan iman din,kamar wasu maguzawa ko kuma wadanda basusan addininsu ba,seema diyace ga tsohon ambassador din nigeria a England,kuma 'yar qawace ta kurkusa a wajen mom,cikin manyan qawayenta makusantanta,an dauko cancankat an kawota gidan da sunan su saba da bassam kafin maganar aurensu,an kawota sashen iman din ba tare da neman yarda ko amincewarta ba,basa yiwa iman din kallon komai face qasqantacciya wadda bata da wani daraja ko kima saboda bata fito daga gidan nau'in mutane da suke da abun duniya ba wato kudi.
Dukkan abinda suka ga dama yi suke a sassan nata,idan ka shigo zaka tsammaci seema ce matar gidan,saboda gaba daga iman din ta tattara tabar musu gidan,tayi qaura zuwa dakinta tana aiwatar da al'amurata,idan kaga ta fito tofa saidai idan wani dalili me qarfi ne ya fiddota,tana gamawa kuma zata koma,bama kasafai zaka ganta din ba,tunda babu kayan abinci bare tace xatayi girki,kayansu lemuka da madara kawai data tara a dakinta sune abincinta,wanda suma suna kan hanyar qarewa.
Hausawa sukace ba'a bawa kura ajiyar nama,a nan kuwa na bawa bassam,gaba daya bassam ya ja iman ya ajjiye gefe,ko cigiyarta baya yi bare nemanta,domin kuwa ya samu dukkan abunda yake buqata daga wajen seema,tsula tsiyarsa yake,ya samu lasisin fiye da yadda yayi tunani,don zuwa lokacin ya samu makarin lalurarshi ba tare daya bari jessica ta sani ba,babu abinda ya banbanta seema da matarsa,dukkansu basu da wata damuwa ko tunanin ranar nadama.
*_KOMAI NISAN DARE gari zai waye_*
Tunda gari ya waye yau sashen nata shuru yake,babu motsin bassam bare na seema,ko ba'a gaya mata ba kuma tasan sun fita ne tare,don wannan din ba wani baqon lamari bane tattare dasu,hakan ya bata damar fitowa parlor ta dan zauna,saboda ta rage muguwar kewa da zaman kadaicin dake damunta,zuwa yanzu ta fara qosawa,ta kuma fara gajiya da abinda idanuwanta suke gani,sau tari zuciyata tana gaya mata ta gudu,ko tayi yaji,saidai dukka haqurin da take tana yine saboda ta kafa hujja ya kuma zame mata hujja,ba'a wajen yagana kadai da kullum take sake tausarta ba,a'ah.....har sauran al'umma da duk mutumin da zai qalubalanceta a duk sanda ubangiji yaga damar zartar da hukuncinsa akan zamanta.
"Salama alaikummm" sautin muryar dake dauke da gurbatacciyar hausa ya samu mazauni a kunnuwan iman,cikin mamaki ta daga kai don jin daga inda sallamar ta fito.
Zabgegiyar macace sanye da mini skirt wanda inda zatayi kyakkyawan tsuguno ba abinda zai hana bayyanar tsiraicinta,sai armless chiffon shirt v neck shape daya bayyana kusan rabin qirjinta,kanta yasha lodin attach,yayin da hannunta yasa fixing na faratan kanti,takalmin qafarta me igiya ne,mai azabar tsinin dunduniya kamar wadda ta shirya tsokane idon duniya,tafkeken sun glasses din daya kusa cinye rabin fuskarta na riqe a hannunta tana kallon iman,kamar yadda iman ke kallonta,tana son tuna a inda ta taba ganin fuskarta,da kuma abinda ya kawo wannan halittar cikin gidan
"Zan iya shigowa?" Ta tambayi iman tana ci gaba da kallonta,bata da zabin daya wuce ce mata
"Bismillah" tana nuna mata wajen zama,saita qaraso cikin taku kamar zata karye saboda tsinin takalminta,ta zauna saman kujerar tana ajjiye jakarta gefe,har yanzu kuma idanunta yana kan fuskar iman,wanda har kallon ya soma sanyata ta tsargu.
Kaf sashen nata bata da wani ruwa bare lemo na roba da zata iya bata,don haka ta gyara zamanta tana duban matar
"Kene matar bassam ko?" Ta tambayeta tana dage girarta
"Eh nice"
"Woww......a fili kafi kyau akan hoton daya nunamin" turus iman din tayi,kada dai ace kwashe kwashen bassam ne har yakai suka fara biyoshi har cikin gida,lallai zai kai gabar da kuma ba zata iya ci gaba da zuba masa ido ba"
"Am jessica.....oh....sorry ....ya taba gayamin baki karatu ba,ko secondary school baki kammala ba ko,bari nayi magana da ausanku" sosai maganar ta daurewa iman kai,saidai kafin ta gama wannan tunanin ta sake jefata a wani
"Da fariko......nazo wajenki ne da kyakyawan zuciya,zuciyana babu haushi a kanki,abinda yasa nayi shawaran zuwa na fitar dake daga duhu shine,na farko ke yarinya ne,bakasan komai akan duniya ba,na biyu kuma baka taba tsokanana rigima ko wani abu ba mara dadi tsakanina dakai......ba kamar matan bassam na baya ba"
"Mata kuma?" Iman din fa fada a bayyane cikin mamakin daya fito fili ya bayyana qarara saman fuskarta.
Kai Jessica ta kada tana dan qaramin murmushi
"Yes,wives na bassam ba,nasan baki sani ba......but keep calm,zan miki bayanin komai .......idan zaki iya tunawa watanni da suka wuce an taba toro miki da pics na mijinki shi da wata,to nice wannan din" zumbur iman ta miqe cikin bacin rai
"Tashi ki fitarmin a gida annamimiya arniyar banza,me kikazo kuma yimin?,saboda kinga wancan lokacin na qyaleki ban kulaki ba,shine kikayo tattaki har cikin gida?" Hankali kwance Jessica ta dubeta
"Karki tashi hankalinki mana,koda na tashi na tafi,tafiyana babu abinda zai canza,saima wargaza miki naki rayuwan,ki tsaya ki saurareni,daga qarshe koma meye saika fada" wani sashe na zuciyarta taji yana umartarta ta bata dama,saita koma ta zauna tana huci,saidai ba cikin kujerar ba,a hannun kujera ta zauna wannan karon,da shirin kota kwana,ko zata kawo mata rainin hankali,idan seema ta samu daurin gindin mom tana abinda taga dama.....ita kuma jessica fa?,na meye zata sakewa sauran?.
"Kamar yadda na gaya miki sunana,ni din ba 'yar garin nan bace,abinda ya kawo nan din karatu ne,shekarata goma tare da bassam muna soyayya dashi,asalin fara soyayyarmu kuwa ya nuna min zai aureni ne,nayi masa tuni da bambancin addininmu yace babu matsala,shi wannan ba matsala bane a gidansu,tun a sannan mahaifinsa yana da rai,ashe bassam ya fada ne kawai saboda ya samu kaina ya lalatani,ni kuma a sannan ban sani ba,na bashi amanar kaina da rayuwata sai yadda yayi dani,na sani tu a lokacin bassam yana da farinjinin 'yammata,wanda yawancinsu kudi da kyau da yake dashi yake rudarsu,to ban damu ba sosai saboda ban zaci yana nemansu bane kamar yadda yake nema na,sai daga bisani na gane hakan,mukayita tashin hankali dashi,daga baya na haqura na qyaleshi saboda na fuskanci a jininsa ne,bazai daina kulasu ba,naci gaba da biye masa tare da nace masa kan maganar aure na,amma har muka dibi shekaru biyar bassam yaqi yarda da maganata,a haka muka shiga shekara ta shida,a sannan ne na samu ciki,wadda na tabbatar da cewa bassam ne yayimin shi,tunda a sannan babu wanda nake kulawa saishi,qememe yace a zubar dashi ko na rabu dashi,ni kuwa naqi,saboda a tamu al'adar mu ba abun ku ya bane don kina tare da saurayinki kinyi ciki kin haihu,kina iya tara yara hudu biyar har fiye da haka da saurayi,sai daga bisani idan kuna tare a daura muku aure da yaranku.
Barazanar daya shiga yimin yasa na tattare na koma qauyenmu,ya daina jin duriyata da labarina gaba daya,acan nayi rainon cikina na haifi yarinya mace,sai data isa yaye shekara daya da rabi na dawo rayuwar bassam,nayi gyara na musamman saboda nasan lagonsa,ina dawowa kuwa ko takan cikina baibi ba aka dora da sabgogi,abinda bai sani ba lamfo nake masa ina bibiyar duka rayuwarsa,saidai ashe nima lamfo yayimin,sanda na dawo masa da maganar aurenmu yace shi Allah ya tsareshi,me zaiyi da ragowar wasu,maganar ga batan rai,tunda ko ragowar wasunne ni ai shine ya fara nunan hanya,a sannan munyi bacin rai dashi irin wanda bamu taba yi ba,na tattare komai nawa muka rabu,amma a raina akwai shirin daukan fansa,saboda haka na fara binciken abubuwan da suka shafeshi da yake boyewa,wanda idan suka bayyana zasuyi destroying dinsa.
Cikin abinda na gano kuwa harda aure da yayi na mata uku,daya ya saketa,biyu yana zaune dasu ba tare da kowacce tasan da 'yaruwarta ba,sannan mamanshi ma batasan da auren ba,saboda auren sirri yayi abunsa na watanni,idan ya gama morar yarinya saiya rabu da ita ya koreta.
A sannan daya daga cikinsu nada ciki,kishi yasa na dawo rayuwar bassam,na fara nunawa matansa cewa akwai wata fa tare dashi,sai muka shiga gwabzawa dasu,inda daga qarshe basu cimma nasara ba,lokacin daya diba na sakinsu yayi ya rabu dasu.
Unfortunately ba'a dauki dogon lokaci da rabuwarsu ba na tsinci labarin xaiyi aure,dana tareshi da zancan kansa tsaye yacemin eh aure zaiyi,abun ya girgizani ya kuma bani mamaki,na dinga son insan wacece wannan data sauya ma bassam ra'ayi lokaci daya,ya kuma aminta zai aureta?,saidai ban samu wannan damar ba,saboda gida dana koma can garinmu,'yarmu da bassam baisan da ita ba bata da lpy,inacan kuma ban dawo ba har ya rage saura kwana uku daurin aure,wannan shi ya wargazamin duka plan dina,amma dana bawa sister na labari,saita kawo shawarar na kassara mazantakansa,tunda dai shine taqamar kowanne namiji,ta yadda babu wata mace da zai iya tsinanawa komai indai bani ba,a wajena ne kawai zai iya kasancewa namiji,wannan itace hanya guda daya da zata mallakamin shi,tasa ya dawo tafin hannuna"
"Sosai shawarar ta yimin,ta kuma faranta min rai,ana ya gobe daurin aure na tura masa Tex,na tayashi murna,nayi masa kuma albishir din abinda ke shirin samunsa,ya kirani ya zazzageni,yace shi zan yiwa barazana,ni kuma nace masa maji ma gani.
Bayan yaje ya tabbatar da abinda na gaya masa,wannan shine abunda yayi sikar dawowarsa wajena,muma sake zama kamar miji da mata ni dashi,yaso kasancewa tare dake qwarai da gaske,saboda yadda zuciyarsa ta cika da sha'awarki tun sanda ya fara ganinki,don ko lokuttan da yake tare dani ke yake ambata......yaso yayi mu'amala dake da farko kamar yadda yakewa kowacce mace,bansan me ya gamo ya kasa aiwatar da wannan ba,ya juya manufar zuwa ta aure a kanki,amma daya daga cikin dalilan da na sani shine......ya aureki ne don ya bunne barnar da yake aikatawa,saboda kedin kina da qananun shekaru akanmu,ba zaki takurashi ko hanashi yayi yadda yakeso ba.
At last saqon da nazo dashi gareki na ceton rai ne,saboda ni na riga na fada,no way out......bassam ya fara harka da wata yarinya serah,yarinyar da nake da dukkan tabbaci da yaqinin tana da cutar HIV,ban kuma ankare da hakan ba saida suka fafa nisa a mu'amala,zuwa sannan kuma me afkuwa ta afku......anan ne kuma na fahimci cewa ya warke ya samu makarin sihirin da nayi masa,idan kinsan har yau bai nemeki ba......to ki kubutar da kanki.....ki tseratar da quruciyarki,idan kuma an riga an gamu......sai nace miki ina miki jaje,ni ban damu ba da kaina,saboda ko babu komai na hada iri dashi......." Saita miqe tana maida glass dinta
"Dukka cikin kalamaina babu qarya ko daya,idan akwai ubangiji ya hukuntani,na fada miki ne sabida nayi ceto ga innocent soul,na barki lafiya".
Zata iya cewa inuwar jessica itace abu na qarshe data iya gani,sai bude idanunta tayi taga daya daga cikin ma'aikatan gidan mata a gefanta[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 36
Sai data sake bude idanunta sosai taji tana yi mata sannu sannan ta fahimci suma tayi a wajen,a hankali qwaqwalwarta ta fara tariyo mata abunda ya faru zuwan Jessica da kuma abubuwan data shaida mata,kuka sosai ta fashe dashi,sannan ta miqe da sauri ba tare data kalli matar dake gefan nata ba,tsanar gidan da tsanar duk wani abu da kuma duk wani mutum dake gidan tana darsuwa a ranta,bassam?,bassam.......ashe shidin furen kan juji ne?,ashe baqin maciji ne shi mai dauke da mugun dafi?,irin dafin da idan ya tsartu ga gangar jiki yake ɗai ɗaita jiki,ya kuma haifar da mummunar illar da bata warkewa.
Takai ta kawo yafi sau shurin masaki,ta rasa wacce shawara ya kamata ta yanke?,meye abu na qarshe daya kamata tayi?,don dai tabbas indai ya tabbata dukka abinda jessica ta fada haka yake.....babu wani sauran zama tsakaninta da bassam har gaban abada.
Fitowa na ukun da tayi zuwa falon kamar me neman wani abu,yayi dai dai da shigowar bassam da seema,saidai wata irin shigowa sukayi,tana gaba fuuuu yana binta a baya
"Haba mana seema....tun a hanya nake fama dake ki tsaya ki saurareni.......na rantse miki babu wani abu da yake tsakanina da ita fa?" Ko juyowa ta kalleshi seema batayi ba ta shige dakinta,kana ta fito ta sake wuceshi,ya soma takawa zai bita yana kiran sunanta,saidai tuni ta fice abinta.
"Damnit" ya fada yana yarfar da hannuwansa,da alama abun baiyi masa dadi ba,wasu hawaye masu dumi suka saukowa iman tana kallon fuskarsa ba tare da ya sani ba,babu abinda take hangowa sai lokacin da ya yaudareta,ya kawota duniyarsa bisa kyakkyawan zaton zata samu dukkan wata kulawa data dace da diya mace,ta miqa masa dukkan yardarta,ta zama butulu kufan wuta ga ya ameen dinta,mutumin da ya sota fiye da kowa a duniya
"Ke kuma meye kika wani tsaya kina kallon mutane kamar baki sansu ba" cikin muryar kuka ta fara magana
"Ina kallon mayaudariya kuma maha'inciyar fuska,azzaluma wadda bata damu da gobenta ba bare na wani,fuskar da take iya fuskantar kowanne zunubi,take iya mu'amala harda kafirai maqiya Allah da ma'aiki irinsu Jessica" sosai taha reaction na fuskarsa ya sauya sanda ta ambaci sunan Jessica din
"Ke!,banason hauka da rashin hankali fa?,kisan me bakinki yake fada,to sai meye?,sai mene?,babu abinda zan nema ban samu ba cikin rayuwata,sai na kasa jin dadin rayuwata?,sana ragi kaina?,bazai yiwuwu ba,kinga....ni ba kalar mazan da suke daukan raini daga matayensu bane"
"Raini shine abu mafi sauqi da zaka samu daga gareni idan na yarda na zauna dakai......"
"Ba sai....." Maganarsa ta tsaya sanda yajiyo muryar mom tana qwala masa kira,hankalinsa ya tashi,saboda ya tabbatar seema qararshi takai wajen mom,ba'a cika sakanni ba mom din ta bayyana cikin parlor din,kamar kullum cikin takun qasaita take takowa cikin falon,taku dai dai kamar qasa ba zata iya daukarta ba,saboda jin izza da kuma isa
"Me ka yiwa seema?" Tambayar da tayi masa kenan tana cika tana batsewa,gami da jefa harara ta musamman ga iman,wadda take tsammanin kamar tana da hannu kan bacin ran seeman data hada kayanta tana iqirarin tafiya
"Bab....ba komai fa mom....kawai......"
"Bassam" iman ta kirashi a kaurare,saboda a yanzun idanunta basa ganin kowa,bacin ranta kuma yana ninka na baya ne
"Wuce muje sassa na daga kai har seeman" mom ta fada tana tsareshi da idanu,da hanzari iman tasha gabansa ganin yana yunqurin fita
"Dakata malam.....yau zamana dakai ya qare a gidan nan,bazan iya zama da fasiqin namiji ba"
"And so what?.....ga hanya nan ki tafi,ke kika rasa bani ba,don na taimakeki,na miki gata,na kawoki rayuwar wadata shine zaki dinga fiffiqemin kina min wannan fitsarar" ya fada a tsawace.
Baya tayi tana girgiza kanta,zuciyarta kamar zata fado,sai kuma ta juya da gudu tayi dakinta,duk da gunjin kukan da take amma tana jiyo muryar mom tana cewa
"Ko bata fada ba zamanku ya qare,a gabana saboda ita din ba 'yar gidan mutunci bace?,dama ni na gaji da wannan auren,gwara ayi komai a gama tsakaninka da seema,nima sai hankalina yafi kwanciya"
Ma'ajiyar jakankunanta ta nufa ta fara hargitsosu tana dubawa ko zata dace da wadda keda kudi a ciki,saboda ta tabbatar a yau din ta tashi bata da komai.
Saidai har ta gama bincikenta bata samu kudin da takejin zasu kaita inda take lissafa zata je din ba,abu daya ta sani,koda a qafa ne.....koda me zaya faru ba zata sake kwana cikin wannan gidan ba,gidan da dashi da maqabarta a wajenta bashi da maraba.
Hijabin da take sala ta janyo ta zura,sannan ta sanya slipper din da take yawo dashi tsakanin bedroom dinta zuwa parlour,taku daya biyu sai ta tsaya cak,ta kuma sauke ajiyar zuciya,ta dawo da baya da hanzari ta buda wata locker ta sanya hannu,saiga atm ta fito dashi,tsahon xamanta a gidan ta manta dashi,saboda koda yaushe akwai kudi available kuma cash,qaramar purse da batayi niyyar dauka ba ada ta koma ta dauka,ta jefa atm din da wayarta a ciki,cikin wani irin hanzari da kuma sauri kamar wadda za'a kama ko ace dawo ta qara gaba.
Karo na farko a rayuwarta data doshi tasha da sunan tafiya wani gari,kai tsaye ta nema motar dake lodi zuwa maiduguri,bayan ta tsaya a wani atm machine ta cira kudaden da tasan zasu iya kaita duk inda ta nufa,tun cikin napep akan hanya tasan cewa bata da wani qwarin gwiwa da zata doshi inna malam ko uwa uba yaya sadiqu da wata matsala data shafi aurenta,matuqar ba dan saukowar da sukayi bane takeso ta rushe wannan sassaucin a tsakaninsu,a yanzu bata da kowa.....bata da wanda zata dosa idan ba yagana ba,ita kadai ce madafarta,ita daya ce takejin zata tallafi wannan raunin nata.
Tafiya mai cike da wahala da quncin zuciya tayi,don tunda suka tashi daga kano har suka isa maiduguri......tsahon awannin batakai koda ruwa bakinta ba,a hakan a lexirouse taje......saidai yadda takeji kanta dama jikinta kamar wadda ta tafi a kori kura ko kuma 'yar qurqura,wahala tako ina,don ko bayan sun sauka da qyar ta samu me abun hawan daya amince zai kaita unguwarau yagana sabida dare da yayi,uwa uba shi daya ne ya gane kwatancen da taketa yi masa da qyar,ya tsula mata kudi kuwa sosai,amma bata damu ba,don ba wannan bace matsalarta,burinta shine ta ganta gata ga ya gana,ta kuma karba mata 'yancinta,ta rabata da auren bassam a kanta.
Tsoro ne ya kama yagana sanda taga iman din,daga bisani mamakin ya maye gurbin tsoron
"Hajaru.....daga ina haka a wannan daren?" Maimakon ta bata amsa saita fashe da wani irin kuka,tamkar rarraunan marayan daya rasa uwa da uba duka a lokaci guda.
"Subhanallahi,hajar wani ne ya rasu acan kanon?" Kai ta girgiza mata alamun a'ah saboda ganin yadda hankalinta yayi mugun tashi
"Ki lallabata a hankali" alhj bukari mijin yagana ya fada bayan ya gama tausar iman din,ya fice ya basu waje.
Sai data rama sallolin dake kanta,ya gana ta gabatar mata da abinci duk da cewa dare yayi,amma sai ta kasa ci,abinda yasa ta hada mata abu me ruwa ruwa da kuma zaqi wanda take ganin zata iya sha.
Ba wani da yawa tasha ba ta ture,bata matsanta mata ba ta dauka ya rufe,sannan cikin kwantar da hankali ya gana ta sake tambayarta.
Kamar wancan karon.....babu abinda iman din ta rufewa yagana,cikin matuqar tashin hankali take tafa hannaye tare da dauko dogon salati
"Allah mun gode maka daya kare mana ke,Allah abun godiya,wato shi yasan manufarsa da tun farko yaaa farkarsa tayi masa sihirin da ya zama hoto,da tuni yanzu wani zancan ake akanki kenan iman ba wannan ba?" Yagana ta fadi tana dafe kanta cike da zallar kaduwa da kuma tsoro.
Kai iman din ta jinjina hawayen mai radadi da zafi suna sake sauka akan kuncinta
"Ki kwanta kiyi bacci,kada ki sanya wata damuwa cikin ranki,aure kamar an rabashi an gama,ai zama ya kuma qare,babu wani zancan gyara ko sasanci,da wannan cutar?,mu godewa Allah daya tsayar ma iya nan,yanzu zanje mu tattauna da alhaji,don musan ya za'a bullowa abun,dole khalilu ya sani shima,tunda abune daya shafi jininka" sai data tabbatar iman ta kwanta sannan ta yunqura ta miqe ta fice zuwa dakin mai gidanka.
Idan tace tayi cikakken barci a daren tayi qarya,juyi kawai ta dunga yi tana tariyo rayuwarta,tun daga sanda ta fara mallakar hankalinta har zuwa yanzu,abubuwan da suka dinga faruwa,musamman lokacin aurenta da bassam,da yawa gangancinta ne ya janyosu,ta runtse idanunta tana jin wani ciwo a qirjinta tana hango kanta tsaye gaban ga ameen tana zazzaga masa rashin kunya dukka akan bassam,ta fashe da kuka mara sauti bayan tayi qoqarin rufe bakinta,tana jin wani irin kaico da muguwar nadama suna shigarta,jikinta ya dinga kakkarwa,kadan ya rage hawan jininta ya dawo da mugun qarfi,cikin taimakon Allah ta dinga ambatar sunan Allahn,yakawo mata dauki komai ya daidaita,gab da asuba wani wahalallen bacci mai mafarkai barkatai marasa dadi yayi awon gaba da ita.
Lokacin data farka don yin sallar Asubar kanta yayi wani mugun nauyi,ta lallaba cikin toilet din dake dakin ta daura alwala tazo ta bada farali,ta dan jima saman abun sallar tana addu'o'i na tuba neman rahama gafara da yafiya da kuma sauqi a dukkanin rayuwar da zata risketa a nan gaba.
Sai data tabbatar ta gaji da zaman sannan ta janyo wayarta don duba lokaci,sai idanunta suka fada kan envelope dake fuskar wayarta,wadda ta fado da sunan bassam,tasa hannunta ta bude wayar sannan ta bude envelope din ta fara duba saqon
*_Ni Bassam balarabe madaki,na saki matata iman saki daya_*
Sau biyu gabanta ya fadi lokaci guda bayab ta gama karanta gajeran saqon,ta duba da kyau tabbas number bassam dince,saita lumshe idanunta tana sakin wani numfashi me nauyi daga qirjinta,wanda bayan fitar numfashin......sai taji kamar ya fita ne tare da dukkan wani nauyi daya jima a qirjinta,nauyin da taji ya saukar mata tun ranar da aka daura mata aure,watanni tara baya kenan cikin na goma,bata ji kuma ya sauka ba sai a yau din,maimakon taji dimuwa ko kuma damuwa,a'ah ,sai ta jita sakayau,a nan taja pillow ta maida kanta ta kwanta,tana lumshe kyawawan blue eyes dinta,cikin zuciyarta da kuma labbanta dake motsawa tana fadin
"Alhamdulillah....alhamdulillah,Allahumma salli ala sayyidina muhammadin wasallim" tun tana fada da qarfinta har wani irin bacci ya rinjayi qwayoyin idanuwanta suka rufe ruf,ta lula duniyar bacci.
"iman.....iman" taji ana kiran sunanta sama sama,saita buda idanunta,suka sauka kan yagana dake tsaye gefanta,qarasa bude idanun nata tayi ta miqe ta zauna tana ambaton sunan Allah,sai a sannan yaagana ta samu waje ta zauna tana dubanta
"Inata tararrabin baki samu barci ba,yanzu kuma na koma tararrabin baccin lafiya kuwa kikeyi?,tun daxu ko motsawa bakiyi?,kayan abincinki tunda duminsu har sun huce" gefanta taga jeran kwanukan abincin,mamaki ita kamta ya kamata,saboda bata da wani nauyin bacci,amma kuma ace har an shiga an fita sau nawa bata ji ba
"Alhaji ne zai fita,ni kuma banason ya fita ba'a tsaida matsaya ba" ba kasafai iman din ke magana ba idan ta farka daga barci batayi brush ba,saboda haka ta cewa yaagana tana xuwa,ta shiga bandaki,ta wanko bakinta sannan ta dawo
"Ya sauqaqewa kowa wahala yaagana,da asuba ya aiko da sakin ma ta saqon waya" duk da cewa yaagana taji haushin hakan sabida rashin mutunci ne da rashin kima,a rasa ta yadda zaa saki mace saboda son a wulaqantata saita saqon waya,amma kuma jin dadinta yafi yawa,jin cewa komai yazo qarshe,batayi qasa a guiwa ba ta shaidawa alhaji,saidai ya girgixa kai
"Dole sai an kirashi anji ta bakinsa,saboda haka ina ganin zuwa gobe ko jibi,ku shirya sai mu wuce kanon tare,akwai wasu kayana da sukazo dama,suna kasuwar kantin kwari" da wannan maganar suka tsaida matsaya,ta kuma shaidawa iman din,kai kawai ta kada kana tace
"Allah yasa muna da rai".
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 37 Kwana biyun da tayi gidan yaagana sai taji kamar an canzata ne,duk wani takura da quncin zuciya da takeji babu shi,abu daya ne yake sanyata faduwar gaba zuwa biyu,yaya malam da inna zasu kalli abun?,zasu karbeta kuwa?,idan sun karbetan alaqarsu zata koma kamar yadda take da?,ko kuma ta tabarbare kenan?,wadan nan tambayoyin suke cin ranta,suke kuma takurata lokutta da dama idan ta tunasu Randa suka tasamma kanon sammako sukayi,saboda haka goma na safe acan tayi musu,basu sauka gidan malam ba,sai da suka fara biyawa gidan kawu muntari,gidan alwalin iman din,wanda ta koma gidansa da zama lokacin aurenta da bassam din,sannan suka qarasa gidan malam din.
Kamar wata baquwa haka ta zama,ta kasa sakewa gaba daya,motsi kadan sai ta kalli inna,ita kanta innar tayi mamakin ganinta tare da yaagana da kuma alhaji,saidai bata ce komai ba,ganin harda kawu muntari Basu xauna gidan kawu muntari ba,don haka a gidan inna suka karya aka kuma dora abincin rana,zuwa lokacin mazan suna rumfar malam din,da alama kuma tattaunawa sukeyi,daga bisani ne malam din ya leqo yayi kiransu su dukka suka isa rumfar tasa.Hajaru..inason ki sani cewa duk abinda ya samu bawa muqaddarine daga ubangijinsa,yanzu yanzu muka gama magana da mijinki,mun kirashi kuma ya tabbatar mana da sakin da yayi miki,to amma kuma shi malam mahaifinki ya kafe kai da fata kan bai aminta da abinda kika zo dashi ba.munaso ki bude baki ki gaya mana,tsakaninki da Allah meye ya hadaku dashi?" Kanta a qasa,hawaye ya cika mata idanu,tanajin quna da zafi a ranta,ta gaji da zancan bassam da tarin matsalolinsa,tunda dai har ya sahale mata ya kamata a rufe babinsa hakanan,to amma hakan ba zata yiwu ba,dole saita gaya musu abubuwan da suka wakana. A nutse ta labarta musu komai,ya gana data zame mata kamar shaida itama ta gaya musu duk abinda ta sani,parlour din ya dauki shuru,sai sheshseqar kukan iman din. Gyaran murya malam din yayi
"To yanzu yaaya mu me xamuyi?,muda bamu isa komai ba?,ai saidai muce Allah ya kyauta na gaba,riqon hajar kuma yanzu ai yafi qarfinmu,bamu da muhalli da irin abincin da take ci,saidai ko a cigita cikin dangi ko akwai inda zata iya zama dasu" sosai maganar malam din ta girgiza iman,sautin kukanta ya qaru,hankalinta ya sake tashi fiye da yadda take a da,ta waiwaya tana ruqon inna,sai innar itama taja jikinta gefe tana cewa
Wa?,ni binta,yo zantukan malam dukka akan hanya suke" tausayin iman ya kama alhaji da yagana,ran yagana ya baci sosai,ta kalli iman
Tashi ki shiga ciki" ta miqe tsam tana jin jiri yana dibanta,har sai data bace sannan yaagana ta dawo da kallonta kansu
Duk wannan zantukan da kuke kai da binta zancan banza kuke,wai ku dole saikun nunawa duniya bakwason imani,fushi kuke da ita,zancan banza ne kuke,wallahi wallahi kuka sake na tafi da hajaru maiduguri saikun manta kalarta" alhj mijin yaagana ne ya karba
Malam ni a tunani na kaine zaka yi mana wannan fadan bamu xamuyi maka ba,ka taba ganin inda hannunka ya rube ka yanke kayar?,bayan haka kuma.a yanzu dai inajin babu sauran kalar nadamar da ta rage hajar bata yita ba,babu ita,kuma dama ance ba'a qwace garma a hannun yaro ko?,idan ya gaji yaji wuya da kansa zai cillar da ita,saboda haka,ina mai aron bakinta nima,kuyi haquri ku manta da komai,kalar tata qaddarar da kuma jarrabawarta kenan,Allah yasa kuma ta cinyeta Kiranta yaagana tayi,kowa da kalan nasihan da zaiyi mata,cikin kuka da zubda hawaye ta sake duqawa ta nema gafarar inna da malam,dukka suka amsa da cewa sun yafe mata,saidai malam yace aje ayi mata gwaji a ranar,don a sake tabbatar da lafiyarta,haka kuwa akayi,result ya fita cewa bata tare da wani ciwo banda hawan jinin data samo a can,shima kuma likitan ya bada tabbacin indai zata samu kwanciyar hankali da nutsuwa zata rabu dashi, tension ne ya kawo mata shi. Ya saddiqu kuwa har yanzu jiya iyau,mu'amalarsu sam bata koma kamar ta baya ba,har sai da malam ya kirashi ya masa fada sannan ya sauko,ya rage daure mata fuska. Batasan cewa sabawa umarnin iyaye koda kai keda gaskiya ba indai ba sabon Allah suka umarceka ba babban bala'i bane sai yanzu,ranar da sadiqu yasa motoci a gaba akaje aka kwashe kayanta rankatakaf daga gidan bassam.a ranar tayi wani irin ni'imtaccen bacci,baccin da rabonta da irinsa tun ranar data sanya qafa tabar gidan nasu,bacci harda makara,a ranar data sake tabbatarwa da cewa babu ita babu bassam kenan,sunyi hannun riga har abada. Iya furniture din da taje dasu gidan da kuma motar hawanta data zo cikin sadakinta kadai ya sadiq din ya dauko,banda wannan tsinke nasu bai shigo cikin kayan ba Shawara yayi da ita ya tarkata kayan furniture din aka saida,motar kuma tace a ajjiyeta,don ko son ganinta batayi,don haka sai ya jata ya kaita garage dinsa,don shima yanzun ya bude nasa qaramin garage din gyaran motocin,har ma ya dauki yaran unguwa su hudu suna koyon aiki a wajen,suna kuma taimaka masa
bayan wasu watanni Sanda ta samu nutsuwa abu na farko daya fara zuwa kanta shine karatu,a yanzu bata da burin daya wuce ta dawo da karatunta,ta shaidawa malam,ya aminta da hakan,saboda tun farko yasan burin ameen kenan a kanta, ya sadiqu ma yayi murna sosai da har yanzu karatun bai bar kanta ba,kuma shine ya shige mata gaba,ta samu takardun qualifying da secondary School certificate,sannan ta samu damar zana jamb dukka cikin shekara guda,komai nata ya hadu yadda ya kamata,ya sadiqu ya daye tuquru wajen sama mata makaranta,har ta dinga mamakin yadda ya maida kai,saboda har yanzun 'yar tsama suke,saidai katsam sai gashi makaranta ta samu,muma course din data nema,murna kamar tayi me? Tun ana saura kwana bakwai ta fara zuwa din babu irin fada da hudubar da bataji ba kan qawaye,daga bakin inna ne,daga bakin malam ne uwa uba kuma daga uban gayyar ya sadiqu. Zuwa yanzu itakam aita gurzu,ta kuma gane duniya,ba sai an mata ma magana aka qawaye irinsu munira ba,munirar da suka jima suna gaisawa amma bata taba gaya mata aurenta ya mutu ba,sai ranar data wanki qafa taje gidan da sunan ziyara sannan ta samu labari,daga nan kuwa tayo gida wajen iman din cikin tashin hankali. Saidai kuma yadda ta samu iman din qalau cikin walwala yasa jikinta ya danyi sanyi,ganin munira a gidan sam bai yiwa iman dadi ba,don ita yanzu bata qaunar dukkan wani abu da yake da alaqa da bassam,ko kuma zai tuna mata dashi,a yanzu rayuwarta dadi take mata,tana jin kamar an tariyo mata da rayuwarta ne,saidai akwai abu daya da tasan ta rasashi,akwai abu daya da takeji cikin zuciyarta cewa tayi missing,tana jin akwai wani babban bangare abu mai muhimmanci kuma jigo cikin rayuwarta data rasashi wato ameen..abunda ke daure mata kai kuma shine,babu wanda ya taba yin zancansa a gabanta..da kunnenta dai bata taba ji ba,babu wanda ya taba yi mata maganarsa,tunda tazo gidan bata taba ji anyi labarinsa ba,ita kuma bata taba tambaya ba,inaaaa .ina ta isa tayi zancansa ita din?,bata da wannan qwarin gwiwar sam,saita tattara komai ta ajjiyeshi gefe guda,bawai don ta manta ba. Tun munira na zuwa iman nayi mata hannunka mai sanda.tana daure mata fuska da rashin sake mata,har takai ga ta fito gaba da gaba da gaya mata
Tunda na fito munee ban taba zuwa gidanku ba nikam.inaga ba.me zai hana mu haqura da wannan ziyarar,muci gaba da gaisawa kawai a waya idan da yiwuwar hakan?" Sosai taga rashin dadi qarara samn fuskar munira,saidai ya zamar mata dole tayi mata hakan,saboda ta fuskanci abinda ya sameta munira ce ta bada gudunmawar afkuwarsa kaso saba'in cikin dari,shi yasa ta gwammace su nesanci kuna gaba daya ita da ita,a yanzu mutum daya take tare da ita,suke kuma shawara wato bushira,saboda ta tabbatar ita din qawa ce ta arziqi,data fito daga gidan dattako da sanin ya kamata. Fara zuwan iman makaranta taci qwal ubanta ba kadan ba,taji jiki ta jigata,saboda shi karatu ko yaya ka barshi,to shima saiya maka nisan da baka taba tunani ba,saidai naci da jajircewa sune tushen dukkan wata nasara,haka ta sakawa ranta himma naci da kuma jurewa,da kadan kadan sai gashi ta fata ganewa,ana kuma dan tafiya da ita babu laifi,saidai ba kamar sanda take kafin aurenta ba,bata damu da hakan ba,ta sama ranta tafi tafi wataran zata dawo da kanta wannan matakin da ikon Allah.
bayan shekara biyu Turare shine abu na qarshe data fesa saboda cike kamalar kwalliyar tata,ta maida turaren saman madubi ta ajjiye tana kallon fuskarta jikin madubin dake dakin. Kyakkyawar fuskar hajar ibrahim khalilu iman fuskar da a yanzu tafi cikar kamala fiye da shekara biyu baya,fuskar data cika da tarin annuri da kuma alamu na qarin shekaru,alamun da suka qara ma fuskar tata cikar kamala,kyau da kuma haiba,sai cikar haduwar hankali da kuma sanin ciwon kai da suka bayyana akan fuskarta,a hankali ta gyara daurin kanta hagu da dama ta tabbatar yayi,ta murmusa har dimple dinta ya lotsa daga dukkan kumatunta
Alhamdulillah.ta fada a bayyane,kamar yadda ya zame mata jiki a duk sanda ta kalli kanta,taga kuma ubangiji ya saita mata rayuwarta,ta fara maida abubuwan data rasa a baya a rayuwarta masu yawa,tana godewa Allah da miyagun qaddarorinta basuyi nisan zango ba,tana godewa Allah da bai dubi halinta ko kuma abinda ta aikata ba. cikin rahama tausayi da jin qansa ya wadata rayuwarta da abubuwa masu kyau. Cikin kayanta ta laluba mayafin daya dace da shigarta da 'yar jakar hannu da take dura takardunta,ta yafa ta hada da takalmi sannan ta fara takawa zuwa tsakar gidansu,cikin wani taku da ba nata ba,wanda wala'alla sauyin yanayi da kuma rayuwa ya sanya dukkan dabi'unta na ainihi sake fitowa. A hankali ta tako zuwa tsakar gidansu,qamshin turaren wuta na kaya yana surarowa daga jikinta saboda tsabar yadda ya kama jikin nata,ya hade da sassanyan body mist da take amfani dashi Tsakar gidan nasu tabi da kallo,gaba daya ta rasa meke shirin faruwa a gidan da inna ta kasa zaune ta kasa tsaye,kwana kusan uku kenan innnar tana yiwa gidan kwalema. Iya tuquru da iman din ake aikin,kasancewarta wadda dukka ayyukan gidan suna wuyanta dama,ta riga ta saba,saidai sam ta kasa tambayar innar dalilin kwalimar. Ko yanzun ma kallon innar take ita da mufida sunata sauke kayan kitchen din innar ana fitowa dasu,yarinyar cikin dangin inna na nijer take,tazo mata hutu ne,saboda gama zana jarrabawar common entrance da tayi,da iman din aka fara aikin,amma ganin lokacin makaranta yayi yasa ta saki aikin taje fa shirya.
Sannunku da aiki ta fada tana qarasowa inda suke tana rataya jakarta
Yauwa.kin fito Inna tafada tana dan dubanta kafin ta maida kanta taci gaba da aikin da takeyi
Eh inna,harma naso na makara" tayi maganar tana duba agogon fata mai azabar kyau dake daure a tsintsiyar hannunta. Tana daga kai suka hada idanu da mufida,ta saki murmushi yarinyar
Wannan kallon fa? Iman ta tambayeta itama fuskarta a sake
Wallahi kinyi kyau yaa iman,haka nakeso idan na qara girma nima na shiga jami'a,na kuma zama 'yar gayu irinki
Yar gayu,'yar gayu,'yar gayu,bakinki baya gajiya da gayamin wannan sunan?" Dariya mufidan ta saki
Don Allah inna yaa iman ba 'yar gayu bace?,kuma kyakkyawa
Oho muku,wannan zancan naku yafi qarfina.ungo nan inna tayi maganar tana daukar dari biyar daga kudaden dake gefanta ta miqa iman din
Idan kin fito ki biya ta kasuwa ki samomin turaren bakhur
Bakhur kuma inna?"Ta tambayi innar cikin mamaki
Eh shi,laifi nayi kika tsareni haka da kallo?Kai ta kada
A'ah inna,gani nayi kina da turaruka,harda wadanda baki amfani dasu ba,ko wancan satin ma na kawo miki wani turaren wuta Wannan din shi nakeso..ki wuce ki tafi ko kuma ki bani aikena
Sai na dawo" iman din tafada zuciyarta na motsawa,tuna mata da sunan turaren tamkar wani fami ne a rayuwarta,sunan kawai ya tuna mata da wani abu jigo,haka ta ratso ta soron gidan dan fita qogar waje Sauka idanunta yayi kan dakin ya sadiqu,nan ma dai kamar cikin gidan,an fidda komai na cikin dakin,babu komai a cikinsa da alama shima kwalemar ake,tanason ganin ya sadiqun,amma sai taji ba zata iya shiga dakin ba,don haka ta saka kai zuwa waje zuciyarta na mata wasu wasi Kofar gidan dukka babu daliban malam din,da alama kowa yayi jasa waje,don dama sha daya tayi lokacin tashinsu kenan,babu kowa sai malam din dake zaune saman kujerar da yaje karatu,snaye da farin yadi qal da kuma farin rawani na wani lallausan plain yadi Malam din badai tsafta da kuma kwalliya ba,duk qwaqwarka ba zaja taba rasashi cikun tsafta da qamshi ba,duk kuwa da cewa mafi yawan kayan sawarsa harma da rawaninsa yafi tu'ammali da farare,amma ko yaushe qal zaka gansu kuna fes,hakanan malam din baisan saka tsumma ba,tun a lokacin ma da bashi da mataimaka koda yaushe cikin kyakkyawar shiga yake bare yanzu Sai data duqa tama mallam sallama,ya kuma sallameta da kudin mota kamar yadda ya saba,duk da sana'ar da takeyi amma sam shi bai damu da wannan ba,ta raba a hankali taci gaba da takawa zuwa titin unguwarsu,kwanyarta cike fal da tunanin aiken innar har zuwa sanda fa samu abun hawa ta wuce makarantar.
Daga bakin gate ta sauka ya biyashi,itakuma ta soma takawa zuwa cikin makaranta.huguma
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 38
Kamar ko yaushe daga shigarta ta fara fusgar hankalin maza da dama,duk inda ta ratsa binta ake da kallo,tun abun yana damunta harma ya zame mata jiki,ba mazan ba,hatta da wasu matan suma kallon suke binta dashi a yawancin lokuta,saidai babu fuskar da zaka tunkareta da wata magana,saboda sam bata barin fara'a saman fuskarta har dangane da ajinsu,shi yasa mutane ke kiranta da mabambantan sunaye. Wasu na mata kallon miskila,wasu na mata kallon me girman kai,wasu nacewa ta isa tayi,ai tana da kyan da zata nunawa kowa,mata da yawakuma na kishinta ne sabida tana da kyan dake fusgar hankalin samari ko abokan huldarsu. Itakam bata damu ba,saboda abunda ya kawota kawai takeyi,kuma darajar addua da takewa kanta da rayuwarta,Allah ya tsareta daga dukkan sharri na miyagun malamai harma da daliban,so bataga abunda zai dameta ba kuma. Awa uku kawai dama ke gareta cikin makarantar,saidai a tsahon awa ukun aiken inna ya tsaye mata a rai,bata kuma san dalili ba,kawai dai tasan ta tuna mata da ya amin,saboda shi daya ne a gidan ke mayatar son turaren bakhur,don haka ana tashi ta wuce kasuwar ta siyama innar aikenta,sannan ta zarce asibiti,saboda yaune ranar da zataje taga dr,don duk bayan wasu watanni tana zuwa,saboda gudun dawowar matsalarta,shawarace dr din ya bata,kuma taga alfanunta. Mutum biyar ne a gabanta,tana zaune tana ta juya turaren a hannunta har zuwa sanda aka kirata,saita maida jakarta ta ratayata,sannan ta nufi office din. Da sallama abakinta ta tura qofar ta shiga,ya daga kansa yana amsa sallamar tata,sai fuskarsa ta zarce da mayalwaciyar fara'a,ya maida kansa yana qarasa rubutunsa cikin file amma kuma yana cewa
"Hajjaju,yau kece a gari?" Fuskarta da dan nata murmushin ta amsa masa sanda take zama
"Nice dr
"Marhaban dake" saita sake murmushin tana cewa
"Na gode dr" rufe file din yayi,ya tattara dukka hankalinsa akanta,suka gaisa sannan ya fara mata tambayoyi,daga bisani ya gwada komai.komai normal yake,ya ajjiye kayan gwajin da murmushin nan dai na fuskarsa
Alhamdulillah,hajjaju lafiya ta samu,saidai duk da haka mu bamu gaji da ganinki ba,sannan ba zamu bada shawarar ki daina zuwa ba,koda sau daya.ne ko biyu a shekara" ya fada yana rubutu a file dinta
Tunda komai ya zama normal dr inaga.ai no need naci gaba da zuwa din ko?" Kai ya gyada
Idan hakan yayi miki fine godiya tayi masa sosai sannan ta buqaci amsat file din ta maida reception,saidai yace
Noo..barshi a nan hajjaju,kawai abinda nakeso na duba a jiki
Ok dr,na gode" ta sake masa godiyan tana nufar qofa ba tare data kawo komai cikin ranta ba
Ammmm.hajjaju taji ya ambata sanda ta murda hannun qofar zata fice,waiwayowa tayi,suka hada idanu,idonsa fes bisa kanta
Kice hadiza sabi'u ta shigo
Ok dr ta fada a ranta tana mamakin kallon da ya bita dashi a yau,karon farko.
Tana zaune cikin dakin nata daga bakin katifarta,ta ware fanka sosai iska na shigarta tako ina,sanye take da wata buba ta wani yadi mai sulbi,sai dankwalin inna data dauka ta daura shima mai sulbi,hannunta riqe da biro tana bin assignment din data gama da kallo cike da nazari tana dubawa,tare da bin qwaqwafin inda tayi ba dai dai ba.
Motsim shigowar mufida ya sanyata daga kai tana duban yarinyar,tun dazun suketa aikinsu ita da inna,yau din ko nemanta ba'ayi ba,duk kuwa da cewa aikin abinci innar takeyi,abincin ma wanda iman din ta qware sosai akai,wato hadin wainar shinkafa Agogo iman din ta fara kalla tana duban mufida data dauro alwalar sallar magariba tana qoqarin saka hijabinta,kawaicinta a yau ya qare,ta rasa gane abinda ke wakana cikin gidan
"Wai nikam mufida..inna baqi garega gobe cikin gidan nan?"
Au baki sani ba?" Yarinyar ya fada,da alama tana zumudin bada labarinne
Ban sani ba mufeeda" iman din ta fada tanayin wani kalar tausayi
Duk gyaran nan da akeyi har dakin yaya sadiq?,baqone zaizo gobe,inna tacemin d'anta ne zaizo daga qasar waje,kullum sai ta bani labarinsa,tace tunda ya tafi can baizo ba sai yanzu,tace yana da kirki sosai.sunansaaaaa.ummmm,ya aminu" matsananciyar faduwa da gabanta yayi har sai da biron hannunta ya subuce ya fadi,dama ya amin ne zai dawo?,kowa a gidan ya sani amma banda ita?,indai hakane kuwa kenan basu haqura ba,har yanzu akwai haushinta qasan ransu. Kafin ta sake wani tunani kiran sunanta da ya sadiq yake qwallawa daga qofar dakin nasu ya katseta,saita miqe da sauri,saidai kuma yadda dukka wata laka ta jikinta ta mutu ya sanyata cin tuntube,saura kadan ta fadi,ta dai daita kanta tana amsa sannun da mufida take mata,ta qarasa qofar dakin,ta yaye labulen tana cewa
Yaya sadiqu gani"
Ungo don Allah,hadamin shi,yanzu nakeso nasha" ya fada yana miqa mata yar babbar baqar ledar,data buda sai taga jayan fruit ne, fruit salad yakeso ta hada masa kenan Kitchen ta wuce kai tsaye ta fara aikin,tana aikin tana kallon yadda aka gyara kitchen din,ga jerin kayan abinci nan da aka rage ayyukansu,gobe kenan za'a qarasasu. A sanyaye ta gama hadawa,ta miqa inna din ta fara diban nata,sauran ta ajjiyewa ya sadiq din ta komo daki,data shigo dinma litattafan ta tattare waje daya ta haye katifarta,bata da qwarin gwiwar ci gana da duba assignment din gaba daya,ta rasa mene yake mata dadi,wanne yanayi take ciki,ya amin zaizo?,yaya haduwarsu zata kasance?,da wanne ido zata kalleshi? Tanajin mufida na tashinta tasha nata fruit salad din amma tace mata ta qoshi,wani irin fargaba mutuwar jiki gami da kasala ke dibanta,wanda ita kanta batasan dalili ba,saidai jikinta ya gama mutuwa murus,cikin wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita. Can cikin barcinta hancinta ya dinga debo mata kalolin qamshin girki,ta bude idanunta a hankali,ta juyasu cikin dakin nata,wayam yake babu mufida,da alama tuni ta fice,sai ta miqe da hanzari tana duba agogon wayarta. Qarfe tara ne na safe,yau din lecture daya gareta,itama kuma kamar ta jiya ce,sha daya na safe su gama qarfe daya,saita aje wayar,ta zamo daga katifar tata ta isa bakin qofa tana dan dage labulen tana kallon tsakar gidan,tsakar gidan nasu dako yaushe yake a tsaftace yau a kacame yake,ta saki labulen,ta koma da baya ta dauko set na kayan wankanta sannan ta sake fitowa. Sai data gaida inna dake ta faman loda waina a cooler,tadan tsokani mufida dake da son aiki bata gajiya sannan ta karbi ruwan zafi ta wuce wanka,tana shiryawa tana mamakin yadda kowa bai bi ta kanta ba bare ayi maganar zuwan ya lamin a gabanta,banda mufida ta gaya mata,ta tabbatar babu wanda zai gaya matan. Tsaf ta shirya cikin dinkin bubu na atamfa,wadda tayi mata kyau qwarai,jikinta sai fidda wani sihirtaccen qamshi yake kamar kullum,ta hada duk abinda zata buqata tayo tsakar gidan
Ba zaki tsaya ki karya ba." Kai ta gyada
Sai na dawo dai inna
Allah ya kaimu Wucewa dakin malam tayi,yana zaune da qur'ani gabansa da aka rubuta da jar tawada jikin wasu farin papers
Tun kwanaki naso a rubuta miki qur'anin nan ki wanke ki qara ruwa ki dinga sha..amma zan saka ayi miki keda mufida" malam din ya fada bayan sun gama gaisawa yana miqa mata kudin makaranta
"To a bani wannan malam tunda na gani?" Ta fada tana langabe kai,don a yanzu sau tari tafi jin dadin hira da malam din akan inna. Kai ya girgiza
"Wannan?,banda wannan,na muhammadu aminu ce" dif wuta ta dauke mata,sai ta miqe gwiwa a sanyaye tana yiwa malam sallama,idanunta suka sauka kan wata qanqareriyar shadda da hula tangaran,harda takalmi duka sabbi
Kilan duk na zuwanshi ne?" Ta tambayi kanta,sai ta fita tana mamakin yadda suka daukaki zuwan nasa,sunata shirye shirye kamar wadanda zasuyi wani biki. Ta dakinsu dake soro ma koda bata shiga ba tasan lallai dakin yasha gyara sosai,tana jiyo muryar ya sadiqu da alamu waya yake,sai ta saka kai ta fice a hankali Kusan karatun yau din gaba daya bata wanu fahimceshi dari bisa dari ba,tadai tsinta iya abinda zata tsinta,batasan me yaketa raba mata hankali da kuma dauke mata hankali ba,don koda aka tashi sai data jima kafin ta baro makarantar Tana cikin napep amma duk matsawar da zasuyi gaba zuwa gida sai taji wani iri
Don Allah idan ba damuwa juya dani kabuga" ta baiwa mai adaidaitan umarni
Ba matsala,amma zaki biya
Ka fadi nawa ne zan biya in sha Allah" ba musu ya gangara gefe,sannan ya juya kan motar suka koma baya. Haka kawai taji ba zata iya tunkarar gidansu ba,ba zata iya shiga gidan yanxu ba,ta sauke wani numfashi me nauyi tana lumshe idanunta,tana jin yadda iskar hanya ke bugun fuskarta,ta tabbatar a yanzun idan ya ameen din baya gida to ya kusa isa gidan,shi yasa ta yanke tafiya gidan kawu muntari wajen umma hassana. Suna isa ta fito ta miqa masa abunda yace ta bashi,ta saka kai cikin gidan bakinta dauke da sallama. Ta samu yaran gidan sunata shirin tafiya islamiyya,tana taya umma hassana shiryasu suna taba hira,har ta sallamesu,gidan yayi shuru ba kowa,sai yaron da take goyo Bandaki ta shiga ta canza pad din jikinta,sannan tayi alwala,duk da ba sallah zatayi ba,don dai kawai taji dadin jikinta,kafin ta fito umma hassanan ta zuba mata abinci,ta zauna tana ci suna hira. Bata jima sosai da cin abincin ba jikinta dukka ya mutu,taji tana jin bacci,saita kwanta umman ta bata waje ta fita qarasa ayyukanta,bata jima ba kuwa bacci yayi awon gaba da ita. Ba ita ta farka ba saida akayi sallar la'asar,shima qarar shigowar text a wayarta dake saman kanta ya farkar da ita,ta miqe zaune tana salati,ta jawo wayar ta duba,sai taga saqon daya shigo da number dr ahmad ne,gajeran saqo ne kamar haka
Barka da warhaka hajjaju,cewa nayi bari na gaisheki,fatan kin wuni lafiya,bissalam_*
Dr ahmad kuma?" Ta tambayi kanta cikin mamaki tare da maimaita karanta saqon,abunda ta kawo kawai a ranta shine yayi mistake na tura saqonne,saboda haka saita ajjiye wayar kawai,ta gyara daurin dankwalinta daya zame sakamakon santsin gashinta,ta miqe zuwa tsakar gida wajen umma hassana. Ta sameta tanata hada hadar yin dambu,gashi yayi mata yammaci,ta kama mata,nan da nan suka dora,ta tayata suka tsaftace wajen sannan suka koma daki suka dora hirarsu. Sai bayan an dan jima da idar da sallar magriba,harma.taci abinci sannan tayi ma umma hassana sallama,tana ta mamakin zuwan iman din da kuma dadewarta,har tana tsokanarta da cewa
Allah yasa ki dore da wannan zumunci" murmushi kawai iman din tayi,saboda ita kanta tasan ba zuwan Allah da annabi tayi ba. A hankali kamar wata tsohuwar barauniya take takawa sannu sannu,tun daga qofar gidansu zuwa cikin gidan,ta saki ajiyar zuciya sanda ta fuskanci dakin soron a rufe yake,saita qara sauri amma kuma cikin takatsantsan,ta samu ta shige dakinsu tana sauie ajiyar zuciya,duk da cewa bataji motsin wani abu ba. Jakar hannunta ta ajjiye,ta cire kayan jikinta tana canzawa mufida ta shigo
Yaa iman,yaushe kika shigo,yanzun nan inna ke maganar dadewarki
Kaina ne yake ciwo mufida yanzu na shigo..ina innar?"Tana rumfarta a zaune
"Ita kadai ce?"Eh,ai.babu kowa agidan,tun la'asar su ya sadiq da baqon baturen da suka zo dashi suka fita,basu dawo ba kuma bayanin yayi mata dadi,don haka ta fita a gurguje tayi duk wani uzurinta da zai fiddata tsakar gida ta dawo daki abinta,itadai haka nan takeji..batason su hadu da yaa ameen,batasan kuma me yasa ba
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 39
Washegari ma tashin wuri tayi,ta shirya a gurguje,ta cimma inna a dakinta tana zaune tana sauraren labaran siya, volume din can qasa,ta tadda zata iya jin duk wani motsi.
Binta da kallo innar tayi sanda take gaya mata zata wuce makaranta
"Allah ya kiyaye hanya,saikin dawo"
"Ameen" ta amsawa innar tana ficewa sa dan hanzari,cike da fargaba da kuma tsoron kada su hadu din,shima dai a ranar bata dawo ba sai bayan magrib,tana gidansu bushira,amma ta aikowa da innar yara kan tana can din.
Kayan jikinta kawai ta cire ta sauya wasu,ta zauna gefan katifarta jin shigowar saqo bayan ta jawo wayar tana dubawa
_Amincin Allah ya tabbata a gareki yake kyakkyawa,da fatan kin yini cikin koshin lafiya_
"Dr ahmad?" Ta sake tambayar kanta cikin mamaki,anya ko yana sane yake tura mata wadan nan saqonnin?,ko yauma mistake din yayi?. Bata lalubo amsa ba mufida tayi sallama ta shigo,iman ta daga kai tana dubanta,shadda ce a jikinta me kyau qwarai,dinkin doguwar riga,da alama sabuwace,don bata cikin kayanta kwata kwata da tazo dasu
"Yammatan inna,wannan kyau haka?,ina kikaje?" Iman din tadan tsokaneta,dariya tayi itama tana zama a qasa kusa da iman din
"Taro akayi fa yau,wallahi yaaya iman kinyi missing,baqon inna dan balarabe.......au,ashefa tace danta ne,yaya ameen,shine ya hada taro,ya bude wani qaton shago nayin dinki,kinga kyan da wajen yayi yaa iman?,sai naji inama ni tailor ce,kekunan dinki,injin stone,keken waiving komai dai yaya iman,baki gani ba wallahi".
Sallamarsa ce ta gauraye tsakar gidan,cikin muryarsa mai nauyin nan,wadda a yanzu ke bayyana cikar mazantaka nutsuwa da kuma kamala a tattare dashi,lumshe idanu iman din tayi,wani abu mai nauyi yana tsarga mata,kamar yasa zancansa suke,saita dubi mufida
"Dukanku yau kuna can kenan"
"Eh mana,harda inna da malam fa,wai dan balaraben nan ashe ya iya dinki,sai gashi yahau keke shima yaa iman?" Mufida ta fada cikin alamun mamaki,harda kama baki,duk da yanayin da jiki da zuciyarta ya shiga amma sai tadan murmusa kawai
"Tsohon tailor ne" daga haka ta sake bude wayarta ba tare da tana da abunyi ba
"Yaa iman.....na kawo miki abincinki?" Kai ta girgiza mata,bata jin zata iya cin wani abu
"Na qoshi mufida,kedai sannunki,na gode" sai yarinyar ta matsa wajen kayanta ta canza kayan jikinta,sannan ta fice daga dakin.
Iska mai nauyi da zafi iman din ta fitar tare da sauke ajiyar zuciya,tana ci gaba da taba screen din wayarta,zuciyarta na lulawa duniyar tunani,wanda muryar mufida ta katseta
"Yaa iman kizo inji inna" dokawa qirjinta yayi,ta daga kai da sauri,tana son tambayar mufidan waye da waye a falon,amma tuni yarinyar ta shilla abunta da gudu ta koma.
Sunan Allah ta kiraya kafin ta tashi,saita zari dogon hijabinta ta zura,ta ajjiye wayarta ta fito ta doshi falon,zacuyarta na harbawa da sauri.
Tana yaye labulen wani irin kwantaccen qamshi ya cika mata hancinta,ta bude bakinta a hankali tayi sallama,muryar data amsa mata sallamar ta sake sanyata ta daburce,kanta na a qasa ta kasa dagashi,batasan waye da waye a falon ba,batasan kuma inda zata zauna ba,don haka ga zame mata dole ta daga idanunta ta zabi wajen zama.
Karon farko idanunta suka sauka a kanshi,yana zaune saman center carpet saboda aka shimfida falon innar,wanda iman din kanta batasan yaushe aka sakashi ba,sanye yake da shadda ruwan hanta,sai maiqo take da qyalli tare da fidda qamshi,baqar sumar nan tasa ta ainihin bafillace tana nan a kansa,ta qara kyau cika da kuma wani qyalli da sheqin baqi,duk bata iya ganin fuskarsa sosai,amma tana iya hagen wani lafiyayyen gemu daya zagaye ya kuma qawata fuskarsa,ya qarawa fuskar kyau da kuma cikae kamala da kwarjini,da amaa sunansa na cikakken namiji,da hanzari ta dauke kanta daga wajen,duk da har yanzu hankalinsa nakan mufida,da alama akwai wani zance da sukeyi daya dauke masa hankali,kamar ma labarin qasarsu take bashi.
Cikin sauri ta samawa kanta waje,sai a lokacin ta lura da baraka(yayar alameen wadda ta riqeshi) daga gefe tana sallah,da yake falon na inna akwai yalwa,sai kuma ya sadiqu dake gaban kayan kallo da batasan sanda aka kawosu ba shima yanata qoqarin hadasu.
"Ina yini yaaya,an dawo lafiya?" Waiwayowa yayi a hankali ya dubeta sau daya,sai ya kautar da idanunsa,yadan saki gajeran murmushi
"Bazan amsa ba,saida kowa ya gama yimin sannu da zuwa sannan ke?" Sadda kanta tayi qasa,cikin mamakin yadda ya amsa mata a sake,kamar wani abu bai faru ba,kamar babu abinda ya gitta tsakaninsu,kafin ta bada amsa muryar baraka ta ratsa tsakani
"Banda abinka aminu dan makaranta ai bashi da wani sukuni,babu zama ko iman?" Nauyi ya kuma saukar mata,ita kanta yaya barakan kunyarta da nauyinta takeji,saita gyada kanta ta daga kai ta kalleta
"Ina yini yaa baraka,ya hanya?"
"Lafiya lau imani,gamu yau a kano,ya gida ya makaranta?"
"Alhamdulillah" ta amsa mata tana murza yatsun hannunta,tanaji kamar zata nutse,musamaman sa kwanyarta take mata tariyar abinda ya shude shekarun baya,duk da cewa ba wata magana data yana hadata mara dadi da yaa barakan ko a baya,amma ta tabbatar tana da labarin komai.
Hirace qasa qasa mufida da amin sukeyi,sai yaa barakan dake janta da hira,yayin da sadiqu ke nashi aikin,kafin daga bisani ya saki aiki yaja tsaki
"Nafa gaji gaskiya,kaga ka taso muje kawai na rakaka,kaga dare yayi,idan mun dawo ko zuwa gobe a qarasa"
"Alright" ya amsa a taqaice yana miqewa
"Idan na dawo maci gaba ko" yace da mufida,ya tako a hankali ya gifta iman din,idanunta ya sauka saman qafarsa daa sake haske da fresh,zaratan yatsunsa sun cika da gashi
"Yaaya zamuje mu dawo"
"To kwace ina gaisheta" suka saka kai suka fice,yayin da yabar qamshinsa mai yawa a hancin iman din,ya kuma bar zuciyarta da tunani da kuma wasi wasin inda zasu,duk da yadda take jan zuciyartata amma ta nace dason sanin inda suka tafin,har sai da inna ta shigo sannan ta samu sasauci,ta bata abun shara tace ta gyara spare dakin dake kusa da nata,baraka zata kwanta a ciki.
Haka kawai ta dinga kasa kunne taji shigowarsu,bata samu jin shigowar nasu ba kuwa sai wajen sha daya da rabi na dare,ta sake lumshe idanunta tana jin muryarsa daga can nesa yana magana,da alama yana daga soron,bai shigo cikin gida ba,ta sauke numfashi tana gyara kwanciyarta zuwa daga side din.
Basu sake haduwa ba ita dashi tun daga ranar,washegari dama yaya baraka ta koma,ita kam sunyi sallama.
Satinsa biyu taji labarin ya koma daga bakin mufida,abun da ta danji ya mata susa a ranta kenan,lallai tabbas duk wata alaqa dake tsakaninsu da amin din ta lalace kenan,banda haka......inda yadda ya dauketa a baya yanzunma hakanne,ba shakka itace mutum ta farko da zata fara sanin komawarsa.
A bakin mufidan takejin labarin nan da wata shida zai gama karatunsa ya dawo gaba daya,yace ma a nan za'ayi bikin salla qarama dashi,mufidan ta dauko wayar inna da tace shine ya siyawa innar,ta nunnu mata sabon shagon da tace sunje bikin budeshin.
Shagone mai kyau na dinkawa da kuma saida kayan sawa,sutturu kala kala daga na maza har na mata,ba wani qatoto bane,amma kuma yana da yalwa da kuma girma,bugu da qari yadda aka tsara wajen dole ya burge mutum,an tsara komai bisa tsari me qayatarwa,sannan ya sadiqu shine shugaban wajen da zai dinga kula da gurin.
Kanta ta jinjina,har yanzu ya amin bai rabu da dinki ba kenan,yana nan cikin jininsa?,saita miqawa mufida wayar tana murmushi tare da cewa
"Gaskiya yayi kyau wajen"
"Wallahi yaa iman saima kinje,yace ayimin dinkin sallata acan ma,har ya zabarmin atamfofi,wallahi dan gidan innar nan yana da kirki sosai sosai yaa iman" murmushi ya subuce mata,mufidan ta tuna mata da wani abu,ta tuna mata sanda take kamarta a shekaru,sanda ya amin din yake nata take tashi,sanda yakeji da ita,yake kula da komai.nata cike da kulawa da takatsantsan
"Sosai ma kuwa" ta amsa mata tana jijjiga kai,sai mufidan taci gaba da bata labarin ya amin din da kirkinsa,ita kuma ta bata lokaci tana sauraren yarinyar.
Ko a washegari tana ta kasa kunne taji ko inna ko ya sadiqu ko malam wani zaiyi maganar amin da ita,saidai babu wanda yace mata komai,abun sai ya bata mamaki,amma kuma ita a qashin kanta ta gayawa kanta,suyi mata maganarsa suce mata meye?,a sanda ta yankewa kanta hukunci ba wanda tayi shawara dashi,sannan a yanzu duka rayuwar amin da mu'amalarsa bai shafeta ba,indai zata yiwa kanta adalci,ya kamaci ta tsame kanta,da wanna ta sanya abun wani sashe can na cikin ranta,duk da ta sani abune mai yiwuwa ace ta mantar da kanta al'ameen din.
*_BAYAN WATA UKU_*
Tsaye take a parlor din inna tana hada tea,bayan ta gama duk wani shirinta na tafiya makaranta,don hatta da jakarta ma tana falon innar,sai data gama hadawa tsaf sannan tafara kurba tana tsaye kusa da fridge.
Labulen uwar dakan inna aka daga,innar ta fito cikin atamfarta mai kyau England,tayi tsaf da ita,kana ganinta kasan tana cikin jin dadi da samun kulawa sosai,don tsufanta da shekarunta basu wani bayyana ba sosai,musamman da yake ba wani haihuwa tayi me yawa ba,mayafinta a hannu iman ta kalleta
"Au fita kema zakiyi inna?"
"Eh amma yanzu zamu dawo ai,cewa mufida tayi hanzari ta fito" sai ta ajjiye cup din hannunta tana daukan jakarta da mayafinta itama
"Naji ya sadiqu yana magana dame adaidaita,idan hanya daya zamuyi ku saukeni a makaranta mana,na huta fita titi tarar abun hawa"
"Bari sadiqu yazo muji" inna ta amsa mata tana zura hijabinta,dai dai lokacin sadiqun ya shigo,shima a shirye tsaf cikin wani tattausan yadi da al'ameen ya kawo musu iri daya shi dashi
"Inna game adaidaita yana qofar gida yana jira"
"Ya sadiqu idan hanyatace ku saukeni nima"
"Muje,amma sai mun fara biyawa ta inda zamu din kan a qarasa makarantarku"
"Ba matsala idan ba dadewa zakuyi ba,nima akwai sauran lokaci" da haka suka dunguma suka fita gaba daya,bayan ya sadiqun ya kulle gidan,saboda babu kowa,malam ma ya fita.
Sam bata fuskanci inda zasu ba sai da suka dauki hanya taji ya sadiqu yana yiwa inna bayani
"Yayi qoqari gaskiya sosai,shi yasa kudin hannunsa suka kusa yankewa,filin babba ne,ya siya kayan gini da yawa,farawa zasuyi"
"Aminu badai qoqari ba,Allah yaci gaba da dafa masa"
"Ameen inna,gaskiya dai kam,yayi dabara da bai saki sana'arsa ba,kinsan wasu daliban idan suka fita qasar waje,sai suga ai faduwa ce suyi sana'a,zama suke cima zaune sai abinda gwamnati ta aiko musu dashi,sanda ma.basu samu ba haka zasu rungumi hannu" kai inna ta jinjina
"Kaga kuwa wannan aiba dabara bace,ni nasan aminu da zuciyar nema,bazai taba zama haka ba dama" kaman bata a cikin motar haka tayi,saidai kunnuwanta na tare dasu,har zuwa sanda suka qaraso unguwar suka soma shiga cikinta.
Sababbin gidaje ne a unguwar,kana gani kasan mazauna cikinta duka basu jima da fara tarewa ba,saida akwai gidaje ba laifi,unguwace me kyau da tsari,a hankali har suka qaraso bakin wani kango,wanda zagayeshi kawai akayi da doguwar katanga.
Cikin adaidatan tayi zamanta,ganin babu wanda yayi mata tayin ta fito din,bayan wajen minti talatin sai gasu sun sake fitowa sun ci gaba da tattaunawa,bakin inna cike fal da addu'a akan amin din,har sanda suka qaraso bakin motar ya tayar suka tafi.
Bayan watanni biyu shirye shiryen daukar azumi ya kankama,rana daya taga an fara gyaran gidan nasu,an gyara tsakar gidansu an shimfida marbles,parlor din inna an sassaqe an masa tiles,haka rumfar malam ma,bandakin gidan shima ba'a barshi a baya ba,sai dakinsu ta sadiqun shima da aka maida shi tiles da tiles har jikin bango,sannan akabi gidan aka yi masa fenti.
Dama can gidan nasu gini ne tsayayye me qwari da kyau,ga kuma innar gwanar tsafta,sai gashi ya sake dawowa sabo fil,aka shirya komai a muhallinsa,cikin qanqanin lokacin gidan yayi wani haske gwanin sha'awa.
Cikin taimakon Allah da huwacewarsa aka dauki azumin ramadan,sannu a hankali kwanakin suka fara shurawa,har aka shiga goman qarshe,sai gashi ana zancan jibi sallah,a ranar ne iman din suka tafi qunshi da gyaran kai ita da mufida,yanayin cikowar sallah daban wajen masu lallen da gyaran kai,wannan yaja musu basu suka dawo gida ba sai bayan sallar isha'i.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 40............Inna a bani abinci,kamar banci komai ba wallahi" iman ta fada tana tuje dankwalin kanta,sassalkan gashinta da yasha gyara ya bayyana,ta zauna saman kujera tana jawo flask din data gani,ta bude ta tsiyayi kunun ciki Anan parlor din inna taci abincinta ta qoqarta tayi sallar asham,qarfe tara da wani abu saiga ya sadiqu,mufida ta anshi ledar hannunsa bayan tayi masa sannu da zuwa,ya amsa yana zama,iman ma tayi masa,sai mufidan ta matso tana shirin ajiye masa ledar
A'ah dauke,ai ba tawa bace,kayan sallarku ne aciki" murna sosai ta kama mufida,ta miqawa inna ledar,innan ta fara fidda kayan ciki tana dubawa. Atamfofine kala uku a dinke na manya,dinki me kyau da tsari,sai kuma lace guda daya,sai na mufida kala biyar itama,atamfa uku lace biyu,dukkaninsu kana ganinsu zasu burgeka,daga dinkin har kayan kasan wanda yasan kan abunne ya zabesu
Wannan inji al'ameen,saiki zaba kalolin hijaban da kukeso gobe idan na fita sai nasa a dinko muku,da size na takalmin mufida,ke dama 38 ne ko?" Ya fada yana kallon iman,kanta ta gyada gami da amsa masa da
Eh". Godiya inna taci gaba dayi kamar ameen din yana wajen,yayin da sadiqu ya soma bata labarin yadda shagon daya bude keta samun hubbulowar jama'a
Wallahi inna baki gani ba,yadda kikasan an yiwa wajen yayyafin farinjini,sai yanzu nake gasgata dabarar ameen din,daa inata cewa kar ya bude,ashe shi ya dade da sanin albarkar dake cikin dinki"
Banda abunka ai tsohuwar sana'a ce da qasar hausa ta gajeta,mutane ke raina sana'ar,amma duk wata sana'ar hannu ai albarka gareta,har yanzu akwai manyan gidajen da basu bar gadonsu ba,saidai sun zamanantar da ita kamar yadda aminun ya zamanantar da ita shima
Gaskiya dai,ai na gani" ya sadiqun ya fada,yana rufe bakinsa wayarsa ta dauki ringing
Kinga shine ma yake kira" sadiqu ya fada yana duban inna
Dan halak kenan,yaqi ambato" ta fadi tana murmushi,suna gama gaisawa ya miqawa inna,bayan sun gaisa tayi masa godiya sosai,sannan ta hadashi da mufida,a nan ne suka dan jima suna magana,da alama zolayarta yaketa yi tana dariya. Tsam iman ta miqe,ganin yadda koda yaushe suke sake maidata kamar wata bare ko baquwa a cikinsu,saita wuce dakinta ta barsu a parlor din. Kira ne ya shigo tata wayar sanda ta gama wanka ta dawo don sauya kaya,bata samu dagawa ba har sai da aka sake kira,ta qarasa fesa turarenta ta ajjiye ta qaraso ta dauki wayar tana duba me kiran. Dr ahmad ne,ta danji mamaki,don bai taba kianta ba,iyakarta dashi tex,shima iyaka gaisuwa ce,ita kuma ta maida masa masa da thanks,ko tace masa na gode sosai. Tana daga tsaye ta daga kiran,sallama yayi mata daga bangarensa ta amsa masa
Har na fara tunanin ba zaki daga wayata ba
Saboda me?,nasani ko wani maganin ka samomin?" Dan qaramin murmushi ya saki
Wannan karon idan akwai wanda za'a bawa maganin ma nine" bata gama fahimtar maganarsa ba ya sake sako gaisuwa
Ya gida ya ibada"
"Alhmdlh,ya akaji da marasa lafiya?"
Gamu nan,mun godewa Allah" shuru ne yadan ratsa,kafin daga bisani ya sake magana
Inata miqo gaisuwata hajiya amma bana samun wata gamsashshiyar amsa banda ta godiya,ni kuma ba godiyar nan nakeso naji ba"
Toooo..to me kakeson ji dr?" Dan murmushi ya saki
So nake a tambayeni dalilin yin gaisuwar" dan murmushi kawai ta sake,saboda yadda yayi maganar ya bata dariya
Ai nasan akwai kyakkyawar mu'amala tsakanin likita da mara lafiyansa ko?"
Duk da hakanma..amma yanzu wannan likitan yanason sake qarfafa alaqa da dangantakar dake tsakaninsa da patient dinsa,bayan waccar alaqar" ya zuwa yanzu ta sansano wani abu a cikin maganganunsa,amma sai tayi kamar bata fahimta din ba
Idan babu damuwa,inaso ayimin izini nazo yawon salla,koda ba za'a bani barka da sallah ba" Dr ahmad yana da kima da mutunci a idanunta,amma saidai batajin zata bashi wannan damar,ita a yanzun gaba daya ta sare da lamarin maza,tsoro suke bata,to ta bawa dr ahmad din damar zuwa malam ya ganshi tace masa meye?
Kayi haquri dr.ba yanzu abubuwa sunmin yawa
Sai yaushe kenan?" Ya ritsata da tambaya,kasa gano amsar daya dace ta bashi tayi,sai kawai bakinga ya subuce da fadin
Nan gaba kadan zan saka ranar" ajiyar zuciya ya sauke,duk da ba haka yaso ba amma yace
Allah ya nuna mana lokacin" kasancewarsa bame zafi ba,hakanan bashi da tsawwalawa,yana da sauqin kai da kuma saurin fahimta.
A sauqaqe yadan jata da hira,bai kuma matsa da yawa ko ya kaita bango ba yayi mata sallama,suka katse wayar dukansu. Tana ajjiye wayar ta waiwaya wajen mufida wadda ta shigo rungume da kayanta,har yanzu akwai farinciki qarara saman fuskarta
Yaaya iman..wannan sallar xan sha kwalliya wallahi,irin taki da daurin nan da kikeyi xakiyimin" murmusawa tayi
Aikam dai ya kamata" ta amsa mata a taqaice,saboda haka kawai takejin batason magana. Kwanaki biyu a gaba musulmi suka sauke azuminsu,washegari akayi idi,ranar sallar suna gida,saidai sunyi kwalliya gaba dayansu,sunata baqi jifa jifa inna na saukarsu da tuwon sallaj da basa fashin yinsa duk salla,a ranarma taga inna nata shirye shirye,kamar wancan karon na zuwan ameen din,ta tabbatarwa ranta shi dinne zaizo,saiai bata sani ba,gobe ne ko kuma jibi.
Karfe sha daya na safe ta gama shirinta tsaf cikin kwalliya,cikin daya daga cikin sababbin atamfofinta,sam bata da matsala sutura koda shekara nawa zatayi bata siyeta ba,hakan ya sanya zaiyi wuya ka ganta da kaya ka sake ganinta dasu a kurkusa. Tsaf ta gama shirinta,saidai tana dubawa yaga mufida da zasu fitan tare bata shirya ba
Wai meye haka mufida?,tsaiwa zanyi jiranki?"
Nafa fasa zuwa yaa iman,yaya ameen ne zai dawo yau" sai da taji qirjinta ya amsa,amma ta dake ta amsa mata da to ai shikenan,ta yiwa inna sallama ta wuce gidan kawu muntari.
Wuni guda hankalinta a rabe yake gida biyu,idan alameen ya dawo yanzu ya dawo kenan,ta yaya zasu rayu gida daya tare ita dashi?,wannan tambayar itace ya hanta sukuni,harta qaraci wuninta ta dawo gida. Koda takoma gida boyon kanta tayi a daki,ta kuma fake da ciwon kai,ta tilastawa kanta baccin wuri,washegari kuma still ta sake fita,data dawo dinma ta qunshe kanta a daki,a rana da uku ne yunwa ta sanyata tashin wuri,bataso amma dole haka ta fito,tana sanye da doguwar rigar bacci mai kauri da taushi,sai baby hijab data dauran saman kanta,ta tsallake mufida dake bacci ta fito tsakar gidan nasu ta zarce kitchen. Gidan shuru ba motsin kowa,da alama basu tashi ba,don haka take komai cikin takatsantsan karta tashi wani,kitchen din nasu ba kasafai ya fiya dattin dare ba,sabida suna gama girki inna ke sawa a wankeshi kota wanke da kanta saboda gudun zaunuwar qwari,don haka dan sake goggoge shi tayi,ta duba abinda suke dashi,ta dora breakfast din,cikin ranta tana danjin marmarin yin girkin,saboda tadan kwana biyu bata shiga kitchen din ba.
Tana aikin tana lissafin inda zataje yau din,taga miscal na munira,saidai bata bi ta kanta ba har yau,muniran nata nacin ci gaba da qawancensu,da kuma son wanke kanta game da aurenta da bassam,tana gaya mata itama batasan haka bassam yake ba,da bazata bari ya samu iman din ba,ita duka wannan yanzun ba shine a gabanta ba,an riga an wuce wajen,tunda dai qaddararta tazo da sauqi tana godewa Allah,kawai dai sam a yanzun bata sha'awar qawancensu da muniran baki daya,shi yasa taketa ja baya da ita,layinta na yanzun ma sabo ne data canzashi baya ya fara zuwa makaranta,batasan ya akayi muniran ta samu number ba.
Wani mummunar faduwar gaba ce ta ziyarce tana kwashe kaskon qarshe na chips din data soya,daga dan nesa kadan take jiyo muryarsa,da alama yana bakin qofar shigowa tsakar gidanne,a hankali muryar take kusantota,bugun zuciyarta na qara daduwa,duk da haka ta aro jarumta tana ci gaba da kwashe dankalin don kar ya qone,har zuwa sanda taji muryar tasa fa fito sosai,da alama yana baki qofar kitchen din kenan a tsaye,sai a sannan ta fahimci waya yake,waya kuma cikin taushi da Idan ban takuraki ba zan iya samun ruwan dumi?" Ya fada cikin laushin muryar san nan da ya sanya wani abu ya tsarga mata,sa'annan ya kuma tuna mata da wani lokaci acan baya,lokaci me matuqar dadi cikin rayuwarta,lokacin da duk safiya yakanzo ya tsaya kamar haka,yakanzo yana mata hira tana aiki,ko yana tayata..idan kuma da idanun inna yakanyi monitoring dinta.
Ci gaba yayi da wayarsa hankali kwance yana kallon wani wajen,saita juya jikinta na dan rawa kadan,ta debo masa ruwan zafi,tunda ba kamar baya bane da take da yaqinin zaizo,wanda take debo ruwan ya samu ya huce kafin yazo sha.
Gashi" ta fada tana miqa masa,sai a sannan ya waiwayo,itama kuma sai a sananan taga fuskarsa tarwai,ya sake hada wani kyau cikar kwarjini da kamala,gashin da ya barwa fuskarsa ya sake maidashi cikakken matashi mai jini a jika,kyansa kamar ya ninka na baya,saboda ya cakuda da ilimi hutu da jin dadi,ba kamar na baya ba dake hade da fita nema a kullum,cikin zafi rana ko ko kuma ruwa. Batasan yadda akayi ba ta saki kofin ya sube,sai ga cup din shi sa ruwan da yake dauke dadshi sun zama pieces qasan tiles.
Subhanallah" ya fada da hanzari yana cire wayar da yakeyi din daga kunnensa,cikin sauri ya duqa yana cewa
Garin yaya haka?,ai ban karba ba,bakiji ciwo ba dai ko?" Kanta ta girgiza alamun a'a,sai ta juya da sauri zuwa cikin kitchen din nemo tsintsiya a rude
A hankali mana" ya fada da dan sauri,saboda yadda yaga tana tafiya da sauri sauri,har tana shirin taka fasashen tangaran din
Move ya fada yana qarasawa kitchen din,a hankali ya maida wayarsa aljihu,sannan ya matsa inda dust bin da tsintsiyan yake,ya daukosu,ya duqa a hankali ya sharesu ya zuba a dust bin din,sannan ya matsa kusa da flask din,ya bude ya zuba wani ruwan zafin ya fice a kitchen din yana cewa
Ki dinga lura Gaba daya ji tayi jikinta ya sake,ta kasa ci gaba da aiwatar da komai,ta koma jikin cabinet na kitchen din ga jingina tana sauke numfashi,har yanz rawan da jikinta yakeyi bai dai daita ba,ta kusa minti goma sha biyar a haka,sannan ta motsa taci gaba da aikin,wanda ba jimawa mufida ta tashi,ita ta kama mata wasu ayyukan,don gaba daya wani karsashi na jikinta babu shi ya gudu. Har ta kammala aikin bata sake ganin wulgawarsa ba,sai kawai ta zarce da wanka,ta fito ta shiga dakinta ta shirya tsaf,sosai tayi kyau cikin wani lace da aka yiwa dinkin riga da skert, color din lace din ta haskata sosai da sosai,lite makeup tayi kamar yadda ta saba,fatar fuskarta nada kya da sheqi,hakan yasa yawancin lokuta koda lite makeup tayi zakaga tai masifar yin kyau,koda lio gloss kawai ta shafawa lebbunanta,ko abincin bata iya ci ba ta dauki mayafinta da jaka ta nufi dakin inna. Daga bakin qofar falon tadan tsaya,gabanta ya fadi saboda jiyo muryarsa da tayi daga cikin falon,kamar ta koma,saidai kuma babu yadda za'ayi hakan ta kasance,saidai cikin biyu ayi daya,ko tayi shahada ta shiga ta nema izinin fita,ko kuma ta koma fa haqura da fitan,wanda a zahiri tana buqatar ta fita din. Mayafin kayan ta ware ta yafashi saman kafadunta,sannan ta dan runtse idanunta kafin ta sanya hannu ta bude labulen ta shiga da sallamarta. Ameen dinne ya amsa hankalinsa nakan hada tea,yana zaune saman center carpet da kayan breakfast a gabanshi,yayin da inna ke saman kujera can gefanshi suna hirarsu. Bai daga kai ya dubeta ba har tazo ta gotashi zuwa gefan innar,murya a qasa tace "Inna zan fita...yau zanje gidansu
Au,ai na tsammaci aiki kika samu" cira kai tayi ta dubi innar
Aiki kuma inna?"Eh,da naga kina sintirin fita kullum..halayyar da kika tsiro da ita kenan iman?" Ajjiye cup din yayi ya miqe a hankali ya fice daga parlor din,hakan ya sanyainna ta maida hankalinta sosai ga iman,fuskarta a dinke tsaf fiye da daxu.[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 41
*_KU BIBIYENI TA AREWABOOKS DOMIN SAMUN SABBIN PAGES DA DUMINSU_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62beaa7c93b638ade30a0e93
41
"Baqin hali da baqar zuciya kika koyo?,daga ina?,duk fice ficen da kike ina sane fa,nayi shuru ne na zuba miki ido naga gudun ruwanki.....tun zuwan aminu na farko na karanci take takenki,bakyason ganinsa saboda ya miki laifi?,bakyason ku hadu ko?,duk wata sabga data shafeshi ko ta shafi uzurinsa baki saka hannu babu ke a ciki,shine yanzu kika tsiri fita saboda ya dawo gida,to baro kiji,saidai ke kibar gidan,saboda aminu ya dawo gida kenan,idan ma baqinciki kikeyi saidai ki yishi ki gama ke kadai......mara tunani kawai" tunda inna ta fara fadan kuka ya kubce mata,haquri kawai take bata,tama rasa da bakin da zatayi mata bayanin da zata fuskanceta,sam abinda innar ta fahimta ba haka bane......sai ta miqe da sauri sauri ta fice daga parlor din,ganin innar ta kasa fahimtarta.
Dakinta ta isa,ta fada kan katifarta tana sakin wani sabon kukan,ta yaya zata fahimtar da inna kunyar alameen takeji?,yaya zata ganar da ita nauyinsa takeji?,tana nadamar furucinta a kansa ne na baya?,tana nadamar ayyukanta na baya,da kuma jin kunyar lafuzanta,duk sanda ta ganshi saita tunasu,saitaji kamar a yanzune take ce masa bata sonshi,kamar a yanzune take furta me zatayi dashi,kamar a yanzune take fadin Allah ya kiyaye ta aureshi,bata gaba ko fushi dashi......saboda bai cancanci tayi ba.
Haka ta dinga kukanta ita daya,mufida ta jima a kanta cikin rashin jin dadi tana bata haquri,kafin ta wuce ta bar mata dakin.
Ta jima ahakan,kafin daga bisani bacci ya dauketa,baccin da tayi na awa biyu,bata farka ba sai qarfe daya saura,kai tsaye ta daura alwala,ta dawo ta sauya kayan jikinta zuwa masu sauqi wadanda ba zasu dameta ba.
Kitchen ta zarce ta fara musu shirin abincin rana,tayi alqawarin faranta ran innar da dukkan wani abu da tasan tanaso,zai kuma faranta mata,indai kula da amin ne damuwarta zata gyara in sha Allah,saidai tana tunanin yadda hakan zata kasance,tana tunanin yadda shi kansa zai karbeta ta koma kamar da.
Lafiyayyen girki ta tsara,wanda ta jima batayi irinsa ba,sannan ta hada lemo,don a yanzun basu da matsalar wajen sanyi,fridge biyu keda innar,daya a falonta,daya na rumfar malam,ta saka a ciki don yayi sanyi.
Kamar yadda ta saba haka ta hada tray guda na abincinsu takai parlor din inna,sannan ta koma daki ta zuba nata taci,abincin bai shiga da yawa ba,saboda yadda ranta yake babu dadi,haka abincin bai mata taste a baki ba,tadaiyi qoqarin dora walwala akan fuskarta saboda innar,data gama ci ma sai ta dawo parlor din ta zauna suka kunna kallo,saidai gaba daya hankalinta bashi a wajen
"Kinga mufida.....nasan yayunki na hanya sun kusa isowa,dinga daukan abincin nan a hankali kina kaiwa dakinsu,ga muqulli ki bude" inna ta fadi,mufidan ta tashi ta karba muqullin,duk iman din sai taji ba dadi,saboda aikinta ne,amma ta bari,tunda mufidan zata iya,ta dinga diba da kadan da kadan harta gama din,bayan minti wajen goma iman ta tuna da lemon,tasan basu fiya son abu yayi sanyi da yawa ba,gwara a cire musu shi a kai musu,kafin suci din xai huce,don haka ta miqe,ta cire lemon ta nufi dakin bayan mufida ta gaya mata sakaya qofar kawai tayi bata rufe ba.
Hankali kwance ta tura qofar,saboda tasan babu kowa a ciki,wani sanyin dadi ya bugi hancinta,dakin ya sakw wani girma kyau da haske,tunda akayi gyaran bata taba shigowa dakin ba sai yanzu,ko ina tsaf tsaf,tiles din nan yasha guga,mamakin ma wanda ke gyara musu dakin haka ya kamata,ta duqa a hankali tana ajjiye jug din,dai dai lokacin da ameen ya fito daga toilet.
Da sauri ta miqe,har jug din na rawa kamar zai biyota,saida ameen din yace
"Kula fa" batayi zaton yana dakin ba,hannun rigarsa a nade zuwa gwiwa,ya cire links din rigar,fuskarsa zuwa hannun da qafar tasa duk jiqe da lema,da alama alwala yayi,hakan ya bawa kwantaccen gashin dake hannunsa damar sake kwanciya lif,sai taja da baya tana shirin fita,ya sadiqu ya sako kai.
Dubanta yayi sosai
"Yau kuma a gari inji maqi baqo?" Binsa tayi da kallo,yana qarasawa gami da bude kwanukan abincin
"An gama nunqufurcin kuma yau anyi abinci kenan" ameen dake ware hannun rigarsa bayan ya shimfida abun salla ya xuba mishi idanunsa
"Xakazo muyi sallar tukunna ko sai ka gama sharhin?"
"Da alwalata fa,amma dai bari na sake wata.....idan kin shiga ki cewa inna mun dawo" wannan ya bata damar juyawa da hanzari ta fice,tana godewa Allah da bai samu damar sauke mata nashi kason ba.
"Wannan abun sam banajin dadinsa ba sadiqu" amin din ya fada sanda sadiqun ya fito daga alwalar
"Me akayi?" Tsaiwarsa ya gyara
"Ya za'ayi a takura yarinya haka?,dazu dazun inna ta gama yi mata fada,sannan kai kazo da naka zaka dora?,duka takurar ta meye ne?,kowanne bawa da kalar tasa qaddarar,kuma duk yadda ta riskeshi haka zai karbeta,don ban auri iman ba a baya ba wani abu bane,ba hakan na nufin dukka wata kyakkyawar alaqa dake tsakaninmu ba ta yanke,bata sona ne.....kuma ba wanda zai zauna mata dani,ta samu rabonta nima kuma na samu nawa,komai.ya qare a tsakaninmu,ba wata sauran alaqa,amma kuma har yanxu tana nan a matsayin qanwata.....to kuma meye na tsananin?"
"To akaramakallahu......tayar mana da sallah" sadiqu ya fada yana jinjina karamci irin na amin din,yana tuna irin wahalar da yasha a asibiti shekarun baya sanda iman din ta zama ta wani,amma ko a sannan nunawa yake ba silarta bane,muqaddari ne daga Allah.A yanzun kuma yana qoqarin sake share komai tsakaninsu,da kuma yunqurin maida matsayinta irin nada,lallai iman din tayi asara iya asara,asarar da bayajin zata maida kamarsa,tunda kusan zaice mai rabo ta dauka......
Ranar wuni tayi cikin gidan,kuma cikin parlor din innar,babu inda taje,duk don ta faranta ran innar,sai kuma taga ma gaba daya ma baya zama a gidan,daya shigo yake fita,da alama akwai wani abu me muhimmanci da yaketa aiwatarwa,wanda ya hanashi zaman.
Hudu ga sallah ya shirya zuwa jigawa wajen yaya baraka,mota har qofar gida mai kyau ya dauka shata shi kadai,batasan mufida zata bishi ba,sai gani tayi tana shiryawa,tayi shuru tana tuna shekarun baya da suka shude,a irin lokaci irin wannan itace kan gaba wajen tafiya jigawan,idan sukaje a qalla sukanyi kwanaki uku acan,yaaya barakan tana lelenta gami da ina ka aje da ita.
Tana parlor tana yiwa inna moping ya shigo parlor din,sanye yake da wata danyar shadda ruwan sararin samaniya,wadda ta dinku ta kuma zauna a jikinsa.hakanan ta dace da jikinsa,kansa babu hula,hakan ya bayyana kansa daketa qyalli,da alama ta samu gyara ainun,hular tana riqe a hannunsa kawai,da alama baida sha'awar sakata,kallo daya zaka yi masa kasan cikakken dan gayu ne,wanda yasan ma'anarsa,bawai a baki kawai ba,har a aikace,duk indanya gifta kuma sai ya bar tsarabar qamshinsa mai sanyi a wajen.
Kallo daya tayi masa ta sadda kanta qas,wani kwarjini yake mata a yanzun sosai fiye da shekarun da suka shude,bata sani ba ko a yanzun yafi cika idanu ne,shekaru da cikar sametakarsa da suka bayyana muraran oho
"Ina kwana?" Ta fada kanta a qasa,don tasan ba zata iya hada idanu dashi ba,waiwayawa yayi yayi mata kallo daya ya amsa da
"Kin tashi lafiya?" Yasa qarasa takawa zuwa ciki,idanunsa kan agogon bangon parlor din innar
"Alhmdlh" ta amsa masa a gajarce,saboda sam bata saba da irin wannan gaisuwar tasu ba,baquwace a gurinta,kuma sun fara irinta ne tun sanda komai ya lalace a tsakaninsu.
Kamar ko yaushe ya tsugunna a ladabce ya gaida inna,ta amsa tana cewa
"Tashi aminu karka bata jikinka,wajen a danyace yake bai bushe ba" sai ya saki murmushi kawai yana cewa
"Inna zamu wuce"
"To ma sha Allah......sai yaushe kenan?"
"Eh to,ina jin ba zamu wuce gobe ba,saboda cikin satin nan nake saka ran fara shiga office,kuma har yanzu ban gama shirya komai da komai ba"
"To madalla,madalla......bari na baka saqo ka kaiwa barakan" sai inna ta miqe zuwa cikin dakinta,tsalelen agogon hannunsa mai tsada ya kalla,sai ya sauke hannunsa yana sake gyara zamansa,yana dan tsokanar mufida da lallausan muryarsa,akan yadda ta zaqu su tafi,har zuwa sanda inna ta dawo da leda babba ta miqa masa,ya amsa suka sake sallama
"Allah ya kiyaye hanya" kalmar data amsawa mufida da ita kenan sanda take ce mata sun tafi.
A ranar tayi zaton zata sake sosai,saboda dodon nata baya nan,amma sai taji sam ba haka bane,hasalima gaba daya sai takejin wani kewa da rashin dadin zaman gidan,daga bisani ta alaqanta hakan da rashin mufida,tunda zuwa yanzu sun saba sosai,har inna na shawarar daukota gaba daya,tunda tasan da gudu iyayenta zasu bata ita.
**** *WASHEGARI.......* Samun kanta tayi da tsara abinci me kyau,abincin ma kalar wanda tasan ya amin din yanaso,tunda taji sunyi waya da inna,ya tabbatar mata zuwa yamma zasu taho,yasan zasu qaraso kafin magariba,tunda tazarar dake tsakanin jigawar da kano bai wuce awa biyu da rabi ba.
Sosai innar taji dadin abunda tayi,itama hakan sai ya faranta ranta,tunda dama tayine saboda innar,burinta kuma ya cika,innar ta dinga janta da hira,abunda ya jima bai faru a tsakaninsu ba.
Sai hudu na yamma ta gama komai,ta fada wanka sannan ta shiga dakin don ta kintsa jikinta.
Tsaye tayi a bakin madubi tana kallon fuskarta,ita kanta tasan yau fuskar tata ta cika da annuri,hakan kuma yana da alaqa da yadda suka wuni yau da inna cikin dadin rai,sai ta samu kanta da yiwa kanta alqawarin lallai zata ci gaba da yin hakan,kodon ta samu irin wannan kulawar data rasa a baya.
Barin gaban mudubin tayi da sauri ganin lokacin sallar la'asar na nemam qwace mata,ta isa ma'ajiyar kayanta,ta fitar da wata doguwar riga mai budadden hannu,wuyan me kwala ne,haka nan qasar rigar a bude yake sosai,ta saka ta shafa powder da lip gloss,sannan ta saka hijabinta ta tada salla.
Tana idar da sallar ta fara azkar dinta na yammaci,kamar jira wayar tata take ta idar din ta dauki kida,ta miqa hannu ta dauko tana duba me kiran,dr ahmad ne,kuma ko shekaran jiya ya kirata ya gaisheta kamar yadda yace,saita daga wayar ta kara a kunneta hadi da sallama.
Cikin sakewa da sauqinsan nan ya amsa mata,sannan ya fara gaidata,abunda yake dada sakata jin nauyinsa kenan,shi bai wani damuwa da ta gaisheshi,mutum ne mai.matuqar sauqin hali da sauqin kai,saita maida.masa gaisuwar,ya amsa sannan ya fara janta da hira.
Tadan saurareshi,saboda tana kunyar qin tsayawar,don sau biyu yana kira tana taras da miscalled kuma.bata bi kiranka,kuma ko a yanxun bai mata qorafin rashin daga wayar ko kuma qin biyo kiransa ba.
"Har yanzu lokacin baiyi ba da za'a bani dama nazo?" Kanta ta girgiza kamar tana gabansa,amma a furuci sai tace dashi
"Kayi haquri" ajiyar zuciya ya sauke
"Inata haquri hajjaju......amma zan gaya miki gaskiya,kawaici kawai nakeyi,inason nazo mu tattauna seriously,zuciyata kullum qara ragwancewa takeyi,kada naje ina zaune ayin overtaking" duk da ta gama gano manufarsa a kanta,amman yanzun da ya fara bayyanawa sai da abun tajishi wani iri,batasan me ya dauki dr ahmad ya fada sonta haka ba,amma koma meye tanaso su rabu lafiya,saboda mutum ne daya girmamata qwarai da gaske,ya kuma taimaki rayuwarta sa shawarwari da kuma kulawa ta musamman irin ta likita,amma zance na gaskiya ita a yanzu kwata kwata babu wanu tsari ko maganar aure a ranta,batajin akwai wanda zata iya bawa filin zuciyarta ya shiga.
"Akwai lokaci"
"Ya ubangiji,ka nunamin wannan lokacin" taji ya fadi da confidence dinsa,saita sake masa murmushi kawai.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 42
Ana idar da sallar magarib da hijabin jikinta ta shiga falon inna,ta sameta itama ta kammala sallar
"Inna kinga su mufida shuru har yanzu"
"Zancansu nake nima a raina,ke nake jira kizo ki kamo min su a waya"
"To" ta amsa dashi,saita zauna ta fara lalube a wayarta,cak ta tsaya daga bisani,tunawar da tayi alameen inna keso a kira mata ba ya lamin na shekarun baya ba,sai ta sauke wayar tana dan duban inna,saboda bata da number wayarsa a halin yanzu,batason kuma ta fadi inna ta tunzura,saita miqe a fakaice,ta dauko wayar inna ta saka numbers din ta fara kira.
Dab da zata tsinke taji ya daga,muryarza fes,da wannan sautin mai nauyi da kuma taushi yayi sallama,saida gabanta ya fadi sannan ta amsa sallamar a hankali,shuru ya ratsa tsakani na aqalla sakanni goma,daga can bangarensa yayi shuru yana saurare,duk da zuciyarsa ta gama shaida masa wacece,amma ko afuska baiyi alamun da zai nuna ya gane din ba
"Wace?" Ya jefa tambayar kai tsaye,zare wayar tayi daga kunneta a hankali,wani abu yana mata susa a qirji,dama bai kamata ta kira ta kama wayar ta qanqame ba,saita miqawa inna tana cewa
"Gashi"
"Yauwa" inna ta fada tana karba,miqews tayi ta matsa gaban kayan kallo ta maida gaskiya plus wanda suke gabatar da shirin zamantakewa,sai da innar tace
"Gashi" sanna ta juyo ta karba wayar,tana shirin sakata a charge ya sadiqu ya shigo falon
"Inna kinjisu al'ameen shuru ko?"
"Eh yanzu muka gama waya dashi,ashe mota ce ta basu matsala a hanya"
"Haka yace wallahi,ya kirani"
"To Allah yakiyaye,ya kawosu lafiya"
"Ameen ameen.....me kuka dafa ne inna,inaso zan fita" yayi maganar yana kallon iman,kafin ta amsa masa sai kuma yace
"Yi sauri ki zubomin,na makara" miqewa tayi ta zuba ta kawo masa,yana ci suna hira da inna,har ya gama ya miqe zuwa dakinsu da sunan zaiyi wanka,iman din na kallonsa tanason tsokanarsa kan zance ya fara zuwa ne,saidai ganin yana sauri yasa ta barshi har ya fice.
Ba'a rufa awa daya ba sallamar mufida ta fara iskowa cikin gidan,ta shigo dakin innar bakinta a washe,tana janye da wani babban buhu da yafi qarfinta
"Inna mun dawo" ta fada tana sakin buhun gami da zubewa
"Lale maraba da mutanen jigawa tarin Allah" tsokanarta iman ta fara yi,daidai lokacin da muryar amin ta bayyana a tsakar gidan shima yayi sallama,gabanta ya fadi kamar ko yaushe,ta lumshe idanunta tana kiran sunan Allah,sai kuma muryar tasa ta gauraya data ya sadiqu,dukkansu suna yunqurin shigowa parlor din
"Kaima ance ka siya mota kaqi,ka tsaya wani noqe noqe,kullum baka da aiki sai shatar mota,kana zaune zan siya mota,ka zauna kallo,ana gama maganar gidansu yarinyar nan motar zan hara" ya sadiqu ya fada sanda suke shigowa falon,yana kan gaba,sanye da wata dakakkiyar shadda ruwan hanta,ya kafa hula abunsa yayi kyau sosai,shima sadiqun a wadan nan shekarun sai hamdala,saboda tuni ya daina aikin gyaran mota,ya fara sana'ar siyar da sabbin spare parts na motar,kuma samu yake sosai
"Zan siya,komai a hankali ake abinsa mr sadiq" ameen dake shigowa rataye da jaka a bayanshi ya bashi amsa,ya zarce da sauke idanunsa a fuskar iman wadda keta qoqarin gyara zamanta ba tare da dalili ba.
Ita ta fara masa sannu da zuwa sannan ta zame jikinta tabar dakin,duk sanda yake waje batajin sakewa kwata kwata,sai taji kamar ya cika dakin,bata iya wani qwaqwaran motsi.
Takusa minti arba'in a zaune gefan gadonta,suna musayar text da dr ahmad daya matsa mata ta tayashi hira,mufida ta shigo janye da wata leda ta miqa mata
"Gashi inji yaa baraka" ajjiye wayar tayi ta janyo ledar tana cewa
"Toooo,me muka samu?" Cikin ranta tana mamakin yadda yaa barakan ta aiko mata da saqo haka?
Mangoro ne mai kyau da yawa,wanda a wajen fatarsa kore ne,amma ta ciki ya nuna,irin mangwaron da take matuqar so,sai gyada mai bawo dame gishiri mai yawa kowacce a qulle daban,sai dinya da yawa.
"Kai duk wannan nawa ne?" Kai mufida ta gyada
"Tace sanda kuke zuwa da ya amin sune kayan da kika fiso" wani nauyi da kunya suka kamata,tabbas haka ne,a sanda take mutum kafin ta zama BUTULU KUFAN WUTA,ashe yaa barakan bata manta ba?,hakanan abunda tayiwa dan uwanta bai sanya ta gaza aiko mata da tsarabar ba?,wanne irin karamci ne har haka?.
Fita tayi da kayan ta adanasu,ta diba gwargwadon yadda zai isheta ta dawo daki.
*************Daga tsaye take cikin parlor din innar daga wajen bakin qofa, breakfast take hannu baka hannu qwarya saboda gab take data makara,sanye take da wata abaya saqar qasar dubai,wadda ya dace da jikinta,tayi mata kyau matuqa,saika zata daga wanca jinsin ta fito.
Ta jiyo takun takalmin daga tsakar gida,amma bata kawo komai ba saboda hankalinta bai wajen,sai da aka yaye labulen falon,haske ya cika falon tare da sassanyan qamshinsa sannan ta ankara da waye.
Al'ameen ne,cikin wasu irin suit masu matuqar kyau da aji,idanunsu suka sarqe cikin na juna,take bread din da take qoqarin hadiyewa ya tsaya mata a wuya,ta hadiyeshi da qyar,sai kuma qwarewa ta biyo baya.
Dagowa yayi a hankali daga qoqarin cire rufaffun takalmansa daketa qyalli saboda yadda suke fes babu ko digon qura a kai yadan dubeta
"Ki nema ruwa kisha kafin abinda kikaci ya dawo" ya fada a hankali cikin nutsuwar nan tasa,yana qarasa fidda takalman,ya tako zuwa cikin falon bakinsa dauke da sallama,daidai sanda inna ta bude labulen uwar dakanta ta fito tana cewa
"Wannan gaggawar da kike ba dole ki qware ba.....ba'a yiwa abinci haka ai.....aminu......ka fito?" Cikin girmamawa ya gaidata ta amsa masa cikin kulawa
"Ina kwana?" Ta gaidashi tana daukar jakarta,wani irin kunya ce ta kamata,bataso yaga kamar ganinsa yasa ta qware din
"Kin tashi lafiya?" Ya maida mata
"Alhamdlh.....inna na wuce" ta amsa masa hadi da yiwa inna sallama,saboda tana da tabbacin matuqar taci gaba da tsaiwa cikin falon bata isa ta yiwa idanunta shamaki da kallonsa ba.
"Ka zauna kaci wani abun mana" inna tace dashi bayan fitar iman,saiya girgiza kai
"Ana jirana inna,kuma yau zan fara shiga office din,bai kamata naje a makare ba,sannan ma kuma akwai abubuwan daya kamata ace nayi settling a yau din" addu'a sosai innar ta kwarara masa,ya miqe cike da jin dadi da kuma qwarin gwiwa ya fita,yana jin dadi da kuma farinciki mayalwaci cikin qirjinsa,ko babu komai,ya samu wadda ta zame masaadadin mahaifiya,yake kuma samun da ɗaɗan addu'o'in da yake ganin tasirinsu cikin rayuwarsa,lallai babu ko shakka,inna nada wani madaukakin matsayi da kima a idanunsa.
Already akwai mai napep dinsa,yana qofar gida yana jiransa,yana shiga ya gaidashi cikin girmamawa,sannan yaja motar suka fara gangarawa zuwa bakin titi.
Har sun gota yatsaidashi,ya sanyashi ya koma da baya,iman dince a tsaye tana duba agogon hannunta,sam bata kula da tsaiwarsu ba
"Shigo mu saukeki" muryar amin din ta cika kunnenta,ta daga kanta da sauri ta saukesu a kanshi,ba ita yake kalla ba sanda yayi maganar,wayar hannunsa yake latsawa,ta janye idanunta daga kanshi ta fara takowa a hankali ta shiga motar,sanna yaja suka fara tafiya..
Shuru ne ya ratsa motar,ba qarar komai saita iskar dake shiga tana fita,da kuma daddadan turaren jikkunansu daketa gauraya cikin motar,duk juction din da suka tsaya sai idanuwa sunyi musu ca,shi kam idanunsa nakan wayarsa baisan me ake ba,tana tajin qarar tura saqo na watsapp.
A junction din qarshe wata budurwa ta ratso ta tsakiyar motocin ta yiwa mai adaidatan magana tanaso ya sauketa a gaba,ya girgiza kai alamun a'ah,murmushi tayi,idanunta nakansu iman din
"Hala ango da amarya ka dauko ko?,nice couple,wallahi kun dace,tun acan baya na hangoku,kun burgeni sosai" dubanta sosai iman din tayi,yayi da amin ya daga kai yayi mata,sai aka rasa mai bata amsa,harta ratsa ta cikin motocin ta bace musu.
Tsaiwa maganar tayi cikin zuciyar iman din,zuciyarta ta dinga azalzalarta ta kalli yadda suka dace din ita da ya amin ta madubin motar tana qoqarin kaucewa, lastly dai daga qarshe haka zuciyarta ta rinjayi idanuwanta,takai dubanta ga madubin,cikij rashin sa'a ya daga kansa yana duban hanya saboda jin sun koma tafiya slowly......karaf idanuwansu suka hadu,cikinbl wani irin hanzari da waskewa ta kauda idanun nata. Qaramin sauti taji ya fita daga bakinsa,wanda idan har ta canka dai dai murmushi yayi mata,gabanta ya fadi,kada dai ace ya ganta,tun daga lokacin bata sake wani qwaqwaran motsi ba har suka sauketa yaja sukayi gaba.
Wunin ranar a makaranta babu abunda take tunawa illa wannan dan zaman nasu da sukayi a tare,wani lokaci sai taji kamar jikinta yana tashin qamshin irin turarensa ne,ranar gaba daya bata da wani kuzari sam a jikinta har aka tashi.
********Aiki sosai alamin ya kama babu kama hannun yaro,babban kamfani ne da suka bashi babban matsayi,kamfani ne dake kula da gine gine da kuma qawar gidaje,suna da rassa iri iri a fadin qasar nan,babban reshensu yana a china,albashi suka sanya masa mai tsoka,amma duk da albashin da zasuke bashi.....da baiyi niyyar yin aiki dasu ba,hankalinsa yafi karkata ga bunqasa harkar dinke dinkensa,kamar xasuyi fada da sadiq ka hakan,saidai daya zauna sukayi shawara da inna da malam,malam ni ya nusashe dashi alfanun karbar aikin,zaiyi amfani da albashinsa ya bunqasa wajen ba tare da yabar aikin ba,wannan shawarar tayi masa,ya kuma gamsu da ita dari bisa dari,don yasan cewa abinda babba ya hango,yaro ko yahau bushiyar rimi bazai hangoshi ba.
*******A hankali ta gyara yafen mayafin doguwar rigar da take jikinta,sannan cikin sanyi ta dauki tray din dake jere da abincinnasu ta soma takawa zuwa dakin nasu,don dai babu yadda zata yine,amma gaba daya batason wani abu da zai kawo kusanci ko ya sanya su kebe da ya amin din.
Idanunta ta lumshe tana zuqar iska sosai zuwa huhunta sanda ta tsaya qofar dakin,ko ina na jikinta kamar an zare masa laka,ta tabbatar ya sadiqu baya nan,yatabbata zance yake zuwa,don kuwa magana har ta fasu cikin gidan,a yau dinma yana can,saboa haka tana da yaqinin ameen dinne kadai cikin dakin,tunda ya dawo ba zata iya tuna sanda ta shiga kai masa abinci yana shi daya ba,yawanci ma a yanzu a falon inna yakeci,idan kuma a dakin nasu zaici,mufida ke tsayawa daga soro tayi musu knocking su karba ta koma ciki,to yau mufidan tana dan zazzabine,bata jin dadi sosai.
Sallama tayi daga bakin qofar dakin
"Shigo" taji muryarsa tarrr yana bata umarni,wani abune mai qarfi cikin muryar lamin din,wanda duk sanda yayi magana koda bada ita yake ba sai taji ta saukar mata da nauyi saman zuciyarta da wani irin yanayi mai wuyar fassarawa,bataso ta shiga din,bata qaunar hakan,saboda haka tayi kamar bata ji ba ta sake maimaita sallamarta
"Come in" ya sake fada daga cikin dakin,a yanzu kam idan taci gaba da tsaiwa yasan cewa tayi ne tana sane,bata da wani sauran chance illa kutsa kai zuwa cikin dakin,idanunta sauke a qas,saidai tana shiga natural sanyin da dakin yake dashi,da kuma mayen qamshin nan nasa yayi mata sallama.
Yana zaune saman daya daga cikin kujerun dake gefe daya a dakin,wandda tayi kyau sosai a mazauninta,saboda yadda dakin ya qara kyau fili da kuma qayatuwa,sanye yake da wata baqar jallabiyya bai gajeran hannu,wadda tayi masifar haska fatarsa,kamar wani balarabe cikin jinsin wadanda basu cika hasken fata ba,sumarsa na nan a kwance cikin tsafta da burgewa,kai zaka dauka ba shine mutumin da bai jima da dawowa daga office ba,wayace maqale a kunnensa,yayi relax cikin kujerar sosai,babu lallai ka iya jin abinda yake fada.
Bata yarda ta kalli sashen da yake ba,qarasa a hankali wajen da suka ware saboda cim abincin tana dora tray din
"Miss you too.....i will call you" kalmar da taji daga bakinsa kenan,wadda taji kamar zuciyarta zata tsinke ta fado
"Zo nan" taji ya fada cikin wata murya dake nuni da umarni kai tsaye,cak ta tsaya,sannan ta waiwayo a hankali,dai dai sanda yake sauko da qafafunsa qas tare da matsowa zuwa gaba kana ya zauna sosai.
*_Arewabooks link_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62beab3c93b638ade30a1fc7
_please follow me_
@HUGUMA
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 43
*_follow my account @arewabooks as HUGUMA,for latest pages_*
"Dage curtains din" ya sake fadi kafin ta qaraso inda yake,sai ta koma a hankali zuwa bakin qofar ta yaye labulen yadda ya buqata,waje ta bayyana tarwai,ta yadda duk wanda zaya wuce zai hangi cikin dakin,sannan ta tako inda yake,tana jin qafafunta kamar sun lanqwashewa,kamar ba zasu iya daukarta ba.
"Uhmmm,zauna a nan" ya fadi yana pointing mata wajen da yakeso ga zauna din,wajen ta kalla,a qa'ida yayi mata kusanci dashi da yawa,bata da yaqinin idan ta zauna kafin ga tashi zuciyarta ba zata fashe ko ta tarwatse ba,ko kuma wani abun bazai sameta ba,dole taja qafafunta ta zauna a hankali a wajen,saidai a matuqar takure da kuma dar dar
"Iman..." Ya kira sunanta da wani irin heavy sound,wanda banda ta riqe numfashinta da kyau ba shakka zata samun daukewarsa na wucin gadi,duk da haka bata tsira ba,sai daya haifar da wani yanayi na daban cikin zuciyarta
"Me yasa kike qoqarin canzawa?,ko kuma nace kika canza?" Ya dakata a nan,ya zuba mata idanunsa dake da nauyi da kuma dafi a kanta
"Yanzu meye hakan?,kalli yadda kika zauna?,dodo ne ni ko meye?,duk wani abu da yake cikin idanunki ina iya karantarsa cikin lokaci qanqani......,bcoz.....nine mutum na farko da zan gayawa duniya wace ke,idan don abunda ya faru ne ki aje wanna issue din a gefe,ya wuce har gaban abada.....inaso ki saka a ranki da zuciyarki,babu wata kalma data taba shiga tsakaninmu dake makamanciyar wannan,ki sawa ranki har yanzu ya lamin dinki ne,wanda bai gurbata alaqar da take tsakaninku ba......idan hakan shi ya haifar da wannan ciwon,ki manta dashi,ki dawo iman dana sani a baya,na sani......kina takura kanki kan abinda ya shude har abada.....ki canza ki kuma gyara,ran inna yana baci,idan kuma kikaci gaa da wannan silly behavior din......ranki zai baci" yana kaiwa nan hawaye suka sauko mata,hawaye masu dumi,wasu maganganun nasa sun dada maga,wasu kuma sun tashi hankalinta,sun kuma sakamata shakku,tare da wani yanayi na tsaka me wuya.
"Ehnnnnn.....idan kin gama kukan kya iya tafiya" ya fadi yana komawa baya,yayi relaxing jikin kujerar ya janyo wayarsa yana dannawa.
Cikin dauriya da juriya ta goge hawayen fuskar tata,sannan tayi magana cikin harshen dake nuna anyi kuka
"Kayi haquri,zan gyara"
"Da kyau,Allah ya tashemu lafiya" ya amsa mata yana ci gaba da danna wayar still,saita miqe,tana takawa a hankali har tabar dakin.
Ita kadai tasan me takeji a cikin zuciyarta,ita daya tasan yanayin da maganganunsa suka jefata
"Su koma kamar da?,kamar yaya lamin da iman din inna?,kamar wata alaqa bata taba hadasu ba,hakan fa yana nufin yankewar komai da komai a tsakaninsu kenan" wadan nan maganganun ta dinga juyawa cikin ranta,barci kuma ya qauracewa idanunta,tana jin wani suya cikin qirjinta,har sai bayan da dare yayi nisa sannan ta samu baccin yayi gaba da ita.
*******Cikin kwanakin taga abinda ya fada mata din a aikace,da gaske ya maidata iman dinsa tada,ya dawo da caring irin na yaya da qanwa dake tsakaninsu,saidai a wannan karon akwai jan girma a ciki,wani lokaci harda wannan dadadden miskilallen halin nasa,ya koyi yi mata fada idan tayi ba dai dai ba,ba kamar baya ba da kome tayi zai dinga qoqarin bata kariya a idanun mutane,akwai haduwar jini tsakaninsa da mufida,don haka 'yar gidansa ce ita din,yadda zaiwa mufida hakanan yake mata,babu wani banbanci a tsakani,tayi qoqarin ganin ta warware itama,ta ajjiye komai a gefe ta koma yi masa kamar daa,saidai akwai wani strong feeling cikin zuciyarta,mai matuqar qarfin da itakanta take kasa controlling kanta a yawancin lokuta,sau tari sai ta bude WhatsApp dinta ta ganshi a online,kota duba dp dinsa,duk da ba ma'abocin saka hotonsa bane,a dp din,duk wani movement nashi hakanan ta samu kanta da interest akai,saidai babu wani abu data gani na daban tattare da alamin din,face fsohuwar alaqar da take tsakaninsu zalla da ya sabuntata.
Rana daya ta kalli kanta a madubi taga tana ramewa,abunda ya bata mamaki,ta kalli kanta ta sake kalla,tasan akwao stress na karatu,amma koma behind it akwai wani abu da ake kira rashin sukunin zuciya.
Tun da bata da wani aboki ko qawar shawara saishi,a yanzun kuma batajin zata tunkareshi da wannan batun,abu me matuqar saka jin kunya ga duk wanda aka budewa karatun,bushira ce kawai tazo ranta,duk da suna haduwa a chart suyi hira da ita,amma a yanzu ba shakka tana buqatar ganinta,tasan cewa ita kadai ce zata bata gamsashshiyar shawara bisa amana da kuma sirri,wannan yasa ta kirata tun safe ta gaya mata tana zuwa,da yammaci tayi qoqarin gamawa inna komai,ta shirya tsaf cikin atamfarta riga da skert,ta dora babban hijabi me hannu da ya saukar mata har qasa ruwan makuba neat dashi abun burgewa,kalar ta farare ce,hakan ya sanya yayi mugun mata kyau,don ko ita data tsaya gaban mudubi ta gani,tana godewa Allah kan tarin baiwarwakin da yayi mata,babu wanda zai kalleta ko a mafarki yace ta taba aure,duk da auren a suna ne kawai,bai amsa sunansa ba.
Gayu da qamshi sun matuqar zaunar mata,don haka ko zama kayi sosai kusa da ita kana iya diban tsarabar sassanyar qamshinta,wanda sai kana gab da ita ne zaka jishi.
A parlor ta tadda ina ta shaida matan zata fita gidansu bushiran,bata hanata ba,bushira sananniya ce,sannan tana yawaita ziyartar iman din,ta kalli mufida dake bacci a kujerar falon inna
"Ga 'yar rakiyar tawa tayi bacci"
"Eh saidai ki maza kije ki dawo"
"Yanzu kuwa inna in sha Allah" ta amsa mata tana sanya plate shoes dinta daya dave dace da shigarta ta nufo waje.
Kamar ko yaushe cikin nutsuwa tsari da kamun kai take tafiya,duk da yadda idanuwa kan mata caa idan ta fito amma bata daga kai bare ta damu dasu,tasan ita din wace,ta kuma san mutunci da darajar kanta,cikin mintina qalilan ta isa gidansu bushiran.
Ta samu gidan ba kowa sai ita,tana ta wainar fulawa,wadda qaninta ya roqeta tayi musu shida abokansa,kujera taja ta zauna zata tayata
"A'ah,wallahi bakiga yadda kikayi kyau ba,kada ki bata jikinki da manja,rigimar alqasim ce kawai ya tsiri na musu waina,ni da nake karatun exams,kedai bari na saka miki kici kawai" saita zaro plate ta saka matan,tana ci tana bude mata flask din tana zuba wadda ta soyu.
"Naji kince akwai magana,tun dazu nake dakon shigowarki" ta tambayi iman din bayan ta gama ci,yanayin yadda fuskarta ya koma kawai ya gayawa bushira she's serious kan maganar daya kawota.
"Magana xamuyi dake bisa yarda dake da amincin da yake tsakaninmu,duk duniya ba wanda zan iya gayawa wannan maganar saike,na dauki tsahon darare da kwanuka ina qaryata kaina,saidai kuma kan nawa shima qaryatani yake,har kuma ya rinjayeni.....bushira na kamu da son ya alameen" ta qarashe maganar cikin wani rauni,har idanunta suna tara hawaye.
Tsoro mamaki ko razani ta tsammaci gani daga fuskar bushira,amma sai murmushi da nutsuwa akasin wadancan ababen ya bayyana,abunda ya bata mamaki,ta tsaya tana duban bushira.
A kalla minti biyu suna a haka sannan bushira ta magantu
"Na baki mamaki ko?,to ai hajiyata wannan maganar a bude take,ke kika yaudari kanki kika kuma ha'inci kanki,kin dade kinason ya alameen.....rudar kanki kikayi,da kuma salon taki qaddarar data jefo miki da bassam,ya rikita qaramar zuciya da qwaqwalwarki dake ginuwa a lokacin.....kika dauki son da kikewa ya amin kika bawa bassam,a zatonki bassam din kikeso,bayan kuma bashi kikeso ba......bassam ya taka sahun barawo ne kawai a hausance" dif iman din tayi,tana jinjina kaifin basira da hangen nesa irin na bushira,ta karanta tsaf abunda ta jima tana surantawa a ranta da tunanin yadda zata fito dashi.
"Me kike jira da baku koma bigiren da kike akai ba keda ya ameen a yanzu tunda kuna da dama?" Kanta ga girgiza cikin alhinantawa kanta
"Mun koma......amma ba irin bigiren dake kike hasasowa ba......na koma matsayina na qanwarsa ne kawai,yakuma gayan iya hakane buqatarsa"
"To shine me?,zama zakiyi kina kallo ya zama rabon wata?,ko bari zakiyi ya subuce miki,a wannan zamanin da nagarta tayi wahala,samun miji na gari yake neman zamewa diya mace garari?,idan zaki tashiga ki maida kanki zuciyarsa cikin siyasa......bazan boye miki ba,randa na sake ganin ya amin nima ya tafi dani wallahi,kawai don nasan ajiya ce ta amana shi yasa na basar kawai" dole bushiran ta bawa iman dariya
"Da gaske nake miki,ki qoqarin daidaitawa kafin kiji sold out" wannan karon dariyar iman din sai data fito,ta daki cinyar bushiran
"Wai sold out kamar kaya"
"Tabdi,irin ya alameen ai kayanne masu tsada"
Wannan maganganu da kuma tattanawa da sukayi da bushira ta dade tana juyasu cikin ranta,tana aunasu a mizanin dacewa da kuma rashin dacewarta,tabbas soyayyar al'ameen ta yiwa zuciyarta wani wawan kamu da batasan yaushe hakan ta kasance ba?,idan har zata budi idanu taga ya zama rabon wata ta auna ta kuma gwadawa zuciyarta zata iya jurewa?,bataga mafita kota ina ba,to amma kuma ta yaya zata dorashi akan irin mizani da saitin da bushira ke mata nuni?,akwai abubuwa masu tarin yawa dake sanya zuciyarta cikin kunya nauyi da kuma shakku duk sanda zata daga kai su hada ido da ya ameen din,a fuska take qoqarin maida komai ba komai ba.....kamar yadda ta gaya matan shi a nashi sashen haka yake,saidai ta sani abundan ya farun wani abune da zai matuqar wahala ya gogu a zahiri.
Zuwa yanzun zuciyarta na gaya mata kamar ya alameen din yafi qarfinta,tako ina qofofin samu da kuma na arziqi ne suke bude masa,sabon shafin wadata da arziqi wanda suka bayyana hatta da saman fatarsa,zaka dauka cewa ba cikin gidan nasu yake rayuwa ba,duk da cewa gidan nasu a yanzu a layin yana cikin sahun gidaje dake da kyau da kuma tsari,can qasan ranta zuciyarta tana rawa tare da kwana da kuma tashi da fargabar kada ya kamo zuciyar wata ko shi a kamo tashi.
Bai cika shekara da kama aikinsa ba kawai yazo da takardun gida,gidane me kyau da kuma tsari daya siyawa malam din,da sunan su tashi daga nan,a barshi a mazaunin makaranta,su kuma su koma sabon gida,da farko malam ya fara fada
"Yaya zakayi haka aminu?,wanne irin bahagon tunani ne wannan kayi?,kai da kake da fili kake kuma gini?,muke saka ran ku gama kai da sadiqun kuyi aure kwana kusa?" Lafazin auren da malam ya ambata shi ya sanya iman miqewa tsam ta fara takawa tabar wajen,saboda ambaton kalmar dai dai yake da bugun guduma a tsakiyar kanta,batasan ya suka qare ba,daga bisani dai ta tsinci maganar tabbatuwar tashinsu,ta fara hada kayanta kamar yadda taga kowa yanayi,ranar wata alhamis bayan sallar magrib suka bar unguwar,bayan sunyi sallama da kowa.
Ginine me kyau irin na zamani,gidane madaidaici,wanda bai cika girma sosai ba,hakanan ba qarami bane,kamar gidan amarya,an tsara komai bisa tsari da kyau da kuma burgewa,duk wanda yazo sai ya yaba gidan,hakan 'yan rakiya da sauran 'yan uwa suka dinga fatan alkhairi tare da fatan tarewarsu a sa'a.
***********"Wayyo" tadan fada can qasan maqoshinta,tana miqewa daga durquson da tayi,har yau dakunansu basu gama zama ready ba,gyaran gidan suketa yi,wuni na uku kenan,saidai zuwa yau alhmdlh komai ya kusa kammala.
Ja da baya tayi tana kallon kanta a sabon madubinta,ta fito tar,duk da cewa batayi wanka ba amma ba zaka iya gane hakan ba,tana sanye da wata doguwar riga me zubin A shape,ta wani black cotton material ce mai touches na white,kanta kuwa siririn mayafin rigar ne ta daure kanta dashi,amma qanqantarsa ya sanya baifi rabin gashinta ya rufe mata ba.
Kishirwa take ji,don haka ta ajjiye sabbin kwalaben turarukan data siyo bayan ta gwada fesa daya,ta taka a hankali zuwa parlor din gidan don ta dauka ruwa a fridge tasha,kasancewar yau garin akwai hucin rana babu laifi,duk da cewa yamma liqis ne yanzun.
Sai data shaqi qamshin dake parlor din na sabunta da kuma turaren da suka kunna wanda tuni har ya gama cinyewa,saidai qamshinsa yana nan,ta qarasa fridge din ta bude ta dauko pure water guda daya ta bula ta fara sha,sannan ta juyo a hankali da nufin komawa dakinta.
Tsaye yake cikin parlor din,sanye da suit dinsa,hannunsa riqe da brief case,bata tsammaci ganinsa ba ko kadan a irin wannan lokacin,wannan yasa ruwan da take sha ya zarce mata take kuma ta qware,ta hau tari sosai.
https://arewabooks.com/chapter?id=62beaa7c93b638ade30a0e93
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 44
"Ya salam,garin yaya?" Ta furta sanda yake qarasowa inda take tsayen,kasa daga kai tayi bare ta bashi amsa,tana jin haushin kanta na yadda duk sanda zasu hadu sai tayi misbehaving,batason taci gaba da yin abubuwan da zasu janyo ta bada kanta
"Sannu" ya fada yana ja da baya kadan,kafin takai ga amsawa yace
"Ina inna?"
"Tana daki" ta amsa masa ba tare data iya daga kai ta dubeshi ba,qamshin turarensa ke haifar mata da wani abu cikin zuciyarta
"Qyaleta" ya fada yana juyawa zuwa qofar da zata fiddashi daga parlor din,ta kuma sadashi sa sassan su shida sadiqu,a sace tabi bayansa da kallo,kullum sake kyau yake da kuma sake zama wani na daban,cikakken namiji me aji,hutu jin dadi da kwanciyar hankali na sake bayyana muraran,tun daga kan fuskarsa har saman fatarsa.
Kadan ya rage ya kamata sanda take kallonsa,cikin wani irin hanzari ta dauke kai lokacin da ya waiwayo
"Me kuka dafa?" Yayi mata magana kamar yadda ya saba yi mata ayanzu,cikin dakiya shariya wani lokaci tare da burbushin halayyarsan nan miskilanci
"Tuwo ne" sai yadan murza goshinsa da yatsunsa
"Zan iya samun wani abun nadaban,wanda bazai wuce rabin awa ba" kai ta gyada masa,sai ya juya yaci gaba da takawa,maimakon itama ta koma dakin,sai kawai ta zarce kitchen,a yanzu bata da burin daya wuce yace yana buqatar abu kaza,wanda ita kuma a yanzu ba kasafai hakan ke hadasu ba.
Cikin minti talatin din da ya buqata ta gama shirya komai,ta dauki wayarta ta laluba number dinsa,sai datayi kamar zata kira sai kuma ta fasa,kada ta zaqe da yawa,don haka ta dawo parlor tayi zaune kawai bayan ta kunna tv din dake aiki cikin parlor din,hannunta riqe da wayarta tana duba wasu hotuna da sukayi biki a nijer watannin baya da suka wuce.
Tun kafin ya qaraso qamshinsa ya cika wajen,abinda ya qara gudun zuciyarta kenan,tana ga qoqarin hana kanta daga kai ta kalli qofar,wani sashe na zuciyarta kuma na azalzalarta,a haka sallamarsa ta cimma parlor din lallausar muryar nan tasa.
Sanye cikin wani lallausan farin yadi mai shara shara,wanda har kana iya hango singlet dinsa ta ciki,Hannunsa daya saye cikin aljihunsa,daya hannun kuma yana amsa waya dashi.
Fadin yayi kyau ma bata baki ne,wani sassanyan kyau mai tafiya da aji da kuma nutsuw,sumarshi tasha gyara sosai,lallai ta yarda ameen data sani a yanzu ba shine alameen din data sani a baya ba,komai ya saka yi masa kyau yake,ado mai cike da tsari da tafi da hankali.
Karamin dining da aka sawa innar a parlor wanda taketa mita akanshi ya nufa,har yanzu wayar yake amsawa,yayin da iman din ta gaza tashi daga inda take zaunen,saboda ta tabbatar idan taje din sai tayi wani abu da ba dai dai ba kamar yadda ta saba.
Parlor din ya dauki shiru bayan ya gama wayar,sai qarar plate da spoon dinsa daya fara cin abincin bayan yayi serving kanshi,cikin nutsuwa yake kai abincin bakinsa,fitowar inna ta katse shurun da ya wanzu a wajen,ta qarasa inda yake tana tambayar yaushe ya shigo
"Tun dazu inna,har na shirya zan sake fita ma,nasan aiki kike shi yasa nace a barki" tana daga kan kujerar amma kunnenta na wajen,fiye da rabin hankalinta yana kan hirarsu,tunda ya shigo din hankalinta ya gaza kwanciya,shigar da yayi ta tabbatar mata fita zaiyi,abun tambayar shine ina zashi da yammacin nan lis?.
"Don Allah inna idan sadiqu ya shigo kice ya jirani,na kira wayarsa ban sameshi ba"
"To shikenan,a dawo lafiya"
"Ya ameen a dawo lafiya" mufida itama ta fada,dole itama tabi sahu,ya amsa ba tare daya duba sashenta ba ya fita.
Kamar ya fita da dukkan wata walwala tata da kuzari,sai taji duk zaman parlor din bai mata dadi,wayarta na a hannunta tana chart,saidai kuma a hankali ta daina fahimtar abunda take dubawa cikin wayar
"Na zuba mana abinci yaa iman?" Mufida ta tambayeta,sai ta kashe datar tana kallonta
"Banajin yunwa yanzu kam,ci abincinki,sai zuw anjima" tayi maganar tana zamewa saman doguwar kujerar falon,bayan ta saka mufida ta miqo mata remote ta canza tasha.
Duk da kallon da take yadan dauki hankalinta,saidai hakan bai hanata duba agogo ba duk bayan wasu mintuna,suna nan zaune a parlor har sanda malam ya shigo inna tayi wajensa,falo ya zama daga ita sai mufida,da yake yarinyar mayyar kallo ce,takwas tara goma duka tayi a idanunta,babu alamun shigowar ameen din,a hankali ta dinga jin zuciyarta tana takurewa waje guda,wani abu ya tsaya mata a wuya,a hankali zuciyarta ta fara yi mata zafi,saita lumshe idanunta kawai tana sauraren bugun zuciyarta.
Sallamarsa ce ta ratsa tsakar gidan har zuwa parlour din,saita maida idanunta ta lumshe,tana jiyoshi lokacin da yake shaidawa inna ya dawo,sai kuma muryarsa cikin taushi yake kiran mufida wadda ta fara gyangyadi,bata da dogon bacci,hakan ya sanya yana kiranta ta miqe ta fita waje,saita buda idanunta tabi mufida da kallo har zuwa sanda yarinyar ta dawo parlorn.
Dauke take da wata baqar leda mai adon zaiba,bakinta har kunne ta fara magana
"Ya iman,tashi ki gani" qarasowa tayi gaban iman din ta tsugunna ita da ledar tana qoqarin ciro kayan ciki
"Ya ameen ne ya bani,zance yaje yau,yacema tace tana gaisheni" tabbas inda mufida tasan yanayin da zata shiga da ba zata bata wannan labarin ba,gaba daya tun daga cikin kwanyarta zuwa tafin qafarta kamar an xuba mata kiyashi haka ta dinga jin wani abu,kamar ana yamutsa kwanyarta,tana daga kwancen ta kasa amsawa mufida kamar yadda ta kasa tashi,da idanu tabi kayan da yarinyar ke fitowa dasu da idanu,pepper chicken ne sai meat pie da samosa,sam bata fahimtar abunda mufida ke fadi,taga dai tana miqo mata kayan bayan ta kaiwa inna ta dawo,abu daya ta iya shine girgiza mata kai,sannan ta kira sunan Allah can qasa ta yunqura ta sauke qafafuwanta qasa,ta fara takawa a hankali zuwa dakinta,saidai tana jin kamar qafafuwanta ba qasa suke takawa ba,kamar gangar jikinta ba zata iya kaita daki ba.
Tana shiga ta murzawa dakin nata key,ta kuma sulale a qasa a hankali ta saki wani kuka mara sauti,saidai mai cin zuciya da kuma gangar jiki gaba daya,don gaba daya ta cure waje daya,jikinta kuma ya kama rawa,sanyi take ya lullubeta,saita sake qanqame waje daya,ta tura kanta tsakanin cinyoyinta.
Wani irin zafi zuciyarta keyi,wanda ya sanya hatta da hawayen dake fita a fuskarta masu zafi ne,indai har da gaske mufida take,indai har ameen ya fara zuwa zance,hakan na nufin ya fara son wata?,hakan yana nufin zuciyarsa ta fara qaunar wata ba ita ba?.
Ya ilahi zata iya jurewa?,zuciyarta zata iya dauka?,bata da tabbas.....bata da tabbacin hakan,amma ta sani cewa gagarumar matsala da damuwa ke fuskantota,ta yaya zata tunkari ameen da batun soyayyarsa?,ta yaya zata bayyana masa abunda take ji a zuciyarta,ta yaya zata gaya masa tun da can da yanzu shine dai cikin zuciyarta?,shine ya mamaye dukkan wani sashe na zuciyarta da kuma rayuwarta?,saita xame a wajen ta kwanta gaba daya saboda yadda kanta yake sara mata,bata damu da sanyin da yake busowa ta wajen ba.
Sau biyu mufida tana knocking qofar amma saidai tayi mata gyaran murya,daga bisani data gaji bata qara bugawar ba.
Tayi kuka a ranar iya son ranta,kukan da sai daya sanya taji kanta kamar an saqala mata dutse saboda nauyin da yayi mata,batasan yawan lokacin data dauka kwance a wajen ba,illa dai daga bisani taja jikinta zuwa saman gadonta ta kwanta da qyar,jikinta saboda zafi kamar ana hura wuta,a zahiri kuma wani irin sanyi takeji sosai a jikinta.
Tayi sa'a sallar asuba bata kubce mata ba,saidai tana rawar dari tayi alwalar tazo ta tada sallar,bayan ta idar saita bude key din data sakawa dakin,ta dawo ta kwanta tana sake curewa sosai,saboda azabar zazzabi da sanyin dake ratsa mata qasusuwa,ta lumshe idanunta,har yanzu tana jin qunci da zafi da zuciyarta take mata.
K'arfe bakwai mufida ta shigo dakin
"Yaa iman....ya iman" baccin wahalar daya fara daukarta ya katse,sai ta bude idanunta a hankali tana duban yarinyar
"Ki fito,kizo kiga motar da ya lamin ya siyo,haddadiya,yanzu yaje ya daukota,kinga yadda tayi kyau kuwa?" Taci gaba da bata labari,ba tare data lura da yadda idanunta suka sauya ba
"Ki taso ki gani inji inna"
"Bazan iya tashi ba mufida" cak ta tsaya tana kallonta sosai,ta matsa kusa da ita
"Jikinki hucin zazzabi yakeyi yaa iman,dama baki da lafiya?,sannu......bari.naje na gayawa innar" mufidan ta fada fuskarta cike fal da damuwa,sai ta juya da hanzari ta fice daga dakin.
A 'yar qaramar farfajiyar gidan motar ke fake,inna sadiqu da kuma lamin din kansa suna tsaye jikin motar,sadiqu na qoqarin budewa ya shiga ya kunnata,saboda yace yanason yaji ya kafiyar engine dinta yake kamar yadda aka tabbatarwa da lamin din,motace da bata cika girma ba,amma sai azabar kyau da daukar ido,ta tsaru sosai,duk wanda ya kalleta sai ta bashi sha'awa.
"Inna....inna" mufida ta fara kiranta kafin qaraso,dukka sai suka waiwayo
"Inna wallahi bata da lafiya,bakiji zafi a jikinta ba" sake murfin motar lamin yayi ya maida hankalinsa ga mufida dake bayani,sadiqu kuwa tuni ya shige cikin motar yana qoqarin kunnata.
"Dama bata da lafiya amma ta shige daka ta kwanta,a gidan nan dama ita da aminu ke wannan shashancin banzan......,kice mata ta fito taci abinci ta samu magani tasha" amsawa mufida tayi ta koma ciki,babu jimawa ta dawo
"Inna ta kasa tasowa fa" yarinyar ta fada fuskarta cike fal da damuwa
"Ko zaki duba ki gani inna,ciwo baya yiwa iman ta dadi tun ba yau ba" lamin ya fada,fuskarsa na nuna alamun kulawa
"Zan iya dagata ne,idan ka bibiya langwai ne fa kawai irin nata" ya sani sarai kara kawai inna keyi,don haka saiya qwanqwasa baqin glass din motar,sadiqu ya sauke.
Yana qoqarin gaya masa engine me kyaune sosai ya rigashi yana cewa
"Ka shiga ciki ka duba iman mana"
"Me ya sameta kuma?" Ya tambaya yana dan yamutsa fuska
"Kamar zazzabine haka mufida tace"
"Master qyaleta,tasowarma ba zatayi ba sai an dubota?,ita har yanzu kallon yarinya takewa kanta" qas yayi da muryarsa yadda inna baza ji ba
"Ni kakeso naje na fiddota?,me hakane sadiqu?" Fuskarsa ya kalla saiya sheqe da dariya,ya kunce seat belt din daya daura ya fara qoqarin fitowa yana cewa
"Inason wannan mood din naka,idan ka zama serious ko?,u are looking wani boss....banda ni dinma nine tsoro zaka dinga bani kenan ko?" Murmusawa yayi kawai da salon murmushinsa mara zurfi,ya ciro kansa yana amsa mishi
"Kai dinne wani lokaci kamar na makeka,bakasan me ya dace ba kwata kwata?" Shidai ciki yayi yana cewa
"Sai kayita yi kuma,da wasu shanyayyun idanunka a wajen" murmushi ya bishi dashi,hakan daya fada sai ya tuna masa da quruciyarsu,sanda yake tsokanar iman dame idanun mage,idan shi din ya shigar mata kuma,shima ya karbi rabonsa dame shanyayyun idanuwa.
Minti kusan goma ya bayar da rata saboda ya basu daman yin duk abinda zasuyin,sai ya fara takawa zuwa cikin parlour din,jikinsa sanye da baqar jallabiyya me sulbi,ya boye hannayensa cikin aljihunta.
Saman daya daga cikin kujerun parlour din take zaune,ta dafe kanta da tafin hannunta daya,wandata dogare hannun nata da gwiwar hannunta a hannun kujerar da take kai,dan kwalinta me sulbi daya janye baya saboda sulbinsa da santsin gashin kanta ya bayyana gaban gashinta sosai.
Yana shiga inna na fitowa daga kitchen
"Zan kintsa dakin malam,idan ruwan yayi dumi ki gwadawa mufida ta sauke miki,ki samu kisha kiyi wanka ko zakiji qwarin jikinki,amma da wayonki kina zaune da ciwo,ko kamar mufida yanzu ba zata zauna ba" ta juya ta fice tana qananun mita.
Tabbas taji shigowarsa da tsaiwarsa a wajen,koda bataji ba qamshinsa data riga ta haddaceshi ya riga ya gama gaya mata wanzuwarsa a wajen,amma tana sane taqi waiwayowa,bataso ta juyo ta kalli idanun nan masa masu wani irin qarfi da kuma tasiri a tattare da ita,batason ta juya su hada idanu har yaga raunin da ya mamayeta.
Tana jinsa sanda ya tako zuwa side din da take,sai ta zabi sauke qwayoyin idaunta zuwa qasa,har zuwa sanda ya samu mazauni dab da qofarsu ta kitchen,ya zauna hannun kujera
"Ina kwana" ta gaidashi da dasashshiyar muryarta
"Lafiya ya jikin?"
"Da sauqi"
"Ma sha Allah" ya amsa yana janye idanunsa daga kanta bayan ya mata duba guda daya,koda batace komai ba...ko bai kalleta sosai ba ya san jiya zuwa yau din da gaske taji jiki,cikin gidam yafi kowa iya karantar ciwonta.
Waiwayawa yayi inda mufida ke zaune yace ta duba ruwan yayi zafi,ba jimawa ta dawo ta amsa masa,sai ya miqe da kansa ya shiga kitchen din.
Farin ruwa inna ta dora,ya laluba da kansa ya nemo kayan qamshi ya watsa a ciki,ya bari ya tafasa sannan ya hada tea din ya bawa mufida takai mata,shi kuma ya dora wani ruwan ya tafasa farin ruwa yadda ya saba,ya juyeshi a mug,ya fito dashi a hannunsa yana jiran ya huce zuwa matakin dumi yasha yadda ya saba.
Idanunta a lumshe take kurban tea din,zafinsa na ratsawa sassan cikinta,kamar wadda ke shan magani haka take jinsa,batason yiwa inna musu ne kawai,ya qarasa ya rage fankar parlor din,dai dai sanda wayarsa ta fara fitar da wani daddan busar sarewa.
Hannunsa ya sanya a aljihun gaban rigarsa ya zaro wayar
"Morning.....how was your night?" Abunda ya fadi kenan,sai yayi shuru yana saurare. Ci gaba tayi da riqon cup din,ta kasa ci gaba da shan tea din,cikin rashin sa'a ta saci kallonsa,murmushi yake fitarwa saman fuskarsa,koda batasan wanda ya kirashi ba tayi hasashen hakan,saita sauke kanta,ciwon kan nata yana sake qaruwa
"Ba wani labari.....gaskiya zaiyi wuya,autarmu ce babu lafiya" batasan me akace masa ba taji dai yace
"Ok....bye" ya katse wayar ya saka a aljihu,shuru ya kuma ratsa wajen,ya maida hankalinsa ga ruwansa hankali kwance yan auna zafinsa,jin bai huce ba har yanzu,saiya fara yin hanyar barin parlor din
"Kiyi qoqari ki shirya muje kiga likita,ba'a zama da ciwo haka nan,Allah ya sawwaqe" bin bayansa tayi da kallo ba tare data shirya ba,hawaye na tara kansu zasu biyo kuncinta,yaushe ta fara wannan dakon?,yaushe kuma zata saukeshi?,wanne irin qoshin wahala ne ya sameta haka?,sai tayi hanzarin dire cup din,ta kuma miqe da hanzari zuwa dakinta duk da yadda kanta yake sara mata,don batason tun a nan wajen hawayen su fidda kansu.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 45
Duk yadda taso kaucewa tafiya asibin tare dashi bata yiwu ba,saboda bata da wata hujja da zata bayar na aiwatar da hakan,tafuyarsun tare tasan babu abinda zata haifar mata illa fama mata wani tabo da miki dake tsaka da ciwo da kuɗa,yake kuma jan ruwa mai zugi cikin tsokokin zuciyarta,haka nan ta shiga tayi wanka,ta shirya kanta cikin doguwa riga saqar k'asar turkey,wadda take a bude sosai me hannun roba,two colors brown da baqa,tayi mata kyau sosai,duk da yadda fuskarta ke cikin yanayi,a haka idan ka kalla zaka zaci straight skart ce daga qasa sama kuma ta dora baqar half gown,da mayafin rigar ta yane kanta ba tare data tsaya rolling ba,ta saka wani black plate half cover shoe,wayarta kawai ta fito.
A parlor ta yiwa inna sallama ta fice,tun daga qofar falon ta hangi mufida,ta shirya tsaf abunta,anata murna zaa fita da ita.
Ta maida idanunta kansa,duk da bayansa kawai take iya hangowa amma sai daya haifar mata da faduwar gaba,shaddace a jikinsa me tsada ko a idanu,amma an mata dinki yarbawa,iya gwiwa mai gajeran hannu da manyan aljihu hagu da dama,sai dogon wando,shima half cover ya saka irin na maza mai asalin kyau da tsadan,daga nesa kadai kana iya gane tsaftarshi qwarai bare ka matso kusa dashi kayi arangama da sassanyan qamshinsa,ganin yana qoqarin juyowa sai ta dauke kanta zuwa wani sashen daban....kafin ta qaraso har ya bude qofofin motar,da kansa ya budewa mufida front seat yana tsokanarta,tana murna kuwa ta shige,ya maida ya rufe ya zagaya nashi seat din ya shiga,daidai sanda iman din itama ta shiga baya.
Bismillah yayi ya tada motar,yayi reverse sannan ya daidaitata cikin layin suka dauki hanya.
Hirarsu suke shida mufida abinsu,kamar ma babu wani cikin motar sai su,kanta yana jingine da murfin motar,idanuwanta a lumshe,duk wata kalma ko harafi da zai futa daga bakinsa tana saurare,duk wata magana da zaiyi mai ma'ana ce,wadda ke nuna zallar hankali tare da nutsuwar wanda furucin ke fita daga bakinsa,da alama ita kanta yarinyar tana ji dashi sosai,tana kuma jin dadin hirar tasu,cikin excitement take bashi amsa,duk da ba cikin lafiyarta take ba,amma jirar tasu saita dinga burgeta.
"Akwai asibitin da kike zuwa inji inna,meye address din?" Ya fada yana karkata akalar motar tashi zuwa babban titi,ta cira kai a hankali,tana mamakin yadda ya iya tuqi haka cikin nutsuwa da qwarewa,ta dade da saninsa,shi ba mutum bane me karban aron abun hannun abokai,tun a wancan lokacin akwai abokansu da yawa dake da mota,babu yadda basuyi dashi yazo ya koya ba ko ya dinga aran tasu amma yace sam,zaman wajen dinkinsa yafi masa wannan yawace yawacen.
Hakan kawai taji batason kaishi asibitin,amma tunda ya riga da yasan nan din take zuwa ba yadda zatayi,a hankalibta fada masa sunan asibitin,tayi zaton zai tambayi hanya sai taga yaci gaba da hirarshi,tafi tafi sai gasu a asibitin.
Cikin nutsuwa yayi parking,ya kashe motar yana fadin
"Alhamdilillah" ya zare belt dinsa ya fita ya budewa mufida qofa.
Tabbas son yara cikin jininsa yake,had yanzu kuma bai barshi ba,daga yadda yakewa mufidan zaka gane hakan,ta tabbatar matsayinta mufidan ke shirin hawa,gurbinta take nema mayewa,ta kalli yadda yake riqe da hannun yarinyar,sai taji wani abu ya taba ranta,dab da zasu qarasa entrance na asibitin ta danyi kiranta,bai juyo ba amma ya zame hannunsa daga nata,sai yarinyar ta tsaya shi kuma yayi gaba,ta qarasa ta kama hannunta,sannu tayi mata,ta dauka ko tafiyar ce bata yi mata dadi shi yasa ta kirata ta tsayata.
Tafiyar tasu ba daya bace koda lafiya take bare yanzu da bata jin dadi,don haka kafin ta qarasa har an fidda file dinsu yana biyan consultation fee
"Hajiya iman....wani aure kika qara ne?,gaskiya kina da sa'a,duk mazanki babu na yarwa,harma wannan yafi wancan kyau ma sha Allah,duk da kema ba baya bace,shi yasa kike samo irinsu" wata nurse halima ta fada,irin matan nan ne masu barkwanci da kuma shegen surutu,kafin iman din tace wani abu ta sake duban alameen
"Yallabai inafa tayaka murna,ka dace da mace gaskiya" ta gefan ido take satar kallonshi tana son taga ya yanayinsa yake,saidai bata gane komai ba,hasalima sabgarshi yake da wayarsa kamar ma bay wajen
"Wata nawa ne cikin?za'a saka jikin record din kadin nayi miki bp da kuma weight dinta yallabai" sai a sannan ya daga kai ya dubu nurse din,tun asali bayason mace me yawan surutu shi kam,ko don ba kowanne lokaci ba kuma da kowa magana ta cika damunsa ba,ya tabbatar da sadiqu ta samu saidai ya matsa ya basu waje
"Sorry madam,ba matata bace,ba awo tazo ba,just tazo ganin likitanta ne"
"Ayyah sorry,kuyi haquri,dr ahmad ne,yana ciki ma,amma akwai mutum kusan shida a gabanku,idan sun fito sai ku shiga" bai bi ta kanta ba ya fito da kudin ya ajjiye mata a gabanta,ta dauke ta fara rubuta musi receipt ta saka a file din nasu.
Mabanbantan wurare suka zauna suna ci gaba da hirarsu da mufida,har zuwa sanda layin yazo kansu.
Shine a gaba suna bayansa,da sallama ya shiga,dr ahmad na rubuce rubuce kan wani file ya daga kai yana amsawa,har zai maida kansa ya hangi shigowar iman din,hakan yasa ya ajjiye biron da yake rubutu dashi,murmushi kwance saman fuskarsa ya miqe tsaye,hakan ya sanya alameen waiwayawa ya dubi iman din.
"Bismillah,ga wajeku zauna"yayi musu izinin zama bayan sunyi musabaha da ameen,mufida ma ta gaidashi,ya amsa mata cikin sakin fuska.
"Yaya?,jikin ne?" Dr ahmad ya tambayeta cike da kulawa,ya tattara dukka hankalinsa da nutsuwarsa a kanta,kai ta gyada a hankali saboda jin da take kamar zai cire
"Subhanallah" ya fada adan rikice
"Jikina ya bani dama,tunda nayita kira jiya babu amsa,haka tex ma......garin yaya haka ta faru hajiya?" Ya sake tambaya fuskarsa a narke cikin matuqar kulawa,abunda ya sanyata jin wani iri,ta daga idonta a hankali zata saci kallon alameen dake tsaye,hannayensa duka zube cikin aljihun rigarsa,tunda suka shigo dama bai zauna ba,yana jingine da bangon office din,yayi crossing legs dinsa.
Taci sa'a tsimammun idanuwansa suna kanta shima,suka hada idanu,sai ya miqe ya tsaya sosai bisa qafafunsa yana cire hannayensa daga aljihu ya maidasu qirjinsa ya harde,cikin wata qasaita yayi magana
"Eheenn....ki bude baki ki masa bayani,ko kuma na baku space,tunda akwai sirri tsakanin likita sa patient ko?" Ya fada a hankali yana raba bayansa da bangon,sannan ya fara takawa,murmushi dr ahmad ya saki
"Kawai dai naga alama tana tsoron yayan nan namu,but she can explain ai ko a gabanka dinne"
"Kada ka damu abokina.....idan kun gama ina waje" yayi maganar yana sake bashi hannu,sannan ya nufi qofa,mufida ta tashi ta biyo bayansa,sai ya dakata yace da ita
"No,ki xauna ku fito tare"
"To" ta amsa masa tana komawa ta zauna.
Wani abu mai tauri ne ys tsaya mata a wuya,kunnuwanta na jin takun fitarsa daga office din,wato ko oho?,bai damu da ita ba?,baya kishinta kenan,har zai iya fita ya barta da dr ahmad din,bayan ta tabbatar da duk wanda yaga reaction na dr ahmad zai gane cewa akwai wani manufa mai qarfi a zuciyarshi dangane da ita?.da gaske babu komai a zuciyar ameen a kanta ko kuwa me?,yana son tabbatar mata ta fita daga kansa?.
A dabarance ta janye idanunta tare sa sauke ajiyar zuciya,ta maida ga dr ahmad daya taso daga seat dinsa,ya dawo kujerar dake opposite dinta,bayan ya turata baya kadan,cikin sanyin murya yake mata magana
"Meye damuwar?,can you share it with me?" Yayi tambayar yana kallonta,sanya nata idanun tayi itama cikin nasa,tana karantar damuwa da yayi qarara da lamarinta,sabanin alameen din,da bata tsinci kowanne sauyin yanayi dangane dashi ba,illa dai zallar nuna tausayi,wanda dama ko ba'a kanta kadai ba,shi mutum ne mai tausayi,musamman ga na qasa dashi
"Banaso ki koma yanayin da kika baro a baya,ina fargaban komawar taki,saboda babu lallai abun yazo da kyau,kada ki sanyani yin asarar da ban shiryata ba" idanunta ta dauke daga kansa,tana jan numfashi tare da sauke ajiyar zuciya,ta maida bayanta jikin kujera ba tare datace komai ba.
Wayar land line dame office din ya janyo,nurse ya kira kamar yadda ta saba don tayi mata awon BP,ya maida wayar ya ajjiye yana tattara nutsuwarshi a kanta.
Tunda suna doso wajen hankalinta ya dauko ga ameen,hannunsa riqe da wata leda mai dauke fried plaintain,guda daa kuma yana hannun mufida tana ci,zuna zaune daga saman motar tashi,da alama labari take bashi kamar yadda ta saba,fuskarsa na fidda wani qaramin murmushi,yayin da yake dan cilla qafarsa kadan.
Yanayin yadda yayi fresh da kuma yadda motar ta dace dashi dole ya dauki hankalin kowacce mace,komai isa kyau da kuma taqamarta,don babu abinda baya dashi wanda zaija hankalin,kwarji na musamman yake dashi,ita kanta tana mamaki wani lokaci, totally ba lameen din shekarun baya bane wannan,wani rauni taji yana cika zuciyarta,tana ji a jikinta alamun faduwarta kan samun soyayyarsa da rashin nasara dake tunkarota.
A hankali ya sauka daga saman motar,ya ajjiye abunda ke hannunsa,fuskarsa a sake ya miqawa dr ahmad hannu suka sake musabaha
"Kun gama dr"
"Mun gama yayanmu.....Allah yasa na canki dai dai" murmushi kawai yayi masa ba tare daya amsa ba
"Don Allah ayimin alfarma a kulamin da ita,akwai damuwa cikin ranta dakeson tada ciwonta" sauke idanunsa yayi akan iman din dake gefe guda,sai ya ciro key din motar daga aljihunsa yana dauke idanunsa daga kanta,sannan ya dannan ya bude musu motar yana cewa
"Ku shiga ciki ku jirani". Sai daya tabbatar sun shiga sannan ya maida hankalinsa ga dr ahmad
"Thank you Dr,amma kuma...wanne damuwa ne haka?"
"I tried to get the information daga gareta amma bata gayamin komai ba,please....kune kuke da kusanci sosai da ita,kuyi qoqari wajen relieving mata damuwarta"
"Ok" ya amsa masa a taqaice
"Can i say goodbye to her?" Ya tambayi alameen,sai ya daga kafadunshi yana takawa zuwa gaba
"Why not?"
"Na gode" ya fada shima yana biyo bayansa.
Tana jinsa ya buda motar ya shiga,saidai bata dago kanta ba,idanunta naga yatsun hannunta tana murxasu a hankali,sosai qirjinta yake mata zafi,kalmar
"Hajjaju" ta shiga kunnenta saitin window din da take zaune,ta daga kai ta kalli dr ahmad dake mata murmushi,a hankali kuma ta saci duban alameen,sai taga wayarsa ma yake qoqarin sakawa a charge
"Allah ya bada lafiya,an hanani address bare nazo nayi dubiya ko?" Murmushi ta fitar na yaqe,wanda bahaushe yace yafi kuka ciwo
"Shikenan,hope to visit you soon,sai munyi waya.....,yallabai.....godiya nake" ya fadawa alameen
"Don't mention it" ya amsa masa,sai ya kunna motar abunda yasa dr ahmad ja baya kenan yana kallonsu har suka fice a asibitin.
Ajiyar zuciya ya sauke yana komawa ciki,har ga Allah yana bala'in son iman din,tun farkon zuwanta asibitin,a sannan ma bai gane matar aure bace sai daga baya da matsaloli sukayita kunno kai,yasan wala'alla wahalar data sha a aurenta na baya yasa ta kasa sake masa,amma yasan a hankali in sha Allah komai zai kawo qarshe,zai kuma shawo kanta.
Ta tafas batace ba tunda suka shiga motat,hirarsu suke shida mufidan kamar dai dazu,hawayenta taketa riqewa,bataso su zuba ya gani,ita kadai tasan ciwon da qirjinta yake mata,wanne irin cin fuska ne ya lamin din yayi mata haka?,ko yaya?....sam babu wani digo na kishinta ko kuma soyayyarta akan fuska da ayyukansa?.
Sai daya tsaya a hanya a wani guri ya siya fruits masu yawa,bayan ya tambayi mufida dame dame sukafi so sannan suka wuce gida,a 'yar harabar gidan dake dauke motar tasa yayi parking,mufida ta fara ficewa da ledojin,rashin qwarin jikinta yasa take komai slowly,ta buda murfin motar zata fita taji yace
"Wait" saita dakata din kamar yadda yace,hannunsa ya sanya a hankali ya saita mudubin gaban motar zuwa saitin fuskarta,ta daga idanunta a hankali tana kallon wajen,saiga fuskarsa tarwa,tsimammun idanunsa a kanta masu nauyi da kwarjini.
Ita ta fara janye idanun nata kamar kowanne lokaci,kafin daga bisani muryarsa ta ratso kunnenta
"Wacce damuwa ce a ranki haka?" Yayi tambayar a dake,cikin ginshirar nan tasa,koda bata kalleshi ba tasan fuskarsa babu alamar wasa,to amma a nata ganin bai kamata yayi mata wannan tambayar ba,tayi imani cewa yafi kowa sanin amsar tambayarsa,koda bata buda baki tayi masa bayanin komai ba,hakan da yake mata kamae titsiye ne.
Bata amsa ba,kuma bata da niyyar cewa komai,shi kuma bai fasa kallonta ta cikin mudubin ba,hakanan ta dunga jin idanunsa na yawo cikin jikinta kota ina,tsahon wasu mintuna kafin ta sake ji yake
"Alright.....shikenan,abu daya zance miki.....lafiya abace mai daraja,saiki kula,zaki iya tafiya" daga haka ya soma cire belt din dake jikinsa,ta saka hannunta a sanyaye ta bude motar ta fito,tana tafiya kamar iska na yawo da ita haka takejin jikinta,zuciyarta a quntace waje guda,kwanyarta cunkushe,a hankali kamar ba zata qarasa ba ta cusa jikinta zuwa parlor dinsu.
*FOLLOW ME ON AREWABOOKS DOMIN SAMUN CI GABA,SABBBABIN PAGES GALLA GALLA*
*_KUFAN WUTA_*
*SABABBIN PAGES DA DUMINSU SUN SAUKA*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾
https://arewabooks.com/chapter?id=62bc3f8a7660dfc79da17d20
*YADDA AKE BUƊE ACCOUNT A AREWABOOKS*
Bayan kaje play store ka ɗakko ya sauka a kan wayarka. Za'a cike Form ɗin kamar haka: -
*Enter your name:* (Cikakken sunanki)
*Enter your mail:* (Email ɗinki)
*Enter an username* (Sunanki)
*Enter your password:* ( misali 12341234)
*Confirm password:* (misali 12341234)
Sai a taɓa *Sign Up* shikenan an buɗe account a ArewaBooks💃🏻😂.
*Continue with Google* - Idan kana da gmail/email akan wayarka kawai Continue with Google za'a taɓa zata buɗe maka account a ArewaBooks kaitsaye.
*Register* - Shine cike form domin buɗe account a ArewaBooks.
*_AREWABOOKS LINK kai tsaye_*
https://arewabooks.com/chapter?id=62bc3f8a7660dfc79da17d20
Masu iPhone
Zaku iya bibiyar shafinmu
https://arewabooks.com
*_Kuzo mu haɗa ƙarfi da ƙarfe domin gyara tafiyarmu. Koba komai ɗan uwanmu ne bahaushe ya zauna ya tsara ya kuma buɗe App... Ɗin domin cigabanmu da jin daɗinmu. Wannan abin alfaharine_.*
*_MARUBUTA DAKE NEMAN ƘARIN BAYANI KO MASU KARATUN MA, ZAKU IYA NEMANMU TA WANNAN NUMBER_*
+234 903 177 4742
_Alkairin ALLAH yakai gareku masoya a duk inda kuke, tare da fatan alkairi muna sonku irin trillions ɗin nan😍😘😍🥰😍😊_.
*_YADDA ZAKA SIYA LITTAFI A AREWABOOKS_*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾
*Recharge* - inda ake shiga domin saka kudi cikin account.
*Balance* - Zai nuna kudin account dinku da zaku iya sayayyan littafai cikin kasuwar ArewaBooks.
*Credit/Debit Card* - Hanyar farko kuma mai dadi wajan Recharge din account dinku.
A inda (Enter your amount) za'a saka kudin da akeson Recharge din sai a taba "Proceed". Zaibude muku inda zaku saka bayanan katin banki, kuna gamawa kudinku zaishiga account dinku kaitsaye (instant).
--------
Akwai wasu hanyoyin saka kudi a ArewaBooks account kamar:
*Bank Transfer*
*Airtime Transfer*
Saidai su ba kaitsaye bane (instantly) sai ArewaBooks ta tabbatar da Transfer din, amman bayakai 1hour za'a gansa a Balance.
*Bank Transfer* - kamar yadda akwai bayani a sama da kuma account number ArewaBooks.
_Account No_ - *1220077999*
_Account Name_ - *Arewa Books Publishers*
_Bank_ - *Zenith Bank*
Bayan anyi Transfer dinne sai a cike wannan Form din:
Amount Paid: - Nawa aka tura?
Name used for transfer: - sunan da aka saka wajan turowa
Transferred time: - lokacin da aka turo
Name of bank: - sunan bankin da aka turo dashi
Deposit date: - ranar da aka turo
Sai ayi SUBMIT.
*Airtime Transfer* - muna bada shawaran ayi amfani da *Debit Card* kokuma *Bank Transfer* akan *Airtime Transfer* , amma idan yakama babu mafita saishi tau muna amsar:
MTN,
9Mobile
Glo
Airtel
Amma kamar yadda akayi rubutu a sama afara tuntubar ArewaBooks a WhatsApp domin akwai percent da ake cirewa na canji(convert) kafin kudinka yashiga Balance.
*WANNAN SHINE BAYANAN*[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 46
Sanarwa da inna kawai tayi ta dawo ta wuce daki,ta zube saman katifa tana maida numfashi,kwanyarta na tariyo mata duk abunda suka faru,tana shakka zuciyarta kuma nason tabbatar mata,ta juya ta gyara kwanciyarta tare da runtse idanunta,tana son ta mance da komai ko zata samu sauqin azabar da takeji tun daga gangar jikinta zuwa zuciyarta,saidai bayan kowacce daqiqa tunanin ameen ne a rai da zuciyarta,azabar da takeji kuma tana sake qaruwa,bata samu sassauci ba.
Fruit da magungunan da mufida ta ajjiye mata tace ya ameen ne yace ta tabbatar tasha ta bisu da kallo,me yasa yake bata fake caring?,me yasa yaketa pretending?,bayan tasan ba haka bane?,a yanzu ba wadan nan abebadan take buqata ba,koda taci ko tasha tasan babu wani magani da zasu iya yi mata,zuciyarta shi takeso,shi take da buqata,shine magani kuma abincinta,amma me yasa yaketa avoiding dinta?,yanata nuna bai gane komai?,yanata nuna a yanzun yaren dake kan fuskarta bashi yake ganewa ba?, pillow ta jawo ta cusa kanta a qasa gami da qanqameshi tana fatan Allah ya kawo mata barci ko zata samu sassauci.
Addu'arta kuwa taci,dogon barcin daya dauketa har gefin magariba sannan ta farka,ta ambaci sunan Allah da sauri ta shiga bandaki,ta daura alwala ta dawo ta fara bada bashin sallolin dake kanta,bata tashi ba sai datayi sallar magariba.
Tadan samu relief kadan,ta jawo ledar magungunanta ta dubasu,saita fara shirin miqewa,dai dai lokacin mufida ta shigo
"Yauwa,ashe kin tashi ma,bari na gayawa innan"
"Tsaya mu fita tare" ta fada tans miqewa tare da tambayarta
"Ba kowane a gidan?" Dan dubanta tayi cikin rashin gane ma'anar tambayar tata,amma duk da haka tayi qoqarin amsa mata
"Yaa sadiqu ya tafi zance..." Gabanta ya doka,tana fargabar jin amsa ta gaba
"Ya alameen kuma tunda suka fita unguwa da malam basu dawo ba" saita jinjina kai,tayi gaba mufida ta biyo bayanta.
A parlor ta cimma inna,tana zaune tana gyara saitin stations na radio dinta,akwai tv,amma sam bata wani damu inna ba,idan sun kunna takan kalla,amma idan basu kunna ba saita wuni a kashe ba tare data kunna ba.
Daga kai tayi tana yiwa iman din sannu,ta amsa tana zama saman kujera
"Kinsha magungunan naki?"
"Yanzu dai zansha" ta amsa mata,sannan tace mufida ta samo mata abincin dan kadan a kitchen.
Tana tsaka daci taji sallamar malam,already mufida ta gaya mata tare suke dashi,hakan na nuna sun dawo kenan,sai ta ajjiye farantin gefe saboda yadda taji abincin ya tsaya mata.
Ballar maganin tayi ta riqe cikin tafin hannunta,ruwan na riqe a cup amma tana wassafa yadda zata tanqwara kanta tasha maganin,saboda tun asali bata qaunar magani,sai an sha fama da ita takesha.
Shigowar malam ta sakata ajjiye cup din,taci gaba da riqon maganin a hannunta tana masa sannu da zuwa,sai idanunta yakai kan wanda yake bayansa,ameen ne tsaye sarqafe da hannayensa a qirji,hada ido sukayi,saiya dauke kansa kanshi tsaye bayan ya kalli hannun ta,koda ba'a gaya masa ba yasan yadda zatasha maganin take taraddadi,ya juya a nutse ya fice daga parlor din,yana amsa wayarsa da aka kirashi sanda ya juya din.
Miqewa tayi itama ta koma daki ta barwa inna da malam parlor din,duk da cewa malam din yana da tashi rumfar,amma qila a nan yayi sha'awar zama.
Ko data koma ciki ta taras da miscal din dr ahmad masu yawa,daga bisani kuma taga tex dinshi,duka yana mata sannu da jiki ne,tare da bata qwarin gwiwar kauda damuwa daga ranta,aje wayar kawai tai bayan ta gama karantawa,indai sai damuwa ta fita daga ranta,to tabbas bata da guarantee din ranar warkewa.
Washegari ma haka nan ta wuni,jikin da sauqi,amma babu wani kuzari sam tattare da ita,a dakinta tayi kwanciyarta,bata yarda ko sau daya ta fito sun hadu dashi ba,saidai duka taji muryarsa sanda zai fita,ta lumshe ido wani abu na tsarga mata sanda taji ya ambaci sunanta yana tambayarta,har zuwa amsar da mufida ta bashi,hakanan sanda ya dawo ma taji shigowarsa,hatta da zaman cin abinci da sukayi a parlor shi da sadiq,da fitarsa daga parlor din sanda wayarsa ta dauki ruri,sai zuciyarta ta cilla ta bishi bayan fitar tasa,tana ji a jikinsa da wata zaiyi waya.
Kasa nutsuwa zuciyarta tayi,daga qarshe ta dauko headphone dinta tayi connecting da wayarta,ta kunna suratul baqra cikin qira'ar sheik khalilul kusari,ta rage volume dai dai yadda bazai dameta ba,wannan ya taimaka matuqa wajen janye hankalinta,har ta samu barci ya fara fusgarta.
*****A kwana na biyu ne taji qwarin jikinta,ranar ta wuni a kwance,ta samu barci kuwa sosai yadda ya kamata,hakan ya sanya koda ta tashi fresh ta jita,ta fito parlor tana laluben inna,sai a sannan mufida ta gaya mata ta tafi karben lefen 'yar gidan kawu muktar,ta jinjina kai tana mamakin baccin da tasha,saita koma daki ta cire kayanta ta fada wanka.
Tsaye tayi gaban mudubi daure da towel tana kallon fuskarta,ta fada tayi fayau da ita,sai haske data qara,blue eyes dinta sunyi tas dasu,manta ta jawo ta fara qoqarin shafawa mufida ta shigo
"Ya iman kinyi baquwa"
"Baquwa kuma?" Ta tambaya cikin mamaki
"Eh" shuru ta danyi sannan tace
"Baki santa ba?" Kai ta girgiza
"Ban santa ba,amma dai 'yar gayu kamarki" murmushi iman din tayi,har fararen haqoranta suna fitowa
"Ke kam akwai ki da son gayu mufida,jeki kice mata ina zuwa" ta amsa da to ta juya ta fita tana dariya.
A nutse ta shirya kanta cikin wani Cotton material,ash colour ne mai zanen manyan flowers,dinkin riga da skert ne me kyau daya zauna a jikinta,comb tasa tana taje kanta mai laushi da tsaho,ta duba ma'ajiyar ribbons dinta ta saka daya ta kame gashin nata dashi,ta kalli gashin nata ta cikin madubin,sai takejin ya mata datti tana buqatar zuwa a wanke mata shi,duk da ba wani datti bane me yawa,jikinta tabi da turarenta mai taushin qamshi ta feshe,saita dauki wayarta da zummar idan ta gama da baquwar ta kunna data ta duba group na ajinsu taga me ake ciki,don kwana biyu bata hau ba,daxun kuma tana tsaka da bacci wata abokiyar karatunta da suke mutunci sosai ta kirata,ta bata haquri kan zata kira idan ta tashi.
Sanda ta qarasa parlor din idanunta na kan wayar,sai data shiga sannan ta cira kanta tana yin sallama.
Sanye cikin wani lace orange da aka yiwa dinki bunu na zamani da aka wadata da stones masu walwali,ta yane kanta da mayafi medium,wanda tadan jashi baya,daurin kanta daya fara daga gaban goshinta ya zauna das,ya kuma sake qawata kwalliyarta,matashiyar budurwa ce wankan tarwada,wadda a qalla shekarunta baxasu haura ashirin da biyu ba,tana da doguwar fuska da siraran labba,sai gashin gira wanda ya zarta gashin idanunta cika,tana da kyau irin wanda ake kira da matsakaicin kyau,a wasu guraren kuma direct za'a kirata da sunan kyakkyawa,shigarta kadai zata gaya maka a waye take,hannunta riqe yake da wayarta tana latse latse,gefanta kuma wata matashiyarce,itama cikin doguwar rigar atamfa,saidai ita din batakai wannan kyau ba,kamar yadda a ido kawai zakasan bata qarasa shekarun wancar din ba.
Idanun iman qur bisa fuskokinsu take takowa,saboda duk cikinsu babu fuskar wadda ta sani
"Sannun ku" ta fada da tattausar muryarta,zuciyarta na raya mata batan kai sukayi,ba gidan suke nema ba
"Yauwa sannu" matashiyar dake sanye da lace ta amsa murya qasa qasa,idanunta fes bisa fuskar iman wadda tuni ta qaraso wajen tana dauke idanunta daga kansu karo na barkatai da batasan adadin ba..
Cikin zuciyarta iman take mamakin kallon da baquwar ke binga dashi,mutum ce ita data tsani kallon qurilla,balle ga baqo....baqonma irin wannan da batasan daga ina take ba,kuma me take kallon oho.
A nutse ta samu one sitter ta zauna ta dauke pillow din dake kai ta maida saman cinyarta
"Sannunku ko?" Iman din ta sake maimaitawa,sai matashiyar dake gefe ta amsa wannan karon
"Ina gajiya ya gida?" Iman ta maida musu gaisuwarsu,sannan ta miqe,har yanzu dai tana mamakin su waye,daga inda kuma suke din.
A nutse ta wuce zuwa kitchen don ta gabatar musu da ruwa,kamar yadda suka saba al'adar gidan,koda basusan baqo ba,kallo suka bita dashi,kafin daga bisani su janye idanunsu kusan a tare
"Wai itace autar?" Matashiyar dake gefe ta tambayeta
"Nima dai ina doubting......banga suna kama ba,amma......bari na kirashi kawai" saita dauki wayarta data ajjiye a gefe,ta fara zuba numbers dinsa cikin wayar,wanda ta jima da haddace digits din.
Tabe baki iman tayi bayan ta gama guntun tunaninta akan su waye cikin kitchen,koma su waye kansu suke batawa lokaci idan suka gane ba gidan da suke nema sukazo ba,ta qarasa ta samu babban tray ta zuba robobin zobo mai sanyi da sukeyi suna zubawa a fridge saboda sha,ta hado musu da pure water shima mai sanyi sosai,ta dora cups ta nufo falon.
Tun kan ta qaraso ta fahimci waya take,saidai ba zaka iya jin me take fada ba,har ta qaraso din kuwa bata iyajin komai ba,saboda yadda take maganar kamar wadda ke rada
"Eh......dama mamaki na shirya baka,idan baka yarda ba ka qaraso muna cikin gidan ai" ta fada da wata iriyar murya can qas.
Qarasa dire musu plate din kawai tayi ta koma seat din data taso ta sake zama,ta fuskanci dai gidan nasu sukazo,to amma wajen wa?,for now dai ai ya kamata su fadi wa suke nema,to amma koda waye taji tana waya yana da alaqa da gidan nasu.
Sosai qirjinta ya harba sanda zuciyarta ta raya mata idan ameen ne fa?,siriryar iska mai zafi ta futar daga hunhunta wai ko zaga samu relief,iya wannan tunanin ya sanyata jade girar sama data qasa,ta tsuke fuskarta tas,tsohon tsimammen miskilancinta ya motsa,ta maida qafarta daya kan daya,sannan taja wayarta ta bude,ta fara bin charts din group din ajinsu,gefe daya zuciyarta na qwarara mata gwiwar bata da alaqa da ameen,ba yadda za'ayi tana surukar gidan ta iya tunkarar gidansu.
Parlor din ya dauki shuru,iman din ta maida hankalinta ga chart dinta,sai qarar tv dake tashi kadan kadan,sam taji baquwar batayi mata ba,ta yaya zakizo gidan mutane ki samu guri ki zauna,ki kasa fadin wacece ke?,jin kai ne ko meye?.
A karo na kusa hudu daya abokiyar tafiyan tata ta dubeta,tadan tabata kadan,kafadunta ta dage kana ta daga gira sama ta sauke,ta aje cup din ruwan data sha
"Sunana samha" a nutse iman ta daga kanta ta kalleta
"Wannan kuma qanwata ce subai'a,muna neman iman ne,qanwar alameen" a nutsen ta amsa mata,ambatar sunan al'ameen din da tayi sai da gaban iman din yayi wata mummunar faduwa.
"Gani" kallonta samhan tayi sosai sannan ta dan saki murmushi
"Ayyah,ban san fuskarki ba,shi yasa ban ganeki ba,ya jikin naki?"
"Alhamdulillah"
"To Allah ya qara sauqi"
"Ameen" ta amsa mata a taqaice ta maida kanfa ga wayarta,har yanzu qirjinta bai daina bugawa ba,wani irin fargaba ce ta dinga saukar mata tana kashe mata gabban jikinta,duk yadda samhan taso ta dinga janta da hira amma hakan ya faskara,banda ma bata da tabbacin wacece ita?,kuma wajen wa tazo.....da babu abinda zata zauna yi a parlor din.
Ganin bata samu sakewa da iman din ba yadda ya kamata saita koma hirarta da mufida,da yake mai hira ce mufidan saita sake mata suka taba hirara.
*_Assalamu alaikum,fatan kowa yana lafiya,don Allah ina neman alfarmarku,wani muhimmin abu ya tasomin cikin satin nan har zuwa satin gaba,zaku dinga ganin 1page,idan kuma na samu sarari zaku dinga ganin guda biyu har zuwa sanda uzurin nawa zai kammala,ina fatan za'ayimin afuwa,na gode_*👏🏾👏🏾👏🏾
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 47
Zaman gaba daya ha gama gundurarta cikin parlor din,sam babu wani armashi ko ma'ana,ta gama yanke iya mintocin da idan suka cika zata tashi daga zaman da sam bashi da wata fa'ida a idanunta.
Sallamarsa ce ta ratsa tsakar gidan,cikin husky voice dinsa,wadda duk sanda zata jita sai ta haifar da wani abu mai nauyi dangane dashi a gangar jiki da zuciyarta,don ko a yanzu ma lumshe idanunta tayi tana jin yadda ko wane sashe na jikinta ke amsawa,bude idanunta kuwa yayi dai dai da zare rufaffun takalmansa da yayi ya sako kai zuwa parlor din.
Tsaye yayi daga bakin qofa,hannyensa boye cikin aljihun wandon suit dinsa,idanunsa saman fuskar samha,yayin da fuskar samhan ta wadata da murmushi tana dan jan mayafinta tana rufe rabin fuskarta
"Suby'a har da ke?" Ya fada yana sakin hannayensa tare da takowa a nutse zuwa cikin parlor din,cikin murmushi suby'a din tace
"Ya zanyi mata yaya,indai batazo dubiyar nan ba babu zaman lafiya,tunda taji auta babu lafiya ta hanani sakat"
"Da kyau" ya amsa yana qoqarin maida idanunshi kan iman,wadda ta miqe zumbur kamar wadda aka tsikara,sannan ta wuce kanta tsaye zuwa kitchen ba tare data waiwayo ko kuma ta saurari kowa ba.
Da idanu ya rakata kafin ya janye dubansa daga kanta cikin mamakin reaction dinta,sauke kallonsa yayi ga samha wadda itama ta bishi da kallo,suka hada idanu
"Are you okay?" Ta tambayeshi yanayin fuskarta yana dan canzawa akan yadda ta kalleshi lokacin da ya shigo parlor din,ta hanyar dage mata girarsa ya amsa mata yana sake qarasowa don samun kujerar da zai zauna akai,mufida tayi masa sannu da zuwa,ya amsa yanabin ruwa da drinks din da aka ajjiye musu da kallo.
Bata tsaya ba sai data dangane da jikin cupboard din kitchen din,ta dafe hannuwanta dasu tana qoqarin saidaita gudun zuciyarta saboda hakin da yakeson sarqafeta,koda baice komai ba ta gama karantar komai din,samha budurwar ameen ce,ta kuma zo dubata saboda taji bata da lafiya,hakan yana nufin batasan tarihin abinda yake tsakaninsu ba,wannan shike tabbatar mata da gaske ya ameen ga wanke dukka wata tsohuwar alaqa da dangantaka data taba hadasu da gasken gaske kamar yadda ya taba furta mata.
Kokari take ta fitar da hawaye daga idanunta ko hakan zaisa ta samu sassaucin wani abu mai tauri daya tsaya mata a wuya,ta sunkuyar da kanta qasa a hankali sanda kukan ke zuwa mata,ta kuma saka hanunta guda daya ta toshe bakinta dashi don kada ta fallasa kanta,wasu hawaye masu dumi suka fada kai kawo saman fuskarta,sai taji tsaiwar na neman gagararta,ta sulale ta tsugunna sosai tana cusa kanta a tsakanin cinyoyinta,tabbas ta rasa ya ameen,ta rasashi rashi na har abada,babu abinda idanunta ke hango mata a yanzun sai fuskarsa tare data samha,daga nan inda take tana iya jin muryan samhan,duk da bata iya fahimtar me suke fada,sai tasa tafin hannuwanta ta danne kunnuwanta dasu tana runtse idanunta.
Kuka take wanda ke tafe da qunci nadama da kuma dana sani,bata taba tunani a rayuwarta zuciyarta na qaunar ya ameen ba har haka,bata taba kawowa akwai lokacin da nadama da tashin hankali kan barin ameen zasu risketa ba har irin haka,dama da gaske ne da ake cewa dama sau daya take zuwarma dan adam a rayuwa,itakam da alama ta rasa tata damar,me yasa ya ameen bazai kalli qwayoyin idanuwanta ya karanci meke cikin zuciya da ruhinta ba kamar yadda ya saba mata?,me yasa zai barta ita daya sonshi yana wajigata ta duk inda yaga dama?,idan ma horo ne ya zuwa yanzu zuciyarta ta gama horuwa,koda yadda zuciyarta ta cika fa tumbatsa da qaunarsa kawai ya barta tabbas ta karbi dukkan sakamakon daya kamata.
Batasan sanda innata shigo gidan ba,saidai kawai ta tsinci muryarta tana doso qofar kitchen din tana kiran sunanta da alama nemanta take.
Da hanzari ta miqe,ta kuma juyawa qofa baya tana fuskantar sink na kitchen din,ta kunna famfo ta tara hannayenta ta fara wanke fuskarta,dai dai sanda innar ta qaraso tana fadin
"Me kike haka a kitchen ne tun kusan rabin awa?" Rasa amsar da zata bawa inna tayi,batason ta buda baki da zummar magana innar ta gano tayi kuka,amma dole ta amsa matan indai baso take ta zagayo taha fuskarta bane
"Kokarin dora abinci nake inna"
"Bansan ma me kuka zauna yi ba har yanzu ace ba'a dora abincin dare ba,ki fara samun wani abun me sauqi ki dorawa baqin nan,nace sai sun dakata mun gaisa sosai tunda yanzun na shigo ni"
"To" din da zatace ta maqale mata,ta kasa kunne taji takun fitar innar amma bataji ba,a maimakon hakan sai taji innar tana takowa zuwa cikin kitchen din,abunda ya kidimata kenan ta fara kame kame,sam bata qaunar wani ya fahimci halin da take ciki akan ameen din,matsala ce da ita ya jawowa kanta da hannunta ita kadai,ita kadai din kuma ya cancanci tayi kuka da ita,a sanda dukka masoyanta suke jiye nata zuwan wannan rana....a sannan din ita kuma nata idanun suka rufe,bata ji bata gani,bata hango aibu dacewa ko kuma rashin dacewa.
A gabanta inna ta tsaya,ta kasa daga idanunta balle ta kalli innar tamkar wata mara gaskiya,taji lokacin da innar ta motsa bakinta da niyyar yin magana,sai kuma taji ta maida ta rufe,ta kuma ja da baya taba cewa
"Karki dauko girki mai wahala don kada su qosa da jira" daga haka ta juya a hankali ta fice daga kitchen din.
Lafiyayyar taliya tayi data wadata da kayan lambu,ta shirya komai a tsare,sannan ta kira mufida daga nan inda take din tazo ta dauka,ba tare data fito parlor din ba ta zarce da dora abincin dare na gidan gaba daya.
"Well-done" ya furta a nutse sanda mufida ta ajjiye tray din abincin a gabansa sanda yake zaune saman carpet din parlor din yana amsa wayar bashari,shugaban babban shagonsa da a yanzu yaketa qoqarin ganin ya maidashi company,parlor din babu kowa yanzun,don inna ta basu waje tunda taji iman ta gama abincin.
Da hannu yayima suby'a alama kan tayi serving nasu,tayi yadda yace din,saidai samha ta maqale kafada alamun ba zata ci ba,miqewa yayi tsaye bayan ya cire wayar daga kunnensa
"Ku kammala kafin na fito,kiyi tasting girkin ki fadamin abinda kika ji" daga haka ya maida wayar kunnensa sannan ya taka a hankali ya fice daga falon.
Sai daya bacewa ganinta ta janye idanunta daga kanshi tana sauke ajiyar zuciya,suby'a ta zungureta
"Wai meye hakan?" Murmushi samha ta saki
"Farkon ganina dashi.....ban taba tunaun wata rana zai soni....ko xan sameshi ba suby'a,matan dake sonshi sunyi yawan da har nake ganin ni bazan samu ba" baki suby'a ta riqe,tana mamakin samhan,miskilace ta haqiqa,wadda ba kasafai namiji ke burgeta ba,tana da kyan da yasa ba kowanne namiji take tsayawa ta kula ba,bare har ta buda baki tace tana sonshi,alameen na cikin namiji na farko data taba furtawa da bakinta tana sonshi,har kuma take gaza boye son,bata wasa da sanya da dukkan wani abu daya shafeshi.
"Amma suby'a,anya ko yarinyar nan jinin man ce?"
"Kamar yaya?" Suby'a ta tambayeta tana kallonta cikin rashin fahimta
"Basa kama kwata kwata,saidai kowanne cikinsu da color din nashi kyan,na biyu kuma jin kanta yayi yawa...... infact ma,sai nakeji a raina bata yimin ba,innarsu ta fita kirki" murmushi suby'a tayi
"Kinga,kice dai kawai bata yi mikin ba,amma idan batun jin kaine ina kika baro man din naki?,ko kin manta saboda yanzun kin sameshi?"
"Manta kawai,bani abincin na dandana naji abunda yakeso naji din" ta fadi tana kallon taliyar yadda ta shiryu a idanuma,tun ba'a kaita baki ba.
Tabbas taji different aroma and taste,tasan kuma duk hannun da yayi abincin yasan abunda ake kira da girki,saidai batasan me yasa zuciyarta taqi gamsuwa da harshenta ya yabi girkin ba,daga qarshe ta ajjiye spoon din,ta koma da baya ta zauna tana turama ameen saqo.
Sai daya gama wayarshi tsaf sannan ya tura qofar parlor din nasu,babban parlor din daya wadatu da kyau da kuma tsafta,ko ina a shirye yake da kayan alatu masu kyau da daukan hankali,kusan komai na cikinsa black and white ne,ya sauke wayar yana fadin
"Alhamdulillah" har sau uku qasa qasa amma a fili,shi kansa yasan nasibi da budi da ubangiji yaketa yi masa abune da ba kowanne bawa bane ya samu hakan,cikin shekaru kadan amma ya fara riqe dukiyar dako a mafarki bai taba kawowa kansa zai mallaketa ba,yaci gaba da takawa a hankali zuwa daya daga cikin qofofin bedrooms guda biyu dake parlor din,har ya qarasa tasa,ya tura ya shiga.
Dakin kwanane wanda zai burge duk wanda ya ganshi,komai dake cikinsa fari ne,da alama wannan shine zabin mamallakin dakin,komai tsaf a kammale kamae parlor din,qamshi ne kawai ke fita daga cikinsa da kalolin qamshin air freshener da kuma turarukan da yake amfani dasu wanda suka fara kama bedroom din nashi.
Saman mirror dinsa dake cike da kayan shafa na maza ya isa ya dora wayarsa akai,ya balle belt din jikinsa ya fidda wandon,sai boxer daya rage,sannan ya fara balle rigar jikinsa ya fiddasu daya bayan daya,take faffadan jikinsa wanda ke murde yake kuma cike da gargasa daga qirjinsa zuwa hannuwansa suka bayyana,matsawa ya sakeyi gaban mudubin ya dauki towel yana nutsa yatsunsa saman sumarsa,gami da furzar da iska mai zafi daga bakinsa,abinda ke nuni da cewa a gajiye yake lallai.
Wata qofar ya buda ya shige,sannan ya maidata ya rufe.
A qalla mintuna ashirin cif yayi cikin toilet din daidai sanda wayarsa ta fara tsuwwa,yana cikin nau'in mutanen dake dadewa a toilet,ya fito sanye da rigar wanka data tsaya masa iya singalalin qafafunsa da suka jiqe da ruwa,gashin dake jikinsu suka kwanta luf,hannunsa dayan riqe da towel yanata goge sumar kansa da kyau,jikinsa ba abinda yake sai fidda qamshin shower gel din da yake amfani da ita.
Yana ci gaba da goge kan ga qarasa ga wayar tasa,ya zuba mata idanu a haka ba tare daya taba ba,yana karanta saqon samhan daya shigo wayarsa ya kuma bayyana saman screen din
"I ate,what next?" Qaramun murmushin gefan baki yayi,sai ya ajjiye towel din daga gefe,ya dauki wayar yana maida mata amsa
"Ina da son abinci.....if i said that......ina nufin different types of food,so get ready....." Yana sending mata ya ajjiye wayar,ya daga idanunshi ya maida kan fuskarsa data bayyana tarwai a fuskar madubi da dan sauran danshi a kanta.
Idonsa ya dan rufe kana ya bude,fuskar iman ta gifta cikin kwanyarsa haka kawai, different reactions nata a mintunan da suka gabata suka fara dawo masa,sai ya dauki tunanin ya cilla gefe,ya dauko body cream dinsa ya fara shafawa bayan ya saita wayarsa yadda zata karanto masa saqonnin da yake dasu ta email dinsa,tunda ya baro system dinsa a office bai taho da ita ba.
Ta fara nisa da aikin abincin,kamar yadda tunaninta yayi nisa da gangar jikinta taji inna na kiran sunanta,ta ajjiye albasar da take qoqarin yankawa ta waiwayo tana amsawa,duk da qwalla ce qasan idanunta,amma kuma a nata ganin zata kaucewa kowacce tuhuma saboda zata kafa hujja da albasar da take yankawa.
Dan zuba mata idanu innar ta sakeyi
"Idan akwai sauran abincin can da kika dafa kibari basai kin dora wani ba,malam yayo waya,bazai samu tahowa yau ba,zai kwana a can"
"To" tace tana tattare kayayyakin
"Lafiyarki kuwa?" Inna dake shirin fita ta dakata ta tambayi iman din,bata da wata amsa da zata bata,don haka ta gaya nata yanayin da takeji kawai
"Kaina ne yake ciwo" jim kadan inna tayi
"To basai ki lalubi maganinnki kisha tun yanzu ba?,Allah ya sawwaqe"
"Ameen" ta amsa mata tana sake danne zuciyarta,ta tattara komai a tsaitsaye saboda yadda ciwon kan keta qara gaba ta wuce daki.
Alwala tayi tayi sallah,saidai ta kasa tashi daga saman abun sallar,tayi imani a yau idan batasha maganinta ba akwai matsala,ta miqe a hankali tana duba ma'ajiyarsu cike da dauriya,saidai ta taras babu komai,ta dafe goshinta tana kiran sunan Allah.
Tasan dole ta nemo maganin indai tanason samun sassaucin radadin da take ji,matsalar su daya,a yanzu basu da dan aike a gidan,duka almajiran malam an barsu a tsohon gida,yanzu acan suke karatunsu,unguwar tasu kuma wata iriyar unguwa ce,wadda idan kana neman abu sai kayi tattaki ka fita daga cikinta,bata da sauran option face ta fita din,don haka da hijabin jikinta ta zura slipper ta dauki wayarta ta fito.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 48
Har yanzu suna parlor din,saidai zuwa yanzu sun miqr tsaye,da alama suna shirin tafiya ne,kanta ta kawar tayi hanyar dakin inna,ta samu innar tana hada wasu kayayyaki a leda,da alama baquwar tasu zata bawa
"Yaya?" Innar ta tambayeta tana dubanta
"Maganin ciwon kan nan zanje dubowa inna"
"To....amma kuma darene ai,ko kuma bari na yiwa aminu magana,idan zasu fita ya fita dake" bataji dadin abunda inna tace ba,batason hada tafiya dasu kwata kwata,inda tasan tafiyar tata ma zatayi dai dai da tasu da bazata fito ba har sai sun wuce,a yanzu kuma tattalin duk abinda zai bata ran innar takeyi,saboda haka babu damar musa mata,sai ta amsa mata da to,tabi bayan innar sanda take fita daga dakin riqe da ledar.
Suna fitowa zuwa parlor din yana daga labule shima yayi sallama,kallo daya iman tayi masa ta janye idanunta zuwa wani sashe na daban,saboda wani kishi da taji yana shirin shaqe mata kafar iska,wani mugun kyau taga yayi mata cikin qananun kayan da ya saka,sun daukeshi fiye da yadda za'a gaya ma mutum,kana masa kallo daya zaka san cewa hutu wayewa da ilimi sun ratsashi qwarai da gaske,idan dai batayi kuskure ba tana iya ganin yadda samha ta kafe ameen din da idanu,fuskarta kuma na aika masa da saqon murmushi,saita janye jikinta a hankali zuwa baya,ta lalubi kujera daya ta zauna akai,tana qoqarin controlling kanta.
Duk sallamar da sukewa inna tana jinsu,da ledar da suka ajjiye da sunan kayan dubiyarta
"Al'aminu.....xaka biya da iman da Allah zata duba maganinta,kanta ke ciwo"
"Ya salam.....sannu,jikinne ya dawo?" Samha ta fada cikin nuna kulawa,fuskarta na bayyana damuwa.
Kanta kawai ta gyada mata ba tare data dubeta ba,tana iya jin idanun lamin din a kanta,har zuwa sanda ya janyesu yana amsawa inna,suka qara sallama dukka sukabi bayansa tana zaune a wajen ko motsawa batayi ba.
"Tashi kije kada su jiraki" inna dake neman wajen zama ta fada,saita gyada kai
"Zan tashi inna,so nake kan yadan dai daita" ta fada tana tallafe kan nata da tafin hannunta
"Sannu....Allah dai ya sawwaqe wannan ciwon ya yayeshi"
"Amin" ta amsa qasa wasa muryarta na dan rawa saboda hawaye da suke qoqarin taruwa cikin idanunta.
Bata motsa ba har sai da mufida data musu rakiya ta dawo tace ya lamin yace ta fito sannan ta miqe tana ficewa,ita kuma yarinyar ta fara tattare wajen.
Shuru cikin motar ya dauka bayan wucewar mufidan takai saqon da alameen din ya aiketa dashi,shi yana qoqarin saka frequency na gidan radion arewa zaiji labaran dare da yake mayen jin news ne.
Ajiyar zuciya samha ta sauke,tana dan kada yatsunta,ta waiwaya a hankali zuwa sashen da lamin ke rage volume tana duban fuskarsa daga side daya,ta lumshe idanunta kanata bude,daga cikin abubuwan dake burgeta tattare da lamin din yanayij nutsuwarsa da kuma komai nashi bisa tsari da aji,lumsassun idanunsa da kuma kwantaccen gashin dake habarsa zuwa gefe da gefan fuskarsa,wanda ko sau daya babu wanda zaice ya taba ganinsa ba'a tsare ba
"Man" ta kirashi kai tsaye da wata kwantacciyar murya,kansa ya daga suka hada idanu,sai ta sakar masa murmushi,sexy eyes dinsa suna sake tsuma soyayyarsa dake zuciyarta
"Dakai da iman,waye ne yafi miskilanci ne?" Karamin Murmushi ya saki,yana relaxing bayansa da kujera da yake kai,sannan ya gane tafukan hannayensa waje guda yana dubanta
"Ni din miskili ne?" Ya tambayeta yana dage dukka girarsa sama,abunda ya qara masa kyau da kwarjini kenan,sai ta lunshe idanunta sannan ta gyada kai
"Kwarai kuwa,don har yanzu ban manta abubuwan da suka faru ba kafin na sameka" murmushin gefen baki ne ya kubce masa,sai ya gyara zamansa sosai ya na fuskantar gaban motar,dai dai sanda iman ta fito daga ciki,tana kuma takowa a hankali,iska na kada hijabinta daga hagu zuwa dama,dama zuwa hagu,jikinta ba kuzari abinda ya qarawa tafiyarta slow kenan,idamunsa fes a kanta,sai ya dora hannunsa daya kan sitiyarin motar daya hannun kuma ya fara qoqarin tayar da motar sannan yace
"Wala'alla kiga dabi'u masu tarin yawa dake kamanceceniya tsakanina da iman....saboda ita din raino ce" da sauri samha ta kalleshi
"Rainonka?,amma kuma man....sai nake ganin kamar ba sister dinka bace ta jini,ina nufin uwa daya uba daya"
Dubanta yayi kafin ya dauke kansa ya mayar gabansa
"Me yasa kikace haka?"
"Kawai zuciyata na rayamin haka,kuma akwai tarin alamomin tambaya akan fuskarka data iman"
"Ba lallai sai kowa ne da kuka fito ciki daya bane take zama 'yar uwarka ai,ko suby'a a yanzu ta zama 'yar uwata,ko ba haka bama,musulunci ya kulla dangantaka ta 'yan uwantaka a tsakanin kowanne musulmi,bare inna da malam,inda akwai wani matsayi daya gota na uwa da uba,tabbas sun cancanceshi.....ko kinsan lamin ba kowa bane face almajiri?"
"Almajiri?" Ta tambaya cikin mamaki tana dubansa da kyau,saiya gyada mata kai ba tare daya waiwayo ba
"Yes,hala kinyi mistake da kika fara soyayya da almajiri ko?" Ya fadi wani ciwo na motsuwa cikin ransa na abunda ya shude shekarun baya can,murmushi ta saka
"Ko kadan,koda akwai matsayin da kake ganin yafi na almajiri muni ni bai dameni ba,kuma baya gabana,saboda muhammad al'ameen din gundarinsa nakeso" lafazinta ya sanyashi waiwaya ba shiri ya kalleta,lokaci daya yaji matsayinta ya qaru a ransa,a da yana wani hasashe da kuma d'ari d'ari a kanta,amma a yanzu ta wanke komai.
Kafin ya amsa mata iman ta qaraso,ta bude gidan baya daya side din ta shiga,suby'a ta amsa sallamar tata tare da yi mata sannu,yayin da samha a wannan karon batace da ita komai ba,lokaci daya wani kishin iman din taji ya kama zuciyarta da mugun qarfi,duk wata soyayya da kulawa da take qoqarin bata babu ita ta zagwanye,kishi ya maye gurbinta,itama iman din bata lura da wani sauyi daga samhan ba,saboda dama ba wai qaunar shishshigin da take mata take ba,ta tattara dukka hankalinta ta mayar ga window,tana kallon gine gine da kuma titunan da suke giftawa.
Kasa kasa take iya jin hirar da samha kewa amin,amma ba zaka iya jin me take gaya masa ba,idanuwanta ta mayar ta lumshe kawai,tana jin sautin bugun zuciyarta da qarfi,addu'a take sukai inda zata sauka ta fita a motar,don ko meye za'a bata ba zata yarda ta dawo a cikinta ba.
Bata tashi bude idanunta ba sai da taji sun sauka daga titi suna gangarawa zuw cikin wani layi,ta bude idanunta a hankali tana kallon unguwar.
Kofar wani gida ya tsaida motar,gidane mai bene hakanan mai girma tun daga yanayin katangarsa ta waje,yana da tsaho a fuskar gidan ma,gininsa a tsaye yake,ko ba'a gaya maka ba kasan masj gidan akwai abun,duk da yanayin ginin na nuna ya dan kwana biyu.
Suby'a ce tayi mata magana tana shirin fita
"Allah ya qara sauqi,sai anjima"
"Ameen,na gode" ta amsa da muryarta data cakuda da sanyi,tana sake maida kanta gefe
"Man....shikenan?,sai yaushe?" Samha ta tambaya a narke tana duban ameen,idanunsa na kallon gaban motar,yayin da ya yiwa sitiyarin motar qawanya da hannuwansa duka biyun
"I will see you soon"
"Ka tabbata?" Saiya jinjina kai wannan karon bayan ya kalleta
"Na tabbata"
"Is okay,byee,qanwarmu,Allah ya bada lafiya" ta fada tana kama murfin motar ta bude sannan ta fice,iman din ba zata iya tantance ta amsa mata ko bata amsa ba,illa dai tasan tayi qoqarin motsa labbanta,amma batasan sautin ya fita ko maqalewa yayi ba,samhan ta zagaya a hankali yana tsaye har zuwa sanda ta bude murfin qofar gida ta shige bayan ta tsaya tayi waving masa hannunta.
Shuru ya ratsa motar na wasu mintuna
"Taso ki dawo gaba" umarni ya fita kai tsaye daga bakinsa,umarnin daya sake tattaro dukka wani kishinta da bacin ranta waje daya,abunda ya matsa mata qwallar da take dannewa ta gangaro mata,sai tasa gefen hijabinta ta tsaneta,sannan ta bashi amsar da ita kanta batayi tsammani zata iya bashi ba
"A'ah,a nan zan zauna" shuru ya sake ratsawa na second biyar kafin taji ya saka hannu ya buda murfin motar,ya fito a nutse yana takawa zuwa side din da take zaune,hannu yasa ya buda murfin motar
"Fito" ya fada da dakakkiyar muryarsan nan wanda duk sanda yayi amfani da ita wajen yi mata magana......maganar ke shiga har cikin qashi da bargonta.
Kamar yadda yace haka taja jikinta a matuqar mace ta fita,ta bude gaban ta shiga,ya maida murfin bayan ya rufe,ya zagayo seat dinsa ya shigo ya maida mufin shima ya rufe.
Takure jikinta tayi gaba daya waje daya,tana jin wani mugun kusanci a tsakaninsu,zuciyarta na sake canza yanayim bugunta,qamshin turarensa ya mamayeta gaba daya,kai kace tayi mayafi ne da suturarsa,kwantar da kanta tayi saman cinyarta bayan ta rungume gwuiwoyinta cikin jikinta,tana fatan hakan xai bata dukka wani qwarin gwiwa da take nema,xai kuma hana hawayen dake idanunta zuba.
Tanajin sanda ya tashi motar,hawaye suka silalo mata masu dumi,wane irin hukunci ya ameen din yake mata haka?,saita kifa fuskarta kawai tana ta gayawa kanta cewa bai kamaci tayi kuka ba a yanzu,a jikinta takeji kowacce rana zuciyarta na sake samun rauni ne,raunin da ta tabbatar indai haka zata ci gaba da kasancewa......watan watarana zata gaza,zata gaza ci gaba da daukar komai.
Basuyi tafiya mai nisa sosai ba taji ya sake tsaida motar,ya fita ya zagaya seat din baya ya dauki kwalin maganin daya sulale a hannunta ya shiga pharmacy din dake gabansu,bai jima ba ya fito,ya sake shiga motar yana dan sauke numfashi sannan ya tada motar,dai dai sanda wayarsa ta dauki ruri,ya daga wayar ya sakata a handsfree yana ci gaba da tuqinsa
"Kana ta inane?" Muryar ya sadiqu ta cika motar
"Na fita maida baby......daga nan kuma zan shiga ayimin aski,bana jin dadin kaina haka" kalmar babyn tayi matuqar yiwa iman din zafi,ta runtse idonta gam tana ambaton sunan Allah
"Oh okay,yanzu zan qaraza gida nima,idan ka dawo ma jone"
"Ba case" ya amsa masa yana kashe wayar,saiya ajjiyeta a tsakaninsu ya maida dukka hankalinsa ka tuqin da yake,saidai lokaci zuwa lokaci wani abu na dan dauke masa hankali.
Ko qwaqwaran motsi taqiyi,har cikin ranta takejin kamar da biyu ameen din yake komai,ta yaya zai dinga pretending ne a kanta,bayan duk duniya shine mutum na farko dayafi kowa karantar zahiri da badinin zuciyarta,shin ina wannan karatun?,ko shina ya zagwanye tare da dukka soyayyar daya gwada mata a baya?,ko shima ya tafi tare da dukka wata qauna tata dake ran ameen din?,baisan wani irin ciwo me zafi yake dasawa ranta da rayuwarta ba,baisan yana kasheta bane deep inside her.
Katafaren gidan aski ne na isassun maza wanda ya amsa sunansa,koda sau daya ka dubi wajen kasan waje ne dake tafe da tsari da kuma ilimi gwanin burgewa,baya ga aski har manicure and pedicure,duk inda kaga yaje aski ko gyaran farce a kano to babu yadda zaiyi ne,yafi ganewa na nan wajen,ya cire belt dinsa ya buda qofa a nutse ya fice.
Tunda ya fita idanunta na alumshe,saidai qarar da wayarsa ta fara yi akai akai ya fara damunta,dole ta juyo da fuskarta a hankali zuwa sashe da wayar take wadda keta haske kiran na sake shigowa.
Sign na heart ne kawai ke blinking akan screen din,ta zubawa screen din wayar idanu,zuciyarta na ci gaba da bugawa a hankali,haka wayar taci gaba da shigowa tana kuma yankewa har kusan sau uku.
Tana shirin dauke idanunta don ragewa kanta bugun zuciyar saqo ya shigo a karo na qarshe maimakon kira
_"Nasan duk yadda akayi driving kake man,duk da na qiyasta for now yaci ace ka isa gida,hala kun tsaya wani guri ne, anyways..... take care of yourself"_
Wani abu me matuqar zafi cakude da bacin rai ne ya tasowa iman,me wannan matar ke nufi?,batasan waye ameen a wajenta ba?,koda babu komai batasan shi din yayanta bane?,batasan sunfi kusa ba?,kalamanta na nuni da tuhuma da kuma shakka a fakaice,saita daga hannunta a zafafe da niyyar kashe hasken wayar don ta daina ganin gilmawar saqon a idanunta,dai dai lokacin da ya bude motar,idanunsa ya sauka a kan wayar,kana ya janyesu ya maidasu kan fuskar iman,qwayar idonta ta shiga cikin tashi,saita janye idanun nata tana kuma qoqarin maida fuskarta daya side din dai dai sanda ya jefa mata tambaya
"An kirani ne?" So take ta cire masa shakkun abinda ya gani din,kada ya dauka damuwa tayi da wayar yasa har haka,saboda zuwa lokacin ya dauki wayar yana buda Tex din
"Kararta ce take damuna,am trying to mute the sound" murmushin gefan baki ya saki mara sauti,wanda ita kanta iman din bata ankara da hakan ba,shuru na wasu sakanni ya sake ratsa wajen da alama saqon yake karantawa,kafin daga bisani yace........
GIRMA DA KIMAR IYAYE TA WUCE WASA,A DUK SANDA KA SABAWA MAGANARSU KODA KA FISU GASIYA,INDAI BA KAUCEWA FADAR ALLAH BANE,KO YAYA...KO YAYA SAI KAGA BA DAI DAI BA,DUK WADDA TA ZABA IRIN ABUNDA IMAN TAYI,ZATA IYA GAMUWA DA SAKAMAKON DA YAFI NA IMAN,wallahi wallahi iman nata da sauqi,da Allah yaga dama sai ta hadu da cutar hiv din daga jikin bassam har qarshen rayuwarta,sabawa umarnin iyaye yana daga cikin gagga gagga laifuffuka da bai kamata ayi sakaci ko sasauci wajen fadakarwa a kansu ba,littafi yanzu ya zama kamar wani madubine da al'umma suke kalla su gyara wani abu da ba dai dai ba,Allah yasa mu dace
*please follow me on arewabooks*
HUGUMA
Add my story to your library for more latest pages
https:/arewabooks.com/chapter?id=62bff720a306c9b48f09f552
Thanks.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 49
"Fito ki duba cikin biyun wanne ne zai miki maganin,an samu different colors" ya fadi mata yana juyawa, trying to call number samha din.
Gaba yayi tana binshi a baya,tana jin sanda yake baiwa samhan excuse,tare da alqawarin kiranta idan ya gama abunda yake,tabi bayansa da kallo ta cikin hasken fitilun dake wajen,wani abu mai nauyi na sake ratsa qirjinta da zuciyarta.
Dab da zasu shiga wajen saiya rage saurinsa,harta cimmasa suka dai daita tazarar dake tsakaninsu sannan suka shige,babban store ne,wanda bayan magunguna suna saida abubuwa iri daban daban na ciye ciye.
Da hannu yayi mata nuni da area din magungunan suke,ta fara takawa a hankali tana shiga wajen,idanunsa na biye da ita,kafin daga bisani ya janyesu yana qoqarin dai daita kansa.
Tana duba magunguna amma kuma hankalinta na wani waje na daban,zuciyarta ta nace maimaita mata duk abubuwan da suka faru tun daga zuwan samha har zuwa tsaiwarsu qofar wajen
"Wow....wacce iriyar sa'a na taka yau din?" Da sauri ta waiwaya jin muryar data sani na magana,kuma daf da ita ake maganar,dr ahmad ne,yana sabe da wata baby girl wadda aka yiwa kwalliya dai dai gwargwado,gashinta yasha adon ribbons masu kyau.
Bakinta ta washe masa kamar yadda hake binta da murmushi,don dai ita din ba zata kira abunda tayi masa da sunan murmushi ba
"Dr,barka da dare"
"A'ah,ki barni na fara gaisheki mana hajjaju,banyi tsammanin ganinki a yanxu ba a wannan wajen,sai gashi Allah ya dubi idanun bawan Allah" murmushi ne yaso qwace mata ganin yadda yayi,ta miqa hannu don ya bata yarinyar tana cewa
"Zo baby....ya sunanki?" Ba qyuya kuwa yarinyar ta taho wajen nata,duk da batasanta ba,sai dr ahmad ya buda baki yana kallonta
"What?,lallai kin ciri tuta wajen milha" ya fada cikin mamaki,saita dauke idaunta daga fuskar yarinyar,wadda ganinta sak fuskar dr ahmad din
"Me kenan?"
"Bata yarda da kowa sai wanda ta saba gani,zaiyi wuya kiga taje wajen baquwar fuska" murmushi tayi kawai maimakon amsa maganarsa,ta rasa abun cewa don haka tace dashi
"Kana tana yawon dare kenan?" Da sauri ya daga hannayensa sama
"Rufamin asiri hajjaju,wallahi ba haka nake ba,kada a kashen kasuwa" murmushi ya kubce nata ganin yadda ya haqiqance har da saurin rantsuwa
"Maganin hajiya ne ya qare shine na fito nemo mata" saita gyada kanta tana ci gaba da yiwa yarinyar wasa,yarinyar taji ta burgeta,ta kuma kwanta mata a rai,duk da dama itadin mayyyar yara ce,saboda yadda ta taso itace qarama a gida,bata da qani ko qamwa,idanun dr ahmad a kansa,yana fargabar ya zamana wani ne ya kawota ba,ya hadiye abunda ke taso masa ya daure ya tambayeta
"Kefa?,Allah yasa ba 'yan overtaking bane sukayi overtaking din dani" qaramin murmushi ta maida masa itama,sannan ta amsa mishi
"Nima maganina na fito nema,ni da ya ameen ne"
"Oh... okay" sai taga kawai ya dauki kwando ya fara zuba daukan kaya yana zubawa,bata kawo komai a ranta ba,tunda tasan cewa yana da iyaye,sannan uwa uba mutum kamar dr ahmad din bazai kasa shigowa guri kamar wannan ba ya fita bai dauki komai ba.
Mintuna kusan takwas ya sake dawowa inda suke,ya cika kwandon da kaya
"Muje na biya kudi,daga nan sai mu gaisa da yayan namu ko?" Kamar tace mishi a'ah,sai kuma wani abu ya darsu a ranta,don haka kai tsaye tace masa
"Ok,ba damuwa" yaso amsar milha amma tace masa a'ah
"Ina ka samo baby ne me kama da kai?"
"Magana ce daya kamata ayita a nutse,bazan gaya miki komai akai ba,har sai randa aka bani dama nazo ni dake muka zauna sosai.....don Allah ki tausayamin ki gajarcemin wannan jiran da bansan lokacin yankewarsa ba" ya fadi yana marairaicewa,yanayin maganar tasa yasa murmushi kubce mata,dai dai sanda ameen dake tsaye yana jiranta ya daga kansa daga wayarsa da yake dannawa,idanunsa kuma basu sauka ako ina ba sai a kansu,kallon second uku yayi musu ya sauke kan nasa again akan wayar tasa,kamar bai sansu ba,ko bai gansu ba,yaci gaba da latsa wayarsa.
Daga can qasan zuciyarta taji wani dadi ya zarta mata kadan kan ganinsu tare da ya amin din yayi,duk da ba haka taso ba ace ya dauje idanun nasa da wurwuri haka,ta tsurawa fuskarsa idanu sanda suke takowa inda yake tsayen,zuciyarta cike da hope din ya sake daga idanu ya gansu taren,saidai kuma addu'arta bata ci ba,don har suka qaraso wajen tamkar baisan Allah yayi ruwan halittarsu ba,har sai da dr ahmad yayi masa sallama sannan ya daga kansa yana amsa masa,suka miqawa juna hannu.
Ci gaba tayi da satar kallon fuskarsa sanda suke gaisawa da dr ahmad,wai ko zata karanci wani abu na sauyawarsa ko kuma wani yanayi na daban,saidai duk qwaqwarta ta kasa gane komai,tilas ta kama kanta daga nacin kallon da take masa,qwaqwalwarta ta shiga searching,daga bisani ya karba milha daga hannunta,ya matsa kadan daga inda suke tsaye yana ta yiwa yarinyar wasa,sai kuma ya fara takawa a hankali yana komawa cikin store din,yana tafe yana daukar mata kayan wasa da sauran kayan ciye ciye na yara.
Bai tashi dawowa ba saida uban siyayyan kayan wasa dana ci kala kala,dai dai sanda aka gama yiwa Dr Ahmad lissafi ya kuma biya da cash,shima ya matsa aka lissafa ya basu atm dinsa suka cira,don bau wadataccen kudi a hannunsa.
Tare suka jero da dr din suna taba hira,saika dauka sunsan juna ne,hirace irin tasu ta maza data shafesu,tana biye dasu a baya,saidai gaba daya ya ameen din ya gama kwance mata duk wani lissafi nata da yayi saura,duk wata hanya da zata saka masa tarko ko kuma ta gane wani abu ya tosheta.
A seat din gaban motar dr ahmad din ya ajjiye yarinyar,ya kuma ajiye mata ledarta a gefanta,sannan ya sha sumarta ya cewa
"Byee baby"
"Byee uncle"ta amsa masa tana dariya tare da kada hannunta,ya maida murfin ya rufe mata,sannan ya nufi motarsa.
"Bamuyi haka dakai ba dr,yanzu nacewa ya ameen me?,kawai daga haduwa saika hau yimin siyayya,shi kansa ya amin din ai bazaiji dadi ba" iman tace da dr ahmad,wanda ya jajirce sai ta karba uban siyayyar da yayi da sunanta
"So nake innar dama ta tambayi waye ni,qilan hakan zaisa a bani damar bayyana kaina,amma maganar ya ameen na tabbatar bashi da matsala,muje kawai" yayi gaba riqe da ledar.
Tsaiwa tayi ta kasa binsa kamar an riqe mata qafafu,inda tasan haka zata faru da bata tsaya ba,tana kallonsa har zuwa sanda ya isa bakin motar amin din,ya zagaya ta window yayi magana,sai taga ya dage booth din motar ya saka ledar ya rufe,sanna ya waiwayo inda take tsaye,ya sakar mata murmushi yana daga hannuwansa biyu,alamun komai yayi dai dai,sai a sannan ta fara takowa a hankali kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki.
"Matsoraciya kawai,kina da yaya mai sauqin hali da kuma fahimta amma bakisan hakan ba" yafada yana dariyar tsokana,itadai bata iya cewa komai ba,sai yayi gaba ya bude mata murfin motar,ta zura jikinta a hankali,tana ji dama baya ya bude mata ba gaba ba,ya maida ya rufe yana cewa
"Na gode hajiya.......yallabai godiya nake" yaja da baya don ya bashi damar tada motar,kafin ya juya zuwa tashi motar.
Shuru shine abinda ya wanzu a motar,daga ita har shi babu wani da yake cewa da dan uwansa komai.
Inda so samu ne kuka takeson tayi ko zata samu relief,kuka irin sosai din nan,duk wannan abun da tayi tayi ne saboda ya ameen din,tayi ne di ta caje zuciyarsa ko zata tsinci wani abu da zai bata qwarin gwiwa,saidai da alama babu komai a ciki da yake da nasaba da ita,hawayen sun taru ta maidasu har batasan adadi ba
Wani tuqi yake ba irin wanda yayi daxu ba,ya qara speed na motar fiye da dazu sosai,hakanan ya tattara hankalinsa da idanunsa kan titi fiye da dazun dai,a haka suka qarasa gida,yayi parking sannan ya kashe motar
"Ki daga booth ki kwashe tarkacen can.....don idan kika barsu zanyi sadakarsu ne" wani kallo ta watsa masa da yafi kama da harara,yau inda akwai wasa tsakaninsu saita yaba masa maganganun da wala'alla zuciyarta zata sassauta,bata taba yardarwa kanta ameen kwata kwata bata gabanshi baya kishinta ba sai yanzu,qafafuwanta suna rawa ta soma takawa cikin gida ba tare data tsaya diban kayan ba,saboda hawayen da taketa riqewa daya balle mata.
A zafafe shima ya fita daga motar yabi bayanta,taku hudu qwarara ya cimmata ya kuma sha gabanta,cikin wani irin zafi yake duban fuskarta
"Abokin wasanki ne ni?.....nace ki kwashe kayanki ki taho kibarsu cikin motata?,inyi me dasu?" Ya fada cikin muryarsa da tayi nauyi,take kuma cike fal da fada.
Gudun hawayen fuskarta suka qaru,sai kuma a sannan ya lura dasu,sassauci ya sauki saman fuskarsa ba kamar dazu ba,yaja numfashi yana qoqarin danne kansa
"Wadan nan hawayen kuma na meye su?,me akayi miki?" Yafadi yana hade girarsa waje guda,qas tayi da kanta ba tare data iya cewa dashi komai ba,tsahon wasu sakanni sannan ta bude baki a hankali
"Ciwon kaina ne ya dawo" idanunsa ya dauke daga kanta,daga can bakin qofa ya hangi sayyadi,yaron da malam ke aikowa gidan wasu lokutan ya kawo sakonni,cikin kaurin murya ya kira yaron,ya qaraso da hanzari a ladabce,saiya nuna masa motar
"Jeka ka bude bayanta zakaga leda ka daukota gaba daya"
"To" ya amsa mishi yana juyawa.
A hankali ya dauke idanunsa daga kan yaron ya maida fuskar iman din,sai ya hade hannayensa a qirjinsa ya zubawa fuskar tata idanu yana iya ganin yadda hawaye yake diga yana faduwa qasa,kallonsa yana da matuqar dafi da kuma tasiri a jikinta da zuciyarta,saiya qara mata wani weakness daya sanya ta kasa dogara da kanta sai data jingina da bangon hanyar da zata sadaka da parlor din,ta kuma boye fuskarta cikin hijabi.
Dawowa sayyadi yayi da ledar a hannunsa,ameen ne ya karba ya ajjiyeta a gefe,taku uku ya qare ya rahe tazarar dake tsakaninsa da iman din,yatsaya gab da ita sosai,cikin wani irin lallausan murya yace
"Yanzun ciwon kan kikewa kuka haka?" Batasan me zatace dashi ba,shima bai jirayi amsarta ba yace
"Ki qoqari ki tsaya haka,don ciki zaki shiga,ni kuma ba zamu shiga tare ba kina wannan kukan inna ta dauka wani abune ya faru" sai ya saka hannunsa a karon farko tsahon rayuwarsu yaja hijabin data duqunqune fuskarta dashi ya fara qoqarin wareshi.
Kam ta riqe hijabij,qaramin murmushin da iyakarsa fatar baki ya saki,ya gwada mata irin nasa qarfin,tashi guda ya cireshi gaba daya,har hakan ya kusa haifar da fadawarta jikinsa,saidai ya tareta da hannunshi kana ya matsa baya.
Hannayensa ya zuba a aljihun wandonsa yana kallonta,ya tsare gida sosai kamar bashi ba
"Zagaya muje ta bayan gida" ya bata umarni kai tsaye,dole kayi shakkansa yadda ya sauya fuska lokaci guda,ta fara takawa kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki shi kuma yana biye da ita suka bi ta hanyar bayan gidan.
Saida yasa ta wanke fuskarta a bakin famfon wajen,ya miqa mata handkerchief dinsa mai cike da sassanyan qamshi ta dauke danshin fuskarta dashi sanna ya mata nuni data wuce,ta taka a hakali zuwa ciki ya rakata da idanunsa.
Babu kowa a parlor din sai tv dake aiki,ta qarasa cikin qarfin hali ta kasheta,sannan ta nufi dakin inna,labulen tadan daga kawai ta gaya mata ta dawo,zata wuce tasha magani ta kwanta,innan tayi mata sannu ta zarce dakinta tana jin sanyi cikin ranta na yadda innar bata ga fuskarta ba,kota kan kayan da suka baro waje bata sake tunawa ba,tabi lafiyar katifarta bayan tasha maganin tana sauke ajiyar zuciya,taji relief a cikin zuciyarta qwarai,hakan kuma bai rasa nasaba da dan caring da ya ameen ya nuna mata,duk da bai taka kara ya karya ba,ta rufe idanunta tana hango yadda lumsassun idanunsa suka bude da kyau sanda ta kusa fadawa jikinsa ya kuma ja baya da sauri,saita sauke ajiyar zuciya tana tura kanta qasan pillow.
[7/19, 10:02 PM] Mummyn Yara: 50
Da gaske ta dinga yaqi da zuciyarta cikin kwanakin don ganin ta samarwa da zuciyarta nutsuwa,saboda yadda takejin yanayin jikinta komai zai iya faruwa da ita.
Duk wata hanya da zasu hadu da ita tayi qoqari ta tosheta,saidai duk da hakan bata tsira da jin muryarsa da kuma tunani da zuciyarta ke yawan kawo mata,wanda take yaqi qwarai wajen kawar da wannan,saidai kusan a banza wai man kaza,data kore tunanin batasan lokacin da zai mamayeta ya dawo ba.
A haka ta dinga juriya tana dannewa,tayi qoqari ta maida hankalinta kan karatunta,saboda karatune da ko yaya damuwa ta shiga cikinsa sai kaga ba dai dai ba,hakanan tana shekarar qarshe,kada ya rage mata ta zama cikakkiyar nurse.
*********Safiyar wata lahadi,a ranar bata da wani uzuri da zai fiddata waje,don haka bayan ta gama komai na ayyukan gidan tayi wanka ta sake komawa ta kwanta,babu jimawa barci ya debeta.
Can cikin barci yunwa ta tasheta,ta sauko a hankali daga gadonta,ta miqe ta shige toilet,bakinta ta sake wankewa ta dauraye fuskarta ta tsaneta da towel sannan ta fito,ta jawo hijab dinta iya gwiwa ta zura,saboda yau din weekend,tasan ba za'a rasa mazan gidan a kusa ba.
Parlor babu kowa,saidai tana iya dan jiyo muryoyi daga parlor din malam,sai ta zarce dakin inna taga ko zata sameta?.
Bata ciki,ba kowa ma a ciki,ta dan kalli dakin,sai taji ya kamata ta sake kintsa mata shi,duk da atsaftace yake,amma wasu kayan ba guraren daya kamata a ajjiyesu kenan ba.
Ta rufe dakin tana juyowa sukayi kacibus da inna
"Yanzu na dubaki ban ganki ba"
"Eh ina wajen malam,muje ciki dama inason ganinki" gaban iman din ya fadi,saboda a yanzun babu abinda taqi jini irin ta batawa inna ko malam rai,tun bayan kuskuren data tafka a baya,jikinta babu qwari tabi bayan inna.
Atsaye ta sameta tsakar dakin
"Wannan kayan na waye?,tun rannan sayyadi ya shigo dasu,yanayin jikinki yasa ban miki zancansu ba,na manta dasu ma a dakin sai daxu ina neman wani sabon rawanin malam" idanunta takai ga ledar,gabanta ya sake faduwa,ta tuna da ita,shaf ta manta da ita sai yanzu,ta dubi inna taga yadda ta tsareta da idanu,koda bata yi mata hakan ba babu wani 'yar boye boye tsakaninta da inna,tayi wannan alqawarin daga sanda mai faruwa ta faru,har zuwa randa ita ko innar wani zaibar wani a duniya
"Dr ahmad ne ya bani"
"Wayeshi?" Ta tambayeta yanayin fuskar innar yana sauyawa
"Likitan dake dubani tun ina gidan bassam,ranar dana fita siyo magani muka hadu dashi a store din"
"Kina nufin a gaban aminu?,kuma ya sani?" Kai ta gyadawa innar a sanyaye,shuru ya ratsa dakin na kusan minti guda
"Shikenan,kije,dama malam yace yanason ganinki" gaba daya sai gabbanta suka saki,ta kasa motsawa,ta kuma kasa hadiye tambayarta sai data jefawa inna ita
"Malam kuma inna,wani laifin nayi?" Kallonta tayi,sai taji tausayinta ya tabata,don haka tayi mata murmushi
"Babu wani laifi,shikenan babu ganawa ko tattaunawa tsakanin uba da diyanshi sai ya zamto wani laifi suka aikata masa?" Ajiyar zuciya ta sauke,ta samu relief yanzu,don haka ta juya ta fita a dakin innar,innar ta bita da kallo a sace harta qarasa fitar,saita sauke ajiyar zuciya,ta laluba gefan gadonta ta zauna tana fadin
"Ya Allahu,ya Allah ka shiga wannan lamari,Allah ka kawo mafita ya rahman,Allah kai kasan yadda zakayi da bayin nan naka,ya Allahu" murya qasa qasa,qafafunta gaba daya sunyi sanyi,ta jima a zaune kafin ta miqe ta shiga abunda ga kawota dakin.
Yankewa tayi kawai ta fara shiga kitchen ta samu wani abun ta toshe yunwar dake sakadarta kafin ta wuce wajen malam din,haka kuwa akayi,ta biya ta can ta hada tea tasha,ta samu ragowar soyayyan qwai tana murmushi ta fara gutsira tana ci,da alama na mufida ne,sabida tafi kowa son soyayyen qwai a gidan,tadanji cikinta yayi mata dai dai sannan ta wuce wajen malam din.
Tun kafin ta shiga rumfar malam din ta fara jiyo muryarsa mai cike da nutsuwa da taushi,da alama wani bayani yakewa malam din,ta tsinci kanta cikin faduwar gaba kamar kowanne lokaci,ta zuqi iska sosai sannan ta fesar,ta tabbatar shigarta parlor din sai yabar baya da qura,basu taba hada wajen zama dashi ba bata tsinci zuciyarta cikin wani sabo kuma mahaukacin sonshi ba,abun kamar jarrabi a gareta,haka ta tattaro dukka wata jarumta da juriyarta ta yaye labulen tare da yin sallama.
Idanunsa ya dauke daga kan paper din dake hannunsa ya saukesu a kanta,ya motsa labbansa yana amsa sallamar tata kafin ya janyesu ya sake maidawa kan takardar gami da dakatawa da bayanin da yakeyi.
Tun hada idanun da sukayi dashi karo na farko ta janye daga kallonsa,tun kuma a sannan ya sakar mata wasu dafi masi qarfi xuwa kowanne sashe na jiki da zuciyarta,yayi azabar kyau cikin shadda wadda aka yiwa wani irin dinki,yar ciki me dogon hannu da wata daga sama kamar top,taji aikin hannu da zare mai kauri,dinkin ya zauna masa kamar yadda shaddar tayi bala'in tafiya da qirarsa da kyan surar da Allah yayi masa,sumar kansa a kwance sai qyalli takeyi,kwanakin data dauka bata ganshi ba sai taga kamar an qara masa kyaune,wani abu mai sanyi ya ratsa zuciyarta,idan hancinta ba qarya yayi mata ba qamshinsa ne kawai cike a falon,wani sihirtaccen qamshi da batasan da wanne kalar turare yake amfani ba,tun yana lamin dinsa asal qamshinsa na dabanne,gwani ne wajen iya zabar kalar turare
"Maraba da autar inna,hajaratu ayar Allah" malam ya tsokaneta da suna da kuma salon da a baya yake tsokanarta dashi,murmushi ta saki,saboda abun yayi mata dadi sosai,abune data jima rabon data jishi daga bakin malam din,wannan dalilin ya sanya ta zabi zama kusa da malam din,saita zarce mazauninsa,ta zauna dai dai qafafunsa a qasan carpet ta soma gaidashi.
Cikin kulawa ya amsa mata,ta maida dubanta ga lamin
"Barka da safiya" hankalinsa na kan takardun gabansa ya amsa mata,hakanan ya sadiqu shima takardun dai yaketa dubawa yana shiryasu.
Ita d malam suke dan taba hira,yayin da sadiqu da amin din suka karkata da hada takardun,suna kuma dan musayar maganganu a tsakaninsu,duk da hirar da suke da malam din amma hankalinta na kanshi,a sace take kallonsa ta gefan idonta,glass din da ya sanya a yau din ya qara masa kyau da kwarjini na musamman,ta yarda sanya abu ma ya karbeka baiwa ce,shikam yana daga cikin baiwarsa,tun zamanin da yawancin suturunsa ma ba masu tsada bane,bare yanzu da kudade suka fara zaunar masa.
Ta lura da yadda wayarsa keta haske yana kasheta,da alama kira ne yaketa shigowa,sai taji rata ya raya mata samha ce,take zuciyarta ta jagule,karo na qarshe yadan saki siririn tsaki ya kashe wayar gaba dayanta wanda cikin rashin sa'a ya kamata tana kallon nasa,da wani mugun hanzari ta dauke kanta kamar bashi take kallo ba,tana iya jin siririn murmushi mai qaramin sauti daya fitar,yaci gaba da aikinsa.
Kusan mintuna talatin sannan suka kammala
"Komai yayi dai dai,rana kawai mukeso malam ya sanya mana da za'a bude company din" alamin ya fada a ladabce da nuna tsananin girmamawa,daya daga cikin abubuwan da suka sanya malam din yakejin bala'in so da qaunar alamin din,wani irin yaro ne da Allah ya zuba masa sanin ya kamata,mai matuqar ladabi biyayya tausayi da kuma girmama na gaba,ba shakka duk da iyayensa basu mori komai daga kyakkyawar haihuwar da sukayi ba,amma kuma sun barwa duniya kyakkyawan iri abun misali,mutane da yawansu basusan ba malam bane ya haifi lamin din ba,sai dalili ya kawo,kai malam din ya jinjina
"Ina ganin mu barwa ranar juma'a ko?,bayan saukowa daga sallar juma'a,tunda kace akwai masallaci daura da ma'aikatar"
"To Allah ya kai mana rai da lafiya" ya amsa a ladance
"Ameen ameen" malam da sadiqu suka amsa
"Sanna kuma...." Ya sake magana yana motsawa
"Akwai wani abunda na soma nema yanxu haka,shirye shirye nason bude compy na saida spare parts na motoci da kuma maida tsofaffin motoci zuwa sababbi wanda nake saka ran sadiq zai ja ragamarsu,abun yana da wahala ne malam da kuma buqatar kudade,to amma kuma cikin ikon Allah da muka fara aiki kan abun,sai komai yake zuwa mana da sauqi,mun samu manyan mutane da suke da sha'awa kan abun,kuma zasu zuna share dinsu,yanzu haka muna saka ran nan ba da dadewa ba shima za'a gama komai yafara aiki"
"Allahu akhbar,Alhamdulillah,mun godewa Allah,ubangiji ya qara sanya albarka cikin lamuranka kai da 'yan uwanka,ba shakka wannan babban abun alfahari ne a garemu.....ke hajar,kiramin innarku" ya fadi yana duban iman,tarin walwala da farincikin dake saman fuskarsa ba zasu misaltu ba.
Ko minti daya bata cika ba inna ta shigo,ta ajjiye wasu kwanuka gaban malam din,ta koma gefe daya ta xauna tana sauraren bayanan malam.
Ita kanta kasa boye murnarta tayi,tayi musu addu'a sosai tare da fatam samun nasara kan duk wani abu da suka sanya a gaba.
"To ku bani hankulanku nan,akwai muhimmiyar maganar data sanya na buqaci ganinku,na kuma taraku a nan....." Sanun cewa duk sada malam din yayi haka magana me muhimmanci zaiyi yasa kowa sake shiga nutsuwarsa,suka kuma zubawa malam din idanu suna jiran abunda zai fita daga bakinsa.......
*afwa da qaramin page,nayi busy ne👏🏾👏🏾*[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: "Alhamdulillah.....Alhamdulillah,mungodewa
Allah da yadda rayuwa tayi da kowannenku,kuma
ubangiji gayi muku baiwa da kyauta wadda ba
kowane ya samu kwatankwacinta ba...….ya zuwa
yanzu kowanne ya samu duk wani rufin asiri na
rayuwa,ya kuma samu madogara da madafa
koda babu ranmu,abu guda daya ne ya rage
muku,ku dukka ukun kun isa kun kuma kai
munzalin daya kamata ace kowa nada aure a
cikinku......" Matsananciyar faduwar gaba ta
saukarwa iman,jin malam ya ambaci kalmar
aure,uwa uba kuma cikin jawabin nasa harda
ita, kenan ko meye zai fito daga bakin malam
din.……kowanne irin hukunci ne ya shafeta?,harda
ita a ciki kenan?,take taji gaba daya jikinta ya
saki.tafin hannaventa dana gafafunta sukayi wani Saki,tarn hanhayenta dana q'dravunta sukayiWanl
irin sanyi,saita fara murxasu tana addu'a cikin
ranta, ko meye zai fito daga bakin malam
din,indai maganar aure ce Allah yasa a tsameta a
ciki,ta maida hankalinta tana son jin qarashen
bayaninsa
"Dukkaninku kowa yana da sukunin ajjiye
iyali,gurin zama da sana'ar yi,sannan hankali a
yanzu ya game kowa a cikinku……..kema kuma kin
qara hankali,a yanzuk kinsan dai dai,kinsan ba
dai dai ba, kinsan me ya kamata, kin kuma san
abinda bai kamata ba,saboda haka,inaso kowa a
cikinku ya gabatar min da wanda zuciyarsa ta
kwanta masa dashi,duk da dau na fara samun
labarai daga wajen innarku,amma inason naji ta
bakin kowa"
Shuru ne ya ratsa parlorn,aka rasa wanda zai
fara magana a cikinsu,iman dai kanta na
qasa,yayin da lamin iya nashi idanun ni a
qasa,yana caccaka yatsansa cikin carpet din qasa,yana caccaka yatsansa cikin carpet din
dakin, fuskarsa babu yabo babu fallasa,sadiq
kuwa sai faman shafa sumar kansa yake yana
murmushi
'"Waye babba a cikinku ne?,ya fara magana"
malam ya fada ganin alamun jin nauyinsa sun
bayyana a fuskokinsu
"Nine" sadiqu yayi hanzarin fada,abunda yasa
lamin daga kai,ya jefeshi da harara kai
tsaye,murmushin fuskarsa kuma ya dara na dazu
"Mara kunyar banza, mayen aure kawai"
"Babu komai,ni ai tawa maitar ce ta fito fili,amma
dai na tabbata bankai wanda kusan duk asuba
kafin ya tafi sallah sai yayi wanka ba"harara, auk magandr dd sukdy Can gas sukdyI,la
yadda babu mai iya jinsu,saika dauka wani abun
suke tattaunawa,lamin din baisan duk abinda ke
faruwa dashi sadiq din yana sane ba sai
yanzu,tabbas badon su malam na wajen ba sai
yakai masa mugun naushi
"To malam babba,muna saurarenka" malam ya
fada yana crossing qafafunsa waje guda,qas yayi
dakai yana sake shafa kan nasa
"Eh....ni sunanta fatima,gidansu yana unguwar
dorayi,sunan mahaifinta alhj usman"
"'Ma sha Allah,ka rubutan cikakkem address da
komai,zan sanya ayimun bincike akanta kafin ka
shaida mata ta gayawa iyayenta su saurari
zuwanmu.
"'In sha Allah" sadiq ya furta kansa a "To... kaifa malam aminullahi" malam ya furta
yana murmushi,idanunsa akan lamin
din,hakanan zuciyarsa,wadda ke cike da fata da
buri,duk da jikinsa yana bashi abune mai wuya
gurguwa da auren nesa inji bahaushe,koda
burinsa da fatansa basu samu tabbatuwa ba
bayajin cewa hakan rashin kyautawa ne face
tsantsar adalci da zai gwada masa. Ba malam kawai ba,hatta da inna idanunta
akansa suke,duk da tana kallonsa ne afakaice,ta
yadda babu lallai ka gane kallon nasa take kai
tsaye,haka kawai ta tsinci zuciyarta na bugawa
fiye da yadda ta saba buga matan,itama nata
idanun cike suke da fata da kuma burin,burin da
itama rashin tabbas yafi rinjaye a cikinsa,iman
kuwa......gaba daya rinse idanunta tayi,tanajin
inama ace mallam bai gayyaceta wannan waje
ba,inama ace ita daya ya kebe?,saidai amsar data
fito daga bakinsa zuwa ga malam ta sanya taji
gaba daya jikinta ya dauki rawa, kamar wadda
aka yiwa wanka da ruwan qanqara "Sunanta samha,mahaifinta alhj mutallab
garba,a unguwar court road take,nan wajen
tudun murtala,duk wanda ya nemi gida
mahaifinta zaa kaishi har can" Nannauyar ajiyar zuciya inna ta sauke tana
saukar da idanunta qas, wani abu na son rige
zuciyarta amma tana yaqi dashi,cikin taimakon
Allah ta kawar dashi,saidai zuciyar gaba daya taqi
karbar yanayin da lamin din yazo dashi,saidai a
hakan tana gayawa zuciyar tata,dole ta rusuna,ta
kuma karbi dukkan abinda lamin din yazo dashi a
matsayin zabi hannu bibbiyu.
"Ma sha Allah,alhamdulillah" malam ya fada
wani nauyi yana cika muryarsa,yana kuma rage
armashi da karsashin maganarsa "Kai bani da matsala, unguwar tasu ina da aboki
acan,malam gambo,zan masa magana akai,idan
ya kammala zan shaida maka kaima ta shaidawa
iyayenta"
"Allah ya qara girma da lafiya" lamin din ya amsa
yana russunar da kansa ga malam
'"Amin amin" ya amsa yana waiwaya gefen iman
"To nazo kanki auta" yayi furucin yana
murmushi,saidai kiranta da malam din yayi wani
nauyi taji ya hau kanta,tanajin kamar gaba daya
mutanen duniya aka tara mata suke kallonta
suna kuma sauraren ta basu amsa game da wani
in baracu tanail a
suna kuma sauraren ta basu amsa game da wani
gagarumin al'amari daya tunkarosu,tanaji a
ranata da zuciyarta wanna shine titsiye mafi
wahala da kuma fargaba da zata fuskanta tsahon
rayuwarta
"Waye shi?,a ina kuma yake?" Malam ya jefa mata
tambayar da shi kansa yasan babu lallai a samu
cikakkiyar amsa daga bakinta,tunda dai bai taba
jin anyi zancan wani cikin gidan ba tun bayan
fitowarta daga gidan bassam,kuma shi shaidane
na yadda take barin samarin nata a waje,wani
lokaci sadiq yake sawa ya sallamesu. Yatsanta takeson ta motsa wai don ta tabbatar
qwaqwalwarta na aiki kuwa yadda ya
kamata? idan tana aiki wa zata kira sunanshi ta
gabatarwa da malam shi?,wa take saurare?, waye
ta bawa damar da suka fahimci juna da zai iya
tsayawa a mizani da ma'aunin mijinta?,idan duka
ya cika wadan nan yana da gurbi a
zuciyarta?,gurbin da zai bashi damar zama
mijinta?,ta zauna dashi cikin soyayya qauna da
kulawa?,sam!…...duka biyun babu ko daya da
wani da namiji zai samu daga gareta. Akwai dimbi tulin tarin masoya,saidai babu
wanda ya samu koda taku daya na fili a zuciyarta
da sunan tana so qauna ko jin shaugi a
kansa,mutum daya ne dai tak!,wannan wanda
yafi kowa sanin wacece ita duk duniya.......wanna
wanda yafi kowa sanin ciwonta!..
......wannan
wanda baya ga iyayenta shi daya zai iya tsaiwa ya
gayawa duniya wace ita ya kuma tabbata
hakanne!….
...Wanda koda yayanta da suka kwanta
ciki daya,tanajin bashi da wannan qwarin gwiwar
da kuma cancantar.
„.shine dai kuma mutumin
data butulcewa!…
„..butulci mafi munil,ta karya
zuciyarsa!,ta iya kallon tsabar qwayar idanunsa ta
shaida masa BANA SONKA! ,ALLAH YANKIYAYE NA
AUREKAI,DANA AUREKA GWARA NA KASHE
KAINA!,ta zame masa KUFAN WUTA!,ta tafi ta
barshi da tarin tabo da ciwo!,ta zabi waninsa,waninsa din da baisan ciwonta ba,ta
kasa waiwayarsa,zuciyarta ta dode,ta kasa tuna
komai,ta kasa tuna wayeshi a tare da ita,taji masa
mummunan ciwon da ba kasafai masoya ke
warkewa ko su mata ba.....shin a yanzu,a dalci ne
ta tsammaci samun juyowar soyayyarsa
gareta,ko kadan. Take kwanyarta ta fara mata
hasashe da laluben cikin masoyanya dake
karakaina,wadanda suketa turo da applications
nasu waye ya cancanta?,wa take gani ya kamaci
ta gabatar da sunansa?, waye zai hau mizani ko
nagartarsa zata iya maye mata koda kwatar
kwatar wannan babban gibi?
"Dr Ahmad" ta samu kanta da furtawa ba tare
data gama tantancewa ba,ita kanta sai da sunan
ya fita sannan ta tsaya tuhumar kanta,yaushe ta
bashi damar da yaketa nema akan zuwa ya
sameta su tattauna har suka gama fahimtar juna
Ladaamanchi7tamhavar data dashi?,da har zata bada sunanshi?,tambayar data
sake sauke duk wata gaba ta kuzari datayi saura a
jikinta
"Wayeshi?" Malam din ya tambayeta kanshi tsaye
idanunsa a kanta,zuciyarsa nata fadin inama
inama.…...saidai dole abar komai a yadda yazo,yafi
tunanin haka Allah ya tsara,bayason yiwa kowa
shishshigi cikin al'amarinsa
"Likitan da nake gani ne"
"Kin tabbatar?" Ya jefa nata tambayar dashi
kansa yasan bata gama cika ba,yana fatan ko
yaya ne hankalinta yakai kai
"Eh" ta amsa tana gyada kai,tare da bawa kanta
qwarin gwiwa.
"To ba laifi, ki bawa wani cikin yayunki address
dinsa da komai da komai,ubangiji ya zaba mana
abunda yafi alkhairi,Allah yasa kuma dukkaninku su zamto silar qarin arziqi da shiga aljannarku"
"Amen" muryoyin mutum uku suka amsa,banda
iman da bata gama tantance wanne hukunci ta
yankewa kanta ba,me kyau ne ko mara
kyau,waye dr Ahmad a badininsa,meye
halayyarsa,duka bata sani ba,illa dai tasan kawai
ta bawa malam sunansa. addu'a malam din yasa
alameen ya rufe musu da ita,zuciyarta ta dinga
bugu kamar zata faso qirjinta sanda daddadan
muryarsa mai taushi ke fita cikin sautin addu'ar
da yake karanta ga da harshen larabci, murya ce
mai tarin daraja da muhimmanci a wajenta,iya ita
kadai idan taji yana saukar mata da wata
nutsuwa,saidai a yau jin muryar ya haddasa mata
tara qwalla mai yawa cikin idanunta,tana kuma Tuna mata da cewa tayi bankwana da zama mammallakiyar me murya da dame ita sun kusa zama malamin wata A sanyaye inna ta taso daga inda taje zaune bayan malam ya sallamesu,ta qaraso inda ta
ajjiye kwanukan abincin malam din ta fara
budesu a nutse,ta zuba komai yadda ya
kamata,sai ta koma ta zauna wajen,
Kallonta yayi,kamar zaiyi magana sai kuma ya
fasa,ya dauki kwanon abincin,ya saka hannu
kamar yadda ya saba yayi bismillah ya fara ci.
Kasa hadiye abunda ke ranta inna tayi,gani
take kamar ba yanzu malam din xai gama cin
abincin ba,kamar baya sauri,sannan uwa uba
yanayinsa bai nuna zaice komai ba
"Malam…..….kagayadda abun ya kasance ko?" Kai
ya gyada
"Eh,Allah ya sanya hakane yafi alkhairi" sosai
fuskarta ta nuna damuwa "Amma malam shikenan kuma?,me yasa ba zaka
ankarar dasu ba?,me yasa ba zaka qarasa aikinka
ba?" Tsame hannunsa yayi daga abincin,ya
ajjiyeshi a gabansa, murmushin dake cike da
kamala dattako da dattijankata ya subuce masa
"Ashe duk abubuwan da akewa hajar ana sonta
har yanzu?" Kai ta karkada,tasan malam din yana
sha'awar tsokanarta ne kawai, banda haka har
akwai wanda ya kaishi son iman din,da rashin
son ganin abunda zai zama illa ko aibu ga
rayuwarta,maida dubanta tayi gareshi ba tare
data iya bashi amsa ba,shima a sannan fuskarsa
ta koma serious
'"Duk yadda kikai ga son ganin iman da amin sun
zabi junansu baki kaini ba binta,kullum ko a dare
ko a rana idan na saka goshina a qasa,ad du'ata ko a rana idan na saka goshina a qasa,addu'ata
itace,ya Allah idan da alkhairi a tarayyarsu,idan
har tarayyarsu zata zama wani sabon mataki
kuma tsani na dorewar zumunci da ganin
mutuncin juna muda 'ya uwan aminu Allah ya
qulla,idan kuma har tarayyar tasu zata haifar da
sharri,yankewar zumunci ko tabarbarewar
al'amura,Allah ya hada kowa da rabonsa na
alkhairi.
.…..ta iya yiwuwa ubangiji ya duba cewa
babu alkhairin,shi yasa ya aiko da abun a
haka,…...idan mukace zamu matsa ko mu takura
to tabbas zamu yiwa Allah shishshigi ne,sai ya
qyalemu da iyawarmu muyita shan wahala,kuma
bugu da qari shi kansa yaron bamuyi masa adalci
ba,a baya bamu iya tanqwara diyarmu ta aminta ba,a baya bamu iya tanqwara diyarmu ta aminta
dashi ba....sannan kuma a yanzu shi zamu
dubeshi muce ya auri diyarmu?,bayan ina da
tabbacin ko ruwa mukace ya fada zai fada babu
musu?,ba dai dai bane wanna,saboda haka, mu
tattara muci gaba da gayawa Allah,da kuma
addu'ar zabi mafi alkhairi" .
Kai inna take jinjinawa,ta yarda ta kuma gamsu
da bayanan malam,babu son rai ko son zuciya a
cikinsu ko kadan,hakanan sun sake saukar mata
da nutsuwa,saboda haka ta dai data kanta,tare
da fadin "Ubangiji yayi zabi mafi alkhairi"
"Amen bintu" sunan da ya saka inna sakin
murmushi,shi kuma ya dauki plate dinsa yaci
gaba da cin abincin,yana kuma janta da hira.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 52
Empty take jin qwaqwalwarta sanda take takowa daga parlor din malam zuwa dakinta,fayau take jinta kamar wadda ke tafiya saman iska,kwanyarta kamar an share mata komai,ba zata iya tantance a wanne yanayi take ciki ba.
Tana saka qafa a dakin wayarta dake charge ta dauki ruri,ta ja qafafunta zuwa inda wayar take,don dama tana da buqatarta,ta riga ta sani,malam din baya daukar magana biyu,don haka tunda ta furta dole tasan yadda komai zai tafi.
Dr Ahmad shike kira,tamkar yasan dambarwar dake faruwa a kansa,taja da baya a hankali kamar zata zube a qasa,sai kuma Allah ya taimaka ta samu gefan gadon ta zauna,ta latsa wayar dai dai lokacin da take dab da katsewa.
Ajiyar zuciyarsa ce ta fara sauka a kunnuwanta,kafin daga bisani yace
"Ni kadai nasan damuwa da kuma dimuwar da nake shiga,duk sanda na kwadaitu da son jin muryarki,na taki rashin sa'a baki daga kirana ba"
"Duka wannan ta qare, finally iman na gayyatarka zuwa gidansu a yau" sak yayi a wajen kamar wanda jinin jikinsa ya qare,daga wayar yayi ya kalla,ya kuma tabbatar iman din ya kira,amma duk da haka.....mamakin da ya shiga yasa ya kasa shuru
"Idan wasa kikemin,ki tamakeni ki gayamin,kada sai daga baya,saboda wallahi zuciyata ba zata iya daukan wannan wasan ba"
"Mun taba irin wannan wasan dr?"
"Ko kusa"
"To kana iya daukarsa duk yadda kaso,either ka daukeshi da wasanne ko kuma ka daukeshi a gaske" saita zarta yatsunta ta shafe wayar ta kashe,ta kuma zame a hankali ta kwant a wajen.
Jinjinawa girman katobara da kuma aika aikar da take shirin yiwa rayuwarta tayi,tasan cewa ba komai ta aikawa kanta da kanta ba illa wani dan qaramin ta'addanci da zai iya zama silar wargajewar dukka wani farinciki a rayuwarta na din din din,ko sau daya bata taba jin dr Ahmad a koda gefan zuciyarta ba.....kai bama shiba,tana jin hakanne akan kowanne da namiji illa halitta daya,abu daya ta sani shine,tana matuqar ganin girma da kimarsa,saboda kasancewarsa nagartaccen mutum,hakanan kuma nutsatstse ne,bashi da makusa tako ina,saidai ita zuciyarta ba wannan take hange ko kuma kalla ba,duk wani bugunta da fitar numfashinta qwalli daya tak tana kiran al'ameen ne,saida shi din yayi mata nisan kiwo,nisan dake alamta mata bazaiji kiranta ba.
Idan taqi zaben dr ahmad hakan bazaisa malam ya qyaleta da zancan aure ba,idan bata zabi dr ahamd ba batasan kalar wanne zata zaba ba,qila a sannan babu me quality dinsa ma sam a kusa.
Waiwayawa tayi tana duban tex din daya shigo wayarta dava dr Ahmad
"Godiya tayi kadan wajen bayyana miki farincikina da kuma yabawata da karramawar da kika yimin a yau,ki zuba idanun ganina,ki kuma tanadi wanne kalar tukuici zan baki" rufe wayar tayi haskenta ya bace daha screen din,ta lumshe idanunta kana ta maidashi wani side din cikin rashin sanin madaafa.
Wata iriyar juriya da dakiya ta ara wadda bata taba tunanin samunta anan kusa ba,to juriyarce ma ko kuma zuciyarta ce ta gama qeqashewa?,ta qone babu wani qauri yanzu da yayi saura?,ta fita tayi aikace aikacenta tana qarfafawa kanta gwiwar cewa,babu ita a zuciyar ameen ya kamata itama ta fiddashi daga tata zuciyar,ya kamata ta jingineshi ta fuskanci reality dinta,a haka ta gama girkin rana ta kuma dora dana dare.
Loma daya inna tayi a abincin ta sake kallonsa cikin mamaki,saboda a yau girkin sam baiyi kama dana iman din ba,qwararriya a fannin girki,tarin kura kurai fal cikin abincin,saita qyaleta bata yi mata magana ba,saidai ta leqo sanda take ta hidimar hada sanwar dare ba tare da ita ta sanyawa cikinta koda qwayar shinkafa ba tun tea din safe tace da ita
"Ki tattara hankalinki waje daya iman,yau din akwai yiwuwar malam zaiyi baqi,kiyi abinci me kyau"
"To inna" ta amsa mata da salon son nuna she's okay
"Ko na turo miki mufida?"
"Qyaleta inna,damuna zatayi da surutu" kai ta jinjina kawai,uwa uwa ce,ta karanci zallar damuwa kan fuskarta,duk da qoqarin boyewar da take,saita juya ta fita ranta fal damuwa,cikin zuciyarta tana cewa
"Ya hayyu ya qayyumu,ya rahmar rahimin,bi rahmatika nastagisu ya Allah".
Karfe biyar da ashirin da bakwai ya shigo gidan,ta jiyo muryarsa a parlor amma bata taba kawowa kanta zai qaraso kitchen din ba,wannan amannar data yi ya sakata ta sakankance,taci gaba da yanka albasa saman chopping board,a hankali kamar wadda ke yankae naman jikinta,saboda yadda zuciyarta da gangar jikinta ke neman gazawa da yaqin da take tayi da kanta kan hana kanta tunane tunane.
A hankali yake takowa zuwa kitchen din,hannunsa dauke da cup din daya cika da damammen fresh yoghurt na L&Z da fura,bai samu suger a parlor din ba,shi yasa ya yanke qarasowa kitchen din,mufida yaso bawa ta zuba masa,saboda baison zaqi da yawa yasa ya yanke zuwa da kansa.
Yana saka qafarsa ya hangeta,bai tsammaci tana cikin kitchen din ba,sai ya dakata daga bakin qofar kitchen din saboda babu hijabi ko mayafi a jikinta,yayi matuqar qoqarin ganin ya hana idanunsa qare mata kallo amma hakan yaci tura,kamar wanda ake ingizawa ya bita da kallo,tun daga qafafunta dake sanye da slipper na robber zuwa sama,skart dinta daya zauna sosai a jikinga ya fidda shape na qugunta,hakan rigar jikinta duk da cewa gefenta daya yake iya hangowa,gashinta dake daure cikin dankwali ya fito ta qasa yabi bayanta sosai ya kwanta,saboda gashin buzaye gareta irin na inna.
"A'uzu billahi minash shaidanir rajim" ya furta a hankali cikin zuciyarsa,jin wani abu ya fara yawo cikin jininsa,sai yaja da baya ya koma a hankali,yana fatan kada ta ganshi gudun zubewar mutuncinsa a idanunta.
Mufida dake kallo a parlor ya miqawa
"Jeki ki kai mata ta zubamin,amma kada ya wuce cokali daya,sannan kice mata idan babu mayafi a jikinta ta nema ta saka"
"Tom" yarinyar ta fada tana miqewa da sauri ta karba tayi kitchen din,ya zame a hankali ya zauna saman kujerar yana sauke ajiyar zuciya yana ci gaba da kiran sunan Allah tare da korar shaidan daga zuciyarsa,jiran fitowar mufida ya amsa furar ya wuce ne kawai ya tsaidashi,amma banda haka da tuni ya tsufa a daki,don dama yunwa ta dawo dashi ya shigo ya samu abunda zaici ya koma,to abincin da zaici ya tarar yayi sanyi,shi kuma bai iya cin abincin daya huce har haka ba,inna tace yayi haquri a gama na dare,don dama girkin ba kowa zainiya cinsa ba,wannan ta sanya ya nema furar.
Idanu iman ta zubawa mufidan sanda take gaya mata saqon ameen din
"Na nemi mayafi na saka?,kenan ya shigo?,yaushe?" Duka ta maimaita tambayar wa kanta da kanta,sai data karba cup din xata zuba masa sugern hancinta ya zuqo mata qamshin turarensa wanda ya tabbatar mata da shigowar tasa,to amma batasan yaushe ba,kuma har ya fita bata ganshi ba.
Tana gama afawa ta miqawa mufidan,sannan ta janyo hijab dinta wanda tun dazun dashi ta shigo ta saka taci gaba da yankan albasarta.
Ta sake komawa duniyar data fito wato duniyar tunani,tayi nisa sosai,har bata iyajin motsin abinda ke gefe ko kusa da ita,a hankali hancinta ya fara shaqo mata wannan mayen qamshin,qamshin da aduk sanda ta shaqeshi saiya birkita mata duk wani lissafinta,tadan tsaida yankan albasar,tanajin kamar akwai mutum a cikin kitchen din,kuma a gefanta,kamar duminsa ma take ji,ta waiwaya a hankali take fuskarta ta fada cikin tashi.
Kwayar idanunsa cikin tata yake kallonta,dab da ita yake tsaye,riqe da cup din a hannunsa,take dukkanin jikinta ya amsa,saita dan matsa kadan kamar yadda shima yaja baya,yabi albasar da take yankawa da kallo,koshi da yake namiji amma sam baiga nutsuwa cikin aikinta ba,hasalima wata albasar bata gama baruwa gaba daya ba
"Ya akayi aka zuban gishiri instead of sugar?" Yayi maganar da lallausan muryarsa wadda ta sake kashe mata jiki.
Cikin dakiya ta fiddo idanunta waje
"Gishiri?,sugar dai" ta fada adan daburce,batason yadda yaje kafeta da mayun idanunsa,ita kadai tasan me yake bar mata,wanda a yanzun wannan yanayin da yake barwa jiki da zuciyarta zai iya zama barazana ga dukkan wata jarumta data shirya aiwatarwa.
Cup din ya miqa mata kawai batare da yace komai ba yana ci gaba da kallonta,a hankali ta miqa nata hannun zata amsa,abunda ya kawo haduwar yatsansu waje guda,kowanne kuma ya janye hannunsa, cup din yayi qas zai fadi ya tarwatse,cikin wani zafin nama da kuma mazantaka ya sanya daya hannun nasa ya taroshi,sannan ya dorashi saman drawer din kitchen din,ya taka a hankali ya rabeta,ya dauki wani cup din da kuma sugarn ya fice a kitchen din a hankali,yanajin yanayinsa kamar yana shirin canzawa zuwa wani irin feeling dake kashe gabban jiki,wanda a yanzu baya nemansa ko fatan zuwanshi.
Hannayenta duka biyun ta saka ta kama kanta sosai,tana tambayar kanta da kanta meye yake damunta ne haka?,me yasa ta gaza samun nutsuwa?,saita matsa inda ya ajjiye cup din,ta saka yatsanta ta lakaci furar ta dandana.
Tabbas gishiri ne ta zuba maimakon sugar,ta sauke ajiyar zuciya mai matuqar nauyi,kamar zata hado da zuciyarta,ta tura cup din cikin sink,ta matsa wajen chopping board din ta dauki wuqar tana kiran
"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" taci gaba da yankan.
*_BAYAN WASU AWANNI_*
Sosai ta tsurawa kanta idanu a gaban madubin,cike da wasi wasi da kuma tunanin anya abunda take shirin aikatawa shine dai dai?,to idan ba dai dai bane meye yafi dacewa ta aikata din?,me zatayi?,zata zauna ne har sai ruwa ya qarewa dan kada ko kuwa?.
"Ya iman,baqonki yazo" muryar mufida ta katse mata tunaninta,ta waiwaya a hankali ta dubeta
"Yana ina?"
"Yana qofar gida,amma naga ya ameen ya masa iso,ya bashi kujera ma ya zauna"
"Ya ameen?" Ta fada cikij dimbin mamaki
"Eh,sun gaisa ma sannan ya wuce" baya tayi a hankali ta zube saman gadonta,ya ilahi me ameen yake buqata da ita ne?,ko sai ya manna mata ciwon zuciya zai qyaleta,sai yaga ta haukace sannan zai daina nunawa duniya ya daina yi da ita?,kullum kwanan duniya sai yayi abunda zai tabbatarwa da kowa baya qaunarta baya kuma kishinta,ta gaji da gani hakanan,yana kasheta ne ba tare da kowanne makami ba,ya kamata yabarta hakanan
"Me za'a ce masa?" Mufidan ta katseta
"Kikai masa ruwa da lemo,ina zuwa" ta fada ba tare da tana da tabbacin iya futar tata ba.
Ta jima zaune a wajen tana dai daita kanta sannan ta miqe,ta fesa turare sama sama,ta yafa mayafin daya dace da kayan jikinta sannan ta fito,takunta a kasalance,zuciyarta babu dadi ko kadan,ta gayawa inna ta fita,innar ta bita da kallo
"Saikin dawo" ta amsa mata a sanyaye.
Tunda ta fito idanunsa na akanta,murmushin dake nuna zallan farincikin da yake ciki yaqi gushewa daga kan fuskarsa,miqewa yayi kafin ta iso ya kuma gyara mata kujerarta
"Barka da fitowa sarauniyar mata"tale labbanta kawai tayi ta yadda tsokokin fuskarta suka bada shadow na murmushi,don kwata kwata babu wani digo na farinciki da zai haifar da murmushi na ainihi a saman fuskarta
"Barka kadai likita,ya na ganka kai kadai?,ina babyn?" Ta tambayeshi tana shirin zama
"Milha?,tana wajen mamanta" shima ya amsa mata yana zama
"Halan batasan zaka fito zance ba?" Ta tambayeshi tana qoqarin bude masa robar lemo,duk a qoqarinta na kauda dukka wani alamu da zai alamta samuwar matsala rashin walwala ko takura a tattare da ita.
Dariyarsa taja hankalinta
"Da kin zaci diyata ce kenan?,eh diyata dince,amma bani na haifeta ba,'yar lil sister dina ce......any way na godewa Allah,ko babu komai hakan yana nufin ana kishi na" murmushi ta qirqira kadan tana aje masa cup din.
Baibi takan lemo ba sai gaisuwa da suke sabuwa,ya kuma gabatar mata da kanshi,cikakken suna da tarihinsa,ya kuma sake jaddada mata soyayyarsa sannan ya rufe da cewa
"Ina fatan za'a karbeni a yadda nazo,gani dai qaton tuzuru ne ni,wanda yasha gori har ya godewa Allah" murmushi tadanyi kawai kanta a qasa tana murza yatsunta
"Idan har kin aminta dani,kin kuma amince zaki aureni,toki gabatar dani ga malam,ba dogon lokaci nakeso a dauka ba,so nake ayi komai a gama ki zama mallakina"
"Amma bakajin ka tauyi kanka,kana saurayi zaka fara da bazawara?,ba kuma zaka samu matsala daga gida ba?"
"Wace bazawarar?" Yayi tambaya yana dube dube,kamar me neman wani abu,lamarin da yasa dole murmushi yafita daga fuskarta
"Ki ajjiye wannan batun please,bashi ake yayi yanzu ba,ana yayin samun nagartaccuyar macene,wadda ta fito daga gidan tarbiyya" saita jinjina kawai bata iya cewa komai ba.
Bai jima sosai ba yayi mata sallama,yana jaddada mata ta gabatar dashi,ga komai nashi da ake buqata suna iya yin bincike a kansa,ya tafi ya barta da gift na zobe mai kyau,wanda bai bar wajen ba sai daya tabbatar ta sanyashi a yatsanta,ya zauna kuma yayi matuqar yi ma zara zaran fararen yatsunta kyau.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 53
Kwanakin da suka biyo baya gaba daya gidan cikin hidima da shiri suke na bikin bude katafaren kamfanin ameen din,wanda suke samar da dukka wani nau'i na suttura na qasashe daban daban,kama da dinkakku da wanda ba'a dinka ba,na maza da mata yara da manya,abayas ne yadididdika laces harma da mayafai takalma da jakankuna,ga bangaren qwararrun teloli da yanzu yanzu ka siya kaya za'a canza musu kamanni da dinki na kece raini kowanne kala kakeso,wajene da zai kafa tarihi mai dimbin yawa,kuma guri ne da duk wanda ya kalla sai ya juya ya sake kallonsa,shi kansa ameen din ya qarar da duka abinda ya mallaka a wajen,saidai sam bai damu ba,sabida yana da kyakkyawan zato da kuma fatan zai maida adadin abinda baisan yawansu ba.
********Yammaci ne lis,wanda yayi dai dai da washegari itace ta kasance ranar juma'a,ranar da za'a gudanar da bikin bude companyn IB COUTURE,ya zabi ya sakawa wajen sunan malam ne,saboda girmamawa a gareshi,da kuma nuna jin dadinsa da godiyarsa bisa halaccin da yayi masa a rayuwa.
Zaune suke a 'yar qaramar harabar gidan ita da dr,wanda wannan shine zuwansa na biyu bayan malam ya bata saqon ta shaida masa cewa ya turo da magabatansa,ya gama bincike a kansa ya kuma tabbatar da ingancinsa.
Gaba daya ya sanyata a gaba da kallonshi,ya kasa boye mata abunda ke ransa,farinciki zumudi da kuma fatan zuwan ranar da zaace ta zama tasa
"Allah yasa kada malam ya saka doguwar rana" dan dubansa tayi
"Ka shirya kenan?"
"Na dade ai a shirye Hajiya,ke kadai nake jira dama" murmusawa tayi kadan
"Inda zai tambayi shawarata,zance masa a bari sai na gama dukka sauran watannin da suka ragemin a makaranta,saboda hankalina yafi tattaruwa waje daya"
"Mene?" Yafada da sauri yana fidda idanu,sai kuma ya hade tafukan hannayensa waje daya
"Ki rufamin asiri,kar kimin haka,indai makarantace baki da matsala dani,practical dinma sai kiyi a asibitina,koda bakiyi ba gaki ga likita matsalan me kike dashi?" Dai dai sannan aka tura dan madaidaicin gate din gidan mota ta fara yunqurin shigowa.
Dauke idanunta tayi sanda ta fahimci motar alameen ce ke shigowa ta maida wani sashen daban kamar bata ganshi ba,batason su hada ido ko waga magana ta hadasu bare zuciyarta ta karye,duk wani guntun qwarin gwiwa data tattaro ya zagwanye ya barta da tarin rauni.
,don haka ta waiga da dan sauri.
Yaya baraka ce,miqewa tayi a nutse murmushi na subucewa daga fuskarta,matar nada kima da daraja a idanunta,ko sau daya kuma ko a fuska bata taba nuna mata wani canji ba kan abunda ya faru tsakaninta da alameen ba,yadda ta saba mata har a lokacin da kuma yanzu babu wani abu daya canza
"Yaa baraka....." Ta kirayeta tana qarasawa bakin motar,fuskar iman qunshe da murmushi,sai itana ta juyo tata fuskar kamar gonar auduga
"Hajaru hanjartu" sunan da take kiranta dashi tun zamanin quruciya,tun sanda suke zuwa mata hutu jigawa
"Sannu da zuwa yaya,ashe kina hanya?" Ta fadi tana duban 'yar budurwar diyar yaya barakan,wadda a hakan itace autarta
"Wallahi dai kin gani,sai da aminu yaje ya daukoni,wai lallai sai nazo bikin buda kamfani,ni kuma naga me zanzo nayi ga inna ga malam,sai yace wai malam dinne yace lallai lallai nazo din"
"Gaskiya ne,ai ya kamata" iman din ta fada har yanzu fuskarta da murmushi,tana kuma dauke idanunta daga kewayen da ameen ke tsaye,ta fara qoqarin amsar jakar hannunta,diyarya badi'a tana gaida iman din,ta amsa mata cikin kulawa tana sake cika da mamakin girman badi'a,yarinyar da idan sunje qauyen take goyata a baya,ta taya yaa baraka rainonta.
Ita tayi musu jagora zuwa cikin gidan suna taba hira abunsu da yaa barakan a sake kamar yadda suka saba a baya,kusan daura da dr ahmad xasu wuce,don haka tadan dakata sanda ya miqe tsaye yana gaida yaa baraka
"Bari na rakata ciki"
"A fito lafiya" ya bata amsa cikin nuna kulawa,ya bi iman din da kallo,abinda yasa ya gaza ganin tahowar ameen,har sai daya kusa gotashi.
Cikin girmamawa ya bashi hannu sukayi musabaha,sannan ameen din yayi gaba,saidai kafin yakai ga qarasawa ya dakata,ya bawa sayyadi jakar kayan nasu yace ya qarasa musu da ita ciki,sai kawai ya koma cikin motarsa ya tasheta ya fita daga gidan.
Sosai suka kaure da murnar ganin juna ita da inna,don an dan kwana biyu ya barakan batazo garin ba,an saba da juna an zama tamkar 'yan uwa,har kowacce tsakanin inna da yaa barakan takejin 'yar uwarta cikin jikinta sosai.
Bata baro ciki ba sai data tabbatar inda yaa barakan zata zauna ya saitu,ta samu dr ahmad din ma yanata waya,fitowarta yasa ya sauke wayar,ya tarbeta da murmushi
"Barka da fitowa gimbiya" murmushi ya kubce mata,taja kujera tana shirin zama qofar gidan ta sake budewa,saita maida hankalinta ga can maimakon zaman.
Tun kan ta qaraso fa ganeta,bushira ce,suna hada idanu suka sakarwa juna murmushi,ta miqe tana tunkararta
"Wata sabon gani,yaushe a gari inji maqi baqo?" Iman ta fada tana dariya,harara bushira ta watsa mata
"Au haka ma zakice?"
"Tuba nake" iman ta fada tana fadada murmushinta,saboda tasan ta yiwa bushiran laifi,sai suka gamu a hanya sannan suka sake takowa zuwa ciki
"Dr......ga childhood friend dita,sunanta bushira" iman ta fada sanda suke qarasowa inda dr ahmad ke zaune.
Cikin fara'a suka gaisa da ita,kasnacewarta itama bushiran gwanar kirki ce da fara'a,sai ya miqe
"Hajjaju zan wuce gaskiya hakanan,na fuskanci kina da baqi da yawa yau,bari na basu aronki na yau kawai" murmushi tayi sannan ta taka masa har qofar gida inda motarsa take fake sukayi sallama ya wuce,sannan ta dawo ciki.
A inda dr ya tashi ta samu bushiran zaune tana jiranta,hannunta riqe da wayarta
"Waye wannan kuma?" Bushiran ta fara da tambayar iman sanda iman din ke saka jan kujera daya ta zauna akai
"Ba zamu koma ciki ba kika zauna a nan?" Iman ta maida ma bushira tambayarta da tayi
"Nan dinma ai yayi,mu gama gaisawa dake,saiki rakani ciki na gaida inna" kai iman din ta gyada,shuru na kusan sakan uku ya ratsa sannan tace
"Ya kika ganshi yayi ne?" Tayi tambayar da dan guntun murmushi saman fuskarta,murmushin da ya sanya bushira ta zuba mata idanu kafin ta amsa mata
"Yayi,bashi da wata makusa,yana kuma da kirki a idanu"
"Haka dabi'arsa ma ta badini da malam ya bincika" kai bushira ta jinjina
"Wayeshi din?"
"Dr Ahmad, shine wanda zan aura" tayi maganar babu wani armashi ko confidence a tattare da ita,ido bushira ta zuba mata sosai,ta buda bakinta a hankali
"Ina kuma ya lamin din?" Lumshe idanu iman tayi,ta kuma bude lokaci guda tana girgiza kanta,yanayin fuskarta ya canza a take
"Yafi qarfina zuwa yanzu,don kuwa ya fitar da wata matar,ya lamin ya kasa gane duk wata kulawa da nake bashi soyayya ce,ya kasa gane duk wani motsina a kansa zazzzafar qauna ce,ya kasa fahimtar furucina motsina da aiki na,kamar yadda yake fahimta a baya" sosai bushira ta gyara zama ta kuma ajjiye wayarta,tana iya hangen wani pain mai kaifi daga zuciyar iman din
"Indai har ya lamin ya cancanci a soshi,me yasa zaki jira sai ya gano wani motsi da action naki?, just go straight forward.......ki sameshi ki furta masa kamar yadda ya furta miki,meye a ciki?,dan uwanki ne kuma yayanki ne" kai iman ke kadawa a hankali a hankali
"Bazan iya ba bushira.....bansan ta yaya zan tari namiji nace masa ina sonshi ba,karfa ki manta,har abada ni din diya macace,ya ameen kuma namiji ne"
"Akan hakan kin gwammaci ki rasashi?,kin gwammaci wata ta sameshi?"
"Ina addu'a,kuma Allah yana sane idan har na cancanci na sameshi ta kowacce hanya bazai hanani shi ba,idan kuma ahmad ya zabarmin na gode masa,bazan iya cusa kaina zuwa ga wulaqancin namiji ba bushira,a wannan matsayin da nake kai,addu'a da tattarawa ubangiji lamarina shine kawai abinda yafi dacewa dani"
Kai bushira ke jinjinawa,sosai iman tayi matuqar bata tausayi,maganganunta akan hanya suke,tabbas kowacce mace tana buqatar kare martaba da kuma kimarta wajen namiji kodon gaba,amma ita a nata hasashen,case dinta dana alamin daban yake da sauran cases.
Miqewa iman tayi tana daukar jakar bushiran
"Mu shiga ciki bushira,mintuna kadan suka rage a kirayi magrib" miqewa tayi tabi iman din,tana kallon yadda aketa kokawa tsakanin zuciyarta da kuna qwarin gwiwar da take dashi.
******yadda gurin ya qawatu haka ya cika da jama'a wadanda suka halarci taron bude kamfanin,sosai kamfanin ya qayatar,ya kuma bada mamaki fiye da zato,waje ne mai girma da tsari,kowanne sashe daban.
Floor na farko anan masu dinki suke,dinki kowanne nau'in sutura,second floor wanda xaka hau sama shi kuma anan suke ajjiye kowanne kaya da aka gama hadasu dama wadanda ba'a dinka ba game son siyansu a haka,da sauran tarkacen su takalma da kayan ado,third floor kuwa acan office na mai kamfanin wato lamin da sauran ma'aikata yake.
Bayan bude kamfanin ta hanyar yanke wani dan zare,tarin 'yan press suka cika ma'aikatar,aka kuma gama komai akan idanunsu,sannan akayi qwarya qwaryar walima jama'a suka shiga suka ga yadda waje yake da ayyukan da za'a dinga gudanarwa,daga nan wasu suka fara ma lamin sallama da fatan alkhairi,abunda ya fara rage cinkoson kamfanin.
A hankali take takawa cikin kamfanin,bayan an ajjiyesu waje na musamman ita da inna da mufida an gabatar musu kayan ciye ciye da shaye shaye da kowa yaci a wajen,sosai kamfanin ya burgeta,tana kuma jinjinawa lamin na yadda ya zama tsayayyen namiji,bai bar sana'arsa ta asali ba,hasalima ya qara qaimi ya kafa kanshi ra hanyarta,ya kuma zamanantar ta zama abar sha'awa ga kowa.
Doguwar barandar ta dinga bi tana kallo qasan kamfanin har sai data kai qarshenta,wanda a wannan kwanar office din din CEO yake wato lamin,ganin taka qarshe sai ta fara qoqarin juyowa ta dawo
"Me yasa samha....i told you har yanzu akwai mutane da yawa,da kin zauna abunki iya abunda kika yimin ma i appreciated it" muryar lamin ta ratsa kunnenta,yana rufe baki kuma muryar samhan ta biyo bayanta
"Yanzu my man.....daga abun arziqi,a qa'idama fa dani ya kamata a gabatar da komai ina ta damanka.... but ka bani excuse kuma na karba,na bari sai da aka ragu,don nazo.naga kamfanin mijina laifi nayi?"
A hankali iman ta juya idanunta zuwa sashen da takejin muryoyinsu,lamin na tsaye daga qofar office dinsa,sanye da suit da yayi amfani dasu a wannan rana iri daya da ya sadiqu ash da da ratsin orange dan kadan,suit din da sukayi masifar tafiya da imanin mutane,sai samhan tana tsaye itama tana fuskantarsa,sanye da Dubai abaya zoom material,ta yane kanta da mayafin abayar,an qawata mata fuskarta da makeup,da alama takanas taje akayi mata ita,qafafunta sanye da high shoes masu tsinun dunduniya,qaramar jaka ce a hannunta dakuma wata leda wadda ke dauke da gift data shirya musamman saboda lamin din.
Dauke numfashinta iman tayi,ta sake dage takunta da kyau,qirjinta na bugawa saboda kusancin data gani tsakanin lamin da samhar,taku biyu idan ya qara yana iya hade tazarar dake tsakaninsu,saidai bata kai ga cimma nasarar barin wajen ba kamar ance masa ya juya suka idanunsa ya sauka a kanta,yasan tabbas ta gansu shida samhan
"Zonan" ya fada a dake cikin salon bada umarni,maganar da taja hankalin samha itama,saita iman din ta tsaya cak ba tare data waiwayo ba
"Rakata ta gaida inna" ya fadi yana sanya card dinsa jikin qofar office din zai bude.
Idanun samha qur akan iman sanda take qarasowa inda iman din take,wadda tunda ta tsaya bata juyo ba,daga sama har qasa take qarewa dressing dinta kallo,wani abu taji ya caki zuciyarta me kama da kishi,me yasa tunanin yin irin wannan shigar bai shiga kanta ba?,ta tambayi kanta,dressing me aji wanda kana kalla zai gaya maka mamallakiyar shigar tasan me takeyi.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 54
Tare suka jero,saidai girman kai ya kama kowa,kowacce ta gaza yiwa 'yar uwarta magana,kishi yana cin zuciyar kowaccensu,yayin da samha tata zuciyar ta cika da qyashi irin na kyan da iman din tayi,zuciya nata raya mata yanzun qila tare suka taho da ita a mota guda,wala'alla ma ita ta zauna a gaban motar,wannan kwalliyar qila shi ya fara ganinta kafin kowa ya gani,yanzu da wannan kyan nata suke rayuwa gida daya dashi?,gaskiya batajin zata juri barin iman din ta dinga zuwa mata gida duk sanda sukayi aure da alameen din,duk da itama me kyau ce,amma batasan me yasa kyan iman din ya tsole mata ido har haka ba,tana da azababben kishi,ita kanta tasan da haka,tayi.mamaki ma da yazo mata da sauqi akan iman din,bata iya furtawa,saidai yana cinta cikun zuciya qwarai da gaske,wala'alla ko don ta lura basa wani good time da alameen dinne yasa bakinta ya iya har yayi controlling kansa ba.
Daga qarshe shawarar zuciyarta tabi,wadda ta kwabeta kan ta daure zuciyarta ta tanka mata
"Dake da ameen bansan wanda yafi wani miskilanci ba,duk miskilancin da ake fadin ina dashi sai nazo na tarar da wani kuma daban" ko kadan maganar tata bata burgeta ba,saima haushinta daya ninku cikin zuciyar iman din,wannan wanne irin rashin ajine da xaki biyo mutum cikin taro irin wannan,da familynsa a wajen da komai,bayan gidansu da kika tattaka da qafafunki kikaje,wannan duka bai isheki ba
"Innar tana tacan" ta tsaya daga baya tana yiwa samha nuni da wajen da innar take,saita qarasa jikin glass na ginin saman ta tsaya,tana ci gaba da kallo farfajiyar kamfanin,inda tsirarin mutane da suka rage suke ta kai komo,wasu na fita wasu na shigowa,saidai fiye da rabin hankalinta ba a na wajen yake ba,ya lula duniyar tunani.
Zafi sosa zuciyarta take mata,tanata qoqarin controlling kanta ne,tana ta hadiye abubuwa, bataso su taru suyi mata yawa,tana fata Allah ya cire mata amin daga ranta kwata kwata,kwana take ta kuma wuni tana addu'a,batason ta nacewa kanta da damuwa kan abunda ba zata samu ba,batason zuciyarta ta dinga wahala akan abunda tasan yayi nisa daga gareta,bataso ta dinga damuwa da tarayyar samha da amin,tanaso wadan nan abu uwan su fita daga ranta ko xata huta,saidai babu wani ci gaba da take gani kan abunda take roqo din,ta dai sanyawa ran nata lokaci ne.
Ruri wayarta ta fara yi,a sanyaye ta daga tana kallon screen din wayar,dr ahmad ne,ba zata iya share kiransa ba,saboda yana matuqar damuwa da al'amuranta da kuma bata kulawa ta musamman.
Ita tafara masa sallama,ya amsa mata yana tambayarta yanayin taron,yaso zuwa qwarai amma ranar yana da patient da zaiyiwa theatre har mutum uku,dole ya haqura
"Alhamdulillah,taro ya tashi lafiya" ta bashi amsa a taqaice
"Ma sha Allah,Allah yasa albarka"
"Ameen,thanks" shuru ya ratsa wayan,cikin zuciyarsa yana ji muryarta batayi masa yadda ya saba jinta ba,kamar tasan tunanin da yake kenan tace dashi
"Zamuyi waya anjima please"
"Alright, take your time and be safe"
"Thank you" ta sake amsa masa tana katse wayar,a yanzun bata jin zata iya wata doguwar magana,shi yasa tayi masa sallama.
Numfashi ta fitar daga bakinga hade da iska,tana ci gaba da kallon waje,cikin jikinta takeji kamar ana kallonta,idanun kuma ya wuce na mutum daya,sai ta maida hankalinta ga wajen,tana tsammanin daga canne wasu suke hangota.
"Alameen" muryar yaa baraka ta bayyana daga bayansu,da sauri gaba dayansu suka juya,babu wanda yasan da tsaiwar ya baraka a wajen,iman ta sauke kallonta ga alameen dake tsaye a baya ta wanda a yanzu ya waiwaya ga yaa baraka,saidai akwai tazara sosai a tsakaninsu,batasan tsahon yaushe ya dauka a tsayen ba,kamar yadda gaba dayansu basusan tsayin lokacin da itama ya barakan ta dauka a tsayen ba.
Dukkaninsu suka taka zuwa inda take tsaye
"Me kuke a waje?,innar aka bari ita daya a ciki?" Shafa kwantacciyar sumarsa mai kyau da qayatarwa yayi
"Ba ita kadai bace,tana tare da baquwa"
"Baquwa kuma muka samu?...." Bata tsaya jin amsarsa ba kuma sai ta shigo da wata maganar
"Wannan matattakalar taku badai yawa ba,yanzu kullum haka zaku dinga dawafi daga qasa zuwa sama?" Sai da sukayi murmushi gaba dayansu,dai dai sanda suka fara takawa zuwa ciki,suka sanya yaya barakan a tsakiya
"Akwai na'uran dake ragewa mutum tsahon tafiya,daga sama ta kawoshi qasa,ko kuma daga qasa ta kaishi sama"
"Ayho,koda naji" daga haka kuma sai hirar ta koma tsakaninta da iman din kawai,kusan wasu abubuwane da batasaji game da iman din ba take tambayarta,kamar karatunta da sauransu,a haka suka qarasa inda innar take.
Kanta ta dago daga hirar da sukeyi da samha tana amsa sallamar tasu,shigowar tasu a haka sai wani abu ya mintsini zuciyar inna,ta bisu da kallo a yadda suka shigo din,tana jin inama inama,inama ace.....
Tunaninta ya katse sanda yaa barakan take zama tare da mitar barin innar ita daya,murmushi inna tayi
"Basu barni da kadaici ba ai,ga mufida muna tare,daga baya ma saiga diyata kuma ta shigo" duba sashen da samhan take yaa baraka tayi,kasancewar batasan wacece ba batace komai ba,dakin ya dauki shuru kamar qiftawar tsawa,inna ta san lamin din nada kara,bazaya iya gayawa yaa barakan wace samha ba,amma tayi zaton iman zata gabatar da ita sai taga wayarta ma take dannawa kamar bata cikin dakin,tilas tadanyi gyaran murya
"Baraka,gafa surukar tamu,yarinyar da ameenu zai aura in sha Allahu" da hanzari ta kalli gefanta inda samhan take,a sannan ta sadda kanta qasa tana kuma dan murmushi dake nuna kunya
"Too ikon Allah"abunda ya barakan tace kenan,bayan ta gama amsa gaisuwar samhan dakin shuru ya sake dauka,sai inna dake qoqarin jefowa samhan hira saboda kore zaman shurun nasu,duk wanda ya kalli fuskar ya barakan yasan ta canza,ba haka yanayinta yake a dazu ba,saidai bata ce komai ba,amma tana biye da hirarsu da inna.
Lamin ne ya duba agogonsa bayan ya sauke wayarsa da aka kirashi
"Inna ko zaku wuce kada ku gaji da zaman,an kai malam yaron daya kaishin ya dawo"
"To babu laifi,hakan yayi" daga haka suka miqe suka fara shirin tafiyar.
Yaa barakan tana tason yin magana da lamin,saidai samhan tana maqale dashi sanda suka fito gaba daya,tana masa magana qasa qasa,har suka qaraso bakin mota.
Inna lamin ya budewa gaban motar,sai taqi shiga tace samha ta shiga,tadan doje kadan kan innar ce zata shiga,bata sake jan zancan da tsaho ba ta bude ta shigan,ya baraka ta fara shiga baya,sai iman sannan samhan,yaa baraka ta leqa ta window
"Yau komai dare idan ka dawo ka nemeni,inason yin magana da kai"
"To in sha Allah" ya amsa mata cikin girmamawa yana rufe murfin motar.
Cikin motar ma dif kowa yayi,samha aka fara saukewa sannan su aka qarasa gida dasu.
Kamar jira ya barakan take,suna shiga parlor abinda ta soma shine qorafi,a sannan iman tuni tayi daka,saboda gajiyar da takeji a jikinta.
"Yanzu inna,ta yaya kuna gani kuka bar aminu ya dauko wannan yarinyar?" Dubanta inna tayi tana cire abun hannunta
"A iya abunda ido da kuma bincike ya nuna bata da wani aibu,tuni malam ya gama duk wani bincike a kanta,abunda yasa ma yace kizo din lallai,ina kyautata zaton jibi za'a kai kudaden aurensu shi da sadiqu.....dana 'yaruwarsu ma gaba daya" zama ya baraka tayi,gaba daya wuta ta dauke mata,ashe ita abunda take lissafi tattare dashi da kuma iman din ba haka bane,yaya amin din zai aikata wannan gangancin da kuma katobarar?
"Amma binta,tsakanin da Alla ta yaya gida bata qoshi ba za'a bawa dawa?,har iman din bada ita za'ayi?" Murmushi kadan inna tayi,inda ita ke da ikon sarrafa al'amuran zuciyar kowannensu,da tuni ta gama da tabbatarwa ameen iman
"Dama ce aka bawa kowa ya zabi abokin rayuwar da yake ganin yafi dacewa dashi baraka,baka isa sauya abunda Alla ya rubuta ba" kai ta girgixa,a karon farko da takejin zata ja da wani hukunci akan lamin din tsahon shekaru sama da ashirin da uku
"Zanyi magana da malam,wannan ba abunda zaa zuba idanu bane ace haka Allah ya tsara bane,a fara jarrabawa,idan bai yiwu ba sai ace haka Allah ya tsara din,ni zanga malam din da ameenun ma gaba dayansu"
"To Allah yayi jagora" abunda inna ta iya fada kenan saboda kara,uwa uba can qasan zuciyarta sai ya cika da fata da kuma burin cika da tabbatuwar abinda baraka ke hari.
*IMAN*
Tun bayan shigarta daki Allah ya taimaketa barci me nauyi ya dauketa,baccin daya dauketa lokaci mai tsaho,koda ta farka taga lokacin data share tana baccin bata damu ba,saboda tasan tana fashin sallah,sannan babu wani sauran aiki cikin gidan,tun kafin su fita ta gama komai na gidan,saita dan yaye labulenta tana hangen waje,sararin samaniya har tayi duhu wanda ya gauraya da ragowar hasken magariba da bai gama dusashewa ba,ta saki labulen a hankali ta kuka zarce bandaki.
Ruwa mai dumi sosai ta saka tayi wanka,ta fito tana qamshin shower gel dinta mai taushi,gaban madubi ta tsaya,ta tsane jikinta ta mulkeshi da mayukanta masu kyau da tsada,wanda zuwa yanzu sun zame.mata jiki ta saba amfani dasu,sun karbeta matuqa,qamshinsu kuma ya zauna sosai a fatarta,ta gyara gashinta shima ta feshe shi da hair mist,sannan ta shirya cikin wasu ready made data siya a wani kanti,riga budadden hannu da straight skeet,kayan basu da nauyi sam,shi yasa take sonsu takejin dadin sakasu,cikin kayanta ta duba hijabi qarami da bai wani sauko da yawa ba ta zura,zaman dakin ya isheta,don haka ta qarasa inda wayarta take ta dauko tana dubawa,saqonni da kuma miscal masu yawa,wanda batasan dasu ba,sabida saka wayar da tayi a silent tun sanda zata kwanta,saita zarce da fita waje kawai wayar na riqe a hannunta.
Ba kowa cikin parlor din,amma ta dan jiyo murya daga sashen dakin inna,tunawa da tayi yaa barakan tace tanason ganin ameen komai dare yasa ta yanke fita can bayan gidan ta zauna abinta,don babu mamaki shi dinne suna tare,itako batason duk wata harka da zata hadata dashi,a yanzun lallaba rayuwa da kuma zuciyarta takeyi.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 55
Wani yanayi me haifar da walwala ne ya sauka a zuciyarta sanda ta fita qaramar harabar tasu takuma zuqi fresh air dake kadawa,iska ce mai wani irin taushi a cikinta,kamar ta farkon shigowar damina,idanunta suka sauka a hankali kan motarsa dake fake adan filin gidan nasu,tabbacin ya dawo kenan,dole kam ta kama kanta itama,saita kalli hagunta da damanta,tana shawarar daga wanne side zata zauna,karkata zuciyarta tayi da bangaren hagunta,wanda yake daura da wajen ajiyar motar sannan kuma ventilation ne da suka jere tukunen shuke shuke,ba kasafai aka fiya zuwa wajen ba,saboda daga nan zai sadaka da qofar babban parlor dinsu ameen din dake dauke da dakunan baccinsu,wajen yana da dan tsaho,hakan yasa idan kana daga ciki ciki ko daga baki baki ba zakasan da wani a farko ko qarshe ba.
Tana takawa tana duba saqonnin dake wayarta,kusan fin rabinsu daga Dr Ahmad ne,wanda yaketa mata bangajiya da kuma alhinin rashin samunta a waya,har ta qaraso wajen,ta daga ido taga plastic chair guda daya a wajen,takai hannunta guda daya da bai riqe da wayar ta niyyar jawota.......sai kuma ta tsaya cak,cikin sakanni kuma zuciyarta ta balle da wani irin gudu,qarfin jinta ya qaru,kamar yadda harbawar jinin dake jikinta ya birkice ya sauka daga kan tsari,fitar muryar alameen din na dauke da wani saqo da bata taba ayyana jinsa daga ba daga gareshi
".............duka ba haka bane yaa baraka.....kuma nima nasan da wannan,amincewar kowanne sashe shine jigon zamantakewa,sannan na roqeki kibar wannan maganar, let bygone be bygone,abunda ya wuce ya riga daya wuce,tun a wancan lokacin na shafe babinta daga raina da zuciyata gaba daya,na maidata matsayin wadda muka fito ciki daya,koda bata taba auren wani ba a yanzu bani da sha'awar aurenta kwata kwata bare ta taba auren wani, I can't.....bazan iya ba yaa baraka,infact ma a yanzu dai bana son iman kwata kwata,soyayya dai irin ta aure,kiyi haquri,ki kuma yi qoqari ki fahimceni,bazan iya ba" so take ta zauna din ko zata daina jin abunda takeji amma kuma batason taci gaba da sautaren maganganun dake fita daga bakin ameen din,kalaman da sukayiwa kunnuwa da zuciyarya matuqar munin da ba zata iya fasalta kamarsa ba,cikin juriya da jajircewa ta fusgo numfashinta da yake qoqarin yi mata wahala,ta cira qafafunta ta kuma tunkuda kanta da kanta zuwa gaba da sauri da sauri.
Cikin taimakon Allah ta lalubi hanya tas ta maida kanta zuwa daki,ta wurgar da wayarra ta bude bandakinta,ta kuma saki rufa afamfo ta dinga tara tafukan.hannuwanta tana watsawa a fuskarta,bata damu da yadda jikinta yake jiqewa ba,illa dai hucin da takeji.kamar yana fita daga saman fuskarta duk sanda ta watsa ruwan,a hankali a hankali ta soma jin na'urorin jikinta suna dai daita,saita kashe famfon,ta kuma ja da baya ta sulale a hankali zuwa qasa,a lokacinne kuka ya samu hanyar fita.
Tayi kuka kwatankwacin kukan datayi sanda ta gane waye bassam,waisu dama maza basu da alqibla?,waisu maza dama idan ka kamu da soyayyarsu baka tsintar komai face wahala da tashin hankali?,dama haka soyayya take?,me yasa soyayya bata karbeta ba kwata kwata,me yasa take wajigata?.
Me yasa zaki tsaya fana wahal dake tana wajigaki?,ki karbeta aduk yadda tazo miki kawai,idan ta barki kema ki barta ki huta,ki maida hankali da tunaninki ga barayin da ake da buqatarsu,a yanzu komai yazo qarshe tsakaninki da ya lamin,kin samu cikakkiyar amsar da kika jima kina lalubenta,meye kuma yayi saura?,a nan wajen cikin hali na zafi da quncin zuciya zuciyartata ta yankewa kanta da kanta hukuncin,hukuncin da takejin koda bataso xata tilasta kanta,ta tanqwara kanta ta karbeshi a haka,ta miqe ta zare kayan jikinta da suka jiqe,ta fito ta canza wasu cikin wani irin yanayi na siyawa kai jarumta,da son danne qunci da halin tashin hankali da zuciya ke fuskanta.
Saqon qarshe data fara dubawa taci karo da maganganun ameen ta koma ta sake dubawa
_"Ki shaidawa malam,gobe idan Allah ya kaimu su kawu zasu zo,sai a basu lokacin da yafi dacewa,kiyi mana addu'a,Allah yasa wannan shine matakin ingantacciyar rayuwa a garemu gaba daya"_
Da qwarin gwiwarta ta maida masa amsa,tana jin wani confidence yana shigarta sanda rauni yake qoqarin rinjayarta,ta ajjiye wayar gefanta itama ta zauna cikin matuqar kasala da mutuwar jiki,lokaci yayi da zata ajjiye komai,ta haqura itama,duk da tasha gayawa kanta wannan kalmar,amma tana saka ran wannan snine karo na qarshe da zata gayawa kanta haka.
Turo qofa mufida tayi ta shigi,ta ganta ta mudubin dakin don haka bata juyo ba
"Ya iman.....ya ameen yace akai masa abinci" ta mudubin ta zubawa yarinyar idanu
"Akai masa abinci,wato amfaninta kenan kai abinci?,me zaiyi da abincin da hannuwan wadda baya so suka dafa?,daga yau ta yanke,ta kuma canza,ta tashi daga wannan iman din zuwa wata daban" tayi dukka wannan tunanin da hukuncin cikin zuciyarta
"Kice musu a kwance nake,a kishirya food flask din a nutse kikai musu da daya da daya,zaki iya"
"Tom" yarinyar ta fada tana dan kallonta,sabida yadda taga yanayinta,batace dai komai ba ta juya ta fita sannan taja mata qofar.
Ba zata iya fita tayi magana da kowa ba,don haka taja wayarta ta turawa ya sadiqu text kan saqonnda dr ahmad din ya bayar,bayan ta tabbatar ya tafi saita kashe wayar gaba daya,ta hada da qwan dakin gaba daya ta kashe ta koma ta kwanta lamo,kamar ba daxu dazu ta tashi daga kwanciyar ba,bawai barci takeji ba,a'ah,tanason ta tattara duk wani courage nata da zata fuskanci rayuwarta da mutanen da take rayuwa dasu daga gobe idan Allah ya kaimu.
*********Da sakakkiyar fuskar dake boye da damuwa fal bayanta ta fita ta kama dukka wata sabgar data saba,kamar kunnuwanta basuji komai ba,kamar kuma babu wani ciwo cikin zuciyarta,ta yadda ba shakka duk wani abu daga tilastawa kanka yinsa zaka aikatashi,koda zuciya da gangar jiki bata gamsu da hakan ba.
Qarfe sha daya na rana tana dawowa falon xata ciri charger dinta datayi charge da safe ta tadda yaa baraka na fitowa daga dakin data sauka,'yarta na tsaye saqale da jakar kayansu
"Ke kuwa baraka,aiko azahar kya bari kikai idan su malam sun dawo daga kai kudaden auren nan" baki ta tabe
"A'a...a'ah,ai gwara na tattara komatsaina,tunda na fuskanci gidan yanzu ya zama gidan marasa son gaskiya,zamana kuwa bazai amfana komai ko ya rage komai ba" iman dake takowa parlor tasan komai,saidai babu wanda yasan ga sani din,cikin dauriya ta kalli badi'a
"Ke badi(haka take kiranta wasu lokutan)yanzu ko dan zaman nan ma na sati daya kiyi mana baxaki iya ba,qafarki qafar yaaya?" Murmushi badi'an tayi
"Makaranta wallahi yaa iman,yanzu ma kinga don a weekends muke,amma dai in sha Allah wataran zanzo" kai ta jinjina tana fidda dan murmushi
"Muna zuba ido....ya baraka da sauri haka?" Murmushi tayi
"Kada ki damu diyata kinji,zan dawo ko don saboda ke,bawai na tafi kenan ba" tayi maganar duk da tasan bawai lallai iman da duk wanda ke wajen ya fahimci abinda take nufi ba,hakan kuwa yake,saidai akace babba babbane,inna ta fahimci inda maganarta ta sanya gaba.
Tsaf murmushin fuskarta ya dauke sanda ta hangi shigowarsa,sanye cikin jallabiyya milk color mai gajeran hannu,duba daya zaka yiwa fuskarsa ka gane yana tsaka da barci ya taso,saita janye jikinta daga wajen,ta zagaya wajen chargenta ta cira,ta dawo daga bayan yaa barakan tace
"Yaa baraka zan shiga wanka,ina da makaranta yau,Allah ya tsare hanya,ya huta gajiya,Allah ya qara zumunci"
"Ameen imani" ta amsa mata cikin kulawa da jin dadi,ta yiwa badi:a magana kan ta biyota ta karbi saqo,batako waiwayi inda yake ba tayi gaba,tana jinsa shima yana qorafin ta tsaya su malam su dawo,ya karbi motar daga hannun sadiq,koda bai kaita jigawa ba ko wudil ne ya ajjiyesu,saidai fir taqi tace ko minti guda bata qarawa cikin ikon Allah.
Wani abu yadan tarar mata a wuya,ya sadiq ne kenan ya tafi kaisu,saidai da qarfi tayi qoqarin kawar da abun,ta duba wani seat na turaren jiki sabulu da spray ta bawa badi'a,dadi sosai ya kama badi,tayita maga godiya ta fito da abunta.
Da idanu ya kalla kwalin bayan badi'a ta fito dashi tana nunawa yaa barakan,yasan kudinsa sarai,don ya taba siyawa samha gift dinsa,saidai batayi amfani dashi ba,sabida tace scent din bai mata ba,shi kuma ya siyo ne saboda irin launin qamshin da yakeso kenan,sai yace ta barwa suby'a ya canza mata da choice dinta.
Bata sake fitowa ba har sai data kammala shirinta na fita zuwa makaranta,tayi kyau cikin fararen kayansu data dora baqar after dress akai,komai na iman din mai kyau ne da sanyi kamar dai yadda take ada can,wannan yanayi nata yana ja mata farinjini da masoya masu yawan gaske a cikin makarantar dama wajenta,sauqinta daya,bata bada fuska,miskilancinta idan ya motsa ba zaka taba cewa wannan iman din bace.
Komai take a ranar dauriya ce kawai take yinta,amma bata da wani kuzari ko karsashi,a duk sanda ta tuna a yau za'a bada ita ga wani,a yau kuma za'a bada alameen ga wata sai zuciyarta ta buga,saidai tanata gayawa kanta, she's ready to face any challenge......zata kuma iya jurewa,zata iya dauka.
Daga makaranta bayan ta gama duk abinda takeyi kasa wucewa gida tayi,sai ta wuce gidan kawu muntari wajen matarsa,mutuniyarta ce qwarai,ta tarbeta kamar koda yaushe,suka gaisa ta tambayi kawu muntarin
"Kawunki har yanzu bai dawo ba,tun daxun dai daya shigo bayan sun dawo daga kai kudaden auren yayanki,sai kuma ya sake fita,yace malam yayi masa waya ya dawo,yaron dake nemanki yace wakilansa na hanya.....to tun lokacin dai bai dawo ba".
Idonta kawai ta lumshe,zuciyarta na gaya mata shikenan,ta faru ta qare,alameen ya zama alqawarin wata,kamar yadda itama wala'alla kawo yanzu ta zama alqawarin wani,sai kuka tayi maza ta kauda wannan tunanin da kuma duk wata fargaba data taso mata,sanda zuciyarta ta tuna mata da kalamansa,kamar a sannan yake gayawa yaa baraka su.
Tana idar da magriba tayi haramar tafiya,dai dai sanda kawu muntari yayi sallama ya shigo gidan,saida gabanta ya fadi data tuna daga inda yake,suka gaisa,yayi mata Allah ya sanya alkhairi sannan sukayi sallama ta wuce gida.
Daga baya baya tasa me napep ya ajjiyeta,ta qarasa takowa a qafa,idanunta kan motar dake fake a qofar gidansu,data duba da kyau sai taga motar lamin dince,kuma suna tsaye a jiki shida ya sadiqu suna maganganu,ta wucesu a hankali ba tare data ji ko ta saurari abunda suke tattaunawar ba.
Da idanu yabi bayanta sanda take giftasu ta gefe,cikin takunta a hankali,sai kuma ya lumshe idanunsa yana janyesu,ya sake maida hankalinsa ga sadiq sukaci gaba da maganar da sukeyi yana jin wani baqon abu cikin zuciyarsa,wanda bai iya tantance meye ba.[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 56
Tunda ta shiga cikin gidan taketa tattalin farincikinta,da wankanta da cin abinci duka tanayi ne cikin son share kowanne tunani da dora sabuwar rayuwa bisa tsakiyar zuciyarta.
Tana dakin malam ya aiko kiranta,kamar wancan lokacin batasan ba ita kadai bace sai data shiga rumfar tasa,suna zaune sadiq din da ameen,a wannan karon wayar ameen din tana a tsakaninsu,da alama wani abu suke kalla,shigowarta kuma bai canza komai ba,sai ta rabesu ta isa ga malam ta yiwa kanta mazauni ta fara gaisheshi,ya amsa mata cikin kulawa.
"Alhamdulillah,kowannenku akwai alqawarin aure akansa nan da watanni shida,mun sanya hakane saboda kusan kowanne bangare a shirye yake,iman....kece zakiyi haquri,don ba lallai yayi dai dai da sanda zaki gama jarrabawarki ba,saiki addu'a Allah yasa haka ne yafi zama alkhairi"
"Ameen" ta amsa idanuwanta a qasa,sannan kuma ta miqe tabar dakin ba tare data bari ta kalli koda sashen da yake ba bare yaga idanuwanta.
*********Yanayine mai matuqar wahala wajen jureshi,yana da matuqar daki tsanani da kuma wahala me yawa a cikinsa,ba qaramin abu bane kaso mutum so mai yawa,baya ga yawan kuma yake cike da zallar gaskiya da sahihiyar soyayya,kana sanya ran samun koda kwatankwacin abinda kakeji ne a matsayin tukuici da sakamako......sai kuma ya zamana abunda zai dawo maka shine dauke kai.....rashin nuna halin ko in kula da yanayin da kake ciki.
A duk da hakan ta dinga dorawa hadi da lallaba rayuwarta,ta kuma rungumeta a yadda tazo mata,tayita tasa al'amuranta a gaba tana watsa damuwarta baya,saidai duk da hakan babu wata nasara me yawa data ci,domin kuwa a kwance damuwar take a qasan zuciyarta,duk wata walala da fara'a dake saman mu'amalarta ta yau da gobe fake ce,wato jabu.
A hankali ranakun suka dinga zuwa suna wucewa fewww kamar ana jansu,watannnin da malam ya sanya na aure suka dinga qaratowa,a lokacinne iman din ta dinga wata rama a tsaye tana qarewa,saidai hakan bai hanata duk wasu sabgogi nata ba,musamman makaranta da karatunsu ya sake daukar dumi,dama bahaushe yana cewa idan aski yazo gaban goshi yafi zafi,sau tari inna na binta da kallo fana qiyasta ramar datayi,sau daya ta kwatanta yi mata magana tace mata
"Inna,makarantar nan babu sauqi,don dai kawai burina ce da tuni na barta,bakiga karatun dake gabanmu ba inna da sai kin tausaya min" da wannan amsar ta fuskanci inna,ta qyaleta akan hakanne amma badon ta gamsu ba.
A lokacinne sadiqu yayi mata zancan motarta wadda ta taho da ita daga gida bassam,motar da tun a sannan take ajjiye,cewa tayi a tattara a saida komai daya danganci gidan bassam din,saboda batason koda tuna cewa ta taba rayuwa dashi,aka siyar din kuwa,saiga kudi tarin yawa,ya buqaci jin me take so ayi mata dasu,tace ya tarkata kudin kawai ya bawa inna ta ajjiye mata,saboda a yanzun bata da nutsuwar sanin me za'ayi mata dasu.
A nutse sannan kuma a hankali shirye shirye suka gudana cikin gidan na auren cikin ruwan sanyi,bata data cewa kamar yadda bata da wani feeling akan auren,dukkan wata kulawa da tattali tana samunta dari bisa dari wajen dr ahamd,ta yadda gwanine ta fannin soyayya,ta kuma yadda da cewa likitoci ba baya ba wajen iya soyayyar, they are very romantic,saidai kwata kwata babu wata gamsuwa ko burgewa tattare dashi a ranta.
Hutun da suka samu juma'a asabar da lahadi taji tana sha'awa matsawa daga bigiren da take izuwa wani,tayi gajeran tunani akai,nijer yayi mata nisa,hakama maiduguri,sai ta yanke zuwa jigawa,gurin data jima bata je ba,duk da cewa garin na daya daga cikin garuruwan da take qauna,sai faduwa tazo mata dai dai da zama,dama kuma yaa baraka tana yawan qorafin yadda ta zubar da ita gaba daya.
Ta sanarwa inna batun tafiyar,inna ta gayawa malam,babu wanda ya hanata,saboda gidan yaa barakan kamar gidane a wajensi gaba daya,a ranar tahau shirinta,ta kuma kwana dashi,washegari qarfe goma na safe ta gama komai,ta fidda qaramar jakar hannunta ta matafiya,mayafinta na rataye bisa kafadarta batakai ga yafawa ba ta fita parlor.
Mutum na farko data fara gani alameen dinne,sanye da shadda wadda aka yiwa dinkin zamani,yana zaune saman carpet,ya tanqwashe qafafunsa yana cin funkaso da miyar da tayi da safen,hularsa na aje gefe,wayarsa kuma na saman hular a ajjiye,sai muqullin motarsa daga qasa daban shima.
Kamar ko yaushe gabanta ya doka,wani sassanyan kyau me aji yake fitarwa,sumarsa dako yaushe take qara kyau tayi kwance tana ta qyalli,tadan saci kallon hannunsa,har yau bataga mutum mai tsananin gayu da tsafta dake cin abinci da hannu ba irin ameen ba,yayi masifar iyawa kuma,abun sai ya zama wani ado,kamar irin yana cin abincin ne in a stylish way kuma gangan.
"ina kwana" ta gaidashi ba tare data kalleshi kota tsaya ba tana takawa zuwa gaba,shima hankalinsa na ga tv ya amsa mata yana ci gaba da cin abincinsa a nutse.
Qaramar ajiyar zuciya inna ta sauke a fakaice tana fuskantar iman
"Har kin fito?"
"Eh inna,inaso na isa ne kafin rana tayi zafi,kinga ya baraka da zumudi harta kirani wajen sau biyu fa wai na taho kuwa?" Tafada murmushi na subuce mata,kyawawan farare kuma jerarrun haqoranta suna bayyana.
Sunan ya barakan data kira yadanja hankalinsa,da idanu yadan dubeta sanda blue eyes dinga kega inna,amma yana iya hangen fuskarta tar,fuskar data qara haske amma ta dan sirance kadan,a yadda yake kallon wajen ba zaka taba zaton ita yake kalla ba,saboda tsabar qwarewa wajen iya basarwa,jigawa kenan zata je?,amma ko jiya da daddare sunyi waya mai tsaho da ya barakan amma bata gaya masa ba,hakanan ita dinma jiyan daya dawo ya taddasu parlor amma baiga alamun zata wani waje ba.
Zaren tunaninsa ya katse sanda inna ta miqe tana cewa
"Malam yasan kayarsa,shi yasa kafin yafita yabar miki saqo yace koda zaki tafi kafin ya dawo din"
"Wallahi inna,banaso rana ta take din nan ban isa ba" tayi maganar tana kallon agogonta dake daure a tsintsiyar hannunta,daga bisani kuma ta sauke,ta maida dubanta ga mufida,wadda taqi magana tun daxun,cikin qaramar dariya tace
"Wai har yanxu fushin ake dani saboda nace bani zuwa dake?,yanzu banda abunki mufida.....kwana uku fa kacal zanyi na dawo,ta yaya zamu yoye mubar inna ba mataimaki?,ki bari na miki alqawari kuna hutu zan kaiki,indai ya baraka ce tana maraba da kowa" sai a sannan ta saki ranta.
Inna ta dawo da saqon tana miqa mata ya miqe shima,ya dauki dukka kayansa
"Zan wuce inna,sai na dawo"
"Har ka gama?"
"Eh ya isa haka"
"To Allah ya bada sa'a,a dawo lafiya,Allah ya tsare" ta rakashi da kyawawan addu'o'inta kamar yadda ta saba gami da fatan alkhairi,sannan ta maida hankalinta ga iman tana sake mata bayanin saqon malam da kuma kudin motar daya bayar a bata.
A hankali take takowa zuwa harabar gidan,tana tunanin tashan da zataje ta samu mota mai kyau wadda kuma zata tashi da wuri,ta buda qofar gidan ta fita tare da fatan samun abun hawa da wuri,saboda unguwar tasu wani lokaci wahalar abun hawa akeyi.
Batayi nisa ba taji nishin mota daga bayanta,bata damu ta juya ba don tasan adai dai take ba sama hanya take tafiya ba,motar na gotata kadan tayi parking,sai a sannan ta dubi motar.
Ya ameen ne,kafin ta qaraso taga ya bude front seat,hakan yana nufin kenan ta shiga. Tsaiwa tayi sanda ta qaraso wajen,saboda murfin motar ya rufe hanyar da zata iya wucewar
"Shiga mu tafi" taji ya sake fada,ta kalleshi idanuwansa na kan hanya,fuskarsa kuma sam babu alamun fara'a ko kuma wasa,lallai yau akwai damuwa,idan batayi wasa a yau din ciwonta zaisha sabon fami,ita da ameen din a mota daya?,da kuma kusanci irin wannan?,bata da sauran option face shigar,ta janyo murfin motar ta rufe,ya dage dukka gilasan sama tada motar ya fara gangarawa a hankali,sannan ya saka hannunsa ya kunna ac madaidaiciya yadda ba zaka takura ba.
Shuru ne ya ratsa cikin motar,sai wani slow music dake tashi can qasa cikin qaramin sauti,tafiyarsu ta dauki kusan mintuna goma,sannan lallausar muryarsa mara son hayaniya ta motsa
"Da gida yaa baraka zaki baki gayamin ba?" Yayi maganarne idanunsa nakan kwalta,hannunsa daya kan sitiyarin motar,daya hannun kuma yana zagaya labbansa da 'yan yatsunsa.
Yadda yayi maganar koda bata kalleshi ba tasan 'yan sarautar ne suka motsa masa,tafi kowa sanin halayyarsa ciki dabai,sau da dama tana iya gane mood dinsa daga sound dinsa ba tare data kalleshi ba.
Bataga dalilin da yasa saboda zata wani waje sai ta gaya masa ba,kamar hakan a yanzun bashi da alaqa da rayuwarta.
"Na zaci ka sani" itace amsar data iya bashi kawai,saiya waigo ya dubeta ya kuma maida kansa ga titin duka cikin abunda baifi second uku ba,kafin yace komai wayarsa ta dauki qara,yadan saci kallonta,sai ya sauke hannunsa guda daya ya latsa wayar ya maqalata a kunne
"Wa'alaikumussalam....." Yafada da muryarsa mai nauyi a wasu lokutan,murmushi ya danyi,abunda yasa iman juyar da kanta sosai ga taga tana tabe baki
"Alhamdulillah" ya sake shuru kafin ya kuma cewa
"Zan kiraki,ina tuqi ne..... okay,nima haka,byee" ya zame wayar a hankali ya maidata inda take,bai kuma cewa komai ba,itama bata sake magana ba,don dama bata son magana a tsakaninsu,taci gaba da kallon titi.
Kamar zatayi magana sanda taga yanata wuce tashoshin motar daya dace ace ya sauketa,amma kuma daga bisani itama sai ta shareshi,tunda yafi kowa sanin ya daukota,tun tana saka ran zai sauketa a wata tashar qila a gaba har ta debe tsammani,saboda sun fara barin kano,sun wuce tamburawa ma,don haka saita zaro wayarta kawai ta kunna data ta shiga WhatsApp.
Tayi chart mai yawan gaske da qawaye da kuma dangin da take mu'amala dasu,tanata kasa kunne taji yace sauko amma shuru,sannu a hankali sai gasu a garin wudil,ya gangara gefan titi,ya shiga wani layi,tabi layin da kallo tana mamakin yadda aka samu layi me kyau da girma haka cikin qauye,saika dauka cikin unguwar gadon qaya dake birnin kano kake,baiyi nisa a layin ba taga ya tsaya,ya dauki wayarsa yayi kira
"Gani na qaraso..... okay.... okay" wayar ya ajjiye ya sake taka mota zuwa gaba,sannu a hankali sai gasu a qofar wani babbar katanga,ya sake daukar waya yayi magana,bai sauke wayarba mutum ya fito daga babbar qofar dake maqale da katangar
"Ku qaraso ciki mana" mutumin ya fada da murmushi,yana yiwa wani dake zaune a wajen magana kan ya bude qofar,ya dage musu alameen din ya saka kan motar ciki,sai gasu a wani katafaren waje dake da yalwar shuke shuke iya ganinka.
Baice komai da itaba ya fita,saidai ya zagayo side din da take yabuda murfin motar,take iska me kyau da dadi ya fara shiga tana fita,ya juya cikin takunsan nan mai cike da aji yabi mutumin sukayi ciki,ba jimawa suka bace cikin wajen.
A hankali take nazartar wajen,data lura da kyau ya fahimci gidan gona ne,saidai da alama wajen ya mutu ne,ma'ana ba'a aiwatar da komai a ciki,taci gaba dabin wajen da kallo,saita sauke ajiyar zuciya ta sake jan wayarta tana duba lokaci.
Batasan me yasa. Ya daukota nan yakeson bata mata lokaci ba,duk da cewa ta sani inda motar hayane babu lallai ma ace yanzu sun kawo wudil din.
Tana tsakiyar tunanin taji ana sallama,ta waiwaya a hankali,su biyu ne a tsaye riqe da manyan ledoji guda hudu,da alama mutanen karkara ne
"Hajiya yalallabai ne yace a kawo,a saka a cikin mota"
"To bismillah baba" ta fadi tana bude musu seat din baya,suka saka ledan suka rufe,basukai ga bacewa daga wajen ba taga bullowarsa tare da mutumin,kusan minti goma suka kashe a waje suna sake magana sannan sukayi sallama,ya sake shigowa motar,yayi bismillah ya kunnata suka fice daga wajen.
Tun kafin su shiga wajen ta karanci tasha suka shigo,a nutse ya sanya motarsa a ciki,bau saurari masu tararsa suna tambayarsa inda zashi ba,da alama yasan wajen wanda zashi,baiko tsaya ba har sai daya qaraso.
"Bismillah muje" yafada yana bude motar,yadda yace haka ta biyoshi a baya,tana tsaye sukayi magana da wani,kafin a bude qaramar golf,lamin din yace ta shiga,aka debo wadancan ledojin aka saka a ciki,ya qaraso bakin window din motar
"Ki gaisheta,Allah ya kiyaye" yayi maganar idanunsa tar akanta
"Ameen" ta amsa ba tare data iya dubanshi ba,sabida tasan tayi qarya a yadda suke very close ta iya kallon qwayar idanun nasa,janye dubansa yayi zuwa ga driver din
"Mutumina ayi tuqi a hankali"
"In sha Allahu yallabai,ni daka biyani harda riba,gaggawar me zanyi kuma?"
"To Allah ya tsare"
"Ameen ameen" daga haka yaja da baya,shi kuma ya tashi motar suka fara ficewa daga tashar,zuciyarta natason ta waiwaya saboda ta tabbatar yana tsaye yana kallonsu amma ta hana kanta aiwatar da hakan,ta saki ajiyar zuciya sanda suka hau titi tana duban hanya,duk da ya biya kudin motar wa ita kadai babu takura babu matsi,amma hakanan kawai taji tafiyar ta rage armashi,ba kamar dazun ba.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 57
Ina ka saka ina ka aje yaa baraka ta dinga yi da iman din,farincikinta ya kasa boyuwa,kamar zata goyata,wanda dama ko a baya kusan hakace tsakaninsu da ita.
"Aah,shine ya kawoki?" Ya baraka ta tambayi iman din sanda ta isar mata da saqonshi,farinciki na taso mata
"A'h,yadai ajjiyeni a wudil,yaje wani waje ne" farincikin data soma ji sai ya koma,batajin zata iya qyale wannan abun yatafi a haka,ba zata barsu duka su biyun suyi asarar kyakkyawan yabanya da iri ba,kara da alkunyar malam da inna tayi yawa,ta tabbatar dukkaninsu suna da buqata da kuma interest akan tarayyar iman da ameen,amma dukkaninsu suna duba wani abu daya faru a baya suna dauke kai da bawa ameen din dama,bayan dukkaninsu asara ce ace kowanne bangare sun rasa wani tsakanin iman da ameen din.
Sosai ya baraka ke ririta iman,cikin kwanakin data debo zatayi,sun sake sabo sosai a tsakaninsu,suna zama suyi hira mai yawa,irin wadda a baya basu taba yin irinta ba,a nan ta sake jij tarihin ameen din da kyau,tayi shuru tana tariyo maganganun da yaa barakan ta gaya mata,lallai sun sha gwagwarmayar rayuwa,kuma dama yawancin irinsu ameen din ariqi Allah yake musu na ban mamaki,gashinan kuwa,kome ya saka kansa zaiyi sai Allah ya sanya masa albarka.
Kwanakin da iman din taso yi wajen yaa barakan ta koma gida bai samu ba,saboda zazzabi da ya kama ya barakan,iman dince ta dinga kula da ita,tayi treating nata sosai,cikin kwanaki biyar ta soma murmurewa,ta warware sarai abunta.
********Karfe takwas saura ne na dare,suna zaune a tsakar rumfar ya barakan wadda ke wadace da haske saboda qaramar wutar solar da ameen din ya hada mata,tuwon dare suke ci,iman ya baraka yaranta maza ukusai autarta,kana ganinsu xakasan cikin walwala suke,har iman din.
Wayar yaa baraka ce tahau tsuwwa,iman dake zaune dab da wayar ta dauko tana duba mai kiran,AMINULLAHI ne a jiki kamar yadda ya barakan tayi saving
"Waye?" Ta tambayeta kafin ta miqa mata,batace komai ba sai ta miqawa usama da yafi kusa da ita ya miqa mata,yayin data ja kwanon tuwonta a hankali taci gaba da ci.
Har sukayi wayar suka qare batace komai ba,yaa barakan ta ajjiye wayar tana sake jan kwanon abincinta
"Qarfe nawa zaki tafin gobe?" Ta tambayi iman,ta daga kanta tana dubanta
"Sai wajen yamma inajin,tafiyar ranar nan bata da dadi ga motar haya,duk sai ka jigata kafin ta isa gida,sannan juma'a ce,zuwa yamma an sauko daga masallaci....akwai wani abune?" Kai ta girgiza
"O'o'o'o imani,akwai saqo ne da nakeso na baki ki kaiwa inna"
"Okay" ta fada tana ci gaba da cin abincinta.
Gefanta ta duba itama inda tata wayar ta kada,da alamun kira kenan,dr ahmad ne,dama kuma kusan lokacin kiransa kenan,sai ta tsame hannunta tana daukar wayar ta miqe a hankali,ya baraka ta bita da kallo,itama tasan me kiran,haka kawai take kishi dashi,bata sani ba....ko kishin da ya kamata qaninta yaji ne ita take jiye masa?,tana kallon sanda iman ta wanke hannunta ta kuma shige daki,saita sauke idanunta a hankali tana addu'a qasan ranta,zuciyarta tana motsuwa.
**********Washegari tunda suka tashi suka kammala abincin safe iman taga ya baraka nata hidimar hada dambu
"Shi kike sha'awa kuma yau yaya?" Iman ta tambayeta tana murmushi sanda take tayata tsinke zogale
"Wallahi,kuma baqi zanyi ma yau din" daga haka bata sake tambayarta komai ba,don ba dabi'arta bace bin qwaqwafi ko yawan tambaye tambaye.
Sun dan dauki lokaci kafin su gama hada komai,ta dauraye hannunta ta tashi tana bude tukunyar da badi'a ta saka musu ruwan zafi na wanka,ta diba ta sirka tana cewa
"Naga alama kadan ya rage dambun nan ya gama turara,bari kiga na fara shiri"
"Don Allah ki qara kwana yaa iman" badi'a ta fada tana kwabe fuska,don sosai taji dadin zuwan iman din,taji kuma dadin zama da ita,ta qaru da abubuwa masu yawa sosai,hakanan ta qara mata sha'awa da kuma qaimin zama nurse itama
"Makaranta badi'a" ta fada tana dan fidda blue eyes dinta
"Kai" badi'ar ta fada tana dan kare fuskarta tana dariya
"Me?" Iman ta tambayeta
"Wadan nan idanun naki ya iman.....aisai su tsiratani,kinga sheqin da suke a hasken rana?,na yarda da maganar kawu aminu kam"
"Me yace?" Ta tambayi badi'ar cikin mamaki
"Idanun imani na musamman ne,akwai wasu abubuwa masu yawa a cikinsu,amma ba kowa ne yake ganewa ba,amma ni nafi kowa fahimta da karantar haka' haka yace,amma nima yanzu na gani,idanunki na gayu ne" murmushi kawai iman din tayi,bata iya amsawa badi'a ba,sai kawai ta tsugunna ta dauki botikinta ta shige bandaki tana cewa
"So kike dai ki tsaidani badia,idan na biye miki lokaci zan bata,azahar ta kusa".
Koda ta fito alwala ta daura ta shige dakin d aka sauketa,ta tsane jikinta da kyau ta zube kayan shafarta ta fara gyara jikinta,komai na iman din mai ajine,farawar karatunta yazo mata da sauyawarta zuwa 'yar gayu ta gasken gaske,duk da cewa dama tunda ta taso ita mai son ado ce,Allah kuma ya hadata da lamin dake fiddata cikin tsararrkinta da dinkuna masu ban sha'awa,wanda ko a sannan sai jikin wance da wance,style kuwa duka yaran layinsu a wajenta suke karba.
Cikin wani lallausan lace mai zanen manyan flowers ta shirya,ba makeup tayi ba,amma yadda hodar da ta saka tabi fatar fuskarta man leben ya haska jajayen labbanta....daurin kanta ya zauna da kyau cikin wani style mai ban sha'awa ya sanya zakayi zaton zama tayi tayi kwalliya,iman me kyau ce har yau har kwanan gobe,kyanta yana da wani irin sanyi da kuma fusgar hankali,inda Allah ya rufa mata asiri,ta tashi gidan tarbiyya,batasan shigar banza ko fidda tsiraici ba,da mazan da zasu halaka ta sanadinta suna da yawa.
Tsakar gida ta fito zata shiga rumfar yaa baraka ta dauko jotter dinta da tayi amfani da ita jiya ta barta,zata qarasa rubutawa badi'a sunan wasu litattafai da zata dinga dubawa saboda turancinta ya zauna sosai,ya barakan dake cikin daki tace ta duba mata dambu ya nuna,ta zame murfin tukunyar ta bude buhun ta debo tana tabawa,dai dai lokacin da sallamarsa ta ratsa tsakar gidan,abunda batayi zato ko kuma tsammani ba,don haka ta waiwaya gefanta inda qofar shigowa take.
Aminullahi ne,cikin shigar manyan kaya,komai nashi fari tas,kayan da suka qara masa cika kwarjini da kuma kamala,fuskarsa tayi fes fresh da ita,ba abunda take fitarwa sai annuri,gashin kansa dana fuskarsa yasha gyara,duk da cewa matafiyi ne amma jikinsa bai nuna hakan ba,sassanyan qamshinsa ya busa da iskar dake kadawa cikin tsakar gidan ta kwasoshi da gudu izuwa hancin iman,yanayin da ya haifar mata da faduwar gaba,tsimammun idanunsa masu dauke da wani magnet suka so kashe mata jiki da zuciya,cikin tata jarumtar ta janye idanun nata tana amsa sallamarsa,tare da qoqarin saka dambun data debo da yatsun hannunta a baki ta fara taunawa.
Idanunsa sauka kan labban nata da suke qyallin lip balm,tana motsasu a hankali saboda taunar da takeyi,ya dauke kansa da sauri saboda wani abu daya zuba cikin jikinsa,ya waiwayawa ga usama da musa da suke biye dashi
"Kun dauko komai?"
"Eh kawu" sai yaci gaba da takowa zuwa cikin gidan,wanda kafin ya qaraso iman ta shige rumfar yaa barakan,a saurin da take na dauko jotter din tayi tabar masu falon.
Saidai kuma sanda ta dauka take shirin juyowa tuni ya cire rufaffun takalman qafarsa ya sanyo qafarsa zuwa parlon,dole cikin hikima ta koma da baya ta zaune cikin kujerar da tafi kusa da ita tana buda shafukan jotter,batason a yau ta bashi dama ko qofa ko guda daya da zata bada kanta ko aikata wani abu ba dai dai ba,don haka tabi sahun 'yan sannu da zuwa ta marabceshi kamar kowa,dai dai sanda ya baraka ta iso falon fuskarta cike fal da fara'a
"Wai dama da gaske kake?,kai dake da tarin ayyuka fal a gabansa?,da kayi zamanka ai tunda na warke,itama iman din anjima kadan zata koma"
"Bazan nutsu bane idan banzo na ganki ba" ya qarashe furucin idanunsa na sauka akan iman,tayi masa wani kyau daya jima bai gani ba,shigar ta karbeta abundanita bata sani ba,abunda yadan ja hankalin ya baraka,ta gefan idanu take qoqarin gano me yake kalla?,saita saki boyayyen murmushi kafin ta amsa masa
"To ai gani lafiya qalau alhmdlh,babu abinda ya gutsireni ko?" Maida dubansa yayi gareta,cikin girmamawa ya fara gaisheta
"Barka da yamma,mun sameku lafiya?"
"Alhmadlh,ya inna da malam,ya ka barosu?"
"Lafiya qalau,sunce na gaidaki da kyau"
"Na gode sosai,na warware" waiwayawa tayi inda iman take
"Iman,muna da ruwa kuwa?" Sai a sannan ta daga kanta,cikin wani salo da bilhaqqi batasan tayishi ba tayi maga a yangance
"Ba za'a rasa ba" saita ajjiye jotter din ta fara takawa a hankali zuwa tsakar gidan,inda a rumfar da aka kafawa qofar dakunan yaa barakan dan madaidaicin fridge dinta da lamin din ya siya mata yake,kamar wanda ake jansa haka yaji zuciyarsa na mararin binta da kallo,amma ya nuna matuqar mazantaka ya danne kansa
"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" ya dinga maimaitawa,baisan me ya faru dashi ba,wani tsohon abu......wani tsohon miki keson tasar masa,wani tsohin feelings da kuma wani mataccen yanayi daya jima da zubdashi a wani waje mai nisan gaske.
Da ruwan dama sauran lemon kunun aya datayi musu a jiya ta shigo saman dan faranti,tana shigowa ya baraka ta miqe
"Zuba masa ina zuwa,bari na sauke dambun"
"Ki bari na sauke yaaya" iman ta fada tana sauri saurin dire masa ta fice
"A'ah,wanka zan shiga ai daga can,ni kaina zafi nakeji,wasu zannuwa na nakeso kiyi musu iron inason sakasu anjima zan leqa suna hayi" bata saurareta ba ta nuna mata dutsen gugar ta sanya kai ta fice.
Daga tsakar gida ta yiwa yaran magana kan kada wanda ya shiga parlor din,ta sauke dambun,ta saka badi'a shiryawa ameen nasa a fulasai masu kyau sannan ta wuce wankan.
Daga can parlor kuwa kamar an buge mata gwiwoyinta haka iman taji,bata shirya zama dashi waje daya ba amma yaa baraka ta rushe mata dukan plan din nata,hasalima inda socket din gugar yake yana daura da ameen dinne,saidai duk da haka ba zata bari yaga lagonta ko karayarta ba,don haka ta qarasa gabansa ta tsugunna,ta bude lemon ta fara tsiyaya masa a cup daidai misali,sannan ta dauko zata miqa masa.
Batasan duk abinda take ya kafeta bane da ido sai data miqa masa lemon,maimakon yakarba sai yaci gaba da sauke mata nauyin idanunsa
"Gashi" ta fada cikin jarumta,duk da yadda taji zuciyarta kamar ta fara narkewa
"Mantawa kikayi cikin gidan nan ba mata bane kadai akwaisu usama?" Da mamaki ta dago ta kalleshi,saidai ta kasa jurar kallonshin,saboda idanunsa sun ninka nata a nauyi da dafi mai tarin yawa
"Su usama kuma?"
"Eh,ko su ba aure a tsakaninku?.....duk da ban sani ba ko wancan likitanne ya baki wannan damar......" Daga haka ya miqa hannu zai amshi cup din,ta fada nazari kan ma'anar maganarsa,abunda yasa bataga tahowarsa ba,sai sukar dumin hannunsa saman nata hannun,take ya ratsa dukka wasu sassan jikinta qashi da jini yakai ga qwaqwalwarta cikin sakannin taqaitattu.
Kamar jan wayar wuta hakanan kowannensu yaji,suka janye hannunsu lokaci guda,sanadin barewar lemon kenan saman skeet dinta,ta miqe da sauri sakamakon sanyi daya ratsata,kallon kallon sukayi na second biyu,sai ta juya da hanzari ta fita a parlor din.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 58
Ajiyar zuciya ya saki yana maida jikinsa zuwa bayan kujerar yayi relaxing yana sauke ajiyar zuciya,wani yanayi na bin dukka sassan jikinsa,gajiya na sauka a gabbansa kamar wanda aka yiwa duka,gajiyar da tuqin ma da yayi daga kano zuwa jigawan bai jita ba,a haka yaci gaba da kasancewa,shi baisha ruwan ba bai kuma sha lemon ba,hakanan bai buda idanunsa ba har saida ya baraka tayi sallama cikin parlor din,idanunta kan fuskarsa sanda ya bude idon nasa tana karantar yanayinsa
"Ya bakasha komai ba?"
"Am ok,da ruwana a mota ma.....qarfe nawa masallacinku suke tayar da sallar juma'?" Yayi tambayar yana duba agogon hannunsa don kaucewa tuhumar ya baraka
"Qarfe biyu ne"
"Ok,bari muje can muyi salla mu dawo,naga biyun saura" saiya miqe yana kashe wayarsa ya barta nan saman kujerar,ya zare agogon hannunsa yana kiran usama
"Kuyi alwala mu wuce masallaci,kuna kusa da masallaci amma ku dinga zama a gida?,ba zaku tafi da wuri ba har sai kunji an kira sallah?,kunsan falalar zuwa masallaci da wuri kuwa?" Da wannan fadan suia fita tsakar gida,badi'a ta zuba masa ruwa a buta yayi alwala,ya cire babbar rigarsa ya bata suka wuce masallaci shida 'yan mazan.
Tana daga daki tana jiyo badi'a dake shanshana rigar ameen
"Kai jama'a,kawu wanne irin turare yake sakawa?,waishi wanne irin dam gayune?,komai nasa qanshin yake,yaaya,Allah rannan da yazo ya kwana yace na hada masa kayan datti cewa nayi basuyi datti ba,don ni dai qamshi naji sunayi" bata ji dai amsar da ya baraka ta bata ba,amma taji badi'ar tayi dariya sannan ta wuce zuwa cikin parlorn.
Shuru shuru basu dawo ba,harsai da ya barakan ta fara jajjabi da cigiyarsu sannan taji shigowarsu,muryar usama taji yana lissafa mata gidajen 'yan uwa sa sukaje,yaje gaida tsofaffi cikin danginsu da kuma yi musu alkhairi kamar yadda ya saba,wannan al'adarsa ce kuma dabi'arsa ce duk sanda ya shigo jigawa zaiya zagayawa dattijai da manya na gari dama na cikin familynsa,wannan ya sanya masa farinji da kuma daukaka,sannan ya siya masa soyayya mai tarin yawa daga wajen mabanbantan mutane,iyayensa da suka rasu kuma suka samu addu'o'i masu tarin yawa daga makwancinsu.
Tanaji ya baraka na kirata,sai kawai ta miqe ta tayar da sallah abunta,data idar ma zamanta tayi,sai data ji tana sake kiranta sannan ta tashi,ta sauya kayan jikinta tun dazun zuwa wata bubu ta material ruwan makuba mai dan haske kadan,ta yane kanta da mayafinta ta nufi dakin.
Shi ta fara gani,sabida ya zauna ne yana fuskantar qofar shigowar,cikin babban faranti aka zuba musu dambun shi da usama da musa suke ci tare,yana da wannan sauqin kan qwarai da kuma son mutane,a jininsa yake,ita shaida ce,kanta ta kawar cikin basarwa da nuna halin ko in kula ta qarasa wajen ya baraka
"Ya zaki zauna daki kowa yana zaune yana cin abinci?" Murmushi tayi,murmushi da ya qawata fuskarta qwarai
"Sallah nayi,yana raina,har Alla Allah nake na idar" agogo ya barakan ta kalla
"Ai gwara ki hanzarta,don kamar qarfe biyar naji yace zaku wuce" dan turus tayi,ita sam bata wani kawo tare zasu tafi ba,kuma ko yanzun batajin zata bari su tafi tare,bata marmarin hakan,gwara kowa yayi hanyarsa
"Ko?,tafiyar tamu zatayi dai dai?,ko na biyo shi a motan kasuws gudun bata lokaci?" Tas ya gano inda ta dosa,ya kafeta da idanunsa daga nesa inda yake zaune yana karantar fuskarta
"Aha saboda wahalar dakai?,ki gama a nutse,abunda baki hada bama na taho miki dashi idan zan wuce maiduguri" a hakali ya dauke dubansa daga kan iman ya maida kan ya baraka,me zataje yi a maiduguri kuma?,iyakar saninsa a danginsu basu da kowa a can bare yace zumunci ko kuma wani abun zai kaita,bai tambaya ba,sai ya maida kansa kawai ga abincin da suke ci.
Karo na biyu kenan badi'a ta shigo dakin,ta dubi iman dake xaune sosai abunta,kamar ba ita ya ameen din ke jira ba
"Yaa iman.....yace ki fito,ke kadai suke jira wallahi,har ya kunna motar" a nutse ta dubeta hankali kwance
"Tare mukazo da xaki damu yana jirana?,ba nace miki yayi gaba zan taho a bayanshi ba?" Dan buga qafarta kadan tayi sannan tace
"Wallahi na gaya masa....shine ya sake turoni"
"To kije ki maimaita masa,tunda saqon dai dana baki kenan" daga haka ta jawo wayarta tana duba kiran dake shigowa,ba kowa bane dr ahmad ne,saita daga wayar ta kara a kunnenta.
Kashe motar yayi yabar key din a jiki bayan badi'a ta gama bayaninta,ya zuro qafafunsa a hankali ya taka zuwa cikin gidan,ransa yadan baci amma kuma ya danne,zuciyarsa nata lissafa masa abubuwa iri iri kan ma'anar qin tafiyarta dashi.
Kai tsaye dakin da take ciki ya nufa,yasa hannu a nutse ya yaye kabulen dakin,hasken da ya bayyana shi ya ankarar da ita wanzuwarsa a wajen.
Wayar dake kunnenta fa sauke,yabi wayar da kallo kafin ya maida dubansa kan fuskarta
"Tashi ki wuce muje" ya bata umarni kai tsaye cikin dakakkiyar muryarsa yana kallonta tsakiyar idanunta kanshi tsaye,irin kallon da a baya yake mata can shekarun baya duk sanda tayi wani laifi yakeson kuma nuna mata tayi laifin ba tare da ya magantu ba.
Bata da zabi illa miqewa da tayi,saidai fuskarta ba annuri,ta qarasa inda ta ajjiye akwatinta ta kuma dora mayafinta akai sanda tayi shirin tafiyarta tun na dazu,ta yafa mayafin ta fidda takalmanta ta sanya duka yana tsaye,saita tako a hankali zuwa bakin qofar fita,sai kuma taja ta tsaya,saboda babu wani sauran space daya rage mata da zata iya fita,idan kuma tace zata saka kai a hakan ta fita to ba shakka saita fara mannuwa da jikinsa.
Kamar xata saki kuka yadda ya tsaya ya zuba mata idanunsa yana kuma hukuntata dasu ba tare da ya dauke kallonsa ba,ya kuma sani cewa lallai saiya matsa din xata samu hanya,duk da yadda ta dauke masa kai amma jikinta yana karbar horo yadda ya kamata,idanun ameen din nada wani irin tasiri tattare da ita,don ko sanda tasha giyar maqaryaciyar soyayyar bassam tayi tatil bata iya kallon qwayar idanunsa ta gaya masa magana kanta tsaye
"Zan wuce" ta fada ganin bai da niyyar matsawa
"Wuce" yace da ita,ta daga kai tana duban hanyar daya bata,tazarar bata da wani yawa,idan ba mugun kulawa tayi ba saita shafeshi,wannan wanne irin sabon abune kuma ya amin din yazo dashi?.
A hankali kuma cikin takatsantsan ta soma ratsawa ta gabansa,sai dataje tsakiya ya rufe hanyar,numfashinta gaba daya ya tsaya a maqogoronta,da tabbas ko yaya ta motsa cikin faffadan qirjinsa zatayi masauki
"Duk randa na sake cewa ayi abu kika musamin zakiga yadda zanyi dake,idan kin manta na tuna miki....lameen ne.....yayanki daya raineki da hannunsa tun kina majina a hanci,wannan girman da kuma auren da kika tabayi bazai sauya komai ba" ya qarashe maganar yana duqawa har tana jiyo saukar numfashinsa saman fuskarta,ya sabule jakarta data ruqo
"Wuce ki jirani" ya fada tana dai daita tsaiwarsa,wuf tayi ta samu ya fice,qafafunta na sarqewa saboda tsaratan da tayi,saboda ta tsammaci lamin din rungumeta kawai zaiyi saboda tsabar kusancin da yayi yawa a tsakaninsu.
Luf tayi a gidan gaba,tana jin yadda kowanne sashe na jikinta yake amsawa,ajiyar zuciya take saukewa a jejjere,idanuwanta a rufe har zuwa sanda badi'a ta kawo mata jakarta ta sanya cikin motar,tazarar kusan minti biyar taji muryarshi,ta karkata kanta zuwa gefe a hankali,ta hangeshi yana rabon kudi wa su usama da abokanshi,fuskar nan a tsume,batasan me yasa idan ya hade rai irin haka yake qara masa kyau ba,sai ta maida idanunta ta lumshe,don bata fatan ya juyo yaga tana kallonshi ta kunyata,ko kuma ajinta ya zuba.
"Subhanallazi sakkara lana haza wama kunna lahu muqrinun,wa inna ila rabbina la munqalibun" ya furta addu'ar da lallausar muryarsa bayan ya kunna motar,har zuwa sannan bata yarda ta bude idanunta ba,a hankali ya fara motsata suka fara barin layin.
Wata tafiya sukayi ba um ba um um,sai daga bisani ya dannan wani karatu wanda ke magana kan bin iyaye da kuma haqoqinsu akan dansu,a hankali karatun ya dinga shigarta,ya kuma kashe mata dukkan wata laka ta jikinta,sosai karatun malamin ke shiga duk wani bargo na jikinta ya kuma bi ta magudanar jini,lallai da gaske a baya ta tafka kuskure mai girma a rayuwarta,Allah ne yaji qanta ya kuma tsamota,da kuma addu:ar da ta tabbatar su innan sunci gaba da yi mata ita,koda a zahiri sun nuna basa tare da ita.
Ko wayar da dr ahmad keta faman yi mata kasa dagawa tayi,tayita rejecting tana maida idanunta ta kulle,sunyi nisa sosai ya sake kira
"Koki kashe ko ki sata a silent,ko kuma ki daga,qararta yana damuna,idan kuma na karba ta tafi kenan,ta window zan cillata" sosai kalamansa suka bata mamaki,wai yaushe ya lamin din ya koyi zafi haka?,tadan saci kallonsa da hanzari ta kuma dauke kanta,har yanzu fuskarshin a cakude take,sai kawai ta tura masa gajeran saqo tans hanya,idan ta isa gida zata sanar masa,ta kashe wayar gaba dayanta ta jefata a jakar hannunta,ta gyara zamanta da kyau ta lafe cikin kujerar motar.
Sun baro jigawa da wuri,to amma wajen shigowa kano anan matsalar bata lokacin take,sun tadda tarin traffic a hanya daya dinga bata musu lokaci,wannan yasa basu isa gida ba sai ana sallar isha'i,don suna shiga ma a toilet din farfajiyar gidan ta daura alwalarta tayi ciki,Allah yasa ma ya tsaya a wani masallacin hanya na matafiya sunyi magarib,ya kuma siya musu takeaway.
Da idanu inna ta bisu sanda suka shigo mata,wani abu na taba zuciyarta,tana kuma rayawa cewa inama a matsayin miji da mata suka shigo mata?,sunyi bala'in dacewa,irin dacewar data amsa sunanta,sannan fili da badini kuma babu ta inda basuyi marching ba.
Mufida kam dadi ya isheta yaa iman ta dawo,sadiqu ya kalleta
"Idan tayi aure naga ya zakiyi,ba zaki iya zama gidan nan ba kenan" sadiq na gama fadawa miqewa ameen yayi,hannayensa cikin aljihunsa yace
"Zan shiga na watsa ruwa,a gajiye nake,idan ka shigo xakaji yadda ake ciki da mutanen nan,dazun inakan hanya sun kirani"
"Okay,karka damu,ka huta sosai,ko zuwa gobe ma tattauna"
*********** Da sauri da sauri kwanakin bikin da aka sanya suke qara rage kansu,lokaci yaci gaba da wullawa yana kuma matsantowa,ya zuwa lokacin iman din sam ko a jikinta bata wani jin cewa aure zatayi,kawai kallon kowa da komai takeyi,a yanzun hankalinta gaba daya yafi tattara ga karatunta,saboda batason ta samu wani kuskure ko tasgaro,tanason koda bata tsira da komai ba ta tsira dai da karatun nata.
*********Ranar wata laraba da yammaci ta dawo daga makaranta sukaci kacibus da yaa baraka a qofar gida,tana rataye da jakarta,sadiqu na biye da ita da wata babbar leda a hannunsa
"Ashe da rabon dai zamu hadu,shi yasa ya gana ta zaunar dani" ta fada fuskarta fal murmushi tana duban iman,murmushi itama iman din ta maida mata,a wannan karon ta cika da mamakin yawan ganin ya baraka da take a gidansu,wanda a baya sam ba al'adarta bace,takan jima bata shigo kano ba saida wani dalili,amma kuma data tuna bikin dake cikin gidan nasu harda na dan uwanta qwaya daya tilo sai mamakinta ya ragu,saidai kuma taji ta ambaci yaagana,badai bikin da ya rage sati kusan hudu ta tahowa tun yanzu ba?.
"Don Allah ya baraka ki bari sai gobe,kinga fa yamma tayi sosai,kafin kije dare yayi,kuma naga ya lamin din baya kusa bare ya kaiki koda tasha ne" ima din ta fada cikin kulawa
"Ahaf.....rabu da dan nema,dama banaso yasan nazo din ai,saidai yaji labarin zuwan nawa....kedai ki kwantar da hankalinki,tun ana saura sati tahowa kano ya sameni,sai an gama komai 'yan jigawa zasu kuma ganina" murmushi kawai iman tayi wanda ya tsaya mata iya wuya,ita kanta kenan tana farinciki da auren samha da dan uwanta,saidai sam bataga laifinta ba,babu wanda bazaiso ace nashi yaci gaba ba,dole a nan sukayi sallama ta bata sallahun gaida mata da badi'a ta sanya kai zuwa cikin gidan.
A hankali tayi sallama cikin parlor dinsu,saidai a maimakon ya gana dake zaune a parlor din ita da inna ta amsa,saita rafka mata guda,gudar data sanyata karaya,wasu tarin tawagar hawaye suka danno kai,saidai tayi qoqarin tsaidasu,sannan uwa uba salatin da taji yaagana ta rabza wanda ya sanyata tsaiwa cak cikin tsoro tana dubanta...
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 59
"Yau me zan gani ni aishatu?" Ta fada tana kame baki tare da qarewa iman kallo,kallon da ya sanyata ta tsargu,ta kuma soma bin jikinta da kallo,mufida ce da itama ta tsorata tayi qarfin halin tambaya
"Mene yaa gana"
"Amarya nake gani gayanta,babu wani canji,babu kuma wani abu da zai nuna maka cewa amarya ce,wannan abun kunya har ina?,ke binta kina me?" Cikin kara da kuma alkunya irin ta innar ta miqe tana murmushi,ba zata iya cewa yaagana komai ba a matsayinta na yayar mijinta,sai kawai ta fada kitchen tabar su mufida da dramer.
Cikin sanyin jiki dana gwiwa iman ta fara takowa,a qalla tadan samu wani qwarin gwiwar,tsoron da ya ganar tasa taji ya ragu
"Wallahi yaagana kin masifar ban tsoro,na dauka wani abun kika gani a jikina"
"Wani abunne mana,wannan abun kunya har ina?,kina can zaki qare a yawon boko,auranki saura 'yan satittika amma baki canza daga yadda na sanki ba?,to Allah ba za'ayi wannan abun kunyar damu ba,wannan auren dole ayi masa shiri na musamman ehe...saboda wancan babu rawar da muka taka,so nake ki canza gaba daya,idan ba kyakkyawan sani akayi miki ba banason a ganeki" baki kawai iman din ta saka tana kallon yadda yagana ta haqiqance,wai ko don basusan yadda takeji bane a zuciyarta?,jinta take kamar mutum mutumi,basusan ta fidda miji bane saboda ba zata iya cewa malam bata da kowa ba?,ta fidda mijine saboda ta fuskanci sun shirya aurad da ita?,batason tace bata da tsayayye kada hakan ga sake bata musu rai.
Duk lissafe lissafen da yaagana ta shiga yi kallonta taci gaba dayi,so take ta sarara mata ta barta ta shiga dakinta ma ta raba kanta da kayan jikinta.
Kamar bushira tasan me akeyi saiga sallamarta,ajiyar zuciya iman ta saki
"Yauwa,don Allah bushira qaraso"
"Eh qaraso ciki,dama ke nake nema" yaagana ta fada,akwai kyakkyawan sani da kuma alaqa mai kyau tsakaninta da bushira,tun zamanin rikicin aurenta da bassam
"To gani yaagana,Allah yasa ba laifi mukayi ba?" Ta fada tana dariya hadi da neman wajen zama
"Qatoton laifi ma kuwa,zaman me kuke naga amarya gaya babu kayan hadi?" Kallon iman bushira tayi,ta danne dariyarta sanda iman din ta rausayar dakai,duk ta zama kalar tausayi,da alama kwata kwata lissafin yaagana baizo dai dai da kwanyarta ba a wannan lokacin,babu abunda maganar ke qara mata sai sake jefata a rudu da takeyi
"Kiyi haquri ya gana,daga gobe in sha Allah xaki fada ganin canji"
"Yauwa,so nake kowa yatabbatar yanzu zatayi aure,kuma ita din jinin kanuri ce,nan da kwanaki biyar ma idan zan tafi tasata zanyi a gaba mu wuce borno,idan hidimar ta matso ma dawo tare,saina tsumata na jiqata da kyau" miqewa kawai iman din tayi,ta kuma ja hannun bushira,saboda duk wata dauriya tata ta qare,kuka ke shirin kubce mata.
Suna shiga dakin kuwa ta saki kuka sosai,bushira ta fidda idanu tana jawota zuwa kafadarta,babu musu kuwa ta dora kanta akai
"Meye haka iman?,so kike ki tadawa mutane hankali?" Da qyar ta samu tayi controlling kanta,cikin sautin dake dauke da kuka kanta ta fara magana
"Wai me yasa bani da sa'a kwata kwata bushira?,me yasa soyayyaa take zuwa a hagunce?,cikin mummunar rashin sa'a" da sauri bushira ta dakatar da ita
"Ki gyara kalamanki iman,yanzu kuma me kikaga anyi?" Wani dunqulallen abu mai ciwo ta hadiye kafin ta iya bata amsa
"Kinga fa,wannan auren nawa sukewa murna haka?,wannan auren nawa kowa yake ciwa alwashi?,auren da har yanzu bani da tabbacin na shirya ko ban shirya ba?" Hannu bushira tasa tana goge mata hawayen,ta kuma ja tsaki
"Wannan shine tashin hankalinki?,indai shine ki kwantar da hankalinki,indai har kina yin addu'a kici gaba dayi,na tabbatar da cewa ubangiji yana tare dake,kuma yana sauraronki,hakanan bazai kunyataki ba" cikin hikima da tatausan harshe da qawar da tasan ciwon qawarta bushiran ta saukar da ita qwarai,har iman din ta shiga wanka bayan ta sanya mufida ta kawo musu abinci.
"Na jiki kina gayawa yaagana wai daga gobe zan fara gyaran jiki,toni bazan iya wannan aikin ba,hasalima bansan wajen wani gyaran jiki ba yanzu,iya mayukan da nake amfani dasu sun isheni,idan baya sona a haka har sai an masa gyaran jiki ya haqura" iman ta fada suna tsaka da cin abincin ita da bushira.
Murmushi ya kubcema bushiran
"Shikenan,saiki shirya bin yagana maiduguri ta kaiki ta killaceki" wani kallo tabi bushira dashi
"Babu inda zani,don a satin nan din ma da take zance,muna da abu mai muhimmanci cikin makaranta"
"Kinga to muyi magana,Alla yagana da gaske take,kuma matuqar taga bamu fara anan ba,babu wanda ya isa ya hanata tafiya dake,idan kinason ta barki ki yarda kawai a fara goben ta gani,idan ta tashi tafiya saiki bata uzuri,wala'alla ta yarda,idan don wajen gyaran jikine,ga AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISES" ambatar sunan ya tuna mata da wajen,ba shakka matar duniya ce wajen iya gyaran jiki,ita ganauce ba jiyau ba,hakanan ya tuna mata da lokaci irin wannan,lokacin da batajin bari,lokacin da suke kan digimi da rawar qafar aurenta da bassam,ya Allah!....kada ka kawo abunda bazai wuce ba, tafada tana lumshe idanunta,har kwanan gobe tana jin haushi da kuma zafin aurenta da bassam,inda ace tana da iko da zata dawo da rayuwarta ta baya ta shafe bassam a ciki,tunda suka rabu basu hadu ba,batasan ma wacce rayuwa yake ciki ba,bata kuma fatan haduwarsu ko jin labarin nasa,don hakan kamar famin ciwone zaiyi mata.
"Bani number dinta nayi loosing tawa tunda na canza layi,don a karan kaina ina buqatar zuwa wajen matar dama,har kema,bawai sai amare ko matan aure kawai ba,ko babu komai zaka kwaso sirrin qamshi da sirrikan gyaran jiki"
"Ni kuwa nasan da haka,ga number don bana rabo da ita,kona rasata ma ina da ita a rubuce saboda bacin rana irin haka" wayarta ta buda ta fara karanta mata number kamar haka 08067558902.
Iman din tayi serving ne kawai ba tare da tana da tabbacin cewa zata je wajen ba,duk da yadda tayi amanna da yaqinin iya gyara da kuma sirrikan qamshi masu gigita hankalin abokan zama dama oga mai gida gaba daya,amma da yaagana ta tashi tafiya ta tabbatar zata tafi da itanne kamar yadda tace,babu shiri ranar daga makaranta ta wuce wajen,sukayi total ta biyata kudaden gyaran jikin na tsahon satittikan da suka rage,tayi mata transfer take ta tura mata,rai da zuciyarta fal haushi,don tana ganin kamar asarar kudinta tayi.
Kwata kwata ko a mafarki bata kawo zancan fidda anko ba a ranta,amma saiga bushira da atamfa
"Bushira......wai meye hakan?,ko aurena na fari banyi anko ba sai yanzu?,wai da wanne irin farinjini dr ahmad yaxo muku ne?"
"Aurenki na fari daban da wannan ai,shi kuma dr ahmad ai kowa da irin nasibinsa" kai iman din ta kada ta jawo wayarta tana latsawa
"Banga amfanin yin anko ba,saboda ba taro zanyi ba ni"
"Eh ai dama iya na ran yini ne malamarsu sai walima kuma"
"Itama walimar bance ma dr zanyi ba"
"Ni na gaya masa da kaina" bushira ta bata amsa tana miqewa
"Already ma yaagana ta bada kudin an sarota,duk meso ki hadani dashi,karki damu kanki sai kin shiga harkar bikin nan" daga haka bushiran tayi gaba abunta,sai iman din ta bita da kallo,tana mamakin yadda suka daukaki lamarin gaba dayansu.
Dauke kanta tayi bayan fitar bushiran ta mayar kan wayarta tana neman number dr ahmad din,karon farko da zatayi kiranshi tsahon tarayyarsu,tana son suyi magana dashi,batason wani bidi'a ko wani abu daya danganci shagalin biki,saboda a yanzun gaba daya ba wannan bane a gabanta.
Sau wajen uku tana kira amma number taqi shiga,sai ta ajjiye wayar tabar kiran,ta miqe ta ta dauko wata qaramar hula mai santsi ta sanya a kanta,gashinta dake fake cikin ribbon ya fito ta qasan hular,baqi sidik dashi mai santsi da daukan idanu,saboda ita din ba baya bace wajen kula da gyaran kanta da jikinta gaba daya,wata irin 'yar gayu ce iman wadda bata wasa da duk wani abu daya shafi gyaran mace,kama daga turaruka mayukan da sabulai na wanka masu kyau da qamshi,don ko lalle da wuya ka dubi yatsunta ka ganshi fari babu jan lalle,dama ba kasafai ta fiya yin baqin lalle ba.
Bata tsammaci samun kowa a parlor din innar ba,saidai tana sanya qafarta dashi idanuwanta suka fara cin karo,yana zaune qasan tiles saman dardumar daya shimfida,sanye yake cikin wani lallausa yadi ruwan sararin samaniya wanda aka yiwa dinki me kyau da aji irin na matasan zamani,hannunsa dake sanye da lafiyayyen agogo na fata me tsada na kamfanin Prado yana riqe da paper da kuma biro yana ta rubutu yana kansile wani,kaya ne masu yawan gaske a tsube a tsakiyar parlor din,kama daga atamfofo laces mayafai da jakankuna.
A hankali ta janye idanunta daga kansa,ta rasa yadda zata hana kanta jin faduwar gaba duk sanda haduwar waje daya ta gamasu,dai dai lokacin da ya sanya yatsansa guda daya ya sake gyara zaman glass din fuskarsa,ya daga kansa a hankali xaiwa anty hassana matar ya muntari magana,idanunsa suka sauka a kanta sanda take takowa fuskarta na fidda murmushi,idanunta akan fuskar anty hassana
"Kai....anty yaushe kika shigo?" Iman ta fada da muryarta data zama mai wani irin sanyi
"Shigowata kenan inna tace na zauna na duba kayan nan ko akwai abunda babu a ciki,to bamu gama ba kuma sai gaki kin fito" qarasowa tayi ya zauna a hannun kujerar dake dab da anty hassana ta fara gaidata sannan ta duqa tana daukar yaronta dake saman cinyarta Tana dan masa wasa,kana cikin basarwa ta gaida ameen din ba tare data dubi sashen da yake ba.
"Lallai amarcin nan da Alama zai karbeki da kyau,irin wannan kyau haka?,amma ko wace tayi miki wannan gyaran jikin ta iya...." Kamar wanda aka fusga hankalinsa ya daga idanunsa a hankali ya sauke a fuskar iman din sanda take duban jikin nata gami da tabe baki
"Wallahi yaagana ce,haka kawai ina zaman zamana ta tattago min aiki,ko naje ayimin ko ta wuce dani maiduguri,haka ta sakani ba shiri na fidda kudina naje na biya" sauke idanunsa yayi daga kanta yana fidda wata ajiyar zuciya,ilahirin gangar jikinsa tana amsawa,sai ya ajjiye abun rubutun ya miqe yana xuba hannayensa a aljihun rigarsa
"Idan kun gama dubawa mom(haka yake kiran anty hassanan)kuyimin magana,sai aga abunda ya kamata a qara din"
"To to shikenan,ba damuwa" ta amsa masa,saiya juya a hankali yana takawa har ya fita a parlor din,abunda ya bawa iman damar sakewa ta zauna sosai sukaci gaba da hirarsu da anty hassana,harma ta manta cin abinci ne ya fiddota,bata bar wajen ba sai da antyn tayi maganar kayan lefen ameen dinnne ake hadawa,ta duba taga sunyi?.
Maida dubanta tayi ga agogo tana son hadiye da kuma basar da abinda ke taso mata,sai ta miqe tsaye
"Ba lokaci anty hassana,kema ai kinsan kan kaya sosai,munyi da me gyaran jikin nan kada nayi yamma sosai"
"To shikenan" daga haka ta samu ta wuce kitchen,ta zuba abincin ta tsaya a nan ta cusa shi,don dama ba wani abincin kirki take iya ci ba,a haka take tilasta kanta saboda gudun ulcer,don a jikinta ta fara ji kamar tana son kamata ne.
Ba lokacin tayi niyyar fita a gidan ba amma dole ta fidda kayanta don yin wanka,sai ta tuna sunyi da bushira zata zo da yammar,don haka ta qarasa wajen wayarta da niyyar kiranta kada tazo bata cimmata ba.
Envelope guda biyu dake nuna shigowar saqonni daga mabanbantan gurare cikij wayarta ne suka nuna,ta zuba musu idanu kafin ta shafa fuskar wayar ta bude ta nufi ma'adanar saqonnin nata.
[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: 60
Daya saqon daga banking da take amfani dashi ne,suka turo mata alert na shigowar kudi a wayarta naira dubu dari hudu da hamsin,mamaki sosai ya kamata,ta duba sunan wanda ya turo babu suna,pos agent ne,da alama daga wani shagon pos din kudin suka shigo,to waye zai turo mata wadan nan kudaden?,fita tayi ta buda daya saqon
*_Assalamu alaikum warahmatullah,ga saqo nan na gyaran jikine,here is my new number_*
Dr ahmad ne yazo kanta,layi ya sauya kenan,shi yasa koda ta kira kiran bai shiga,ta sanshi da busy,wala'alla wata sabgar ce ta riqeshi,saita sauka gaba daya,tayi copyiny number ta fara trying layin daya turo saqon,saidai kuma abun mamaki a kashe ta sameta,gajeran saqo kamar haka ta tura masa
*_thanks_* ta sauka ta sake kiran bushira
"Ai saidai kiyimin haquri yau amarya,wallahi umma ta aikeni gidan basira,amma zamu hadu gobe in sha Allah"
"Ba matsala,ki gaisheta" ta sauke wayar tana shiga bandakin.
Tsaf ta shirya cikin atamfa riga da skart,jikinta ba abinda yake fiddawa sai qamshin hadaddiyar humrar da turarukan jiki dana kaya da aka samar a amaryar kb global enterprises,ita kanta a karan kanta jin dadin qamshin turaruka take,abinda ya sanyata ta fara amfani da abinta kenan,ta dauko hijabinta da yasha karin guga kala da kayan jikinta ta sanya,sai tayi wani irin kyau me sanyi,kyakkyawar fuskarta ta fita ta tsakanin colour din hijabin da yayi masifar fidda kyau da haskenta wanda ya cakuda da lafiyayyen gyaran jikin da take samu daga amaryar kb global enterprises.
Tayi sallama da inna da anty hassana ta wuce zuwa farfajiyar gidan,daga can sashe daya na 'yar farfajiyar gidan nasu ta hangi malam da amin,malam din na daga tsaye,amin din ya russuna kadan da alama magana sukeyi.
Cikin girmamawa ta yiwa mallam din barka da warhaka
"Ina zuwa da yammacin nan" dan murmushi ta saka tayi qas da kanta,tanajin nauyin yi masa bayani,a jikinta takejin idanunsa na kanta
"Zanje waje me saida turare ne"
"To yayi kyau,kada kiyi dare"
"In sha Allah" ta fada tana takawa zuwa gaba a hankali ta tura qofar ta fice a gidan.
Layin nasu babu mutane sai jefi jefi,hakan baya rasa nasaba da kasancewar yammaci ce,duk da dama dai unguwar bata fiya cunkoson jama'a ba.
A hankali iska ke kada hijabin jikinta daga hagu zuwa dama,lokaci lokaci tana saka hannu tana riqeshi saboda yadda yake damunta,kwanyarta na mata tariya na da lissafin kwanakin da suka rage mata na zamantowa matar wani,sam bataji tahowar motar ba,sai uban horn da ya kusa gigitata,saitinta ya tsaya,ya sauke glass na motar,idanunsu suka hadu waje daya,ita ta fara janye idanunta kamar ko yaushe
"Tunanin me kike haka har kin fara hawa hanya baki sani ba" ya fada da muryarsa mai nauyi da kwarjini,har yanzu idanunsa na bisa kanta,amsar da zata bashi ta laluba ta rasa,ita sam banda ya fadi bata wani lura ta hau kan hanya ba,kafin ta gama qulla amsar da zata bashi,har ya bude murfin motar dake daura da ita
"Shigo muje" seat din ta kalla sannan ta kalleshi,kamar zata musa masa,amma bataga alamar wargi ko wasa saman fuskars ba,a dinke take tsaf,sai tayi taku uku ta qarasa jikin motarta saka jikinta a hankali sannan ta janye qafafunta ta maida murfin ta rufe,a hankali ya danna ya dage dukka gilasan sama,a boye ya sauke wata boyayyar ajiyar zuciya tare da qoqarin danne kanshi da zuciyarsa,wani irin qamshi jikinta ke fiddawa wanda bai taba jin qamshi me taushi irinsa ba,ya kunna ac motar ya daidaita sanyinta,sannan ya tashi motar cikin wani kasalallen tuqi suka fara tafiya.
Kamar wadda aka hana ta gaza ce masa komai,tana so ta gani ne yasan wajen da zata ko kuwa?.
Zaman kurame kawai sukeyi,zaman duka ya gundureta,gaba daya ya cikata da kwarjininsa ya cika motar gaba daya,baya ga qamshinsa da ya cika mata hanci ya haifar mata da wata irin kasala da kuma wani irin yanayi mai nauyi a zuciya.
Sannu a hankali sai gasu a amaryar kb global enterprises,mamaki ya kamata,ta dan juya kanta kadan da nufin duban sashen da yake zaune,saidai yayi mata kwarjini da yawa,ta gefan idanu dai tana iya ganin yadda ya maida hankalinsa ga gabansa,baiko juyo sashen da take ba,abinda yasa itama ta dake kenan,ta sanya hannu ta buda murfin motar ta kuma fice a hankali.
Ta mudubin gaban motar yake hangenta,tana takawa a hankali,wani irin cat walking take,wanda idan ka nutsu tsaf zaka fahimta,haka yanayin tafiyarta yake,sai ya janye idanunsa daga kanta yana gargadar kansa.
Taci sa'a ita daya take jira,don haka suna zuwa basu bata lokaci ba aka fara yi mata,tasan makamar aikinta,ba bata lokaci suka kammala,ima din tayi tsaye a gaban babban mudubin dake wajen tana kallon fuskar tata,yadda kullum take sake kyau da sheqi kamae ta jariri,ita kanta tasan gyaran yana karbarta yadda ya kamata,saidai gaba ta laluba zuciyarta kaf babu wani abu me suna farinciki ko qanqani a cikinta.
Waiwaya tayi ta miqa hannunta sanda take miqa mata wani turare da kullum take mulke jikinta dashi baya gama gyaran,ita kanta tana son turaren qwarai saboda yadda yake da wani irin sassanyan qamshi,ta karba ta zuba ta shafe jikin nata,ta maida zaman hijabinta a jikinta sukayi sallama ta fito.
Turus ta tsaya cikin madaukakin mamaki,alameen ne a booth din motar,ya harde qafafunsa waje daya,wayarsa a hannunsa,sai earpiece da ya sanya kunne daya,da alama waya yakeyi,kallo daya zaka masa ka karanci zaman bai wani dameshi ba,take zuciyarta ta shiga taraddadin ba ita ya zauna jira ba,qila wajen wani yazo.
Ta fara takawa da zummar ta wuce sai suka hada ido dashi,ya katse wayar a nutse ya zare earphones din dake kunnen nasa,sannan ya sauka daga saman motar a hankali,ya taka yana bude murafun motar,dole ta dawo ta bude ta shiga itama ta rufe murfin ya tada motar,saidai a wannan karon sauke gilasan motar yayi duka iska ta dinga shiga tana fita ba kamar wancan karon ba,a hankali yaje furzar da iska daga bakinsa,saiya qara gudun motar ba kamar daxu da suka tafi akan low speed ba.
Titi suka hau sosai,yayin da ta kama gefan mayafinta tana wasa dashi,tunani iri daban daban fal zuciyarta,ta rasa da wanne zata fara,abu daya yafi damunta zamansun tare waje daya,babu abinda ke haifar mata sai matsala daga zuciyarta zuwa gangar jikinta
"Dame dame kuka tsara zakuyi na biki?" Tambayar tazo mata a bazata,har sai data waiwaya ya dubeshi sanda yake kallon titi,ta dauke kanta tana son yiwa maganar tasa muhalli,tanajin kamar ba ita ya kamata ya yiwa wannan tambayar ba,me ya kawo tambayar gareta
"Babu abinda aka tsara" ta amsa masa kai tsaye,saboda tana ganin babu amsar data wuce haka,baice komai da ita ba yaci gaba da tuqinsa har zuwa sanda suka tsaya a qofar katafaren wani shago na saida furnitures.
Har ya gyara parking ya fito ya zagayo inda take zaune ya bude mata murfin motar tana zaune
"Bismillah" yace da ita idanunsa nakan shagon,sai kuma ya fara takawa zuwa gaba a hankali,bata da wani zabi illa fitowar,duk da batasan me ya kawosu wajen ba.
Bata fuskanta ba kuwa saida suka shiga cikin babban store din,ya sadiqu ta samu a tsaye a ciki shida anty hassana
"Wayarki saura kadan ta zama mara amfani,ayita kira bakya dagawa" ya sadiqu ya fada cikin mita,dai dai sanda alameen yayi zaune kan wata kujera dake wajen,ya kuma ci gaba da amsa wayarsa,wayar data dinga ji cikin jikinta kamar da samha yake.
"Banji ba wallahi yaya" ta fada tana kiciniyar ciro wayar daga jaka
"Kinga yanzu ba wannan ba,ki zagaya ki zabi kalar furniture din da kikeso,dare yana qara yi,anty na sauri zata koma gida"
Kamar wadda aka bugewa qafafu sai ta koma ta zauna kan daya daga cikin kujerun dake wajen
"Ya ana magana kika koma kika zauna?" Kai ta girgiza,bata jin zata iya aiwatar da komai a yadda takejin jikinta,ta lura ba iya bushira da yaagana suka daukaki abun ba,kusan kowa ma hakane,kamar dama sun gaji da zamanta,har yanxu bata rufa shekaru biyar a gabansu ba,hakanan duka duka har yanzu shekarun haihuwarta basu wuce ashirin da uku cikin da hudu ba
"Ya sadiqu,ga anty sannan kuma ace da kaina zan zaba kaya?,don Allah kayi haquri bazan iya ba wallahi" ta qarashe maganar tana jin wani weakness yana ratsata
"Kaga sadiqu muje,mu zaki tsaya yiwa fulako" cewar anty hassana tana jifanta da harara wasa,qas tayi da kanta itadai,batasan yadda al'amarin ya kaya ba,illa dai tasan bayan tsahon wasu mintuna anty ta qaraso wajen tana ta sumbatun kayan,da kuma kudin daka kashe wajen siyansu,suna daga motar taga fitowar ameen daga shagon hannunsa dauke da receipt,bata iya qara cewa komai ba har suka sauke anty hassana su kuma suka dunguma gida.[7/19, 10:03 PM] Mummyn Yara: "




Menu
Dashboard
My Library
Create Story
Home
About us
FAQ's
Privacy Policy
Terms of service
Logout

KUFAN WUTA